DUHU DA HASKE by Sakina Isma'il Cameroon [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: utilise ce lien pour intégrer mon groupe whatsapp : https://chat.whatsapp.com/kpwdzw5aq7c2pr2ncz3ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *by* *sakeena ismail cameroon* *(mom muwadda*) 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *marubuciyar* *bazan zauna da kishiya ba* *mijina attajira* *mugun uba* *sai na yanzu da aka fara mai suna duhu da haske*✍️ *kamar yanda na fara lfy allah ubangiji yasa na gamashi lfy* page 1&2 bismillahi rahmani rahim *******Zaune take a kan kujerar dake cikin office din kamar kullun sai juyi take akan kujerar,kallo daya zaka mata ka fahimci tana cikin damuwa, yau ma dai tunanin da ta tsabayin kullun takeyi...dama rayuwata zata canza?dama rayuwata zata koma kamar da?"duk da kuwa lokacin ma bawai ina cikin farinciki bane?amma gwara wancan lokacin akan yan...jin da tayi ana mata nocking kofar office din ne ya sata dawowa cikin haiyacinta"Shigo." Ta fada kamar bata son yin maganar, turo kofar aka yi aka shigo,ba tare da ta dena juyi akan kujeran ba,ba tare da kuma ta kalleta ba tace "Whatttt ?" matashiyar buduwar da kallo daya zaka mata ka fahimci itta din seketariyar tace,ta bude baki kamar jira take ogar tata tayi magana nama,a take ta bata amsa kamar haka... "Ranki ya daɗe kin yi baƙi?" Tsaki wacca aka kira da ranki ya dade taja hade da buga teburin dake gabanta da karfi har sai da seketariya ta tsorata, dagowa tayi hade da tire glass din dake idonta, sai ga fararen idanunta sun baiyana, zubawa budurwar dake gabanta idanu tayi lokaci daya kuma sai ta dauke idonta taga kallon budurwar da take yi. Shiru seketariya tayi tana kallon ogar nata, kyakkyawa,farace sosai dan saboda tsabar hasken da tayi ma har wani yellow- yellow take yi,tana da godon fuska da kuma dogon hancinta daya ƙawata fuskarta dashi sai karamin bakinta dake dauke da Pink din lips idan baka santa ba ma zaka dauka jambaki ta saka,amma a zahirin gaskiya ko powde bata sakawa balle jambaki da kwalli,amma duk da haka tafi wasu da suke mek up din haduwa da kyau. dauke ido sakatariya tayi daga kallon ogan nata da takeyi, hade da juyawa da niyar barin office din sai taji ta kirata "Safna!". Ta kira sunan ta, juyowa Safna tayi tana kallon ogan nata,amma sai taga kayanta ma take hadawa,da alama tafiya zatayi, badan tasan halinta ba da zata iya cewa bata kirata ba ma. har ta fudda rai zatayi magana sai kuma taji tana fadin... "Bazan iya ganin kowa ba".. Ta yi maganar a lokacin da take ficewa daga cikin office din. baki bude Safna tabi ogan nata dashi hade da girgiza kai. tana fita bata tsaya ko ina ba sai wajan ajiye motoci, kafin ta karasa wajan motarta ta kunna ta ,dan haka tana karasa wajan wani daya daga cikin ma'aikatanta ne yazo ya bude mata murfin motar, numshe mai ido tayi kana ta buɗe su,wato alamar godiya,kafin daga visani ta shiga motar. "Ba komai Madam a sauka lfy.." Cewar saurayin dan ya fahimci godiya tayi mai daya bude mata mota,saboda Babu wanda bai san halinta ba,na rashin yin magana. batare da ta ce dashi komai ba tayiwa motar key hade da barin Company . *Nasarawa J.R.A* a gaban wani katon gida tayi hone,in na faɗa muku kyau da gidan yayi ma bata lokaci ne. daya daga cikin security's din su ne yazo ya bude mata gate. Shiga tayi ta motarta tanufi wajan ajiye motoci taje tayi parking,sannan ta fito rike da hand bag dinta"da sauri security's din sukaxo suna mata sannu da zuwa, kai kawai ta iya geda musu sannan ta juya da niyar shiga cikin gidan,sai ɗaya daga cikin security's din ya mika hannu da niyar karbo jakar hannunta, ta daga mai hannu hade da fadin..."Sau nawa zan gaya maka Yusuf?". Tana kaiwa nan ta bar wajan. badan suna tade da itta ba, da sam bazasu taba fahimtar maganar ta ba,saboda in ta fara bata karasawa, Saboda maganarta bata wuce kalma daya zuwa biyu,in kaga maganar ta ya wuce kalma biyu toh da ƙaninta take magana.. tana shiga palon ta tarar da wata mata fara amma kana ganin hasken nata kasan na mai ne ba hasken taba,sabanin na yer tata saboda itta kallo daya zaka mata kafahimci hasken tane ,harkalla Maman nata zata iya yi shekaru 45 zaune take ,akan kujera mai zaman mutun daya ta mika kafafuwanta akan daya daga cikin kananun teburin da suke tsakiyar palon,daya kuma kayan motsa baki kala- kala akai,dan in kaga yawansu ma zaka rantse na mutun goma ne, nan kuwa itta ce kadai takeci,kuma bawai zata iya cinyewa su ba. dagowa tayi tana kallon yer tata da ta shigo yanzu tare da fadin..." AFIYA ya naga kin dawo da wuri yau ?" Maimakon AFIYA ta amsa mata sai ma kallon a bubuwan dake gaban Mamar nata da tayi tana girgiza kai,hade da barin palon ta wuce dakinta. har tazo gaf da bakin kofar dakin nata sai ta sinkari muryar Mamanta na cewa...."Wallhy ki kiyayeni AFIYA yanzu ni zanyi magana kiyi min banza ?" "Sorry Mama." Cewar AFIYA tana karasa shiga dakinta,hade da banko kofah da karfi. "Ki karye kofar ai kudin naki ne sai ki canza wani Hajiya Fatima Maman AFIYA ta fada wacca aka fi kiranta da Hajiya Batulu mai abun mamaki. *cikin layinsu afiya* Majalisan cike yake kamar kullun,daya daga cikin samarin ne ya kalli sauran sai ya fara magana kamar haka.."Ni wllhy da zan samu Afiya ta amince ta aureni da wllhy na more,dan wllhy ina sonta". "Tabbb! kai kuma Aliyu ka rasa wa zakace kana so sai karuwa?". Cewar daya daga cikin samarin. toh ni ina ruwana da wani karuwancinta,ni dai in har zata amince ta so ni ,ta aureni ai shikenn,tunda na tabbata ko shogabangasa aka bashi Afiya da gudu zai amince wllhy, ballantana ni da ba kowa ba,saboda kawai itta din karuwa,sai kuma akace baza'a aureta ba,bari na maka wata tambaya Faisal yanzu in ance ka kawo hujja kana dashi ne ?".Bani dashi Aliyu amma ai babu wanda baisan cewa ita ɗin karuwa ce ba." Cewa Faisal. "Ai shikenan ni dai baza'aci naman wani dani ba." Aliyu ya fada yana mai mikewa, "Ina kuma zaka je Aliyu?"Samarin dake wajan suka hada baki wajan tambayar Aliyu. "Gida zan tafi". "Yanzu dan kawai na fadi gaskiya shine zaka ce gida zaka tafi?."Faisal ya fada yana kallon Aliyu, "Kaga Faisal ka rike gaskiyar ka." Aliyu ya faɗa haɗe da juyowa ya bar wajan. "Kai ma dai Faisal kana da matsala wllhy kasan halin gayennan tsarai ba'a gulmar AFIYA a gabansa amma har yau ka kasa fahimtar hakan."Daya daga cikin samarin ya faɗa. "Dan kawai yana sonta sai inƙi fadar gaskiya? Ni a bunda yafi komai bata min rai ma shine wacca yake yi dan ita bata ma san yana yi ba." Faisal ya karashe magana cikin bacin rai shima,hade da mikewa. "Ina kuma zaka je kai ma?"Zanje nayi shirin zuwa masallaci ."Faisal ya basu amsa hade dayin gaba. "Toh ka jira mu tafi tare mana mu ma muje gida muyi alwalan mutafi masallacin ." Musa ya fada shima yana mikewa dashi da Umar, Ranar dai ahaka majalisan ya watse, Gidan su AFIYA kuwa tana jin a bunda Mamanta take cewa amma uffam bata ce ba,dan tasan halinta tsarai. Ajiye hand bag dinta tayi akan makeken gadonta ta shiga rage kayan jikinta, Kallon dakin nayi,dakin yayi kyau ba kadan ba,duk da kuwa babu wani tarkace sosai a ciki, Dan daga gado sai wardrobe sai kuma dressing mirror,sai abun ajiye ta kalma,da kuma na ajiye jakunkuna"sai dan karamin TV dake manne a bango. Tana gama rege kayan jikinta ta fada toilet, Wanka tayi hade da alwala sannun ta fito. Mai ta dauka ta shafa,sai turaruka, Gaban wardrobe taje Bangaren kananun kaya ta bude,riga mara nauyi ta dauka,wadda rigar in ta saka bazai wuce guiwarta ba,ta saka Bayan tagama shiryawa?" Hijabi ta saka akan karamin rigar dake jikinta ta tada sallah Sallar azahar da batayi ba tun dazu tayi, hade da la'asar da aka kira yanzu, Bayan ta idar da Sallah tashi tayi ta nade sallayar ta ajiye,hade da tire hijabin shima ta ninkeshi ta maidashi ta ajiye amahalinta fita tayi ta nufi kitchen, Tana zuwa palo ta iski Mamanta Zaune har yanzu sai faman ciye- ciye take har yanzu,tazo ta wuce ta ba tare da tayi mata magana ba, Da kallo Hajiya Batulu tabi yer tata dashi hade da girgiza kai. *Kitchen* Masu aiki ne guda uku suke ta faman aiki,daya na girki daya kuma na wanke -wanke,daya na mopping din kitchen din,dan in kaga kitchen din zaka ranse ba aiki akayi a ciki ba,saboda ko ina saff yake Babu dadti ko kadan,wannan umarnin AFIYA ce, Saboda kwata- kwata bata son ƙazanta ko kadan, saboda akwai wani lokaci da ta shigo kitchen din ta tarar ba'ayi wanke- wanke ba ƙuda sai bin kwanukan suke,fada tayi musu sosai a karshe dai ranar AFIYA bataci abincin gidan ba. Sai da ta je restored ta ci abinci. "Barka da wannan lokacin Hajiya."Masu aiki suka hada baki wajan fadi . "Tnx". Ta furta a takaice, saboda kwata,-kwata bata iyayin godon magana saboda wahala yake bata Kujera ta samu ta zauna ba tare da tayi magana ba, "Hajiya kina bukatar wani abu ne ?."Cewar daya daga cikin masu aikin "Coffee,." Ta sake fadi. Kai mai aikin ta geda ta shiga hadawa AFIYA Coffee din, Ba'a fi mintuna biyar ba ta kammala hada Coffee din dazo ta rusuna har ƙasa ta mika mata, Karba AFIYA tayi,tana fadin..."Tnx USNA!."Murmushi USNA tayi tare da fadin.."Ba komai Hajiya asha lfy".Kai AFIYA ta geda hade da mikewa ta bar kitchen din. Kara zuwa tayi ta wuce palon ta koma dakinta Mamar ta sake bita da kallo, A zuciyarta kuwa fadi take ni wllhy yanzu kam rashin maganarki Afiya ya fara bani tsoro,ta fada cikin ranta tare da mikewa,da niyar wuce sama jin muryar dan autarta ne ya sata dakatar da hawa saman da tayi niyar yi, Wani yarone da bazai wuce shekaru 15 zuwa 16 ba ya taho da gudu da niyar rungumar mahaifiyar tashi ko mai ya tuna kuma sai naga ya tsaya hade da sosa keya,yana fadi "Mama sannu da gida." Harara ta dalla masa tare da fadin... "Na dauka ai fado min zaka yi ai tunda Kai kayi girma amma baka san kayi girma ba". Ta fada hade da juyawa ta fara hawa matattakalar, Jiki a sanyaye yaron ya wuce dakin yayarsa dan yaga motarta awaje yasan ta dawo. Nocking yayi,amma shiru ba'a bude ba sai ana biyu aka bude, Kasan cewa bacci ne ya fara daukarta shiyasa bataji ba ana farkon sai ana biyun taji. Ganin kanin tane ya sata sakin murmuchi daya sa kyawunta kara baiyana, Hannu ta bude mai atake kuwa ya fada jikinta yana sauke ajiyar zuciya kamar karamin yaro, Harkanla sun kai 5 second a haka sai daga visani Ta sakeshi hade da bashi hanya ya shiga ciki sannun ta maida kofar ta rufe, Dakin ta koma ta tarar dashi zune akan kujeran gadon ya rafka uban tagumi, Cikin mutuwar jiki ta karasa kusa dashi ta zauna,hade da tire mai tagumin da yayi, Dagowa yaron yayi yana kallon yayar tashi cikin so da kauna,dan sai yazo wajanta yake samun farinciki. "Whatttt? Ta tambayeshi kamar ana mata dole yin maganar, Yaron bai amsa ba,sai da ta sake yin magana akaro na biyu, "Mama?"Ta sake cewa,kai yaron ya geda mata alamar eh, "Okay sorry." Kai kawai yaron ya iya gedawa,duk da kuwa ita ma yayar tasa bawai godon magana zatayi mai ba amma ko ba komai yana jin dadi zama ta ita, saboda in yana cikin damuwa tana kwantar mai da hankali, "Kaci a binci ?"Kai ya girgiza alamar a'a,kai ta geda,hade da mikewa, ta fita tabar dakin. Bata wani dau lokaci ba ta dawo hannunta rike da plate din a binci,da ruwan roba zama tayi a gefensa ta shiga bashi a bincin kamar karamin yaro,sai ana uhu ne ya rike hannunta ya juya kan spoon din zuwa bakin yayar tashi, Kai ta girgiza alamar bataci, "A'a Aunty Afi kema fa na tabbata bakici abinci ba,dan haka dan Allah! ki karba."Ba yanda ta iya,a haka dai ta bude baki ya sa mata a bincin,a haka dai suka shiga bawa juna har suka cinye a bincin, Sun shaku sosai dan sai in suna tare suke dan samun farinciki, "Kaje kayi wanka.", Ta fada hade da dauko wayarta zatayi kira, "Aunty wa zaki kira kuma?." "USNA."Ta bashi amsa "Kawo plate din na kai tunda fita zanyi."Mika mai kawai tayi ba tare da tayi magana ba, Karba yayi ya bar dakin,ita kuma ta koma ta kwanta tayi shiru kamar mai bacci...., *Sakeena ismail Cameroon ce*✍️ *07049322735* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU Da HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Sai na yanzu da aka fara mai suna duhu da haske✍️* Page 3&4 Free book Bismillahi rahmani rahim *******Karba yayi ya bar dakin, komawa tayi ta kwanta tayi shiru kamar mai bacci,nan kuwa ba bacci takeyi ba idonta biyu tana tunanin rayuwar duniya da kuma halin irin na mahaifiyasu"dan yanzu kam abun nata ya dena bata mamaki ma,tsoro yake bata, Tana nan kwance tana tunani tunani har baccin barawo ya saceta, Mohseen kuwa yana ajiye plate din da sukaci a binci dashi a kitchen dakinsa" ya wuce,cikin sanyin jiki ya tire kayan sa,ya shiga wanka. Ba itta ta tashi daga bacci ba sai bayan magriba,tana tashi a gurguje ta shiga toilet ta watsa ruwa hade dayin alwala,ta fito ta shirya cikin kayan bacci riga da wando,sannun ta saka hijabi ta tada sallah, Data idar da sallah azkar ta shigayi,a takaice dai ba itta ta tashi daga sallayar ba,har sai da aka kira sallar i'sha tayi sannun ta mike ta ninke sallar hade da tire hijab din jikinta"ta linke ta ajiye. Zama tayi a kan gado hade da dauko Laptop dinta ta fara aikin daya rege bata samu tayi a kanfani ba. Hannu ta sa ta dauki wayarta dake gefen gadon tayi dialing wata number,ana dagawa,naji tace.... USNA coffee tana kaiwa nan ta kashe kiran. Badan komai tafi son USNA ta hada mata coffee ba sai dan duk cikin masu"aikin tafisu safta har ma da iya girki,shiyasa in dai harkan a binci ne toh itta takeyin komai. Kuma bata shiga harkan da ba nata ba,da lilin dayasa tasu ta dan zo daya kenan. Ajiye wayan tayi ta fara aiki, Ba'a dau lokaci sosai ba sai ga USNA rike da coffee a hannunta" ta shigo bayan ta kwankwasa ta bata izinin shigowa,sannu tayiwa hajiyar tasu sannun ta bata Coffee ta tafi. *Washe gari* Kasan cewa tana fita motsa jiki kafin ta wuce wajan aiki shiyasa"yau ma dai ta shirya saff kamar kullun,cikin kayan motsa jiki,riga da wando,wandon ya dan dameta kadan daga sama,kasan wandon kuma a bude take,sai riga mai karamin hannu gashin kanta ta tufke,ta yanda in ta fita motsa jiki bazai da me ta ba. Bayan tagama tufke gashin nata"wula mara nauyi ta dauka ta rufe kanta dashi,hade da rataya jakar goyonta"sannun ta fice daga gidan. Badan komai yasa bata son motsa jaki a gidan ba,sai dan tafi son ta fita waje tasha iska, Da lilin dayasa take fita motsa jiki a waje kenan,kuma uwa uba in har tana motsa jiki a gida zata ginda ganin kayan takaicin da zai bata mata rai a banza,itta kuma batason hakan ta faru,dan in har hakan ta faru ko taje wajan aiki babu wanin aikin da zata iyayi, Kasan cewa safiya ce Shiyasa ba kowa a unguwar tasu"ko da yake ma koda rana ma mutane basu fiya zama sosai ba a unguwar,kasan cewa unguwar ta masu kudi ne, Sedai kafin ka karasa cikin layin nasu akwai majalisan da samari sukeyi da yamma. Gudu tayi sosai,dan har kalla sai data dau kusan rabin awa tana gudu sai daga baya ta sagaita da gudun da takeyi. Tun data fara gudu take lura dashi duk da kuwa ba yau ne ranar sa na farkon daya fara zuwa wajan ba. Kana ganinsa"kasan ba abunda ya kawosa wajan ba kenan,saboda yanayin yanda yake motsa jikin ma kasan ba sabawa yayi ba, Ganinta da yayi ta samu waje ta zauna a kan daya daga cikin kujerun dake wajan da akayi da simenti ne ya sashi yanke shawara zuwa yau ya gaya mata a bundake cikin zuciyarsa, Dan ya kamu da sonta sosai duk da kuwa da farko ba son allah da annabi yake mata ba,dan da farko saboda kudin da take dashi ne?yasa yake son ya aureta",amma a yanzu so gaskiya yake mata saboda AFIYA ta hadu ko ta wana bangare, Dan ko da bata da kudi?zata samu samarin da suke sonta"ballantana yanzu ga kudi ga hutu daya zauna jikinta. Zaune take ta fito da ruwan dake cikin dan karamin jakar goyon da take saka karamin tawal da take goge zufah dash da kuma ruwan da zatasha. Balla murfin jarkan tayi ta kafa a bakinta akai da niyar sha sai taji anyi "sallama" a gabanta dagowa tayi dan ganin waye sai idanunta suka sauka akan na Aliyu,saye yake a gabanta ya kura mata ido kamar idon nashi zai fado kasa" Kallo daya tayi mai ta tauke kai, ba tare da amsa sallamar da yayi mata ba,sai ma kara daga ruwan jarkan da tayi ta kafa a bakinta"ta fara sha, Sai data sha kusan rabi sannun ta tire bakinta a kai, Murfin ta maida ta rufe,hade da maida jarkan cikin jakar goyon data zo dashi, Igiyar kambos din dake kafarta data kwance ne ta gyara, Dagowa tayi da niyar mikewa sai ta gansa tsaye a gabanta"ga wani irin kallo daya kafata dashi" Wani irin tsaki ta ja'a daya sa Aliyu dawowa cikin haiyacinsa,hade da tsotsa keye. "Sorry ya fada?, Nan ma dai bata kulashi ba, sai ma mikewan da tayi ta tsoma tafiya da niyar barin wajan, Da sauri sauri ya soma bin bayanta"hade da fadin...dan allah dan annabi AFIYA ki saya ki saurareni nayi miki alkawari bazan wuce minti biyar ba, Aliyu ya fada yana karasa inda AFIYA take saye,dan tun lokacin daya hadata da Allah ta saya cak ta dakatar da tafiyan da takeyi? Saboda itta mutun ne da bayaso a hadashi da allah,dan in har an hada ta da allah toh zance yakare. Tana nan tsaye,itta bata tafi ba ?itta bata juya ba ? Bai damu da rashin juyawan da batayi ba,shi dai tunda har ya samu ta saya ai shikenan, A gaban ta yazo ya saya,tana ganin haka ta maida fuskarta ta dayan gefe tana jira taji mai zai fada mata ? 3 minute ta fada ba tare data kalli inda yake ba. Ya fahimci inda maganar ta ya dotsa tsarai,wato tana nufin ya cinye mintuna biyu saura uku. Dan haka,da sauri sauri ya soma magana kamar haka....wllhy AFIYA tun lokacin dana dora idanuna akanki naji kin kwanta min arai,naji duk duniya babu macen da nakeso sama dake! Ina sonki AFIYA dan allah ki amince da soyayyata nayi miki alkawari bazan taba yaudararki ba... tun lokacin da Aliyu ya fara maganar so ta juya tana kallon shi,sabanin dazu dako inda yake bata kalla ba. Aliyu yana da kyau babu laifi,duk da kuwa bakii ne shi,amma bakin nasa irin mai kyau din nan ne,fuskarsa na da dan fadi, yana da hanci dai dai misali,dogone amma jikin da yake dashi ne yasa ba'a ganin tsayin nashi sosai. Dauke kai tayi daga kallon shi da takeyi,hade dayin tsaki,dan ba karamin haushin kanta taji ba,data saya tana kallonshi"dan itta kwata kwata kallon mutun bai dameta ba, saboda ko mata ma bata sayawa ta kura musu ido,ballan tana na miji? Kallon agogon dake daure akan tsintsiyar hannunta tayi taga har takwas takusa, Dan haka tafiya ta somayi da sauri da sauri, tana barin wajan, Da gudu aliyu ya sha kabanta,yana fadin haba AFIYA taya zan baiyana miki a bundake cikin zuciyarta amma zaki tafi ba tare da kince komai ba? Sorry,namakara ta fada..hade da ci gaba da tafiya. Har ta fita daga wajan aliyu na saye awajan data barshi bai motsa ba,sai daga baya ya fara tafiya shima cikin mutuwar jiki. Mahaifin aliyu ya kasance shima daya daga cikin attajiran unguwar tasu,badan komai yada Aliyu yake zaman majalisa ba,sai dan tun lokacin da allah yayiwa mahaifinsa rasuwa baffan su ya cinye dukiyar tare da matar babansu"kasan cewa shi- shi kadai ne a wajan mahaifiyarsa"matar mahaifinsa kuma yana da yaya kusan bakwai,da farko dai yaso yayi rigima dasu akan cinye mai gaado da sukayi,sai mahaifiyarsa ta hanashi tace ya kyalesu"wanda yake dashi ma ya mutu ya barshi ballanta dukiya,a haka dai aliyu ya hakura da dukiyar amma badan yana so ba,sai dan yiwa mahaifiyarsa biyayya. Kasan cewa yayi karatu sosai yana da diploma shiyasa ya dauki ta kardun nashi,ya shiga nemon aiki amma babu inda bai je ba,amma bai samu ba,wata ranane yaji wani yana cewa mamar babansu ne ya hana a bashi aiki,saboda duk inda yaje nemon aiki ana kawo mata bayanin komai, Shiyasa ya hakura da nemon aikin,ya mikawa lamuransa ga allah. *Kunji lbrn aliyu kenan* Tana zuwa gida a gurguje tayi wanka ta shirya cikin dogowar riga na materiale,sai ta yane kanta da karamin mayafi, Tayi kyau sosai hand bag dinta ta dauka kalar ta kalmin kafarta,wayoyinta da key din motarta data dora akan dressing mirror ta dauka ta sakasu a hand bag dinta, Sannun ta fice daga dakin bayan ta kulle dakin, zuwa tayi ta wuce palon ba kowa, Bata saya ko ina ba sai wajan ajiye motoci,bude murfin motar tayi da niyar shiga sai taji kaninta Mohseen na kiran sunan ta,aunty Afi ! aunty afi!!dakatar da bude motar da tayi niyar yi tati, ta zuba masa idanu har ya karaso inda take, Good morning aunty Afi? Mohseen ya fada, Morning kanina ya kake?lfy lau aunty dama naga kamar fita zakiyi na shiga ki ajiye ni a school ne ? Kallon sa tayi na yen second ni sai ta maida kallonta ga drave din dayake saye yana jiran Mohseen ya fito su tafi, Sorry baba?"ta fada tana kallon baba drave . Bata saya amsar baba drave ba ta kalli Mohseen ?hade da cewa...shiga mutafi,kai yaron ya geda jikin murna ya balla murfin mota ya shiga gaba ya zauna a mazaunin mai zaman banza. Shiga tayi itta ma tare da yiwa motar key aka wangare musu gat ta ja'a motarta ta fice daga gidan. Tuki takeyi cikin nitsuwa,suna hira jefi jefi,amma yawanci yiran na Mohseen ne yafi yawa saboda itta daga hummm sai uhumm,har suka karasa *ADo bayero* *University* 5k ta fito dashi daga cikin jakarta ta mikawa Mohseen,cikin murna ya karba hade dayi mata godiya sannun sukayi sallama ya fita ya nufi cikin makarntarsu"itta kuma ta ja'a motarta ta wuce kanfani...., *Sakeena ismail Cameroon ce*✍️ 07049322735 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske* *typing*....