[19/04 15:19] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Ƙirƙiraren labari ne,ban yi shi don cin mutumci kowa ba.Duk wanda ya zo daidai da rayuwarsa to akasi aka samu. 1 #ƘASAR COTE D'IVOIRE #Babbar asibitin Abengourou A tsorace nake ƙara tushe kunnuwana ko zan samu sa'ar toshe ma'adanar sautina da ke zuƙo min wata murya mai cike da tashin hankali.Sai dai yaudarar kaina nake,domin kuwa toshe kunnen da na yi hakan bai canza zane ba .Na kai hannu da niyyar ɗaukar pilow ko shi Allah zai sa na dace,hasken ɗakin ne ya ɗauke ɗif wanda ya yi sanadiyar tsayawar na'urar da ke kore zafi. Ƙaiƙayi na fara ji yayin da sauro da zafi suka ce salama alaikum,shegiyar muryar nan mai shegen naci sai ƙara ƙaimi take wurin roƙon abin da ban san mi take so ba “ku cece ni ! Ku cece ni don Allah babu kowa ne?” Na ja tsuki bisanin na lalubo wayata na kunna fitila,duk abokan aikina baccinsu kawai suke a gajiye.Na miƙe tare da nufar ƙofa,na murɗa handle na fito ,ga mamakina ko ina na asibitin akwai hasken wuta sai ɗakinmu da kuma wani ɗakin da ke can gabashi wanda akwai ƴar tazara tsakani. Haka kawai na ji zuciyata na tunzura ni kan na je na duba tako ɗaya ,biyu,ina daɗa matsawa ina kuma daɗa jin sautin muryar nan mai neman taimako har na isa bakin ƙofar daidai nan hasken ɗakin ya dawo.Na kutsa kai,sai na tarar da nurse biyu da wani Dr a tsaye kan wata matashiyar budurwa ,gefe kuma wata jemamiyar tsohuwa ce zaune ta na kaɗa ƙafa. Duk kallonsu ya dawo kaina,ni ma su nake kallo ɗin. “Ayodele mi kike yi a nan? Babu aiki ne ɓangaren ku?” Dr ya tambaye ni,na buɗa baki da niyyar yin magana na tsinkayo wata murya kuma na ce min “Ayodele please ki taimaka min ban mutu ba!” Inda sautin ya fito na duba,sai yanzu na lura da idon budurwar rufe suke ruf kamar mai yin bacci.Da mamaki nake tambayar kaina ‘dama mai bacci ya na iya yin magana?’ “Ta rasu ne! Ƙoƙarin cire duk abubuwan da ke jikinta ne muke amma sun ƙi fita” Dr ya katse min tunani. “Amma yanzun nan fa ta min magana akan na taimaketa ba ta mutu ba” na faɗa . Duk kallon mamaki suka bi ni da shi,hakan yasa na ci gaba da cewa “tun ɗazu fa ita ta hana ni bacci kururuwar ta ce ta tashe ni” “Ayodeleee?” Dr ya kira ni da wani sauti,bisanin ya tambayi nurse ɗin “ku tun ɗazu da muke nan kun ji kururuwar ne?” duk kai suka girgiza alamun a'a. Sai ya maido kallonsa gare ni “to kin ji ta yiyu kunnuwanki ne ba su jiye miki daidai ba” “Mi sunanta?” ita ce tambayar da na yi,“Emeka” ɗaya daga cikin nurse ɗin ta ban amsa. A hankali na fara taka ƙafata sai dai kafin na isa ga Emekar tsohuwar nan ta taso tare da tsaya wa a gabana “ina za ki je? Mi za ki yi?” ta jero min tambayoyi haɗi da jifata da wani mugun kallo mai ratsa ɓargo da tsoka don sam bai da daɗi. Dakyar na fizgo numfashi tare da jarumtar kallonta cikin tsakiyar ido ,kawai sai na ga mugun razani a nata idon tare kuma da saurin ja ta bani wuri ba tare da na san dalilin yin haka ba. Kai ga Emeka na yi tsaye bisanin na kai hannu kan fuskarta na ce “Emeka ?” “Ayodele ta fa mutu,ya kike yi wa matatta magana kamar zautatta?” Dr ya tari numfashina.Ba tare da na dube shi ba na ce “ba ta mutu ba Dr ! Doguwar suma aka sa ta” “Wa ya sa ta doguwar suma? Nan fa asibiti ce kuma mun san aikinmu ” “Dr ita wacce ta saka ta suman ta san kan ta! Ina iyayenta suke?” na tambaya. “Daga ita sai Kakarta suka zo,kuma ga ta can ta fita” cewar nurse. Na ɗago kaina sai na ga tuni tsohuwar nan ba ta nan,wato abin da na fahimta ita ce Kakar Emeka. “Ayodele ki taimaka ki damƙa ni ga iyayena Kakata ba ta sona shi ne take son kashe ni,ta ɓoye ruhina cikin asusun ƙarfe ta lashi takobi ba za ta fiddo shi ba har abada” shiru na yi ina sauraren esprit ɗin Emeka da ke yi min magana ba tare da ni kaina na san shi ne ba. “Dr yanzu ma ba ga shi ta na yin magana ba?” “Mtsw! Ayodele fita! Fita na ce !” Dr ya yi min wata muguwar tsawa. Tako ɗaya na yi na tsaya,cikin fushi ya kuma cewa “kenan ba za ki fita ɗin ba?” Murya a raunane na ce “ba ka ga ta riƙe min hannu ba ne?” Duk ido suka waro Dr har da ɗora hannu a kai ya ce “wai Ayodele haukata ni kike son yi? Ku kun ga ta riƙe ta?” ya tambayi nurse suka girgiza kai. Da mamaki nake kallonsu bisanin na mayar da dubana ga Emeka wacce ta riƙe ni gam ta na girgiza kai idonta na shatatar da hawaye. “Ke kaɗai ke jin abin da nake cewa da kuma ganin abin da nake don Allah kar ki biye su” cewar Emeka . Cikin jin haushi Dr ya fizgo hannuna da niyyar fitar da ni da ƙarfin tsiya sai dai sam ya kasa sakamakon ɗayan hannun da ke riƙe da Emeka . “Dr ni fa na fara jin tsoro! Ina ga fa gaskiya ne! Dubi yadda hannunta ke jone kamar a rinƙe shi ɗin kuma ....kuma gadon kamar ya na motsa wa” nurse ta faɗa. Dr ya sake min hannu,ya ce “ba zan yi mamaki ba don Abeno cike take da ƴaƴan matsafa da Mayu....” bai rufe bakinsa ba Emeka ta fara shaƙuwa,da sauri duk suka nufeta tare da saita na'urar aiki a kanta. Ni kuwa ganin numfashinta ya dawo kawai sai na sulale na koma can ɓangaren mu.Kasa bacci na yi sai zaune da na yi na rabka uban tagumi ina tunanin abin da ya faru.Gadon bayana ne ya fara yin ƙaiƙayi,tare kuma da wata irin tsira wa tamkar ana nitsa wasu abubuwa gefe da gefen kafaɗuna. Dishi-dishi idona ya fara,ban san ya aka yi ba na tsinci kaina a wata duniya wacce na fi kyautata zaton ta mafarki ce. Wani ƙaton gida mai ɗauke da ɗakuna kashi-kashi,ruhina ya sallama.Babu wanda ya amsa min haka ba wanda ya ɗago ya dube ni sai tsohuwa wacce tun farkon shigowata na ji yaran gidan na ambaton sunanta da “Yaba” Mugun kallon nan mai cike da hassada,ƙyashi haɗi da baƙin ciki ta jefo min bisanin ta miƙe tsaye ta zo gare ni.“Mi kike so kuma yanzu?” “Abin da kika ɓoye!” na bata amsa. “Maganar ahali ce wannan bai shafe ki ba,kin dai yi naki ikon don haka ki....” ban bari ta dire ba na tari numfashinta da “ki bani cikin lumana ko kuma na ƙwata ta ƙarfin tsiya! Yin haka kuma babba asara ce gare ki domin duk abin da kika ɓoye zan fito da su ne” Tsoro ne na gani shimfiɗe ƙarara a fuskar Yaba,bisanin ta yi gaba ni kuma na take mata baya har cikin ɗakinta na laka wanda aka yi ma rufin kara. Ƙarƙashin gado ta duƙa ta fito da wani asusun ƙarfe tare da miƙo min shi,ban ɗauki lokaci ba wurin buɗe shi.Baƙin hayaƙi ya fito kamar fitar iska ya tashi sama,guntun ƙyallen atamfa na gani sai na ɗauke shi bisanin na aje asusun na fito. Daidai nan kuma na farka daga baccina,na dafe gefen goshina da yake sara min bisanin na buɗe idona taram .Da sauri na tashi ganin Emeka a tsaye ta na min murmushi. “Na gode sosai Ayodele,kin ceci rayuwata!” ta faɗa tare da ƙoƙarin karɓa wani abu daga hannuna da nake jin na jimƙe ba tare da na san mine ne ba sai da na kai dubana sai na ga ƙiren atamfar da na yi mafarki ne. Emeka ta ci gaba da cewa “wannan zanen ankon bikina ce,Inna Yaba ta yi amfani da shi don kashe ni saboda kawai zan auri bare wanda ba cikin danginmu ba.Na gode!” ta na gama faɗar haka ta fice ta bar ni sake da baki ina tunanin kar dai ace mafarkin da na yi gaskiya ne? ?????? [19/04 15:23] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* 2 Har aka fara kiran asallatu ban rumtsa ba,ina ta saƙa da warwara don gano ainahin abin da ke faruwa da ni sai dai ga banza wai an tsikari kakkausa. Ƙarfe biyar na asubahi abokan aikina suka tashi don gabatar da sallah.Har suka ida ina nan zaune ina reto da ƙafafuna, A'ishah ta dube ni cike da kulawa ta ce “Ayodele lafiyar ki kuwa?” “Ƙalau nake!” na bata amsa. “Mi ya samu fuskar ki duk ta yi ja?” ta sake tambayata,ban bata amsa ba sai wata nauyayyar ajiyar zuciya da na sauke. Fatima da ke jan casbi kusa da ita ta ce “ƙila mafarkin da ta saba yi ne yau ma ya sake zuwar mata” Na ɗan harareta na ce “don ban da aikin yi sai mafarkin ɓoyayyen masoyi ko?” duk suka yi dariya bisanin A'ishah ta ce “Ya kamata dai ki tashi ki wanke fuskar ki tun da ba sallah za ki yi ba” Na dube ta na ce “lokacin da nake tawa ibadar ki na ina ne?” Ta taɓe baki ta ce “ibadar da kike yi marar alƙibila? Ke fa kan ki ba ki san wane ne kike bauta ma ba” “Ubangiji nake bauta! Kuma na yi imani da shi,kamar yadda kuke bautar naku da ba ku taɓa gani ba” na bata amsa. Fatima ta ce “don Allah ku bar zancen Addini! Mu je mu ida aikinmu mu kama gabanmu” Hakan kuwa aka yi,bayan na wanke fuskata mu ka shiga fara duba maras lafiya ƙarfe tara na buga wa duk mu ka sauka daga aiki. Kasancewar banda abun hawa yasa na zo bakin titi,dakyar na samu taxi ita ma wata tsohuwa ce.Gidan baya na zauna,mutum uku na taras a ciki hakan yasa duk mu ka matse. “Mtsw ! ” ta kusa da ni ta ja tsaki a karo na uku,na kasa haƙuri na ce “ya dai?” Kamar jira take in tanka ta ce “ah toh! Gari yanzu ya lalace ko ina ka je sai ka ji ana zancen Mayu ! Abun baƙin ciki har da yara ƙanana suke kama wa” Ni kuwa na ce “kuma wallahi in kika bincika kaso casa'in na Mayun garin nan tsofi ne....” ban rufe baki ba motar ta yi wani ƙuuu! Ta tsaya. “To shikenan kun yi sara da mutum sama sai ku fito!” shi ne abin da mai taxi ɗin ya faɗa ya na mai jan tsuki,sai kuma ya fita. Ƴan dube-dube ya yi bisanin ya umarci kowa ya fito,duk mu ka sauka sai wani tsoho da ke gaba mai cin goro bakinsa duk yayi ja. “Ka yi haƙuri ba su san da kai ciki ba ne shi yasa har suka tsokane ka” mai taxi ya faɗa cikin wata irin murya mai rauni. Kamar wani sarki tsohon nan ya fito tare da tsirtar da yawu abun mamaki sai suka zuba ga jikina da kuma na matar da muke hirar. Dariyar shaƙiyanci ya fara bisanin ya ce “halan ku baƙi ne a Abengourou? Na ce ku baƙi ne?” kamar wasu ƴaƴansa haka yake mana ihu,tuni wannan matar ta zube ƙasa ta na basa haƙuri. Raina ne na ji ya ƙara ɓaci,zuciyata ta kawo min wuya.Ban san mi ya shiga kaina ba kawai dai na samu bakina da furta “dara ta ci gida !” sai tsohon ya ɗago da ƙarfi ya na kallona,jikinsa har rawa yake wurin ƙetara wa bakin kwalta ya karɓo ruwan leda ya zo ya fara wanke daidai inda ya tsirta min yawunsa masu ɗauke da jan goro. Na lumshe ido ina jin zuciyata na ɗan doka wa tare da ƙoƙarin yaƙarta akan tafarfasa da take. Cikin taxi mu ka koma don kuwa ta tashi,fafur tsohon nan ya ƙi shiga direba sai magiya yake. Har za mu tafi na ce “ita kuma wannan da ka riƙe?” Jikinsa na rawa ya ɓallo goro ya bata,na dubeta na yi mata alama da ta karɓa hannunta na rawa ta amsa tare da kai goron baki,mai taxi yayi mata key. Mun ɗan tafi kaɗan matar ta fara aman baƙin wani abu kamar ranta zai fita,a dole duk mu ka sauka daga taxi ɗin na tari wata sai gida. “Washhh! Na gaji” shi ne abin da na furta ina mai zube wa kan tabarmar kaba wacce Momah ke zaune ta na gyaran wake. Wani kallo take bi na da shi wanda yasa na tsargu na ce “Momah ya dai ?” Sai ta ja wata doguwar ajiyar zuciya ta ce “wa kika tsokana a saman hanya?” “Da aka yi mi fa?” na tambayeta. “Idon ki na ga sun canza launi” ta ban amsa. Na yi ƴar dariya tare da canza zancen “babu ruwan ƙanƙara masu sanyi?” “Babu sai dai ki sha na tulu,ɗiyar Asabe ta rasu duk can aka saye ƙanƙarar ” “Wace daga ciki?” “Zeinab mana! Ai kin san dama ta jima babu lafiya” Na dafe ƙirji na ce “tun yaushe a ba ta da lafiya? Ban sani ba” “Eh to ba a fi sati ba! Don a gida aka yi jinyar ta ba kowa ya san da rashin lafiyar ba” Jiki babu ƙwari na miƙe don sosai mutuwar ta dake ni a kaf faɗin unguwarmu gidansu kawai nake shiga.Ina tafiya sai na ji kamar ana take min baya na waigo sai dai ban ga kowa ba.Ɗaki na shiga na cire kaya,ɗaurin ƙirji na yi na fito na yi wanka. Bayan na gama na zuba kunu a roba na fara sha kenan wayata ta ɗau ringing,na ɗauka ban kai ga magana ba na ji muryar A'ishah na ce min “Albishirin ki?An kawo kuɗin aurena yanzu haka har an tsayar da ranar buki?” cike da murna na shiga tambayarta “da gaske? A'isha kar fa a ce ƙarya kike min” “Allah gaske ne! Ki zo Please ” Na ja dogon numfashi na ce “sai dai zuwa gobe tun da yau akwai inda zan je” “Ke dalla wacce magana kuma kike? Ko ma ina za ki je ki jingine tafiyar kawai ki zo nan kin ga fa Fatimah nan” Jin haka yasa na ce “ok gani nan zuwa!” sai ta kashe ,ni kuma na miƙe na je na saka kaya ko mai ban shafa ba na fito na sanar da Momah. “Masha Allah! Ki dai dawo da wuri kin ga zan shiga gidan mutuwa zuwa biyar na marice” “To Momah!” na amsa tare da fitowa waje.Cak na tsaya ina kallon yadda unguwar ta ɗauki wani duhu har wani hayaƙi ke tashi.Cike da mamaki sai na ga na ƙofar gidansu Zeinab ya fi yawa,a fili na furta “to! Mi kuma ke faruwa?” kiran A'ishah da ya shigo shi yasa na watsar na nufi bakin titi na samu abun hawa sai gidansu. Ai kuwa gaskiya ne an kawo lefen ,ina shiga na ta gani mutane masu zuwa yin barka.Bayan na gaishe da Mamarta na wuce ɗakinta,nan mu ka ta yin ihun murna tare da tsara yadda bikin zai kasance.Bayan mun ci abinci ne na yi tambaya “ A'isha wai wane ne za ki aura?” “Cousin ɗina ne! Dama kin san tun farko ya nuna ya na sona sai kuma abun ya watse tun da ya tafi Lagos to ya dawo shi ne fa aka kawo lefe” ta ban amsa cike da murna. “Aikin mi yake na ga lefen Masha Allah kamar matar gwamna” cewar Fatimah,na karɓe zancen da “ai kuwa dai! Ko bra da pant kawai abun kallo ne uwa uba sarƙoƙin da na gani har da na zinare” “Na faɗa maku Lagos ya je wurin diga ya samo kuɗi sosai yanzu haka ya fara kasuwanci!” A'ishah ta faɗa . “Fatimah saura ke! Ki cewa Nasir ya fito kawai mu sha biki!” na faɗa cikin zolaya,ta kai min dundu a baya ta ce “ Allah kiyaye min ni Dr nake so” Duk muka fiddo ido waje , A'ishah ta ce “wannan masifaffen? Tabbb! Ayodele kin san kuwa ɗazu da na wuce ta gaban su na ji ya na bai wa Dr Jameela labarin ki wai kin ceci wata su sun yi zaton ta mutu” Wani irin ras na ji,yayin da kaina ya sara kamar zai tsage.Ba don ace na yi ƙarya ba da zan iya cewa har mahudanar jinina ta sauya tsarin gudu. Dakyar na iya cewa “bacci ma nake ji bari na kwanta kafin a jima na tafi gida” “Munafuka yanzu da kika ga lokacin sallah yayi ko?” Na dubi Fatimah da idona da nake jin tamkar ana yi min masanye bisanin na lumshe su ba tare da na bata amsa ba.Ina jin lokacin da ta ci gaba da cewa “ A'isha ni kuwa lamarin Ayodele na ban tsoro idonta wani sa'in sai su koma kamar na damusa ” Duniyar da na lula wacce take kusan zahiri ba mafarki ba yasa ban sake jin hirarsu ba. Ranar da Momah ta zo min da zancen za mu tashi daga unguwar da muke zuwa wannan da muke ciki,ba zan manta a ranar da mu ka dira sai da na kwana da ciwo ƙafa mai tsanani.Maƙociyarmu Asabe ce take shaida mana unguwar Mayu sun yawaita duk da har yanzu ba a san su wane ne ba amma mu tashi tsaye wurin addu'o'i.Na sha daga bisanin na warke,abu guda da kuma ba zan manta ba kusan tsofin unguwarmu ba na shiri da su. A cikin baccin nan na ja wata ajiyar zuciya ganin Zeinab ta nufo ni idonta shaɓe-shaɓe da hawaye,bayanta kuma tsofin unguwarmu ne ke biye da ita ko wacce daga cikinsu da wuƙa a hannunta. “Ayodele? Ayodele? Lafiyar ki?” na ji muryar A'ishah wacce ta tashe ni daga bacci,na buɗe ido dakyar bisanin na lumshe su Zeinab ta sake bayyana gare ni sai dai nacin A'ishah ya saka na tashi daga baccin ba don na so ba. “Haba sai ki tsora mutum! Haka kike bacci dama? Ninshari ne wannan kamar kururuwar damusa a cikin daji” ta faɗi haka ta na mai kallona. “Ina Fatimah ?” shi ne abin da na tambaye ta. “Ta tafi gida mana,tashi mu je don Allah ki yi min rakiya daga can sai mu wuce gidan ku” . Toilet na shiga na wanke fuskata sannan muka wuce gun tela,bayan sun gama tattauna komai muka samu taxi zuwa gidanmu. Rana tsaka ne wantsar,duk an yi gudu ba za a wuce ƙarfe uku ba. “Ayodele sallar gawa ce ake yi wai ” cewar A'isha don ta riga ni fita daga taxi,na ziro ƙafata kenan idona yayi tozali da gawar Zeinab wacce maza suka sa a gaba su na sallata. Gadan-gadan na nufe wurin, A'ishah ta riƙe hannuna daga baya ta na cewa “ina za ki kuma?” na fizge hannuna na je na yi tsaye kusa da makara ina mai ɗaga hannu na ce “ku dakata! Ba ta mutu ba ga ta a zaune ta na faman kuka” Farin likafanin da aka rufeta na yaye daidai fuskarta,ni kaina ban san mine ne na faɗa ba ko kuma na yi sai Zeinab ta tashi zaune daram da ƙugunta “Allahu Akbar! Allahu Akbar! Allahu Akbar!” maza suka fara yin kabbara kafin wani lokaci har labari ya kai cikin gida. Sam ban ga tawowar Momah ba sai ganinta na yi a gabana cikin ɓacin rai ta fizgo ni mu ka fito dandazon jama'a,ƙiiii take ja na zuwa gidanmu har mu ka shiga. Daidai tsakiyar gida ta wani tura ni na faɗi ƙasa,cikin ɓacin rai take cewa “wannan wace irin masifa ce? Gadon tsiya,gadon jaraba! Ayodeleeee!” sai kuma ta yi shiru ta na mai dafe saitin zuciyarta,da azama na miƙe ina mai tare ta don kar ta faɗi sai inaaaa tuni Momah ta rinjaye ni ta faɗi ƙasa warwas.... [24/04 14:49] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* 3 Cike da tashin hankali na fara jijiga Momah haɗi da kiran sunanta sai dai ko motsi ba ta yi ba.Idona tuni sun fara zubar da hawaye,na ruga a guje na nufi hanyar fita sai mu ka yi kiciɓis ni da A'ishah.Ita ta fara yin magana ta na cewa “Ayodele yarinyar nan fa an wuce da ita asibiti sai wani shure-shure take ta na kiran sunan ki” “Momah na ciki ta kasa tashi mu je ki taimaka min” na faɗa ina goge fuska da bayan hannu.Ciki mu ka koma , A'ishah ce ta yi azancin zuba wa Momah ruwan tulu masu masifar sanyi.Momoh ta ja ajiyar zuciya,idonta a rufe take yin wani Yare wanda ba Hausa ba haka ba French ba ne. Mu ka kalli juna ni da A'ishah,ban sani ba ko ita ma tunaninmu ya zo ɗaya wato Momah ko aljanu gare ta? Ciwon kai mai tsanani da ya fara farmakata ya addabe ni a lokaci guda na nemi wurin da zan kwanta don idona tuni sun fara lumshewa. A'isha ta riƙe ni ta na cewa “ina kuma za ki je alhalin mahaifiyar ki na cikin wannan hali?” ban bata amsa ba kawai da na janye hannuna tare da samun wuri na kwanta kan tabarma. Momah ta dawo daidai, A'ishah ta ce “ya jikin?” “Alhamdullah! Kin ga abin da ƙawar ki ta jindilo mini ko? Wancan baccin da take Allah kawai yasa masifar da zai haifar ” ba tare da A'isha ta san taƙamaimai abin da Momah ke nufi ba ta kalli inda Ayodele ke kwance har wani girgiza take ta na motsa baki kamar mai yin magana.Ba don ta so ba haka ta yi wa Momah sallama ta yi tafiyarta. Kwanta wa ta ke da wuya,wani hazo ya rufen ido.Tsofi huɗu na yi tozali da su ,dukkansu na san su zan iya shaida su duk da ban san gidajensu ba amma ina ganinsu a unguwa. “Mu za ki tona wa asiri? ” “Mine ne ruwan ki da mu?” “Ita Zeinab ɗin ƙanwar uwar ki ce?” “Ya kuke ɓata lokaci wurin tambayarta? Kawai mu shaƙe shegiya mu kashe ta” Kowacce daga cikin ta faɗa,ta ƙarshen abin da na lura ta na da zafi kuma tsafin maitarta ya fi na kowa ƙarfi shi yasa har take tunanin za ta iya ja da ni. “Ban zo nan don na haɗu da ku ba ku dinga kawo min shirme,ruhin Zeinab nake so ku saki cikin salama kafin na ƙwata ta ƙarfi.Dukkanin ku babu wacce ban san sirrin maitar ta ba,in kuka cika ni zan rusar daular ku” na faɗa cikin kakkausar murya,duk sai suka sheƙe da dariya. “Ke kuwa baiwar Allah miye na gudun ƴan uwanki Mayu?” “Hhhh! To wai mine yasa kika karɓi maita in kin san ba mugunta ne burin ki ba?” “Sannu mai son taimako al'umma,mu je mu yi farauta ke kuma ki zo ki karɓe.Kin san tun yaushe muke son naman Zeinab ? Tun ta na cikin tsumman goyo muke haƙonta sai yanzu da za mu sha romo za ki hana?” Idona ne suka fara yin zafi,a take na ji wani abu na cika su.Na zube su kan tsofin Mayun nan,duk sai na ga sun razana a take su ma suka faɗi wani ɗalasiman tsafi nan take suka rikiɗa suka zama macizai. Ko kaɗan ban son kashe rai,sai dai ɗaya daga cikinsu ta ja masu mutuwar kasko sakamakon shammata ta da ta yi ta cije ni a hannu.Bakina na buɗe na saki ihun azaba yayin da kuma idona ya fitar da wani tartatsin wuta duk sukama wuta su na ihu. Na ja wani dogon numfashi ina mai buɗe idona taram kan Momah wacce ke ta ƙoƙarin ɗaure min hannu da ƙyalle jini sai zuba yake. Mafarkin da na yi ne a yanzu ya dawo min tarau a kwanya,abin da na fahimta kawai ba irin sauran mafarkai ba ne da duk ƴan Adam ke yi nawa ya sha banban. “Tashi mu je na kai ki asibiti,jinin nan ba zai tsaya ba” cewar Momah ,ban tambaye ta komai ba na tashi.Takalmi kawai na saka a ƙafata muka fito waje,unguwar cike take da jama'a kowa mamaki shimfiɗe kan fuskarsa yayin da yake kallon makiran tsofin nan huɗu su na birgima a ƙasa tare da tona ma kansu asiri.Duk wanda suka taɓa kamawa sai da suka faɗa hatta Zeinab. Da sauri Momah ta ja hannuna muka bar wurin,taxi muka tara sai asibiti.“Mine ne ya same ta ?” cewar likita ,da mamaki na dubi Momah jin ta ce “sarar maciji ne” ‘To ta ya aka yi ta sani?’ na tambayi kaina a zuci. Allura yayi min tare da bani wasu magunguna , Momah ta biyasa bisanin mu fito. Tafiyar ƙasa kawai muke ta yi,sam ban ga alamun Momah na da niyyar tarar mana da abun hawa ba ga shi kuma na gaji. “Hum!” ta yi tare da dubana,na dube ta kawai.Sai kuma ta ja ta tsaya,bisanin ta ja ni zuwa gefe “zauna” ta faɗa tare da nuna min dakali.Na bi umarninta,wata tambaya ta jefo min da ban fahimce ta ba “mine ne haɗin ki da tsofin unguwa uhum? Duk yadda nake son liƙe ƙofofin nan sai da kika bi duk kika buɗe su ko? Ayodele rayuwar da kike so mu yi kenan kullum cikin sauya unguwa da ƙasashe?” “Momah ban fahimce ki ba...” ko rufe bakina ban yi ba ta zuba min yatsunta biyar bisanin ta yi zaman ƴan bori a ƙasa ta fashe da kuka.Na rumtse ido don sam ban son ganin zubar hawayenta ko ba komai ita ce gatana,ban san kowa ba daga ahalina sai ita kaɗai. Furucinta ya saka na ware idona kanta,“Ayodele ina roƙon ki daga yau kar ki sake shiga sabgar wani maye ko mayya,babu ruwan ki da su.Ki barsu su yi rayuwarsu,abu ɗaya na sani har abada babu wani daga cikinsu da zai samu zarrar kashe ki wannan ma da aka yi cikin rashin sanin ke wace ce suka yi miki illa” Bakina na samu da tambayarta “Momah wace ce ni ?” Ta min wani kallo bisanin ta miƙe ta kakaɓe jikinta,“tashi mu tafi ” ta umarce ni a doli na tashi ɗin.Sai a lokacin ta nema mana abun hawa muka isa gida,da labarin mutuwar tsofin nan huɗu muka ci karo yayin da Zeinab kuwa tuni ta samu lafiya ta dawo ras. A ranar nan ko abincin dare kasa ci na yi,magani kawai na kora da farau-farau sannan na kwanta bacci.Nan na yi mafarkin wani farin tsoho jawur da shi ya bayyana gare ni,bandejin da aka laulaya min a hannu ya warware bisanin ya saka min wasu ruwa masu masifar sanyi sai kuma yayi tafiyarsa. Washegari ko da na tashi hannuna ya warke kamar ma ban taɓa jin ciwo ba,cike da mamaki na fara ƙwala kiran sunan Momah ina mai fitowa waje “Momah dubi hannuna ya warke ” maimakon ta yi murna akasin haka na gani.Cikin tashin hankali take cewa “shikenan ashe su na biye da mu” “Su wa?” na jefo mata tambaya,“je ki yi wanka lokacin zuwa aiki ya kusa” Na turo baki cike da jin haushi,na cika bokiti na je na yi wanka.Bayan na shirya ne na lumshe idona,na fara yi wa abun bauta godiya kan lafiyar da ya bani bisanin na fito hannuna ɗauke da jaka. “Momah na tafi sai na dawo” “A dawo lafiya” shi ne abin da ta ce min. Sai da ina cikin taxi ne na fara duba wayata ,nan na ci karo da miss call ɗin A'isha da Fatima .Na saki murmushi,har cikin zuciyata nake son ƙawayena. A bakin asibiti na ci karo da su kamar kullum,Fatima na da babur ita ke ɗauko A'ishah tun da kusan unguwarsu ɗaya. Gaisa wa muka yi, A'ishah ta so yi min zancen abin da ya faru jiya sai dai ban bata fuska ba. Ta sauka daga mashin muka ƙarasa ciki,uwanda suka kwana nan suka sauka mu kuma mu ka hau aiki bayan mun ci abinci. Lokacin hutu mu na zaune ana hira A'ishah ta ce “Mansur ya matsa akan lalle aurenmu nan da 2weeks yake son shi,da Mama ta so masa bayanin kan lokacin ba ta gama haɗa min kayan ɗaki ba ya ce babu damuwa duk shi zai yi burinsa kawai a aura masa ni ” “Wayyo! Kin ji daɗin ki wallahi ina ma ace ni ce .Ya kamata mu je mu fitar da anko gobe in mun sauka daga aiki” cewar Fatimah. “Eh dama hakan na raina” hira sosai suke su biyu kamar sun manta da ni,don ko kaɗan ni ban da bakina ba saboda haka kawai na ji na tsani lamarin auren nan da ace ina da iko da babu shakka na hana shi. “Kin yi shiru tun ɗazu halan masoyin ɓoye ake tunani?” A'ishah ta tambaye ni cikin zolaya,na ɗan taɓe baki bisanin na miƙe na ce “ku dai tashi mu koma saura minti biyar” duk suka miƙe,nan mu ka ƙara hawa aiki sai lokacin sallah kawai suke tsayawa su yi ni kuwa da ban san taƙamaimai Addinina ba sai dai na zauna. Zuwa ƙarfe takwas na dare duk mun gaji saboda aikin likitanci sai jajirtace.Ɗakin baccinmu duk muka nufa,mu ka bar stagiaire irin sabbin likitocin da ake kawo wa asibitoci don koyon aiki sai in matsala ta yi tsanani ne sosai suke tayar da mu. A gajiya duk muka ɓingire bacci,babu ma kamar ni da nake jin kamar an min shegen duka. Ƙyalƙyal! Haka nake jin sautin dariya na ƙara yawaita,y wasu muryoyi ke tashi sama yayin da kuma shashekar kuka ke ƙara ƙaimi. Ba tare da na buɗe idona ba na tashi zaune,bisanin kuma na sauko daga bed.Ban buɗe ƙofa ba ita ta buɗe da kanta,wani haske ke yi min jagora ni kuma ina biye da shi kamar raƙumi da akala har na isa wani ɗaki. Tsit suka yi,sai wata murya da ke tambayar “wane ne? Ba za ka yi magana ba? Ka bar haske mu ” daidai nan hasken da ke min jagora ya ɓace hakan ya basu damar ganina mu ka yi gaba da gaba. “Kayiii! Mace a wannan lokacin? ” tako ɗaya na ƙara duk suka ja baya tare da ɓoye wa ƙarƙashin gadajen maras lafiya aka bar mai yi min magana. Abu guda na yi nasarar gane wa,shi a siffar mutum yake yayin da sauran kuma innuwarsu kawai ake gani. “Su wane ne ka gayyato mana a nan ana zaman lafiya?” na jefo masa tambayar . Muryarsa na ɗan rawa ya ce “abokaina ne! Umm.Sun zo ganina ne” Sai a yanzu na ƙare masa kallo,hannunsa na ɗauke da tiyon da ake yi wa mutum ƙarin ruwa. “Don sun zo ganin ka shi ne za su hana mutane bacci? Ce maku aka yi nan gidan caca ne? ” na sake faɗa cikin tsawa. Shiru ya ɗan yi bisanin ya ce “madam ke ɗaya ce kawai kika ji mu,amma normal mutum basa ji ” “Ka sallame su maza kar na sake ganinsu a nan har lokacin da za ka bar asibitin nan in kuma ba haka ba zan yi mugun saɓa maku” ko gama rufe baki ban yi ba ya ce “an gama ranki ya daɗe!” Har na juya zan koma sai kuma na tsaya tare da jefo masa tambaya “shashekar kukan wa nake ji a ɗazu?” Kame-kame ya fara,can cikin ikon Allah idona ya sauka kan wani ɗan yaro da ke kwance kan gado.Esprit ɗinsa na gani a ɗaure ana tsoratar da shi haka kawai,“wane ne yayi masa haka?” na yi tambayar tare da shaƙe mutumen wanda aƙalla zai kai shekar sittin . Cikin magagin wahala ya ce “abokina ne! Wallahi sai da na hana shi amma ya ƙiya” Yadda yake magana zan iya hangen wani koren abu daga cikin bakinsa,ban san da me na yi amfani ba na ciro shi daga bakinsa bisanin na je na saki yaron nan da suke cutar wa sai kuma na koma ɗaki. Ina kwanciya kan bed sai na ji nutsuwata ta dawo daidai saɓanin a ɗazu da nake jin kamar mu biyu ne a cikin gangar jikina. Washegari Da na tashi na yi zaton mafarki ne na yi wannan yasa ban bai wa abun muhimmanci ba.Ɗakunan maras lafiya mu ka fara shiga mu na duba su,na zo daidai gadon wannan mutumen na jiya da dare na ji muryarsa ya na cewa “madam don Allah ki taimaka ki bani kambuna” Da mugun mamaki na dube shi na ce “mi kake magana a kai? Ko wani abu yake ma ciwo ne?” Ya waro ido ya ce “kambun maitata da kika karɓe a daren jiya ” Ras gabana ya faɗi,a fili na furta “kenan ba mafarki ne na yi ba?” “Ki ban abina don Allah na yi miki alƙawari har na fita daga nan ba zan ƙara cutar da kowa ba” ya sake faɗa a karo na biyu,wani baƙin ciki ne ya turnuƙe ni nan take.