✍️ Page 5&6 Free book Bismillahi rahmani rahim ********Tana zuwa kanfani bayan tayi barking din motarta"ta fito ta nufi cikin kanfanin,tun kafin ta karasa ciki ma aikatan suke tayi mata sannu da "zuwa,itta kam ogan tasu kai da hannu kawai take daga musu" har ta karasa ciki, Da yake ta cikin office din seketariya take wucewa kafin ta karasa cikin nata office din,dan haka seketariyarta na ganinta"ta taho da sauri ta karbi jakar hannunta suka wuce ciki, Seketariya na gaba afiya na biye da itta a baya,har suka karasa gaban office din,sai da safna ta budewa afiya kofar ta fara shiga tukun sannun ta shiga itta ma hade da maida kofar ta rufe, Lokacin tuni afiya ta karasa cikin office din ta zauna kan kujera,dan haka safna ma ta karasa ta itta ma ta a jiye mata jakar akan table din, Takardun dannunta afiya tabi da kallo,daga baya kuma sai ta maida dubanta ga safna, Safna na ganin haka ta fara bayani kamar haka...?ranki ya dade bakin da suka zo jiya ne suka bani wannan ta kartun sukace na baki,safna ta fada hade da mikawa afiya ta kartun, Hannu afiya tasa ta karbi ta kardun,ta shiga dubawa, ganin a bunda tagani akai ne yasa ta mikewa da sauri hade da tire farin glass din data saka a idonta wajan taimaka mata gani sosai, Meyesa baki fada min sune suka zoba?ta fada tana kallon safna, Wllhy ranki ya dade ina kokarin gaya miki sai kikace na sallamesu"cewar safna. Kina da hayaniya safna! afiya ta fada kamar ba itta ce ta tambayeta yanzu ba. Yi hakuri ranki ya dade,amma wllhy bada wata manufah nayi hakan ba, saboda na dauka inkin fita kingansu" zaki fasa tafiyan ki saurare su ne safna ta sake fadi. Suna waje lokacin ?"eh suna zaune a office dina safna ta bata amsa" Banga kowa....bata karasa maganar ba ta koma ta zauna dan wannan maganar da ta danyi kanta har ya fara tsara mata", Go afiya ta fada tana kallon safna,dan gani take hadda lefinta hakan ta faru, Sorry madam safna ta fada cikin sanyin murya hade da barin office din. Kanta ta rike da dayan hannunta"daya kuma ta sa ta jawo wani kwalin da take ajiye magungunan a ciki, Kama daga maganin ciwon siki ciwon mara kai gasu nan dai rututu, a ciki, Hannunta data rike kanta dashi ta hada da dayan hannun ta shiga duba paracetamol, tana ganinshi ta dauka ta balla guda biyu ta jefa a baki hade da dauko ruwan jarkan dake saman table,ta balla murfin ta kafa bakinta tasha,sai data tabbatar maganin ya tafi sannu ta tire ruwan daga bakinta hade da rufe jarkan ruwan ta ajiye a inda ta dauka, Laptop din gabanta ta bude ,bayan ta kunna ne ta shiga dube dube wani abu,dan ko ni kaina ma bansan mai ta dubawa a ciki ba, Typing ta farayi a cikin laptop din,sosai ta maida hankali wajan typing din,kana gani zaka fahimci magana takeyi da wani kuma daga gani maganar na da mahimmanci saboda yanda ta nitsu sosai,ta maida hankali akai. Ganin rubutun daya mata ne ya sata shiga cikin tashin hankali, Wayarta ta dauka tayi dialing wata number,da kallo daya zakawa number din ka fahimci bata Nigeria bane. Ba'a dauka ba sai ma Kiran da tagani ana mata daga cikin laptop din dake gabanta" cikin mamaki take kallon kiran dan tunda take dashi bai taba kiranta" video call ba,dan haka kasa dauka tayi har kiran ta kashe, Ba'a kara kira ba dan haka rufe laptop din tayi,tare tun da ajiye wayar dake hannunta" jingina kanta da jikin kujerar tayi,hade lumshe ido,tana juyi akan kujerar a hankali. Tunani takeyi mai zai mata yake kiranta vidéo call,shi da yakeso ya taimakesu" wajan bungasar kasuwancin su mai Kuma nayin vidéo call?" Tambayoyin data shiga yiwa kanta Kenan amma babu mai ansa mata su" Ni kuma nace ..in banda abunki afiya kema kince zai taimakeki wajan bungasar kasuwancin ki, toh in baki dauki video call da yake miki ba ta yaya zai ganeki har ya taimakeki,bayan bai taba ganinki ba?" Waya telephone dake gabanta ne ta dauka ta dannawa safna kira, Tana dagawa tace mata ta sameta a office,toh safna ta fada tana mikewa, Kafin ta ajiye wayar data kirata dashi safna ta shigo cikin office din, Gani ranki ya dade,cewar safna, ohhh good sau nawa safna?"afiya ta fada tana kallon safna dake kallonta itta ma, Dan har ga allah yau kam bata gane mai take nufi ma" Duk da kuwa tafi sauran ma aikatan gane maganar afiya amma yau kam bata fahimci komai ba itta ma. Fahimtar da afiya da tayi na cewa safna bata gane mai take nufi ba? ya sata fadin...afiya! ko aunty afiya!! Murmuchi safna tayi,dan sai yanzu ta fahimci inda maganar afiya ta dosa"dan haka tace toh aunty insha allah. Kowa ya jirani a dakin taro a kwai maganar da zamu tattauna anjima ki gayawa kowa,kai safna ta geda,hade da fadin..toh aunty zan gaya musu" Da hannu tayi mata alamun zata iya tafiya, Bayan fitar safna ta kira kowa a woyoyin office dinsu ta fada musu akwai taro anjima, *Bayan awa biyu* Ma aikane zaune a cikin dakin taron, Daki ne babba sosai,dauke yake da wani doguwar teburi,sai kujeru dake zagaye a wajan,ko wana kujera da a bun magana a gabanshi, Kus_kus sukeyi a saka ninsu,suna tambayar juna a bunda yasa ogan nasu ta tarasu a wannn lokaci,dan in har za'ayi taro?toh kamar gobe za'ayi ake gaya musu, Allah dai yasa lfy cewa daya daga cikinsu,amin dai bello,wanda yake zaune kusa da shi ya amsa" Takun ta kallaman da sukaji ne?ya tabbatar musu" da isowarta wajan, Shiru dakin ya dauka kamar ba'a sune sukeyin magana dazu ba,sai sautin takalman tane kawai kakeji...ji kake kwas. kwas.kwas.kwas. Kara sowa tayi ta zauna a kujeran da aka tanada domin oga,sai ya kasance tana fuskantar" kowa., Kallon su ta shigayi daya bayan daya,inda duk sanda idanunta ya sauka a kansu suke saukar da kai"kasa"sakama kon kwarjinin da take musu" Dan su wani lokaci har mamakin abun sukeyi ma, saboda ko namiji albarka. Sai da tagama kallonsu" saf ta tabbata kowa ya hallara a wajan sannun ta fara magana kamar haka....nasan bakusan da lilin dayasa na taraku a nan ba ?" Bazan iya sayawa nayi muku dogon bayani ba,amma ga seketariya ta nan zata muku bayanin komai, tana kaiwa nan ta tura wata ta karda a gaban seketariya,tare da fadin...duk a bunda zan fada na ciki... "Ku kiyaye aikin ku" Tana kaiwa nan ta mike ta bar dakin taron, ta koma office dinta" Bayan fitarta,safna ta soma karanta musu"a bundake rubuce a takardan kamar haka...ba kwa mai da hankali a kan aikinku, saboda wani babban mutun ya nemi taimaka mana wajan kara bungasar kanfanin nan amma kun rutsa komai,dan haka ku kiyaye gaba,ku mai da hankalin sosai wajan yin aiki, safna na gama karan tawa ta dago tana kallonsu, Yanzu dan allah duk aikin da mukeyi ba dare? ba rana? amma take cewa mu mai da hankali a kan aikin mu wana irin maida hankali takeso muyi bayan wanda mukeyi ko so take mu dawo office din mu dinga kwana? hafsat ta fada cikin jin takaicin Maganar. Wllhy lefin tane hafsat saboda jiya da bakin nan sukazo naje na gaya mata cewa tayi bazata iya ganin su ba,shine yanzu zatace mune bamuwa maida hankali itta ma safna ta fada, A haka dai kowa yake tofah albarkacin bakinsa"da sukaga maganar ba mai karewa bane kowa ya tattara ya koma office dinshi.. *Bayan kwana biyu* "Bayan ta tashi daga wajan aiki" Tuki take cikin nitsuwa da kwarewa,ta hango wasu motoci na alfarma kusan guda shiga suka zo suka wuceta "a guje, Mutane sai basu hanya sukayi,wani irin haushi da takaici ne ya cikata yanda suka wuce kamar zasu bike motarta" Gefen titin ta gangaro tayi parking,tana tunani ko wa suka dauko cikin motar da bazasuyi komai a hankali ba, Bata gama tunanin juci ba, taji wasu suna fadin .. Habib Muhammad Habib kenan,saurayin ya fada wai kana nufin shine dan Muhammad Habib?"watoh shogaban man petir,gaba dayan Nigeria! Kwarai kuwa,cewar dayan,tun lokacin da suka fara magana idanunta suke a lumshe duk a bunda suke fada a cikin kunnuwanta"yake shiga,bata jira sun karasa maganar tasu ba tayiwa motarta ki ta wuce gida. *Washe gari* Bayan tagama motsa jaki, Tafiya take tana duba a gogon dake hannunta"taga takwas har tayi,kasan cewa yau ta dan makara,dan haka ta fara tafiya da sauri da sauri da niyar barin wajan,sai taji ta bugi wani abu. Washhhh taji an fada a lokacin da ta dago da niyar ganin a bunda ta buga din,idonta ne ya sauka a kan wani balarabe dake gabanta, shima a lokacin ne ya dago dan ganin waye ya buge mai goshi, sai idanunsa ya sauka akan nata "wani irin harbawa zuciyoyinsu"yayi a lokacin da idanunsu suka sarke cikin na juna, Zuciyoyinsu ne ya hau bugawa da karfi, A takaice dai sai da sukayi kusan bintuna biyar suna kallon juna sai daga baya afiya ta janye nata idon,tana fadin sarki ya tabbata ga wannan halintan dake gabana, Abunda bata sani ba shine zancen zuci yafito fili, Ji tayi yace...mai kikace?"dagowa tayi cikin mamakin daya kasa boyuwa a kan fuskarta"tana fadin dama kana jin Hausa ?"murmuchin gefen baki yayi daya kara saka afiya suman tsaye,dan ba karamin tafiyar da imaninta yayi ma, Agefe guda kuma mamaki take sosai yanda balaraben dake gabanta ya iya hausa, Yen yasansa ya hada biyu ya hada waje guda ya kyess tasu"ji kake kyes kyess haka sautin yake badawa,a take afiya ta dawo jikin hayya jinta"tare da fadin sorry!tana kaiwa nan ta fara takawa da sauri da sauri tana kokarin barin wajan.... *Sakeena ismail Cameroon ce*✍️ 07049322735 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing* ...✍️ Page 7&8 Free book Bismillahi rahmani rahim ******Bin mayanta yayi da kallo,har ta bacewa ganinsa"taba inda ta bugeshi"yayi yana yatsine fuska,dan sai yanzu yaji zafi a wajan dan har wajan ya dan kumbura,abunka da wanda bai saba da wahala ba ?" Fasa motsa ciki da yayi niyaryi yayi,dama bai saba motsawa a waje ba,yau din ma bai san ta ya akayi yaji yana son motsa jikin a waje ba. Juyowa yayi shima ya bar wajan, Son ! wai sau nawa zan gaya maka bata son ka dinga fita ba tare yen kariya ba ?"wani mutun ya fada... sorry Dad! Habib ya fada yana dan kwantar da kansa"akan cinyar mutumin daya kirashi" da Dad !shafa kansa"mutumin ya shigayi shi kuma yayi lamo kamar karamin yaro, Hummm dan Daddy yazo?sukaji an fada a bayansu"kallon inda sukaji anyi maganar Alhaji Muhammad Habib yayi,matarsa hajiya Maimuna yagani take saukowa,farace amma ba sosai ba,tana da kyau dai dai misali,sanye take da wani laces mai matsifar kyau da sada,tun daga wuyanta har izuwa hannayenta da kuma kunnenta"duk gwala gwalai ne, Cikin yanga da kwarkwasa ta karasa saukowa,tafiya take tana karye kugu,har ta karasa gaban mijin nata" Tun da ta fara wannan abun alhaji Muhammad Habib ya bude baki da hanci yana kallon ta, lokaci daya ya shiga matse kafafu kamar mai shirin yin fitsari, Habib na ganin haka ya mike daga kwancen da yakeyi ya zauna, Hajiya Maimuna kuwa tana ganin alhaji ya fara mutsu mutsu,ta kalli wajan,da yake matsewa, Ai kuwa abun kamar zai fita daga cikin wango,wani dariya ne ya kubce mata,ba shiri ta farayi babu ko kakkautawa, Kallon inda take kallon Habib yayi,lokaci daya kuma ya dauke kai,hade da mikewa, Cikin haushi da takaici ya fita ya bar palon ya wuce bangarensa" Shifah da lilin dayasa baya son zuwa Nigeria kenan,saboda da zaran tagansu tare toh sai tayi duk yanda zatayi wajan gani ya bar wajan. Palon nashi ya shiga, Woww na furta a lokacin da idanuna ya sauka cikin palon,dan ba karamin kyau yayi ba,kallo daya zakawa palon ka fahimci ba makamin kudi aka kashe wajan kawatar da palon ba, Daki ya wuce,nan ma dai ya hadu dan zan iya ce muku ma yafi palon haduwa,a zuciyata kuwa fadi nake daga gani Habib dan gata ne,gaba da baya. Kayan jikinsa ya rage ya fada toilet, Sai daya dau kusan mintuna sha biyar sannun ya fito daure da tawal a gukunshi"sai wani dan karamin tawal din da yake goge sumar kansa daya cika da gashi, Gaban mirror ya je ya saya,ya shiga kallon kansa"Habib na da kyau sosai, Dan kallo daya zaka mai ka fahimci ya hada jini da larabawa, Yana da haske sosai,yana da godon fuska da kuma godon hanci da har yaso yayi masa" yawa saboda tsawo, Lebensa jàne,fatar jikinsa kuwa kamar ka taba jini ya fito saboda haske da kuma hutun daya rasa fatar jikin nashi" Yana da sumar kai sosai, sakamakon kyaran da yake samune ya sa gashin kara baki da kuma laushi Nakurar busar da kai ya dauka ya shiga busar da kan nashi, saboda in yace zai bari ya bushe da kanshi zai iyayin awa daya, Yana gama bushe wa ya dauki man da yake shafawa akan ya shiga shafawa, Sai daya gama gyara gashi saf sannun ya shiga shafa man a jikinsa, Bayan ya kammala duk a bunda ya kamata ne ya wuce gaban wardrobe dinshi,kasan cewa murfin wardrobe din glass ne shiyasa ya jashi a hankali ya budeshi,kananun kaya ya dauka riga da wango ya shiga shiryawa. *Bayan awa daya* Karan shiga motocin cikin kanfanin ne yasa jama an dake harabar kanfanin juyowa,suka zubawa motocin idanu har suka karasa cikin kanfanin sukayi parking, Motoci ne!guda uku amma motan dake sakiya yafi sauran guda biyun tsata da haduwa, Fitowa sukayi daga cikin motar,sanye suke da bakaken kote,iri daya, kallo daya zaka musu" ka fahimci cewa sudin masu"tsaro ne ? karasa gaban wannan motar dake sakiyarsu"sukayi daya daga cikin su ne ya bude bayan motar, A hankali ya zira fararen kafafuwansa"dake sanye da wani kubashu mai shegen tsada da sheeki,sauke kafafuwan yayi kasa,"baki sake samarin dake wajen suke kallon wajan,suna jiran suga ma mallakin kafar,dan sun tabbata ko wayeshi"? Babban mutun ne ?" Kafin su gama tunaninsu"sukaga ya karasa saukowa daga cikin motar, Suna ganin ya fito mai zasu fada... in ba masha allah ba, Yana sanye da fararen kote da tishet,sai bakin wando,sai farin glass dake manne a idanunsa" "taku ya fara a hankali cikin kasaita, kamar baya son taka kasar ya nufi cikin kanfanin nasu"samarin suka bishi da kallo har ya bace musu" Da suka zo bakin kofar shigane ya dagawa masu"tsaronshi" hannu alamu su saya daga nan,dan haka suka bi umarninshi suka saya, Shikuma ya karasa shiga ciki, Zo ?ya fada yana kallon wani sauranin da ya shigo yanzu, Cikin mamaki saurayin yake kallonsa yana so ya gasgata da abunda kunnuwansa suka jiyo masa, In har da gaskene abunda kunnuwansa yajiye masa toh hausa yaji wannan balaraben yayi?, Fahimtar hakan da Habib yayi ne yasa shi fadin..eh cewa nayi kazo! Saurayin na ganin haka kuwa ya karasa da sauri yana fadin gani ranka ya dade? Ina ne offishin shogabanku?nan daka shiga ranka ya dade seketariyarta na ciki, Saurayin ya fada yana nunawa Habib wani bangaren da yafi ko ina kyau a kanfanin, Kai kawai Habib ya geda ya nufi wajan da saurayin ya nuna masa" Safna na zaune taga balarabe a gabanta"jiki na rawa,ta shiga fadin sannu dazuwa yellabai kana bukatar wani abu ne ?mai kakeso ?"haka tayi mai tambayar duka a lokaci daya, Murmuchi Habib ya danyi daya sa safna kiricewa, Ina shogabanki?"ya fada da hausa yana kallon safna, Zaro ido waje safna tayi tana kallon shi"dan tayi mamaki sosai da taji yayi mata magana da hausa, Kasan cewa itta da turanci tayi mai magana, Magana nake kin min shiru? Habib ya sake fadi cikin hade fuska,sai kace ba shine yayi murmushi a yanzu ba?dan yanzu kam abun ya soma bashi haushi"Shiyasa kwata kwata bayanson zuwa Nigeria, Ga office din nata acan bari na gaya mata, Safna ta fada tana dauko wayan téléphone dake gabanta, Kafin kace me Habib har yayi gaba,baki bude ta shiga kallonsa"hade da dafe irji, Shikenan yau kam zan rasa aikina ta fana hade da biyo bayanshi"tana fadin dan allah yallabai karka shiga ka bari na fada mata tukun zan iya rasa aiki na..?amma ina bai maji a bunda dake cewa ba ma,saboda ya riga da ya tura kofar office din ya shiga,ba tare daya saya ya nemi izinin shiga ba, Juyowa yayi zai maida kofar ya rufe sai safna ta rike kofar hakan ne ya sashi sakin kofar ya shiga ciki. A guje safna ta karasa ciki tana fadin...ranki ya dade kiyi hakuri nace ya ....safna bata karasa ba jin da tayi afiya na cewa....kaine ?"ta fada tana nunashi da yen yatsa,kece ?shima ya fada a yayinda idanunshi yayi tozari da kyakkyawar fuskarta" Shiru safna tayi tana kallonsu"daga baya kuma sai ta fita hade da jà musu kofa,ta koma tata office din. Amma meye kawoka anan ?"afiya ta fada, Ai ke zan tambaya me kike anan ?shima habib ya bata amsa" Wani irin murmuchi afiya tayi da daya sa dimpil dinta"lotsawa, Sai daga baya kuma ta bude baki kamar batason yin magana tana fadin... taya zakaxo office dina zaka dinga tambayata meye kawoni nan, bayan kuma nan kanfaninane !ta bashi amsa"daga visani ta koma ta zauna, "Bismillahi ta fada tana kallon Habib daya kafeta da idanu, Bashi da zabin daya zuce zama din,dan shi kansa ya gaji da tsayuwan dan kafafuwansa har ya tsoma mai ciwo,dan haka kujeran ya jà ya zauna. Sai data bari ya zauna sannun ta soma yin magana...ina jinka meke tafe dakai ?" Memakon ya bata amsa"saima tambayarta da yayi shima...nifah na rasa gane komai? Wai dama dake nake magana ?" Ya fada yana kallon afiya, Itta ma afiya bata amsa mai ba,sai ma kara masa tambaya da tayi...kaine H.M.H?"eh nine kina nufin kema kece afiya abubakar? eh nice, Ikon Allah ya fada yana kallon ta,"amma banji labarin zuwanka ba.ta fada tana kallonsa" Wllhy zuwan nawa ne ya taso,ga kuma wulakancin da kikayiwa mutanena rannan,dama so nake nazo na ganki ido da ido ki fada min dalilin dayasa kikayi musu"cin fuska ya fada yana hade rai kamar ba shine dazu yayi magana cikin sakin fuska ba..... *Sakeena ismail Cameroon ce*✍️ 07049322735 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 11&12 Free book Bismillahi rahmani rahim ********"Itta kam bata saya ta sauraranshi ba tayiwa motarta key ta bar wajan"yana nan tsaye sai juya katin dake a hannunshi"yake,yanayi yana murmushi,ya kai kusan minti biyar a haka sai daga baya ya karasa wajan nasa motar,ya bude ya saka kayan daya siya a dayan sit din,sannun ya zaga ta mazaunin drive ya shiga ya tada motar ya bar wajan, Driving yake yanayi yana ci gaba da murmushin da yakeyi,can kasan makoshi ya furta...insha allah Nuriiii" ke tawace," Bazan iya komawa gobe"ba har sai kin amince dani,ya kara fadi. *Bayan ya koma gida da daddare* Sallama yaji tayi daga cikin wayar ya amsa gaisawa sukayi,amma sam bata gane waye ba"dan itta har tama manta da wani mai suna Muhammad !saboda itta kwanta kwata bata damu da samari ba, Waye ta fada,shiru Muhammad yayi a zuciyarsa kuwa cewa yake karfah ace har ta manta dani ?" A fili kuma cewa yayi Muhammad ne" Nuria ! Wana Muhammad ta tambaya,jikinsa ne yayi sanyi,amma ya dage yaci gaba da fadi...wanda kuka hadu a supermarket dazu kika bawa kati,ohhhh sorry wllhy na manta,ba komai ya gida lfy lau ta amsa" Shiru ya biyo baya,da Muhammad yaga dai ba magana zatayi ba sai kawai yayi mata sallama, thanks ta fada tana kashe wayan, Bin wayan yayi da kallo,ya zame ya kwanta akan gadon, *Bayan kwana uku* Kullun Muhammad sai ya kira Nuria sau uku zuwa sau biyar a rana tun bata sauraranshi har ta fara sauraranshi"saboda da farko wayan da yake mata gani take takura ce kawai,sai daga baya taga yanda ya damu da itta sosai kuma duk da bata kulashi amma bai taba fushi dai dai da rana daya yace bazai kara kira ta ba, Kunsan dama hausawa sukace zuciya yana son mai kyautata basa"toh haka ce ta kasance a wajan Nuria ma, saboda irin damuwan da Muhammad yakeyi akanta ne ya sata fara sauraranshi"har ma su dauki lokaci sosai suna hira a waya, Sakamakon wannan abun ne yasa itta ma ta fara jin soyayyar Muhammad din na shiga cikin zuciyarta" Bangaren Muhammad kuwa ba karamin farinciki hakan ya sashi ba, Saboda bashi da burin daya muce yaga ya mallaki Nuria, Abbansa ya sha kiransa ya tambayeshi da lilin dayasa har yanzu bai dawo ba?"amma kullun amsar da zai bashi bai wuce...bangama aikin daya kaini ba abba, Da abba ya gaji da jin magana daya kullun,ga kuma kwanakin daya bashi na nemo matar aure ta kusa cika,cemai yayi kar ya kuskura ya kai wannan kwanakin bai dawo ba, Dariya Muhammad ya danyi, cikin kwarin guiwa ya fara magana kamar haka...karka damu abba insha allah na samu matar aure,kai dai kayi mun addu'a, Allah yasa ta amince, Abba zai tambaya Muhammad yayi saurin fadin karka damu abba kai dai kayi min addu'a kawai, insha allah ina dawowa zan fada maka komai,da haka dai ya samu Abba ya dena takura masa"da kira, *Bayan kwana biyu* Ganin yanda Shakuwarasu"sai kara gaba yakeyi ne yasa Muhammad fadawa Nuria abundake cikin zuciyarsa game da itta, Bai wani sha wahala ba ta amince" Amma da taji garin da yake sai jikinta yayi sanyi, tace daker in iyayenta zasu yedda tayi nisa dasu"jin wannan Maganar ne yasa duk kwarin guiwa da Muhammad yake dashi karyewa, Ganin yanda jikin Muhammad yayi sanyi ne yasa Nuria kwantar masa"da hankali,ta hanyar cewa... insha allah Muhammad in har Allah ya rubuta ni matarka ce"toh babu yanda zasu iya sai nayi aure a Nigeria !in har kaga bamuyi aure ba toh dama can Allah bai rubuta zamu zama mata da miji ba, Da haka dai Nuria ta samu ta kwantarwa da Muhammad hankali, Bayan yaji duk a bunda ta fada,cewa yayi insha allah ke tawace Nuria, Murmuchi kawai Nuria tayi,tana kashe wayan, Bayan Nuria ta sanar da iyayen ta"cewa sukayi saidai in dawo nan zaiyi da zama,amma su baza su taba yedda su barta ta tafi wata kasa ba, bayan kuma itta kadai suke dashi, Amma takirashi yazo" Kinsan Muhammad Nuria tayi ta fada mai iyayenta suna son ganinsa,da toh ya amsa" Zaune yake a gaban iyayen Nuria,wacca take kirasu ummi! da Abie! Shiru yayi bayan ya gaishesu"yana jiran yaji abunda zasuce akan aurensa"da Nuria, Addu'a kawai yakeyi a cikin zuciyarsa Allah yasa su "amince" Gyaran murya balaraben mutumin yayi,ya fara magana kamar haka... habibti ta fada min komai game da soyayyarku, Kuma tun da naganka naji ka kwanta min arai,har naji zan iya baka yata ka aura, Amma ina so ka sani cewa itta kadai muka mallaka a matsayin yah,babu a bunda Nuria ta rasa a rayuwarta,komai na rayuwa ta samu,kama daga ilimin addini har dana zamani duk, Alhamdulillah, Badan komai muka barta take aiki ba sai dan ra'ayinta ne, Saboda duk abunda takeso muma shi mukeso, Dan haka in har da gaske kake son Nuria toh cedai ka dawo nan da zama,saboda bazamu iyayin nisa da yer mu ba,mutumin ya karashe maganar da iya gaskiyarsa, Tunda mutumin ya fara Magana kan Muhammad yake kasa"sai da yaji maganar mutumin na karshe ne ya sa shi dagowa dan tabbatar da a bunda kunnuwansa suka jiyo masa" Kai mutumin ya geda mai alamar haka ne" Cikin sanyin jiki ya fara magana shima,toh nagode Abie kuma insha allah zanyi kamar yanda kace,zan koma Nigeria gobe,saboda dama a bunda ya seda ni kenan ?" Insha allah duk yanda mukayi da abba na zakuji,yana kaiwa nan ya mike ya bar palon. *Da daddare* Habibi kana tunani iyayenka zasu amince ka dawo nan ?"Nuria ta tambayi Muhammad,wllhy in nace zasu amince nayi karya"in kuma nace bazasu amince ba "shima nayi karya,amma dai insha allah komai zaixo da sauki in allah ya yerda?"allah ya yerda"Ameen"Muhammaya amsa" Washe gari har airport Nuria tazo ta kai Muhammad,cikin so da kauna" suka shigayin sallama, Muhammad na dago mata"hannu"kowacce na kwalla, addu'a yakeyi Allah yasa ba yau ne ganinsu ta karshe ba, Allah kuma yasa iyayensa"ko iyayenta su amince ya zo nan ya aure ta"duk da kuwa yasan da wuya iyayensa su amince,da dawowarshi nan,saboda kasuwancinsa" A haka dai yake ta addu'a cikin ranshi har ya shiga jirgi ya dena ganin ta" Jiki a sanyaye itta ma Nuria ta juya ta hau motarta ta wuce gida, *Kanon damo Nigeria* Yana sauka ya samu drive na jiranshi"dan haka fadowa kawai yayi cikin mota suka wuce gida, Da daddare bayan sun gama dinner ne, suka tashi daga dinning din suka koma palo, Yauwa Muhammad kai nake sauraro kace in ka dawo zaka fadamin komai"gyara zama Muhammad yayi akan carpet din,sannun ya kwashe komai,tun daga haduwar sa"da Nuria har yanda sukayi da mahaifin Nuria har izuwa yanzu da yake gabansu" Whattt Abba ya fadi a lokacin da yaji maganar Muhammad ta karshe, Gaskiya hakan bazai taba yuwa ba kasani Muhammad !ta yayama zasuce sedai ka dawo Dubaï !da zama wai saboda kawai kana son yer su" Ka tuna fah Muhammad kai kadai namiji,ba wai fata nake ba,amma yanzu misali idan na fadi na mutu wa zai sayawa kannanka kana can?"toh kasani hakan bazai taba yuwa ba har abadan, Abba na kaiwa nan ya mike a fusace ya wuce dakinsa"Maama ma mikewa tayi ba tare da tace komai ba, tabi bayan mijinta" Jiki a sanyaye Muhammad ya mike ya koma part dinsa" Tabbas hakan bazai taba yuwa ba,duk da kuwa ina son Nuria amma ya zama dole na hakura da itta"in har bazasu amince na aurota ta dawo Nigeria ba" Waya ya dauka ya kira Nuria ya fada mata duk yanda sukayi da iyayensa,ya kuma kara da cewa...ki sani fah Nuria na mijine yake auren mace ba macece take auren na miji ba"dan haka in har da gaske kike sona toh ki lallaba iyayenki,in kuma sunki amincewa dole mu hakura da juna,yana kaiwa nan ya kashe kiran. Nuria ce zaune cikin kuka take fada musu yanda sukayi da Muhammad,ta kara da cewa in har basu yedda anyi auren nan ba mutuwa za tayi, *Bayan sati daya* Wasa wasa Muhammad ya kwanta rashin lfy,da aka kaishi a sibiti bayan gwaje gwajen da likitocin sukayi ne suka tabbatar musu da cewa Muhammad ya kamu da ciwon zuciya kuma sunyi bincike ba komai ne ya hadda sa masa ciwon ba sai dan akwai a bunda yake so da ba'ayi masa ba,dan haka in har suna son dansu ya rayu toh sai sunyi gaggawar yi mai a bunda yakeso, Ba karamin tashin hankali su abba suka shiga ba, lokacin da sukaji bayanen likita, Zaune yake dashi da wani amininsa, bayan yagama bashi lbrn komai, Shiru Alhaji musa yayi sai can kuma ya gyara zama hade dayin murmuchi,dama damar da yake nema kenan kuma ya samu, dan haka ya fara magana kamar haka... alhaji Habib ina da maganin damuwarka amma bansan in zaka amince ba?" Cikin zumudi alhaji Habib yace ka fada min zan amince in dai dana zai samu lfy, Kara gyara zama alhaji musa yayi yaci gaba da magana, Dama akwai yer autata da ta rege batayi aure ba,dan haka mai zai hana ka amince masa da auren Nuria take kowa din,kaga in yaso idan an tashi auren sai a hada masa da Maimuna,in yaso itta Maimuna ta zauna anan itta kuma wancan ta zauna a kasarsu,tunda haka sukeso, Amma fah Muhammad bazai koma can ba cedai ya dinga kai mata ziyara lokaci zuwa lokaci, alhaji musa ya karashe maganar yana addu'a allah ya sa ya amince, Wani irin murmuchi yaga Abba yayi, Yana fadin wllhy hakan ma yayi abokina, gaskiya nagode da wannan shawaran, murmuchi shima alhaji musa yayi yana mai jin dadin amincewa da alhaji Habib yayi cikin sauki, Fadawa Muhammad Alhaji Habib yayi da cewa ya amince da auren amma hakan ba yana nufin ya janye maganar shi, akan komawar shi can ba?"a'a bai janye ba maganar tana nan, Ya kara da cewa in antashi auren harda Maimuna zai hada ya aura,itta ta zauna anan wancan kuma ta zauna acan,in yaso sai ya dinga kai mata ziyara, Kamar Muhammad bazai amince da auran Maimuna ba,sai Kuma daya tuna shi kadai hanyar da zai sa ya mallakar Nuria sai ya mallaki Nuria yasa shi amincewa, Yana kuma addu'a Allah yasa Nuria ma ta amince, Karban number Nuria abba yayi ya kirasu da kanshi,amma akayi rashin sa'a ba Nuria ce ta daga wayan ba,duk da kuwa dama can ba da itta yakeson yin magana ba, Bayan ya gaisa da mahaifin Nuria né ya fada musa waye shi"ya kuma kara da cewa Muhammad ne bashi da lfy tun lokacin dana hanashi dawowa Dubaï da zama ya auri yer ku, nan ne suma suka fada masa suma suna a sibiti tun ranar da Muhammad ya fada musu bazai iya zuwa nan ya aureta ba, Ikon allah abba ya fada ya Kuma kara kirmama soyayyar Nuria da dansa, "Gaskiya suna son juna" Shawaran daya yanke ne ya gaya masa,abun mamaki sai gashi cikin sauki Abie Nuria ya amince,da abba yaga ya amince ne yace insha allah zan samu lokaci nazo,toh Abie ya fada,sannun sukayi "sallama" Sannun ya kashe waya da gudu Abie ya nufi dakin da aka kwantar da Nuria domin yi mata albishir...... *Sakeena ismail Cameroon ce*✍️ 07049322735 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing*...✍️ Page 13&14 Free book Bismillahi rahmani rahim *******Ba karamin farinciki Nuria tayi ba"a lokacin da mahaifinta ya gaya mata iyayen Muhammad sun amince da auren su,amma da taji wai ba itta kadai zai aura ba,ba kuma dawowa zaiyi Dubaï da zama ba,yasa farincikin fuskarta daukewa, Kwantar mata da hankali Abie yayi ta hanyar cewa..haba habibti ke da ba kasa daya kuke ba ?"bafah ganinta zakiyi ba"sedai wata rana idan kin kai musu ziyara kawai Abie ya fadi, Haba Abie kaima fah kace"wata rana zan kai musu ziyara kaga kuwa akwai ranar da zamu hadu kenan ta fada hawaye na taruwa a cikin idanunta, Haba habibti kifah sani ko kin amince ko karki amince bazasu taba janyewa daga aura masa yer Nigeria ba?" Kinga kuwa in baki amince ba,auren wancan zaiyi ya kyaleki kinga kin resa shi har abadan dan haka gwara ma ki amince" Shikenan Abie na amince ta fada tana share kwallan daya zubo mata" Yauwa koke fah habibtina,ki kwantar da hankalinki kinga kina tare damu, Insha allah mahaifin Muhammad din yace zaixo kwanan nan, Da haka dai aka samu aka shawo kan komai, *Bayan kwana uku* Abba yaje yayi wa kawunshi daya rege mai daya filo bayani akan auren,anan ne kawu bala ya bawa abba shawara tunda abun yazo da haka ya fara zuwa can Dubaï din yayi komai in yaso shi da Muhammad kuma sai su saya anan in yaso idan an daura sai ya tafi can din,in yaso idan ya dawo sai itta ma Maimuna ta tare,tunda itta kasarsu daya,kuma anan yake kasuwancin sa,kullun suna tare, Kamar yanda kawu ya fada hakan ce ta kasance,dan abba ya dafi can su kuma sun tsaya anan, Rana daya aka daura auren Nuria da Maimuna,amma na Nuria aka fara daurawa dan haka itta ce uwar gida,itta kuma Maimuna itta ce amarya,dan haka sai Muhammad ya fara tarewa da Nuria sannun zai tare da Maimuna, Ranar da aka daura aure"da dengin Maimuna suka ce suna jira su kai amarya da yamma abban Maimuna ne yayi musu bayanin cewa ba yau ne amarya Maimuna zata tare ba,ba kuma itta kadai aka daurawa Muhammad akwai wata a kasar Dubaï kuma da itta aka faka daurawa,kuma nata aka fara daurawa Kafin a daura na Maimuna! dan haka sai ya fara zuwa wajan ta ya dawo tukun in ya dawo sai itta ma ta tare, Magana kawayen Maimuna da kuma yen biki suka din gayi,wai ta yaya yana gari aka daura musu aure da Maimuna amma zai sallake ya tafi can wata kasa, Maimuna dai bata damu ba, dan tasan Muhammad yafi zama a Nigeria"kafin ma yaje Dubaï sai an dau lokaci, Dan haka zatayi iya bakin kokarinta na ganin cewa bai koma Dubaï da wuri ba, Da kawayenta sukaga bata damu ba, shine suka tambayeta dalilin rashin damuwar tata,da tayi musu bayani daya daga cikinsu"cewa tayi shegiyar kawata haba dama nasan ruwa bata tsamin banza, shiyasa kika barmu muke ta haukar mu _mu kadai, Da haka dai suka karasa wunin nasu da daddare kowa ya watse sai yen uwanta da suka zo daga nisa kadai suka rege, *Washe gari* Wajan karfe goma jirgin su Muhammad ya daga zuwa kasar Dubaï, Sanda ya shiga jirgi gani yake yau jirgin baya sauri dan so yake kawai ya ganshi a gaban sahibarsa, Ni kuwa sakina nace haba angon Nuria wannan wana irin zumudi ne haka?"🤔🤩 *Bayan magriba* Bayan ya sauka a hôtel din da abbansa yake?" Dan babu yanda iyayen Nuria baduyi da shi ba akan ya sauka a gidansu" Amma yaki da suka dame shi ma cewa yayi ya riga da ya bada kudin daki da haka dai suka kyaleshi amma badan suna so ba, Wanka yayi yaci abinci,sai daya kammala komai abba ya zaunar dashi yayi masa nasiha sosai akan ya rike su amana ya kuma yi adalci,kar yaga yafi son Nuria yace zai dinga banban tasu a'a?dolen sane ya sauke nauyin Maimuna,kuma duk matansa ne"dan haka ya rike kowacce da amana, Bayan yagama yi masa nasiha ne suka hau mota suka nufi hanyar gidan daya kama musu Kafin ya samu nasa gidan, Tunda abun yazo a kurarran lokaci, Maimuna ma dan yana da gidaje daya gina masa ne har guda uku acan shiyasa abun yazo da sauki, Kasan cewa an rigada an kai Nuria dakinta,dan haka suna zuwa,suka tarar da itta da Abien ta itta ma bayan an gaisa ne"aka shiga yi musu nasiha sannun suka tashi suka tafi, Ranar dai an sha soyayya sosai sai nan da nan Muhammad yake yi da Nuria, *Bayan shekara uku* Nuria ta haihu inda ta haifi danta na miji fari mai kyau gwanin ban sha'awa, kamarsa daya da mahaifinsa amma haske kam na mahaifiyarsa yayo, saboda shi Muhammad yana da haske amma ba sosai ba,dan kalarsa irin kalar nan ne da ake kira da wankan tarwada! Yanzu haka watanshi sha tara a duniya,amma in kaga girman yaron sai ka dauka zaiyi shekara uku, Muhammad duk karshen wata yana zuwa,duba su idan ya tashi komawa da kuke suke rabuwa da Habib wato sunan abba aka sa masa, Badan yaron yayi kankanta ba da babu a bunda zai hanashi zuwa dashi Nigeria, Nuria in ta dauki hutu a wajan aiki itta ma takanje musu lokaci zuwa lokaci, Ranar farko da Maimuna ta fara ganin Nuria ba karamin kishi taji ba" Dan Nuria tafi Maimuna kyau nisa ba kusa ba, Duk da kuwa itta ma dai Maimuna bawai bata da kyau ba ne?" Tana da kyau dai dai gwargwodo,kwai dai baza'a hada balarabiya da ba haushiya ba, Abunda yafi konawa Maimuna rai shine bai wuce na yanda Muhammad yake nunawa Nuria da danta soyayya a gabanta ba ?" Dan a bun yana kona mata rai sosai har gani take kamar cin fuskane" *Bayan shekaru biyar* A cikin shekaru biyar din nan a bubuwa deyewa sun faru a ciki kuwa har da rayuwar iyayen Muhammad da direvansu sunyi accident! Ta hanyarsu ta dawowa daga bikin da suka je daga kauye,wanda yer drevanshi ne take aure,shine drevan ya gaiya ce shi"daurin auren,kasan cewa Alhaji Habib mutumin kirki ne"shiyasa yace hajiya indo ta shirya suje tare suyi musu allah sanya alkhairi, shine dalilin su na zuwa,kauye,ashe basu sani ba mutuwa ne yake kiransu"dan daga abba har maama da drive ba wanda ya rayu daga cikinsu duk sun mutu, Kannensa ma Allah ya basu sa'a basu je ba,da tuni abun har dasu zai faru, Sunyi kuka sunyi kuka har sun gode Allah, Dan kowa yaji mutuwar Alhaji habib Ibrahim, dan babu wanda bai sanshi a kasar ba"kasan cewar shi babban mutun, Itta ma dai Maimuna tana da yara biyu a yanzu,aisha,da kuma mufeeda,itta Aisha sunan hajiya indo aka sa mata" wato mahaifiyarsu Muhammad mufeeda kuma sunan mahaifiyarsu Maimuna, Mufeeda ce babba sai kuma Aisha,basu da tazara sosai,dan mufeeda tana da shekara daya aka haifi Aisha kasan cewa konika tayi,wai itta bata samu na miji ba,shiyasa tayi duk yanda zatayi ta kuma kara samun wani cikin Amma Still data tashi haihuwa macen ta kara haifa,abun ya batawa ran Maimuna sosai, Ohhh ni sakina sai kace ke kike bada haihuwan ?kima godewa Allah tun da kinsa mu" A haka dai rayuwa taci gaba da tafiya inda Habib yayi karatunsa a kasar Dubaï,dan acan yayi karatusa gaba daya, Su kuma su aisha a nan kasar Nigeria!sukeyi, Bayan sungama secondari aka kaisu kasar india,suka ci gaba da karatunsu acan, Tun lokacin da habib yayi digirinsa na farko,mahaifinsa ya dorashi akan dayan kasuwancin sa,watoh kasuwanci da alhaji Habib ya bari seda a damfopi da leces,kasan cewa suna da babban kanfanin da suke da injin da sukeyin a tamfopin da leces din dashi,dan saboda tsabar kyau ma yasa kasashe daban daban suke zuwa suna tsarawa suje suciyar, A yanzu haka suna da kanfani a Nigeria suna dashi a kasar Dubaï,kasan cewa Habib zamanshi yafi yawa a Dubaï ne yasa,aka samo mutanen da zai dinga kulan musu da kanfaninsu da yake nan Nigeria, shi kuma yana kula da wanda yake Dubaï, Shi kuma mahaifinsa yana kula da gidajen man petir daya bude,da a yanzu haka gidajen man shi ya gaza ko ina"a Nigeria dalilin daya sa aka bashi shogaban man petir ta kasa gabaki daya kenan, Dan yanzu bai ma fiya zama a kano ba"dan yafi zama a Abuja ! Kinji labarin Habib Muhammad Habib, kenan safna ta fada dana kallon afiya da tun da ta fara maganar take geda kai kamar kadangare har ta Kai aya, *Cigaban labari* Gaskiya babansa dan gatane dole shima ya zama dan gata"nagode sosai safna da labari,afiya ta fada tana duba agogon dake daure a hannunta" Kai uhu tayi fah safna?" Yanzu a bunda za'ayi kawai ki kulle office din ki sameni a mota sai na ajiyeki a gida tunda ni ma tafiya zanyi, To aunty gani nan zuwa safna ta fada ,sannun ta fara hada kayanta, Batafi mintuna biyar ba tagama hada su ta fito harabar kanfanin,ta nufi wajan ajiye motoci,tana zuwa ta shiga motar suka wuce" Shiru babu mai magana har suka karasa kofar gidansu"safna, Toh aunty nagode sosai,amma me zai hana mushiga tare ku gaisa da ammi na"a'a safna yamma tayi amma insha allah zanxo ranar lahadi tunda babu aiki sai mugaisa,toh aunty sai kinzo nagode sosai,safna ta fada tana shiga cikin gidansu ta karamin gete,hannu ta dagawa afiya a lokacin da take juye hancin motarta, Bayan ya fita daga kanfanin ta"bai saya ko ina ba sai kanfanin su,ya jima a can dan sai daya shiga ko ina yaga ko ina normal sannun ya fito, Sai daya saya yayi sallah sannun ya nemi restored mai kyau ya samu yaci a binci sannun ya wuce gida Yana zuwa gida kai saye part dinsa ya wuce "yana zuwa ruwa ya wasa,bayan ya fito shiryawa yayi cikin farin tishet mai karamin hannu da kuma gajeran wando daya saya mai iya guiwa, sannun ya feshe cikinsa da turarukan masu sanyin kamshi, Wayoyinsa ya dauka ya fita daga part din ,wata karamin kofa nagani ya shiga, Sai kawai nagansa a cikin wani lambu mai masifar kyau,wajan da aka ajiye kujeru ya nufa ya zauna, Hade da lumshe ido iskan dake wajan na ratsa shi, Har kalla ya kai 2 second a haka sai daga fisani ya bude idanun nasa,wayoyinsa daya ajiye a kan teburin dake gabansa ne ya dauki daya daga ciki yayi dialing wata number,bugu biyu an dauka, Sallama yaji anyi ya amsa sannun ya fara magana,ammi barka da wannan lokacin,ta daya bangaren aka amsa barka dai ibni!ya Nigeria yatsine fuska yayi kamar dama jira yake a sosa masa ida yake masa kai kayi dan haka a take ya somayin magana,wllhy ammi babu dadi kwata kwata,ni wllhy jibi ma zan dawo ya fada da harshen larabci, kuma dama tun dazu da harshen suke magana,. Haba ibni! gidan mahifinka ne fah ka dena haka" Haba ammi kefah naga alama ko kewata ma bakiya yi"saboda kwata kwata baki damu dana dawo ba,ya fada kamar zaiyi kuka, Sorry ibni, ina missing dinka mana,kai dai kayi musu ko sati daya ne sai ka dawo, Daker dai ya amince zaiyi sati daya,dan sai data hana da rarrashi sannun ya amince"Sallama sukayi ya kashe wayan........, *Sakeena ismail Cameroon ce ✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing....✍️* Page 15&16 Free book Bismillahi rahmani rahim *********"Sallama sukayi ya kashe wayan,maida wayan yayi ya ajiye akan teburin daya daukota dazu"gyara zamansa yayi ya jingana da jikin kujerar hade da lumshe ido,iskan dake kadawa a wajan na ratsashi a ko ina na cikin jikinshi, Lokaci daya ya na yinshi ya fara sauyawa,a take kuwa ya mike da sauri sauri zuwa ciki, Part dinsa ya wuce yana shiga bai ko saya a palo ba kai saye daki ya shiga, Kayan jikinsa ya rege, tawal ya dauka ya daura a gudunsa,sannun ya shiga toilet, Wani irin a jiyar zuciya ya sauke a lokacin da ruwan yake sauka a kanshi, Sai daya tabbatar komai nashi ya dai dai ta sannun ya kashe ruwan,wani tawal daban ya sake daukowa ya daura akan kugun sa, Alwala yayi ya fito dan ankusa kiran sallar magriba, Mai ya dan shafa kadan da turare, wajan wardrobe dinsa yaje ya bude,gajeran wango ya dauka ya saka,sai farin jallabiya,irin nasu na larabawa,watoh mai godon hannun, Lokacin har an fara kiran Sallah, dan haka sallaya ya shin fida ya tada sallah,kasan cewa baya zuwa masallaci in yazo kasar Nigeria,saboda in yaje mutane suyi ta kallon shi,shi kuma baya son kallon kwata kwata, Tun mahaifinsa na takura masa da sai yaje masallaci yayi Sallah shima har ya dena,saboda Shima yana ganin yanda mutane sukeyi akansa in sungan shi, Sallah yayi yana idar ya zauna ya shiga yin azkar bayan ya gama azkar,alkur'ani ya dauka ya shiga karan tawa, "A takaice dai bashi ya rufe alkur'ani ba sai da aka kira sallar i'sha,sannun yayi addu'a ya shafa sannun ya rufe alkur'ani, Mikewa yayi_yayi sallar i'sha yana idar ya tashi ya nade sallayar ya ajiye, Kujeran dake hade da gadon ya koma ya zauna, Yana jiran daddyn sa ya dawo daga sallah ya shiga ya gaishesa kafin ya kwanta" Shiru yana nan zaune,har kusan mintuna goma, Nifah dalilin daya sa bana son zuwa kasar nan Kenan,kullun mutun na gida kamar mace"ya fadi,yana mika hannu ya dauki daya daga cikin wayoyinsa" Nemo number dinta yayi,zai danna kira,sai kuma ya fasa, Humm itta tayi min ba dai dai ba, bata kirani ta bani hakuri ba sai ni zan kirata,ya fada hade da maida wayan ya ajiye, Sai kuma ya sake dauka bari dai na kira tunda nayi niyar taimako bai kamata na fasa ba,yayi maganar hade dayin dialing number nata, Afiya kuwa tana komawa gida ta tarar da mahaifiyarta zaune a palo itta da wani alhaji ga Kayan motsa baki data tara mai a gabansa,sai ci yake,kana gani kasan ba iya cinyewa zai ba, ko da kuwa su biyu zasuci, Kallo daya tayi musu ta dauke Kai ta wuce" dakinta"hajiya fatima kuwa abun ba karamin bata mata rai yayi ba,da ba gaida bakonta ba,dan haka tayi alwashi Yana tafiya zatayi maganinta, Tana shiga dakinta ta jefar da Jakarta a kan gabo,sai takalmin kafar ta data tire shima ta jefashi a kasa, Gefen gadon ta zauna,hade da dafa kanta dake mata mugun tsarawa, sakamakon hakan ne ya sa jijiyoyin kan fitowa, Tire maya fin kanta tayi_tayi wurgi dashi itta ma, tire ribbon da tayi parking gashin nata dashi tayi sai ta saka hannun akan ta shiga yamutsa gashin kan,kasan cewa kan a tsefe take shiyasa a take gashin kan ya har gitse a lokaci daya ta fice daga cikin hayyacinta, kamar ba itta ba,ta dawo kamar mahaukaciya ! Kifah kanta tayi a sakiyar cinyoyinta ta saki kukan da take ta rikewa tun dazu" Wani irin kuka takeyi dan kallo daya zaka mata ka fahimci ta dade tana son yin kukan amma bata samu damar yi ba, Budewar kofar da taji anyi ne ya sata gakatar da kukan ta takeyi ta dago, manya manyan idanunta,dan ganin waye" Mamarta ce ta shigo, fuskarta babu ko fara'a a ciki,duk da kuwa dama can ba wani fara'a ce da itta ba ?"amma na yanzu daban ne, Karasowa tsakiyar dakin tayi,afiya na ganin haka ta mike,tana tambarta lfy, Mama lfy?kafin ta rufe bakinta taji saukar maki akan kuncinta,dafa wajan tayi,lokaci daya kukan da takeyi ya tafi,idonta ya kara ja sosai, jijiyoyin kanta suka kara fitowa, Kallon mamar take tama rasa bakin magana, Ki shiga hankalinki afiya,kar kiga kudin ki mukeci a gidan nan ya hanani yi miki wani abu, Kina ganina da mutun amma kizo ki wuce ko sannu baza kice masa ba, ballantana na sa rai zaki gai dashi?" Toh bari kiji zaki iya min wani abu na hakura amma wllhy baki isa kiwa bakina na jure ba,kuma ko kina so ko bakiya so sai na aure shi,sai muga mai zakiyi ?" Haba mama kullun fah sai kin kawo na miji a gidan nan da suna zance,in anyi magana kice aurenshi zakiyi, Baza har kuga nawa zaki aura ?"afiya ta fadi, "Toh uwata" Tana kaiwa nan ta sa kai ta bar dakin, shikenan mama kiyi duk a bunda zakiyi, Tana nan zaune har akayi magriba da i'sha bata tashi a inda take ba,kasan cewa bata Sallah yau, Knocking taji anayi, batace komai ba, ballantana mai knocking din yasa rai zata bada ijinin shigowa! Turo kofar akayi a hankali,dagowa tayi ta dora akan fuskarsa kekkyawar kaninta, Cikin tashin hankali Mohseen ya karasa gabanta ya suguna ya shiga tambayarta"...aunty Afi maiye sameki?" ya naga kumatunki ya kumbura?" mai yasa ki kuka ?"duk a lokaci daya yaron yayi mata wannan tambayan,itta dai da ido kawai take binshi dashi,data rasa abunyi sai kawai ta rungume yaron ! Shiru ko wannensu yayi, Har kanla sun kai 5 second a haka sai daga baya ta sakeshi tana sauke a jikar zuciya, Jeka kwanta kanina gobe zamuyi magana, Kai Kawai yaron ya iya gedawa sannun yayi mata sai da safe ya bar dakin, Itta Kuma afiya badan komai yasa ta fada mai hakan ba sai dan dana so ya tafi ya barta ne,dan tana bukatar kasan cewa itta kadai, Yaron na fita da minti biyar ta mike ta je palo sai data tabbatar mama bata nan sannun ta dawo dakinta, tarar da wayarta tayi na ringing,tana dubawa taga babu suna dan haka bata dauka ba, ta tabbata mama ba Kuma saukowa zatayi ba in ta hau sama, Wata katuwar akwatin ta ta jawo, wardrobe dinta ta bude ta shiga debo kaya tana zubawa a ciki,dan itta kanta bata san adadinsu ba, Sai da taga akwatin ta cika fam ta kaya sannun ta rufe,duk kananun a bubunwanta da zata wukata sai data dauka, Takarda ta samu da biyo ta danyi rubutu layi biyu,ta ajiye,kara dauko wata tayi ta sakeyin wani rubutu da tafi wancan yawa, Dauko dayan ta kardan tayi ta hada da wanca dake hannunta ta fito,karkashin kofar Mohseen ta ajiye daya,daya kuma taje ta tura shi ana mama,tana gamawa ta koma dakinta ta dauko akwatin ta ta fita, Cikin sanda ta fita ta kofar baya,dan in tace zata dauki motarta su mama zasuji, Dan haka da kafa ta fita tana fita babu kowa a unguwar duk da kuwa dare baiyi sosai ba amma babu kowa a waje"kasan cewa unguwar masu kudi,ko da rana ma basu fiya fitowa ba, ballantana da daddare,saboda kowa na cikin gidansa, Bakin titi ta nufa ta danyi yafiya kadan kafin ta Karasa bakin titin,saboda gidansu yana da dan nisa da bakin titi kadan, Tana zuwa titi kuwa tayi sa'a ta samu abun hawa da wuri dan haka shiga kawai tayi ta fada masa inda zai kaita suka wuce, Kira daya yayi mata da yaga bata dauka ba sai kawai ya kyaleta, Tashi yayi ya wuce Cikin gidan, domin gaisawa daddyn sa kafin ya kwanta" Bayan yaje sun gaisa baifi mintuna goma yayi a wajan sa ba,yayi musu sai da safe ya dawo, Jire jallabiyan yayi ya dau kayan bacci riga da wango masu taushi ya saka, Remote ya dauka ya kara gudun AC ya hau makeken gadonsa ya kwanta,yayi rubda ciki yan danjin mararsa na danyi mai ciwo kadan kadan, Daker ya samu bacci! dan kwana yayi yana juye juye akan gadon sai daf da a subaha ya samu bacci ba shi ya tashi ba sai wajan 8 na safe, Ranar dake dan fitowa daga cikin labulen ne ya sashi bude ido a gankali,ganin ranar daya fito sosai ne ya sashi mikewa da sauri,ya fada toilet, Wanka da alwala yayi a gurguje ya fito,da sauri sauri ya shiya,yayi Sallah, Bangaren afiya kuwa hôtel tace wa mai a daidaita ya kaita,ta kwana acan kafin zuwa gobe tasa mu a bunyi zaiyi., *Washe gari* Tun 6 na safe ta tashi,waya ta dauka ta kira safna, Safna data idar da sallah kenan taga kiran afiya ya shigo wayarta,cikin mamaki ta dauka tana tambayarta lfy, Aunty lfy kuwa naga kin kirani da sassafe nan ?" Babu komai safna saboda na yer da dake ne shiyasa ban kira kowa ba sai ke" Haka ne aunty! meye faru toh,ya naji muryarki wani Iri?" Kinga safna bana