“Wato ka ma taɓa cutar da wasu kenan?” Muryarsa na ɗan rawa ya ce “wallahi yara biyu ne kawai na shanye ma jini bayan su babu wanda na cutar” Na lumshe ido,nan take abun da yake kira da kambun maita ya bayyana gare ni daga nan inda nake zan iya hango shi cikin jakata wacce ke can ɗakin baccinmu. ‘Duk wanda ya kashe shi ma a kashe shi,don haka kai ma dole ka bi su’ na faɗa a zuci ina mai juya wa zan fita hargaginsa ya tsayar da ni na juyo. Duk hankalin kowa ya koma kansa,nishi kawai yake ya na zarar ido. A'isha ta nufe shi ta fara dubasa,kafin wani lokaci ya ce ga garinku nan ya mutu. Wani kallo na ga ta na jifata da shi na tuhuma,sai kuma ta fita babu jima wa suka shigo ita da Dr . Rubuce-rubuce aka yi bisanin a sanar da ƴan uwansa suka fita da shi. Har muka sauka daga aiki A'ishah ba ta bar min kallon nan ba,tuni na tsargu.Ko da na je gida hankalina kasa kwanciya yayi,haka na wuni sukuku Momah ta yi tambayar duniya amma na ce da ita babu komai. Da dare bayan duniya ta yi tsit na buɗe jakata na ciro kambun maitar nan,wata ƴar ƙaramar halitta ce mai rai sai motsi take.Sai da na ƙura idona da kyau sannan na fahimci Kunkuru ne,hannuna na rawa na ɗauko shi nan take ya ɗauki wani irin haske kamar an kunna ƙwan lantarki. Muryar Momah na ji daga sama ta na mai cewa “kambun wane ne?” na juyo a razane ina kallon ta,sai dai abin da ya fi ɗaga min hankali shi ne iya muryar ce kawai ke ta Momah amma fuskarta ta canza ..... [24/04 14:49] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Page 4 Fuskar Momah sak ta tsohuwa irin uwanda sun ga jiya da yau.Tuni tsoro yayi min dabaibayi ya ɗaure min zuciya,cikin wata irin murya wacce ba tata ba take shaida min “wannan halittar da ke hannunki ta na da matuƙar haɗari ki yi gaggawa mayar masu ita kayar su.Kin san kuwa mi ake kira da Kambun Kunkuru? Maita ce mai shegen naci masu ita za ki ga ko mutuwa suka yi sun dinga yin fatalwa kenan domin son duniya ba zai taɓa gushe wa ba daga zuciyarsa” Momah na gama faɗar haka kamar ƙyaftawar ido ainahin fuskarta ta dawo normal. Wani numfashi na ga ta ja ta na mai kafe ni da ido,da sauri na mayar da Kunkurun cikin jaka ina mai cewa “Momah ke ce?” Maimakon ta ban amsa sai kawai ta fashe da kuka,hankalina ya ƙara tashi na shiga tambayarta can ta tsagaita da kukan tare da yi min umarni na je na kwanta. Ban musa ba na kwanta sai dai fa ko kaɗan babu ɗigon bacci a idona.Tunani kawai nake,zuwa yanzu na fahimci akwai wani ƁOYAYYEN SIRRI(MRS SADAUKI) da Momah ke ɓoye min sai dai ban san shi ba. Kamar wacce take karantar zuciyata na ji saukar furucinta “Ayodele ban ɓoye miki tarihin ki ba don wani abu ba,sai don kiyaye ki daga mumunar ƙaddarar da mahaifin ki ke son ɗora ki a kai” Da sauri na yunƙura na tashi zaune na ce “Momah don Allah ki faɗa min wane ne mahaifina? Sannan ya na raye?” “Da ransa duk da na fi shekara ashirin da baro ƙasarmu ta gado,amma ina ji a jikina bai mutu ba” “Mine ne dalilin ki na guduwa to?” “Zan faɗa miki sai ranar da kika cika shekara ashirin da biyu cicif” “Nan da wata biyu kenan?” na faɗa don birthday ɗina ya kusa.Ta jinjina min kai alamar tabbatar wa,cike da farin ciki na kwana. Washegari da zan tafi makaranta Momah ta jadadda min kan cewa na mayar da Kunkurun nan inda na ɗauko shi “to” kawai na ce mata ba wai don ina da niyyar yin haka ba. Da na fito waje a ƙofar gida na yi rame daidai inda ruwa ke kwanta wa na saka Kambun Kunkuru na mayar da ƙasa,ina ganin yadda yake kallona da manyan idonsa amma Allah na gani ba zan barsa ba ya cutar da mutane. Ko da na isa asibiti na tarar ana ta ɗaga ankon bikin A'isha ,ban ware kaina ba na shiga duba wa tare da tambayar inda suka fiddota. Muna tsaka da aiki A'isha ta zo kusa da ni ta ce “Ayodele kin tuna mutumen da ya mutu jiya?” duk da na fahimci wanda take nufi bai hana ni neman ƙarin haske ba “wane fa?” “Wanda kafin mu sauka ya mutu,gadonsa kusa da na yaron nan mai cutar sikila” “Oh! Na gane shi” “Hum! In faɗa miki an sake maido shi asibiti” “Bai mutu ba?” na tambayeta da sauri,har sai da ta min wani kallo bisanin ta ce “ya mutu! ” Na sauke ajiyar zuciya,ita kuma ta ci gaba da cewa “sai dai fa gawarsa ta ƙi shiga kabari ” A'ishah ta faɗa cikin wani yanayi. Dukkan nutsuwata na bata tare da tambayarta “ban gane ba? To ya su ka yi da gawar?” “Sun maido ta mana! Ta na can MUTUWARE cikin sanyi”ta ban amsa. “Can shi ya sani! Mugun halinsa ne yasa Ubangiji ya nuna masa ishara” na faɗa zan ci gaba da aikin cika takardu don mun ɗan tsaya hutu ne . “Amma Ayodele na tambaye ki mana” “Ina jin ki” na faɗa ba tare da na dube ta ba. Ta ce “mine ne haɗin ki da shi?” na ɗago na zuba mata na mujiya sai na ga ta ɗan rikice da sauri ta ce “ah! Ina nufin mi ya haɗa ku,jiya da ina ƙoƙarin taimakonsa na ji ya na cewa ki yi masa rai kar ki muzanta ni ban shirya zuwa ɓoyayyar duniya ba” “Sai kuma ya ce miki da ni yake?” “Sunan ki na ji ya faɗa” “To ki je ki tambayesa” na faɗa cikin fushi tare da tashi na barta ma wurin. Wunin ranar haka muka yi aiki sam babu walwala har Fatimah sai da ta lura kamar mun samu saɓani.Ta yi tambayar duk muka ce mata ba komai,wurin cin abinci ma haka A'isha ke ta min kallon ƙasa-ƙasa ban san mi take zargi a kaina ba har mu ka zo kwanciya. Addu'o'i na ga ta na ta yi na neman tsari,sannan alamu sun nuna a tsorace take don motsi kaɗan sai ta zabura.Kasa haƙuri na yi na ce “ A'ishah ina son yin magana da ke” Fatimah ta kalla wacce ta sharar bacci bisanin ta ce min “to” Na saki wani murmushi sannan na ce “ki na tunanin ko wani na gani zai cutar da ke zan bari ballantana ni da kaina na cuce ki? Ban san zargin mi kike yi a kaina ba,amma ki sani ruhin Ayodele tsarkake ne .Burinsa kullum ya kawar da mugunta da masu yin ta,na san abin da ya faru a unguwarmu da kuma na mutumen nan sun saka miki shakku a kaina” Ta ja wani dogon numfashi sannan ta ce “wallahi ni lamarin ki ne ya fara bani tsoro,abubuwa kike kamar ƴar autar aljan.Idonki fa har canza kala suke,kuma ba zan ɓoye miki ba wallahi na fara jin tsoron ki” Na ƙyalƙyace da dariya na ce “wallahi ba muguwa ba ce ni ! Kuma ban san mike faruwa da ni ba.Abu guda nake so ki saka a ran ki shi ne Ayodele amanar A'isha ce” Wani gamsashen murmushi ta sakar min ta ce “har na ji zuciyata wasai,yanzu kam zan yi bacci cikin aminci” Sai da mu ka ɗan yi hira bisanin ta ɓingire bacci,na dube su cike da so da ƙauna irin ta jini. Ina shirin yin kwanciya na ji an kira sunana “Ayodele?” na waiga ban ga kowa ba,sai na yi tunanin ko kunnena ne bai ji min daidai ba.Sai dai da mamakina haka aka sake kira a karo na biyu,kawai sai na fito. Ci gaba da kiran sunan nawa aka yi,inda sautin ke fito wa na dinga bin direction ina ta tafiya har na ɓullo wata kwana.Nan na yi kiciɓis da allon sanarwa,sunan *GIDAN GAWA* ne ɓaro-ɓaro da manyan baƙi,a ƙasa kuma hoton gawa ne naɗe cikin farin likafani. Waige-waige na fara ,har zan koma na ƙara jin sautin sunana,muryar ya ta namiji ce ba mace ba.Ɗakunan da aka tanada don ajiyar gawa na nufi na mazan,ƙofar da kanta ta buɗe hakan yasa na kutsa kai. Ƙyalƙyal ! Aka kece da dariya,da sauri na fara dube-dube don tantance shin cikin wane akwatin ne ake dariya. “Ga ni nan” na ji ya faɗa a bayana,na juya na yi tozali da mutumen da A'ishah ke ban labari an maido gawarsa. Ido cikin ido muke kallon juna da shi,bisanin na ce “lafiya ka kira ni izuwa nan?” “Kambuna nake so ki ban” “Ba zan bayar ba doli ka mutu kamar sauran da ka kashe” “Ki bani cikin lalama ko kuma na gayyato miki shugabanmu” “Au! Har shugaba gare ku? Na tambaye ka mi yasa kuke son yin mugunta? Don me ba za ku zauna cikin duniya normal ba kamar kowa?” “Saboda duniyar ɓoye ta matsafa ta fi daɗi,za ka sha jini ka yi ta siddabaru ka na tsoratar da mutane cike da nishaɗi ” Hira ya fara yi min ta yadda suke kama kurwar mutum da kuma yadda suke yi in su na son bai wa mutum tsoro,hakan ya shagaltar da ni sosai sam ban fargaba sai mugayen esprit na ga duk sun cika ɗakin. Ruhika ne na maras imani,wasu ma daga maƙabarta suka zo nan don taimakon ɗan uwansu.Kewaye ni suka yi,ba na ganin fuskokinsu.Wasunsu tamkar innuwa,wasu kamar dunƙulalen baƙin hayaƙi,wasu kuma cikin siffar fatalwa ne da farin likafaninsu. “Auwushhh tangarrsinn,mahulujaaa.An yarhihum khaaaaa!” shi ne furicin da na samu bakina ya na furta wa,duk a tsorace suka ja ba shi kuwa tuni ya koma cikin akwatinsa.Idona na rufe na ci gaba da yin wani Yare ina yarfa hannu,a take wani haske duk ya game ɗakin wanda rufe wa idona bai hana ni ganin halin da suke ciki ba. Tuni duk suka tsere suka bar ni da shi,akwatin da yake ciki na ɗora hannuna akai ya fara ihu ya na “cewa ki yi haƙuri zan tafi wallahi na yi miki alƙawari gobe zan bar gidan gawar nan zan je na kwanta kabar....” bai ida kai furucinsa ba wani haske ya fito daga bakina ya daki goshinsa tsit ya mutu a yanzu kuma na tabbata ko fatalwar ba zai iya yi ba. Kaina yayi mugun sarawa,na dawo garas da sauri na fito waje sai kuma na ci karo da mai gadin wurin.“Wace ce ke?” ya jefo min tambaya,murya na ɗan rawa na ce “dama... Dama!” Sai ya saki murmushi ya ce “yi tafiyar ki” ban san dalilin shi na yin haka ba amma sosai na ji,domin muddin maganar ta yi nisa ya tara min mutane dole a ɗora min Ayar tambayar mi ya kawo ni gidan gawa a wannan tsohon daren. Ko da na koma ɗaki sai da na yi tunani bisanin bacci ɓarawo ya ɗauke ni. Washegari bayan duk mun kimtsa na ga A'isha sai murna take,ban yi ƙasa da gwiwa ba na tambaye ta “wai farin cikin na mine?” “Mansur zai zo ɗaukata,kin ga daga nan sai mu aje ki gida” ta ban amsa. “Au haba? Fatimah ba ta zo da babur ba?” “Ya samu matsala a jiya hanyar mu ta fiddo anko sai ta barsa wurin mai gyara” Mu na tsaka da hira aka kirata,cike da murmushi ta ɗauka bisanin ta aje wayar ta ce “har ma ya iso mu je” Sai da muka fito ne muka haɗe da Fatimah wacce ke zaune ta na shan love.Bakin ƙofar asibitin muka fita ,idona ya sauka kan wata ƙatuwar mota baƙa wuluk mai taya a baya. A'isha ta buɗe mana gidan baya muka shiga ni da Fatimah yayin da ita kuma ta shiga gidan gaba. “Baby ga ƙawayena da nake baka labari ka rage masu hanya” cewar A'isha . “A gaishe ku fatan duk ku na lafiya?” ya faɗa cikin muryarsa irin ta siraran maza ,duk muka amsa da lafiya lau. Ya dubi A'isha ya ce “ya maganar zuwa gidan abinci kenan?” “Mu je mana ai su ma za su ji daɗi,ko ya kuka ce ƙawayena?” Fatimah kawai ta amsa mata,ni kuwa na lula duniyar tunanin ta yaya ya samu kuɗi har haka cikin ƙanƙanen lokaci in dai yadda A'isha ta bamu labari ne Lagos ne ya je to tabbas akwai lauje cikin naɗi. Ina cikin wannan tunanin har muka isa , restaurant ce ta sai wane da wane don ni ban ma san da zamanta ba. Yadda aka tarbe mu kawai ya isa mu gane Mansur sananne ne a wurin. Shi ya zaɓi abin da za a kawo ma A'ishah yayin da ya nemi mu zaɓa da kanmu,amma sai A'ishar ta nuna masa ko wurin aiki cikin plate ɗaya muke cin abinci don haka nan ɗin ma ba za a ware mu ba. Shiru yayi ya na ɗan tunani,bisanin ya bai wa serveur ɗin umarni kan yayi yadda ta ce.Lafiyayen abinci ne,haka muka fara ci hankali kwance ba tare da wani tunani ba shi kuwa Mansur duk ya zama wani iri. Tamkar wacce aka sa ƙugiya ana ƙoƙarin zaƙulo hanjin cikinta haka na fara ji cikina na min ciwo,da sauri na fidda hannuna na ce na ƙoshi. Na tashi tare da tambayar masu kula da wurin ina ne toilet,aka nuna min na shiga.Amai na ta kwarara wa kamar raina zai fita,tsabar azaba har wata zufa ke tsatsafo min ina buɗe ƙofar toilet na yi kiciɓis da saurayin A'ishah... [24/04 14:49] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Page 5 Na yi tunanin ko banɗakin zai shiga hakan yasa na ɗan yi saurin ja baya na basa wuri.Amma da mamakina sai na ga yayi tsaye ƙiƙam hakan yasa na ɗago na dube shi. Kamar mai son tantance wani abu haka yake kallona bisanin ya ce min “fatan dai lafiya?” “Alhamdullah!” na amsa masa a takaice “okay!” ya faɗa tare da koma wa baya yayi tafiyar shi.Na bi shi da kallon mamaki bisanin na take masa baya,ina zuwa sai na tarar ya zauna kujerata wacce na tashi kawai sai na yi tsaye. “Ki zauna mana” ya faɗa cike da kulawa,ban sani ba ko bai lura ba ne ya zauna a nan ɗin oho amma dai haka kawai na ji ban ra'ayin zama inda ya tashi . “Ke ma ki zauna mana ga kujera nan,ki yi tsaye kamar wata soja?”cewar A'ishah,ganin haka yasa na zagaya zan zauna kan kujerarsa ba don na so ba don haka kawai nake jin akwai makircin da ya shirya,cikin ikon Allah wayata ta ɗau ringing,ina duba wa sai na ga sunan Momah . Ina ɗaga wa ta ce “a ina kika tsaya har yanzu ba ki zo gida ba?” “Momah gani nan zuwa yanzun nan” na faɗa cikin rawar murya. “Ki na ina na ce?” “Tare da su A'isha Momah ” na faɗa tare da mayar da wayar a hand free ta yadda za su ji abin da Momar za ta ce sai kuma na yi masu alama da su yi magana,sai dai kafin su kai ga yi Momah ta ce “ki dai yi sauri ki dawo gida sam jikina na bani babu hairan a ind....” ban bari ta kai Aya ba na kashe kiran ina muzurai “zan tafi sai gobe in mun haɗe”shi ne abin da na iya furta wa bisanin na yi tafiyata ba tare da na jira cewar su ba. Bayan na fito daga restaurant ɗin sai na yi tsaye turus,don rasa ta ina zan bi na yi.Tamkar an sauya hanyar, lokacin da muna cikin mota lafiyayyar kwalta ce saɓanin yanzu da na tsinci kaina cikin jeji. Wurin babu gida ko ɗaya sai ciyayi,da na waiga ma hatta restaurant ɗin babu ta ɓace ma ganina.A nan take na fara jin tsoro duk da ni ɗin ba ma'abuciyarsa ba ce,tafiya na fara ba tare da na san inda nake jefa ƙafata ba har na isa wurin da hanya ta tsage ta rabu biyu.Wata irin ƙishirwa nake ji a cikin mintin da bai gaza goma ba,maƙoshina ya bushe ƙamas. Idona suka fara ɗaukar caji,na lumshe su a hankali kuma bakina ya fara fitar da sautin wani Yare.Ban buɗe idona ba sai da na ji ƙarar motoci da zantukan mutane. A bakin titi na tsinci kaina, Allah ya taimake ni na hangi wani gu ana sayar da ruwan leda na tsallaka na sayi leda huɗu a nan tsaye na shanye su.Na ja ajiyar zuciya kamar wacce aka dawo ma da ruhi haka na ji,daga nan na tari taxi sai gida. A can restaurant kuwa sosai hankalin Mansur ya tashi,muryar Momah tamkar busar sarewa haka ta ratsa dodon kunnen shi.Ya so ya tsayar da Ayodele saboda hatsarin da ke da wurin,amma da ya tuna zuciyarsa ba ta aminta da lamarinta ba sai ya ƙyaleta tare da yaƙinin sai dai a yi labarin wata amma ba dai ita ba. Bayan sun gama cin abinci ya ɗauki su a mota,sai da ya fara ajiye Fatimah sannan ya kai A'ishah. “Wai wace ce ita? Wato abinci mai magani ba zai taɓa zama a cikinta ba shi yasa ta amayar da shi.Na tsane ki! Ita kuma uwarta ta wace ce? Ya aka yi har ta san na shirya plan akan ɗiyarta?” ya jero ma kansa tambayoyin ya na mai bugun sitiyarin mota a haka har ya isa tankaɗeɗen gidansa wanda ya ji komai na more rayuwa.Sai da yayi wanka ya sha madara mai sanyi sannan ya kira A'isha suka yi ta hirar soyayya a ƙarshe ya tambaye ta “ya labarin ƙawar ki?” “Wace daga ciki?” “Wannan mai siffar Inyamurai” ya bata amsa,ta yi dariya ta ce “don dai ta na da jar fata ne sosai amma ai ba ta kama da Inyamure ” “Fatan ta je gida lafiya?” “Wallahi ba mu yi waya ba” “To ki kira ta mana,sam ban yi kirki ba da ban bata ko da kuɗin taxi ba ne” “Jira na kirata to” cewar A'isha ta na mai kashe kiran,Mansur ya lumshe ido ya na jin zuciyarsa na ɗan dokawa burinsa guda A'isha ta kira ta ce masa ta mutu. AYODELE Ina isa gida Momah ta wani jawo ni a jikinta ta rungume bisanin ta fara duduba ni kamar wacce ke neman ko na samu wata illa ne. “Daga yau kar na sake jin kin tafi yawo kin ji ko? ” “To Momah ” na amsa. “Ayodele ke ɗin ta daban ce,dole ki dinga taka tsantsan duk da ina da yaƙinin ababen bauta ba su taɓa bari a cutar da ke ba,domin su na tare da ke a ko ina amma ki dinga kulawa ba ko ina ba ne ake zuwa” Momah ta sake faɗa ta na mai kallona cikin ido.Kai kawai na jinjina mata bisanin na wuce ɗaki,kaya na cire na yi ɗaurin ƙirji na je na yi wanka . Ina tsaka da cin dambun shinkafa da Moma ta girka kiran A'ishah ya shigo,gabana sai da ya faɗi a take duk abin da ya faru da ni ya dawo kaina,hakan yasa har kiran ya katse ban ɗauka ba . Lokacin da na biyu ya shigo kuma a daidai nan maƙociyarmu Asabe ta shigo ta na rangaɗa sallama. Na amsa mu na gaisa wa,Momah ma ta fito .Godiya ta zo ta na ta faɗa mana yadda lamarin ya kasance da Zeinab nan muka yi ta hira kan Mayu da illolinsu.Sai bayan ta fita ne na duba wayata ,har zan maida kira kuma sai na fasa na tsunduma zancen zuci ‘tabbas da walakin goro cikin miya! In babu rame mi ya kawo zancen shi? Mine ne na biyana har toilet? Babu shakka akwai abin da ya saka a abincinmu,to shi kuma restaurant ɗin da ya zama kamar ɓatan wata? Hummm! Zan nutsu,na ankare komai sai na gano gaskiyar lamarin’ Abincin ma sai ya fita raina,tashi na yi na fiddo fararen rigunan da nake saka wa na likitanci na wanke su tasss bisanin na kwanta ina yin bacci don jiya mun sha aiki sosai. Tamkar a mafarki na ga wasu mutane masu fararen kaya sun zagaye ni,idona sun min nauyin da ba zan iya ware su duka ba amma tabbas ina iya ganin abin da ke gabana.Kaina na ji an fara shafa wa yayin da sauran kuma ke yin hira cikin wani Yare wanda in ba zan manta ba shi ne na taɓa ji Momah ta yi.Cikin wannan yanayi na lula duniyar mafarki,yau ma kamar kullum sanye yake cikin kayan ƴaƴan sarakuna ya saka kayan yaƙi,daidai ƙugunsa kubai ne mai ɗauke da takobinsa.Gefensa kuma masu tsaron lafiyarsa ne a tsaye cikin shirin yaƙi akan duk wanda ya kawo masu farmaki.Murmushi yake sakar min ya na kallona daga nesa, cikin izzar da ban san yaushe na same ta ba na fara takawa izuwa inda yake muna facing juna.Da sauri na lumshe ido sa'ilin da ya tsaka ɗan yatsansa manuni ya dangwala min jininsa a goshi a nan take wani sanyi ya luluɓe ni yayin da kuma nake jin shigar wasu lamurran da ba zan iya fassara su ba su na ratsa ɓargo da tsokar jikina. “Ayodele? Ayo....” a kasalance na buɗe idona na zube su kan Momah wacce ke faman jijigata da kiran sunana. Ta sakiya wata nauyayyar ajiyar zuciya bisanin ta ce “daga yau kar na sake ganin kin yi bacci a daidai lokacin da tartatsin rana ke tsakiya ban so” Dakyar na iya buɗa baki na ce “don me?” “Lokacin babu wata albarka a cikinsa ,bacci ya haramta ga al'ummar Victoria Falls ” Da mugun sauri na ce “su waye kuma al'ummar Victoria Falls ? A wacce ƙasa ce? Mine ne haɗi na da su?” Da mamakina sai na ga Momah ta rikice,abin da na lura ma kamar suɓutar baki ce ta yi.“Ki na ji Ayodele mu bar wannan maganar,ke dai kawai ki kiyaye abin da na ce.Am...na ce ... Ki taso na koyar da ke saƙar hannu” duk a rikice take,ni kuwa na zuba mata ido.Lokacin baya babu yadda ban yi da ita kan takoya min saƙar hannu ba ta ƙiya,amma yau sai gashi yau take son koyar da ni. Fuskata na wanke,na gyara zama ta fara nuna min yadda ake fara aza zaren farko na Foundation ɗin sannan a fara zarga wa gabanin ta miƙo min ƙarafan saƙar. Abu guda ya ban mamaki yadda na iya tafiya da takun saƙar kamar wacce tun can farko na taɓa koyon ta ,Momah na daga gefe ta ƙure ni da ido .Ko shakka babu ta zurfa sosai cikin tunani duba da yadda na yi mata magana sam ba ta ji ba.Ganin haka yasa na je na fara cika bokiti da ruwa,“oh! Har kin gaji?” na tsinkayo muryarta, murmushi kawai na sakar mata bisanin na ɗauki bokitin ruwan. Ina kai soso fuskata na ji wani irin uban raɗaɗi tamkar na zuba barkono ,da sauri na wanke na fito direct ɗaki na shiga na ɗauki madubi.Ɗigon ja na gani a goshina mai ɗauke da wani ƙaramin tauraro.Shiru na yi ina daɗa kallonsa,“Momah???” na ƙwala kiranta ,ta na shigo wa na ce, “Dubi wannan abun mine ne? Zafi yake min” Cike da kula wa ta ce min “ki jira har ranar da kika cika shekaru ashirin da biyu duk zan yi miki bayani” Na turo baki gaba na ce “ni dai ki faɗa min yanzu” “Ke ban fa son sakarci ,wai haihuwata ma kika yi da za ki tsare ni da tambayoyi ? To ban sani ba” ta na gama faɗa ta shige ƙurya ɗaki. Yadda na matsa wa kaina sanin mine ne har Allah yasa na tuna da mafarkin da na yi,wato na masoyin ɓoye.Har ban san lokacin da na saki murmushi ba,cike da nishaɗi na shirya cikin riga da wando na fita ƙofar gida. FATIMAH Tun lokacin da ta ci abincin da Mansur ya saya masu a restaurant take jin wani mugun sauyi a jikinta.Tamkar wacce ba da lafiya haka ta samu wuri ta kwanta,wani irin tsoro da shakkar saurayin ƙawarta take ji ba tare da ta san dalili ba.Ummarta har tambayarta ta yi abin da ke damunta amma ta ce babu komai.Ta rufe kanta cikin ɗaki kawai ,domin wani irin son kaɗaici ne ya zo mata.Wayarta ta ɗauka ta tura ma Nasir saurayin ta text ,duk da ba ta son shi haka ta ji ra'ayin kula shi.Da wannan ta ɗan rage faɗuwar gaban da take ji,har ta samu ta ɗan saki jiki. A can ɓangaren A'ishah kuwa haka ta kira Mansur ta shaida masa ta yi ta kiran Ayodele amma ba ta ɗauka ba.Har ƙasan ransa ya ji mugun daɗi don dama ya na tabbacin fatalen da ke kan hanya kawai sun isa su kasheta da tsoro. Washegari A asibiti duk muka haɗu,ko kaɗan ban yi ma A'ishah maganar kiranta da ban ɗauka ba hasali ma ban so wata doguwar hira ta haɗa mu. Ina ƙoƙarin saka wa wata mata tiyon fitsari A'ishah ta matso kusa da ni,ta ce “jiya Mansur na tambayar ki” sai na yi shiru kamar ban ji ta ba,ta sake maimaita min sai na ce “ki jira har mu fita mana,ki duba sauran patients ko akwai wanda ba a yi masa aiki ba ” na yi tunanin na rabu da ita kenan amma mu na fito wa ta sake tara ta da zancen “jiya sai da ya tambaye ni ,sam bai ji daɗi da bai baki kuɗin taxi ba” Na ce “ba komai ana tare,ki tuna min don Allah zan baki kuɗin anko sai ki sayo min” “Ok to babu matsala,amma Mansur ya ce min abokansa sun shirya party kin ga ya zama dole a sake fitar da wata ankon ” “ A'ishah yanzu fa babu kuɗi ba lallai kowa ya iya sayen har anko biyu ba” “Zan yi masa magana to,ƙila su abokan su saya maku” “Hum!” kawai na yi,bisanin na ce “wai ita Fatimah ba za ta zo ta kama aiki ba ne?” “Kanta ke ciwo ta na can baya wurin ƙofar emergency ” Da sauri na kewaya ta bayan na sameta a kwance kamar ba likita ba.“Fatimah?” na kira sunanta,ta buɗe ido dakyar ta dube ni ai ban san lokacin da na yi zaune ba na ɗauko kanta na ɗora a cinyata. “Mine ne taƙamaimai abin da ke damun ki?” Murya na ɗan sarƙe wa ta ce “ A'ishah ce sai hirar mijin da za ta aura take yi min,ni kuma wallahi mugun tsoronsa nake ji.Ban so ko kaɗan ana kiran sunansa” shiru na yi na ɗan wani lokaci bisanin na ce “yaushe kika fara jin tsoron nasa?” “Jiya” “Bayan kun dawo daga restaurant ko kuma kafin mu je?” “Bayan mun dawo” ta ban amsa ta na wani irin tari,na lumshe ido ‘ tabbas zargina ya zama gaskiya.Saurayin A'ishah ba mutumen kirki ba ne,to amma wace iri ce ɓoyayyar fuskarsa? Ban sani ba!’ na faɗa a zuci tare kuma da tunanin mafita. Can dubara ta faɗo min na ce “Fatimah a Addinin ku ba a sanar da ku yadda ake karye asiri ba?” “Mi ya kawo zancen Addini kuma?” cewar Fatimah don na santa sarai,ba tun yau take guje duk hirar da za ta kawo banbancin Addinai ba. “Ke dai ki ban amsa” na sake faɗa,ta ce “eh an sanar da mu mana,gaba ɗaya Alkur'ani waraka ce akan dukkan ko wace matsala” Ta na gama faɗa min na ce “ok jira ni” sai na sauke kanta kamar yadda na tarar da shi tun farko bisanin na koma can ciki.Direct office ɗin Dr Haleema na nufa,mace ce mai matsayi babba sannan ma'abociyar Addini ga ta kuma da sauƙin kai ba ta hantarar na ƙasa da ita. A zaune na tarar da ita ta na duba wasu takardu ,da murmushi ta dube ni ta na mai cewa “Ayodele dama ke ce ke buga ƙofa? To zauna” Na zauna tare da gaisheta bayan ta amsa na ce “Dr don Allah a Musulunce wane abu ne ina nufin addu'a ko kuma magani wanda yake saurin kare asirin da mutum ya ci” Cike da kulawa ta ce “sanamaki! Ganye ne mai matuƙar amfani wurin kare tasirin asirin da mutum ya ci ,in an tafasa shi sai a yi addu'a cikinsa a sha” “A ina zan same shi don Allah?” “Wurin masu sayar da ganye ko kuma Islamique center,mike damun ki Ayodele?” “Babu komai Dr na gode,jira ina dawo wa” Ina fito wa daga office ɗinta na je na shiga ɗakinmu inda na aje jakkata,kuɗi na ɗauko sannan na fita bakin hanya.Na samu mai taxi na yi masa bayanin inda zai kai ni,wata cibiyar sayar da maganin musulunci ya kai ni.A can na sayo sanamiki mai kantin ya haɗo min da zuma,sannan na dawo asibiti. Tun daga nesa nake hangen Dr Jaleel ya na masifa,ina zuwa ya ce “daga ina kike? Wa ya baki izinin fita?” “Ka yi haƙuri matsala ce ta ujila ” na furta ina mai sunne kai domin yin ladabi. “Su majinyatan da kika bari fa? In wata matsala ta faru ki sani a bakin aikin ki” nan ya shiga yin min masifa kamar wata ƴarsa kafin yayi gaba. Office ɗin Dr Haleema na sake komawa na nuna mata ,“Ayodele ki faɗa min abin da ke faruwa mana sannan ba ko wane lokaci ba fa ake shansa” “Dr Fatimah ce babu lafiya,kuma na tabbata sihiri ne ke ɗawainiya da ita ki taimaka min ki yi min addu'o'in ciki na bata ta sha don ta galabaita sosai” shiru ta yi,bisanin kuma ta ɗauko moɗar ƙarfe wacce take dafa Lipton a ciki, da ita ta yi amfani wurin tafasa Sanamakin bayan nan ta zuba zuma ta shiga yin karatu ciki.Na yi mata godiya na karɓa,inda na bar Fatimah nan na same ta.Dakyar ta iya tashi zaune ta yi Bismillah ta sha,a nan take zufa ta karye mata.Sai ta fara sauke ajiyar zuciya bisanin ta ce “Ayodele cikina na murɗawa toilet zan shiga ” da sauri ta miƙe,na take mata baya har muka isa banɗakin da aka tanada don likitoci. A wannan wunin tun ina ƙirga adadin da Fatimah ta kewaya har lissafi ya ɓace min, zawayi kawai take mai ɗan uban wari don ko ni da ke tsaye bakin toilet ɗin ina jin warinsa.A ƙarshe dai har ni sai da na shiga toilet ɗin don ta galabaita sosai,idonta tuni sun faɗa ta yi zuru.Ganin an ɗauki sama da minti ashirin ba ta samu wata murɗawar cikin ba,na taimaka mata ta yi wanka sannan mu ka fito.A ɗakinmu ta kwanta,sai a lokacin A'ishah ta san da ciwon yayi tsanani.Ƙarin ruwa na saka mata,bayan ta sha lemu exotic baiwar Allah sai bacci. A'isha ta tsaya tare da ita ni kuma na fita na hau aiki don kusan ban yi komai ba.Sai ƙarfe tara na dare na nufi ɗakinmu,duk bacci suke.Na taɓa wuyan Fatimah na ji babu zazzaɓi ,na je na haye gado sai bacci. “Yaanhun! Uhun ! Uhun!” shashekar kuka ta tashe ni daga bacci,na lalubo wayata na duba.