son tambaya ki nitsu kiji a bunda zan gaya miki, "Toh aunty ina jinki?" Yauwa ba kin taba cemin yayanki dinlali ne ba ?" "Eh dillali ne"yauwa dan allah turo min da number dinshi ina son gida da zan zauna a ciki na yen watan ni,kuma bana son gidan ya kasance cikin gari,ya nemo min wanda ya dan fita cikin gari kadan kuma mai dan kyau,kafin mas'ala ta ya dawo dai dai, Toh aunty amma waca mas'ala ce haka wannan,har da zaki bar gida?" Kinga safna kinfi kowa sani bana son yawan tambaya,zakije ki gaya masa ko Kuma dai zaki ban number shi ni na fada masa ?"saboda ina bukatar gidan nan _nan da awa biyu zuwa uku, Toh aunty bari naje nayi masa magana yanzu zan kara kiranki, okay kawai afiya ta iya fadi tana kashe wayan. Tashi safna tayi ta wuce dakin yayanta,tana zuwa tayi knocking sai daya bata ijinin shigowa sannun ta turo kofar ta shiga, Bayan ta gaishesa ne take fada mata yanda sukayi da afiya,yace babu komai akwai gidaje, Karban number afiyan yayi,ya kirata bayan sun gaisa ya fada mata waye shi,sannun yace mata ta hau online zai tura mata gida jen sai ta zabi wanda yayi mata,toh ta ce tana kashe wayan, WhatsApp ta shiga tana shiga ta bude hotunan gida jen ta shiga dubawa, kuma dama ko wana gida ya rubuta a unguwan da yake, Itta yanzu ba kyau gida take bukata ba, unguwar take dubawa,dan haka wani gidan da taga an rubuta hotoro ta zaba kuma hotoro amma na can ciki ne,gidan na dauke da dakuna guda uku ko wana daki akwai toilet a ciki,sai palo guda daya sai kitchen a gefe,dan haka shi ta zaba ta tura masa"tare da tambayar sa nawa ne kudin,kudin gidan ya tura mata,bayan sun gama komai ne tace ya shirya yanzu zata fadawa safna inda zasu sameta, Bayan tagama da yayan safna ne ta kira safna ta fada mata inda za'a sameta, Tana kashe waya safna ta mike ta wuce dakin yayanta tana zuwa ta fada masa,inda za'a sameta, Key din motarsa ya dauka suka fita,suka shiga mota suka nufi wajan da afiya ta kwatan ta musu" A bakin kofar hôtel din data kwatan ta musu ne suka tarar da itta saye tana jiransu ga katon akwati a gabanta, Tana ganinsu ta fada cikin motar tayi musu alamu da hannu dasu tafi, Tada motar yayan safna yayi suka dauki hanyar hotoro, Aunty ina kwana,lfy afiya ta amsa a takai ce, Yayan safna kuwa uffam baice da afiya ba,wai shi jira yake ta gaishesa, Hummm ni kuma nace indai afiya kake jira ta gaisheka toh zakayi shekara, Safna dai yasan halin kowa dan haka tace aunty ga yayana baku gaisa ba ?" Sannu afiya ta fada,tana kallon titi, Yauwa shima najeeb yayan safna ya amsa" Murmuchi kawai safna tayi,hade da girgiza kai, *Gidan su afiya* Mohseen ne ya bude kofar zai wuce makaranta,yaci karo da takardan da afiya ta ajiye jiya, sunkuyawa yayi ya dauko ya bude ta kardan, Ya karanta, yana gama karan tawa ya koma cikin daki ya boye ta kardan ya fito, Sauka ya shigayi hawaye na taruwa a cikin idanunsa tausayin kansa dana yayarsa na ratsa shi, Yana sauka bai saya yin breakfast ba ya wuce, Yana fita ya tarar da drive na jiranshi dan haka gaishesa kawai yayi ya shiga mota ba tare daya gaida da security din su ba, drive ya ja motar suka bar gindan, Afiya taje taga gida yayi mata kyau sosai,dan haka a take ta karbi number account dinsa ta saka mai kudinsa,haka ma safna bata barta a baya ba dan itta ma sai data bata wani Abu,ta kuma kara da cewa dan allah karsu fadawa kowa Inda take,safna tace in sha allah shi kuma yayan safna cewa yayi shi ina ruwansa,da fadawa wani, A take ta ciwo kayan daki da kayan kitchen ta hanyar online,kuma ance nan da awa daya za'a kawo mata,a haka dai ta shiga gidan ta zauna a haka kafin a kawo mata kayan daki, Awa daya nayi kuwa aka kawo mata kayan daki da kayan kitchen,har ma da kayan girki, Cikin awa biyar angama gyera mata dukan a bunda take bukata, "Gidan yayi kyau babu laifi" Wayarta ta kashe baki daya,ta samu ta kwanta,dan tasan in ta bar wayarta a kunne dole a gano inda take, *Gidan su afiya* Mamace ta tashi daga baccin data sha ta koshi, sai faman hamma take,bude kofar dakinta tayi kenan zata sauka taje ta karya taci karo da takarda a bakin kofa,kamar zata wuce ta barshi sai wani abu kuma yace mata dauki kiga me nene a ciki,dan haka ta sunkuya ta dau ta kardan ta bude ta shiga karantawa, Mama ni na tafi tunda kullun abun naki kara gaba yake yi, Wani irin ansharr ta saki...wllhy afiya baki isa ba"ni zakiwa haka ni zaki to zarta,ta fada sauka tayi fuuuuu kamar zata shi sama ta wuce dakin afiya,tana zuwa ta banko kofar da kafarta ta shiga, wayam tagani babu afiya babu labarinta,jiki a sanyaye ta karasa dakin,lokaci daya kuma ta nemi yinwan da takeji ta rasa" Wata jaka tagani a sakiyar dakin dan haka ta karasa wajan da jakar take,ta sugunna ta bude jakar,wani irin murmuchi tayi a lokacin da idanunta ta sauka akan makodan kudaden dake ciki........, Ohhhh ni sakina,gaskiya hajiya fatima kina son kudi deyewa🤔yanzu kudi yafi yayanki? *Sakeena ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 17&18 Free book Bismillahi rahmani rahim *********"Wani irin murmuchi tayi a lokacin da idanuwanta suka sauka akan mako dan kudaden dake cikin jakar !rufe jakar tayi ta mike tana murmushi,lokaci daya taji yinwar ta ya kara dawowa,ji kake kululululu haka cikin ya shigayi shafa cikin tayi ta bude kofah ta fita ta bar dakin ! Habib kuwa yana idar da Sallah ya mike ya nufi cikin gidan, Dagowa Alhaji Muhammad yayi ya zubawa dan nasa da yafi so yafi kauna"idanu tafiya yake cikin nitsuwa har ya karasa gaban dinning din, Good morning my daddy?"Habib ya fadi a lolacin daya durkusa a a gaban daddy shafa kansa yayi yana fadin morning my son!ya katashi?"fine ya ya fadi a takaice, Oya zoka zauna kayi breakfast,kai ya geda yana mikewa, Kujera na kusa da Dad dinshi ya ja ya zauna, Fitowa tayi daga kitchen hannunta rike da wani kula,ta karaso ta ajiye kan dinning din, Momma barka da safiya,barka dai ta amsa tana dauko plete tayi ta shiga zubawa daddy dankali da kwai din, Tana gama zuba masa ta tura mai plete din gaban sa"sannun ta dauki daya ta zubawa Habib shima, ta tura masa" Yana gama cin abinci ya mike,kallon sa daddy yayi yana tambarsa inda zashi"son ina zaka kuma?"zance wani waje yanzu zan dawo ya basa amsa"shikenan sai ka dawo ka kula da kanka sosai kuma karka fita kai kadai, Kai kawai ya iya gedawa yasa kai ya fice, Masu basa kariya na ganinsa suka mike suna gaishe sa,hade da bude masa mota ya shiga suka rufe,suma suka je suka shiga nasu mai gadi ya wangale musu gete sukayi waje da motocin su, Jinginar da kansa yayi da jikin kujerar motar,hade da lumshe ido yana tunanin meyesa ta kashe waya,meyesa jiya kuma ya kirata bata dauka ba?ohhhh good ya fada hade da dafa kansa,shi yama manta shaff batasan number sa na Nigeria ba" Ina itta da take business ai ya kamata ta daga duk number daya kirata, Ya fadi" Suna zuwa kanfanin nata, kamar yanda ya shiga shi kadai a wancan zuwan nashi toh yauma hakance ta kasan ce,dan ce musu yayi su jira sa a waje, Yana shiga ciki,bayan sun gaisa da safna yake cewa yana son ganin afiya,safna tace masa bata zo wajan aiki ba yau! Kina nufin yau bata zoba?"eh bata zoba,kallon ta yayi na yen second ni, sannun ya dauke kai hade dayin tsaki, sai ya juya ya bar office din, Badan komai yasa ya dan kalleta ba ?sai dan yana son ya tabbatar ne shin da gaske ta zo ko bata zoba" Dan shi da zarar ya kalli idon mutun toh yana iya ganewa in karya yayi" Da yamma bayan Mohseen ya dawo daga makaranta,yi yayi kamar bai san a bunda ke" faruwa ba! Tarar da mama yayi zaune a palo bayan yayi mata sannu da gida kamar yanda ya saba ne ya juya da niyar, zuwa dakin afiya, yaji mama na cewa...toh bata nan sai ka dawo,dan tun jiya da daddare ta bar gidan nan,da sauri ya juya cikin firgici da tashin hankali,kai in kaga yanda yayi sai ka ranse yanzu yaji labari, Da sauki ya karaso inda take ya shiga tambayarta..mama ina ta tafi ?" Kaga Mohseen ka kwantar da hankalinka ta tafi saboda nayi mata fada shine ta kama hanya ta tafi,saboda bata daukeni a bakin komai ba ?" Haba mama meyesa kikayi haka,kince ke kika mare tama ?"eh Mohseen nice na mareta ko zaka rama mata ne,mama ta fada cikin tsawa,cikin tsoro da firgici Mohseen yake kallon mahaifiyarsa, Kai Kawai ya iya girgiza wa ya juya ya wuce sama ba tare da ya kara cewa komai ba, Ohhh na dauka zaka saya ka rama mata ai,mama ta fadi,hade da komawa ta zauna, Zaune yake ko a binci bai ci ba"duk da kuwa aunty Afi tayi mata baya nin komai,amma shi kam duk da haka abun bai mata dadi ba ko ka dan, Wayarsa yaji na ringing cikin fara'a da kuma sauri ya duba ko aunty afiya ce"ganin da yayi ba number dinta bace yasa fara'ar fuskar sa dauke wa, Kamar zai ajiye wayan sai wata zuciya kuma yace mata ta dauka,dan haka yayi saurin dagawa,dan ta kusa tsinkewa, A kunne ya sa ba tare da yayi magana ba,can bangaren kuwa afiya ce kwance akan sabon gadon ta,jin da tayi baiyi magana bane ya sata yin magana..kanina baza kayi magana bane ba na kace "ai Mohseen na jin haka yayi saurin yin magana.... a'a aunty Afi karki kashe dan allah ! Shiru afiya tayi, yana yin da taji muryan kanin tana ne yasa jikinta yin sanyi, Kanina lfy,ina fah lfy aunty Afi bayan kuma bakiya gida, Haba kanina ka sani fah shekaru na ja kuma har yanzu mama bata canza ba"ka sani fa in ta mutu a haka ba tare data dawo kamar ko waca uwa ba ?sai Allah ya tambaye ta, Saboda kasan ni tsarai ranar gobe kiyama sai Allah ya tambayeta akan amanar da allah ya bata saboda mu amana ce a wajanta, Kanina kayi hakuri ka daure ka tayani mai da mahaifiyar mu kamar ko waca mahaifiya da yaya suke da burin samu, Bayani sosai afiya tayiwa Mohseen ya kuma amince lokaci daya ya nemi bacin rai da mama ta sa shi ya rasa, Dan haka suna gama waya da afiya ya ajiye wayan cikin kwarin guiwa ya tashi ya fita domin samowa kansa a bunda zai ci" *Bayan kwana biyu* Kullun da daddare afiya na kiran Mohseen suyi magana ya kuma bata labarin mamarsu, Haka ma safna suna waya da itta,duk abunda yake wakana a kanfani safna na fada wa afiya!kuma tana tura mata komai daya shafi kanfanin, Duk da afiya bata nan amma tana kokarin yin aiki daga inda take in safna ta tura mata, Kusan sau biyu habib na zuwa kanfani amma in ya tambayi safna amsa daya take bashi,afiya bata zo ba"yau ma dai zuwan shi kanfanin kenan,ya tambayeta in ta zo ? a'a yau ma bata zo ba,kina nufin yauma bata zo ba Habib ya tambaya, Eh bata zo ba"kallon kwayar idanunta yayi sai ya dauke kai,hade dayin murmuchin da shi kadai kasan ma'anar shi, Okay Zaki iya kwantan tamin gidan su"nasan unguwar mu daya da itta amma bansan gidan su ba" Eh mezai hana, Kwatance safna tayiwa habib,godiya yayi mata ya fita ya bar office din, "Kofar gidansu afiya ! Saukowa yayi daga cikin motar dan yau shi kadai ya fito ya hana kowa binshi, Knocking yayi, ba'a wani dau lokaci sosai ba aka bude karamin gete din gidan, Kallon rashin sani Yusuf yayiwa Habib, Habib na ganin haka ya mikawa Yusuf hannu! Kallon hannun Habib Yusuf yayi,sai ya kalli hannunsa, tunani yake ya akayi babban mutun kuma balarabe haka yakeson hada hannu da nasa? Fahimtar hakan da Habib yayi ne ya sashi fadin haba abokina! ko baka son musabahan ne ?" A'a ranka ya dade gani nayi hannunka da nawa ba daya bane ba, Nikam banga bam banci hannun na da naka ba" dan haka mugaisa kawai,ce dai in gaisawan ce baka so" Ai Yusuf na ganin haka ya mikawa Habib hannu sukayi musabahan,sunana Habib Muhammad Habib ! Habib ya fadi a lokacin da hannunshi ya hadu dana Yusuf, Zaro ido waje Yusuf yayi yana nuna Habib da mamuniya yatsanshi Hade da fadin kana nufin kaine dan shogaban man petir kasar nan ?kai kakwai Habib ya geda mai, Yauwa afiya nake son gani Habib ya fadi,a lokacin da yake tire dannun sa daga cikin na Yusuf dan wani irin riko yayi mai,da har yasa hannun ya fara ja,abunka da farar fata! Wllhy ranka ya dade madam afiya ta kwana biyu bata gidan nan muma nemonta mukeyi, Wai kana nufin bata nan kwana biyu ? eh wllhy bata nan, Yusuf ya sake fadi Cikin sanyin murya, Kuma kuka zauna ba tare da kun sanar da yen sanda ba" Wllhy hajiya babba ta Hana,da mukace zamu fadawa yen sanda cewa tayi yer tace ko Kuma yer mu ? mukace mata yer tace"tace toh indai haka ne babu ruwan mu da harkan gidanta,tunda mu aiki ne ya kawo mu muyi aikin mu,in ba haka ba kuma zata sallah memu, shiyasa tun ranar bamu kuma cewa komai ba"Yusuf ya karashe maganar cikin mutuwar ciki, Ok ka kwantar da hankalinka zan nemo ta insha allah,fada min number dinka duk yanda ake ciki zan fada maka,kuma karka kuskura ka fadawa hajiya komai,cikin farinciki ya ce toh,ya shiga fada masa number dinsa, Bayan ya gama fada masa number din ne ya tiro 50ya mika masa"karba Yusuf yayi Yana godiya, Mungode sosai ranka ya dade!babu komai babu yawa iya wanda ya rage Cikin aljihun nawa kenan,amma in na sake dawowa zan kara ma, ya juya ya nufi inda yayi parking din motarsa,ba tare daya saya jin godiyar da Yusuf yakeyi mai ba" Kanfanin ya komai yana wani irin murmuchi dashi kadai yasan ma'anarshi" Yana zuwa kai saye office din safna ya nufa, Turo kofar yayi ya shiga,ta dago ta kalleshi, Wai dawowa kayi yellabai ?"eh nadawo,kana nufin har kaje gidan nasu?safna ta kara tambayarsa, Eh naje amma security's sun hanani shiga sunce bazan samu ganinta ba, Dan allah ke kije ki kai ma ta wannan ta kardan tasa hannu saboda ina so zan koma Dubaï gobe,dan dama ba dan itta ba ma da tuni na dade da barin kasar nan dan haka ke kije nasan bazasu hanaki shiga ba,yana kaiwa nan ya ajiye mata wata ta karda a gabanta hade da juyawa ya bar office din, Habib na fita safna ta kira afiya ta fada mata yanda sukayi da Habib,tace ta kawo mata ta kardan,toh safna tace ta shiga hada kayanta,dama kuma lokacin tashin ta"yayi saboda 4 har ta dan wuce" Tana fita ta tari a daidaita ta fada masa inda zata suka wuce" Yana cikin mota yaga santa ta fito ta tari a daidaita ta hau,dan haka shima yayiwa motarsa key ya soma bin bayansu, *Hotoro* Sauka tayi ta mikawa mai a daidaita kudinsa ta karasa bakin gete din knocking ta shigayi ba'a wani jima sosai ba,mai gadin data dauko yazo ya bude mata karamin gete din, Gaisawa sukayi ta wuce ciki,kuma dama afiyan ta fada masa zatayi bakuwa kuma ta nuna mata honton bakuwar, shiyasa safna na zuwa bata wani sha wahala ba ya barta ta shiga, Tun lokacin data dauki mai gadi ta ce mai karya kuskura ya dinga bude kofah ba tare daya sanar da itta ba, Kuma in zatayi bakuwa itta ma tana gaya masa,kuma tana nuna masa hoton bakon da zaixo! Saukowa yayi daga cikin motar ya nufi gete din gidan, Lokacin Kuma mai gadi na kokarin rufe kofah,kara sowa yayi _yayi sallama mai gadi ya amsa cikin sakin fuska,wai shi dole yaga balarabe, Yellabai kana bukatar wani abu ne"eh ina bukatar ganin matar gidan nan, Gaskiya a'a yellabai kayi hakuri amma bazaka iya ganin kowa ba, saboda bata fadamin zuwan ka ba, mai gadi ya fada yana kokarin rufe karamin kofar, Dakata wllhy in har ka rufe kofar nan har da kai zan hada na kama Habib ya fada yana hade rai, Mai gadi najin haka ya fasa rufe kofar da yayi niyar yi, Haba yellabai kana nufin kai dan sanda ne ?"eh ni dan sanda ne kuma in har baka barni na shiga naje nayi bincike a gidan nan ba toh kaima baka da gaskiya kamar yanda mutanan gidan suma basu da gaskiya, Kana nufin a kwai wani abu da suke boyewa yellabai?"kwarai kuwa kai baka gano wani abu ba?" Kwarai Nagano yellabai ! saboda kwata kwata babu wanda yake zuwa wajanta,saboda ni zan iya cewa ma tunda ta daukeni aiki ban taba ganin wani ko wata ya taba zuwa wajanta ba sai yau,kuma ni banyi tunanin komai ba sai yanzu da kayi magana, Good dan gari,dan haka bani hanya na wuce"da sauri mai gadi ya bawa Habib hanya ya shiga,shi kuma ya maida kodar ya rufe, Safna na shiga ta tarar da itta zaune a palo, daga itta sai wani dan karamin riga data saya mata iya guiwa, kanta babu ko dan kwali,idonta na kan TV amma a za irin gaskiya ba kallon take ba,sai rafka sallama safna take tayi amma afiya bata amsa ba, Shigowa palon yayi ya saya bakin kofah ya harde hannayensa waje daya yana kallon ikon allah, Ya kalleta ya kalli safna da take ta faman sallama amma bata jita ba, Kallo daya yayi mata ya gane tana cikin damuwa sosai dan har rama ta danyi, Sallama yayi da karfi daya saka daga afiya har safnan juyowa suka zuba masa ido, Wai bima kayi ?"safna ta fada tana kallon Habib dako motsawa baiyi daga inda yake ba, Shikenan yau kam aunty Afiya zata tireni daga....bata karasa a bunda tayi niyar fada ba taga afiya ta mike da gudu ta nufi wajan Habib batayi wata wata ba ta fada jikinshi,tare da sakin kuka mai sauti, Baki da hanci safna ta bude ta shiga kallon ikon allah, Shima dai daskarewa yayi a wakan,yama kasa runkumarta shikam dan har yanzu hannunsa na harde da dayan Amma dai yana jin kukanta har cikin tsakiyar kanshi, Jin ba dena kukan zatayi ba ne, yasa shi rungumarta shima,hade da shafa bayanta" Ganin ba dena kukan zatayi bane yasa shi dagota"ya sa hannayen sa duka biyu ya rike kuma tunda, Idonsu ne ya sarke cikin na juna,bata dauke idonta ba haka zalika shima bai dauke nasa idanun ba" Bube baki tayi da niyar ci gaba da kukan da takeyi, ya dakatar da itta ta hanyar rufe mata baki da daya daga cikin yen yatsunsa"shiiii ya fadi a lokacin da yen yatsunsa ya sauka a bakinta, Shiru tayi kamar anyi ruwa an dauke"......, *Sakeena ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...*✍️ Page 19&20 Free book Bismillahi rahmani rahim *********shiru nayi kamar anyi ruwa an dauke"share mata hawaye ya shigayi yana yi yana kallon ta"itta ma haka kallon shi takeyi,lolaci daya kuma sai ta dauke idonta daga kallonsa da takeyi ! Kallon gefensu yayi ya ga safna saye har yanzu ta zuba musu ido,itta ma afiya kallon inda yake kalla tayi idanuwanta suka sauka akan safna dake saye amma yanzu kam ta dauke kai daga kallon su da takeyi, Zare ido waje afiya tayi,lokaci daya ta fara zare cikinta daga cikin na habib amma yaki bata dama sai ma ja ta da yayi a jikinsa ya rungume sosai, Suna hada ido dashi ta dalla mai harara sannun ta maida kanta inda safna take saye, Kiyi hakuri safna "babu komai aunty,ga takardan da zaki saka hannu,safna ta fadi tana ajiye talardan a kan dan karamin teburin dake sakiyar palon,ni bari na tafi yamma tayi sosai ankusa kiran sallar magriba,safna ta fada hade da juyawa ta soma tafiya, Safna kisaya in Mr H zai tafi sai ya ajiyeki tunda yamma tayi sosai, Sayawa safna tayi ba tare data juyo ba,tana jiran taji amsar da Habib zai bayer ! Kinga ba tare muka zoba kiyi tafiyar ki kawai,ya fadi yana hada rai,suna hada ido da afiya wani irin kallo yayi mata da ya sa hanjin cikinta kadawa, Safna kuwa tana jin haka ta tafi ! "Muje mu zauna,ya fadi yana tsare ta da idanu, Kamar zata ce wani abu amma ganin kallon da yake mata ne yasa tayin shiru ba tare ta tace komai ba"ta wuce kan kujera ta zauna, Shima zama yayi gefenta,ya zuba mata ido kamar zai cinyeta" Afiiii !ya kira sunan ta"uhumm ta fadi,ina son jin labarin ki,dan na dade da fuskantar kina cikin damuwa"tun sanda nake Dubaï in muna waya ban taba jin kina farinciki da walwala kamar kowa ba, Ina shiga mutane sosai, sakamakon hakan ne in mutun yana farinciki ko akacin haka duk ina ganewa ko da kuwa bana ganinshi,amma in har nayi waya da kai naji muryar ka toh ko yaya ne ina fahimtar hakan, Ya fadi hade tayi mata wani irin kallo data rasa gane kona me,ga kuma wani abu da take gani a cikin kwayar idon nashi" Ina yau darata kawai idanuna suke min, Ta fadi a ciki zuciyarta lokaci daya kuma ta dauke kai daga kallon sa da takeyi, Tun kafin mu hadu na yadda da kai yaya habib,yaji da fadi,humm yau kuma na tashi daga mr HMH din na koma yaya kenan?"ya fadi yana sakin wani irin murmuchi, Eh ko baka so?" A'a Kawai yace ba take daya kuma ce komai ba, Yau kuwa zaka san ko ni wacece"ni ba kowa bace illa karuwa wacca tagama zubar da mutuncinta a titi ba tare da Aur....bata karasa ba taji saukar mari tas!tas!! har guda biyu a kan kuncinta" Dafe wajan tayi,hade da dagowa,idanunta ne ya sauka akan na Habib da idonshi ya canza kala zuwa ja,kallo daya zaka masa ka fahimci maganar da tayi ba karamin bata masa rai yayi ba, Baki da hankali ne ?"ta yaya zaki kira kanki da karuwa kar na garaji,ya fadi,da gaske nake yaya habib ni karu...marin data sakeji ya kuma wanka ta dashi ne ya sata yin shiru ba tare data karasa ba, Wani irin kuka ta saki,lokaci daya kuma sai yaji tausayinta ya kamashi,dan haka baiyi wata wata ba ya rungumeta yana shafa bayanta, Sai daya bari tayi shiru sannun ya dagota, sorry afiiii I'ma so sorry kinji,raina ne ya baci,bana so kina hada Kanki da wayen can mutanen, Kai kawai ta iya gedawa tana sauke ajiyar zuciya, Oya bani labarin ina jinki, Yaya Habib labarin na deyewa zaka iya kai dare anan ka bari gobe sai ka dau na baka" A'a ni yanzu zaki bani dan ina so zan koma gobe ne" Toh ta fadi hade da gyara jamanta da tayi a kasa dan tun dazu ta koma kasa, *Labari* Alhaji abubakar dan kasuwa ne"kuma babu laifi yana da kufi dai dai gwargwodo, allah yayiwa mahaifiyarsa rasuwa a yayinda take haihuwa,shiyasa malam iro ya dauki abubakar ya dam kashi a hannun Matar wani babban abokinsa mai suna sulei kasan cewa su allah bai basu haihuwa ba, Shiyasa a lokacin da malam iro ya basu abubakar sunyi murna sosai, Abubakar na da shekara 10 Allah ya bawa matar sulei ciki, murna a wajan sulei ba'a magana, Bayan wata tara matar sulei Faiza ta haihu ta samu da namiji ranar suna yaron yaci suna abdullahi,sulei da matarsa sunyi murna sosai, *Bayan shekaru biyar* Saura shekara daya abubakar ya kammala secondary ya shiga jamiya, Ana haka ne allah yayiwa malam iro rasuwa,watoh mahaifin abubakar,kasan cewa tun lokacin da allah yayiwa matarsa afiya rasuwa ya kamu da ciwon zuciya, A yanzu haka ma ciwon ne ya kasheshi, Abubakar yayi kuka yayi kuka har ya gode allah, Bayan kwana arba'in, abubakar ya fara ganin rayuwa,kuma dama tunda suka haifi abdullahi suke nuna babbanci a sakanin su,amma na yanzu yafi,dan tun lokacin da allah yayiwa mahaifinsa rasuwa,yake ganin a bubuwa,dan abdullahi zaiyi ba dai dai ba,amma yana yin magana ko kuma ya danyi mai fada toh a kansa zasu sauke,dan ranar ko abincin baza'a bashi ba,a haka dai yake rayuwa a gidan yau dadi gobe kuma akasin haka. Bayan abubakar ya kammala secondary Komai na sakamakon shi yayi kyau,bayan yayi wa sulei maganar shiga jamiya ne,yace shi bashida kudin da zai saka shi jamiya da abubakar yace ba akwai kudin gadona ba,ka biya min dashi mana,ai yana fada mai haka,ya dinga masifah a karshema cewa yayi ya cinye kudin bazai bayer ba, Maganar ba kara min kona ran abubakar