Ƙarfe biyu ta gota,na ja tsuki tare da fita na nufi MUTUWARE don tuni ruhina ya lamunta da lamarin da ke faruwa da ni. Ɓangaren mata na shiga inda ake aje gawa,kwaɗon kawai na taɓa ya buɗe kansa na ja ƙofar na shiga sanyi AC ya ratsa ni sosai bisanin na yi tozali da wata sabuwar gawa don ko wanka ba yi mata ba.Mu na haɗa ido da ita ta bar kukan,a gajiye nake hakan yasa nake jin haushin tashe ni daga baccin da ta yi. “Sai ki tashi ki faɗa min abin da yasa kika jawo ni izuwa nan” na faɗa ina waige-waige don neman wurin da zan zauna,sai dai ban farga ba na ji wani hannu ya jawo ni da mugun ƙarfi na yi baya tare da faɗa wa cikin akwatin mutuwa..... Mai son complete book ɗin nan 800 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [25/04 09:08] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Page 6 Kiciniyar fita daga cikin akwatin gawar na fara sai dai ga mamakina wata gawar na gani a tsaye kan ƙafafunta ta na ƙoƙarin danna ni ciki.Da dukkan alamu akwatinta ne,cikin wata irin murya ta maso duniya take cewa “ki zauna madadina don Allah na ga ke lamarin duniya bai sha maki kai ba,ban shirya zuwa can mazaunar fatale da ruhika ba” Idona na ware sosai kan matar, datijuwa ce a ƙalla ta kai shekara hamsin da ɗoriya fara ce tasss sai tsagen fuskarta na kurmawanci da ya fito raɗo-raɗo. Tabon goshina ne na fara jin ya na motsi,kamar almara sai gani na fito daga cikin akwatin na tsaya kan ƙafafuna. Gawa ta fashe da kuka,cikin tsawa na ce “je ki koma makwancin ki,wato lokacin da malamai ke yi muku wa'azi kar ku biye ma ruɗin duniya ku na yawon dare amma kuka yi kunnen uwar shegu da su kuke fita cikin dare farautar bayin Allah.Yanzu kuma da zanzaro ya tonon gidan Rina gari ya kwaɓe miki za ki neman ki dawo duniyarmu?” Idonta na zubar da hawaye ta shiga akwati ta kwanta wani haske ya fita daga goshina ya daketa tsit kake ji har esprit ɗin nata ya bar motsi,na maido dubana ga ɗayar wacce ke shashekar kuka na zuba mata Mayun idona masu masifar kaifi na ce “ ke kuma ina jin ki” Cikin kuka ta fara yi min bayani “wannan da kike gani mahaifiyata ce,ta ja ni izuwa wani ƙauye ne don yin shagali ita da ƙawayenta a can suka nemi da ta bada jinina su sha da ta ƙiya ne hanyarmu ta dawowa mu ka yi hatsari.Kin ga ban mutu ba sun ɗaure ni da azargagi ne,shirinsu shi ne in an kai ni maƙabarta su je su haƙo ni su tsotsen jini” A ɗan takaitaccen bayaninta na fahimci mahaifiyarta ta na cikin wata ƙungiyar Mayu ce masu shan jini,sannan duk shekara su na gudanar da bikin ƙara danƙon zumunci inda a dole wata za ta bayar da kyautar jini daga cikin ahalinta,kamar ɗa,jika ko ƙane. Kallon tsaf na yi mata,sai yanzu na lura da goshinta da gefen bakinta duk a fashe suke alamun buguwa.Tunani na fara ta inda zan taimakonta,sai dai na kasa samun mafita don ban san fuskokin masu son kaita ƙasa ba. “Ki taimaka min kar ki bari a kai ni maƙabarta da raina ban mutu ba sun juyar da hankulan mutane ne kawai ake min kallon gawa ” muryarta ta katse min tunani. Na ja dogon numfashi bisanin na ce “ki na ji na,a halin yanzu banda mafita amma na yi miki alƙawari zan cece ki ko bayan an haƙa miki kabari ne an saka ki ci to zan zo gare ki” Fararen idonta ta zuba min uwanda sam ba su da ɗigon baƙin ciki,na jinjina mata kai alamar tabbatar wa kan ƙudirina.Ban sani ba ko ta yarda da ni ɗari bisa ɗari,amma a sannu na ga ruhinta da ke dabaibaye da wasu Kambu ya ɗan samu salama. Sai da na shafi fuskarta bisanin na fito,direct ɗakinmu na wuce sai na tarar da Fatimah a zaune. “Kin tashi? Ya jikin naki?” na tambayeta. “Da sauƙi alhamdullah! Na gode sosai Ayodele,haƙiƙa ke ƴar baiwa ce.Da ace musulma ce ke da tabbas ba ƙaramin gudumuwa za ki bayar ba” Na sakar mata murmushi na ce “duk Ubangiji muke bauta ! Banbanci kaɗan ne,sannan shi ke tsara komai iyakacinmu mu yi aiki da baiwar da ya bamu amma komai daga Ubangiji yake” “Zance na hikima! Anya kuwa ruhinki ba na Musulunci ba ne gangar jikin kaɗai ke ta Yahudawa?” Fatimah ta faɗa,dariya na yi na canza zancen “ai yanzu dai kin bar jin tsoron komai ko?” Ta ja tsuki tare da cewa “shi ɗin banza Allah na tsane shi ,amma yanzu ban ji shakkar shi .Wai daga ina kike ko an kawo sabbin patients ?” Na ja ajiyar zuciya domin tambayarta sai ta tuna min da danbarwar da na baro a can MUTUWARE.“Ki koma ki kwanta don kin galabaita sosai ,ni ma baccin nake ji akwai aikin da nake son yi cikin bacci” na faɗa tare da kwanta wa kan gado,Fatimah ta waro ido bisanin ta ce “kin san kuwa a jiya ne ko yaushe da kika yi bacci gidansu A'ishah wallahi sai da kika bani tsoro don ba zan ɓoye miki ba shi ne dalilin da yasa na sulala zuwa gida” Na lumshe ido ba tare da na bai wa abin da take faɗa muhimmanci ba,nan take bacci ya ɗauke.Duk a mafarki aka nuna min maƙabartar da za a rufe wannan baiwar Allah,da kuma duk abin da zai faru da yadda zan kuɓutar da ita. Washegari muka hau aikin safe bisanin mu sauka,tuni Fatimah ta yi tafiyarta A'ishah kuwa a gabana ta kira Mansur kan ya zo ya ɗauke ta.Na taɓe baki don na lura har wani rawar kai take wanda yawancin amare ko kuma wanda za su auri mai kuɗi suke yi. Kafin ya zo ne na samu tsure A'isha da ido na ce “bayan Mansur ya dawo daga Lagos halan kasuwanci ya fara?” shiru ta yi bisanin ta ce “wallahi ban sani ba,kin san in mutum ya je neman kuɗi da zarar ya dawo to fa hutu ne kawai yake,ina ga shi ma bai komi” “To in kuɗin suka ƙare fa? Ke dai ki tambaye shi ƙila ya na kasuwanci ya ɓoye miki ne” na faɗa cikin son jawo ra'ayinta,don zuciyata ta fara aminta kan na rusar maganar auren nan . “Wallahi ba zan iya ba,ƙwarjini yake yi min ba zan iya tambayarsa ba.Kin san kuwa yadda nake jin mugun tsoron Mansur? Wallahi yau da ya zo ɗaukata kasa kallon ƙwayar idonsa na yi” “Hum! Wai dama ki na sonsa ko kuwa yanzu ne da ya zama mai kuɗi kike ra'ayin shi?” “Sosai kuwa! Dama rashin kuɗi yasa ba a bari muka yi aure ba.Abbana ya ce sai na ida karatu duk don kar ran Mama ya ɓace kin ɗan Yayarta ne” Kai kawai na jinjina ina tunanin wani babban al'amari,bisanin na ce mata “okay ni zan tafi in ya zo ki gaishe shi” “Ki jira mana sai ya sauke ki gida” “A'a na gode!” A'ishah ta riƙe ni ta na cewa “ wallahi babu inda za ki je dole mu aje ki gida” Muna cikin wannan yanayi motar Mansur ta tsaya,fito wa yayi.Sanye yake da baƙaƙen suit idonsa manne da baƙin gilashi,cike da ƙasaita ya iso kusa da mu. A inda yake tsaye zan iya hango tsantsar mamaki kan fuskarsa,wanda tuni na fahimci na gani na a raye ne.“sannu angonmu” na faɗa cikin raha,sai ya ɗan daburce ya na mai cewa “oh! Na shagala da kallon amaryata ne shi yasa,fatan ki na lafiya?” “Garas nake!” na basa amsa ina mai kallon tsakiyar idonsa don tuni ya cire gilashin,ya kawar da kai ɓangaren A'ishah ya na mai cewa “amarya ba kya laifi! Mu je ko? ” ga mamakina kamar raƙumi da akala haka A'ishar ta bi bayansa ko kallona ba ta yi ballantana zancen yi min sallama ko kuwa ta yi maganar sauke ni a gida da ta ce. Na rumtse ido tsabar takaici,ganin Mansur ya ci taya ƙura ta tashi duk ta baɗe ni.A hankali na buɗe su tare da bin motar da idon har ta ɓace ma ganina,jiki a matuƙar sanyayye na je na tsaya bakin hanya.Tsabar yadda ruhina yayi baƙi har ban san lokacin da na tsayar da wata farar mota ba madadin taxi,sai da na ji muryarsa ya na cewa “hanya zan rage miki?” Cike da masifa na buɗa baki na ce “aka ce ma banda kuɗi ko na yi ma kama da irin ƴan iskan ƴan matan nan?” Ya waro ido ya ce “keee! To ce miki aka yi motata taxi ce?” Sai a lokacin na farga da mota ce,na yi baya ina cewa “ka yi haƙuri ” “Na ƙi ɗin dole ki shigo na kai gida” Zan kuma ƙara yaɓa masa magana sai na ga yayi min ƙwarjini don babban mutum ne mai cike da kamala zai kai shekara arba'in da biyar.Na haɗe yawu na ce “na gode” amma fafur ya ƙi tafiya ya nace a ƙarshe dai na yarda na shiga. Mu na tafe ya mayar da volume ɗinsa,ƙira'a ce ke tashi ana karatun Alkur'ani.Ban san mi ya shige ni ba,amma sauraren sautin ya saka na fara jin sanyi a raina .“Wace unguwa za mu je” “Unguwar ƴan tsofi” na basa amsa don haka ake kiran unguwarmu.Ya ci gaba da driving,ni kuwa sai sauke ajiyar zuciya nake ina jin nutsuwa na daɗa ratsa ni har mu ka isa layinmu.A ƙofar gida ya sauke ni,na masa godiya ina mai ficewa. A'ISHA Yanayin kallon da Mansur yayi mata ya saka duk wata gaɓa ta jikinta ta yi sanyi.Tamkar za ta shiɗe haka ta ji,ga wani tsoronsa da shakkarsa da ta ji sun ƙara dirar mata.Allah na gani sam ta manta da Ayodele na kusa da ita,hakan yasa ta bi bayan Mansur da take jin ko yanka kanta ya ce ta yi to babu shakka za ta yi tsabar biyayya. Su na shiga mota ya kamo tafin hannunta,cikin salon yaudara yake mata magana “na tsani arniyar can mi ma sunanta?” “Ayodele” ta furzo lafazin dakyar.Ya ci gaba da cewa “yawwa! Daga yau ina so ki nisanta kan ki da ita,kar na sake ganin ku na ƙawancen na yanke shi kowa yayi harakar gabansa ki na ji na ko?” A'isha ta jinjina kai ta ce “in sha Allah ko magana ban sake yi mata” “Yawwa my Ayush! Kar ki sake ce mata ko kanzil! Ki goge lambarta daga wayar ki kafin nan ki tabbatar kin yi blocking nata” “Yanzun nan kuwa Oga!” A'isha ta faɗa tare da fiddo waya ta aiwatar da duk abin da ya ce.Ya saki hannunta,ya na canza akalar motarsa zuwa restaurant ɗin jiya. A'isha na zaune Mansur ke cewa “gishiri bai kama kaza ba yadda nake so,ka san a jiya wasu sun ci da rabonta shi yasa na kawota yau ta yadda komai zai tafi daidai” Wanda zai kawo abincin ya ce “an gama ranka shi daɗe!” can ya tafi ya kawo,tsabar mugunta ta Mansur shi ya dinga bata abincin da Allah kawai ya san adadin tsafin da aka yi masa,ita kuwa sai ci take.Bayan ta gama ya kaita gida zuciyarsa fal farin ciki,“na tsane ki Ayodele! Daga yau dai na yi ma takalme tubkar hanci” ya faɗa a bayyane ya na wata irin dariya. FATIMAH Tunanin kar Mansur ya tarar da ita ya saka ta yi tafiyarta tun da wuri.Addu'a neman tsari take kar Allah ya sake haɗa ta da shi,duk da ta na jin cutar da ya bata ta ci duk ta zawayeta amma hakan bai hanata jin normal tsoro a kansa ba tun da shi ɗin mugu ne.Ta na zuwa gida ta samu tuni ƙanenta ya karɓo mata babur ɗinta daga wurin gyara,sosai ta ji daɗin haka don ta na tunanin ta kaucewa shiga motar mugun saurayin A'ishah. AYODELE Ina shiga gida na tarar da Momah zaune kan tabarma ga wani akwati a gabanta ,ta na gani na da sauri ta rufe shi ta shige ɗaki,na bi bayanta sai na ga ta tura shi ƙarƙashin gado. Ban damu ba don ko magana ban yi mata ba,kayan jikina kawai na canza na fito.Jikina na bani kan na je maƙabarta hakan yasa na fito na samu wata taxi na masa kwantace da inda zai kai ni.Kamar dai yadda na gani cikin mafarki tun daga hanyar da aka bi da ni har izuwa maƙabartar. Daga nesa na yi tsaye,mutane sai bisa suke ido kawai nake bazawa ko Allah yasa na ga kabarin wannan baiwar Allah. Wani ihu ya ja hankalina,da sauri na juya ɓangaren haguna,sai na ga ashe akwai wasu kaburbura ma ta nan.Idona ya sauka kan gawarta,mugayen tsofin nan kuwa jira suke a rufeta su far mata.Ban buɗe bakina na yi magana ba,amma tabbas na kira su izuwa gare ni.Duk da alamun tsoro a fuskarsu yayin da kuma suke ƴar kallon-kallon,ban basu isasshen lokaci ba na dirar masu ko kuma na ce esprit ɗina ya shiga yin faɗa da su har na ci nasara a kansu duk suka gudu. Daidai nan na dawo cikin hayyacina,wasu daga cikin mutanen da ke ƙoƙarin turbuɗeta suka ja baya su na kiran “wallahi da ranta” ina jin haka na yo baya na yi tafiyata. Lokacin da na iso gida na Momah na banɗaki ta na wanka,hakan yasa na yi saurin shiga ɗaki na jawo akwatin ina buɗe wa na yi arba da wani hoto da yasa kaina yayi bala'in sarawa ya na daɗa juyawa...... Mai son complete 800 ne via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [25/04 09:11] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Page 7 A cikin hoton zan iya gane Momah duk da ƙarancin shekarunta a lokacin,hannunta riƙe da baby girl an yi wa gashinta wani tozo daga gaba,gefenta kuma wani gawurtacen namiji ne dattijo amma ka na ganinsa ka ga jarumi. Duk cikin hoton yanayin shigarsu ce ta fi ɗaukar min hankali,ba kaya ba ne irin wannan da muke saka wa ba.A'a nasu kamar fata ce aka sarrafa aka mayar da su kayan,su ma ɗin iya cinya ne a saman riga kuma wata rabaja ce kamar zaren kwakwa. Kaina banda sarawa babu abin da yake,daga bayana na ji taku da sauri na mayar da hoton cikin akwati ina ƙoƙarin mayar wa. “Ayodele mi kike a nan?” Da sauri na miƙe na ce “babu komai Momah ” kallon tuhuma ta fara yi min amma na share tare da fito wa tsakar gida,zuciyata fal fargaba ‘wannan shi ne mahaifina? Wace ƙasa ce wannan ke shiga kamar ta arna? Sai yaushe Momah za ta kai ni gare shi? Ina son mahaifina’ duk a zuci na yi maganar kafin na zauna na kishingiɗa ga katanga.Wasu hawaye masu mugun ɗumi ne suka shiga sintiri a kumatuna, “na fita zuwa kasuwa sai na dawo” na ji muryar Momah ,na buɗe ido ina kallonta sarai ta ga ina hawaye amma ba ta tambaye ni ba ta fice. Ko mi ta tuna oho,sai ga ta kuma ta dawo “tashi mu tafi tare ” na miƙe na ɗauko kallabina na saka takalmi,sai da na wanke fuska sannan na fito.Momah ta rufe ɗaki da gida mu ka wuce kasuwa,tun da mu ka shiga nake jin tsikar jikina na tashi. Ina nan tsaye na ga wata yarinya na jaye da wani tsoho irin masu Bara a kasuwa,sai cewa take “a bamu sadaka saboda Allah da Annabi ” kafe su na yi da ido sun tsaya gaban wata mace mai sayar da busasar zogale. Cike da azama na yi tako ɗaya zuwa biyu na damƙe hannunsa,cike da mamaki yake kallona idonsa da suke a rufe ƙarya ce ba makahon gaskiya ba ne. “Mine ne za ka yi? Kan mi za ka saka hannunka cikin kwagirinta na kuɗi?” na tambaye shi,duk sai ya rikice ya ce “ki yi min rai ƴata,doli ce ta saka nake wannan ɗabi'ar ” “Kake damfarar mutane ba! A yadda kake duk wanda ya ganka zai ji tausayin ka amma ka yi amfani da maganin rufa ido ka na cutar bayin Allah ” Hawaye na ga su na zuba a idonsa ya ce “saboda na ciyar da iyalina ne amma ba da son raina nake hakan ba,amma na yi miki alƙawari daga yau ban sake wa” Na sakar masa hannu,abu guda da na fahimta kaf uwanda ke kusanmu babu wanda ya gani ko ya ji tattaunawar mu.Dube-dube na fara can na hango Momah da ɗan saurina na ƙarasa gun ta. Mun yi gaba kaɗan wani yaro ya faɗi gabana,cike da tausayi na miƙar da shi ina mai tambayarsa “mi kake ma kuka?” da hannu ya yi min nuni ya na magana amma ba ta fita saboda yadda kukan ya ci ƙarfinsa,hannunsa na ja mu ka shiga tafiya direction ɗin da yake nuna wa har mu ka isa wurin wani mutum. Na buɗe baki zan ƙara tambayarsa kawai idona ya sauka kan ƴar ƙaramar baro mai ɗauke da doya. Cikin dake wa na dubi mai sayar da doyar na ce “mi ka yi masa yake kuka?”banza yayi da ni hakan ya ban haushi na yi kururuwa duk mutane hankalinsu ya dawo kanmu wasu tuni sun zo su na tambayar lafiya. “Faɗa masu abin da ya faru” na cewa yaron,cikin ikon Allah yayi bayani yadda kowa ya ji “mu na tafiya ne ni da twin ɗina sai wannan mutumen ya kira mu ya ce mu zo mu karɓi chocolat sai ni na ƙi zuwa Amra ta je ta karɓa shine ta zama doya” “Laaaaha'ilah! ” duk kusan mutanen suka faɗa,amma mai doya ƙiri-ƙiri ya ƙaryata yaron ya ce “ka ji zai ƙulla min sharrin duniya,tun yaushe nake sana'ar sayar da doya a nan an taɓa kama ni ne? To nuna min ƴar uwar taka wacce na mayar” Cike da yarinta yaron ya je ya nuna ɗaya da ke can ƙasa,shi kuma mai doyar ya ɗauki wuƙa ya yanka. Da hannu na shiga taɓi na ce “a gaishe ka sarkin macuta na duniya,wato masanya ka yi to yanka wannan mu gani” na faɗa tare da nuna doyar da idona ƴar ƙaramar yarinya ce ƴar shekara huɗu.Muƙut ya haɗiye wasu yawu,cikin tsawa na ce “ka yanka aka ce ko kuma na kira ma ƴan sanda” Ya ƙanƙance ido zai yi magana amma mutane ba su basa dama ba saboda hantarar shi da suka fara kan ya yanka ko kuma su kashe shi.Hannunsa na rawa yasa wuƙa zai yanka na ce “ba nan ba” sai dai tuni ya yi wulish ya yanka nan jini ya fara tsirta.Kawai sai ya fashe da kuka,wani ya kira ƴan sanda a nan cikin kasuwa ya mayar da ita mutum wurin da ya yanka kuma kusan idonta ne. Ɗan kwalina na keta na ɗaure mata gun,ƴan sanda suka cabke shi kafin ƴan sanda su tafi da su suma don doli sai an kira iyayensu. Neman duniya na yi wa Momah amma ban ganta ba ,a doli na dawo gida. Bakin ƙofa na zauna ina zaman jiranta,kamar wacce aka mitsika na je na buɗe ramen da na saka Kambun Kunkuru.Har yanzu da ransa,sai dai ya ɗan gaji ya kuma ƙara girma.Na kuma mayar da shi a karo na biyu na rufe,ina nan zaune taxi ta tsaya .Momah ta fito,har muka sa kaya cikin gida ba ta ce min uffan wato fushi take da ni. “Mom...” “Yi min shiru! Wato ke ba za ki taɓa ganin abu ki yi shiru ba ko? Kaf kasuwa zancen ki ake ,ko kin yi tunanin ban san abin da kika yi ba? Na san yanzu zancen ya zo har nan unguwar shikenan sai a dinga kasa mu a faifai ana tallarmu duk irin gargaɗin da na yi miki amma kika yi fatali da shi kin kyauta!” ta na gama ta shige ɗaki. Duk jikina ne yayi sanyi,a fili na furta “in sha Allah daga yau ba zan sake shiga sabgar kowa ba,ko da kuwa ace ni ce za su cutar zan yi shiru su kashe ni ” Kamar yadda Momah ta yi hasashe kuwa hakan ce ta faru,zancen Ayodele ya cika unguwar tuni ma wasu sun fara zarginta da mayya.Dama ba su gama tantama akan al'amarin ceton Zeinab da ta yi ba.Yau kuma ta ceto yarinyar da aka mayar doya,tambayarsu ita ce inda a ce ba ta da ido uku ta ya aka yi har take fahimtar abubuwan da ke ɓoye wanda normal mutum bai gani? Wannan al'amari ya ƙara tunzura sauran Mayun da ke unguwar,tare da ɗaukar alwashin sai sun tozarta ta a bainar nasi. ★Washegari Yau juma'a ce,da baƙin cikin abin da A'isha ta min jiya na kwana duk tun a jiyar na yi ƙoƙarin kiranta na wanke ta tasss amma ban same ta ba. Ina isa asibiti na tarar da ita bakin ƙofa a tsaye jikin mota sai uban murmushi take zuba wa,da alamu sallamar Mansur ce za ta yi wanda shi kuma yake a zaune ya fiddo ƙafarsa ɗaya waje. Na danne zuciyata na ce masu “sannun ku da hira” in dai ganye bedi na magana to su ma sun tanka ni,tunani na yi ba su ji ba sai na yi tsaye na ce “duk soyayyar ce haka?” Mansur kawai ya dube ni shi ma bai yi magana ba ,ita kuwa A'isha ko waiwaye . Ganin irin cin kashin da suka yi min ya saka na shige cikin asibiti,na ja ƙyaci ina mai cewa “ai za ki zo ki tarar da ni ” “Ayodele lafiya kike magana ke ɗaya” cewar Fatimah,na ce “ A'ishah ce wai don ta na gaban saurayi ta yi banza da ni ” “Kai haba? Ni kuwa sai da mu ka gaisa har da shi Mansur ɗin” “Hum!” kawai na iya yi bisanin na je na aje jaka na saka farar rigar likitoci. Sai da mu ka yi nisa cikin aiki sannan A'ishah ta shigo,ina jin lokacin da Dr Jaleel ke yi mata faɗa kan ta zo lati sai haƙuri take basa. Cikin sigar wasa na zo daf da ita ina mai cewa “na zata har shi Dr Jaleel ɗin banza za ki yi da shi,ko da yake yanzu masoyin naki bai nan” wani kallo ta yi min ba tare da ta ce komai ba. Ni ma na kama gabana,ko lokacin cin abinci haka A'isha ta ware kanta duk yadda Fatimah ta so ta ja ra'ayinta amma ta ƙiya. Tun daga wannan rana mu ka fara takon saƙa da ita,tun mutane ba su gane ba har suka fahimta.Dr Haleema har zaunar da mu ta yi ta yi mana nasiha amma a banza ,haka zan yi ma A'ishah magana ita kuma ta basar.In muna zaune cikin jama'a sai ta bai wa kowa hannu in ta zo gare ni sai ta tsallake,tun ina yi mata uzuri har ni ma na aro rigar rashin mutumci na yaɓa ma kaina don dama can ni masifaffiya ce ta ajin farko. Yau saura kwana uku bikin ta,ina ji ta na bai wa Fatimah labari “Oga dai ya matsu a yi aurenmu,kin san a baya ya sha wuya sosai wurin soyayyata yanzu lokaci yayi da zai cika burinsa” Fatimah ta ce “ai ke ma ga shi sai zumuɗi kike,na matsu mu miƙa ki gidan Mansur ko hankalinmu ya kwanta” “Ai fa dai na matsu wallahi ” “Ayodele kin ji yaran zamani ko?” Fatimah ta sako sunana,ina jin lokacin da A'ishah ta ja tsuki. Ina cika takardu na ajiye na kalle ta na ce “da wa kike?” shiru ta yi ba ta ban amsa,na miƙe a hassale Fatimah ta sha gabana ta na cewa “don Allah ki yi haƙuri! Kin ga dai ba ta ce da ke take ba” “To da uban wa take?” “Ba ta dai ce ke ba, A'ishah don Allah tashi ki yi tafiyar ki tun da lokacin tashi yayi” cewar Fatimah,kamar jira take ta ɗauki jakarta ta fice. Sosai Fatimah ta yi ta danna zuciyata tare da roƙona kan na je bikinta na nuna mata ba komai ba ce duniya,bisanin ita ma ta tafi. Sai da na gama cika takardu sannan na fito. “Ƴan mata?” Da mamaki nake kallon shi na ce “kai ne?” “Eh wallahi na zo wurin abokina,ashe wannan asibitin kike aiki ?” “Eh! Wurin wa ka zo?” “Dr Jaleel mana,kin san abokina ne yanzu haka shi nake jira za mu wuce gidana” “Ok yayi” “Ba ki faɗa min sunan ki ba,tun ranar nan dai da na rage miki hanya na ji kin burge ni” karon farko da na taɓa jin haka daga namiji,sai abun ya ban dariya ban kai ga magana ba Dr Jaleel ya fito hakan yasa na yi tafiyata. Tun daga nesa nake tsinkayen yadda mutane suka yi dandazo a ƙofar gidanmu.Gabana tuni ya fara dakan uku-uku,ina iso wa wasu suka fara faɗin “Ga ta nan!” can kusan ƙyauren gidanmu na ga Momah a rakuɓe idonta sun yi ja jawur,kallon mutane kuwa tuni ya dawo kaina...... Mai son complete 800 ne via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [28/04 07:41] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Page 8 Da sauri na nufi Momah ina mai tambayar ta “mi ya faru? Lafiya kike kuka?” ba ta kai ga bani amsa ba na ji an wani jawo ni ta baya ,dakyar na iya miƙe wa kan ƙafafuna na juyo ina fuskantar shi.Namiji ne dattijo wanda ya ba shekara saba'in baya ,shi ne ya jawo ni yayin da sauran tsofin da suka haɗa maza da mata suka yo gaba. “Yau dai asirin ki ya tonu,shegiyar yarinya ashe mayya ce ke shi ne kika fake da sunan ceto kike.Wancan Kambun maitar da kika rufe shi muke so ki tono kafin Sarkin Mayu ya ƙara so ” ya faɗa ya na mai yin nuni da inda na rufe Kambun Kunkuru. Banda haske babu abin da wurin yake ,wanda a bayyane yake kowa na ganinsa har da normal mutane.A daidai wannan lokaci ba zan iya yin wani dogon tunani ba ballantana na samo mafita ,duk ma ba wannan ba halin da Momah ke ciki shi ya fi ɗagan hankali. Tsofin unguwarmu sai zagi ne suke a gaban jama'a, miyagun kalamai wanda duk mai zuciya ba zai iya jura ba.Sosai na yi mamakin dalilin da yasa ban ji sarawar kai ba ,saɓanin sauran lokuta da nake harzuƙa na ɗauki ɓoyayyar fuskata. A na haka har Sarkin Mayu ya iso,sosai na yi mamaki ganin mutumen nan da muka taɓa haɗuwa cikin taxi.Bayani suka fara yi masa,shi kuma yayi kamar bai taɓa gani na ba tare da umarta ta “je ki haƙo abin da kika ɓoye” Sai a lokacin na juya na dubi Momah,jiki a sanyayye na duƙa na buɗe ramen tare da ciron Kambun Kunkuru.Haskensa ya ƙara yawaita kan lokacin da yake cikin ƙasa,Sarkin Mayu ya karɓe shi ya na cewa “kin ji kunya ƴar ƙanƙanuwar yarinya da ke amma kin zama muguwa mayya kawai” da mugun sauri na rumtse ido ina jin hawaye na min zuba. Mutane ne suka fara suratai akan sai mun tashi mun bar masu unguwa,zagi kam ya fi cika buhu babu kalar baƙar maganar da ba a faɗa wa Momah.Ita kuka ni kuka,Sarkin Mayu ya ƙara ɗaukar magana inda yake cewa “na baku nan da awa ɗaya kacal ku tashi ku bar nan ko kuma na sa a ƙone ku da ranku” Jama'a suka ɗau ihu,da mugun sauri Momah ta shiga gida na take mata baya.A ɗaki na tarar da ita ta na gangamar kaya,rasa abin da zan ce mata na yi kawai sai na faɗa jikinta ina kuka. “Kukan mi kike? Ina ce ke kika saya mana wulaƙancin da kuɗin ki,tun ranar da kika zo da abin nan sai da na ce ki mayar mai shi abinsa amma kika yi kunnen uwar shegu da ni” ta ida faɗa ta na mai ture ni na yi baya. Daga inda nake ina jiyo hargowar mutane sai juya suke mana cikin gida tare da zaginmu.Cikin ƙanƙanen lokaci Momah ta haɗa kayanmu,dakyar da siɗin goshi muka samu mu ka isa bakin hanya.Ɗaiɗaikun mutane ne kawai ke tausaya mana,ciki kuwa har da Asabe don a gidanta ma Momah ta kai ajiyar sauran kaya. A wannan wunin mu ka bazama neman haya sai dai kamar abun tsiya ba mu samu ba,sai a wata unguwa mai ƙarancin mutane kamar za a fita gari shi ma ɗaki ne ciki guda.A haka dai mu ka share mu ka zauna bayan Momah ta kwaso sauran kayanmu. ★ Komai na ta tafiya cikin tsari, musamman bikin da ya kasance tuwona maina ne.Amayar da angon duk ƴan uwa ne,sosai abun ya tafi cikin tsari. A'ishah sai rawar kai take,abokanta kuwa duk sun haɗu wurin kanmu . Fatimah kuwa sai ƙoƙarin kiran Ayodele take a waya saboda rabonta da ita wajen kwana biyu wayarta ma ba ta shiga,cikin wannan zullumi dai ta yi shagalin bikin. Ranar ɗaurin aure tamkar babu gobe haka aka yi abun hauka musamman ɓangaren Mansur da yake taƙama da Nera.Motocin ɗaukar amarya kaf ɗinsu babu tsohuwa sun jeru rasss sai wacce ranka ya yi ma za ka shiga.A haka aka miƙa A'isha tamfatsetsen gidan mai kama da aljannar duniya,duk yadda ta so Fatimah ta tsaya fafur ta ƙi don dama kan babur ɗinta ta je ko kaɗan ba ta saki jiki da abokan Mansur ba don ƴan magana kan ce sai hali ya zo ɗaya ake abota. Bayan kowa ya watse Mansur ya shigo tare da abokansa.Kallo ɗaya za ka yi wa gizner jikinsu ka ga Nera ce ke magana,suratansu suka fara ita dai A'ishah ta na rakuɓe sai da suka matsa mata ne ta ɗan ɗage mayafinta.Amanar abokinsu suka bata bisanin yayi masu rakiya ya dawo shi ɗaya. “Ki sauko mu ci abinci mana” ya faɗa ya na mai jawo hannunta,cike da mamaki A'isha ta bisa har suka baje kan capet.Ta sha ji daga abokaina abu na farko da ake yi in an kai amarya sallah ce domin nuna godiya ga Ubangiji,amma sai ta yi masa uzuri da tunanin ko yunwa yake ji shi yasa.Ba ta kai ƙarshen mamakinta ba sai bayan da suka cika tumbinansu Mansur ya fara aika mata saƙonnin soyayya har ya kai da ya kusanceta,ko Bismillah ba ta ji yayi ba ballantana wai addu'a. Washegari Tsabar gajiya da ta yi ya saka ta rasa sallar asubah,hasken rana ne ya daki fuskarta ya sa ta yunƙura ta tashi zaune ta na kallon window.Gefenta kuwa Mansur ne ke ta sharar baccinsa,ta kai hannu ta na jijiga shi “Ogana ka tashi ka kai ni toilet ka min wanka please ba zan iya tashi ba” a shagwaɓe take fitar da harufan har ta ci nasarar tayar da shi. Ya buɗe idonsa ya zuba mata su ,iya kallon da watsa mata kaɗai sai da gabanta ya faɗi. “Mine ne?” “Wanka za min ” “Can a gidanku wa ke yi miki?” Ras gaban A'isha ya faɗi jin furucinsa sun yi hannun riga da wanda ya sha faɗa mata satin aurensu. Dakyar ta ƙoƙarta ta je ta yi wanka ta zo ta gabatar da sallah.Ta na nan zauna har Mansur ya tashi daga bacci,direct wurin drower ya wuce ya fitar da kaya masu kyau ya saka. “Ka manta ba ka yi wanka ba fa ” ta faɗa ganin bilhaƙi yake shirin,“uban waye ya faɗa miki manta wa na yi?” Mansur ya faɗa a zafafe ya na kallonta. “Ka yi haƙuri ”shi ne kawai abin da ta iya furta wa. “Ki tashi ki ɗora min breakfast!” ya faɗa ya na mai fesa turare. “To” ta amsa tare da tashi.Tsabar takaici sai da ta zubar da hawaye ,amma a haka ta haɗa masa frite da gasashen kifi don ta ga kusan akwai komai. Kan table ɗin cin abinci ta ajiye bisanin ta wuce bedroom,waya ta tarar da shi ya na yi sai magana yake cikin ladabi.Da ace mahaifinsa na da rai da to babu shakka za ta ce da shi ne yake waya. Bayan ya gama ne ya zo ya rungume ta tare da cewa “har kin gama?” kai ta jinjina masa,“ok mu je” Falo suka koma a tare suka ci abincin, Mansur na yi mata hirar soyayya hakan ya kuma ƙulle mata kai. “Zan tafi wurin aiki,tun ɗazu shugaba ke jirana” ya faɗa tare da miƙe wa tsaye. “Aiki kuma? A cikin satin aurenmu?” “To sai aka yi mi? Kin ga ban so sakarci sai na dawo” ya na gama faɗa ya fice. A'isha ta zube kan salon ta na jin wata irin damuwa na dabaibaye ta,tun kafin aje ko ina auren Mansur ya fice mata a rai.