yayi ba?"dan haka ya yanke shawara barin gidan, Kasan cewa akwai wasu kudi da yake dan tarawa,saboda ranar da babu makaranta yakanje kasuwa ya kula da shagon wani mutun,in an tashi sai ya biya shi dari biyar,wataran in anyi ciniki sosai ma har dubu daya yake biyanshi, A haka dai har ya tara kusan dubu goma, Da daddare bayan kowa yayi bacci,hada kayansa yayi ya dauki kudin ya bar gidan, Washe gari su sulei da matarsa suna tashi sukaga babu abubakar babu labarinsa, Basu wani damu da tafiyar shi ba,dan cewa ma sukayi sun yedda danyen mangoro sun wuta da kuda. Shi kuwa abubakar yana fita,cikin gari ya nufah da farko yayi niyar barin garin sai daga baya ya fasa,yana zuwa cikin gari ya kira wani abokinsa Bashir ya fada masa halin da yake ciki ya tausaya masa sosai,duk da kuwa shima mahaifiyarsa bata raye,sai mahaifinsa,ce dai matar mahaifin ta takura masa,amma hakan bai hana shi taimakon abokinsa ba, Zuwa yayi ya daukesa suka wuce gidansu,suka kwana a dakinsa da shi,washe gari ya gayawa mahaifinsa a bunda ke faruwa,yace ba komai babu mas'ala zai iya zama,matar mahaifinsa najin haka tace hakan bazai taba yuwa ba,ta yaya zata dinga kewar samari har guda biyu kamar wayen nan ta fadi tana nuna su da yen yatsa, Kai in kaga yanda take sai ka dauka sunyi shekara talatin,nan kuwa ko shekara ashrin basu kai ba, A haka dai abubakar ya bar musu gida, Bashir naji na gani babu halin taimakon sa, Yanke shawara kawai yayi daya je kasuwa wajan mai gidan sa,hakan kuwa ta kasance, bayan ya je kasuwa,yace aiki yazo,da mai gidan sa ya gansa da kaya a hannu ya tambayeshi na waye yace nashi ne,kwashe komai yayi ya gaya masa,cewa yayi babu komai zai taimaka masa ya bashi daki a gidan sa kuma dama can bashi da da namiji sai mace guda daya da allah ya basu,dan haka abubakar zai taimaka masa kula da kasuwancin sa" abubakar yaji dadi sosai,dan haka ya shiga yi masa godiya da Kuma addu'oyi kala kala, alhaji Mohseen yaji dadin addu'ar sosai, *Bayan wasu shekaru* Alhamdulillah kasuwanci ya karbi abubakar dan a yan zu haka shima ya buda nasa shagon da taimakon mai gidansa"kuma Alhamdulillah komai yana tafiya yanda akeso dan shagon sai kara bunkasa yake, Dan ba karamin karban sa sana'ar saida a tamfopin yayi ba,dan a yanzu haka babu wanda bai sanshi a kasuwan kori ba, Kuma alhamdulillah ya gama karatunsa na jamiya, Wata rana alhaji Mohseen na zaune a palonsa yer sa fatima wacca aka fi sani da bintu ta shigo palon, Ta samu wuri ta zauna ba tare data gaida mahaifinta ba"ta farayin magana, Baba!ta kira sunan mahaifin nata, na'am yer baba ya akayi?"baba dama ina so kayiwa yaya abubakar maganar auran mu saboda mungama dai dai tawa,nace ya gaya maka yace kunyarka yake ji ta fadi ba tare da jin kunya ba, Allan yer baba alhaji Mohseen ya fadi yana washe baki, Allah kuwa baba, Toh shikenan tashi ki tafi wannan Maganar kamar anyi angama, Cikin murna ta mike ta koma dakinta,ta kwanta ranta fari tas ! Waya ta dauka ta kira wata kawarta mai suna safiya ta fada mata yanda sukayi da mahaifinta,gaskiya kawata kina lokacinki,yanzu baban naki Zaki je ki samu ki sharbawa karya, Ato kawata in ba haka nayi ba fah yaya abubakar bazai taba cewa yana sona ba,ni kuwa kinsa ni tsarai nafi son mai kudi bana son talaka,kuma gashi na samu mai kudin har gida shine zan zauna?"ai ke ma kinsan haka bazai taba yuwa ba, A haka dai suka gama Maganar su sukayi Sallama ta kashe waya, Abubakar yer baba tace min kun dai dai ta,wai saboda kana jin kunya shiyasa bakazo ka fada min ba ka aiko ta, dan haka ina so nan da sati biyu ayi komai a gama tunda ka rigada kagama ginin ka, Tunda ya fara magana kai abubakar yake a kasa har ya kai karshe,a zuciyarsa kuwa cewa yayi yaushe mukayi haka ni da yarinyar nan ?" A fili kuma murmuchi yayi hade da fadin toh baba zanyi duk a bunda kace, *Bayan sati biyu* Anyi bikinsu abubakar da fatima lfy,inda suka tare a cikin rijiyar zaki ! Duk da ba son auren yakewa fatima ba, saboda shi kullun a matsayin kanwa yake ganinta,amma tun lokacin da yaji a bunda taje ta fadawa mahaifinta ya fahimci tana son sa,dan haka shima Kawai ya Maida soyayyar da yake mata a masayin kanwa zuwa masoyiya,suna zaune lfy kuma yana bata kulawa dai dai gwargwodon ikonsa" Sai dai akwai wasu dabi yun da take dashi wanda bata yin haka sai da suka yi aure, Dan kullun yawo take zuwa wajan biki yau tace wannan biki gobe tace wancan biki,ga kuma kudin anko da take yawan tamba yarshi, Ana haka ne ta kwanta rashin lfy suna zuwa a sibiti aka shaida musu cewa tana dauke da ciki har na wata biyu, Ai tana jin haka ta dinga balayi da masifah wai itta yaushe ma tayi auren da zatayi ciki tun yanzu,bayan ko a marci bataci ba? "Itta gaskiya zubar da cikin zatayi,sai da yace in har ta zubar da cikin nan zai sake ta sannun ta hakura, Bayan wata tara ta haifi yer ta mace kamarta daya da mahaifinta,daga kyau da haske duk na mahaifinta ta yo,dan saboda tsabar hasken tama har taso tafi na mahaifinta, Yarinyar na da kyau kin wanda ya rasa, Ranar suna yarinyar taci suna afiya,saboda kyau da Allah yayi mata ne yasa ake ce mata beauty! Nan ma dai fatima tace bazai yuba,ta yaya itta ta sha wahala ta haifi abunta amma zai sa mata sunan mahaifiyarsa ba sunan tata mahaifiyar ba, Ce mata yayi itta ai mahaifiyarta tana raye,shi kuma nasa mahaifiyar ta zasu shiyasa ya saka mata sunan ta,zata tada rigima ya mike ya bar wajan, Haka rayuwa taci gaba da kasan cewa yau dadi gobe kuma akasin haka, *Bayan shekaru 9* Afiya tayi girma dan har an sata makaranta,a yanzu haka ajinta shida a primary, Fatima kuwa har ta tire rai samu wani cikin, Wata rana ranar laraba,tun safe take kwance batada lfy,dan haka daukar ta yayi ya kaita a sibiti suna zuwa aka shaida musu cewa tana dauke da juna biyu na sati uku,murna awajan fatima ba'a magana,dan bakara min Mamaki abubakar yayi ba,dan ya dauka zatayi irin wancan cikin ne,sai kuma yaga akasin haka, Bayan suna yaron yaci suna Mohseen wato sunan mahaifin fatima, A haka rayuwa taci gaba da tafiya, *Bayan shekara 10* Alhamdulillah afiya tagama makaranta a yanzu haka tana nemon aiki, Mohseen kuma yana aji uku a secondary, Wata rana da daddare aka kira baban mu aka shaida masa cewa shagonsu ya kama da wuta,abun mamaki amma yana zuwa ya tarar iya nashi ne kadai ya kama da wutan, Kasan cewa a kasuwa yake ajiye komai nashi,har ma da sauran kufin duk yana ciki dan ya kwashe kudin gaba daya dake banki ya taho dasu kasuwa,da niyar gobe idan Allah ya kaimu zai tura Legos a kawo mai kaya, Da ya fadawa mamar mu ba karamin kuka ta sha ba dan kadan ya rage ta haukace" Saboda mama Allah yayi ta da shegen son kudi, Sakamakon a bunda ya farune yasa abban mu kamuwa da jiwon zuciya! Yau lfy gobe ba lfy,kullun zuwa a sibiti,kudin dake hannun mu sai da yakare duka, Ya kasan ce a bincin da da zamuci ba gagarar mu yake, Gashi kuma iyayen mama sun rasu tun shekarun baya da suka wuce, sakamakon gobaran daya tashi a gidansu da daddare suna bacci, Mamace takalleni wata rana tace min bataga anfanin karatun nawa da nayi ba in har zan zauna a gida na zubawa mahaifina ido bashi da lfy, A haka dai na shiga nemon aiki kullun in na fita bana dawowa sai da magriba, In na dawo nacewa mama ban samu aiki ba tayi ta zagina tace min bani da tausayi,ni da nake da wannan kyau amma shine zan iya barin mahaifina a kwance a haka,ba tare da na samo mafita ba" A haka dai nake fita ba tare da na biye mata ba, Wata rana naje wani kanfani,bayan na sha whala ne aka barni na shiga, Wani babban mutun ne mai kimanin shekaru 60 dan kallo daya nayi masa ma na gane zai girmi mahaifina, Tunda na shigo yake bina da kallo har na karasa inda yake,kujera ya nuna min dana zauna zama nayi ya mika hannu ba tare da yayi magana ba,fahimtar danayi takardu na yake nufin na mika masa ne yasani dora mai takardun a hannunsa, bayan yagama duba ta kardun ne ya dago cikin murmuchi yake kallo na,hade da mika min hannusa alamun mugaisa,ban dauki komai ba kasan cewa ya girmi mahaifina, yasa nima na mika mai hannu muka gaida, Hade da saida min cewa ya bani aiki a masayin pA dinsa nayi murna sosai,ina komawa gida na fadawa mama na samo aiki itta ma tayi murna sosai da jin labarin, Kasan cewa kanfanin babbane, Washe gari na fara aiki, *Bayan wata uku da fara aiki* Kasan cewa ina zama dashi sosai dan haka babu wani labarin daya shafi gidan sa wanda bansa ni ba,dan baya boye min komai,har ma da haihuwan da bai samu ba,na tausaya masa sosai,na kuma kwantar mai da hankali, Wasa wasa shakuwa sosai ta kullu sakanina da alhaji jabir,wato mai gida na,akwai wata rana da yace yana sona naki amincewa a karshe ba bar masa office din nayi na koma gida, Bayan na koma gida nake gayawa mamana,tayi min fada sosai akan kin amincewa da banyi ba,a karshe ma dena min magana tayi gaba daya,sai da tayi kusan kwana uku bata min magana, Dana rasa mafita kawai naje na sameta nace mata na amince, Ranar ba kamin murna tayi ba,dana je na cewa Alhaji jabir na amince, murmuchi yayi yace dama yasan zan amince,dana tambayeshi dalili yace ai yaje gidan mu ya samu mama akan maganar kuma ya bata kudi masu yawa, Naji babu dadi sosai,amma daga baya kuma na sake dashi,shakuwar mu ta kara karfi, Ana hakane wata fatiya ya taso masa, dan haka ya nemi dana rakashi,nace ni gaskiya bazan jeba,ba karamin fushi yayi ba a karshe ma dena min magana yayi, Kasan cewa nima yanzu na kamu da soyayyarshi sosai dan haka na fadawa mama mama tace na rakashi babu komai,ta kuma karfafa min,gwiwa sosai,da nace zanje na fadawa abba na shine ta hanani,tace wai nayi tafiya ta kawai ba sai nayi mai sallama ba,Dana tambaye ta meyesa bata son nayiwa abba na sallama bayan kuma aiki ne zai kai ni can din dan Allah ta barni naje nayi mai sallama,amma ta nuna bata so wai babana bashi na lfy ta yaya zanje nayi mai sallama in har ta isa da ni toh karna kuskura nayiwa abbana sallama,a haka dai na hakura na tafi ba tare da raina ya so ba, Bangaren alhaji jabir ma hakan ce ta kasan ce"dan kuwa shima bai fadawa matarsa tafiyan da zamuyi tare ba,fada mata kawai yayi akwai wani aiki da zaije yayi amma bazai wuce kwana biyar ba zai dawo, Kasan cewa ta yedda da mijinta sosai,dan haka allah kiyaye tayi masa, Sannun ya hau mota ya funi inda mukayi dashi zamu hadu,yana zuwa wajan na shiga mota muka wuce, Abun mamaki sai naga ma inda zamuje aikin cikin WUDIL ne Ashe, dan haka na dan samu nitsuwa,saboda nasan ko ba komai ina kusa da kano, A wani katon gete ne yayi hone mai gadi ya zo ya bude mana gete ya chusa hancin motarsa ciki, Sannu da zuwa mai gadi yayi mana alhaji jabir ya amsa Cikin sakin fuska, Wani nagani ya kara fitowa,yayi mana sannu da zuwa hade da dauko kayan mu ya wuce ciki dashi muna binshi a baya, har muka shiga cikin palon gidan, Yellabai ya banga mutanen da zamuyi aikin tare da su ba ne nambaya ?"haba baby ki kwantar da hankalinki zasu zo amma sai zuwa gobe,wannan gida nane dan haka ki saki jikinki, Shiru nayi sai ido Kawai da nake binshi dashi, Janyo ni yayi ya kamo hannuna muka shiga cikin daki, toilet ya kaini ya hada min ruwa mai zafi yace nayi wanka,sannun ya fito ya barni, Wanka nayi na fito bangan shi ba,dan haka ina gama shiryawa na fito palon na tarar dashi zaune Shima da alama bayan fitarsa daga toilet wanka yaje yayi,dan naga ya canza kaya zuwa kaya mara nauyi,zaune yake akan dinning table ga wannan mutu min da ya shigar mana da kayan mu dazu na gyera abinci akan dinning din,da alama mai aikinsu ne" Yana ganina ya mike yana murmushi nima murmuchin nayi masa,na karaso inda yake,kujera ya jamin na zauna,mai aiki zaiyi serving dina ya hana,shi ya zuba min a binci sannun ya zuba nashi muka soma ci,yana ci yana kallon na,har muka gama,lemon daya zubo tun kafin nazo ne ya dauko ya miko min,karba nayi hade dayi masa godiya,kallon lemon na shigayi dan ni tunda nake ban taba gani irin shi ba,dan kurba nayi na hadiye ina dan yatsine fuska,baby ya dai?"gaskiya lemon na da gas deyewa gaskiya nikam bana son lemo mai gas deyewa na fada ina ajiye lemon, Saurin karba yayi ya samin a baki,hade da cewa haba baby kin taba zama da na miji gida daya tunda kike?"kai na na girgiza alamun a'a,toh dan haka yau kawai zaki sha lemo mai gas kinji,kai na geda oya bude bakin ki na baki da kai na,baki na na bude ya shiga bani sai dana sha kusan rabi sannun ya kyaleni,ban fi minti biyar da sha ba,na fara jin wani irin sha'awa,ga marata dake da daya daure,yana ganin haka ya saki murmuchi hade da dauka ta can ya nufi daki dani,muna zuwa daki ya kwantar dani kan gado,hade da yimin runfah ya shiga kissing dina nima ina ganin haka na shika mayar masa da martani,ga marata da yake kara min tauri da ciwo, Muna cikin haka ne naga ya mike wayarsa ya dauka ya danna wajan yin video sannun ya ajiye,ya dawo wajena, ina ganin shi ya karaso,da sauki na mike na zauna kan gadon sai rike mai wando nake,dan maganin ya rigada ya fara aiki sosai,a lokacin babu a bunda nakeso sama da namiji so kawai nake inji an shigeni amma shi kuwa yaki bani hadin kai sai ma mai dani kwance da yayi yaci gaba da kissing dina sai da yayi mai isar sa sannun ya shigeni,wani irin kara na saki zan mike ya mai dani, Wani irin kuka ta saki hade da juyowa ta kalleshi,idonsa yayi jajur kamar wutan garwashi, yaya Habib ranar ne daya dauke min mutunci na da na nake ta a danawa yaya Habib bazan taba mantawa da wannan mummunar ranar ba,ta fada hade da sakin wani irin kuka mai suma zuciya rungumeta yayi Yana shafah bayanta,ga hawaye da yake saukowa daga idonsa shima......, *Sakeena ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 21&22 Free book Bismillahi rahmani rahim **********Rungumeta yayi ya shiga shafa bayanta,ga hawaye da yake saukowa shima daga idonsa, okay sorry my Beauty, kici gaba"dan na tabbata ba nan ne karshen labarin ba, Yaya dare fah yayi kaga ana kiran magriba,ka tafi in yaso gobe da safe kafin jirgin ku ya tashi kazo na karasa maka, Dagota yayi daga rungumar da yayi mata,yana noke kafada,hade da turo baki gaba kamar karamin yaro"badan yanayin da take ciki ba da babu a bunda zai hanata yin dariya!duk da haka sai data saki kyekkyawar murmuchi daya sa dimpil dinta lotsawa, Baki sake yake kallon ta dan bai taba ganin tayi murmuchi ba sai yau,da yaga tayi yanzu sai yaga ta kara masa kyau sosai,ba dan mutane na cewa yana da kyau sosai ba,da babu a bunda zai hana shi cewa afiya tafi shi kyau, duk da haka kuwa tafini kyau a wajena,ya fadi yana lakutar dogon hancinta, Oya ina jinki ci gaba,in ba haka ba kuma in na tafi bazaki sake ganina ba,ya fada yana kallon ta" Ci gaba da bashi labarin tayi, Ina kuka ina tureshi amma ina baya hayya cinsa ma ballanta na yasan ina yi,sai ma sumbatun da yake tayi,duk ya cika gidan da ihu dan na tabbata har mai aiki da mai gadi duk sunji ihun,tun ina kuka ina tureshi har karfina ya kare,kukan ma daga baya na nemeshi na rasa, shikuwa bashi ya dagani ba har sai daya samu nitsuwa,sannun ya dagani ya shiga bani hakuri amma ina banza ma nayi masa"hannu yasa zai daukeni ya kaini toilet yayi min wanka nasa hannu ta tureshi da karfin data rege min ya fadi kasa,ina ganin haka na mike da niyar zuwa toilet sai naji wani irin zafin da ban tabaji ba na dingaji a kasata,koma wa nayi na zauna kan gadon hade da sakin kuka mai suma zuciya, A karshe dai shi din ya daukeni ya kaini toilet din ya sakani a ruwa zafi,ina ihu da kuka da komai amma bai kyaleni ba har sai daya ga na dena kuka in ya sakani a cikin ruwan zafin sannun ya dagani ya nadoni a tawal ya kara daukoni ya fito dani,ya kaini daki ya kwantar dani ya lullubeni da bargo,nidai sai binshi kawai nake da kallo in kagan shi baza ka taba yedda zai aikata a bunda ya aikata min ba, In natuna a bunda yayi min sai inji na saneshi sosai,yanzu shikenan duk wanda ya aureni a matsayin yer iska zai dinga ganina, Ina nan kwance ina tunani tunani har ya fito ya tarar dani,sallaya ya shimfida ya tada sallah kamar gaske,a zuciya ta kuwa fadi nake ka gama yin zina da wacca ba muharramin ka ba ka shimfida Sallaya kace kana Sallah, ko ta yaya Allah zai karbi sallar naka oho, Yana idar da sallah ya zo ya hau gadon ya kawo hannunshi da niyar rungume ni,na buge hannunshi,babu rarrashin da bai min ba amma nayi banza dashi,a karshe dai kyaleni kawai yayi ya kwanta, Ina ganin ya fara bacci na mike a hankali,na karasa inda na ajiye jakar kayana,dauka nayi na bude na dauko riga mara nauyi na saka,na yafa mayafina,inda waled dinshi yake nake na bude na dauki kudin da nasan zai iya kaini gida,na ajiye mai sauran, Sannun na bar dakin,ina jin wani irin zazzabi na lillibeni dukda kuwa naji dadi sosai da ruwan zafin nan daya sakani a ciki amma,duk da haka ina dan dingisawa, Ina zuwa palo na bude a hankali na fita,na bar kofar a bude gudun kar ince zan rufe su jini,duk da kuwa ba wai dare yayi sosai bane,dan baifi karfe 9 na dare ba,lekowa nayi naga mai gadi baya bakin gete dan haka na fito da sauri na karasa bakin kofar na budeshi a hankali na fita,nan ma ban rufe ba na bar wajan da sauri, Da sauri sauri nake tafiya ina yi ina dan dingisawa har na karasa bakin titi,dare bai yi sosai ba amma babu mutane sosai a waje, tsiraran mune da ba'a resa ba kawai akan titin, Ina karasa kan titi,duk motan da zai wuce ta gabana sai na tareshi,kusan motoci uku na tara amma sunki tsayawa,gajiya nayi da tara,dan haka sayuwa kawai nayi na zubawa sarautar allah ido, Abun mamaki sai naga wani mota ya saya ba tare dana tara ba, Saukar da glass din motar yayi,wani dan matashin tsaurayi ne nagani a gabana,sanye yake da Kayan sojoji,ina ganin haka kafin ma ya bude baki yayi Magana tuni na fado cikin motar,kai kawai ya girgiza hade da tada motar a lokacin dana kammala rufe murfin motar, Bai ce dani uffam ba haka zalika nima bance dashi komai ba, Har munyi nisa cikin tafiya naji yayi magana...ke haka akeyi baki san mutun ba ki fada mai cikin mota,yanzu misali in na kasance mai tsatar mutane fah,yayi magana yana hadarai, Shiru nayi kamar bazan bashi amsa ba sai kuma nace..ba gwara a sace mutun a barshi da mmutuncinsa ba,akan ayi masa fiyade, Baki bude yake kallo na,a zuciyar sa kuwa fadi yake wa akayiwa fiyade, Kamar zai share maganar sai kuma yaga a matsayin sa na soja mai kare hakkin dan adam bai kamata yayi shiru ba,dan haka baki ya bude ya soma magana, Baiwar Allah naji kin ambaci zancen fiyade wa akawa fiyaden? Ni akawa,ta fadi ba tare da taji wani abu ba, Kefah kikace,sojan ya tambaya,kwarai kuwa dan ko Awa daya batayi ba,kaga kuwa ni gwara ma a sace ni ko kuma a kasheni yafi min sauki,dan bana bukatar na ci gaba da rayuwa,gwara kawai na mutu,a dena ganina,ta fadi hawaye na taruwa daga idanunta, Me sunan wanda ya aikata miki hakan, jabir Abdul Rahman,zaro ido waje sojan yayi,hade da fadin, gaskiya zai iya aika tawa, kamar ya soja bangane zai iya aikatawa ba?dan mahaifinsa shine ambassador, kuma kowa ya daura mai gindi dan haka bazaki iya yin komai ba,gwara ma ki hakura da dukkan a bunda ya faru ki barshi da allah, Gaskiya soja ka bani mamaki ashe ma wannan kakin dake jikinka a banza ne,tunda har bazaka iya taima kawa wanda aka zalinta ba,ka sauke ni nagode, Ina saka hannu da niyar bude kofar,yana ganin haka yayi saurin yin parking,sauka nayi na shiga tafiya kasan cewa mun shiga cikin kano kasan cewa basa bacci da wuri yasa akwai mutane sosai a waje,a daidaita na tarar na fada masa inda zai kaini sannun na hau, Wayar mama na kira tana dagawa nace mata ina waje tazo ta bude min kofah,mikewa mama tayi zata fita,kallon mama abba da idonsa yake biyu yayi yana fadin ina zakije kuma fatima,inda inda mama ta farayi kana ganinta kasan bata da gaskiya,amma ta dage tace,motsi nakeji abban afiya zanje na duba nagani,kai kawai ya geda ta fice da sauri, Tana fita cikin dakin sai data saya ta sauke ajiyar zuciya sannun ta nufi kofar fita,tana bude kofah tagan ni saye duk na fita daga cikin hayyacina,kallon sama da kasa ta shiga min,nidai ina ganin haka nabi ta gefenta na wuce ciki,dan itta kanta haushinta nakeji, Da kallo ta bini dashi har na shiga cikin gidan, Yanayin yanda mama taga tafiya ta ne,yasa ta yin wani tunani,da sauri ta rufe kofar gidan ta wuce ciki itta ma,lokacin tuni na shiga dakina na saka sakata, Taba kofar tayi tajita a kulle,sai Kawai ta wuce nasu dakin,dan tasan tsarai in tace zatayi knocking dole abba yaji ta, *Washe gari* Knocking naji anyi amma naki budewa,sai da naga ba dena knocking din zatayi ba sannun na mike daker,dan har yanzu zazzabin bai tafi ba, Bude mata nayi ba tare dana kalli inda take ba,na koma na zauna, Waje ta samu itta ma ta zauna,sai data kare min kallo saf sannun ta fara magana, Afiya ya naga kin dawo jiya da daddare,ba alhaji yace sai nan da kwana biyar zaku dawo ba ?" Kinga mama dan allah dan annabi ki kyaleni naji da a bundake damuna,tunda kin taimaka masa ya cimma burinsa da yakeso a kaina, gaskiya mama son kudinki yayi yawa ki rade dan allah,na fada hade da hada hannayena biyu alamar roko, Koma meye faru karki kara cemin haka saboda ni mahaifiyarki ce ko kina so ko bakiya so,wllhy idan kika sake cemin haka ranki zaiyi mummunar baci nagaya miki,tana kaiwa nan ta mike a fusace ta bar dakin. Bayan ya tashi da asubaha yaga bata kan gadon a tunaninsa ya dauka tana toilet,yana nan zaune har kusan mintuna talatin bata fito ba, mikewa yayi ya nufi bakin kofar toilet din,ya kasa kunne ko zaiji karar ruwa amma shiru,dan ya dauka ko wanka takeyi ne, Jin shiru ko motsin bai ji ba ne ya sashi turo kofar amma wayam,ai cikin rudewa ya fito palon yana kwallawa jibril mai aiki da mai gadi kira cikin rudewa suka karaso cikin palon suna fadin gamu ranka ya dade,ina baby take,kallon kallo suka shiga yinwa juna,dan basu fahimci waye baby ba,dan matarsa ba baby yake ce mata ba,hajiya yeke kiranta dashi, Wai ba daku nake ba ya sake fadi cikin daga murya, Ranka ya dade bamu fahimci wa kake nufi ba salisu mai gadi ya fada, Mu nawa mukaxo gidan nan salisu,ku biyu yellabai,toh banganta ba shine nace tana ina?" Wllhy yellabai bamusan inda take ba, bamu ganta ba,amma bayan nafito daga bandaki naga kofa a bude, Nima tabbas naga kofar palon nan a bude dazu da zan wuce masallaci s amma na dauka kaine ka tafi masallaci shiyasa ban zo na fada maka ba, Wani irin tsaki yaja,ya juya fuuuu kamar zai tashi sama ya wuce cikin daki,ko sallah da wanka bai saya yi ba,ya saka kaya ya dauki karamin akwatin daya zo dashi da key din motarsa ya bar dakin, Tarar da su yayi saye Har yanzu,harara ya wurga musu ya wuce ya barsu tsaye a wajan, Yana fita daga cikin WUDIL ba kunya ya kira mama,tana dagawa