“Babu wankan janaba ballantana a yi maganar sallah anya kuwa na auru? Mine ne ma ya hana shi ko fuska da baki ya wanke?” ta furta hawayen takaici na zubo mata bisanin ta ɓingire bacci. Hayaniyar ƙawayenta ce ta tashe ta,sosai ta yi murnar zuwan su.Sauran kazar jiya ta ɗauko masu kafin a hau hira da girke-girke cike da nishaɗin ƙawarsu ta auri mai kuɗi kowacce ta sasaɓe zane ta ci abubuwa na kayan daɗi ta ƙoshi da za a tafi gida kuwa har da yin tsaraba. AYODELE Tun da muka dawo sabon gida Momah ke fushi da ni mai tsanani ,duk uban haƙuri da magiyar da na ta yi mata kanzil ba ta ce min ba.Hakan ya jefa raunatacen ruhina a cakwakiyar matsala,na bar cin abinci kan ƙa'ida,na kashe wayata aiki ma sam na bar zuwa.Amma hakan bai sa Momah ta tausaya min ba. Kamar kullum wuraren ƙarfe takwas na dare na fito ƙofar gida na yi zaune,unguwar tsit take ko tsuntsu babu. Wani mutum na ga ya bi ya wuce ta gaban ya nufi wani ɗan gangare,na bi bayansa da kallo kawai ina mamakinsa don yau kusan sau uku kenan da ina ganinsa. Zuciyata ce ta raya min na bi bayansa,kamar aikaka haka na miƙe har da haɗa wa da gudu na take masa baya.Mun yi tafiya mai ƴar nisa bisanin na tsaya,domin ya kai wurin da ke da tsananin duhu ba zan iya shiga ba. Idona ne ya sauka ga allon sanarwa mai ɗauke da sunan MAƘABARTA,gabana ya bada ras! ‘Ko shakka babu irin mutanen nan ne masu haƙo kabari don yi aikin asiri ko tsafi’ na faɗa a zuci ina mai ƙara ɗan yin gaba ina ɗigirgire ko Allah ya sa na hango wani abu.Daga bayana na ji an dafa kafaɗa,da mugun sauri na juyo muka haɗa ido a take hanjin cikina suka hautsana..... [28/04 07:43] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Page 9 A lokacin da na juyo na fuskance shi,a sa'ilin ne kuma na tantance fuskarsa duk da ƙarancin haske da ke wurin.Fuskarsa baƙa ƙirin ce mai ɗauke da ƙwalayen idanuwa babu komai sai gurbinsu da ya bai wa jini damar gangaro wa kan lamutsatsun kumatunsa. Zuciyata ta fara rawa,hankalina ya tashi farashin tsorona ya ninku ainun ina ta ƙoƙarin cira ƙafata sai dai bai bani damar ba domin kuwa tamkar an dasa ni haka nake a tsaye ƙiƙam. “Mi bil'adama yake a duniyarmu?” ita ce tambayarsa. Gabana ya ƙara bada wani sautin rasss,tsabar firgici ban san lokacin da na furta “Ayodele yau kin ɗebo ruwan dafa kan ki” “Ayodele? Ayodele?” ya maimaita sunan har sau biyu cike da mamaki,bisanin ya ci gaba da cewa “ƴar sarki Lassey?” A daidai wannan gaɓa samaniya ta ɗauki wani irin rugugi da kuma wata irin walƙiya. Da sauri na lumshe ido jin saukar ruwan sama,wanda suka zame min tamkar wankewar tsoron da ya aure ni.Ji na nake kamar ina kan gajiyar izzata wacce nake juya gawa tare da yin magana da su ba tare da na ji tsoro ba. Na ji saukar hannunsa akan kafaɗa a karo na biyu,“barka da zuwa duniyar ababen bauta,haƙiƙa ƙarfin ruhinki da nacinsa ya jawo ki izuwa nan.Zo ki yi ziyara gun dangin kakannin ki” Na ware idona,a yanzu kam ban san mi ya shige ni ba sam ba na jin tsoronsa haka fuskarsa ma ba na ganin muninta. Tamkar raƙumi da akala ya yi min jagora izuwa tsakiyar maƙabartar wacce take maƙil da kaburbura. Wasu sanaye ya shiga ambato dukkanninsu babu ɗaya na musulmi,kamar almara sai na fara ganinsu su na fito wa daga cikin kabarinsu su na yin zaune. Gabatar min da su ya fara ɗai baya ɗayan har aka kawo kan wani tsoho ya nuna min shi da hannu ya ce “kin ga wannan shi ne kakan ki Sarki Octbar,shi ya haifi mahaifin ki Sarki Lassey,waccan kuma da kike gani Yayar baban ki ce sunanta Déborah bayan ta sauka daga mulki mahaifin ki ya hau.Je ki gare su na san za su baki saƙo ,bayan nan sai na kai ki gun ababen bauta” Gun wanda ya kira da Kakana na je na yi tsayi,hannuna ya kama bai yi magana ba sai jimƙe shi kawai da yayi.Tamkar yadda ake turan abu a xender haka na fara jin sabbin abubuwa na ratsa jijiyoyin hannuna su na shiga magudanar jinina wanda don dole na lumshe ido. Ya na sake min hannu ya shige ƙarƙashin ƙasa,“ungo wannan zoben ki saka shi,na san komai daren daɗewa za ki je Victoria Falls duk da mahaifiyar ki ba ta so.In kin je ki gaishe min da ƙanena ” Déborah ta faɗa ta na saka min wani tsobe a yatsana manuniya na hagun. “Mu je” na ji muryarsa, “André kar ka kaita ko ina ka mayar da ita duniya,a halin yanzu akwai tazara mai ƙarfi ita da karagar mulkinta.In lokaci yayi ababen bauta su za su neme ta da kansu,amma mi zai hana ka nuna mata ababen tarihin shahararrun matsafa da kuma yadda suke wanzar da tsafin?” Sai da ya dube ni da kyau bisanin ya jinjina kansa , Déborah ta ɓace ma ganina a kuma daidai wannan lokaci na tsinci kaina cikin wani hatsabibin daji.Na fara waige-waige,wani irin “wuhummm! Zummm!” nake jin ma'adanar sautina na zuƙo min ai kuwa na toshe kunne,ashe hakan shi ake kiran ainahin ga wofi wai harare cikin duhu don hakan da na yi bai canza zane ba. “Haƙuri za ki yi da sannu za ki saba”cewar André ,bisanin ya shiga nuna min wasu itatuwa wanda suka fi ɗaukar hankalina su ne wanda suke jere su uku an yi masu ado na penti masu nuni da kalolin tsafi da asiri (mai son ƙarin bayani ya nemi littafina na ƳAN ƘUNGIYAR ASIRI) Mun yi yawo sosai sai bayanin abubuwa yake min,cikin haka ne na shagala sai ji na yi na yi baya.“Kar ki bi ta nan...” yayi saurin faɗa sai dai tuni na ɗora ƙafata ɗaya wacce nake jin kamar a garwashin wuta take.Tsabar azaba ban san lokacin da na fasa ihu ba,kaina ya juya daga nan ban sake sanin abin da ya faru ba. “Ayodele keee ?” muryar Momah ta daki kunnena,na ja ajiyar zuciya tare da buɗe idona dakyar da suka min nauyi. “Lafiya kika kwana a titi? Wato ƙofar gida shi ya fiye miki kan ki kwanta a ciki?” Momah ce ke faɗa rai ɓace. Kallon wurin da nake na yi,eh a dai ƙofar gidan ne nake zafin rana na haske ni.Dakyar na yunƙura na tashi tsaye,ƙafata ta dama ce na ji ta riƙe “washhh! Wayyooo Momah ” na faɗa hawaye na min shatata. Abun ka ga uwa tuni ta haɗiye ɓacin ran ta fara taimaka min,dakyar na shiga gida kuka wiwi nake rera wa ita kuma ta na tambayata abubuwan da na yi jiya.Sam ban iya tuna wa ba,to ina ma na ga nutsuwar da zan tuna ɗin. Jiƙe-jiƙen magani ta yi ta bani na yi wanka,babu laifi na ɗan ji dama musamman da ta saka min maganin massage abokini ta min tausa.Wunin ranar dai na dawo ƴar lelen Momah kamar can farko,duk fushin da take da ni ta janye. “Allah sa dai ba jan magana ki ka je ki ka sake yi ba! Na sha faɗa miki ba komai ne mutum yake magana ba,haka ba kullum ya zama dole sai ka yi taimako ba.Amma ba ki ji,kunnen ƙashi ne da ke ! Duba ta dalilin ki inda mu ka dawo,da ace kin zauna ɗam da duk hakan ba ta faru ba” Sama-sama nake jin furucinta don tuni na lula duniyar tunani,wanda ba na komai ba ne sai na mutumen nan mai suna André duk abubuwan da suka faru kuma suka dawo min daram a kwanya sai dai ban san ya aka yi na tsinci kaina ƙofar gida ba. Na ja a jiyar zuciya ‘ta yi yu kuma mafarki ne na yi’ na faɗa a zuci bisanin na lalubo wayata,na kunnata saƙonnin Fatimah da kiranta ne barkatai na yi ta cin karo da su. Kiranta na yi,har sai da ta yi ajiyar zuciya wacce nake kyautata zato ta murna ce. “Wallahi duk kin tashi hankalina,kin kashe waya na je gidan ku kuma kun tashi har wasu sun shiga” cewar Fatimah. “Yi haƙuri ƙawata tashin ne ya zo cikin wani yanayi,ya aiki kuma ku na ta zuwa?” “Ina ta dai zuwa! A'isha yau wajen kwana nawa rabonta da aiki,kin san kuwa Dr Jaleel ya karɓi lambar ki wurina” “Hum! Wasa dai kike,kuma sai kika basa?” “To ya zan yi?” ta faɗa cikin tausayi,tuni na fahimceta don na daɗe da sanin Fatimah na mugun son Dr Jaleel. “Oh! Na gane yanzu haka abokinsa ya tambaye shi,ban faɗa miki ba wani ya rage min hanya kwanaki har ya ce na burge shi wai” Fatimah ta saki ranta,ta ce “wai ne ma? Don Allah Ayodele ki yarda ki fara soyayya a yi mutum kamar jikar almutsutsai” Shiru na yi ,tunanina ya koma duniyar da na je jiya sai na ce mata kawai “Fatimah zan sake kiran ki” ƙittt! Na kashe kiran. So nake na tantance shin wai mafarki na yi ko kuwa gaske ne,ina ta tunanin hanyar da zan bi na gaskata cikin ɗaga murya na ce “Lassey!” Ji kake kwacaaaa Momah ta saki kwandon kwanoni da ta gama wanke wa,dama da gangan na yi don na ga réaction ɗinta. Da sauri kuma ta shiga kwashe su jikinta har rawa yake,na kuma furta “Lassey fa?” sai na yi tamkar waya nake,ina ankare da Momah a wannan karon ma sai da ta zabura.Na saki murmushi na ce “to Allah kyauta sai an jima” Duk motsin Momah a wannan ranar kan idona,ta yi wani irin sanyi liƙis abinci ma dai ban ga lokacin da ta ci shi ba.Sai na ji ta ban tausayi,kusa da ita na ƙarasa ina ɗingishi.Na kwanta tare da ɗora kaina kan cinyarta na ce “Momah gobe zan koma aiki” “Allah kai mu” shi ne abin da ta faɗa ta na cire hullar kaina,“sabon kitso za a yi min?” “Eh na gwara na rufa ma kan naki asiri je ɗauko mai da tsinke da kuma mashaci” Hakan kuwa aka yi, Momah na min kitso ina ji lokaci zuwa lokaci ta na ajiyar zuciya haɗi da “hum” can ta kasa haƙuri ta ce “Ayodele ɗazu ke da wa kuke wa?” “Fatimah ce” “Na yi tunanin musulma ce fa,sai kuma na ji ki na ambaton sunan mahaifinta irin na Kirista” Na gane sarai da Momah wayo take son yi min don ta ji gaskiyar lamarin,amma da yake ni ma hatsabibiyar kaina ce sai ce mata na yi “wane suna kuma?” “Wai ina A'isha ? Har an yi bikin?” Momah ta canza zance,na lumshe ido na ce “bacci nake ji” na yi hakan ne don ɓoye mata abin da ya faru tsakanina da A'isha don za mu iya shirya wa ko da yaushe ,amma in na sanar da Momah ta yi yu ta riƙe abun a rai. ★MANSUR Ya na fita daga gida ya wuce can gidan ogansu,bayan ya gaishe shi ne ya gayyace shi can tamtsetsen falonsa mai ɗauke da hatsabiben aljannu.Ka na ganin wurin za ka gane babu rahama,saboda komai na ciki baƙi ne wuluk hatta da capet da labulaye da kujeru. Bayan sun zauna sun nutsu ogan ya fara bayani “Mansur ƙarshen watan April za ka kawo sacrifice ɗinka,budurcin mata huɗu,sai zuciyar jinjirin yaro sabuwar haihuwa” Hankali tashe Mansur ya ce “oga a ina zan samu jinjiri? Su ƴan matan ba matsala ba ne saboda ina da gumbar susa,ga shi kuma watan Valentin Day ne ba za su wuya ba amma oga saboda Allah....” “Noooo! Bar kira min sunan shi cikin falo! Wa ya faɗa maka muna buƙatar rahama a nan da za ka kira abun bauta ?” Mansur ya kalli ogan nasu da kyau,ƙaton Arne ne mai yaƙi da Musulunci abin da ya fahimta bai son jin sunan Allah tsabar taɓe wa. “Sorry oga! Amma please a duba min a ina zan samu jinjiri?” “Wannan ba matsalata ba ce,sannan abu na gaba ba za ka yi wanka ba sai ka tara janaba sau talatin da tara” ogan ya faɗa cikin bagwariyar Hausar shi. Mansur ya waro ido,dama yau ɗin ya ƙi yin wanka da Sallah ne a bisa sharaɗin ogansu. “A dai duba oga! Yanzu haka ji na nake duk a takure da ban yi wanka ba” “To maganar kake so sai kuma ka je ka yi wankan ka ga abin da zai faru da kai! Tashi ka bani wuri” Da mugun sauri Mansur ya fito,a kan hanya sai tunani yake kan mafita cikin haka kiran Momynsa ya shigo “Allo Momy?” “Na ce sai yaushe za ka zo ka ɗauke ni ne tun jiya na haɗa kayana” ta faɗa daga can ɓangaren. “Gani nan zuwa Momy ” sai ya kashe kiran ya je can gidan mahaifansa. Bayan sun gaisa ta basa fura ya sha sannan ya ɗauki tulin kayanta ya saka bayan mota,wasu ma a gidan baya ya zuba su.Ta shiga gaba suka wuce gida,ya na parker mota A'ishah ta fito da ɗan gudunta irin na sabbin amaren nan amma sai ta tsaya cak ganin Mansur ya zagaya baya na fiddo kaya ,Momy kuwa hannunta riƙe da uwar jaka sai ka ce mai biki. Wani zungureren bido ta fiddo ta shiga yayafa ruwan da ke ciki a tsakar gida ta na yi ta na yin wasu surkullenta. Babu shiri A'isha ta koma ɗaki jikinta na rawa,babu sallama duk suka shigo.Rasa mi za ta ce ta yi kawai ta yi tsaye su na ƴar kallon-kallon,“laaa! A'isha ko ba ki gane ni ba ? Ni ce Mairo Yayar Tani uwarki kin wani yi tsaye kin tare hanya ko ba ki so na zo ba ni da gidan ɗana ” “Momy ai zuwan ne na ga kamar ba na lafiya ba har da kayan jiki sai ka ce wacce za ta dawo nan da zama?” ba ta rufe baki ba Mansur ya zube mata yatsunsa biyar tare da ɗora mata kwandon masifa. Momy ta yi murmushi ta ce “yaro man kaza! Wato A'isha duk wulaƙanci da ku ka yi mana ke da uban ki duk kin manta? Bai da kuɗin aure ƴata karatu za ta yi ba zan sayar da Akuya ba ta dawo gida ta na ci min darni ba” Momy ta kwaikwayi muryar Abban A'isha . Mansur ya ɗora da nasa furicin “daga rana irin ta yau doli ki yi duk abin da Momah ta saka ki saɓanin haka ki saka a ran ki kin ƙulla aure da ƙunci” ya na gama faɗa ya nufi ɓangaren da dama tun can na Momy ne,ita kuma ta take masa baya. A'isha ta faɗi gwaram ta yi zaman ƴan bori ta na jin wani matsanancin tashin hankali.... [28/04 07:45] MRS SADAUKI: *FARAUTAR MAYU* Last free page 10 A'isha na nan zaune cikin halin ƙaƙanikayi Momy ta fito Mansur na bayanta.Kan salon ta hakimce ta sune ta tare da cewa “ A'isha ruwan gidan ma ba za a bani ba sai na roƙa ko kuwa ban isa ba ne?” “Haba Momy ya za ki ce haka? Ai ko ban auren Mansur ke ɗin uwa ce gare ni domin ciki guda kuka fito ke da Mamana ” cewar A'isha ta na mai tashi da sauri har jikinta ke yin rawa ta nufi kitchen. Drinks da abinci ta haɗo mata,ta dire su a gaban Momy sai bayan ta zuba mata komai ne ta tashi ta shige bedroom.Matsanacin kuka ya kubce mata,ta faɗa kan gado ta rusa shi cincin ƙarfinta. Mansur ya shigo,“ A'isha?” ya faɗa cikin sanyin murya kamar ba shi ne ya ga ma yi mata tsawa ba. Ba ta daina kukan ba ballantana ta kula shi,ya isa gare ta ya na mai jawo ta jikinsa ya shiga aikin rarrashi amma ta ƙi yin shiru .Sai da Mansur ya kai ruwa rana sannan ya shawo kanta,ashe shi ma da walakin wai goro a miya.Buƙatarsa ce ta kawo shi,kuma ko da ya samu abin da yake so ya bar ta nan. Cike da baƙin ciki A'ishah ta isa toilet,abu ya tare mata goma da gomiya tara. Kamar wata zararriya ta shiga dukan ruwa ta na cewa “da me zan ji? Wace rayuwa na tsoma kaina ni A'isha? Wayyo Allahna!” sai ta ƙanƙame dukkan jikinta jin tamkar ana kallonta . Ƙoƙarin fita daga bawon wankan ta fara,sai dai tamkar wacce aka jone fatar jikinta da bawon haka ta ji ta liƙe gam.Cincin ƙarfinta ta buga wani uban ihu wanda ya karaɗe duka gidan,sai dai ko motsin wucewar ɓera ba ta ji ba ballantana Mansur ko Momy su kawo mata agaji. Dakyar ta ci nasarar fiddo ƙafafunta waje,sai ta ga su yin wani ja ƙau jawur babu kyawun gani kamar jan nama.Hankalin A'isha bai ida tashi ba sai lokacin da Allah ya bata iko ta tashi kan ƙafafuwanta.Kaf shap ɗinta ya zube kamar an zuba sukari a ruwa,jikinta ne ya ɗauki wani irin rawa ganin ƙugunta kamar muciya saɓanin da can farko da take turbakallah. Towel ta saka ta fito da mugun sauri,bayan Momy ta gani ta na mai fita daga ɗakinta ba tare da ta san mi ya kawo ta ba. Bakin ƙaton madubi ta tsaya ta na kallon kanta,sai kuma ta ganta normal ba ta san lokacin da ta saki ajiyar zuciya ba.“Ashe gizau ne ban canza ba” ta furta cikin murna bisanin ta shafa mai da turare,ta saka kaya sai kuma ta fito falo. Turus ta yi ta na kallon Momy na yayafa ruwa a duk wata kusurwa ɗaki,ba abin da ya fi bata mamaki irin sunanta da na Mansur da ta ji ta na ambato. “In kin gama gulmar sai ki je ki yi abin da za ki yi” cewar Mamy ba tare da ta juyo ba. ‘Ko ya aka yi ta san na fito?’ A'isha ta tambayi kanta bisanin ta wuce kitchen.Girki ta ɗora ,bisanin ta dawo falo ta ɗauki wayarta.Fatimah ta kira,cikin sa'a ta same ta tamkar rariya haka A'isha ta buɗe baki ta na ba Fatimah labarin abin da ya faru da wanda ma ke kan faruwa ba tare da ta san babban kuskure ta aikata ba. Da dare Mansur na dawo wa ya shiga ɗakin Momy,bayan ya gaisheta ne take ce masa “ɗazu matarka ta kira wata mai suna Fatimah ban san ya suke ba,amma kaf sirrin gidanka ta sanar da ita na mu'amalar ka da ita .Hum! Ni kuwa cewa ta yi jarababiyar tsohuwa ko amarci ba ku gama ci ba na zo na tare muku a gida” Ran Mansur ne yayi bala'in ɓaci ,ya tashi da sauri ya fita.Ya na shiga ɗakin ya tarar da A'isha ta zanzare ta ci uban ado,tuni ya manta abin da ma ya kawo shi ya je ya rungumeta. Gabanta ne ya faɗi lokacin da Mansur ke ƙoƙarin yi mata kiss saboda wani uban wari da bakinsa ke yi,warin hammatarsa kuwa ko bunsuru albarka .Amma a haka ta daure suka raya sunnah,cike da kula wa ya dube ta ya ce “daga yau kar na sake jin kin fitar da sirrina ,ko Momy ba ta faɗa min ba zan gane wa” A'ishah dai ba ta ce komai ba ,zai lokacin da zai mayar da kaya ta ce masa “don Allah ka je ka yi wanka” “Ba zan yi ba” ya bata amsa a takaice. “Ko brush ka yi” Mansur yayi saurin juyo wa ya na ƙare mata kallo cikin ido,‘ko dai maganin da na bata har ya karye ne da har ta ke iya faɗa min magana kai tsaye babu ɗigon tsoro?’ ya yi wa kansa tambayar a zuci. “Ka yi haƙuri don Allah ” ta faɗa a ɗan daburce bisanin ta shiga toilet ta yi wanka. Ɓangaren Momy kuwa shiru har yanzu ba ta ji ihun A'ishah ba ,ta yi zaton shegen duka Mansur zai lakaɗa mata.Ganin haƙar ta ba ta cimma ruwa ba yasa ta tashi ta rufe ƙofa da key,kayan jikinta ta cire ta ɗaura wani jan ƙyalle a ƙugu. A cikin jakkar kayanta ta fiddo wata ƙaramar tukunyar laka mai ɗauke da layu da sauran abubuwan shirka sai kuma wani bokitin roba fari mai ɗauke da korayen ruwa,nan ta fara yin surkulle a nan take hayaƙi ya turniƙe ɗakin ba ka jin komai sai hucin narkeken kwaɗo da kukansa. Ta ɗauki lokaci da dama bisanin ta tsaya,murmushin mugunta ɗauke a fuskarta ta ce “ A'isha tun da ki ka yi sanadin shigar ɗana ƙungiyar asiri wallahi ke ma sai na gulala miki,sai kin gwammaci kiɗi da rawarki.Da ni da ke shege ka fasa” ta gama faɗar haka ta buɗe bokitin nan fa kwaɗon nan ya yi tsalle ya fito kamar mai jira. Shegun idonsa tulu-tulu sai faman juya su yake ya na ƙoto.Ba tare da jin tsoro ba Momy ta shafi kansa ta na mai cewa “na wakilta ka a matsayin mai ɗaukar fansata,ina so ka fitini A'isha cikin mafarki da kuma zahiri ka zame mata hawainiya ka na sauya kala kamar yadda aka bani Kambunka” ta na zowa daidai nan ta furta wasu surkulle a take ya ɓace bai bayyana ko ina ba sai a ɗakin A'isha. Ta na zaune kan gado kunnenta maƙale da waya ta na cewa “wallahi Fatimah in faɗa miki har yanzu ma Mansur ya ƙi yin wanka,ban san dalili ba in kuma na yi magana ya yi fushi” Can ɓangaren Fatimah ta ce “to ke kamar ba mace ba,ki rasa dubarar da za ta sa yayi wankan? Kawai ki bari sai ya na kwance ki cika bokiti da ruwa ki zuba masa ai doli ya yi wankan ” “Katifata ta jiƙe?” “Ai ta na da leda” “Ok to zan jarraba na gani” sun yi hira sosai bisanin ta kashe kiran, lokacin ƙarfe takwas na dare bai gota ba. A'isha ta sauko ƙafarta ƙasa da niyyar zuwa toilet sai ta ji wani bala'in sanyi tamkar ƙanƙara,“innalillahi!” ta fusrta da mugun sauri a take kuma ta ji normal . Toilet ta shiga ,ta hau WC kenan ta fara jin kukan kwaɗo ta saki ihu ta fito a guje sai kuma ta ci karo da Mansur ya shigo. Ko tambayarta bai yi ba lafiya take ihu ya zube kan bed,saboda ya gaji sosai ya sha yawo a gari ko zai samu ƴan mata huɗun da aka buƙata sai dai ko guda bai samu ba. Baccin da ya fara da ninshari ya saka A'isha da ke can takure saurin dubansa,shawarar Fatimah ce ta zo mata a kai.Da mugun sauri ta fita waje ta ciko bokiti da ruwa ta malala masa a jiki.Hargowar da ya yi ya saka A'isha sakin bokitin ta na mai dafe ƙirji. ★AYODELE Duk yadda na so in danne muradina akan sanin tarihina kasa wa na yi.Bayan mun gama cin abincin dare na ce “Momah wai mine ne sunan Abbana? Na ga ko lokacin da na yi makaranta Ayodele kawai ake kira na” shirun da ta yi ya saka ni ci gaba da cewa “ko dai shegiya ce ni banda uba?” “Da ubanki Ayodele! Jarumi mai zubar da maza ko a fagen yaƙin wasa.Ke ɗin sauraniya ce ɗaya tamkar dubu,a kaf cikin ƴaƴansa maza da mata,manya da ƙanana ke ce ƴar baiwa” Momah ta faɗa wanda a ƙarshe sai da ta saki murmushi. “To ya na ina? Mi yasa ba mu rayu a tare ba?” “Don na tseratar da ke daga uƙubar da ababen bauta ke shirin tsoma ki yasa na gudo” ta bani amsa ta na mai kallon cikin idona, ta ci gaba da cewa “ko da na ji kin ambaci sunan Lassey na fahimci lokaci ya yi da za ki san tarihin ki,sai dai fa ba komai zan sanar da ke a yau ba sauran sai ranar birthday ɗin ki” Cike da jin daɗi na matso, Momah ta saki murmushi wanda a cikinsa ina iya hango tsantsar farin ciki wanda ban san mi ya wanzar da shi ba sai dai na fi alaƙanta shi ƙila ta na son mahaifina irin sosai ɗin nan. Sai da ta jawo ni jikinta kamar wata ƙaramar yarinyar,kaina na kan cinyarta hannunta kuma na shafa ƙananun kitson da ta yi min. Momah ta ce “kamar yadda na shaida miki ke sarauniya ce to mahaifin ki shi ne Sarkin Victoria Falls inda ya gaji sarautar ne a hannun Yayarsa na manta sunanta ” Da mugun sauri na ce “ Déborah ” ambaton sunan ya saka ƙwan lantarkin ɗakinmu fashe wa ji kake ɗuuuu. Momah ta zabura ta miƙe tsaye,“wa ya faɗa miki sunanta? Wa ya ce miki ana ambaton sunanta a ko ina? Da na ce miki na manta a tunanin ki gaske manta war na yi?” Momah ke faɗa cikin wata irin murya wacce ba ita na santa da ita ba,idonta kuwa wani irin haske suke fitar wa kamar an kunna glov har wani canza kala suke. Jikina ne ya ɗauki rawa ainun, musamman da ƙofofin gidanmu suka fara yin wata irin buga wa su rufe kansu su buɗe ji kake faaa-faaa! Rufin ɗakinmu kuwa kamar zai kware har ɗaga wa sama yake,wata da ban manta inda na ɗora ta ba na lalubo tare da ƙoƙarin kunna fitila ita ma ta yi bindiga ta fashe har ɗiyan hanjinta da garin batirinta na ji a hannuna. Tashin hankali,gobarar gemu Momah ta canza Yare ta shiga suratai.In ba gizau idona ke min ba wasu fararen siffofi ne ke faman shigo wa ɗakinmu tamkar duniyar fatale......... A nan kawo ƙarshen free page,duk wacce ke son complete za ta biya 800 ta akwatin nan 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank sai ki tura shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 MRS SADAUKI NIJAR 🇳🇪 [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCRW☀️ ____________________________________________ 01 Cikin duhun dusar ƙanƙara wata mata mai ƙusumbi ke ta ɗangala sanda cikin sauri har ta isa wani ƙaton kogo mai cike da hayaƙi kamar an yi gobara.Tana shiga kogon ya fara rawa yana fitar da wani sauti,baƙin bargon da ta luluɓe kanta da shi ta sauke kan kafaɗunta hakan ya bayyanar da shafafar fuskarta wacce babu ido,babu tsinin hanci sai iya baki kawai.Bakinta ta buɗe tana yin wani gurnani mai fitar da magana cikin wani yare na ƙarnin baya “ uleja naho kajulu ramhakaya fyayal!” cak kogon ya tsaya da rawar da yake tare da ɗaukar wani irin shiru kamar mutuwa ta ratsa,babu jimawa kuwa wasu fararen halittu suka fara shawagi ko ta ina. Da sauri ta zube kan gwiwanta tana mai buga gundulalun tafukan hannunta a ƙasa tana mai daɗa furzo wasu kalaman. “Za ki iya gabatar da abin da ke tafe da ke” wata murya ta ratso iska ta bata umarni. “Naomi!” ta furta cikin rawar murya. “Alƙaluman doka sun riga da sun ƙafe babu wani canji da za mu iya yi miki” aka bata amsa. “Ita ɗin yarinya ce ƙarama ƙwaƙwalwarta ba za ta iya ɗaukar wannan hatsabibin tashin hankali ba” tana gama rufe bakinta wata tukunyar ƙasa ta faɗo a gabanta ,“ki bata waɗannan ruwan ta sha daga nan komai zai tafi kan tsari” Tukunyar ta ɗauka kafin ta gyara luluɓinta sai kuma ta fito,bai wuce tako uku da ta yi ba sai ta furta wani furuci wanda ya haifar da wata hatsabibiyar guguwa tashi ta zo ta zagaye ta tana fitar da wani iska,sannu a hankali guguwar ke daɗa yin sama da ita a haka ta ɓace ɓat kamar walƙiya ba ta bayyana ko ina ba sai a ƙofar gidanta. Ina zaune ina ƙulla garin magunguna na ji motsi,da sauri na ɗago kai sai na hangi Maa na daidaita rufin ƙyauren gidanmu.Murmushi ne ya wanzu a fuskata ba tare da na ce mata komai ba na ci gaba da kallonta har ta ƙaraso ta zauna kusa da ni tana mai miƙo mini tukunyar hannunta.Na karɓa,sanyin haɗi da wani shock suka ratsa ni yayin da na ji kwaɗayin shan ruwan ciki.Baki na kafa na soma shan abin da ya kasance a ciki don sai bakina ne kawai ya iya tantance mini kallon kitse na yi wa rogo don kuwa ba zallar ruwa ne ba. Ina ajiye tukunyar sai na ji tamkar wacce aka yi wa wankin ƙwaƙwalwa,wasu abubuwa da suka keɓancin mahaifiyata nake son sani. “Maa me yasa ake kiranki da mayya?” “Saboda ababen bauta sun mallaka mini baiwar da ta keɓanta da ta sauran mutane” “Kina nufin makantar ido?” “Eh! ” “Amma ai kina gani duk da babu gurbin ido a fuskarki ” “Naomi??” muryar ƙawata ta katse zaren tambayoyin da nake yi wa mahaifiyata wacce ta kasance jigona,bango abin jiginata. Miƙewa na yi da sauri ina ƙara gyara zaman fatar dabba wacce ta suturta tsaraicina ina mai duben Debora wacce ke sanye da wani tsohon bargo duk ta yane jikinta da shi.Murmushi ta sakar mini kafin ta yi mini alama da hannu,Maa na duba ina mai cewa “zan yi wa Debora rakiya ne” “To kar ki jima saboda lokacin zuwa farauta ya kusa” Maa ta bani amsa,ba tare da na ce komai ba na kama hannun Debora muka fito ƙofar gidanmu wanda ya kasance na kara. “Ya meke labari?” na tambaye ta . Kamar munafuka ta yi ƙasa da murya ta ce “zo mu je na nuna miki wani abu” sai kuma ta fara ɗan gudu-gudu tana nufar bayan gari yayin da ni kuma nake take mata baya har muka isa bakin Teku .Da wani irin kallo na bi ta da shi ina mai cewa "me kuma za mu yi a nan?” Da hannu ta yi mini nuni da can tsakiyar ruwa,sai dai sam ban ga abin da take son nuna mini ɗin ba.Lura da hakan yasa ta ce “yi kamar za ki rufe idonki” hakan na yi na lumshe manyan idona kafin na ɗan buɗe su a hankali sai a lokacin na ga wani abin mamaki wanda tunani da hankali ba za su ɗauka ba.Dogon tsani ne a cikin ruwan tare da shata wata doguwar hanya da alamu za ta ɓulle a wani wurin.Umarnin zuciyata ƙafafuwana suka bi ba tare da na shirya hakan ba na ji sanyin ruwa ya ratsa ni.A hankali nake tafiya har na isa kan tsanin na fara taka matakalansa sai dai ban fi tako uku ba na ji kamar an tunkuɗo ni sai ganina na yi a wani wajen na daban ko kuma na ce wata duniyar wacce ta sha banban da wacce na taso na tsinci kaina a cikinta. Wasu halittu ne masu irin siffata sai dai yanayin launin fatarsu da kuma shigarsu ya sha banban da irin ta duniyarmu.A karon farko da na ji tsoro,don ban taɓa ganin irinsu ba .Ƙafata ta hagu na ɗan mayar a baya ina kallon yadda wani mutum ke musayar wuta shi da maƙarabansa,ina daf da na koma cikin ruwa muka yi ido huɗu da shi hakan ya haifar mini da matsanancin faɗuwar gaba tare kuma da rikicewar tunani.Mun shagala da kallon juna ,ƙarar wani abu da ban san me ake kiransa ba ya dawo da ni hayyacina.Sai da na yi dogon nazari sannan na fahimci cewa ta cikin ƙirjinsa ne aka halba masa abar kashe mutane.Faɗuwa yayi ƙasa,wanda hakan ya jawo hankalin tawagarsa kusan su duka na ji sun ce “yalaɓaiii?” kafin su yo kansa,ɗaya daga cikinsu ne ya zube ƙasa tare da ɗora kansa kan cinyarsa yana mai cewa “Naslam?” cikin tashin hankali yake kamar yadda fuskokin sauran suka bayyana. Abokan adawarsu ne suka fara yi musu sarƙa suna gargaɗarsu da su miƙa musu wannan mutumin kawai suke buƙata in kuma sun ƙi za su kashe su duka su tafi da shi. “Rayukanmu fansa ne akan shugabanmu babu gudu babu ja da baya don haka dakaru ku juya ku fuskance su” shi ne abin da ya faɗa yana mai shimfiɗe Naslam ɗin. A wannan gaɓar ce na ga wani al'amari mai shige da irin rayuwarmu ta can duniyar,yadda su mutanen da ke neman ran Naslam duk suka wani zazzalo harshe waje suna sarrafa shi,kafin ƙyaftawar ido sai gawarwaki nake gani suna faɗuwa. Idona na ji suna yi mini ƙaiƙayi ,babu jimawa suka furzo da wani hatsabibin haske wanda ya tarwatsa taron Mayun duk suka faɗi babu rai sai ɗaiɗaiku ne suka gudu. “Naomiiii?” na ji muryar Debora tana kirana daga ta can ɓangare,kamar kifi haka na faɗa ruwa na koma duniyarmu.Ko da na fito daga cikin ruwa jama'ar gari na tarar duk sun cika wurin suna jiran fitowata.Ko kaɗan babu wani damshi ruwa a jikina a bushe nake ƙamas,sai dai a akwai banbanci tsakanin lokacin da na shiga da kuma yanzu da na fito.Kaf illahirin jikina ya rine yayi baƙi yayin da kuma wani abu da nake tunanin ƙusumbi ne ya bayyana a bayana.Fuskokin wasu cike da mamaki yayin da wasu kuma na hango tsoro da hassada a tattare a ciki. “Naomi me kike yi ƙasan ruwa kusan kwana biyu ba ki fito ba?” ƙawata Debora ce ta zo gare ni tare da tambayata. “Kwana biyu ?” na maimaita yayin da kuma cike da mamaki,ɗaya daga cikin tsofin garin ta matso tana mai nuna ni da yatsa tana mai cewa “dama tun ranar da aka haife ki na hango ajalin mahaifiyarki a tattare da ke saboda kin tabbata butulu ki rasa wacce za ki kashe sai wacce ta kawo ki duniya” sai kuma ta juya ta fuskanci mutanen gari tana mai cewa “kuna ta tambayar wa ya kashe Maa to ƴarta ce” Normal mutane ne kawai suka tsorata da furucinta yayin da su kuma dangina masu ido uku suka rufo kaina suna mai cewa “ita ma a kashe ta” sai dai ko kusa da ni ban bari sun ƙaraso ba na yi wani furuci duk suka ƙame ƙyam a wuri guda kamar wasu bishiyoyi. Magana na soma yi sai dai abin mamaki ba muryata ba ce ke fita,ta mahaifiyata ce.Gargaɗi ne mai ban tsoro haɗi da bushara ga waɗanda suka yarda suka miƙa wuya a bisa sabuwar dokar da na shimfiɗa musu.Kamar yadda ake rusunawa sarki haka duk suka zube suna jinjina mini haɗi da gaishe ni,ƙawata Debora ce kawai a tsaye tana wani mayen murmushi mai fitar da tsantsar farin ciki. Hannunta na kama na ratsa ɗimbin jama'ar muka wuce,har muka isa gidanmu ni da ita babu wanda ya cewa wani kanzil.A ɗaki na tarar da gawar Maa a kwance tuni ta fara ruɓewa tsutsotsi na shige da fice ta bakinta.A lokacin ne na ji wata murya daga can cikin ruhina tana bani mafita da shawari,yayin da ni kuma na yi tako ɗaya na aiwatar da abin da na ji.Hannuna na ɗora a goshin Maa na soma yin wani furuci wanda ban koya ba,kawai zuwar mini yayi.Babu jimawa ta soma bajewa tana komawa hayaƙi a haka har ta baje gaba ɗaya sai sautin muryarta da ya soma yi mini bushara “ ina tare da ke a duk inda za ki kasance ƴata Naomi kar ki yi baƙin cikin rabuwarmu wannan shi ne matakin nasararki,hidimar da za ki yi kuma na san mahaifinki zai yi alfahari da ke.Zan tafi na koma asalina,a duk lokacin da kika yi kewata ki je magudanar ruwa ki cilla dutsen karlis zan jiyo sautin kiranki” tana gama faɗar haka aka kece da ruwa mai bala'in ƙarfi wanda rufin ɗakinmu bai iya tare shi ba.Na yi saurin lumshe idona ina jin sabuwar halittata na yi mini wani irin motsi haɗi da ƙara girma wanda silar haka na ji kafaɗata ta ƙara nauyi hakan ya haifar mini da ɗan rusunawa kamar dai yadda mai ƙusumbi ke yi. An ɗauki lokaci kafin ruwan ya tsaya cak ,sai a lokacin kuma na tsinci muryar Debora na cewa “haƙiƙa kin kasance mai babban rabo ƙawata,ina mai sanar da ke cewa nan ba da jimawa ba amon mulkinki zai ƙetare duniyarmu ta ruwa ya tsallaka duniyar turɓaya ” Sai da na haɗiye wasu yawu masu ɗaci kafin na ce “a yau na ga wata duniya ,wasu mutane na gani a siffar tawaga biyu,ɗayar tawagar ta kasance ta Mayu ce yayin da ɗayar kuma ban san ta mece ce ba abin da kawai na iya gani shi ne fuskokinsu na fitar da wani irin haske mai natsuwa haka ma hannuwansu.A goshin shugabansu na ga abin da ya kusan dakatar da numfashina,wani baƙin tabo ne wanda ya ƙawata goshin nasa ya kuma fitar da tsantsar hasken fuskar tasa” “A yadda kika siffanta su sak sun fito a al'ummar nan da ke bautar wani Ubangijin Ka'aba,sam ba su nuna tausayinsu ga matsafa da kuma waɗanda suka saɓa dokar Ubangijinsu” Zuciyata ce na ji tana wata irin tafasa hakan yasa na juyo a fusace ina kallon Debora wacce ita ɗin ta kasance ƴa ga babban malamin ilimin tarihin duniya.Tun da na ji ta ambaci haka tabbas kuma na san gaskiya ta faɗa ,“dama har akwai masu tsanar Magic a duniya? Shin ba su san tasirin tsafi ba ne ko kuwa sun jahilci lamarin ne?” “Ko ɗaya! Su ɗin sun yi imani a kaf duniya babu wanda ke tafarkin gaskiya sai wanda ya kasance ɗaya daga cikinsu.Wannan dalilin ne ma yasa suke shirya yaƙi duk shekara suna shiga ƙasashen matsafa.Kin ga mu bar maganar nan ma saboda ba ta shafe mu ba” “Ta ya za ki ce ba ta shafe mu ba alhalin kin san duniyarmu ba mu yarda da wani addini ba? In fa suka farmake mu?” ban san me yasa na ji tsoro da shakku dangane da mabiya addinin ba, musamman in na tuna fuskar mutumin nan Naslam. Debora ta riƙo hannuna tana mai cewa “masana tarihi sun tabbatar mana cewa yankinmu zagaye yake da ƙoramai ta yadda babu wata halitta da ta isa ta ƙetaro izuwa nan sai da izinin esprit ɗin ruwa,kina tunanin uwayen gijinmu za su lamunta a kawo mana hari ?” wani irin numfashi na sauke ko ba komai kalaman ƙawata sun ɗan rage mini fargaba amma duk da haka ban yi ƙasa da gwiwa ba na yi shela ina son ganin dukkanin matsafan garin domin zuwa kowacce kusurwar ruwa su kai saƙo zuwa ga aljanai da ruhikan ruwa....... [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 02 Ƙananun shekaruna ba su hana ni jagorantar tsoffi da kuma dattizai zuwa bakin kowacce kusurwar ruwa ba.A tsaye nake ƙiƙam ina kallon yadda ake masayar kalamai tsakanin aljanun ruwa da kuma matsafa,kamar yadda na faɗa musu tun farko ina son a bai wa garinmu kariya haka su ma suka faɗa sai dai aljanun sun ƙi lamincewa da ƙudirinmu kai tsaye sai da suka kawo nasu sharuɗan.Daga ciki akwai bayar da jinin baƙaƙen dabbobi duk ranar laraba, sannan a kowacce ƙarshen shekara ɗaya daga cikin mutanen yankin zai zama hadiya ta aljanai. Shiru wurin ya ɗauka suna kallona,suna jiran amsata a matsayina na shugaba.Ni ma shirun na yi ina nazari,wanda ban san ashe cewa tazarar lokacin da na ɗauka kafin na miƙa yardata ya fusata aljanun ruwan sun komawarsu. “Sun fusata ba za su sake yin magana ba sakamakon shirun da kika yi yayi yawa.A matsayinki na shugaba ya kamata a ce kina bada amsa ne a kai ba tare da nazari ba” ƙawata Debora ce ta yi wannan furucin idonta na kallon tsakiyar ruwa.Dukkan matsafan sun yi amanna da furucinta,ban ce komai ba sai taku da na fara yi ina ɗaga kafaɗata gefen da ke da ƙusumbi na shiga can tsakiyar ruwan.Tafin hannuna na hagu na kalla ina yin wani furuci nan take ya tsage jinina ya soma ɗiga a cikin ruwan.Duk ɗigo ɗaya ina iya jiyo wani nishi daga can ƙasan ruwa,na ɗauki kamar minti biyu a haka kafin na dakatar da zubar jinin sai kuma na soma yin magana cikin sauti ƙasa-ƙasa “joliho kuntahee namaruju kalmari hanaighar kashmuh balbilancaaaa!” babu shiri na lumshe ido jin yadda wata irin guguwar ruwa ta tashi tana tunkuɗo duk wani masarafin tsafi izuwa gare ni. “Ya ke ƴa ga Bazuka ki sani cewa kowanne tasiri da farashinsa,sannan mu halittun ruwa ba mu taɓa mance duk wata alaƙa da aka ƙulla da mu .Za mu bai wa garinki kariya kamar yadda kika buƙata sai dai ki sani a duk lokacin da kika take dokarmu za mu bayyana miki asalin me ake kira da masifa da annoba ” wata murya da ke kama da ta macijin ruwan ta yi mini jawabi. “Hakan ba zai taɓa faruwa ba,zan kiyaye dukkan sharuɗanku” wannan karon na bada amsa kai tsaye. “Mu ne za mu zaɓar hadiya da kanmu,a duk sa'ilin da lokaci ya yi za mu nuna miki mutumin da muke buƙatar jininsa ta mafarkinki ” “Na amince!” “Sannan kuma haramun ne shiga ruwa ranar Laraba ” “Na amince!” ina furta haka kawai sai yanayin garin ya canza ya ɗauki wani irin launin duhu amma ba sosai ba,sararin samaniya ya cika da baƙaƙen giza-gizai yayin da kuma kukan tsuntsaye da kaɗawar bishiyoyi ya tsaya cak. “Aroroke! Aroroke! Aroroke!” shi ne abin da sauran mutanen da muka zo suka fara faɗa cikin murna saboda dukkan alamomin nan da suka bayyana na nasara ne. A hankali na fito daga cikin ruwan ina mai fuskantar su sai duk suka yi shiru tare da sauke idonsu ƙasa don nuna girma a gare ni. “Daga yau na sama wa garinmu suna za a dinga kiransa YANKIN MUTUWA,duk wanda ya shigo sunansa gawa ba wai mutum ba ko dabbar da ba ta wannan garin ba ta shigo na bada izini kafin a zo a faɗa mini a kashe ta” nan ɗin ma jin daɗinsu suka bayyana a fili kafin na wuce gaba su mara mini baya muka koma can tsakiyar gari inda na sa aka ƙara ƙawata gidanmu. Kan shimfiɗar da gawar Maa ta rushe na hau tare da yin kwanciya.Ina lumshe idona fuskar Naslam ta dawo mini da wani mugun sauri na buɗe su tare da tashi zaune ina jin zuciyata na harbawa da sauri.A fili na ja wani tsuki ina jin tsanarsa da su kansu mabiya addininsa.Yatsun hannuna na murza tare da furta kalmar tsafi nan take ragayar da ke maƙale a tsakiyar iccen rufin ɗakinmu ta yo ƙasa ta zo daidai inda nake wata ƴar ƙaramar takarda na gani mai ɗauke da haruffan tsohon asiri.Ban yi wani dogon bincike ba na fahimci cewa wannan takarda daga mahaifina take,mutumin da daidai da sakan ɗaya ban yi rayuwa da shi ba.Rubutun bai da yawa a ido,amma ma'anoninsa sun isa a rubuta dogon labari.Tsam na miƙe bayan na maƙale takardar a ƙuguna,daidai ƙofar da za ta ba mutum damar shiga uwar ɗaga na zube tare da shafar wurin nan take ya ɗau wani haske yana mai bayyanar mini da jan rubutu wanda aka rubuta da jinin mahaifina. “Finstako Bazaku enfinstako naheee” ina furta haka ƙasar wurin ta tsaye sai ga wata ƴar madaidaiciya wuƙa ta bayyana mai ɗauke da sunan mahaifina,nawa da kuma na Maa.Sai da na tsaga jinina ya ɗiga a kai sannan na samu damar ciro ta.Wani mummunan iska ne ya taso daga sama ya cilla ni gefe kafin guguwa ta fara haɗuwa daidai wurin da na ciro wuƙar.Wata siffa ce ta bayyana a gare ni,tun a kallon farko na ga ne shi ɗin mahaifina ne duba da fuskarsa sak irin tawa ce.Hannu ya miƙa mini,daga wurin da nake zuwa inda yake da ƴar tazara amma hakan bai hana ni ɗora hannuna kan tafinsa ba sai ya janye ni muka ɓata cikin iskan guguwa.Wata tsohuwar maƙabarta ce mai zubin ta kiristoci,kowanne kabari da nasa sunan. “Wannan ce hanyar da matsafa ke bi don kawar da maƙiyinsu ba tare da sun sha wahala ba.Da zarar kin ginawa mutum kabari to lissafin mutuwarsa zai dawo hannunki ,ke ce za ki zaɓar lokaci da kuma yanayin da zai bar duniyar bil'adama zuwa ta matattu” shi ne bayanin da Abbana ya yi mini ba tare da na tambaye shi ba. Kallonsa na yi ina mai cewa “ni banda maƙiyi ko ɗaya” “Shi kuma Prince ɗin da kuka haɗu fa? Kin yi tunanin cewa haka kawai ne kika fita daga duniyarmu ta tsakiyar ruwa zuwa duniyar turɓaya? Ya ke ƴata ki sani daga ranar da muƙamin iko na prophecy ya fara aiki a kanki to abu na farko da uwayen gijinmu suke nuna maka shi ne babban maƙiyinka” Shiru na yi ina nazarin furicinsa ,so nake na san ta ya aka yi Naslam ya zama maƙiyina,don na fahimci sarai a kansa ne yake magana. “Dalilin da yasa kika zama maƙiyiyarsa saboda ta silarki ce aka yi galaba a kansa,ba don a ce ya shagala da kallonki ba to da tabbas magauta ba za su harbe shi ba” ya ƙara faɗa kai ka ce shi ke sarrafa tunanina da har yake sanin abin da ban furta ba. “In dai duk abin da ka furta gaskiya ne,to zan so a ce a duk lokacin da yake tsakiyar fafatawa da maƙiya ya zamana ni kuma na bayyana a wurin ta yadda zan zamo rauninsa,ya gane ya kuma fahimci cewa wutsiyar raƙumi ta yi nisa da ƙasa.Ta hakan ne kawai ba zai taɓa sha'awar farmakar yankina ba” Bai ce mini komai ba sai wuƙar nan da ya cire daga gidanta ya miƙo mini tare da nuna mini wani buɗaɗen kabari wanda a jikinsa aka rubuta sunan Prince Naslam. Hannuna na tsaga jini ya zuba a cikin ramen kabarin,babu jimawa wuta ta soma ci balbal.Daga nan kuma kawai sai tsintar kaina na yi a ɗaki,ba tare da na san alƙawarin jini ne na ƙulla Ni da aljanai ba. ★DAULAR ABU NASLAM Tutar daular ce aka juye alamun babu lafiya a yankin.Dakaru haɗi da hadimai sai faman kai komo suke yi suna jiran tsammani na farfaɗowar jagoransu,madubi kuma gun babbar masarautar musulinci. Sarki Haroon mahaifi gun Prince Naslam a tsaye yake a wata kusurwa wacce ta yi daidai da alƙibla.Idonsa a rufe suke,yayin da kuma ya haɗe hannuwansa wuri guda domin nuna ladabi ga Ubangijinsa.A hankali yake motsa bakinsa,duk da ba a jin furucin amma za a iya fahimtar abin da yake cewa shi ne “Ya Hayyu! Ya Ƙayyum! Wato ma'ana Ya Rayayye! Ya dawamamme!” iya shi kaɗai yake furtawa bai dakata ba kuma sai da ya ji murya jakariya Ali yana cewa “shugaba cikin amincin Ubangiji ka'aba Prince Naslam ya dawo hayyacinsa ” “Shukuran Ya Rabb!” shi ne kawai abin da ya furta kafin yake juyowa yana kallon Ali wanda duk ya fita hayyacinsa tun ranar da suka dawo daga yaƙin tsibirin Mayu. Murmushi sarki ya sakar masa wanda ya haifar masa da samun wata ajiyar zuciya nan take kafin cike da girmamawa ya ce “yarima na buƙatar ganinka” “Mu je!” ya furta kafin sarki ya shiga gaba shi kuma Ali na take masa baya har suka shiga ɗakin yarima Naslam inda yake kwance yayin da kuma tsoho Barham ke kula da lafiyarsa. Suna haɗa ido da mahaifinsa ya yi saurin yunƙurowa da niyyar tashi,sai dai raunin ƙirjinsa ya dakatar da shi da wani mugun sauri ya koma ya kwanta yana mai yin wani irin nishi. Barham ya ce “na yi nasarar cire dattin garin mahalbiya,nan da kwana uku in sha Allah zai iya tsayuwa kan ƙafafunsa” Sarki ya ce “Ubangin ka'aba ya albarka ce ka ya ƙara maka ɗimbin ilimin sanin magani” Barham ya amsa da “ Amin ” kafin kuma ya yi wa Ali alama suka fice suka bar sarki shi da yarima. “Ya jikin naka?” sarki ya tambaye shi yana mai dafa goshin Naslam ɗin.Maimakon ya basa amsar tambayarsa sai cewa ya yi “Abih aljanar da nake baka labari ita ce silar raunin da aka ji mini,na gan ta a zahiri tana tsaye gaɓar teku sanyen da kayan arna,ƙusumbin tsutsotsi maƙale a bayanta,idon sharrinta na fitar da gubar tsafi ” “Naslam na sha faɗa maka ita ɗin ba aljana ba ce,wakiliyar duk wasu sheɗanun Mayu da matsafa ce.Ita ce aka damƙawa kundin prophecy domin cika wani baƙin ƙuduri nasu.Amma da ka gan ta wane yunƙuri ka yi?” “Abih ta ya zan iya yin wani abu? Yanzu dai ina so a shirya dawakan yaƙi su ƙara komawa can domin binciko mini ita” Shiru sarki yayi kafin kuma ya fita,cike da bayar da umarni ya sa aka shirya dawakai majiya ƙarfi da kuma dakarun yaƙi . Jakariya Ali shi ne ya shugabanci tawagar,sai dai sama da awa biyar suka kwashe ko kusa da ruwan sun kasa zuwa saboda tsantsan tsaron da aka shimfiɗa musu a dole ya jawo su suka dawo gida a lokacin tuni yarima Naslam ya kasa sukuni ya sa an kawo masa farin ƙyalle haɗi da abin zane haka ya zauna ya zana Naomi kai ka ce ta gasken ce . Ido ya tsura mata cike da tsana yana tambayar kansa a zuci ‘ wace ce ke? Me yasa tun da na shiga zangon balaga kika addabi rayuwata?’ Jin an banko ƙofa yasa shi barin zancen zucin tare da maida idonsa kan ƙofar shigowa.Jakariya Ali ne sanye da kayan yaƙi,zanen ya fara kallo kafin ya cewa yarima “babu wata nasara dangane da tekun can,amma wai don Allah me yasa ka damu? ” Cikin zafin rai ya ce “aljanar mafarkina ce” “Amma fa ita ce ta cece mu lokacin da Mayu suka fara sarrafa tsafi ” jakariya Ali ya faɗa . “Bayan ta yi silar cutar da ni,Ali na tsani aljanar nan tun ba yau ba na fahimci cewa ita ɗin rauni ce a rayuwata” “Yarima a duk lokacin da na ji kana irin wannan zantukan sai na dinga jin cewa kai ma fa tamkar kana ɗauke da ikon prophecy ” Kafin yarima Naslam ya kai ga yin magana wani irin iska mai sanyi ya fara ratso ɗakin yana shigowa,babu abin da ya motsa sai zanen hoton Naomi shi ma ɗin cike da abin al'ajabi yadda bakinta ke ɗan buɗewa tana murmushi..... [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 03 Zanen fuskar Naomi bai gushe yana murmushi ba suka jiyo sautin wata waƙa wacce yarima Naslam ne da kansa ya haramta ta saboda kalaman da ta ƙunsa na tsafi da kuma kirari zuwa ga tawagar dabar Mayu da matsafa. Jakariya Ali ne yayi saurin tsayuwa kusa da window ta inda ya fi jin sautin na fitowa.Wata makauniyar tsohuwa ya gani a durƙushe riƙe da sanda tana rera waƙar tana wani jinjina kai haɗi da murmushi. “Ina ga mun yi baƙuwa ne ,ba don haka ba ai ka haramta raira waƙar nan” jakariya Ali ya faɗa . Yarima da ya cika yayi fam kamar zai fashe ya ce “a kama ta” Da wani irin gudu kuwa jakariya Ali ya fita ,babu jimawa yasa wasu dakaru biyu suka damƙe matar tare da kai ta can ɗakin ajiyar masu laifi ya kuma bada umarnin a ƙara tsaro sosai. Shi kuwa yarima Naslam zanen ya naɗe tare da adana shi ƙarƙashin pilow .Sai a lokacin kawai ya tuna akwai sallolin da suka hau kansa waɗanda bai yi ba,tsuki ya ja a fili yana cewa “duk sharrin aljanar nan ne” Cikin ikon Allah sai ga jakariya Ali ya dawo ,shi ne ya taimaka masa zuwa banɗaki ya yi ɗahara haɗi da alwala sannan ya fito ya soma gabatar da sallolinsa. Bayan ya gama ne,mai magani Barham ya ƙara shigowa ya duba shi tare da basa maganin sha da kuma na shafawa wanda cikin hukuncin Ubangiji sai ya ƙara jin ƙarfin jikinsa. “Zuwa bayan sallar asar zan haɗa maka ruwan magani a bahon wanka sai ka shiga ka yi,amma ina so don Allah ka cire duk wani tunani akan yarinyar da ka zana ” Barham ya faɗa . Yarima Naslam ya ɗago manyan idonsa masu firgita maza ya ɗora kan Barham kafin ya ce “me ka sani game da ita?” Barham ya gyara tsayuwarsa kafin ya ce “ita ɗin ba kamar sauran mutane take ba,an haife ta bayan ɗaukar ran mahaifinta,an raine ta cikin gata da soyayya sannan kuma an damƙa mata muƙamin prophecy a ranar da mahaifiyarta ta yi gushewa wannan dalilin kaɗai ya isa ya tabbatar maka iya tunaninta ma kaɗai ba alkhairi ne ba ga Sarkin goben masarautar nan” “ Ban fahimce ka ba,kana nufin ita ɗin annoba ce ga duniya baki ɗaya?” “A'a! Ita ɗin fa shugaba ce,kamar yadda kake kare Yankinka to ita ma haka jininta ke tafarfasa in aka ce an taɓa ahalin mugaye.Tana da ƙarfin ikon maitar ido,ga kuma baƙar maita ta baki wadda da za a ce ta tofa yawunta a tekun wani yanki da ba nata ba to tabbas da ruwan sun haramta saboda tasirin ƙwayoyin cutar da ke ciki.Na yi magana da jakariya Ali ya shaida mini duk yadda komai ya faru,kuma na gaskata sarauniya Naomi ce saboda abin da na tsinta a yayin yi maka magani” “Me fa?” yarima Naslam ya tambaya. Shiru Barham ya yi kafin ya tako ya iso gun yarima,cikin muryar raɗa kamar mai jin tsoro ya ce “ta jefa maka cutar ayni wato maitar ido, wannan ne ya hana ka motsi ya juye maka tunani ka manta cewa filin daga kake har sai da magauta suka yi nasarar harbin ka” Zuciyar Naslam ce ta fara tafasa kamar za ta faɗo,yana jin ina ma zai ga Naomi a yanzu da babu shakka tabbas da hannunsa zai kashe ta.Haka ya danni zuciyarsa,ya yi ƙoƙari sosai wurin manta wa da ita sai dai kamar abin isimi lokacin yin wankansa na yi na magani idanunsa suka fara yi masa gizon yadda ta kafe shi da idonta masu matuƙar girma da kyawu don tamkar gwal haka suke sheƙi. Jakariya Ali ne ke taimaka masa har ya samu ya shiga ya kwanta cikin bahon wankan,kamar jira ake yi kuwa wani al'amari ya riske shi.Ji yayi kamar an rufe shi bai numfashi kafin ya soma jin wani yanayi wanda sam ba zai iya misalta irin abin da yake ji ba.Jikinsa ne ya ɗauki wata irin kyarma sakamakon wasu halittu da yake gani dishi-dishi waɗanda ya yi imani cewa ba Mala'iku ba ne.Can kuma ya soma wani abu kamar mafarki yana tare da Naomi yana tarayya da ita kamar sauran mafarkansa na baya. Jakariya Ali da ke gefensa tuni ya fahimci abin da ke faruwa,muryarsa na ɗan rawa ya kira sunan yarima Naslam kafin ya ce “innalillahi wa'inna ileyhi raji'un!” nan take komai ya tsaya cak.Yarima Naslam yayi wata irin zabura haɗi da nishi bakinsa na fitar da baƙin jini.Jakariya Ali ne ya yi hanzarin goge masa jinin kafin ya taimaka masa ya yi wankan,da ya fito ma shi ne ya taimaka masa wurin saka kaya marar nauyi kafin kuma a gabatar masa da tafasasshen shayi wanda suke yi ko wane dare.Har ya yi sallolinsa bai dubi kofin shayin ba saboda abin da ke damun ransa,bayan sallar isha'i ne sarki ya shigo da kansa ya duba shi. “Gobe ka tura dakaru zuwa bakin Teku su ƙara binciko mini aljanar nan” yarima ya faɗa yana wani kawar da kai gefe. Sarki ya ce “zan so ka manta da batun yarinyar nan ka fuskanci sabon al'amarin da ke shirin tunkaro masarautarmu Naslam.Sanin kanka ne duk abin da ya cika naci to babu alkhairi a tattare da shi,ba tun yau ba kake faɗa mini kana yin mafarki da aljana to ka sani shigowa da ita masarautar nan daidai yake da ruguza duk wani ginshiƙi da ka gina tsawon shekaru” sai kuma ya yi shiru tare da zuwa ya ƙara ɗaukar wani kofi ya zuba masa shayi sannan ya saka cokali yana juya shi tare da miƙa masa ,ba don ya so ba ya karɓa ya soma sha.Sai kuma a wannan lokacin ne sarki ya ci gaba da cewa “gimbiya A'ishah na waje tana jiran fitowar ka ,zan so a ce ku daidaita kanku tun a yau don a samu a wuce wurin,na san daga lokacin da aka ɗaura maka aure shi kenan matsalarka za ta kau”. Ambaton sunan gimbiya A'ishah shi ya wanzar masa da nutsuwar zuciya,don yana mugun ƙaunarta har cikin ransa saboda ba ƙaramar gudunmawa ta bayar ba wurin haɓaka musulunci a masarautar nan ba. A hankali ya sauko daga gadon da yake,sai dai sam ya kasa jurar tsayuwar a dole ya koma ya zauna.Cikin ɗan ɗaga murya sarki ya ce “Ali?” shi kuwa kamar mai jira haka ya buɗe ƙofar ya shigo tare da ƙamewa. “Ka fito da yarima zuwa waje” ya faɗa tare da ficewa.Jakariya Ali ya ɗauko kujera ya taimaka wa yarima ya hau ya zauna sannan ya soma tura shi zuwa can falo wanda ya cika da ahali da kuma aminnan arziki.Tun daga nesa suka haɗa ido da ita,da wani mugun sauri ta yi ƙasa da kanta cikin kunya tana yin wani sihirtacen murmushi.Har aka ƙaraso da yarima ba ta ɗago kanta ba,haka aka shiga jera masa sannu yana amsa wa amma idonsa na kanta. “A'ishah zo ki gaishe da yarima mana kin wani tsaya wuri guda kina sunne kai kamar ba ke ce a yanzu ki ƙi cin abinci ba saboda shi” mahaifinta ya faɗa yana wani murmushi haka ma duk sauran mutanen wurin fuskarsu cike take annuri in aka cire mahaifiyar A'ishah ɗin da take jin kamar ta je ta kama wuyar yarima ta shaƙe shi har sai ya mutu. Gimbiya A'ishah ba ta ko motsa daga inda take ba,sai da mutanen suka dinga fita zuwa babban falo suka bar su iya su uku don duk inda yarima yake jakariyarsa Ali na tare da shi.Ɗan gefe kawai ya koma yana kallonsu,shi dai ko kaɗan bai ga dacewar yarima da ita gimbiyar ba duk da kuwa cewa ita ɗin kyakkyawa ce ta ajin ƙarshe. “Amincin Allah ya tabbata ga shugaban gobe” ta furta tana mai takowa inda yake tana ɗagowa haɗi da yi masa wani kallo mai tsayawa a rai wanda a can da babu abin da ke matuƙar girgiza yarima irin kallon nan amma yanzu sai ya ji sam bai burge shi ba,hasali ma na Naomi ya tsinta a fuskarta. Da sauri ya lumshe ido yana mai amsawa tare da cewa “shi ne ba ki zo kika duba ni ba tsawon kwana biyu ina a kwance” Murya na ɗan rawa ta ce “subahanallahi! Meke damunka yarima? Ai ban san ba ka jin daɗin jikinka ba,saboda tun ranar da ka haɗa ni da matan nan nake koya musu karatu daidai da ɗaya rana ban taɓa leƙowa waje ba” Wani numfashi ya furzar yana mai buɗe idonsa ya dube ta,iliminta yana ɗaya daga cikin abin da yake so a tattare da ita,“kar ki damu ai na samu lafiya” Shiru ta yi tana mai ɗagowa ta dube shi,ita sai yanzu ne ma ta lura cewa kan kujera ne yake.Sai kuma ƙwaƙwalwarta ta tariyo mata lokacin shigowar su shi da jakariya Ali, kasancewar kwanyarta dama can ba kullum take tafiya daidai ba shi yasa ne ba ta fahimci hakan ba. Rikicewa ta yi ta zube a gabansa tare da soma jero masa tambayoyi,wanda kuma in akwai abin da yarima ya tsana a tare da ita shi ne yawan tambayoyi da kuma wannan haukan da take yi a duk lokacin da wani abu na ƙi ya same shi. Da wani irin sauri jakariya Ali ya matso yana mai dakatar da ita,yana cewa “don Allah ki yi shiru mana” sai ta ɗago kai tana yi masa kallon tsana saboda tun tuni ta san cewa Ali bai ƙaunarta. Yana yi mata wani mugun kallo ya je ya kama kujerar da yarima ke zaune ya soma tura shi tare da mayar da shi ɗakinsa.Har Ali zai tafi sai kuma ya dakatar da shi yana mai cewa “kai ni wurin matar da aka kama ɗazu” Jakariya Ali ya ce “tana da matuƙar hatsari yarima ,da bari ka yi zuwa gobe in sha Allah ka ga lokacin ka ƙara samun ƙarfin jikinka” “Mu je dai ka kai ni ” ya sake faɗa ,ba don ya so ba ya tura shi zuwa kurkukun har suka isa ragar da aka killace ta. Tana kwance a duƙunƙune cikin wani tsohon bargo,hatta kanta a rufe yake amma hakan bai hana ta ganin yariman ba.Cikin wata irin murya ta ce “barka da zuwa yariman musulmai,ka sani killace ni a nan ba shi ne maganin matsalarka ba.Hakan ma babban kuskure ne ka tabka,ko da yake ba ka san ko ni wace ce ba” ta ƙarashe faɗa tana yin wani nishi sai ga bargon da ta rufa a shi ya yi wani irin sama tare da buɗe ta. Yarima da jakariya Ali suka kalli yadda bargon ya maƙale can sama cikin iska.Su duka biyun sun yi imani cewa tsafi ne ta yi,sai dai a yanayin da yarima yake a yanzu ba zai iya ɗaukar wani mataki ba a hannunsa sai kawai yasa jakariya Ali ya juya da shi. ★ A cikin abin da bai wuce kwana uku ba mulkina ya tsaga kowacce kusurwar yankinmu.Tuni na yi ƙaurin suna yayin da kuma gogaggin matsafa daga garuruwan ƙetare ke kawo mini tayin aure duba da yanayin shekaruna ina buƙatar abokin rayuwa musamman don gudanar da mulki yadda ya kamata sai dai ko kaɗan babu wanda ya kwanta mini a rai. Muna zaune kan kututuren icce ni da Debora ,sai kuwa ga wata baƙar mujiya ta soma shawagi haɗi da yin wani kuka. Debora ta furta kalaman tsafi tana mai buɗe tafin hannunta,sai mujiyar ta sauko tana mai sakar mata wata takarda ita kuwa jikinta har rawa yake yi wurin buɗewa.Rubutu ne reras da manyan baƙi,sai dai harufan na tsafi ne kuma ba su yi mini wuyar karantawa ba.A tare muka kalli juna,kafin na miƙe tsaye ina cewa “to a wane yanki ne aka kama ta?” “Ba ta faɗa ba a cikin wasiƙar,amma ina zaton ɗaya daga cikin garuruwan da suka kawo miki tayin aure ne ba ki amince ba” Shiru na yi ina tunani kafin kuma na karɓi takardar,ina furta tsafi rubutun ya goge sai na soma juya ido ina yin magana cikin raɗa rubutun ya soma rubuta kansa ina gamawa sai na umarci tsuntsuwar ta kai wa mahaifiyar Deborah .Ido na birkice suka koma farare tas ta haka ne nake iya hango gudun tsuntsuwar tana keta sararin samaniya tana wuce ƙauyuka tana shiga wasu garuruwa sai dai tana daf da ƙetara wata tutar wani yanki na ga wata kibiyar haske ta jefe ta ita kuma ta faɗi ƙasa ,duk kuma yadda na ƙware a tsafi ban ƙarashe ganin sauran abin da ke faruwa ba...... [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 04 Hankalin Debora sosai ya tashi saboda ta lura da abin da ya faru.Ko kaɗan ban ga laifinta ba saboda na san yadda mutum ke ji in mahaifiyarsa ba ta tare da shi, wannan yasa na damƙo hannunta tare da yin wani irin kalar tsafi na gushe mata da damuwar tare da saka mata nutsuwa na danne ƙuncin zuciyarta. Idonta da suka kaɗa suka yi ja na duba karin na ce “ki sani cewa babu wani sarki da zai gagare ni,ki sa a ranki ummarka tuni ta kuɓuta” Muryarta na fitar da wani irin amo take cewa “ya ke shugabata in ba ki manta ba irin haka ne mahaifina ya tarar da wa'adinsa,silar zaƙulo bincike domin rubuta tarihi ya haɗu da wasu mabiya addini mabanbanta suka kashe shi a ƙarshe sai mahaifiyata ce ta maye gurbinsa domin ci gaba da rubuta littafin kudin binciken duniyar ruhaniya” tana kawowa nan da zancenta sai ta ɗan yi shiru kafin ta ci gaba da cewa “ina jin tsoron kar a ce ita ma Umma nata ajalin ne ya zo” Kai na girgiza mata ina mai cewa “muddin ina raye hakan ba zai faru ba” Rungume ni ta yi tana sauke wata irin ajiyar zuciya,yayin da ni kuma na shiga tunanin hanyar da zan bi na ƙwato Umma ɗin saboda a duniyar nan a halin yanzu banda wani masoyi da na fi so da ƙauna sama da Debora.Cikin hikima na mayar da ita cikin gida gabanin ni kuma na fita zuwa can cikin baƙin jejin garinmu mai cike da aljanai da fatalwa. Cikin tafiyar rauni ta masu larurar ƙusumbi nake tafiya ana take mini baya,ko kaɗan ban san su wane ne ke take sawuna ba kuma ban jin tsoro ko fargaba wani abu.A haka na isa bakin wata iraciyar kuka mai zubin halittar mutum don da baki da hanci gare ta.Ina gama daidaita tsayuwata sai kuwa bisashin ganye suka fara zubowa a kaina kamar ana ruwa kafin ɗanye ƙwaya ɗaya ya faɗo a gabana.