bai ko saya ya gaishe ta ba ya fara magana mama baby ta dawo gida ne,eh ta dawo jiya da daddare,amma ya akayi haka ta faru,wllhy mama tsautsayi ne da kuma irin son da nake mata ne yasa ni aikata haka mama dan Allah ki taimaka kiyi mata magana wllhy ina sonta sosai ina matukar sonta kuma insha Allah nan da ba jimawa ba zan aure ta insha allah,allah da gaske zaka aure ta,eh mama da gaske nake,amma yanzu dai ki fara shawo min kanta tukun,toh karka damu yanzu kuwa zan je na shawo maka kanta,bari naje zan kiraka anjima,toh ya fadi yana kashe waya, Ajiye wayan tayi ta mike ta nufi dakin afiya tana zuwa ta tarar itta da Mohseen da bai dade da dawowa daga makaranta ba,suna zaune, Kai Mohseen bamu waje, mikewa Mohseen yayi ya fita, Zama mama tayi tana washe baki,da kallo kawai na bita dashi, yer Beauty na wutawa akeyi ne,humm kawai na fadi dan nasan bata kirana da wannan sunan sai tana bukatar wani abu, saboda Mohseen da yake sunan mahaifinta ma Mohseen din take kiranshi dashi ballantana ni da nake sunan siruka kawai, Hannu na ta kama ta ci gaba dayin magana kinga Beauty ki yafe masa wllhy yayi na dama yanzu ya kirani yana ta kuka yana fadin wllhy saboda son da yake miki ne yasa yaji bazai iya jiran har sai kunyi aure ba,wa zai aureni din mama? Alhaji jabir mana,yanzu yayi min Maganar aure yace nan da ba jimawa ba zai aure ki,yace ko da wannan abu bai faru ba ma yana da burin son auren ki ballantana yanzu da wani abu ya shiga saka ninku, Naji mama ki tafi zanyi tunani,kin tabbata eh na tabbata yanzu dai ki fita dan har yanzu ina jin zazzabin nan, Wai kina nufin zazzabi kikeyi shine baki fada min ba,humm mama kenan yaushe ma kika saya kika saurareni da har zan gaya miki, Shikenan naji bari naje na samo miki magani,bata saya jin a bunda zance ba ta mike ta fita, Tana fita na mike naje na kulle kofar dakina na dawo na kwanta, Mama kuwa tana fita ta kira Alhaji jabir ta fada masa yanda mukayi da itta yace gashi nan zuwa yanzu zai kawo min maganin,sannun ya kashe wayan, Kasan cewa yana hanya bai karasa gidan shi ba, yasa shi juyar da hancin motarsa zuwa wani pharmacin,magani ya siyo min sannun ya wuce gidan mu,yana zuwa yayiwa mama waya ya fada mata yana kofar gida,kallon inda abba yake kwance tayi taga yana bacci bai tashi ba har yanzu baccinsa yake,dan haka ta mike ta wuce kofar gida tana fita ta hangoshi cikin mota, alhaji jabir na ganinta ya sauko daga cikin motar ya wuce wajan ta, gaisawa sukayi,bayan sungama ne , yake ce mata ga maganin ko zan iya shiga,eh me zai hana,shiga tayi yana binta a baya har suka karasa bakin kofar dakin na,taba kofar mama tayi tajita a kulle,dan haka ta shigayin knocking,jin shiru ne yasa ta yin magana, Afiya nasan kina jina ki bude kofar nan ko Kuma na karya kofar nazo na sameki a ciki naci ubanki, Haba mama kiyi a hankali mana kaga alhaji ka kyaleni kawai dan bakasan halin wannan yarinyar ba,akwai ta da taurin kai akan abu, Jiki a sanyaye nazo na bude kofar,ina ganin jabir sauri nayi na rike kofar da niyar kara rufeta sai mama tayi magana... Allah kina rufe kofar nan sai na tsine miki,yanzu mama saboda wannan dontijon banzan ne zaki ce zaki tsine min?"kwarai kuwa ki rufe kigani,shiga alhaji,kai kawai alhaji jabir ya geda,sannun ya shiga dakin,barin dakin nake kokarin yi sai mama tace in har kika fita kika barshi shi kadai ko kika ki sauraranshi toh shima sai na tsine miki, yanzu dai sai ki zaba tsinuwa ko tafiya,tana kaiwa nan ta bar bakin kofar, Komawa nayi na zauna gefen katifar tawa hade da juya mai baya,tashi yayi yazo ya durkusa a gabanna ya shiga bani hakuri, Baby wllhy na tuba dan Allah ki bani dama ta biyu wllhy zan gyara a bunda na bata,dan Allah ki taimaka min,in har kana so na yafe maka toh ka bani na fada ina miko hannu,mai zan baki baby?"mutuncina daka karbe nakeso ka mayarmin dashi in har ka mayer min dashi toh ni kuma nayi maka alkawari yanzu yanzun nan zan yafe maka kuma mu koma kamar yanda muke a da, Bazan iya ba baby amma nayi miki alkawari zan aure ki nayi miki alkawari in har kin yafe min zanje na fadawa magaba tana su zo a nemamin aurenki, Kaga malam baza ka yimin dadin baki ba fah, Ina kaiwa nan na mike da niyar barin dakin sai naga mama saye a gabana, Kin kyauta mara kunya,yanzu mama saboda wannan dontijon banzan ne kike cemin mara kunya, Anfada miki mara kunya ai dama nasan zaki aikata haka shiyasa na dawo,allah ya tsi bata karasa ba taji an rufe mata baki tana dagowa idanunta suka sauka a kan na Mohseen,haba mama dan Allah ki dena haka,lafiyayyan mari ta dauke sa dashi,dafa wajan Mohseen yayi yana kuka, Kallon yayarsa yayi ya fara magana kinga aunty Afi kiyi mata a bunda takeso kawai ku rabu lfy, Mohseen na kaiwa nan ya bar dakin ba tare daya sake kallon inda mama take ba,mikewa alhaji jabir yayi jiki a sanyaye,yana fadin mama kiyi hakuri laifina ne,amma gaskiya bai kamata ki dinga yin haka ba,yana kaiwa nan ya juya da niyar barin dakin yaji mama na cewa...wllhy in har bakiyi a bunda na umarceki har ya fita ba Afiya toh wllhy sai na tsine miki, Tana kaiwa nan tajuya ta bar dakin, Na yafe ma yaji ta fada, Juyowa yayi ya zuba mata ido,yana son ya karajin a bunda kunnuwansa suka jiye masa,amma baiga alamar zatayi magana ba, Karasowa yayi kusa da itta yana tambayarta..baby kin yafe min eh nayafe maka,amma dan na yafe maka ba wai ina nufin zan aure ka bane, Toh ba komai baby a hakan ma nagode,yana kaiwa nan ya juya ya bar dakin, *Bayan wata biyu* Afiya taci gaba da zuwa wajan aiki,amma sai da mama tayi da gaske sannun taci gaba da zuwa, dan kudaden take cikin account dinta sun kusa karewa,ga kuma aikin da akace za'a yiwa abba dan kodanshi guda daya ta lalace,dan a yanzu haka ma yana kwance a sibiti, Gashi nima kaina bana jin dadin jikina,dan haka ina fita daga cikin dakin da aka kwantar da Abba na,na nufi wajan likita, knocking nayi na shiga,bayan mungaisa da itta ne nake fada mata a bunda ke damuna,ga kuma rashin yin al'ada da banyi ba har na sawon wata biyu, Tes din jini tamin,dubawa tayi ta shiga kallo na cikin mamakin daya kasa boyuwa akan fuskarta,ni dai dana gaji da kallon ne na shiga tambayarta.. dr lfy,na dauka ke budurwa ce ?", eh ni budurwa ce"amma meye faru ?"sakamakon gwaje gwajen da nayi miki ne ya tabbatar min da cewa kina dauke da ciki har na wata biyu, Whatttt, gaskiya a'a a'a dr kar kice haka sau daya aka min fyade to ta yaya ciki zata shi ga bayan sau daya?" Naji ina da ciki amma dan allah dr ki tire min cikin nan bana son shi rayuwata zata lalace,dan allah dr ki taimaka min, shiru dr tayi ba tare da tace komai ba......., *Sakeena ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 23&24 Free book Bismillahi rahmani rahim *********naji ina da ciki amma dan allah dr ki tire min cikin nan bana son shi rayuwata zata lalace dan allah dr ki taimaka min,shiru dr tayi ba tare da tace komai ba, Haba dr ina miki magana kikayi banza dani,yanzu dan allah misali in yer kice da shiga irin wannan halin da nake ciki haka zaki barta ?" In yata ce hana ta tire cikin zanyi,saboda in tace zata tire cikin zai iya yuwa ta rasa ranta,zai iya kuma iya yuwa ta rayu, Yanzu misali idan ta tashi tire cikin ta rasa ranta fah mai zataje ta fadawa allah in ta koma gare shi,kinfi kowa sanin ukuncin wanda ya kashe kansa,da kuma wanda ya kashe wani,kinga zunubi biyu kenan,ko da ace da hadin kanki komai ya faru ma bai kamata ki tire cikin ba saboda duk wanda ya kashe rai shima kasheshi za'ayi, ballantana fiyade aka miki, nidai shawaran da zan baki shine ki bar a bundake cikin cikin ki ya rayu,wata kila in yazo duniya yayi miki maganin irin wayennan mutanen da suke zaluntar yammata,kinga yata ni allah bai taba bani haihuwa ba,ke da kika san kina haihuwa ki daga hannu biyu ki wa Allah godiya,dr hauwa ta fadi tana share guntun hawayen da suka zubo mata, Shikenan dr zanyi kamar yanda kikace kuma na gode sosai da wannan shawaran da kika bani, kuma insha allah bazan taba mantawa dake" ba a rayuwa ta, Saboda bayan mahaifina babu wanda ya taba zaunar dani ya gayamin a bundake dai dai da kuma wanda ba daidai ba,ina kaiwa nan na mike ina share kwallan daya zubo min a kumatu,fatiya na somayi har na kai bakin kofar fita office din sannun na juya na kalleta,tana nan zaune tayi tagumi kana ganinta kasan tana cikin damuwa,kiran sunan ta nayi dr !dagowa tayi tana kallon na, allah ya baki kema yaran jikin sanyin murya ta amsa da "Ameen"sannun na bude kofah na fita na bar office din. Ban koma dakin da aka kwantar da abba na ba,dan nasan in na koma zasu fahimci halin da nake ciki ni kuma bana son hakan ta faru, Wajan aiki na wuce dan ina so naje na fada masa zancen cikin nan dan gwara yasan me abunyi tun yanzu kafin na haihu, Ina zuwa ko knocking ban saya yi ba na turo kofar na shigo,zaune yake yayi shiru yana tunani, Tunda nake ban taba jin ina son mace kamar yanda nake sonki ba baby,ko matata dana aura bana sonta kamar yada nake sonki,tunda muka hadu na dena kula kowa sai ke da matata, Jin budewar kofar da akayi ne yasa shi dagowa ya zuba mata ido,duk sanda ya ganta sai yaji sonta na kara minkuwa a cikin zuciyarsa,ga kuma ranar daya shigeta yaki barin kwakwalwar sa,saboda wannan dadin daya ji,dan zai iya cewa ma tunda yazo duniya bai taba jin dadin mace kamar yanda yaji a wajan ta ba, teburin gabansa dana buga ne ya sashi dawowa daga cikin tunanin daya kara lulawa, Ta kardan dana ajiye a gabansa ne ya sashi kallo na yana jiran karin bayani? Kaga malam budewa zakayi ka karanta,okay ya fadi yana bude takardan,abun mamaki sai naga yayi wani irin murmuchi, ban gama mamaki ba sai da naga ya mike ya ya karaso inda nake ya dagani sama yana juyani kamar ya samu yer tsana, Dukanshi nake a irji amma ya kasa saukoni, Baby wai da gaske ne kina dauke da ciki na,wai da gaske ne baby,kaga malam ka dena tambayata ai ga zahiri nan kagani ai tabbas nagani baby tabbas, nagode!nagod!!e nagode!!!baby ina sonki sosai,da sosai gaskiya ke ta dabance a cikin mata,ke ta dabance a rayuwata,ina sonki sosai,kuma kina haihuwa zamuyi aure,ki kuma haifomin wani yayan,bari ma kiga na kira Dad na fada masa yaje ya tambayam min aurenki Kawai ayi komai a gama kinga kina haihuwa sai kawai muyi aure,barima ki gani, ya fadi yana kamo hannuna yayi waje dani, Ina son yin magana amma yama kasa sayawa ya saurareni saboda murna, Dan haka shiru kawai nayi sai ido da nake binsa dashi,sai da muka shiga mota,sannun na juya na kalleshi nace wai ina zamuje ne haka alhaji ?"Dad zanje na dauko na Kai shi wajan Abba suyi maganar auren mu,saboda so nake yau a gama komai, Wai ka manta abba na a sibiti ne,seda motar yayi a gefen titi,yana fadin..wai kina nufin har yanzu ba'a sallameshi ba?"eh aiki za'a masa shine nake kokarin hada kudin, Haba baby wai meyesa kikemin haka ne,meyesa baki daukeni yanda ni na daukeki bane,meyesa har yanzu kin kasa yafemin ne,kamo hannuna yayi yaci gaba da magana..dan allah baby ki yafe min,haba ba na dade da yafe maka ba,in ban yafe maka ba zanxo inda kake ne,rungumeta yayi yana sauke ajiyar zuciya,wayarsa ne yayi kara,dan haka sakinta yayi ya daga wayan, Hello,banji mai aka ce" a dayan bangaren ba, sai naji yace ohhh good dan Allah kuyi hakuri na manta ne shaf amma gani nan zuwa yanzu,sannun ya kashe wayan,wata number ya Kuma kira ana dagawa,ya fara Magana kamar haka...hajiya zanje wannan meeting din da mukayi magana dazu, zan iya kaiwa dare,dan haka in kin dawo daga wajan aiki kici abincin ki kawai ki kwanta ni sai na dawo,yana kaiwa nan ya kashe wayan, Baby rakani zakiyi muje mu dawo,dan sun kiga da sun je ma,a yanzu haka suna can suna jira na, A'a gaskiya alhaji ni babu inda zani bari ma kaga na sauka,na fadi ina rike kofar da niyar bude shi na fita,sai naji ya rike min hannu hade da rufe kofar sosai,sai daya tada motar ya fara tafiya sannun ya sakar min hannu, Gaskiya ni ka saya na sauka,haba baby ko baki yedda da abunda nace miki bane,ki bari muje ki gani,in ba kowa sai ki dawo, Shikenan wllhy in har na shiga naga babu kowa dawowa zanyi,in kuma ka hanani wllhy a can din zan nemi wani abun da zan sha na kashe abunda ke cikin cikina kowa ma ya wuta, Eh na yedda, shikenan muje,kinga in mun dawo ma daga nan a samu gobe a yiwa abba aikin nan,ya samu ya warke na turo iyayena ayi Maganar auren mu, Taya zakace gobe ayiwa abba aiki bayan ni ban gama hada kudin ba ?"wani irin harara ya dalla min, Shiyasa nace miki baki daukeni kamar yanda ni na daukeki ba, Nidai bance komai ba sai murmuchi kawai da na danyi, Ba wanda ya kara cewa komai har muka karasa can, Ai kuwa kamar yanda ya fada, muna zuwa muka tarar da mutanan a ciki suna jiranshi, Dan haka suka fara meeting din,a zuciyata kuwa fadi nake meyesa bazasu yi meeting din a office ba sai sun zo nan?"da naga dai babu wanda zai bani amsa sai kawai na share maganar, *Bayan awa daya da rabi* Sai magriba suka gama,dan haka yace muyi sallah sai mu tafi,alwala mukayi muka tada sallah, Bayan mun idar da Sallah, Baby ga abinci can da jibril ya dafa mana muje muci kafin mu tafi, a'a Alhaji ni dai gida nake son tafiya, gaskiya ka tashi mu tafi,naji toh tashi muje,kinsan bana son bacin ranki dan zai iya samun dana ma,ya fadi yana mikewa,hannuna ya kamo ya mikar dani,ya daukeni cak kamar baby muka fita,ina ta ce mai ya saukeni amma yaki sai daya kaini har bakin mota sannun ya bude ya saka ni a ciki,shima ya zaga ya shiga,tada motar ya shigayi amma motar yaki tashi,alhaji lfy?ina fah lfy baby mai ne ya kare bari na kira jibril ya je ya siyo maga,dan mai gadi baya nan,kai kawai na geda,shi kuma ya shiga kwallawa jibril kira, ba'a wani dau lokaci ba jibril ya zo, Gani yellabai, yauwa jibril ga kudi kayi sauri kaje ka siyo min mai dan mai ya kare,toh jibril ya fadi yana karban kudin, Baby sauko mu shiga ciki kafin ya dawo, a'a ni bazan je ko ina ba zan jira shi a nan, Babu yanda baiyi dani ba akan na fito mutafi amma naki,a karshe dai fitowa yayi ya zaga bangaren da nake ya bude kofar,kafin nayi magana ya daukeni cak,yana daukata ruwan sama ya sauko da karfi kamar ta bakin kwarya,dama ina son wasa a cikin ruwa sosai a rayuwa ta,dan haka na fara bubbuga kafadunsa alamun ya saukeni amma yaki,wani irin cizo na gantsara mai a hannu a take kuwa ya saukeni hade da fadin washh yana yarfa hannu,bansan sanda dariya ya kubce min ba ina haka ne ya kawo hannu zai kamoni,sai na fara gudu yana bina a baya, har muka shiga ciki na haura can verandar sama sannun ya kamoni da karfi ya rungume ni"kokarin kwace kaina nakeyi amma yaki sakina,dagewa nayi da iya karfina na tureshi,ai a take ya fadi tun daga saman ya fado har kasa, Wani irin ihu na saki hade da saukowa daga matattakalar,ina sauka na karasa inda yake da sauri,zama nayi a gefensa na dago kansa naga jini sai suba yake akan kewarsa"wani irin kuka na saki ina kiran sunan shi amma ina shiru,dan kwalin kaina na tire na daure masa kan,na shiga girgiza shi amma ina shiru,irjinsa na shiga danna wa,sai ya shiga yin tari, alhaji sannu alhaji na fada,kai ya geda min,sannun ya shigayin magana,kiyi sauri kiyi sauri kije ki dauko waya ki kira ambulance azo a kai ni a sibiti kiyi sauri karna mutu baby,bana son na mutu yanzu nafi son sai naga dana tukun kafin na mutu, Karka damu alhaji insha allah zaka ga danka da izin ubangiji, Shikenan naji kiyi sauri toh,kai na geda masa,sannun na mike da sauri na nufi cikin palo,ina zuwa wayata na dauka na shiga kira ambulance din amma ina babu network alkalla na dau kusan mintuna goma ina goda kiransu amma taki da gudu na kuma fita naje na duba shi,naga har yanzu yana numfashi dan haka ciki na kara komawa,kiran mama na godayi amma taki shiga shima,kara fita nayi na koma wurin shi, Na shiga rera kuka, Alhaji wllhy duk na gwada kiransu amma taki shiga, Kinga ki dauko waya ta ki kira matata itta ma likita ce ki fada mata a bundake faruwa, Kai na sake gedawa na koma ciki,wayarsa na dauka na danawa matar sa kira,abun mamaki sai naga ta shiga, Kwance take har ta fara bacci sai taji wayarta na ringing hannu ta sa ta dauki wayan,ganin sunan mijinta yake yawo akan screen din wayan ne yasa ta saurin tashi zaune,hade da daga wayan, Hello ta fada,mai makon taji muryar mijinta sai kuma taji muryar mace, Wacece ke" me kuma wayar mijina yake yi a hannunki ?"kinga madam yanzu ba lokacin yin wannan tambayar bane,kaga alhaji ne ya fado daga bene whatt ya hakan ta faru,kaga dan allah madam ki fara yin wani abu tukun kafin kiyi min wannan tambayoyin, shikenan,ki saurare ni sosai kiji a bunda zan fada miki,shiru tayi ina jin bayanai da matar Alhaji jabir take min har ta kai karshe,sannun tace...jeki yi yanzu zan kara kiranki,kai na geda sannun na kashe wayan,a bubuwan da ta fada mata min ne naje na hada da sauri ta fita wajen da lema,saka mai leman nayi sannun ta shiga shafa masa mai maganin dana hada a keyan nasa,bayan nagama ne na kara daure wajan sannun na sake komawa ciki,narar da wayan ta na ringing,dagawa nayi, duk a bunda kika fada nayi madam ,okay kije ki kula dashi gani nan zuwa yanzu,tana gama fadar haka ta kashe wayan, *Bayan minti arba'in* Tana zuwa cikin tashin hankali ta fito daga cikin mota ta Karasa wajansu" Bamu saya mun karewa juna kallo ba tace na taimaka mata mu kaishi cikin daki,kai na na geda sannun ta rike kafafuwansa itta kuma ta rike kansa muka nufi ciki da shi, Kwantar dashi mukayi akan gado, sannun na fita na bar musu dakin,almakashi ta dauka ta shiga yaga rigar dake jikin sa saboda bazata iya tire masa ba,saboda hadda hannunsa ne ya karye, Tire rigar tayi ta lullubeshi da bargo,sannun ta mike da niyar barin dakin sai ya kamo hannunta da dayan hannunshi wanda baya ciwo, Juyowa tayi tana kallonsa hade da jefo mai tambaya...wacece itta,kiyi hakuri ki zauna zan miki bayanin komai,kaga tambayarka nakeyi wacece itta? PA dita ce"dan tana PA dinka sai akace ku dinga yawo kuna zuwa ko ina tare, Kinga ba abunda kike nufi bane wannan aure ta zanyi, Aure fah kace eh sosai ma aure ?" Ai shikenan,fusge hannunta tayi ta bar dakin tana fita ta tarar dani zaune a varanda,zama tayi itta ma, Humm tun yaushe kuke tare"ta jefah min tambaya, Bamu dade ba madam shine mutumin da ya min fyade,har na samu ciki,naje ki zubar min da shi kika hanani......., *Sakeena ismail Cameroon ce ✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 25&26 Free book Bismillahi rahmani rahim *********Bamu dade ba madam shine mutumin da ya min fyade har na samu ciki, naje ki zubar min da shi kika hanani, Kuma kafin ma nasan ina da ciki kece kika fara fada min, Kuma kika hanani zubar dashi,ta hanyar bani shawara,dalilin daya sa na bar Cikin kenan. Kina nufin ni ce na fada miki haka,kuma kina nufin mijina ne yayi miki fyaden nan da kika gayamin ?"tabbas shine yayi min, Hummm toh a ina ya ganki har yayi miki fyaden,ko da yake ba sai kince wani abu ba,dan na riga da na samu amsar tambaya ta,watoh ke karuwar sace ba,saboda kinga yana da kudi shine kika nani ke masa ko?toh bari kiji yarinya mijina baya sonki bazai taba sonki ba, yaudarar ki kawai yake yi dan babu macen da yakeso sama dani,dan haka ki wuce ki tattara naki eh naki ki barmin gidana,tana kaiwa nan ta mike ta koma ciki. Sannu alhaji,kai kawai ya geda mata"shigowa nayi dakin,ta kalleni ta fara tambaya ta...wai ba nace ki tafi ba,eh madam jakata zan dauko,na fada sannun na nufi in da jakata yake , daukarta nayi na juya zan fita sai naji alhaji ya kira sunana,baby juyowa nayi na zuba masa idanu,hannu ya mika min alamun nazo,cikin sanyin jiki na karasa inda yake kwance, Hummm yanzu wannan yarinyar kake kiranta da baby a gabana?"ko da yake dole kace mata baby saboda nasan da yanzu kana da dah da yagirmeta nisa ba kusa ba,kila ma matarsa zata girmi babyn naka, Ni yanzu ba wannan ba ina so ka fada min matsayi na awajan ka, Haba hajiyata wannan waca irin tambaya ce" haka,ke matata ce mn, Ba wannan nake nufi ba alhaji,ina nufin ni da wancan wa kafi so"saboda dazu tace min kana sonta shine nake son sani yanzu. Kefa rayuwata ce hajiya itta kuma baby zuciyata ce da kuma ruhina,dan haka dukan ku kuna da mahimmanci sosai a rayuwata, Yanzu kana nufin alhaji wannan yer kankanuwar yarinyar tafini matsayi a wajanka, Kinga nifah bance haka ba,haka ne mana alhaji tunda ba'a rayuwa babu zuciya da Kuma ruhi, dan haka kana nufin in babu babyn naka bazaka iya rayuwa ba, Ka kyauta alhaji,tana kaiwa nan ta mike ta tabar dakin, da ido kawai na bita dashi, Cikin sanyi ciki na karasa na zauna gefen gadon,baby! ya kira sunana, na'am Alhaji gaskiya baka kyauta ba daka fada mata haka,kaga yanzu tayi fushi ta bar dakin. Baby nifah ban iya karya ba,shiyasa na fada mata gaskiyan a bunda ke cikin zuciya ta, Naji alhaji yanzu ya jikin naka, humm baby ciwo yakeyi daurewa kawai nakeyi, Sannu bari naje na sameta tazo mu samu mu kaika a sibiti,toh baby amma ki saya ki saurari a bunda zan gaya miki tukun,toh ina jinka alhaji?yauwa miko min wayata,wayan na mika masa,kasan cewa yasan account number dina dan haka ban jima da mika masa wayan ba naji sako ya shigo cikin waya ta,ina dubawa naga,kudine masu yawan gaske ya turo min,cikin tsoro da firgici na dago na kallesa,sannun na somayin magana...haba alhaji wannan kudin fah na menene,me zanyi dasu,dan ko kudin aikin abba ma bai wuce dubu dari uku ba,amma shine zaka tura min har million50 ni mai zanyi da million 50 gaskiya zan dawo ma da kudin ka,na fada na shiga denne denne a cikin wayata, kinga baby dakata ina da dalilin daya sa na baki kudin nan,dan allah karki mayar min da kudin nan ki ajiye shi a wajanki, A'a Alhaji bazai yu ba ni dole na mayar maka da kudaden ka, Shikenan naji zaki mayar min amma dan allah ki bari sai na warke,sai ki mayer min,yanzu kam ki dinga siyo abinci mai kyau da zai kara miki jini da kuma kuzari,da magungunan da zaka iya sha,kafin na warke sai ki mayar min da sauran, Saboda kinsan baby duk a bunda na baki bazan taba mayer miki da mutuncinki dana karba ba,dan allah ki kara yafe min, shikenan alhaji na yafe miki, Allah ya yafe mana gaba daya, "Ameen" ya amsa, Bude wancan karamin wardrobe din zaki ga wani ta kardu ki dauko ki kawo min itta"kai na geda sannun na mike na karasa inda ya nuna min,ina budewa naga wasu ta kardu sannun na dauko na kawo mai,wani waje ya nuna min yace na saka hannu,biron dake cikin jakata na dauka na saka hannun sannun na dago na kalleshi hade da cewa..alhaji na saka hannun ga takardun, murmuchi yayi min yace na boyeshi a cikin jakata, Kamar ya na boyeshi a cikin jakata?"eh ki boye karki nunawa kowa in naji sauki zan fada miki komai,kai na kawai na geda sannun na saka ta kardun cikin jaka. Toh alhaji bari naje na kirawo ta karta tafi mu rasa motan da zata kaimu a sibitin, Kai ya geda min sannun na mike na fita, Zaune take tana kuka,cikin sanyin jiki na karasa,na zauna kusa da itta,kallo daya tamin ta dauke kai, Dan allah madam kiyi hakuri,wllhy badan cikin mijinki dake ciki na ba,da wllhy babu a bunda zai hadani dashi dan tun ranar da yayi min fyade naji duk duniya babu wanda na sana sama dashi, Zaki iya hada min coffee?eh sosai ma mai zai hana bari naje na kawo miki, Kai kawai ta geda,mikewa nayi naje na hada mata kofi, ina fitowa naganta rataye da jakarta,toh madam ina kuma zaki bayan ga coffee na kawo miki, Ki bar coffee na fasa sha tafiya zanyi,tana kaiwa nan ta nufi inda tayi parking din motarta,budewa tayi ta shiga,ta rufe,da sauri na karasa wajanta tare da fadin...haba hajiya ta yaya zaki tafi bayan baki saya mun dauko shi mun kaishi a sibintin ba, Kinga kije ki kira ambulance din sai yazo ya kaishi a sibitin,haba madam ke ma fah likita ce me zai hana ki taimaka masa, kinga ni likintan haihuwa ce"dan haka babu a bunda zan iya yi masa tana kaiwa nan ta yiwa motar ta key,ta bar gidan. *Washe gari* Yen sanda ne cike a cikin dakin sai faman bincike suketa yi,ni kuma ina zaune a varanda tare da wata yer sanda ga ankwa a hannuna! Kallon mai gadi daya daga cikin yen sandan yayi ya fara magana kamar haka..kai kace kaine mai aikin sa ko,kai jibril ya geda alamar eh,toh sanda abun ya faru kana ina?"wllhy yellabai sanda abun ya faru bana gidan, mai gida ya ai Keni na tsiyo masa mai saboda zasu koma sai suka ga mai dinsu yakare, toh ni dai sanda na fita suna cikin mota,bayan na dawo ne na sameta tana kuka dana tambayeta shine ta fadamin a bunda ya faru,shine ni kuma naji ban yedda da itta ba shine na kiraku, jibril ya karashe magana cikin kuka. Okay ka dauki waya ka kira matar tasa kace mata tazo muna nemon ta,kai jibril ya geda,a take ya dannawa dr hauwa waya, Kwance take tana baccinta kamar babu a bunda ya faru taji wayarta na ringing,dagawa tayi ba tare data duba waye ba, Jin muryar jibril na kuka ne yasa ta fadin ya akayi jibril meye faru?"madam yellabai ya mutu dan allah kizo,ai bata bari jibril ya karasa ba ta ajiye wayan cikin tashin hankali ta zira hijabi akan rigar baccin dake jikinta ta bar gidan,tana fita ta kwallawa dreva kira,da saurin dreva ya fito,gani hajiya,kaga ka kai ni WUDIL, Kai dreba ya geda sannun ya kunna mota ya bude mata bayan mota ta shiga shima ya zaga ya shiga gaba,sannun yayiwa motar key suka bar gidan. Tuki yake a hankali tace ya kara gudu,dan haka tafiyan da zata kaisu awa daya sai gashi sunje a minti 35 ,suna zuwa tun kafin dreva yayi barking ta balla murfin motar ta fito ta nufi inda yen sandan suke. Ina ganinta na mike,na karasa wajanta ina fadin..dan allah madam ki fada musu gaskiya dan allah kice musu bani bace na kashe shi ba wllhy ban kasheshi ba,amma abun mamaki sai naga dr hauwa ta daure fuska hade da kallon yen Sanda,wai meyeke faruwa ne yellabai naganku cike anan,kwashe komai daya daga cikin yen sandan yayi ya gaya mata,ya kara da cewa wai tace kinzo nan jiya da daddare kafin mijinki ya rasu, shine nake jira naji haka ne ko kuma ba haka bane ? Gaskiya ni yellabai karya take min,ni tunda na dawo jiya daga wajan aiki da yamma ban kuma fita ba,amma na gwada number alhaji kafin na kwanta bacci amma taki shiga kasan cewa babu network sosai a wannan gidan shine kawai na hakura na kwanta, saboda dama kafin ya tafi yace min ba sai na jira shi ba,in lokacin kwanciya yayi Kawai na kwanta, Toh ni bamma dauka bai dawo gida ba,saboda ya saba dawowa bayan nayi bacci,kuma da yake jiya tunda na kwanta ban farka ba sai dazu da jibril ya kirani, Kila ta samu tabin kwakwalwa, Gaskiyar dai,kam dan tun dazu sai fadi take kinsan komai kinzo nan kafin ya rasu, Kunga ni dan allah muje ku nuna min mijina,ta fadi hade da rushewa da kuka. Yen sanda na gaba tana binsu a baya, gaskiya madam kiji tsoron Allah ki fada musu bani bace na kashe alhaji ba,amma ko kallon inda nake batayi ba, Suna zuwa dakin ta bude gawan,ta fashe da wani irin kuka.sai da wata yer sanda ta kamota suka bar dakin. *Bayan awa biyu* Kafin a ce me dangi da abokan arjiki sunji labarin rasuwar jabir Abdul Rahman ambassador,ya rasu kuma budurwar sa ce ta kasheshi saboda tana daure da cikinsa shiyasa ta kasheshi ta ballaki dukiyar daya bari, Zaune take a sibitin babu a bunda ya dameta duk da kuwa tasan bata kwana a gida ba Amma bata damu ba,saboda tasan ko babu komai zata samo musu kudi. Kasan cewa TV dake cikin dakin a kunne take a take kuwa aka saki sanarwan mutuwar jabir Abdul Rahman ambassador, Jabir Abdul Rahman ambassador ya rasu ne yau a gidan shi dake garin wudil kuma sakamakon binciken da mukayi ne ya tabbatar mana da cewa PA dinsa kuma budurwar sa ce ta kasheshi,amma har yanzu taki amsar lefin da ta aikata,saboda a duk sanda zata bude bakinta fadi take matar marigayi jabir tasan komai,saboda taxo wajan, bayan mun kira matar marigayi jabir mun tambayeta take sheda mana itta jiya tayar motar ta ma ta fashe dan haka babu inda taje,a yanzu haka mun kama Afiya abubakar iro mun kulleta,kuma dai kun san ukuncin wanda ya aikata kisan kai,dan haka,in mun tattara sauran baya nan zamu mika afiya abubakar iro a gaban kotu domin yanke mata hukuncin dai dai da a bunda ta aik......wani irin tarine suka faraji suna juyowa suka ga abba ne yake tari ga kuma jinin da yake fitowa daga bakinta,kuka Mohseen ya saki hade da karasa gaban abban nasu,zama yayi a gefensa abba na ganin haka ya kamo hannun Mohseen ya shigayin manga a hankali, Mohseen beautyna! baza tayi kitsa kai ba saboda nasan wacece itta nasan ta gaba da baya,dan allah fatima kiyi wani abu kar a kashe min itta,ya fadi yana kallon mama da take ta faman zubda kwalla,karka damu abban afiya insha allah zanyi iya baki kokari na, Shikenan nagode fatima kuma dan Allah ki taimaka ki ja yayanki a jiki ki nuna musu kauna,saboda suna bukatar ki matuka,haba abban afiya wai yanzu kana nufin bana nuna musu kenan ? a'a ba haka nake nufi ba,amma ki kara akan wanda kikeyi,yana kaiwa nan ya shiga furta kalmar shahada,daga nan kuma komai nashi ya saki. Wani irin kuka da ihu Mohseen ya kurma dashi daya sa likitocin shigowa dakin a guje suna tambayar lfy, Sannun suka karasa gaban abba gwaje gwaje sukayi suka ga Allah yayi masa rasuwa dan haka zanin gadon suka ja suka rufeshi da shi, Kuyi hakuri Allah da yafi mu sonshi ya dauki abunsa suna kaiwa nan suka bar dakin. *Bayan sati daya* Sanda mutuwar Abba ya riskeni haukacewa ne kawai banyi ba,sakama kon jin mutuwar abba da nayi ne yasa ni yin bari,koba komai naji dadi zubewar cikin,duk da kuwa ba ni ce na zubar da shi ba, naji mutuwar abba ba kadan ba ga kuma irin sanar mamata dana karaji saboda gani nake duk a bunda ya faru itta ta ja mana,da farko itta ta sani na raka jabir wudil na biyu kuma bata ga a bunda ya aikata min ba,tazo ta kara shirya mu,dalilin shiryawan da mukayi ne na zo na kara rakashi wudil din har wannan abun da ya faru yazo ya faru, Da farko da iyayen jabir suka gane ida dauke da Cikin dansu,cewa sukayi a bari sai na haihu,sannun za'a yanke min hukunci, Amma tunda na rasa cikin nan,suka yanke shawara za'a yanke min hukunci da wuri, saboda dama saboda cikin ne yasa akace a daga. *Bayan kwana biyar* Kudin da alhaji jabir ya bani ne a ciki na dauka na bawa mama taje ta samo min lawya,kasan cewa kudin ba kadan aka bashi ba,dan ma mama ta rage wani a bu,amma duk da haka yayi tsayin dakan wajan ganin na kubta daga cikin wanna halin dana shiga, Bincike yaje yayi a WUDIL,inda ya samu CTTV kemera,dake cikin dakin, har ma dana gidan gaba daya,inda yaga sanda afiya take tattaunawa tare da dr hauwa,har lokacin da tace mata taje ta hada mata coffee din, Bayan tafiyar afiya kitchen ne cikin sauri ta mike ta shiga dakin,tana shiga ta zauna gefensa kamar gaske,sai data samu ta dauke mai hankali sannun ta dauki daya daga cikin Pillow's dake kan gadon ta danna kanshi dashi,sai mutsu mutsu yakeyi amma taki tirewa har sai data tabbatar ya dena numfashi sannun ta tire pillow hade da mikewa ta dauki jakarta tayi hanyar waje,tana fita suka hadu da afiya ta kawo mata coffee din, a afiya ta kawo cewa tayi lfy zatayi anan ne afiya tayi da itta su kaishi a sibiti amma taki. Mutane cike suke a cikin kotun inda alkali ya nemi da lawyan wanda ake kara ya fito,fitowa barista lukman yayi,ya bawa alkali shedan daya samu a gidan jabir dake WUDIL! Bayan alkali yagani ya kuma gamsu da komai,a take aka wanke ni daga zargi, A take kuma aka kama dr hauwa inda alkali ya yanke mata ukuncin zama gidan kaso har karshen rayuwar ta,sakamakon wahalar da su da tayi taki amsar lefinta da wuri. *Tunani* Tana dawowa daga WUDIL ta jefar da takalmin ta tada je dashi a kondon shara,ta kuma sace duka tayoyin motarta,ta tire CTTV kemera dake wajan gaba daya tasa ka a shara,sannun ta shiga ciki ta kwanta, Ta ya akayi na manta ban tire na wancan gidan ba ta fada a cikin zuciyarta a lokacin data dawo daga cikin tunanin. Ke malama ki ban hannunki nace a sa miki ankwa, Hannu ta mika musu inda suka tire ankwan dake hannun na suka saka mata, A haka dai kowa ya watse, muma muka tattara muka koma gida. *Bayan sati biyu* A yanzu ba dama na ce zan fita,dan ina fita in mutane suka ganni suyi ta cewa ga karuwar alhaji jabir Abdul Rahman ambassador,wasu kuma suce maganin mai kwadayi kenan Allah ya kara,shiyasa daga baya na dena fita daga gidan gaba daya, *Bayan kwana goma* Wai afi yanzu a haka zaki taci gaba da zama haka bazaki samo aikin yi ba,kindai san Mohseen bai kai da zai je ya nemo mana a bunda zamuci ba, Naji mama zan samo amma ni gaskiya yanzu bazan kara zuwa wajan wani da zummar nemon aiki ba ?zan dauki wannan kudin na bude karamin kanfanina na kuma samo ma aikatan da zasu dinga tayani kula dashi" Shikenan hakan ma yayi, amma fah dole ki nemo mana gida a wani waje daban da zamu zauna mutashi daga wannan unguwar,saboda kinga idon mutane yanzu yana kan mo, shikenan mama amma fah ni bani da wanda zai nemo gida, Karki damu akwai wani abokin mahaifina zan mai magana ya nemo mana gida saboda dinlali ne shi, Shikenan amma dan allah ki tafi ina so zan dan kwanta, Shikenan mama ta fada sannun tasa kai ta bar dakin. *Bayan shekara daya* Yau shekarata daya da bude kanfanin sai da a tamfopin da shadda da kuma leces kuma Alhamdulillah komai yana tafiya dai dai,dan abun sai son barka, A yanzu muna zaune ne a unguwar nasarawa GRA, Sanda mama ta samo gidan dana je na gani ba karamin balayi mukayi da itta ba,nace mata gidan yayi mana girma deyewa,kuma kudin yayi yawa mu nemo gida dan ma dai dai ci mutsiya amma tace lallai sai mun siya,a haka na dau Millon 20 na siyo gidan, bayan na gama siya tace lallai sai na samo security's da zasu kula da gidan,da kuma yen aiki da zasu mana girke girke da share share,dana nuna mata bani da kudin da zan dauko wayen nan a bunda ta lissafa,bata ce min komai ba, Bayan kwana biyu naga security's da yen aiki,abun ya bam mamaki sosai,dana tambayesu cemin sukayi mamace ta daukosu,nayi mamaki sosai da sukace mamace" ta dauke su,a zuciya ta kuma nace toh a ina mama ta samu kudaden da zata dauko masu aiki da security's ?"bani da mai bani amsa"dan haka na share kawai naci gaba da sabgogina. sai wata rana dana nemi takardun gidan da alhaji jabir ya bani na rasa,dana tambayeta nace min itta ta dauka ta siyar da gida ta dauki yen aiki da security's dashi, Bance komai ba na gyaleta, Dagowa tayi ta kallesa,tace..kasan menene yaya Habib kan shi ya girgiza alamun a'a,wllhy in kaga a bincin da mama takeci sai ka zaci na mutun biyar ne saboda yawanshi,kuma tana gama ci bazata dauka ta bawa yen aiki ko almajirai ba a shara zata saka,gobe ma haka zatayi,in kuma taro ko wani Abu ya tashi toh itta zata dauki nauyin yiwa kawayenta komai,abun na damuna, bata taba zama damu ta tambaye mu damuwar mu ba"in kaga tazo wajena toh kudi take bukata tana gama karba kuma take kara gaba sai in sunkare kuma zata dawo. Wannan itta ce labari na yaya Habib......., *Cigaban labari* Sai mun hadu a wani page din domin ci gaba labari, *Sakeena ismail Cameroon ce ✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* (*Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...*✍️ Page 27&28 Free book Bismillahi rahmani rahim *Ci gaban labari* ********"Sorry my Beauty gaskiya labarinki ya ban tausayi, I'm so sorry kinji, Allah kuma ya jikan abba yayi masa rahma, "Ameen "yaya Habib ta fadi cikin kuka, haba Beauty kukan nan ya isa haka,wllhy yaya habib in na tuna nice silar mutuwar abba sai inji na sani kaina,sai inji da ma na mutu nima a lokacin,dama ban fito daga gidan yarin nan ba,dama an kasheni,wllhy haka nake ji a duk sanda na tuna, Subhanalla haba ina ganinki me illimi amma shine kike fadar irin wayennan maganganun!ina so ki sani abu guda daya shine ko wannan abun ya faru dake ko bai faru dake ba dole abba zai mutu in kwanan shi yakare! "Dan kaha ki kwantar da hankalinki, ba saboda wannan abun daya faru dake ne yasa abba ya mutuwa ba ?son da yake miki da Kuma a bunda ba kece kika aikata ba aka dora miki shine ya sa abba jin haushin abun har zuciyar shi yazo ya buga har ya rasa ransa kangani kagani ko kaima kace saboda a bunda abba ya gani a ne ya sashi mutuwa,kasan Allah yaya Habib lefina ne nida mama mune muka karasa abba, shiiii in har bakiya son bacin rai na toh kar na kara jin kin fadi haka kinji, Kai kawai ta iya gedawa. Okay toh ni bari nazo na tafi,ya fada yana mikewa annunsa yaji ta rike mai hannu,kallon hannun nasa yayi sai ya kalleta,lokaci daya kuma sai ta sakar mai hannu, Ya dai?ka tuba lokaci kuwa"eh nagani karfe 9 toh kuma shine zakace zaka tafi yanzu, Toh in ban tafi ba ya kike so nayi?a kwai wani daki ka kwana in yaso gobe da safe sai ka tafi, Humm bakiya tsoro kar nima nayi miki fyade kamar yanda wancan dan iskan yayi miki, Allah ya jikashi da rahma, Hummm kaima kace dan iska kaga kuwa sunan dan iska da kuma mutu min kirki ba daya bane" Wannan ba hujja bace beauty saboda ba a goshi ake rubuta ga dan iska ko mutumin kirki ba, Yanzu ranar ki ta farko da kika fara haduwa da alhaji jabir din kin dauka zai iya aikata wanna mummunar aikin daya aikata miki ne ? A'a toh kingani karki kuskura ki yedda da mutun lokaci daya, Nasani yaya habib amma kai"ka bambanta dasu,taya kika san na bambanta dasu? Saboda halayenka masu kyau ne haka ma iyayenka na gari ne,dan haka na tabbata sun baka tarbiya mai kyau, Toh amma...?kaga dakata yaya habib mu bar wannan maganar, Nidai a bunda na sani shine bansan meyesa zuciyata ta yedda da kai dari visa dari ba, Dan haka dan allah kar ka bi ta wannan hanyar ka chutar da zuciya ta duk da kuwa nasan ba haka kake ba,amma shedan babu a bunda bazai saka mutun aikatawa ba, Shikenan ni bari na wuce dare na karayi, Okay babu damuwa tunda kaki kwana,ko zaka bawa mai gadi na key din motar sai ya kaika, Wani irin harara ya dalla mata dashi,sunkuyar da kai tayi kasa tana wasa da zoben zinarin dake hannunta, Bazaki rakani ba taji ya fada,tana dagowa taganshi a bakin kofah,bin bayan shi tayi har bakin kofar fita, Murmuchi yayiwa mai gadi yana fadin toh abokina ni zan wuce, To yellabai angama binciken kenan?eh angama amma fah kar maganar dana fada maka ya saka ka bar gidan nan, ka bari in na zo gobe zan sallameka da kaina, saboda ni ba police bane wasa kawai nayi maka, Yanzu kana nufin kai ba dan sanda bane ?eh kwarai ma kuwa kanwata ce ta gudu tazo ta siyi gida anan shine na gado inda take dana zo shine ka hanani shiga shiyasa nace maka ni dan sanda ne"ya karashe maganar yana danyin murmuchi. Yauwa Beauty ki hada kayanki gobe da safe zanxo na daukeki, Ka dauke ni muje ina yaya Habib ? Ba kince kin yedda dani ba?"eh sosai ma,toh in har da gaske kin yedda dani toh kiyi a bunda na fada miki, Shikenan yaya zanyi kamar yanda kace Allah kikaye hanya ya kuma kaika gida lfy, murmuchi ya danyi sannun ya amsa da Ameen dan ba karami jin dadin addu'ar yayi ba, Juyowa yayi ya bude karamin gete din gidan da niyar tafiya sai yaji ta kira sunan shi...yaya Habib ! juyowa yayi ya zuba mata ido,tana ganin yanda ya kura mata ido tayi sauri sunkuyar da nata kasa,dama nace dan allah in ka koma gida ka kirani ka fadamin, Okay babu damuwa yanda kace haka za'ayi ya fada hade da murmusawa. *Washe gari* Meye kawoki gidan mu da sassafen nan haka naja ?wani irin harara naja ta dallawa safna, Daga tambaya shine zaki harareni,a toh ba dole na harareki ba, bayan kuma kinfi kowa sanin a bunda ya kawoni,ni bani kadai nazo bama tare nake da aunty basira dan haka gwarama ki tashi muje mu sameta kartace mun shanyata dan kin san halinta tsarai, Dan yatsine fuska safna tayi dan har ga allah baccin baiyi sheta ba ta zo ta tashe ta" Dan Allah malama tashi muje,naja ta fadi hade da kamo hannun safna ta soma mikar da itta, Mikewa safna tayi ba dan ranta yaso ba tabi bayan naja suka fita suka nufi palo, Sannun dazuwa aunty basira "wani irin harara aunty basira tayi musu, Murmuchi safna ta danyi hade da sosa keya. Yi hakuri bacci nakeyi ta tashe ni! Naji karaso muyi magana kara sowa safna tayi ta zauna a gefen basira,sai ya kasance suna fuskantar juna" Yauwa safna ya ake ciki ne kin samo min number nashi kuwa?" *Kwana uku da suka wuce* Safna ce zaune a gidansu kawarta naja yauwa naja kinsan menene kuwa ?"a'a kawata sai kin fada,wllhy yau naga habib Muhammad Habib yazo kanfanin da nake aiki,wai da gaske kike safna ?sukaji an fada a bayan su"juyowa sukayi duka su biyun suka zubawa wacca tayi maganar ido, Wata matashiyar budurwace da bazata wuce shekaru 25ba tana da gaske dai dai gwargwodo,amma hasken nata na mai ne, fuskarta yana da dan fadi kadan, sai dan madai dai cin hancinta,gajeriya ce"dan ko su safna da ta girma ma sunfita tsayi,sanye take da wani material mai masifa kyau,kallo daya zaka mata ka fahimci ba karamin jin dadi takeji ba,dan yer babban gida ce sosai,dan mahaifinta yana daya daga cikin attajiran garin,su biyu ne kadai aka haifa,itta ce babba sai kanwarta naja'atu sai itta basiran,sai a bunda suke so sukeyi a gidan, Wai bada ku nake magana ba kuka share ni ta fada a lolacin data karaso ta zauna a daya daga cikin kujerun dake cikin palon hade da dora kafah daya kan daya. Eh yazo kanfanin mu"kuma kin tabbata shine?eh na tabbata aunty basira, gaskiya ban taba jin wani abu daya sani farinciki irin wannan ba,basira fada tana murmuchi. Yanzu kinsan mai zaki min safna, kai safna ta girgiza alamar a'a ? ina so ki samo min number dinshi a wayan mai gidanki,zaro ido waje safna tayi tana fadin gaskiya aunty basira kiyi hakuri amma gaskiya bazan iya aikata a bunda kika sakani ba,safna na gama fadar haka ta mike ta dauki mayafinta tayi bakin kofah, In nace zan baki 2 million fah zaki samo min? sayawa cak safna tayi daga tafiyan,itta bata juya ba itta bata tafi ba. Dake nake safna nace in na baki 2 million zaki samo min ne " Zan samo miki amma ki bari sai na samo sai ki bani kudin tana kaiwa nan ta bar bakin kofar. *Ci gaba* Ban samo ba saboda a wacca nake tunani samo miki din kwana biyu bata zuwa wajan aiki,saboda tana da wata yer mas'ala,a yanzu haka ma bata gidan su,amma insha allah zan samo,amma ki sani ko na samo miki ba lallai ne ya daga wayar ki ba Kinga malama ke dai kiyi kokarin samo min, Shikenan zan....sai kuma tayi shiru bata karasa maganar da tayi niyar fada ba, Ya dai safna! Wllhy akwai mas'ala, mas'ala kuma?"eh sosai ma, jiya daya zo nemon aunty afiya nace masa bata nan akwai wata ta karda daya bani yace na kai mata tasa hannu saboda yana son zai koma gobe,kinga kuwa yau ne Kenan zai tafi,yanzu bansan mai zanyi ba,ai basira najin haka ta mike tayi hanyar waje suka bita da kallo har ta fice. *Jiya da daddare* Sai wajan karfe 11 na dare ya iso gidan,tarar da su daddy yayi saye a sakar gidan sai masifah yake ta ,sai yiwa masu tsaro fada yakeyi ta inda yake shiga bata nan yake fita ba wai meyesa suka barshi ya fita shi kadai,in kaga yanda yakeyi sai ka dauka Habib din karamin yaro ne"su dai hakuri kawai suke bashi. Suna cikin haka sukaji anyi hone da sauri mai gadi ya wangale gete din chusa hancin motarsa yayi ciki. Wajan parking yaje yayi kafin ya fito har daddy ya karaso wajan. Yana fitowa yaji daddy ya rungume shi,yana fadin..haba my son meyesa baka dawo da wuri ba,ina kaje haka,kaga daddy kayi hakuri, ba gashi na dawo ba,yanzu dai kazo muje ciki nayi maka bayanin komai Habib ya fadi hade da riko hannun daddy,suka nufi bangaren sa dan baya so kowa yaji maganar da zai tattauna da mahaifinsa ko da kuwa hajiya Maimuna ce" Suna shiga cikin palon,ya kulle da sakata suka nufi bedroom, Kan kujerar dake hade da gadon yayiwa daddy ma sauki shima zama yayi yana fuskantar daddy kana ganin yanda ya nisu kasan maganar da yake son yi mai mahimmanci ne sosai. Habibi da alama maganar da kake son muyi yana da mahimmanci sosai,tabbas daddy yana da mahimmanci, Labarin da afiya ya bashi ya kwashe ya gayawa daddy babu a bunda ya boye masa, Gaskiya basuyi dacen uwa ba allah dai ya sa ta gane gaskiya ta shiryu, Allah kuma ya baka sa'a taimaka musu kai ma, Ameen daddy,ina so zan tafi da itta Dubaï gobe in ka amince"dan ban yedda da zamanta a wancan unguwar ba,ina so kaninta Mohseen kuma na kaishi wajan aunty maryam kafin komai ya lefah, shikenan my son hakan ma yayi badan a unguwar nan suke ba ma da ko anan gidan ma zai iya zama amma yanzu dai yanda ka fada min shawaran da kukayi da itta afiyan gwara ya je gidan maryam din zaifi, Haka ne daddy nagode sosai da goyon baya daka bani Allah ya kara girma da nisan kwana "Ameen ya allah my son Allah yayi maka albarka, "Ameen my dad i love you so much,i love you too my son,kaci a binci kuwa? a'a daddy banci ba,toh bari naje na kawo maka"a'a dad kasan bana son cin abinci in dare yayi sosai,dan haka ruwa kawai zan dan watsa sai na kwanta, shikenan son bari na hada maka ruwan saboda nasan ka kaji sosai ya fada yayi hanyar toilet din, Saurin rike hannun shi yayi , haba daddy ka dawo dan allah zan hada dare yayi muje na rakaka part dinka ka kwanta, Shikenan son tunda baka so muje, Fita sukayi daga part dinsa,suka nufi part din daddy, har bakin kofar palon ya rakashi yayi masa sai da safe sannun ya juya ya koma part dinsa"........, *Sakeena Ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* (*Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 29&30 Free book Bismillahi rahmani rahim **********Bayan ya koma part dinsa"kayan jikinsa ya rage sannun ya nufi toilet domin watsa ruwa, sai da yayi