Ɗaukarsa na yi tare da tofa yawuna a kai,sai na soma juya ido babu jimawa yawun suka rikiɗa zuwa rubutu.Sai a lokacin na miƙawa itaciyar ganyen mai ɗauke da bayanin abin da ya kawo ni nan ɗin.Tafin hannuna na ji ya cika da wasu duwatsu,ina dubawa sai na ga suna sheƙi akan kowanne dutse an rubuta karlis .Ban yi jinkiri ba na nufi ɗaya daga cikin magudanar ruwa na je na yi tsaye ina kallon yadda ruwan ke a kwance sun nutsu ko motsi ba su yi.Dutse ɗaya na cilla ina sauraren yadda ƙararsa ya ratsa ruwan tare da soma yin gudu har zuwa inda nake son ya isa. Ba a ɗauki wani lokaci ba wata iska mai sanyi ta soma kaɗawa tana fitar da wani ƙanshi irin na gawa.Can sai ga Maa ta ratso ruwa ta fito,fuskarta ta yi wani fari fat kana ganinta ka ga matatta ga kuma fararen kaya a jikinta. Cike da soyayya na je da gudu na rungume ta,sai dai kamar na jimƙi iskan gas haka na ji babu wata alamar gangar jiki.Da sauri na ja da baya ina kallonta tana wani fitar da murmushi,wani irin tausayin kaina na ji wanda ko ranar mutuwarta ban ji shi ba. “Me kike buƙata Nao?” don haka take kirana a duk lokacin da take shauƙi ko kuma take son isar mini ƙaunar da zuciyarta ke ƙumshe da ita. “Maa shi kenan ba zan ƙara jin taushin gangar jikinki ba?” ita ce tambayar da na yi mata madadin na sanar da ita matsalar da ta kawo ni. Ta ce “Naomi a zangon da nake na fita daga sawun duniyar bil'adama na koma cikin duniyar matattu,ki kira ni da ruhi kai tsaye” Kallonta na yi,tabbas ita ɗin ruhi ce kamar yadda ta faɗa ɗin.Na kai hannu na shafi kumatuna da nake jin wani damshi,wanda na yi imanin cewa ruwan hawaye ne .Murya na ɗan rawa na ce “mahaifiyar Deborah ta faɗa hannun mugaye shi ne nake son sanin ta ya zan ceto ta?” “Babu buƙatar yin haka,saboda ita ɗin ba kanwar lasa ba ce.Za ta iya fitar da kanta kar ki wani damu kanki” Maa ta faɗa . Na ce “amma kuma ita ce da kanta ta aiko da takarda domin sanar da mu” “Ta yi haka ne domin ku ci gaba da rubuta littafin bayanai ba wai don kawo mata agaji ba.Ki sanar da Deborah cewa lokaci ya yi da ita ma za ta ɗauki muƙaminta na rubuta tarihi kamar yadda mahaifinta ya karɓa gun mahaifinsa,ita kuma mahaifiyarta ta karɓa daga mahaifinta,yanzu kuma ƙaddarar littafin tarihi ta dawo hannunta” Maa na gama furta haka sai ta soma nitsewa cikin ruwa haskenta na tarwatse wa haɗi da disashewa.A gaban idona ta ɓata,na lumshe idona ina mai furta kalaman tsafi tare da buɗe su kuma a nan na tsinci kaina a ɗakina. Deborah na kwance amma ba bacci take yi na.Kallonta na yi kafin a takaice na sanar da ita abin da Maa ta shaida mini,da wani irin sauri ta miƙe ta zauna tana kallona can kuma ta soma furzo da wani irin furuci sai na ji tsafin da take yi ba irin nawa ba ne yana da banbanci kamar yadda Hausar wani gari ba ɗaya take da ta wani garin ba. Babu jimawa sai muka soma jiyo kukan jemage yana wani tsala shi kamar zai fasa gidan,a tare muka fita nan muka yi gamdakatar da wani baƙin jemage baƙi ƙirin da shi ga kuma wani irin girma na ban mamaki. Kan ƙafafunsa ya sauka bayan ya cillo wani tsohon littafi ya dira a tafukan hannun Deborah. Kallo ɗaya na yi masa na fahimci cewa shi ne wanda aka wakilta domin tsare littafin ya basa kariya.A hankali ya soma yin tsalle har ya isa gun Deborah,babban farcenta na ƙafar hagu ya kama ya fasa shi tare da soma shan jininta irin sosai ɗin nan don har sai da ta soma yin wani irin haske irin na rashin jini amma ko kaɗan ban yi yunƙurin tsayar da shi ba har sai da ya gama sha sannan ya tashi sama,sai dai bai yi wani nisa ba ya ɓace ɓat. Sai a lokacin na je na kama ta na ja ta zuwa ciki na zaunar da ita,magani na ɗauko na soma rufe mata yatsan da shi wanda har yanzu yake ɗigar da jini. “Ki kwanta ki huta na san kin gaji” na furta. “Ki soma karanta littafin kafin ni na karanta miki ” ta furta tare da miƙo mini,kamar ba zan karɓa ba sai kuma na kai hannu na karɓi littafin na ajiye a gefe.Ido ta lumshe ta soma yin bacci mai kama da mutuwa,wanda na yi imani cewa a cikinsa ne za a miƙa mata wasu asirai da kuma power kariyar kai da kuma ta abin da aka damƙa mata amanarsa. A cikin wannan daren ne na soma karanta littafin tarihi wanda ya ƙunshi rayuwar jarumai da kuma irin gwagwarmayar da suka yi fama a kai.Na samu sirrika dayawa,na yaƙi da kuma yadda ake sarrafa maita ta sigogi daban-daban. Wannan littafin ya ƙara saka mawa zuciyata cewa duk inda babu magic to lalle babu rayuwa mai inganci, Magic shi ne komai na duniya a cikinsa ne za ka samu ƴanci da kuma gata.Rufe shi na yi tare da raɓawa gefen Debora na kwanta,ina lumshe idona na soma jin wani irin motsi a cikin kunnena tamkar ƙwaro na tafiya.Ƙara nutsuwa na yi sai na soma jin tamkar ana yi mini magana ne,amma ta ina? Ban sani ba.Ji na yi ana danne ni ana saukar mini nauyi,na furzar da huci mai zafi jin wasu kalmomi daga wata murya da ban san mamallakinta ba. “ A duk inda kike a faɗin duniyar nan sai na nemo ki,ni ne nan zan kashe ki da hannuna ƙaramar matsafiya muguwa mai idanun maciji” muryar namiji ce amma ban san wane ne ba, sannan ban fahimci abin da yake nufi ba har ya ƙara yin wani furucin “ina ma ace annabi sulaiman bai yi wafati ba,da na roƙi alfarmarsa ya tura rundunar aljanu su gana miki azabar da ta fi ƙarfin tsafinki ” Saurin buɗe idona na yi,ina mai tambayar kaina “wane ne kuma Annabi Sulaiman?” sai dai banda amsar wannan tambayar,in akwai wanda zai faɗa mini ita to bai wuce Deborah ba wannan yasa na kasa haƙuri na kai hannu na shafi fuskarta.Ta buɗe idonta tarau a kaina,sai dai babu ɗigon baƙi a cikinsu da alamu har yanzu ba ta dawo daga balaguron ruhi ba. “Wane ne Annabi Sulaiman?” na tambaye ta,idanunta ne suka dawo normal nan take ta tashi zaune sannan ta bani amsa da cewa “ ya kasance ɗa ga Annabi Dawuda shi ma kuma annabin Ubangijin Ka'aba ne.Yana da matuƙar power don a tarihin annabawa shi ne kaɗai ya mulki mutane da kuma aljanai,sannan kuma yana iya yin magana da dabbobi da kuma jarirai waɗanda bakinsu bai buɗe ba.Ya yi mulki cikin hikima da adalci ga al'ummarsa” Zuciyata ce na ji tana wani irin bugawa na jin bayanin da Deborah ta yi mini.Kamar mai tsoron sake jin wata buwayar na ce “amma me Annabin ke nufi?” “Mutum mai isar da wahayi daga Ubangijin Ka'aba zuwa ga al'umma ” ta bani amsa kai tsaye.Ban ce mata komai ba sai tashi da na yi na fito waje ina kallon taurari ina kuma juya kalamanta. Ƙofar gidan na ji ana bugawa,na je na buɗe sai na ga gungun matsafan garin ne da alamu sun fito maitar dare ne suka biyo. “Ranki shi daɗe mun samu baƙuwar fuska a yankin nan,wani mutum ne maharbi mun tsince shi a wata gona yana bacci.Mun ɗaure shi da duk wata igiyar tsafi amma ta ƙi yin tasiri a kansa saboda girman tsafinsa wannan dalilin ne yasa muka zo zuwa gare ki” ɗaya daga cikinsu ya faɗa . Raina a mugun ɓace na ce “me yasa ba ku kashe shi ba?” Kallon juna suka yi kafin wani kuma daga cikinsu ya ce “ kamar dai yadda ya faɗa miki ɗin ne,tsafinsa nada matuƙar ƙarfi da dukkan alamu mutum ne na daban ko a duniyar ruhaniya” Ban ce komai ba na yi gaba a fusace yayin da su kuma suka take mini baya.Tun kafin na isa gonar nake jiyo numfashin baƙin tsafinsa,ina isa ya yi saurin tashi tsaye muna fuskantar juna.Ɗan saurayi ne da ba zai haura shekara ashirin da takwas ba,sanye yake cikin kayan maharba ya rine gefen fuskarsa da baƙin abu yayin da kuma ƙirjinsa aka zana wata baƙar kunama. Ban tsaya tambayar wane ne shi ba na kai masa farmaki,ya tare kafin kuma mu shiga masayar kalaman tsafi muna haɗawa kuma da yaƙin gangar jiki.Kamar yadda suka faɗa ɗin tabbas shi ɗin na daban ne,ban ida fahimtar haka ba sai da ya kai ni ƙasa ya saita kibiyar tsafinsa daidai idona. Yana jan wani numfashi ya furta “kafin a farmaki baƙo a fara tambayarsa da wace aniya ya zo,duk waɗannan matakan tsaron na ruhikan ruwa da kika saka ba su iya tare ni na shigo yankin nan ba sai ke ce kike tunanin za ki hana ni yin abin da na zo yi?” shi abin da ya furta,amma duk da haka ban saurare shi ba na fito da wuƙar mahaifina na daɓa masa ita a ƙirji daidai kunamarsa yayi wata irin kururuwa da ta saka dajin amsa wa kafin ƙyafta ido sai ganin kunamu muka yi suna zubowa kamar ana ruwa..... [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 05 Yadda baƙaƙen kunamun suka dabaibaye jikina shi ya fi komai ɗaga mini hankali,ga shi kuma masarafin tsafina ya ƙi aiki.Idona ƙurrr kan mutumin da na cakawa wuƙa yana tsaye ƙyam kan ƙafafunsa,yayin da kuma kunamun suka buɗe hannuwansu da alamu umarninsa suke jira su shiga harbata. Tafin hannunsa ya buɗe ya soma yin furuci cikin Yaren tsafi wanda ya sha banban da nawa,a hankali duk kunamun suka yi ɓata dabo sai a lokacin na yunƙura na tashi zaune ina kallonsa cike da mamakin me yasa bai kashe ni ba kamar yadda na yi yunƙuri. “Wane ne kai?” na tambaye shi.Bai bani amsa ba sai nuni da yayi mini da wuƙata wacce har zuwa yanzu tana nitse a cikin ƙirjinsa.A hankali na miƙe tare da zuwa na ciro wuƙar,abin mamaki sam babu ko da ɗigon jini da ya zuba illa kawai alamun an huda ƙirjin. “Banah!” ya bani amsa,na maimaita sunan a bayyane kafin na ce “me ya kawo ka YANKIN MUTUWA?” “Ke!” ya bani amsa kai tsaye,kallon ban gane ba na yi masa kafin na ce “ni kuma?” Kai ya jinjina mini kafin ya ciro wata sarƙa da ke a wuyansa mai tambarin gumki ya miƙo mini,na karɓa tare da juya ta sannan na ɗago na dube shi. “Ba ki ga komai ba?” ya tambaye ni. “Me kake son nuna mini?” “Duba da kyau dai” ya sake faɗa ,sai na nutsu da kyau nan ne na ga gumkin jikin sarƙar zanen mace ne da ƙusumbi a bayanta. Na shafi ƙusumbin da ɗan yatsana,nan take ya kawo wani haske kamar an kunna ƙwan lantarki.Banah ya matso kusa da ni shi ma ya ɗora nasa yatsan kan nawa sai hasken ya ƙaru a hankali kuma muka fara yin sama ƙafafuwanmu suka bar ƙasa muka lula can cikin iska. Mutanen gari ne suka fara fitowa,sai kuma suka shiga yin kiɗa da bushe-bushe yayin da wasu kuma suke rawa.Ban taɓa tunanin cewa wai hakan aure ne muka ƙulla ni da Banah ba sai da wasu ruhika suka bayyana a gare mu suka yi mana bushara da hakan tare kuma da ƙara mana power. Sarƙar nan mai hoton gumkin mace da ƙusumbi ita ce kabancin sadakina,ita Banah ya saka mini a wuya kafin mu sauko ƙasa. Gefe na koma ina kallonsa,ba mummuna ne ba amma kuma ba za a kira shi da mai kyau ba.A kallon farko za ka tabbatar da cewa shi jarumi ne a fagen tsafi,kumatuna da ya shafa shi ya katse mini ɗan guntun nazarin da nake yi a kansa. “Tunanin me kike yi?” ya tambaye ni,da sauri na juya masa baya ina mai basa amsa da cewa “ ban san wane ne kai ba,daga ina kake kuma amma kai tsaye ka zo ka aure ni ba tare da neman shawarata ba” “Naomi ba fa ni ne na tsara haka ba,allolin prophecy suka ga dacewar mu haɗu ni da ke domin mu cika alƙawarin da magabatanmu suka ɗauko” Da sauri na juyo ina kallonsa na ce “to ka riƙe ni matsayin abokiyar aiki kawai” ina gama faɗar haka na soma tafiya cikin rangaji saboda yanayin larurata.Ina jin yana take mini sawu har muka isa gida,Deborah na tarar a tsaye kamar mai jiran zuwana. Da ido ta tambaye ni shi kuma wancan na bayana? Na juya na dube shi da sauri ya ƙaraso ya gabatar da kansa ga Deborah sai na ga yanayin fuskarta sam babu annuri. “Zo ina son yin magana da ke” ta faɗa tare da kama hannuna muka shiga cikin ɗaki. “Ta ya aka yi ya zama mijinki alhalin tarihi bai nuna za ki yi aure ba a doron duniya?” Deborah ta tambaye ni tana wani tsure ni da ido. Ni ma ɗin kallonta na tsaya yi saboda gaskiyar da ta fito daga bakinta wacce na san ita kanta ba san ta faɗe ta ba. “ Ba zan yi aure ba?” na tambaye ta,sai a lokacin kuma na ga ta sha jinin jikinta tare da soma yin kame-kame . “ Tun yaushe kika gano haka?” na sake jefo mata wata tambayar. Ta yi ɗan ƙasa da murya tare da sauke idonta daga cikin nawa ta ce “tun ranar da Umma za ta bar garin nan zuwa neman tarihi a wasu guraren , ta shaida mini cewa ba za ki taɓa yin aure ba muddin alamomin prophecy sun bayyana a gare ki.Ita ce da kanta ta nuna mini tsanin nan da ke cikin ruwa,ni kuma na ja ki muka je” Sosai na ji ɗaci har ƙasan raina jin wai ba zan yi aure ba alhalin a duniyar nan babu abin da na fi so kamar na yi aure na haifi yara.A daidai wannan lokaci ne kuma na ji wani abu game da Banah,ko da a ce auren bogi ne to zan karɓe shi ko ba komai dai za a kira ni sawun ma'aurata kuma zan haifi ƴaƴa. “Ƙusumbin da ke gare ki ba zai taɓa barin maza su yi sha'awarki ba,in akwai waɗanda da za su so ki to ki sani mata ne ƴan uwanki ” Deborah ta faɗa tare da kamo hannuna alamun rarrashi. “Wannan furucin naki duk ƙarya ne,kin faɗi haka ne saboda kin jima kina sha'awarta wannan dalili ne ma yasa kika tunzura ta har kika kai ta karɓa muƙamin iko alhalin wa'adin karɓarsa bai yi ba.Kin san cewa muddin Maa nada rai ba za ki taɓa samun Naomi ba” Banah ya faɗa yana mai shigowa ɗakin. Kallon tsana Deborah ta soma binsa da shi kafin ta ce “muddin ina raye ba zan taɓa bari ka cutar da Nao ba” Ya yi wani murmushi kafin ya ce “na gode da tunatarwa ” sai kuma ya maido dubansa gare ni yana jefo mini kallon so da ƙauna ya ce “ ki sa a ranki Banah yana sonki kuma zai zauna da ke ko da kuwa dukkan jikinki ciwo ne” Wata ajiyar zuciya na sauke jin furicinsa ,kafin na dubi Deborah na ce “ba zan so ki tsani Banah ba saboda shi ɗin murfin rufin asirina ne.Deborah ki sani zuciyata ba za ta taɓa lamunta rashin miji ba” Kai ta girgiza mini tana mai cewa “Banah ba mijinki ba ne,in ma dai akwai shi to ba na ce a jinsinmu ba ne don kuwa tarihi bai nuna hakan ba” Da sauri Banah ya zo ya shiga tsakiyar mu yana mai ɗan ture Deborah ya ce “dama ba tun yau matsafan tarihi ke ƙirƙirar ƙarya ba domin cimma manufarsu” kallona ta yi,sai na kawar da kai ita kuwa da sauri ta fita. ★ “Ba zan taɓa lamunta ki auri ɗan maƙiyiyata ba,ki sani cewa ko bayan raina kika auri Naslam ban yafe miki ba“ Dadda ta faɗa tana yi wa A'ishah wani mugun kallo. “Ki haƙuri Dadda amma ina son yarima fiye da raina,ki sani cewa in kika hana ni aurensa to tamkar kin yi mini shamaki da duk farin cikin duniya” A'isha ta faɗa tana hawaye. Dadda ta yi mata mugun kallo kafin ta ce “da dukkan alamu har yanzu ba ki warke daga cutar haukan naki ba,ɗan matsafiya kike sha'awar aure ki haɗa zuri'a da shi?” Ta dubi mahaifiyar tata da jajayen idonta kafin ta ce “ Dadda babu wanda ya tabbatar cewa Ummi Naslam na yin tsafi,kawai ƙage aka yi mata wannan dalilin ne ma yasa ta bi dare ta bar masarautar nan” “Wato ƙage na yi mata? Don ubanki da idona na gani tana tsafi.Tashi ki ɓace mini ko na sabauta ki ” ta ƙarashe cikin tsawa,da wani irin sauri kuwa A'ishah ta fita daga ɗakin direct can baya ta nufa inda tantabarun yarima suke.Tana zuwa ta yi tsaye tana kallonsu yadda suke ciyar da junansu da kuma yadda suke yin wanka, murmushi ta soma yi tana jin sonsu ba don komai ba saboda yadda ta san muhimmancinsu a gun yarima.Daga bayanta ta ji muryar Barham yana mai cewa “har sai yaushe ne za ki bayyana asalin fuskarki? ” Ba tare da ta juyo ba ta ce “ ranar da ka bar ɓoyen taka!” “Amma ai kin san ni da ke ba ɗaya ne ba,magani nake bayarwa domin sanin wasu tsirrai dole sai na haɗa da Magic ” A'ishah ta juyo tana wani murmushi kafin ta ce “me yasa kake saka mini ido a lamurrana? Bayan ni ai ka san waɗansu masu ɗauke da kambun baka me yasa ba za ka takura musu ba ?” “Ki iya bakinki ko kuma...” ta yi saurin katse shi da cewa “ko kuma me? Ka je ka sanar da sarki? Hahaha! To bari ka ji abin da har zuwa yanzu tsafinka bai nuna maka ba,hatta yarima Naslam maye ne,yana ɗauke da kambun baka ” Cikin zafin rai Barham ya ce “ ki sani cutar kambun bakan yarima daga Ubangijin Ka'aba take ba wai ta tsafi ba ce,ke kuwa uwarki ce ta saka miki ita.A kullum cikin yin ƙoƙarina nake na ganin na magancewa Yarima cutar nan saboda na san hankalinsa zai tashi muddin ya farga” Shiru A'ishah ta yi tana nazarin kalamansa,wai ita Dadda ce ta saka mata maitar baka hakan na nufin kenan hatta Dadda matsafiya ce? Ba tare da ta ce masa komai ba ta yi saurin barin wurin ta koma can sashensu.Sai dai tana shiga ta tarar da Dadda cikin wani irin yanayi wanda da ace normal mutum ce ita da tabbas har taɓin hankali za ta iya samu. Dadda ce cikin siffar maciya tana a tsaye gaban madubi idonta a rufe tana furzo kalaman tsafi tana haɗawa da sunan mahaifiyar yarima Naslam. A'isha ta yi tsaye tana kallon cikin madubin wanda yake ta fitar da tiriri tamkar an ɗora shi kan wuta har wani hazo-hazo ke tashi. Ummi ce ta gani wato mahaifiyar yarima Naslam tana zaune kusa da ruwa da alamu so take yi ta wuce amma ta kasa shiga ruwan.A kallon farko da za ka yi mata za ka fahimci cewa kaf illahin jikinta dabaibaye yake da mugun baƙin tsafi. Dadda ta yi wata mahaukaciyar dariya tana mai fito da harshe waje tana yin wani tsafin A'isha sai gani ta yi Ummi ta faɗa ruwan,ba ta san lokacin da ta fasa ƙara ba ta ce “Ummiii?” hakan ya jawo hankalin Dadda matsafiya ta kuwa juyo da kanta ta kalli A'ishah tare da juya idonta suka fitar da wani haske ya je ya shiga A'ishah nan take ta faɗi ƙasa a sume. Dadda ta yi saurin komawa normal kafin ta je ta dubi ƴarta,hannuwanta ta kama ta soma janta ƙiii har ta kai ta kan shimfiɗa. Wata kwalba ta ɗauko ta gubar tsafi ta buɗe tare da dangwalo maganin ta shafawa A'ishah babu jima ta buɗe idonta tarau sai dai babu ɗigon baƙi. Dadda ta soma sarrafa tsafi babu jimawa kuwa duk maganar da A'ishah ta yi ita da Barham ta shiga tariyo kanta.Dadda ta naushi iska tana mai cewa “ wato dai mugun tsohon nan ba zai taɓa fita hanyata ba” sai kuma ta luluɓa bargo ta fice ta bar masarautar. A ɓangaren yarima Naslam kuwa a daren ranar haka ya kasa sukuni,yana kwance yana tunanin Naomi haɗi da yin surutunsa ba tare da ya san cewa ba zanen hotonta da ke ƙarƙashin pilow yana naɗar duk wata magana da zai yi ta yadda ita kuma za ta ji komai cikin ƙwaƙwalwarta. Sai wuraren ƙarfe biyun dare ya samu bacci mai nauyi ya ɗauke shi,mafarkin Naomi yayi.Wannan karon ba mu'amala suke yi ba,a'a takobi yasa zai sauke mata kai bayan an ce ta miƙa wuya ta karɓi shahada ta ƙiya.Yana datsa mata takobin ta yi kururuwa wacce kai ka ce a gaske ne sai ya ji abin har kunnensa.Daidai nan ya farka yana jan numfashi tare da soma yin magana shi ɗaya. ★NAOMI Duk da ban ji daɗin abin da ya faru ba tsakanin Banah da Deborah hakan bai sa na wani damu sosai ba saboda a ganina kowanne yana da hujjar da zai kalubalanci ɗan uwansa.Ita matsafiya ce mai rubutun tarihi,yayin da shi kuma matsafi ne mai ilimin jeji don maharbi ne. Washegari haka muka zaga gari ni da Banah a matsayinsa na mijina,kafin kuma yasa shela mutane suka taru a ƙofar gidanmu.Sabbin dokoki ya ƙara kafawa kafin kowa ya kama gabansa,haka muka zauna ni da shi ina basa labarina yayin da shi kuma ya yi mini alƙawari sai da dare sannan ya bani nasa labarin.Wannan yasa ko da daren yayi a ƙage na ce masa “ina saurarenka bani labarinka ” Maimakon yayi abin da na ce,a'a sai ma fatar dabbar da na suturce jikina da ita da ya yane ya soma yana shirin kai hannu kan jikina na zabura sakamakon kalaman nan irin na jiya da na soma ji suna ziyartar kwanyata ba tare da na san daga ina suke ba. “Ya Rabb! Ka taimaka ka kuɓutar da ni daga dukkan wani tarkon sheɗanu da mabiyansu.Ya Ubangijin al'arshi ka bani kariya a duk lokacin da na fuskanci uƙubar mushrikai kamar yadda ka bai wa Annabinka Ibrahim.Ya Hayyu ! Ya Ƙayyum ! Ya zul...” da wani mugun sauri na toshe kunnuwana ina mai yin wata ƙara don tamkar ana ɗiga mini dalma haka nake ji, wannan dalili ne ma yasa ban bari na ji ƙarashe ba.Jikina na yin ɓari na ɗauki suturata na mayar kafin na buɗe ƙyauren ɗakin,sauri-sauri haka nake tafiya har na isa ƙofar gidansu Deborah . A zaune na tarar da ita kan wani kututturen icce tana kallon sama,da alamu aikin nata ne take yi wato lissafin taurari.Gefenta na zauna ina mai cewa “ki yi haƙuri” “Ki yi tambayarki kai tsaye” ta faɗa ba tare da ta dube ni ba. “Wane ne Annabi Ibrahim ?” na tambaye ta a raunace don hatta faɗar sunan ma yana yi mini wani irin raɗaɗi. “Yana ɗaya daga cikin masu isar da wahayin da Ubangijin Ka'aba ya umarce su da shi.Kamar yadda tarihi ya zo Annabi Ibrahim ya fito daga cikin al'ummar da ke bautar gumaka amma duk da haka shi tun tashinsa bai taɓa bautar wani Ubangijin ba sai na Ka'aba.Al'ummarsa sun so hallakar da shi ta hanyar jefa shi a cikin wuta amma sai Ubangijinsa ya cece shi ya mayar da zafin wutar sanyi mai daɗi ba mai cutarwa ba” Shiru na yi ina nazarin bayanin da ta yi mini,ina shirin tambayarta wane ne shi Ubangijin Ka'abar sai ga Banah ya bayyana a gabanmu kamar walƙiya.Hannuna ya kama yana yi wa Deborah mugun kallo kafin ya ce “ina mai yi miki kashedi na ƙarshe ki fita idona na rufe” Debora ta miƙe tsaye tana cewa “abin da nake da niyyar faɗa maka kenan ka guji wasa da wuta” Tamkar wata sokuwa haka na tsaya ina kallonsu,sam hankalina ya ƙi tsayuwa wuri guda abin da nake son sani shi ne wane ne Ubangijin Ka'aba?????????? [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 06 Maimakon Banah ya kai mu gida a'a daga nan sai ya wuce da mu gaɓar ruwa. “Shawoli narat kohi jayi!” ya furta kalaman tsafi cikin wata irin murya,babu jimawa wata irin ƙara ta karaɗe wurin kafin ruwan ya soma darewa yana fitar mana da hanya.Haka Banah ya ja ni muka shiga muka fara tafiya,ko tsakiya ba mu kai ba aka soma yin ƙasa da mu har muka dangane da ƙasan ruwa.A nan ne na yi arba da tsoffin garinmu waɗanda suka mutu,wasu tun banda wayo a labari ne na ji mutuwarsu yayin da wasu kuma da hankalina suka yi mutuwar. Kamar yadda ake yi wa baƙo in ya zo a wuri haka suka karrama ni,a wannan lokaci ne na ida ganin ainihin ɓoyayyar fuskar Banah shi ɗin ba iya mutum ba ne a'a jinsi biyu ne. Wani abu aka shayar da ni wanda ya dagula mini lissafi ya juye mini hankali na ji tausayi,so,ƙauna da duk wani abu da ya shafi mutumci sun fita daga zuciyata.Sai dab da za mu fitowa ne sannan aka kawo Maa zuwa gare ni,tana tsaye cikin siffar nan ta matattu sai dai yanayin fuskarta ya nuna tana cikin damuwa kamar ba ta jin daɗin rayuwar wannan duniyar. “Maa” na kira ta ina mai shigewa jikinta,yadda na ratsa ruhin nata na fita shi ya sa ni saurin janye wa na koma kan ƙafafuna. “Naomi me yasa har zuwa yanzu ba ki yi wani aikin bajinta ba wanda zai sa ruhina ya mori aikinki? Dube ni yadda na rame har yanzu ruhikan ruwa ba su yi amanna da ni ba” ta faɗa cikin wani irin yanayi. “Maa sam ban gane abin da kike nufi ba” na faɗa . Ta ce “Ta hanyar kashe mutane ne kawai zan samu abinci Naomi ” ta bani amsa ,wato so take yi na fara sarrafa maita ina damƙe kurwar mutane ina kawo mata jininsu. Tana gama bani amsa aka zo aka tafi da ita,Banah ya kamo hannuna muka fito daga ƙasan ruwan.A lokacin da muka isa gida tuni gari ya soma yin haske,cikin son sake kasancewa da ni Banah ya soma yi mini wasu abubuwan amma na dakatar da shi ta hanyar yi masa wani kallo da idona da nake jin tamkar an yi mini musayarsu.Cikin wata shakkata ya janye daga gare ni kafin ya koma gefe yana kallona,murya a dake na soma magana “ka nemo baƙar akuyar da za a yi hadaya da ita,yau laraba ruhika na buƙatar jini” sai kuma na yi shiru kafin can kuma na ci gaba da cewa “ina son jinin mutum domin shayar da mahaifiyata” Sai da na kai karshe sannan Banah ya ce “domin samun jinin mutum ya zama dole ki fita farautar dare,don yin maita da rana tsaka ba halayyar shuwagabanni ce” sai kuma ya taso ya matso kusa da ni ya tallabo haɓata yana mai ci gaba da cewa “matata zafafa ce,na san ta kowanne fanni jaruma ce kuma ƙwararriya.Zan baki shawara mai kyau amma sai in kina so” “Ina jinka ” na faɗa a dake. Ya ce “ki shirya gagarumin yaƙi domin samo tataccen jini mai tsabta wanda ba a gurɓata shi da maita ba” “Su wa zan yaƙa kenan?” “Garuruwan da ke maƙwabtaka da mu mafi akasarinsu ba su sarrafa tsafi ballantana maita,in muka yaƙe su sosai za mu samu alkhairi ” A cikin bayaninsa sosai na tsinci kishin garinmu da kuma son ci gabansa, wannan dalili yasa na ce “bayan an gama ƙaddamar da hadaya,zan so ka haɗa hankulan dukkan mutanen garin nan sannan ka shaida musu a yau ba sai gobe ba za mu je farauta ruhika” Banah ya yi wani murmushi yana mai cewa “an gama” sai kuma ya fice. Ido na lumshe ina tunanin yadda na ga shugaban nan NASLAM da tawagarsa suna yaƙar Mayu.Da wani irin sauri na buɗe idona ina mai yin magana a fili “ yaƙi cikin tsakiyar dare ya fi ɗaga hankali kan da safe,don haka farmakin dare za mu kai musu” sai kuma na yi wani murmushin mugunta wanda hakan ba ƙaramin sanyaya mini zuciya ya yi ba. Kamar yadda na umarci Banah haka ya kawo mini baƙar akuya har da ma zakaru su ma duk baƙaƙe ne.A gaban al'ummar gari muka je muka shayar da kogi jinin dabbobin kafin kuma mu juyo,Banah ya laƙanci tsafi sosai wannan yasa bai sha wuya ba wurin aiwatar da shirinmu na kai farmaki a garuruwan da babu maita. Dab da shigowar duhun dare Deborah ta zo inda nake,haka kawai na ji ban buƙatar ganinta duk da kuwa wani sashe na zuciyata yana tune da ƙawancenmu. “Abin da kike shirin yin sam bai dace ba! Babu wani sarki da ya zo mana a tarihi cewa ya nuna ƙarfin tsafi ya janyo wani yanki izuwa nasa” Deborah ta faɗa ,ba tare da na kalle ta ba na ce “wannan garina ne,ni ce ke da ikon yin duk abin da ya dace ga al'ummar ciki ba ke ba.Ruwanki ne ki rubuta tarihina a cikin littafinki,in kuma ba ki ra'ayi za ki iya barinsa” “Naom...” ban bari ta kai ƙarshe ba na juyo a harzuƙe cikin hargowa,sai kawai ganin Deborah na yi ta yi sama tare da faɗowa ƙasa cikin rauni.Na nuna ta da yatsa ba tare da na ce mata komai ba,amma sosai ta gane kashedi nake yi mata. Wani irin kallo ta soma jefo mini kafin ta ce “ta yaya kika yarda har wani baƙon haure ya raba mu? ” “Shi ɗin mijina ne,don haka na san ba zai yi abin da zai cutar da ni ba kamar yadda ke kike ƙoƙarin danganta ni da masifar rashin yin aure” Hawaye suka zubo kan kumatunta ba tare da ta goge su ba ta ce “na san kin karanta littafin tarihi,kin gani da kanki muddin shugaban tawagar Mayu ta fito a mace babu ƙaddarar aure a rayuwarta,in kuma ta yi shi to ki sani akwai ranar da mulkin sai suɓuce mata.Sannan yadda tarihi ya nuna ke dai babu aure a tarihinki da ya zo da wanda ma zai zo gaba, sannan na faɗa miki sharaɗi in ma kin yi auren to ki sani ba a wannan duniyar ta ruwa ba” Cike da tsana da takaici nake sauraren jawabinta.Da a ce za a tambaye ni babban maƙiyina a duniyar nan a yanzu to babu makawa zan ce Deborah ce,saboda duk wanda ke da ja da lamarin aurena to ban ɗauke shi masoyi ba. Baya na juya mata a karo na biyu kafin na ce “ina shawartar ki da ki bar gidan nan kafin na yanke miki ɗanyen hukunci” Ba tare da ta ce komai ba ta tafi,babu jimawa kuma shi Banah ya shigo hannunsa riƙe da ƙwallon kwakwa ƙwaya ɗaya.Tsakiyar ido ya dube ni kafin ya ce “muddin kina gama baki da matsafin tarihi to mulkinki ba zai taɓa ci gaba ba saboda a kullum so suke su canza maka ra'ayi akan abin da kake buri” “Me za ka yi da kwakwa?” na tambaye shi ba tare da na bai wa abin da ya gama faɗa muhimmanci ba. “Jirgin dare ne na Mayu ,a cikinsa za mu tafi” ya bani amsa.Kallon mahaukaci na yi masa don sam ban san komai ba game da maita saboda ban taɓa gwada yi ba.Sai da dare ya zo tsakiya ne na ga abin al'ajabi yadda Banah ya mayar da kwallon kwakwa jirgi,kuma ma ni ce farkon shiga bayan shi sai kuma ya soma zagayawa da mu yana ɗibar jama'ar gari waɗanda ke ɗauke da kambu maita ko tsafi. A wani gari jirgin namu ya yi dirar angulu,tsit garin yake kowa na yin bacci .Haka muka zagaye shi kafin mu soma sarrafa mugunta muna fito da su daga gidajensu muna cillawa cikin jirgi,duk wanda ya yi gardama a nan take muke aika ransa ga ruhikan ruwa.Cikin ƙanƙanen lokaci garin ya hargitse da ihuce-ihuce da kukan mata da ƙananun yara,gefe ɗaya kuma wuta ce ke tashi. Har mun shiga jirgi za mu koma sai idona ya sauka kan wani gida,shi kaɗai ne ba mu rogaza ba.Kukan jinjiri na soma ji,cikin azama na dire tare da zuwa na ratsa bango na wuce saboda yadda duk ƙwayoyin tsafi suka game jinina. Wata mata ce na tarar a ciki,gefenta jinjiri ne sabon zuwa duniya don ko cibi ba a yanke masa ba.A hankali na duƙa na ɗauki yaron,sai a lokacin kuma na ji muryar matar na cewa “kar ku kashe mini yaro ” yadda na ga soyayyar uwa da ɗa a cikin ƙwayar idonta shi ya tuna mini tawa mahaifiyar. Ban kai ga cewa komai ba Banah ya shigo,kafin ƙyaftawar ido ya soma jan ragamar ruhinta.Cikin gargardar murya na ji tana cewa “ Ash-hadu an la'ilaha illallah! Wa'ash-hadu anna Muhammadu Rasulullah!” wata irin walƙiya ce haɗi da zubar ruwa suka zo a nan take,yayin da kuma ni da Banah muka zabura muka yi baya saboda ɗacin amon sautin abin da ta furta yayin da shi kuma yaron da ke rungume a hannuna ya ci gaba da canyara kuka. “Mu bar wurin nan yi sauri kafin alƙawari ya karye” Banah ya furta cikin wani irin tsoro wanda ban san dalilinsa na yin haka ba.Ina ɗaga kafaɗa haɗi da sake rungume jaririn a ƙirjina na fito,ina shiga cikin jirgin Banah ya jefo mini wani mugun kallo yana kallon jaririn.Na ƙankance ido ina mai ce masa “kar ma ka fara,ka tuƙa jirgi mu tafi” Ba don ransa ya so ba ya ja ragamar jirgin namu na matsafa har muka isa yankinmu,a ƙofar gidanmu aka zube dukkan mutanen da muka kwaso kafin ni na shiga can ciki na bai wa sauran umarnin su tsaya su tsare mutanen. Kan gado na shimfiɗe jaririn,ina shirin kwanciya na ji wata murya a cikin ƙwaƙwalwata tana shaida mini an samu baƙon haure a yankina. Ba tare da na fita ba na yi surkulle na aika Banah can gaɓar ruwan,bai dawo ba sai da gari ya yi haske sai ga shi saɓe da wata mata. Kan tabarma ya shimfiɗe ta,kallo ɗaya na yi mata tal na ji ƙaunarta ba don komai ba sai don na hango tabon ruhaniya a jininta. Fuskarta na shafa nan take ta buɗe idonta,sai kuma ta tashi zaune tana mai kallona da kuma inda take. “Su wane ne ku? ” ta yi tambayar tana ajiye idonta kan gado inda na shimfiɗe jariri.Da sauri kuma na ga ta miƙe tana cewa “me yasa har yanzu ba a yanke cibi ba?” “Ban san ya ake yi ba” na bata amsa. “Bani wani abu mai kaifi” ta furta,na zaro wuƙata na miƙa mata,da ita ta yi amfani ta yanke cibin kafin kuma ta ciri suturar jikinta ta kulle daidai wurin da ta yanke ɗin. “Gefen cikin jaririn duk yayi baƙi saboda mahaifa ta taɓa shi,a kawo ruwa na yi masa wanka” ta sake faɗa . Banah ya ɓata rai yana shirin magana amma na dakatar da shi,na je na kawo mata ruwan.Sai dai tana saka hannunta ciki ta ce “waɗannan ai masu sanyi ne,masu ɗumi nake so” idona kawai na juya ruwan suka soma tafasa suna fitar da tiriri.Sai ta yi ƙuri tana kallona kafin ta ce “wannan tsafi ne kika yi kuma sarki ya haramta haka” Sai muka kalli juna ni da Banah tare da haɗin baki wurin tambayar “wane sarki?” Kai ta girgiza sai kuma ta soma yi wa jaririn wanka,ta saki murmushi ta ce “mace ce ashe” sai ta fito da ita daga cikin ruwan,ta cire uban kallabin da ta yane kanta da shi ta saka jaririyar a ciki. “Wace ce ke?” na tambaye ta. “Ni kaina ban sani ba,amma sai nake jin tamkar an aiko ni nan ne saboda isar da wani saƙo” ta bani amsa tana mai ɗago kai ta dube ni.Idona ya sauka kan goshinta nan na ga irin tabon nan da ke a goshin NASLAM ita ma yana fitar da haske sai dai bai cutar da ni ba,hakan kuma sai ya yi mini daɗi na ji a raina cewa ko da a ce ita ma wannan Ubangijin Ka'aba take bauta ma zan iya zama da ita. ★ Wuraren ƙarfe tara na safe daular abu NASLAM ta samu wani rikitacen labari.Cikin ƙarfin hali da dakiyar zuciya yarima ya miƙe kan ƙafafunsa bayan ya yi wanka da magani ya kuma sha a cikin shayi. Cikin tafiyar jarumta ya soma ratsa dakarun har ya isa inda Sarki ke tsaye yana jawabin yadda komai zai kasance,kamar kuma yadda Sarkin ya tsara jakariya Ali ne zai jagoranci tafiyar. “Zan tafi ni ma don haka a shirya dokina” ya faɗa yana mai kallon mahaifinsa cikin ido.Sarki ya kawar da kai,don ya san ko da a ce ya yi yunƙurin hana shi ba zai ji ba. Haka duk suka fito kowanne ya hau doki,da yarima zai hawa kan nasa sai da jakariya Ali ya taimaka masa amma a haka suka tafi. Tun a bakin ƙofar shigar garin suka fara cin karo da kayan tashin hankali,babu shiri yarima ya diro yayin da kuma jakariya Ali ya soma take masa sawu. Gawarwakin mutanen da aka kashe,Ali ya kalla sai ya ga duk kusan kalar mutuwar iri ɗaya ce.Ya kai hannu ya damtsi ƙasa sannan ya kai kusan hancinsa ya sunsuna,yarima ya dube shi tare da cewa “me ka fahimta?” “Farmakin Mayu ne” ya basa amsa,ran yarima ya ƙara ɓacewa amma a haka suka ci gaba da duba ko ina har suka shiga gidan da matar nan ta haihu. Cak jakariya Ali ya tsaya yana kallon ustaza Jamila,wacce ta bayar da dukkan lokacinta domin yin hidima ga addininta.Yarima ya ƙarasa yana mai cire rigarsa ta sarauta ya luluɓe ta,tare kuma da baiwa dakaru umarnin a ɗauke ta a kai ta can masarauta tun yanzu ba sai an jima ba...... [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 07 Ustaza Jamila ƙanwa ce ta jini ga jakariya Ali,mijinta ma ya mutu ne a wajen yaƙin haɓaka musulunci sai ga shi ita ma ta mutu wurin da'awar jawo hankulan waɗanda ba musulmi ba.Kamar yadda tsarin masarautar yake,suna aika maza da mata garuruwa don koyar da mutane karatu. Yarima NASLAM ya dafa kafaɗar jakariya Ali yana mai cewa “ dukkan rai zai ɗanɗani mutuwa,ka sa a ranka lokacinta ne ya yi.Mu ma muddin namu yayi babu makawa a duk inda muke mutuwa za ta riske mu” Idon Ali sun kaɗa sun yi ja sosai,muryarsa ma cikin wata irin sarƙaƙiya take fita.“Na yi imani ga Ubangijin Ka'aba,dukkan wata ƙaddara mai kyau da akasinta daga gare shi take.Sai dai babbar damuwata ɗaya ce ,cikin jikinta sam babu shi a yanzu hakan yana nufin kenan ta haihu in kuma ya tabbata haka ina jinjirin yake?” Shiru yarima Naslam yayi na wani ɗan lokaci kafin ya ce “a duk inda yake Ubangijin Ka'aba ne zai tsare shi,ka dai kawai ka sa kyakkyawan yaƙini ga ubangijinka ” kalamansa suka yi tasiri a zuciuar jakariya Ali, wannan ya basu damar ci gaba da binciken ko ina. Bayan sun gama haka suka haƙa rame aka rufe sauran kafin su juyo su dawo masarauta inda Sarki Haroon da sauran al'umma ke dakon jiransu. Suna shigowa sarki ya je ya tarbi yarima tare da soma tambayarsa abin da ke faruwa. “Farmakin Mayu ne,duk sun kashe mutanen gari da alamu kuma sun tafi da wasu.Babban baƙin cikin shi ne ba su bar wani sawu ba da zai sa mu gane ta ina suka fito ” Barham da duk ya ji abin da yarima ya faɗa sai ƙara matsawo yayi yana mai cewa “a yadda ka yi bayanin ya tabbata cewa wannan rundunar Mayun ta samu jagoranci Banah maharbi” Sarki da yarima Naslam sai duk suka maido dubansu ga Barham ɗin,shi kuwa kai ya jinjina kafin ya ci gaba da cewa “tarihin da ya fara zuwa na wannan ƙarnin ya bada labarinsa,Banah maharbi ne kuma babban matsafi wanda ya fito daga tsatson aljanar ruwa.Mahaifinsa ya kasance masinci ne,ya iya ruwa sosai a irin alƙawarin da mutane ke ƙullawa da ruhikan ruwa mahaifin Banah ya yi gamo da wata aljanar ruwa har yayi tarayya da ita suka same shi.Tun da aka haife shi a cikin jeji ya tashi tare da fatale da aljanu,kafin mahaifinsa ya mutu ya koya masa farauta da kuma baƙin tsafi na ƙarnin baya sannan kuma ya ɗora shi kan turbar yi wa aljana ZAƘUMA bauta” Barham na kawo nan da zancensa masarautar ta ɗauki wani salo,guɗa ce kamar an kawo amarya ta karaɗe ko ina kafin kuma iska ya soma tashi babu jimawa kuma aka soma yin wasu yayyafin jini. Hankali a matuƙar tashe Barham ya ce “Attakbirrrr!” Dukkan mutanen da ke wurin suka amsa da “Allahu Akbar!” nan take yayyafin jinin ya tsaya cak wanda duk ya ɓata fuskokin mutane.Sai kuma sararin samaniya ya soma ɗaukar launin ja yana nuno inuwar wata halitta marar kyawun gani can ita ma ta ɓace komai ya dawo normal. Ran sarki da na yarima ya ɓace,saboda ba tun yau suka saba ganin ire-iren waɗannan surkullen ba. Barham ya ce “ Aljana ZAƘUMA ce,wato uwar gijiyar Banah da ita yake tsafi.A kullum yana shayar da ita jinin mutane,ita kuma tana basa ƙarfin iko ” “Ina zan samu shi Banah ɗin?” yarima ya tambaya. Barham ya ce “Ubangijin Ka'aba ne kawai ya san daidai ina yake a yanzu,saboda tamkar guguwa haka Banah yake bai zama wuri ɗaya yawo yake yi gari-gari yana shanye jinin al'ummar yankin” Yarima zai buɗa baki ya sake yin magana amma sarki Haroon ya dakatar da shi ta hanyar cewa “yanzu abin da ya fi muhimmanci shi ne yi wa ustaza Jamila sutura,don haka a kira gimbiya A'ishah ta yi mata wanka” Sai a lokacin ne kawai Ayyub ƙanen sarki Haroon kawai ya saka bakinsa,“ gimbiya A'ishah tana kwance babu lafiya tun jiya,na so na sanar da kai sai kuma wannan al'amari ya danne niyyata ” Hankali a tashe yarima ya ce “meke damunta?” “Ciwon ido ne mai tsanani ,idanunta sun zama kamar gauta ” Ayyub mahaifi ga gimbiya A'ishah ya faɗa . Yarima bai ƙara cewa komai ba ya shiga can ciki,direct kuma sashensu gimbiyar ya wuce. A kwance ya tarar da ita don tun lokacin da Dadda ta fice ta bar ta take nishin azaba idonta sai ƙara ciwo suke yi saboda ta ga abin da bai kamata a ce ta gani ba. Tana jin muryar yarima ta yi ƙarfin halin buɗe idon nata sai dai tamkar mai ɗauke da sabuwar makanta haka take ji dole ta ja su ta rufe. “A'ishahhh?” ya kira sunanta cike da tausayinta.Murya na ƴar rawa ta amsa da “na'am yarima” “Mene ne ya shiga idonki?” ya sake jefo mata tambaya,sai dai ba ta kai ga amsawa ba jakariya Ali da Barham suka shigo. Barham ya matsa kusa da kanta yana ajiye jakar kayan aikinsa,bai ɓata lokaci ba ya soma zuba magani yana wanke mata idanunta duk da yana haɗawa da Magic babu wanda ya sani in ba ita gimbiya A'ishar ɗin ba. Cike da aminci ta buɗe idonta da suka dawo normal tana kallon Barham da yake yi mata ta idanu. “In yau na wanke miki ido kin samu lafiya ki sani gobe ba zan yi ba,zan bar ki da mugun halinki ” “Ban taɓa ganin inda maye yake gorantawa ɗan uwansa ba sai kai Barham” ita ma ta basa amsa ta ido. Ya ce “ni ba maye ba ne,ban taɓa yin maita ba hasali ma ina adawa akan duk masu yinta.Ke ma kin san cewa iya Magic kawai nake yi shi ma ba don komai ba sai don ci gaban masarauta” “Me yasa dole sai ni kake son na bayyana kaina? Don me shi yarima ba ka damu da tasa maitar ba?” ta tambaye shi,sai dai shi Barham ɗin bai bata amsa ba ya juye kansa ya mayar da dubansa ga yarima Naslam yana mai cewa “ba wani babban abu ba ne ya same ta,kawai wani ɗan tsautsayi ne” Yarima NASLAM ya dube ta yana mai cewa “ki kwanta ki huta” sai kuma ya fice jakariya Ali na take masa baya. Wasu mata aka samu suka yi wa ustaza Jamila wanka.Sai da aka ma fito da gawar ne sannan gimbiya A'ishah ta san abin da ke faruwa,sosai ta ji zafin mutuwar har da zubar da hawaye.Ana yi mata sallah aka kai ta gidan gaskiya,sai kuma a wannan lokacin ne jakariya Ali ya nuna rauninsa ya soma yin hawaye waɗanda zubar da su ba ƙaramin sanyaya masa zuciya suke yi ba. Sai da aka yi kwana uku ana jimamin mutuwar ustaza Jamila kafin kuma lamurra su ci gaba da tafiya. A yau ne yarima yasa aka fito da matsafiyar nan da ta raira waƙa tsafi.Gaban sarki aka gurfanar da ita,tare da umartar ta da ta faɗi laifinta. Amma ta yi shiru ta ƙi cewa komai sai yariman ne ya shaidawa sarki yana mai ƙara wa da “a yanke mata hukunci nan take ban son ajiyar mayya a cikin masarautata ” Sarki Haroon ya kafe ta da ido yana kallo kafin ya ce “ki amsa laifinki sannan ki tuba ki rungumi addinin Musulunci domin tsira da ranki” “Babu wani addini da zan shiga,na fi son zama babu alƙibla.Sannan kuma ni ba mayya ba ce duk da ina da ilimin sarrafa maitar,maganar ƙarshe kuma ita ce zan koma gida” Rai ɓace yarima Naslam ya zaro takobinsa da niyyar sauke mata kai amma jakariya Ali yayi saurin riƙe shi yana cewa “ka nutsu yarima kar ka yi saurin yanke mata hukunci jira na kira Barham” Zuciyarsa na ƙuna ya ce “ba ka ji yadda take magana ba sam babu ɗa'a?” bai ma kai ga cewa wani abu ba Barham ɗin ya shigo. Kallo ɗaya ya yi wa matar ya gane wace ce ita,hakan yasa ya ƙarasa gun sarki yana mai yin ƙasa da murya ya ce “kar ku kashe ta,za ta yi mana amfani a nan gaba” sosai sarki yake ɗaukar shawarar Barham saboda shi ɗin aminin mahaifinsa ne sannan kuma dattijon arziki na masarautar. “Ku mayar da ita” sarki ya faɗa wanda hakan sam bai yi wa yarima daɗi ba sai kawai yayi zuciya ya fita daga wurin. Jakariya Ali ya bi bayansa yana mai cewa “ gaggawa aikin sheɗan ne,matar can tana ɗauke da wani ɓoyayyen sirri wanda nake jin cewa ita ce makullin da za mu yi amfani da shi wurin buɗe duk wata ƙofa da ta yi mana wuyar shiga” Ba tare da yarima ya ce masa wani abu ba ya soma cire kayansa na sarauta yana ajiye wa.Toilet ya shiga ya soma yin wanka ko zai ji sassauci,har ya fito jakariya Ali na nan.Shi ne ma ya taimaka masa wurin tsane jikinsa ya saka kayan zaman gida,daga nan sai suka wuce can inda tantabarunsa suke. Yana son tsuntsaye, wannan yasa ko ƙunci yake sai ya ziyarce su yake jin daɗi.Jakariya Ali ya buɗe su,da gudu kuwa duk suka shiga fitowa suna nufo shi,ɗaya ta sauka kan kafaɗarsa ya kai hannu ya damƙo ta yana shafar jikinta yana murmushi. Sai ya ji kamar ana kallonsa,ido ya baza cikin tantabarun nan idonsa ya sauka kan baƙuwar tantabara idonta ƙurrr kansa.Kasancewar bai yarda da canfi ba sam bai kawo komai a ransa ba,haka ya ratsa ya je ya ɗauko ta wani irin shock ya ratsa shi nan ɗin ma bai sa a ransa wai lamari ne da ya shafi sprituality ba. Jakariya Ali ne kawai ya farga da abin da ke faruwa,amma kuma sai ya ja bakinsa yayi shiru.Duk yadda yarima ya so tantabarar ta saki jikinta amma abu ya cuttura kawai sai ya wuce da ita can ɗakinsa yana mai cewa “ban san daga ina ita wannan ta zo ba,da alamu ta ƙi sabawa da sauran ne” Jakariya Ali ya ce “ dama ai kullum cikin samun baƙi tantabaru ake yi,ita ma za ta saba” Cikin ɗakinsa ya sake ta,ai kuwa sai ta shiga yin walwalar. A can ɓangaren gimbiya A'ishah kuwa abubuwa ne duk suka dagule mata,ga rashin ƙawarta Jamila ,ga ɓatan Dadda kusan kwana uku har yanzu ba ta dawo ba,ga kuma yanayin jikinta da take jin ya sauya.Zaune ta yi cikin halin ƙaƙanikayi tana wasiƙar jaki,sai ta ji ana magana ƙus-ƙus ba ta jin abin da ake cewa, da ta nutsu sosai sai ta gane a cikin drower kayanta.A hankali ta je ta buɗe,ɓerayen da suke gurgurar kayanta suka saki ihu a tare wannan karon sarai ta ji abin da suka ce. “Wayyo an kama mu yanzu an yi ƙoƙarin kashe mu” shi ne abin da ɓerayen suka faɗa kafin su fara gudun tsira,har kan ƙafarta ɗaya ya faɗo amma ta kasa yin motsi saboda shock.Ita maitarta iya ta juya baƙi ya dawo fari ce,sai ga shi yau ta ƙara samun matsayi.Jikinta ne ya hau rawa,babu shiri ta nufi ƙofa don zuwa wurin Barham ta sanar da shi sai kuma ta yi kiciɓis da Dadda wacce ta dawo daga jejin Mayu.Da sauri ta ja baya,ita kuwa murmushin mugunta ta sakar mata tana mai cewa “Allah yasa dai ba ƙoƙarin tonawa kanki asiri kike yi ba? To ki sani muddin yarima ya ji labarin ke mayya ce to zai fasa aurenki, ba kuma zai yi jinkiri sauke miki kai ba kin fi kowa sanin halinsa fiye da ni yadda bai da tausayi akan mayu” Idon gimbiya A'ishah ya kawo ruwa,yanzu ne kawai ta yarda da maganar Barham .Tabbas a matakin da take a yanzu ta riga da ta makaro babu ta yadda za a yi ya cece ta. Dadda ta ci gaba da yi mata gargaɗi mai ban tsoro,“ in kuma kin shirya yin mutuwar kare sai ki je ki faɗa ,sanin kanki ne hatta sarauniya Sarat ta bar masarautar nan saboda laifin maita ballantana ke karan kaɗa miya ” “Amma Dadda ni ban ce miki ina son zama mayya ba,don me za ki bani kambunta?” gimbiya A'ishah ta faɗa . Dadda ta bata amsa da “saboda duniyar nan muddin babu maita da Magic to tamkar miya ce babu magi,ki zo na nuna miki mece ce ainihin rayuwar Mayu na tabba in kika ga irin shagalin da ake yi ke kanki za ki ji daɗi ki kuma gane gata ne na yi miki ” shiru gimbiya A'ishah ta yi kafin ta je da gudu ta rungume Dadda. ★YANKIN MUTUWA Zuwan baƙuwar haure daga duniyar turɓaya shi ya canza mana yanayin shigarmu.Na ajiye fatar dabba na koma saka kaya,waɗanda Banah ne da kansa ya shiga duniya shi da sauran matsafa suka kwaso su a can duniyar tuɓaya.Kai tsaye za a iya cewa suka sato,saboda dare ne suka bi suka dinga shiga kanti suna ɗebo kaya bayan an kawo haka aka zube su aka rabawa kowa ciki kuwa har da ƴar jaririya da na samo wacce har zuwa yanzu ba a saka mata suna ba. Ummilo shi ne sunan da nake yi wa matar wacce duk ƙoƙarin Banah na son saka mini tsanarta bai yi nasara ba. Zaune na yi ina kallon yadda take bai wa baby madarar da aka tatso daga dabbobi.Hannu na kai na shafi fuskar Babyn ina mai cewa “Ummilo wane suna kika zaɓa mata?” Ta yi wani murmushi mai ƙayatarwa kafin ta ce “ina son sunan Jamila saboda na riƙi ƴa mai irin sunan nan” sai kuma ta yi wani irin shiru kamar mai yin nazari,a nan ne na fahimci cewa kamar ƙwaƙwalwarta na son tuna wani abu da ya danganci rayuwarta. Ina shirin yin magana sai gani na yi gari ya ɗau wani irin duhu,yayin da kuma mutanen da na zube suna yi mini hidima suka soma yin ihu.Duk yadda na so yin tsafi abu ya cuttura,kamar minti biyar sai komai ya dawo normal.Idona na sauke ƙasa sai na ga duk ɗigon jini ne ta ko ina kamar an yi ruwansa,ina ɗago kai kuma muka haɗa ido da Banah fuskarsa kicin-kicin kafin ma na kai ga tambayarsa sai cewa yayi “ tun da kika shigo da jaririyar nan a yankin nan bala'i ya soma sauka,don haka mun yanke shawara ni da sauran matsafa za mu bayar da jininta matsayin hadaya ga ruhikan ruwa........ [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 08 “Ta ya za ka ce a ɗauki jaririya a kai wa Teku matsayin hadaya? Wannan sam ba mai yiyuwa ba ne.Wannan al'amarin da ya faru kuma ko kaɗan bai da haɗi da da jaririya Mila wani baƙin ƙulli ne daga maƙiya kuma zan binciko na gani duk masu hannu a ciki” na faɗa . Banah ya ƙanƙance ido yana kallona,na je da sauri na ɗauki Mila daga kan cinyar Ummilo na goge mata fuskarta da yayyafin jini ya ɓata.Can ɗaki na yi tsinke,ina daidaita mata kwanciya ya shigo yana mai cewa “ita kuma Ummilo sai yaushe za ta tafi tun da kin karya doka kin ce ba za a kashe ta ba” Ba tare da na juyo ba na basa amsa da “ nan ɗin masarautata ce,Ni ke da ikon barin wanda zai zauna da kuma wanda zan kashe,ka tsaya iya matsayinka na mijina in ina son shawarinka ni ce da kaina zan neme ka” Cike da takaici Banah ya fito daga ɗakin ya jefi Ummilo da wani mugun kallo wacce yake jin tsanarta sai dai fa alƙaluman tsafinsa sun kasa rubuta sunanta .Direct can bayan gari ya nufa,bai yi nisa ba ya soma furzo kalaman tsafi nan take busashen ganyen da ke zube a ƙasa ya soma tashi sama kafin kuma ya haɗa wata baƙar guguwa wacce ta yi ambaliya da gangar jikinsa ya ɓata .Cikin wani kogo ya bayyana mai ɗauke da kunamu baƙaƙe ƙirin kuma ga su manya-manya.Suna ganinsa duk suka soma basa hanya,shi kuwa haka ya dinga ratsa tsakiyarsu har ya isa can ƙarshen kogon inda wata halitta ke kwance tana ƙyafta ido kamar mai jin tsoron buɗe su ɗin. Zubewa yayi yana mai yi mata sujuda ba tare da kuma ya ɗago ba yake cewa “kin ce in na dinga shayar da ke jini za ki ɗaga martaba ta fiye da duk wani mai iko a duniyar nan,amma me yasa Naomi ke yi mini gardama akan hukuncin da na zarta alhalin hatta maganin laƙani na sa an shayar da ita shi” Ba ta basa amsa ba,sai fara saukowa da ta yi daga kan dutsen da take kwance ta zo ta fara hawan bayansa tare kuma da laulaye shi da bindinta.A hankali ta zagayo kanta kan ƙirjinsa,babu ɓata lokaci kuma ta buɗe bakinta tare da kafa masa haƙoranta masu mugun tsini ta soma tsotsar jininsa na wani lokaci kafin ta tashi sama tana wani irin kuka kamar jiniya.Dukkan kogon ne ya tsaya cak kamar babu wata halitta mai numfashi,muryarta ta soma fitowa “ka karya dokata,na faɗa maka duk wacce za ka aura to ya zama dole ka yi tarayya da ita a wannan daren sannan ka bani jinin budurcinta.Tun da har ka bijire to ya zama dole a gare ka da ka yi haƙuri da wasu ƙananun al'amurra.Sannan ita wannan mata da kake tsana ta kasance shugaba ce a wata mazaɓar duniyar ruhaniya muddin ka yi kuskuren cusa kanka a lamarinta to za ka tsinci litininka a laraba ” Sai da ta dire kalamanta sannan Banah ya ɗago,idonsa sun kaɗa sun yi ja kamar na baƙin maye.Aljana ZAƘUMA ta soma saukowa daga can saman ta zo dab da shi ta na hura ƙirjinsa wanda ya fitar da sawun haƙoranta,sai kuma ta ci gaba da cewa “a jefa jiragai cikin ruwa domin fara saye da sayarwa tsakaninku da wasu garuruwa,ta wannan hanya ce zan samu yadda nake so” tana gama faɗar haka ta cillo shi tsakiyar gari.Bai ma koma can gida ba ya wuce gaɓar ruwa,sai ya tarar da manyan jiragai guda biyu.Tsaye yayi ya lumshe ido tare da soma yin magana da ruhikan ruwa,bayan sun amsa masa ne ya tsaga yatsansa jini ya zuba a cikin ruwan da kuma jiragen. ★Naomi Bayan fitar Banah kalar nawa tsafin na yi don binciko su wane ne suka fara yi mini zamba cikin aminci,sai dai babu wanda aka nuna mini fuskarsa illa aljana ZAƘUMA.Banda ilimin tarihi wannan yasa ban san wace ce ita ba,haka na fito na samu Ummilo na tambaye ta. “Babu matsafin tarihi a wannan yanki naku?” ita ce tambayar da ta yi mini. Na ce “akwai sai dai mun yi kare jini,biri jini da ita kwanan baya” Ta ce “ke ce shugabar duk wani da ke garin nan,don haka ki aika kawai ta zo” na yi shiru na wani ɗan lokaci kafin na ga kuma eh ta yi gaskiya. Takarda na nemo da tawada na soma yin rubutu,bayan na gama sai na dinga murza ta ina yin furucin tsafi a hankali babu jimawa kuwa takardar ta fita daga hannuna ta yi sama.Ido na birkice ta yadda komai zai wakana ina gani,cikin aminci Deborah ta samu wasiƙar na yi tunanin ba za ta zo ba sai ta bani mamaki kuwa yadda ta ɗauko hanyar zuwa nan tana tafe iska na ƙara yin gaba da ita. Tana isowa ciki sai na ga ta yi tsaye tana kallon Ummilo kafin da sauri ta buɗe kuɗin da ke rungume a ƙirjinta.Sai ta rufe shi tare da sake kallon Ummilo cikin wani irin yanayi ,kamar wacce ba ta son taka ƙasa haka ta ƙaraso tare da yin tsaye. “Ranki shi daɗe ga ni na samu saƙonki ne a yanzu” ta faɗa cike da ladabi,sai kuma na ji babu daɗi yadda ta zubar da duk wata dangantaka da ke tsakaninmu ta bani matsayin shugabarta. Da ido na yi mata nuni da ta zauna,ta cire takalminta na fata ta zauna tare da maida hankalinta a gare ni. “A cikin tarihi wace ce aljana zaƙuma?” “Aljana ce mai matuƙar santsi da farin fata,tana ɗauke da kambun Maitar shan jini.Lokutan da ta fitowa shi ne dare musamman wuraren jeji ko kusa da rijiya.Tana jan hankalin mazaje musamman maharba don su ne suka fi shiga jeji,tana fitowa cikin siffar barewa haka za ta yi ta wasa da hankalin maharbi har sai ya faɗa tarkonta sai ta ja shi izuwa duniyarta” Deborah ta faɗa tana mai buɗe littafinta sai ta nuno mini hotonta,kallo ɗaya na yi masa na kawar da kai.Sosai ta fito a siffar mayyar shan jinin kuwa don bakinta kaca-kaca yake da jini. “Kika ce maharba sun fi shiga tarkonta ?” na tambaya. “Eh haka tarihi ya zo da shi” “Meke faruwa bayan ta kama mutum?” “Tana kai shi wani kogo ne,sai ta basa zaɓi biyu.Na farko zai bauta mata,in kuma ya ƙi zaɓi na biyu shi ne za ta kashe shi” Ummilo na duba ina mai cewa “dukkan alamu sun nuna ita ce ta zo yau don har yayyafin jini aka yi” “Hakan na nufin tana son jan ra'ayin wasu mazajen ne ,don haka mu zama cikin shiri” Ummilo ta faɗa . Deborah ta girgiza kai tana mai cewa “ Aljana ZAƘUMA ba ta taɓa bayyana a wurin da ba a ambace ba ko kuma sunan ɗaya daga cikin waɗanda ke baƙin tsafi da ita.Tun da kuka ga ta zo to tabbas a garin nan akwai mai yin aiki da ita” Da wani mugun sauri na dube ta,a cikin ƙwayar idonta na hango tana zargin mijina Banah da wannan ɗanyen aikin.Ban san me ta gani ba ita a nawa idon sai ci gaba ta yi da cewa “ta yiyu kuma wucewa ne kawai ta zo yi,don haka za ki iya yin watsi da lamarin mu gani in za ta sake dawowa” Numfashi na furzar tare da jinjina kai,Ummilo ta karɓi littafin tarihin tana mai cewa “ina mugun son labarun tarihin ƙarnin da ya wuce musamman a kan maita,shin a page lamba ta nawa ce zan samu tarihin Mayu da kuma yadda suke rikiɗa daga bil'adama zuwa dabbobi?” Deborah na shirin yin magana Banah ya shigo hannunsa riƙe da manyan kifaye,da dukkan alamu kuma ya ji tambayar da Ummilo ta yi duba da yanayin yadda fuskarsa ta cika da tsantsar mamaki. “Jira na zo na fayyace miki komai Ummilo ” ya faɗa yana mai miƙawa wata hadima kifin ya zo kusa da ni ya zauna sannan ya karɓi littafin tarihin ya mayar wa Deborah da kayanta sannan ya kamo dukkan hannuwan Ummilo ya ce “a duk lokacin da mutum yake son rikiɗa zuwa dabba da farko zai ɗan rage tsayi sannan ya furta kalaman tsafi yana mai tsayar da ƙwayar idonsa wuri guda ba tare da ya ƙyafta ba.Bari na nuna miki ta yadda za ki gane sosai” sai ya saki hannuwanta tare da yin tsugunne ya soma magana a hankali amma duk muna iya jiyo sautin.Cak kuwa ya tsayar da idonsa suka bar motsi,babu jimawa ya koma narkeken kare baƙi ƙirin yana wani fito da harshe waje. Duk da ni ma yau ne karon farko da na ga canjin siffa sam ban ji wani tsoro ba sai ma burge ni da lamarin ya yi na soma yin murmushi. Cikin firhici Ummilo ta furta “ Ya Ubangijin Ka'aba ka tseratar da ni daga sharrin wannan halittar” sai kuma ta soma yin ihu tare da tashi za ta zuba a guje,ni da Deborah muka yi saurin taro ta yayin da Banah ya yi baya yana haushi cikin hassala. Hakan da yake ba ƙaramin ƙara firgita ta ya yi ba,ni kuma lura da hakan yasa na juya na yi masa tsawa sai a lokacin kawai ya dawo cikin siffar bil'adama. Ummilo ta soma furzo wani zance “kar ki cutar da ni Ummu A'ishah ki sani ban taɓa aikata maita ba,wacce ke maƙale a ruhina ba sayenta na yi ba kyauta ce daga wasu ruhikan da ke zuwa mini cikin MAFARKI (MRS SADAUKI akwai littafin nan na MAFARKI complet mai so zan barsa shi a 700 maimakon 1k) .Ban so ki bari in ba haka ba zan tona miki asiri na faɗa kowa ya sani ke ce mai yin Maitar dare” tana kawowa nan sai numfashinta ya tsaya cak sai da muka tallabe ta tare da shimfiɗe ta. Deborah ta ce “ da dukkan alamu ita ma ta fito a yanki da ke maita duk da dai a yadda take furuci Maitar ba ta yi ƙarfi ba.Sannan ita wannan Ummu A'ishar tana ɗaukar siffar kare ne a duk lokacin da za ta yi maita ” Banah ya matso yana cewa “ai da na san haka ne da na ɗauki wata siffar,amma sam ban yi haka da wata manufa ba” Na ce “kar ka damu na fahimta,daga yau sai ka kiyaye” ya jinjina kai. Deborah ta ce “ni zan koma,in ta farka ki ce ina yi mata sannu da jiki” haka muka rabu. ★ Yarima NASLAM ne kwance yana yin bacci yayinda tantabarsa ke tsaye ƙiƙam tana kallonsa sai da ta gaji don kanta kafin ta ɗaga fukafukinta ta je ta sa ƙafafunta ta ciro shi sama tare bi ta window da shi ta fita.Haka ta dinga zaga duniyar ɓoye da shi yana cikin wani yanayi wanda shi ba bacci yake yi ba kuma idonsa ba a farke ba. Cikin wani jeji mai cike da dragon ta sake shi ,shuuu yayi kamar zai faɗi amma sam jegaran ba su bari hakan ta faru ba haka suka buɗe fukafukinsu wuri ɗaya ya faɗo a sama. Kafin kuma su kai shi kan wata lafiyayar shimfiɗa da aka yi da ganyen furen floris. Yarima NASLAM ya ja wani dogon numfashi tare da ɗan ware idonsa,nan ne ya yi arba da sarauniya Naomi cikin shigar ganye,ta rufe ƙirjinta da fatar lemun zaƙi kugunta kuma ta suturta shi da bayan albasa.Gashin kanta kuwa ya ci ado da ganyen lemu,tafiya take yi cikin yanga da jan hankali har ta zo gare shi.Kan shikinsa ta kwanta tare da yi masa rumfa kafin wasu lamurra su biyo baya waɗanda suka kusan sheƙa shi lahira.Yana gama samun nutsuwa ya farka daga baccin,a kan shimfiɗarsa ta asali ya samu kansa ƴar tantabarsa na can gefe tana bacci. Ya dafe kansa yana jin wani irin takaici na rufe shi,saboda shi babu wacce ya tsana irin aljanar mafarkinsa.A gajiye kamar wanda yayi mu'amalar a gaske ya ƙoƙarta ya tashi tare da shiga toilet,sai dai fa babu ruwa ba ciki babban bokitin ruwan ba.Ya ja tsuki ya fito kafin ya soma ƙwala kiran sunan jakariya Ali,dama ɗakinsa yana kusa da nasa babu jimawa kuwa ya shigo hannunsa riƙe da sharɓeɓiyar takobi duk a tunaninsa farmaki ne aka kawo musu. Turus yayi ganin iya yariman ne kawai a ɗakin,ya yi saurin ajiye takobin yana mai cewa “ranka shi daɗe me kake buƙata?” “Babu ruwa a banɗaki” yarima ya faɗa yana jin ƙyanƙyamin kansa,da sauri jakariya Ali ya fita babu jimawa ya dawo jaye da baro an lodo ruwa a ciki.Banɗakin ya shiga ya juye ruwan kafin ya fito,sai a lokacin yarima ya shiga sai ya ga hatta bahon wankan Ali ya cika masa shi da ruwan. Kwanon da ake zuba ruwa a ciki domin yin alwala ya ɗauka ya soma wanke hannunsa sau uku bayan ya ɗauki niyyar wankan.Daga nan yayi ɗahara sai ya wanke kansa tasss kafin ya game jikinsa duka,daga ƙarshe ya kurkure bakinsa ya kuma yi shaƙar hanci.Sai a lokacin kawai ya ji nutsuwa ta ratsa shi sai ya shiga bahon wankan ya kwanta a ciki,tunanin gimbiya A'ishah yake son yi amma da zarar ya fara cankar surarta sai fuskar Naomi ta zo ta yi fakan-fakan a dole ya haƙura ya fito ya ɗaura alwala ya zo ya fara yin sallar nafila. A ɓangaren gimbiya A'ishah kuwa tsakiyar dare Dadda ta tashe ta,tana shirin yin magana amma Dadda ta toshe mata baki tare da janta suka je bakin window suka yi tsaye suna fuskantar farin wata da ke wasar ɓuya cikin giza-gizai. Dadda ta soma yin magana a hankali tana cewa “a wurin Mayu dare shi ne lokaci mafi tsaro domin farauta,duk da cewa ana iya sarrafa maita safe ko rana amma irin wannan lokutan an fi yinta a cikin siffar bil'adama yayin da ita kuma ta dare ake ɗaukar ɓoyayyar siffa.Yau zan nuna miki romon da muke sha duk dare ni da sauran Mayu na wannan Daular ” Cike da mamaki gimbiya A'ishah ta ce “dama bayan ke akwai wasu Mayu a cikin daular nan?” Dadda ta yi wani irin murmushi kafin ta ce “idonki za su yi matuƙar mamaki in ki ka ga wasu mutanen” tana gama faɗar haka sai ta jimƙe hannun gimbiya A'ishah tana furta wasu surkulle nan take suka sama wasu ƴan ƙananu kamar sauro tare da tashi sama suka bi ta window..... Za ku iya fara yin payment domin shiga paid group . 500 ta wannan account: 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank Shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ 09 Yana ɗaya daga cikin tabi'un Mayu yin yawon dare a lokacin da mutane ke yin bacci,saboda babu dare yana ƙunshe da sirrika dayawa.Gimbiya A'ishah baki da hanci ta buɗe tana kallon duniyar ƙasa,cike kuma da burge wa da ban sha'awa take ware idonta tana kallon gidajen da aka rufe babu bismillah.Kamar misalin tukunya ce babu murfi,haka idon Mayu ke gane gidajen da ba a ambaci sunan Allah ba a lokacin da ƙafa ta tsana za a kwanta. Suna cikin shawagin suka yi ta haɗuwa da jiragen dare na Mayu, waɗanda suka kasance na tsafi ba wai zahiri ba. “Duk ina za su je Dadda? Ya na ga mutane cikin gwangwanin kifi?” gimbiya A'ishah ta tambayi mahaifiyarta sai dai kafin ma ta bata amsa wani jirgin na tsintsiyar tsaye ya bi ta gabansu shuuu yana ɗauke da wata tsohuwa da kuma ƙaramin yaro. Dadda ta yi murmushi tana mai cewa “A'ishah a duniyar ɓoye abubuwan da ba za su taɓa faruwa ba ne a duniyar zahiri suke gudana a nan ɗin.Muna amfani da duk wani abu da kika sani matsayin jirgin farauta,kamar irinsu turmi,jan zanen isimi,tsintsiyar tsaye da sauransu.Ke ma in kina sha'awa ai za ki iya hawa madadin ki yi yawo kamar leda” “To mene ne banbancinsu Dadda?” “Sauri! In kin hau jirgi kin fi saurin zuwa inda kike so,ko ba ki lura yadda mutane ke ta wuce mu ba?” “Na gani,amma me yasa mu ba mu shiga ba?” “Dama ina son fayyace miki komai ne,amma yanzu da zarar wata tawagar mayun za ta wuce zan tsayar da su don rage mana hanya” Ai kuwa babu jimawa sai ga wata tsohuwa zaune kan baƙar akuya mai ƙahonni dogaye.Dadda ta tsayar da ita tare da neman alfarma,tsohuwar ta ƙara matsawa gaba gimbiya A'ishah ta fara hawa sannan Dadda daga ƙarshe.Kamar wani babur haka akuyar tsafin ke keta hazo da su. Gimbiya A'ishah wacce duniyar ɓoye take sabuwa a wurinta sai cewa ta yi “ita ma akuya tana cikin jerin jiragen yawo?” Wannan karon tsohuwar ce ta bata amsa bayan ta yi ƴar dariya mai fitar da zallar tsufanta,ta ce “ jikata ita akuyar nan protector ɗina ce,suna da banbanci da jirgin dare saboda ita tana numfashi sannan kuma tana kare ni daga dukkan sharri” gimbiya A'ishah ba ta kai ga cewa wani abu ba tsohuwar ta yi ƙasa da ƙahonnin akuyar sai ta yi shuuu ta fara yin ƙasa har ta sauka a wani babban gawo wanda ya cika tanƙam da Mayu da kuma matsafa. Girki ake yi kan wata tunkunya wacce ke da zanen ƙwarangwal ta buɗe baki.Gimbiya A'ishah ta sauko daga kan akuyar tana wani riƙe Dadda ,ita kuwa sai cewa ta yi “ wannan ita ce TUKUNYAR MAYU ( ga mai son complete na Tukunyar Mayu yayi mini magana zan yi masa discount) duk dare muna haɗuwa a nan mu ci abin da wasu daga cikinmu suka yo farauta” Sai kuma Dadda ta ja ta suka ƙarasa,hannu ta saka cikin tukunyar da ke ta faman tiriri ta tsamo wani abu mai kamar zare amma su a wurinsu nama ne,bakin gimbiya A'ishah ta kai ita kuwa ta buɗe ta saka mata sai ta soma ci tana jin wani irin yanayi na ratsa ta. Dadda ta saki murmushi tana jin wani sanyi na luluɓe ta,a yanzu shirye take tsaf wurin tursasa ƴarta ta auri yarima Naslam ba don komai ba don ta san a cikin tabi'ar Mayu babu kara babu jin kunya,hatta uwar da ta kawo su duniya suna iya damƙewa ita kuma babban burinta shi ne ta bayar da yarima NASLAM a dafa shi kowa ci kamar yadda yasa aka yanke wa Ummarta hukunci kisa daga kawai asirinta ya tonu ta damƙe kurwar iyayen jakariya Ali. Bayan sun gama cin naman sai idanun gimbiya A'ishah suka ƙara buɗewa ta soma gani tarau ,babu abin da ba ta iya gani da ke jikin mutum ko dabba.Rawa suka soma yi suna zagayen wuta,duk da mutane sosai hakan bai hana ta gane wasu fuskokin ba sosai kuma ta yi mamaki kamar yadda Dadda ta ce mata tun kafin zuwansu. Alfijir na dab da ketowa suka koma gida,ta inda suka fita ta nan suka shigo.A gajiye duk suka zube suka ta yin rankon baccin da ba su yi ba. A ɓangaren yarima Naslam kuwa tun bayan sallar asubah ya je ya samu sarki da maganar aurensa da gimbiya A'ishah.Ya yi haka ne duk don ya bar mafarkin Naomi,ba tare da ya san alƙaluman ƙaddara sam ba su rubuta masa auren wata mace ba bayan maƙiyiyarsa. Gari na yin haske sosai sarki ya bada shelar baikon yarima zai kasance a yau bayan sallar asar in sha Allah. Jakariya Ali ne ya dinga taimaka masa wurin shiryawa,yana daidaita masa hullar sarauta a kai ya ce “kana ganin kun dace kai da gimbiya A'ishah?” “Me ya ja ra'ayinka wurin yin wannan tambayar?” cewar Yarima yana kallon mai tsaron lafiyarsa Ali . Shi kuwa kai tsaye ya ce “na ga ba sonta kake yi ba” “Haka kuma ban ƙinta“ “Duk da haka dai ya kamata a ce ka yi dogon nazari,na fi yi maka sha'awar auren soyayya gaskiya” “Ita ma ina sonta tun da har na damu da ita” yarima ya faɗa yana mai zuwa bakin gado ya yi zaune,jakariya Ali ya duƙa ya soma saka masa takalmi yana mai cewa “in kana son mutum bai kai sai ka faɗa ba,ayyukanka ne za su bayyana hakan” “Ko ma dai mene ne na yanke shawarar zan aure ta,kuma ta dace da ni tun da tana da addini sosai iya wannan ya wadatar” yarima ya faɗa yana tsayar da idonsa kan tantabarsa wacce ta yi wani saƙo kamar mai sauraren hirar da suke yi. Jakariya Ali ya juya ya dubi inda yake kallo,sai ya saki ɗan murmushi kafin ya je ya ɗauko ta ya miƙawa yarima.Ya karɓa tare da soma shafar kanta,“zan je na duba na gani in sun gama shirya wurin taron” Ali ya faɗa tare da ficewa. Yarima ya miƙe tsaye tare da zuwa bakin window yana kallon yadda ake ta kai komo cikin masarautar.Ko ina yayi kyau,hatta dawakai an yi musu ado na sarauta .Dokinsa wanda yake hawa a duk lokacin da zai fita yayi wani irin kuka,tantabarar hannunsa ta fizge tare da fita a guje tana kaɗawa yarima iskan fukafukinta da sauri ya lumshe ido kafin kuma ya ware su yana kallon yadda ta je ta hau kan dokin,duk wannan ɗin ma bai sa ya zargi wani abu ba kawai murmushi ya yi tare da fita. Masjid ya fara zuwa,bayan an gama sallah ne duk aka dugunzuma zuwa wurin da aka ware domin gudanar da shagalin bikin baikon. Zinare sarki ya ware masu yawa ya bayar matsayin kyautar mun gani muna so.Ayyub wanda ya kasance mahaifin gimbiya A'ishah da matuƙar farin ciki ya shaida wa dukkan taron jama'ar ya bai wa yarima damar auren ƴarsa,duk sai aka yi kabbara tare kuma da yin addu'o'i kafin a fita zuwa can inda za a yi wasar dawakai. Ta madubin tsafi Dadda ke kallon komai,tun lokacin da aka yi shelar yin baikon ta shirya baƙin tsafi mai ƙarfi ta tura domin hallaka yarima.Ita dai gimbiya A'ishah cike take da farin ciki duk gajiyar nan ta jiya sai ta neme ta duk ta rasa,duk da cewa kuwa ta sha bacci sosai sai wuraren goma na safe ta farka.A bakin mahaifiyarta kuma ta ji abin da ke faruwa,sosai ta so a ce ta fita ta ga yadda komai ya wakana sai dai hakan haramun ne a masarautarsu zuwan mata a irin wannan taron. Cikin rangaji ta ƙaraso ta zo ta yi tsaye ita ma tana kallon yadda ake wasar tseren .Wani irin murmushi ya suɓuce mata lokacin da ta ga yarima Naslam ya je kusa da dokinsa za su yi wasar tseren shi da wanda ya yi nasara akan dukkan dakarun da aka tsara wasar da su.Ita ma Dadda nata murmushin ta saki tana jin cewa saura ƙiris burinta ya fara cika don ta jefa kibiyar tsafi akan dokin yarima saboda in ya hau shi sai ya masakance. Yarima ya hau kan doki yana mai ambaton sunan Allah tare da yin kabbara,Dadda ta ɓata fuska tana mai ɗan satar kallon gimbiya A'ishah wacce har yanzu murmushi ya ƙi barin fuskarta. “Dadda dube shi ki ga yadda yake da ƙwarjini da cikar zati, wannan shi ne mijin A'ishah ” “Haka ne ki yi fatan Allah yasa ya ci gasar kar ya kwabsa abin ya zama abin goranta miki” Dadda ta faɗa tana mai shafar madubin haɗi da yin wani surkulle daidai nan su yarima suka fara gudun.Ƙafar dokin ta ƙure da ido ta na shirin aika masa wata gubar tsafin kawai sai ganin bakin tsuntsuwa ta yi ya caki madubin ya tarwatse. A tare suka ja ba,kafin su kalli juna.Da wani irin gudu kuma gimbiya A'ishah ta fita don jikinta ya bata babu lafiya,mayafinta ta ja ta rufe fuskarta lokacin da ta isa filin sukuwar. Yarima NASLAM wanda ya lashe wasar tseren dokin ya juyo yana kallon inda take a tsaye,suka haɗa ido da sauri ta sunne kai tana wani murmushi kafin ta juya da sauri ta koma.Ya ja numfashi yana jin a ransa ya yi dacen mata. ★ An ɗauki tsawon lokaci kafin Ummilo ta farfaɗo wannan karon ma tana yin wasu kalamai a cikin Yaren da ban fahimci me take nufi. “Alhamdulillahi lazhi ahayana ba'ada ma'amattana wa'ileyhi nushur” ta furta tare da ware idonta a kaina,na sakar mata murmushi na ce “sannu Ummilo” ba ta amsa ba sai martanin murmushin da ta maido mini tana mai shafar gefen fuskata kafin kuma ta miƙe ta fita.Haka na take mata baya sai na ga ta shiga banɗaki,can kuma ta fito ta soma wanke hannuwa da baki da fuska da hannuwanta hatta kai da kunne sai da ta shafa haɗi kuma da wanke ƙafafu. Mayafinta ta gyara kafin ta zo ta fara yin wata irin bauta da ban san ta mece ce ba,ni dai ido kawai na tsura mata da na ga ba ta da niyyar idawa kawai na je gun baby Mila na ɗauke ta dama tun ɗazu ta tashi.Madara na soma bata tana sha tana kallona cikin ido, murmushi na saki ina jin sonta na ratsa ni. Banah wanda tun bayan abin da ya faru ya koma can ƙofar gida yayi tsaye,sai yanzu ya shigo yana mai tambayata “mene ne can Ummilo ke yi?” “Ina kifin har yanzu ba a gama dafawa ba?” na tambaye shi ,don sau tari in yayi mini tambayar da raina bai so ba nuna masa nake yi kamar ban ji ba sai na ɗauko masa wani zancen. Fita ya yi ba tare da ya ce mini komai ba,can kuma sai ya dawo riƙe da kwano yana tiriri.Kamshin kifin ya daki hancina,nan take yawuna ya tsinke sai na shimfiɗe Mila na karɓa na soma ci shi kuma Banah yana aukin kallona.Ina gama ci na ji wata kasala ta rufe ni,sai na kwanta ni ma sai a lokacin kuma Ummilo ta shigo. Banah ya ce “ga kifi nan da Naomi ta rage ki ci” Da fara'a kuwa ta karɓa tare da gyara zama ta sa hannunta,sai dai fa ta gagara ci sai yamutsa fuska take haɗi da yunƙurin kai shi bakinta.Can dai ta haƙura tare da ajiye kwanon tana mai girgiza kai ta ce “in na ci wannan ai tamkar na cinye kaina ne,a'a sam maita ai ba hauka ba ce da zan ci jinsina ” Banah ya ƙanƙance ido yana kallonta kafin kuma ya fice ya bar mu.Maƙoshina ne na ji yana wani irin zafi kamar ana hura wuta,murya kamar ta mai koyon magana na ce “Ummilo sanyi nake ji ki rufe ni” sai kuwa ta miƙe ta ɗauko bargo ta luluɓa mini.Daga wannan kwanciyar ban ƙara farkawa ba sai washegari da zakara ya fara cara,na buɗe idona da suka yi mini nauyi kafin na yunƙura zan tashi sai dai na kasa sakamakon bayana da na ji ya riƙe kafaɗata ta ƙara nauyi. “Banah?” na kira sunansa kasancewar ni da shi ke kwana a ɗaki ɗaya,Ummilo kuwa cikin jerin ɗakunan da aka yi daga baya take kwana ita da Mila. Shiru ban ji motsinsa ba,sai na ƙara yunƙurin tashi a wannan karon gangar jikina ta baro shimfiɗar sai dai na gagara tsayuwa kan ƙafafuna na faɗi kwacaaa.Jeren kwanukan da ke ɗakin duk ya baje,ƙarar ta jawo hankalin Ummilo ta shigo tana tambayar lafiya sai dai muna haɗa ido da ita ta ɗau haske.Da sauri ta zo ta taimaka mini na miƙe tsaye tare da riƙe ta gam,murya na ɗan rawa na ce “ki kai ni banɗaki na yi wanka” ita ce ta kai ni,sannan kuma ba ta fito ba sai da ta yi mini wanka.Bayan ta saka mini kaya sai ta miƙo mini wani icce ta ce na riƙe,na karɓa ina jin ƙusumbina da ya ƙara girma ya rinjaye ni na yi mini wani motsi..... My book is only 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [28/04 13:15] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐 """"""""""""""""""""""" LoVe aNd HoRrOr StOry☠️ ```MRS SADAUKI```💫✍️ FCWA☀️ ____________________________________________ Daga yau discount ya ida. Last free page 10 Wata rusunawar dole ce ta zo mini saboda girman ƙusumbina ya wuce a yi kwatance sam tsayuwa ko tafiya babu sanda ba zai yiyu a gare ni ba.A haka na fito daga banɗakin ina jin wasu canje-canje na daɗa ƙaruwa a jikina,ban zame ko ina ba sai a ƙofar gida inda mutane birjit ke a wurin dukkansu kuma a ƙarƙashin ikona suke.Tamkar sun ga ubangijinsu haka duk suka tsaya da abin da suke yi suka zube ƙasa tare da yin kwanciya suna yi mini wani irin kirari da ba a taɓa yi mini shi ba.Idona na ƙanƙance ina kallon Banah da ke can ɗan nesa da ni yana wani irin murmushi da ban san mene ne ma'anarsa ba,don ko kaɗan ban zargi cewa a cikin kifin da ya bani na ci ba ne wannan girman ƙusumbin ya ƙaru. “Sabbin dokoki sun sauka,don haka al'ummar gari ku kasance cikin shiri ga dukkan abin da shugaba za ta zartar” Banah ya faɗa yana mai takowa yana doso inda nake hannunsa riƙe da kwari da baka. Sai da ya zo dab da ni sannan ya saita kibiyarsa a sama yana mai furta ɗalasiman tsafi,ji kake shuuu kafin wata wuta ta baje a sama.Babu kuma jimawa sauran jama'ar gari suka fara ɓullowa ta kowace kusurwa,tuni wurin ya ɗauki harama ya cika tanƙam.Sai kuma a lokacin ne na soma yin magana,“daga yau an zartar da yin hadaya duk ƙarshen mako,ruhikan ruwa su ne ke da alhakin zaɓar wanda suke so ko dai mu ɗauke shi mu bayar ko kuma su da kansu su kira mutum zuwa can domin ɗaukar ransa.Abu na gaba shi ne duk wani jinjiri da za a haifa sai an kai shi bakin kogo uwa gijiya ta saka masa albarka tare da ƙa'ide masa adadin shekaru ko watannin da zai yi a duniya” Yanayin fuskokinsu duk sun nuna ba su ji daɗin wannan sabon tsarin ba,sai dai babu wani mai zarrar yi mini magana duba da irin ƙarfin ikon da ya ƙara hawa kaina ba tare da ni kaina na shirya masa ba. A haka aka watse na koma ciki na tarar da Ummilo a zaune ta yi uban tagumi.Tana ganina ta miƙe tsaye tare da nufo ni,“na tuna wace ce ni ” shi ne abin da ta furta mini.Cike da jin daɗi na ce “kin tuna? Kai wannan babban abin farin ciki ne amma ya na ga ba ki murna?” Idonta ya kawo ruwa tana mai cewa “na fito a yankin da aka haramta maita da kuma tsafi,ba tare da shuwagabannin sun yi la'akari cewa ba babu wani babban tarihi da magabatanmu suka shuɗe suka bari kamar Magic,ita Maitar ma ba ta fiya ƙarfi ba. Surukina kafin mutuwarsa ya yi matuƙar ƙoƙarin wurin ganin ya daƙile duk wata baƙar shirka,sai dai abin takaici Mayun ne suka haɗin gwiwa wurin kai shi barzahu.Wannan ya fusata mijina har ta kai shi da yin wani tsari shi ne kafa masarauta,yasa an gina babban wuri tare da yin shelar duk wanda ya shirya karɓar addinin gaskiya to ya shigo a cikin sabon ginin da aka yi.Ta wannan hanyar ce aka yi walƙiya aka gano mayu da matsafan cikinmu,sai ya soma yaƙarsu har ya yi nasara a kansu.Sai dai abin da bai sani ba ita maita bibiyar jini take yi,ga shi dai ya kashe tushenta amma bai cire inda ta yabanya ba.Sannu a hankali lokaci na tafiya mace-mace ya fara yawaita a daular,a bisa binciken wani mai bayar da magani ya gano cewa cutar maita ce sai kuma aka ƙara ƙarfafa tsaro.Tun ana yi wa mutum afuwa in an kama shi da cutar maita har aka zo zamanin yarona inda ya yanke ɗanyen hukuncin cewa duk wanda aka kama da laifin maita ko tsafi kisa ne kawai” tana kawowa nan ta yi shiru tare da kamo ni tana cewa “zo ki zauna hakan za ki gaji sosai,ya kamata ma Banah ya nemo miki sanda mai kyau” Kan kujerar da aka sassaka da icce ta zaunar da ni kafin ta ci gaba da bani labarin. “Mahaifin matar ƙanen mijina shi ne mutum na farko da ɗana ya fara cirewa da hannunsa saboda laifi mafi muni da ya aikata ya kashe mahaifan hadiminsa wanda ya ɗauka tamkar amininsa.Ƙarfin wannan raɗaɗin ya saka ita kuma matar ƙanen mijin nawa ta ɗauki tsanar duniya ni da ɗana ta ɗora mamu” nan ɗin ma shiru ta yi tana kallona tsakiyar ido da dukkan alamu akwai wani sirri mai nauyi da take son sanar da ni wanda baki ba zai iya furtawa ba. Ta idonta kuwa ta shaida mini cewa “ni mayya ce! Ina ɗauke da kambun Maitar prophecy” sai kuma ta yi saurin janye idonta daga cikin nawa kafin ta je da sauri ta shige ɗakinta.Na lumshe idona tare da buɗe su kafin na yunƙura dakyar ina dogara sanda na take mata baya. A zaune na tarar da kan shimfiɗarta,na ajiye sandar hannuna ni ma na zaune tare da kamo hannunta.Sai ta ɗago ta dube ni tana wani irin murmushi da ya fi kuka ciwo kafin ta ce “ban taɓa yin maita ba,ban taɓa cin ɗan wani ba kawai dai abin da na sani wani lokacin ina rikiɗa na zama kifi a irin haka ne har ita Dadda ta ganni cikin wannan siffa shi kenan ta je ta sanarwa sarki ai ni ma mayya ce.Ba tare da maganar ta fita waje ba aka titse ni sai na faɗi gaskiyar magana,in kuma na yi shiru na ƙi faɗa gobe gaban al'ummar gari za a yanke mini hukuncin kisa bayan an tabbatar shi ne kawai na yanke shawarar bin dare na gudu.Amma duk da haka bai ishi Dadda ba sai da ta jefe ni da baƙin tsafi ta haukata ni” Na ce “don me yasa kika gudo kika bar ahalinki? Me yasa ba ki zauna ba ki sanar da su babu wata baiwa a duniyar nan da ta wuce maita? In ma ba ki son a sani ai sai ki ɓoye kayarki ” Kai ta girgiza mini tana mai cewa “akwai wani garin magani da ake shaƙawa mutum a hanci muddin yana da ɗigon maita a jininsa to zai bayyana cikin ɓoyayyar siffarsa ne ya dinga tonawa kansa asiri” Na ja dogon numfashi kafin na ce “shi kuma yaronki fa,kin yi tunanin halin da zai shiga bayan tafiyarki? Me yasa ba ki taho da shi ba?” Wani murmushi ne wannan karon ya suɓuce mata bai bayyanar da tsantsar farin ciki da dukkan alamu tana mugun son ɗan nata.Ta ce “Ba fa yaro ne ƙarami ba,ko a lokacin da na bar masarauta ya haura talatin da ɗaya kawai dai a idona ne nake ganinsa ƙanƙane” “Me sunansa?” Kai ta girgiza cike da kunya tana mai cewa “a al'adarmu ba mu faɗar sunan ɗan fari, wannan yasa na yi masa laƙabi da Noor” Samun kaina na yi ni ma da yin murmushin kafin na ce “me Noor ɗin ke nufi?” “Haske!” ta bani amsa. Na ce “zan so na gansa kuwa,da na ji daɗi sosai ni ma zan yi babban yaya” ina faɗar haka sai ta ɗan ƙara matsawa ta jawo kaina ta ɗora kan cinyarta,sai ta cire luluɓin kaina ta soma warware manyan kitson kaina tana mai cewa “wata rana za ki gansa ai ” “Yaushe kenan?” “Ranar da lokacin komawa ta can ya yi,ai zan tafi da ke ne ki ga yayanki in ya so sai Banah ya tsare miki daularki ” Shiru duk muka yi,bayan ta gama warware kitson sai kuma ta ɗebo ruwa ta zuba yaɗo ta wanke mini dogon gashina sannan ta ƙara yi mini wani kitson mai kyau duk da ƙwaya biyu ne kacal amma ya yi kyau.Wunin ranar ne muka ƙara yin wata shaƙuwa ta musamman ni da Ummilo ta dinga bani labarin Yaya Noor lokacin da yana ƙarami da kuma abubuwan da yake so da waɗanda ke saurin saka shi fushi. “Wane abinci ya fi so?” na samu bakina da tambaya. “Gurasa da zuma,yana matuƙar son cin gurasa yana dangwala ta a cikin zuma” ta bani amsa tana murmushi. Na ce “ni ma ina son zuma,kullum in na je farauta sai na je na nemo ta na sha” “Wato yayanki kika ɗauko wajen son zaƙi.Bani labarinki,ina iyayenki suke?” Ummilo ta faɗa . Wani iri na ji duk babu daɗi kafin na ce “dukkansu sun mutu,shi Abbana ban san shi ba ita kuwa Maa a ranar da na karɓi prophecy ɗina ta yi gushewa.Ina sonta sosai,ina jin kewarta a kodayaushe samunki ne ya maye mini gurbinta nake jinki tamkar ke ce ita” na ƙarashe faɗa hawaye na silalo mini masu zafi.Na ƙanƙame ƙafar Ummilo ita kuwa ta shiga shafar kaina haɗi da rarrashina kafin ta ce “ina matsafiyar tarihi sai yaushe za ta zo?” “Ta ce na yi miki sannu da jiki ma tun jiya ” “Ina amsawa,ina ne gidansu?” “Ita ma ba ta da iyaye mahaifinta ya rasu,mahaifiyarta kuma an damƙe ta” “Ayya ki ce ta dawo nan wurina sai mu zauna tare” Ummilo ta faɗa ,sam ban ji zan iya yi mata muso ba hakan yasa ba tare da na shawarci Banah ba na ƙara aika saƙon wasiƙar tsafi zuwa ga Deborah ba ta kuma ɓata lokaci ba ta zo har da ƙullin kayanta.A ɗakin Ummilo na yi mata masauki ,a ɗan wunin da muka yi a tare sai kuma muka ƙara ɗinkewa ni da ita muka manta mun taɓa samun saɓani. Da dare muna zaune bayan mun gama cin abincin,Ummilo na ririga Mila da ke yin rigima ta ƙi yin bacci sai ta soma rera waƙa wacce ta saka mu duk nutsuwa.Ba da Yaren da muke magana ba ne,haka kuma ba Yaren tsafi ba ne wani yare ne can daban da ita kaɗai ta san ma'anarsa amma sosai na ji daɗin baitin.Babu jimawa Mila ta yi bacci sai ta shimfiɗe ta tana murmushi tare da cewa “a duk lokacin da Noor ya fitine ni da kuka wannan waƙar nake rera masa ko kuma in ina son saka shi bacci” "Amma Ummilo da wane yare ne wannan?” na tambaya,Deborah da ke rubutu cikin littafin tarihi ta yi karaf ta bani amsa da “Yaran serena ne,yare ne da halittun ruwa ke yi ita kuma waƙar suna yinta ne domin janyo wani ruhi zuwa gare su domin aiwatar da abin da suke buri” Ido na tsura mata ina kallonta ta hasken farin wata,kafin na ce “ ta ya aka yi kika sani?” “Ta ya ba za ta sani ba,matsafiyar tarihi ce fa” Ummilo ta faɗa . Deborah ta yi murmushi tana mai cewa “tun jiya da na yi tozali da Ummilo na cika da mamakin me ya kawo Siren a nan” Na ce “ai na lura da yanayin yadda kike kallonta,to sai da safenku zan je na kwanta” na faɗa tare da lalubo sandata na miƙe na shiga ciki. Kan gadona na kwanta tare da yin shiru ina nazari,can sai ga Banah ya ratso rufin ɗaki ya shigo.Sam hakan bai kuma bani mamaki ba,illa kawai na mujiya da na zuba masa ina kallon yadda jikinsa ya ƙara rinewa kamar wanda ya fito daga cikin rijiyar kunama. Gefen gadon ya zauna tare da miƙo mini wata ƴar kwalba ya ce “shafa mini” ba tare da na miƙe daga kwancen da nake yi ba na karɓa na soma shafa masa sannu a hankali tiririn dafin jikinsa ya soma disashe ganina. ★ Da dare bayan gama bikin baiko sai aka zauna kan teburin cin abinci.Yarima NASLAM ne da dakarunsa masu taya shi yaƙi,suna cin abinci suna raha yayin da shi kuma yayi shiru yana ta juya gurasar da aka ajiye a gabansa ya kasa ci.Jakariya Ali da ke gefensa ya ce “bari na nemo maka zuma in ba za ka iya ci da markaɗaɗen yaji ba” Ya ɗago ya dube shi tare da yin murmushi kawai, Jakariya Ali ya fita zuwa madafa bai wani sha wahala ba don ya tarar da masu aikin kula da abinci ita ta miƙo masa zumar ya karɓa kafin ya zo ya kawowa yarima. Cikin ƙarfin hali yarima Naslam ya karɓi zumar ya soma dangwala gurasar a ciki ya kai bakinsa,sai dai ko kaɗan bai ji wani ɗanɗano ba.Gudun kar ya ɓata wa kansa lokaci sai ya ture abincin, Jakariya Ali ya dube shi cike da mamaki yana shirin yin magana yariman ya miƙe ya nufi ƙofa sai a lokacin ne kuma Ali ya hango baƙin tambarin maita ya fito yau a bayan wuyan yarima Naslam.Cikin bugawar zuciya shi ma ya miƙe ya fita,bai zame ko ina ba sai gidan Barham.Kamar zai ɓalla ƙofa haka yake bugunta,Barham ya buɗe yana mai kallonsa da mamaki yake cewa “lafiya dai ko?” Sai da ya shige ciki tare da rufe ƙofar sannan ya basa amsa da “ina fa lafiya yau baƙin tabon maita ya fito a wuyan yarima sam ya kasa cin abinci” Barham ya saki kofin hannunsa yana mai kallon jakariya Ali cike da tashin hankali,kafin ya ce “tabo? Wane iri? Baƙi ko ja?” “Na faɗa maka baƙi ne” “Hakan na nufin bayan kambun baka yarima na ɗauke da ɗigon baƙar maita ?” Barham ya faɗa tare da zuwa ya ɗauko wani littafi sai dai duk bincikensa ya kasa samo gamsashiyar amsa ,tsabar firgici goshinsa har ɗigar da gumi yake.Ya ɗago ya dubi Jakariya Ali cike da rauni yana cewa “babu abin da na samu a binciken da na yi” Ali ya ce “ya zama dole mu nemo mafita tun yau kafin gari ya waye ,saboda muddin aka kwana to Maitar za ta rinjaye shi ya fara sarrafa ta ” Idon Barham suka kaɗa suka yi ja,ya rasa meke yi masa daɗi kafin can ya ce “yawwa ina matsafiyar tarihi da aka damƙe?” “Tana can a kulle” ya basa amsa. “Mu je ka kai ni can ita ce kawai za ta bamu mafita” Barham ya faɗa tare da ɗaukar wata takarda.Haka suka dugunzuma zuwa can inda ake ɓoye masu laifi,ko kaɗan babu wanda yayi gigin hana su shiga saboda duk wani dakare a ƙarƙashin ikon jakariya Ali yake shi ne shugaban dakaru gaba ɗaya. Suna zuwa suka tarar da ita a zaune tana yin rubutu a ƙasa,ba tare da ta ɗago ba ta ce “me kuka zo yi? Kun zo tafiya da ni ne a kashe ni ?” Sai suka kalli juna kafin Barham ya yi shahadar cewa “wane laƙani ne ake yin amfani da shi domin daƙile bujurowar baƙar maita tsafi wacce ke bibiyar jini?” Ta ɗago da sauri ta dube su kafin ta ce,“ba zan taɓa faɗa ba ,kamar yadda yake son tozarta al'ummar Mayu da matsafa shi ma sai na bari ya tozarta a idon duniya kowa ya san wane ne shi” Barham ya furta surkullen tsafi sai ga shi tsundum cikin ragar da take ciki,har ƙasa ya zube alamun roƙo kafin ya ce “kar ki dubi wannan ɓangaren,ki dubi matsayinki na babbar matsafiyar tarihi ki sanar da ni laƙanin” Ta kawar da kai tana mai cewa “babu wani laƙani da zai daƙile maitar yariman masarauta ,sai dai a basa magani domin ɓoye ta.Daƙile ta duka kuma dole sai sarauniyar matsafa ce da kanta za ta iya yin haka” “Bani na ɓoyewar” Barham ya faɗa ,ta juya masa baya tana mai cewa “yana can a kusa da duniyar ruwa,fure ne na floris mai matuƙar muhimmanci da zarar ka kai gare shi za ka ji ƙamshinsa na sanar da kai shi ne abin da ka zo nema“ Barham ya miƙe yana yi mata godiya,yana shirin tafiya ta ce “ban ƙare jawabi ba,masu tsaron furen nan fararen fatale ne da ba su aminta da irin tsafinka ba” Barham ya juyo cike da tsoro kafin kuma ya dubi Jakariya Ali ya ce “na gode” Yana fitowa sai kuma suka fara shawarar ta yadda za a yi su fita daga cikin masarauta ba tare da kowa ya gani ba.Jakariya Ali ne ya je inda ake ajiye dokin yarima,kamar yana magana da mutum haka yayi masa bayanin komai kafin ya jawo shi ya fito. Barham ne ya fara hawa don shi ne ya san hanya sannan shi Ali ɗin daga ƙarshe.Cikin amincin Allah suka fita daga masarautar zuwa inda aka shaida musu za su samu maganin,ana kawowa wurin kuwa ƙamshi ya buge musu hanci kafin su yi wani yunƙuri kuma fatale duk sun zagaye su shi kuwa Barham ganin mutuwa a maƙoshi tsautsayi yasa ya furta baƙin tsafi,sai kuwa aka damƙe su aka jefa ɓoyayyar duniya. A can masarauta kuwa yarima Naslam ne kwance a ɗakinsa,har aka yi sallar asuba bai farka ba sai da hasken rana ya hudo ya daki tabon maita na wuyansa,wani irin kuka yayi da ya girgiza masarautar.Daidai nan free page ya ida,duk mai son shiga paid group zai biya kuɗin karatunsa 500 via 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 *Daga yau discount yake idawa 13.April* *NB:* Da zarar book ya kammala kuɗinsa 1k ne. MRS SADAUKI