kusan mintuna goma sha biyar a ciki sannun ya fito daure da tawal a kugunshi,zama yayi akan kujeran dake gaban mirror sannun ya dau man shafawa ya shiga shafawa a jikinsa, Bayan yagama shafa man mikewa yayi ya karasa gaban wardrobe ya bude ya tiro rigar bacci mai gobon hannu haka ma wandon dogone" Saka kayan yayi, yana gama sakawa,ya shimfida Sallaya ya tada sallah, Rama sallolin biyu da ake binshi yayi,watoh sallar magriba da i'sha, Yana idar da Sallah bai saya yin askar ba ya mike ya nannade sallayar ya ajiye,sannun ya dauki remod ya kara gudun AC sannun ya hau gadon ya kwanta bayan yayi addu'a" Tun a subaha daya tashi bai koma ba, wayar sa ya dauka ya kira number Yusuf bugu biyu ya dauka, Hello ranka ya dade,yauwa Yusuf kana da number Mohseen ne ?eh ina dashi ranka ya dade, okay ka turomin yanzu ina jira, okay bari na turo maka ya fada yana kashe wayan, Bai fi minti biyu da kashe waya ba sai gashi ya turo masa number din. Kiran number din ya shigayi, Zaune yake ya idar da Sallah kenan yaji wayarsa na ringing daukar wayan yayi ya duba,ganin bakuwar number ne ya sashi saurin dagawa dan a tunaninsa ya dauka afiya ce" Aunty Afi jiya baki kirani ba na shiga damuwa sosai,shiru Habib yayi yana sauraran yaron, lokaci daya yaji son yaron da kuma tausayinsa ya kamashi, Kanina ba aunty afi bace amma nasan inda take a yanzu haka ma itta ce tace na kawo mata kai,dan haka ka nitsu sosai ka saurari a bunda zan gaya maka,toh,yauwa ka hada duk a bubuwanka masu mahimmanci a cikin jakar da kake zuwa makaranta dashi yanda in ka fito babu wanda zai zargi wani abu,kar ka dau ko kaya kala daya in kazo zan siyo maka wasu kayan,amma uncle kayan nawa fah suna deyewa,in na tafi ina zan samo irin su, murmuchi Habib ya danyi tare da shafah dan karamin gemunsa daya dan tara, Kaga kanina zan siyo maka kayan da yafi naka yawa kaji?zaro ido waje Mohseen yayi,tare da cewa Uncle kayan fah zasu kai kala dari,dariya ya danyi saboda shi dariya ma ya bashi, wai kaya kala dari kawai yake cewa masu yawa,sai da yagama yin dariya sa,sannun ya ci gaba da magana....kaga kanina kayanka basu deyewa ni zan siyo maka kala dari biyu kai dai kazo,kaji? magana Mohseen zaiyi amma ya kasheshi ta hanyar cewa,kaga lokaci na kurewa kayi a bunda na gaya maka,na baka minti goba ka gama ka sauko zan yiwa Yusuf Magana in ka fito shi zai kawoka inda nake"dan haka in ka fito idan dreve da yake kaika makaranta yace zai kaika kace masa kai Yusuf kake son ya kaika kaji,toh uncle, good oya yi maza! maza!! ka sauko kar mama ta tashi,kai yaron ya geda sannun ya kashe waya,a bubuwan sa da suke da mahimmanci sosai ya shiga hadawa,duk Kayan makarantar shi ya dauka ya saka a Cikin jakar, Bayan Habib ya kammala waya da Mohseen ne ya sake kiran Yusuf yana dagawa yace masa yanzu Mohseen zai fito,dan haka ya dauke sa, Kwatancen inda zasu hadu yayi masa,sannun ya kashe wayan,mikewa yayi shima ya fada toilet wanka yayi ya shirya cikin farar tishet da farin trousers ya dora bakin suit akai,gaban mirror ya karasa ya dauki a gogon zinarin dake kai ya daura,katon brush din take kan dressing mirror ya dauka ya kara kwantar da gashin kansa da yake kwance lub lub,ga kuma baki da shekin da yakeyi shiyasa yawanci in yazo Nigeria yake saka Cap amma yau sai yaji baya son sakawa dan haka turarukan sa kawai ya dauka ya kara fesawa,ya dauki bakin kobacu din daya ajiye ya saka,sannun ya dauki key din motarsa ya fita ya kulle dakin ya bar part din,ya fita ya nufi wajan ajiye motoci,tun kafin ya karasa wajan motar tashi ya kunna dan haka yana zuwa ya bude murfin motar da niyar shiga sai masu saronshi suka karasa da sauri suna gaishe shi hade da tambayarsa inda zasu,kamar zai ce su zauna,sai kuma ya tuna irin yanayin da Dad dinsa ya shiga jiya da kuma irin fadan da yaga yanayi musu kawai ya mika daya daga cikin masu basa kariyan da yafi yedda dashi key din motar da hannu ya nunawa sauran dasu koma wajan zamansu,shi kuma ya shiga mota, Arafat yaja motar suka bar gidan, Can karshen layin yaga wani mota a pake dan haka yace wa Arafat daya saya, Kaga saya anan, Arafat,sayawa Arafat yayi, shikuma ya shiga kiran number Yusuf, Yusuf na dagawa,yace... Yusuf kuna wajan da nace ku sameni ne ?"eh yellabai tun dazu muna can dan mun kai mintuna goma sha biyar ma da zuwa,okay gamu a bayanku kuzo, Okay gamu nan zuwa,sannun ya kashe wayan,kallon Mohseen yayi da yake kallon sa tun sanda ya fara waya da habib,fito muje gashi can, Kai Mohseen ya geda sannun ya sauko daga cikin motar suka nufi inda su habib yayi parking, Kwankwasa glass din motar yayi, Arafat ya sauke glass din, Sannu ko,yauwa sannu ga mai gidan nn a bayan mota, Habib najin haka ya sauke glass din shima,ya leko da kansa, Yusuf karaso mana, karasowa Yusuf yayi cikin fara'a, yellabai barka da asubaha ?yauwa barka dai Yusuf,wannan ne kanin nawa kenan ya fada yana nuna Mohseen dake rakube a bayan Yusuf tun sanda yaga habib,eh shine yellabai, Okay kazo mu gaisa,ina kwana Mohseen ya fada,daga inda yake, Lfy amma ni ba irin wannan gaisuwan nakeso ba,ko da yake shiga mutafi kila in kaga auntyn ka zaka yedda mu gaisa, Zaro ido waje Yusuf yayi lokacin da yaji habib ya ambaci sunan afiya, Yellabai anganta ne ?eh na gano inda take Amma karka fadawa kowa har ma da mama, toh meyesa kar a gaya mata, kaga ta damu da batar tata ne"a'a ko kadan bangani ba,okay dan haka karka kuskura ka gayawa kowa,kai din ma saboda yedda da afiya yake maka ne yasa nima naji na dan yedda da kai. Shikenan ranka ya dade duk a bunda kace haka za'ayi,yauwa godiya nake Yusuf,ba komai yellabai ai yiwa kaine, Okay shigo mu tafi Mohseen,dan allah ka tabbata wajan aunty na zaka kaini ba siyar dani zakayi ba, Shi abun ma yaso bashi dariya amma ya dage ya hadiye dariyarsa,yace insha allah ba siyar sa kai zanyi ba, murmuchi Mohseen yayi sannun ya bude gaban mota ya ya shiga dan bazai iya zama da wannan balaraben ba,sai shegen kyau kamar aljani,ya fada a zuciyar sa,abun mamaki sai yaji yana cewa toh Mohseen ni kake cewa kamar aljani,cikin mamaki Mohseen ya juya yana kallon sa sai kuma yayi saurin dauke kai saboda kwar jinin sa bazai barshi ya kalleshi ba, Sorry uncle bazan karaba,okay ba komai kanina, Toh Yusuf ka turomin account number dinka in na zauna sai na turo maka wani abu ko, Toh insha allah yellabai godiya nake sosai, Okay babu komai sai munyi magana, Muje Arafat,toh mai gida,gada glass din motar daya sauke dazu yayi sannun ya ja motar suka bar wajan. Tana bacci taji ana mata knocking,mikewa tayi daker ta nufi bakin kofar ta bude idonta ne ya sauka akan na kaninta haka ma bangaren Mohseen,tunda yayi knocking yake kallon bakin kofar dan haka yana ganinta ya fada jikinta hade da sakin kuka,itta ma kukan ta fashe tashi tanayi tana shafah bayan kaninta, Kanina waye kawoka nan ?dagowa daga jikinta Mohseen yayi ya juya yana nuna habib, Kallon inda Mohseen ya nuna mata tayi yana nan saye ya zuba musu idanu yana kallonsu dan ba karamin burgeshi sukayi ba,kallo daya zaka musu ka fahimci shakuwan dake sakanin su,yaya Habib hmmm ya amsa ashe kai ne,kayi hakuri dan allah Ban kula da kai ba,humm taya za'a kula dani tunda anga kani,shiru tayi batace komai ba sai ma kara sowa da tayi ta fada jikinsa hade da facewa da kuka, Ohhh good wai me haka ne Beauty ko so kike na maida shi ne "saurin girgiza kai tayi tana share kwallan daya zubo mata, Okay toh maza ki goge wannan hawayen karna kara gani kinji, Kai ta geda sannun tace musu su shigo ciki, Ciki suka shiga gaba dayan su, Yauwa bari naje na dafa muku wani abu dan nasan ba wanda ya kariya a cikin ku, Toh aunty afi kiyi sauri ki defah dan wllhy wani irin mugun yinwa nakeji,saboda tun jiya da rana rabona da naci a binci,dan tun wanda naci a school, Meyesa ?habib da afiya suka hada baki wajan fadi. Kece baki kirani jiya ba shiyasa,ohhh good haba kanina meyesa zaka bar cikinka da yinwa, kar na kara gani ka bar cikin ka da yinwa kaji,kai yaron ya geda alamar toh, Yauwa haka nakeso,yanzu dai bari naje na hada muku breakfast din ku bani mintuna kadan zan kammala,toh aunty afi a yi girki lfy,kai kawai ta geda sannun ta wuce kitchen ta bar palon ta, Dankalin turawa da kwai ta soya musu,sai pepper soup din fish da tayi musu,mintuna kadan gida ta dauki kamshi, Sai hadiye yawu yake tayi a palo dan tun dazu yake ta jin kamshin, Kallon inda Mohseen yake zaune yayi yaga hankalinsa na kan TV dan haka mikewa yayi ya nufi kitchen din Shima, Tsayuwa yayi a bakin kofah ya harde hannayensa biyu waje daya yana kallon yanda take kwashe pepper soup fish din,tana zubawa a kula,har tagama ta rufe ta je ta ajiye akan Trey din data dora su dankali akai,sannun ta dauka zata fita kitchen din idonta ya sauka akan nashi,ya habib na dade ko? a'a kamshin ne ya cika min hanci shiyasa nace bari nazo na duba, Murmuchi ta danyi sannun tace.. toh gashi angama muje sai kaci,kai ya geda sannun yasa hannu ya karbi katon Trey din dake hannunta haba kawo dan allah na kai, kaga kayi wanka bai kamata ka dau a binci ba, Wani irin hararan wasa ya dalla mata sannun yasa kai ya bar kitchen din, Komawa tayi ta dau kayan tea sannun tabi bayanshi, *Bayan yen mintuna* Yauwa da fatan dai kin hada kayanki da nace ki hada?eh tun jiya da daddare na hada, okay good,maza kije kiyi wanka ki shiya kizo mu wuce" tana son tace wani abu amma yanda ya hada rai ne yasa tayin shiru ta wuce ciki, *Bayan minti 30* Karan takun takalman ta yaji ta cikin korido,dan haka zubawa wajan yayi da idanu,har ta fito daga cikin korido,sanye take da bakar abaya ta yane kanta ta mayafin abayan,fuskarta babu komai sai dan lipstick din data saka, Bakin takalmi ne a kafarta,takalmin yana da dan tudu kadan,hannunta na hagu rike take da jakarta,sai na dama kuma da take jan karuwar akwatinta tashi, A hankali take takowa har ta karasa sakiyar palon. Sakin akwatin tayi ta nemi waje ta zauna, Nagama,okay Shawaran da yayi da Dad dinshi ne ya gaya mata,ya kara da cewa insha allah nayi magana da Yusuf zai dinga fada mana komai,ta wannan hanyar ne kadai zamu iya gyara mama zamu iya nuna mata kudi baifi yaya ba,zamu nuna mata,ko da kudin wata rana karewa zasuyi, Hakane amma yaya Habib har Dubaï zan tafi na bar kanina, Wai yanzu baki yedda dani ba ?"a'a ba haka bane yaya Habib !toh yane hakane mana ki sani cewa aunty maryam zata kula da Mohseen fiye da yanda take kula da yayanta ma kuma na tabbata shi kanshi Mohseen din zaiji dadin zama dasu,saboda in munce zamu tafi dashi muje mu sakashi makaranta a can bazai ji dadin zama acan ba tunda bai saba da kasar ba,kedin ma bawai kin tafi har abadan bane,muna gama komai zaki dawo kasar ku, Shikenan na amince, Uncle aunty maryam tana da yaya sa'anni na? eh sosai ma kuwa mohseen dan haka gaka ji dadin zama sosai acan kuma zaka dinga yin vidéo call da aunty afiya kullun kaji,kai ya geda yana murmushi, Yauwa passport dinki na nan ko ?"eh tana nan,okay good,yanzu dai sedai mu wuce Abuja da daddy in yaso sai ayi miki komai yau zuwa gobe sai mu wuce Dubaï din, Kai kawai ta geda,sannun ya mike ya fita suna binshi a baya, palon ta rufe da key sannun tabi bayan su, Tarar dashi tayi yana mangana da mai gadi, Yauwa kagama hada komai,kai mai gadi ya geda dan tun dazu daya zo yace masa ya hada kayansa, Kudi masu yawa ya mika masa dan ko shi kanshi baisan yawanshi ba dan ragowar daya rage cikin aljihunsa ne ya kwashe duka ya bashi, Kallon kudin mai gadi ya shigayi cikin tsoro da firgici dan tunda yake bai taba rike kudi masu yawa irin haka ba, Yallabai wannan kudin ai sunyi yawa, murmuchi Habib ya danyi,sannun yace....kaje ka nemo sana'a, Nagode sosai yellabai Allah ya sakada alkhairi, Ameen ya Allah,gashi madu da kara dubu 100k ne kawai,iya a bunda ya rage a hannuna kenan,kai jama'a nayi kudi jama'a nace nayi kudi,haka madu ya ginda fada da karfi,kai madu mai haka, habib ya fadi, Ashe so kake ka samo wanda zai kwace kudin kafin ka bar unguwar nan tunda kana gani babu mutane sosai. A toh nayi shiru hajiya,ya dai fi yanzu dai ka dauki jakarka kaje sai mun sake haduwa,daukar gana maskon shi yayi sannun ya kara musu godiya ya bar gidan. Kai kawai habib da afiya suka girgiza sannun suma suka fita, Mohseen kam dariya ya dingayi, Suna fita Arafat na ganin afiya da sauri ya rakasa inda take,barka da fiyowa ranki ya dade barka,afiya ta fada a takaice, Karban akwatin ta yayi ya saka a boot sannun ya taho da niyar bude mata kofar sai yaga habib ya bude mata, thank you my yaya murmuchi yayi mata kawai,shiga tayi ya zaga ta dayan site din shima ya shiga ya rufe,sannun Arafat ya ja motar suka bar unguwar, Wayarsa yaji na ringing yana dubawa yaga sunan daddy na yawo,dan haka saurin dagawa yayi ya kara a kunne,barka da safiya my dad,barka mai son antashi lfy ?lfy lau daddy,dazu naje part dinka na tarar baka nan na tambayi adam yace min ka fita eh naje na dauko su ne a yanzu haka muna hanyar zuwa gidan aunty maryam, daga can zan dawo gida na dau kayana sai muwuce Abuja in yaso gobe idan Allah ya kaimu sai mu wuce Dubaï din, Okay babu damuwa tunda nima yau zan koma sai mu tafi tare,ohhh wllhy na manta shaff kace zaka koma yau ba damuwa,bari na kaisu gidan aunty yanzu zan dawo,okay son sai ka dawo,okay ya fadi yana kashe wayan. Ya naga kayi parking Arafat ?ai mun iso ranka ya dade,toh har mun karaso, eh mana ai ka dan dade kana waya,okay bari na shigo na fito sai mu wuce gida,okay yellabai a fito lfy, Allah yasa, Muje ko?kai afiya ta geda sannun ta fito, dan satar kallon gidan tayi,gidan yana da kyau Shima sosai,part uku ne a gidan,amma na dayan gefen yafi girma da haduwa, Babban part din na mai gidan ne,daya part din kuma na aunty Maryam ne"dayan kuma na babban danta watoh safwan wanda yayi aure a ciki a yanzu haka yaransa biyu, Maryam sunan aunty maryam kenan,sai Usman,sunan mahaifin matarsa, Aunty Maryam na yaya uku, safwan, Aisha Ibrahim, Ibrahim ne dan auta a yanzu haka yana ado bayero university, Itta aisha shekara ta biyu yanzu da kammala makaranta,kuma an sa mata rana dan baifi saura wata biyu ayi bikinta ba, Shiga cikin palon sukayi da sallama,zaune suke suna breakfast gama dayansu sai sukaji sallmar mutumin da basuyi sammani ba,laa wllhy bro ne Aisha ta fada hade da mikewa ta nufi inda yake da sauri ta rungume shi,meye haka Ayush yanzu fah kinyi girma ya kamata ki dena haka,ke da muka kusa aurar dake" Haba bro kawai nayi farinciki ganinka ne ,okay naji sakeni toh,babana anya ba batan hanya yayi ba kuwa dan tun rannan naji kazo ina zuba ido zan ganka amma baka zoba sai yau, aunty maryam ta fada,karasowa yayi ya zauna akan kujera,ai dai gashi nazo, Ina wuni uncle lfy lau habib ya gida ya ka baro su ummi,mijin aunty maryam ya fada,wllhy lfy lau alhamdulillah, Baki mukayi ne,eh wllhy Beauty ku karasa ku zauna cewar Habib karasowa su Mohseen sukayi cikin palon, aunty ina kwana, Mohseen ya fada lfy lau dana sannu dazuwa,yauwa Mohseen ya amsa sannun ya karaso ya zauna,ina kwana,kallon afiya aunty tayi tana fadin lfy lau masha allah aunty ta fada, Habib wannan fah ko daga Dubaï take ne itta ma dan naga kalarku daya murmuchi kawai Habib ya danyi yana fadin yauwa uncle gwara dana sameka dama ajiya na kawo muku kafin naje Dubaï na dawo,tasowa alhaji Bello yayi ya karaso cikin palon yana fadin...toh wanan wana irin ajiya ne haka, Mohseen ya nuna masa yace wannan na kawo muku ku rike min shi kafin Allah ya dawo dani,kace na samu dah aunty ta fada itta ma ta karasa ta zauna kusa da Mohseen tana shafah kansa"sunkuyar da kai kara yayi, Toh kunya ta kakeji kenan,yauwa aunty bari naje na dawo na dauketa daddy na jirana na kisan yau zan wuce shima zai koma abuja, Haba dama nasan,da a bunda ya kawoka da tuni har ka koma bazan ganka ba,shafah kansa kawai yayi ya juya ya kalli gefen inda afiya yake zaune, beauty bari naje na dawo yanzu sai mutafi ko,okay sai ka dawo, Toh uncle sai anjima,okay habib ka gaishemin da sirikina,zaiji insha allah, Yauwa na samo aboki Ibrahim ya fada yana zama kusa da,inda hakane nima na samu kawa Aisha ta fada tana dariya ta karaso ta zauna kusa da Afiya hannu ta mika mata afiya ta bata nata hannun sukayi musabaha,ni sunana Aisha, Afiya, Afiya ta fada a takaice,masha allah suna me dadi,kema haka cewar afiya, Yana fita ya shiga mota suka wuce gida........, *Sakeena Ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pourUtilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*✍️ (J.W.A) Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✏️ *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 33&34 Free book Bismillahi rahmani rahim *********Sallama su'kayi ya kashe wayan, ajiye wayan yayi ya nufi toilet,kasan cewa yayi wanka d'azu dan haka brush da al'wala kawai yayi" ya fito sallaya -ya shim fida,yayi sallah raka'a biyu kafin daga visani ya mik'e ya nade abun sallah,kayan dake jikinsa ya tire ya canza zuwa kayan bacci masu taushi"bayan ya kamma'la ya karasa gaban ma kunni ya kashe duk fiti'lun dake" cikin dakin,da yake wayarsa na hannunsa Shiyasa yayi an'fani da shi ta hanyar haska fititar Wayar ya karasa gaban gadon bayan yayi addu'a sai ya kwanta, Bangaren afiya ma hakance ta kasan ce "saboda kafin su rabu a palo yace mata ta kwanta da wuri saboda Gobe da wuri jirgin su zai tashi,kasan cewa daddy tsanenne ne shi'yasa suna zuwa ya kira daya daga cikin yaran sa"ya bashi passport din afiya ya je"yayi mata duk a bunda ya da ce,kuma kafin yaron nasa yaje ya kira wani daya d'aga cikin ma aikatan airport din yayi mi'shi baya nin komai a take ya amince zai tai'maka masa, Bayan yaron nashi daya aika ya je ne,ya dawo yace gobe da karfe sha'daya jirgin nasu zai tashi, *Washe gari* Tun'da tayi sallar a'subaha bata koma ba k'ayanta ta karasa shiryawa a cikin a kwati,gyara dakin tayi bayan tagama shirya a kwatin nata" "A gogon dake manne a bangon d'akin ta duba,karfe bakwai tagani da yen mintuna, mikewa tayi ta fada toilet,wanka da brush tayi ta fito,jik'in Ta sai kamshin sabulu "yake tayi,kara sowa tayi gaban mirror ta ja kujerar Dake"gaban mirror ta zauna,mai dinta ta dauka ta shiga sha fawa, *Bayan yen mintuna* Saff tagama shiryawa tayi kyau har ta gaji, Kara sowa tayi gaban mirror ta dau jakar hannunta ta bude ta dauk'i man lebe ta saka kadan a kan lebenta" Sannun ta mai dashi cikin jakar ta rufe" Kallon kanta tayi a cikin mirror,duk da babu powder da kwalli a'kan idon ta ba,amma ba kara min kyau tayi ba, A zuciyata kuwa fadi nake allah ne kadai yasan irin kyaun da za tayi in ta saka powder da kwalli, Sanye take da kananun kaya riga da wango, rigar iri daya da wandon, Wango yana da f'adi sosai dan a bude take, duk da tana da hips Tabar kallah amma duk da haka wandon bata K'amata ba? Rigar kamar jacket haka take,amma tana da f'adi kuma a bude take"shi yasa ma ta saka karamar riga daga ciki tunda jacket din mai dogon hannu ne,kuma tana da tsawo dan ta dan wuce cin'yar ta kadan" sai kanta data y'ane da mayafi mai dan f'adi In na fada muku irin kyau da tayi ma bata lokaci ne" Tun da'zu ya shigo dakin yake ta sallama amma bata ji shi ba?shiyasa ya Rungume hanna yensa a iriji yana kallon ta" Yana nan saye yana kallon ta"dan shi kanshi ba karamin kyau tayi masa ba? Yana nan saye yana kallonta, Afiya kuwa taga ma kallon kanta Kenan ta juya ta ganshi saye yana kallon ta, Kai kawai ta girgiza sannun ta karasa inda yake"tsaye, Allah ya k'ama ka ta fadi tana ci gaba da kallon sa itta ma" Saurin dauke i'donsa yayi"hade da cewa...nima ramawa nayi jiya ba haka K'ikayi mun ba?" Naji amma tun dazu mai kake kallo?kin fini sani mai nake kallo ai, Ni ban sani ba? Kinyi kyau ya fada yana kallon ta da wayen nan lum cessun idanun nashi dake rikita Y'ammata,dauke kanta tayi tana fadin...k'aima kayi kyau cikin wannan jallabiyan n'aka, ka fito a balaraben ka sosai, Da gaske ya fada hade da saka tattausan hannun sa ya j'a dogon hancinta"kai kawai ta iya gedawa sakama kon jin taushin hannun shi" da kuma sanyin da hannun y'ayi, Ya dai, still dai kan nata ta kara geda wa, Kallon a gogon dake daure akan tsintsiyar hannunsa y'ayi ya sake"mai da kallonsa hareta,zo muje muyi breakfast lokaci na tafiya dan har tara da kwanta tayi,bai jira cewar'ta ba ya kamo hannunta ya bude k'ofah suka bar dakin suka nufi palo, Suna zuwa palon Afiya na ganin daddy tayi saurin janye hannunta daga rikon da habib y'ayi mata,sannun tayi gaba tana karasa dinning table din,da kallo habib ya bi Afiya dashi, Daddy ina kwana?"afiya ta fada a lokacin da ta durk'usa,lfy lau yata an tashi lfy?lfy lau itta ma ta amsa" Daddy barka da safiya,habib ya fada a lokacin da shima ya karasa dinning table din,hade da ja kujera dake kusa da daddyn nashi ya zauna" Lfy lau son,zauna mana Y'ata shiru tayi bata mike daga burku shen da tayi" ba,tashi ki zauna y'ata daddy ya kuma fadi... a'a daddy ni zanci nawa a palo, Kin gani,jiya n'ace miki ke yer kauye ce"k'ika ce...ke"ba yer kauye bace ?yanzu ba gashi nan ba, kaga son ba ruwan ka da itta wannan ni da itta ne,ai shikenan Dad nayi shiru,ya dai fi maka, Yauwa y'ata zoki zauna K'iyi breakfast d'inki ni nagama nawa Daddy ya fada yana mik'ewa, Bata tashi ba har sai da taga ya bar wajan sannun ta mike"sai kizo ki zauna ai, Harara ta dalla mai sannun ta j'a kujera ta zauna bayan ta gama zuba a bincin,ta soma ci, *Bayan sun gama cin a binci* Kiran daddy y'ayi a waya ya ceda masa sun gama cin a bincin yace gashi nan zuwa,kashe wayan y'ayi ya juya ya kalli bangaren da afiya Take"zaune,yauwa tashi Kije ki dau ko akwa'tinki kizo mu tafi,nima bari naje na dauki nawa,kai kawai ta geda sannun ta Mike"ta nufi ciki, Shima mikewa y'ayi ya wuce nasa dakin domin dauko nasa a kwatin, *Kano* Bayan basira ta bar gidan su safna, Gidansu da koma tana zuwa ta kira daya daga cikin matukan jirgin tace mai dan allah ya duba mata wayen da zasu je Dubaï yau,in a kwai sunan habib Muhammad Habib a ciki ya kira ta ya gaya mata,kasan cewa Ma tukin jirgin saurayin ta ne,shiyasa tana fada masa sunan ya gane su waye,dan haka a take ya shiga fada mata cewa...yau Abuja zasu tafi sai gobe zasu wuce Dubaï din, Shikenan Mahmud zamuyi magana anjima amma dan allah ka samo min ticket nima ina so nan da awa biyu na je Abujan,kuma dan allah ka taimaka kayi duk yanda zakayi na samo Visa nima na wuce Dubaï din gobe,haba baby ke ma dai kinsan bazaki samo Visa gobe goben nan ba, shima alhaji Muhammad Habib Ibrahim din dan yana da hanyoyi ne shiyasa,ba dan haka ba shima bazai samo wa- wannan yarinyar da nake kyautata zato surikarsa ce visa ba,stop plsss stop Mahmud,naji amma dan allah ka taima ka min zan baka sosai in na dawo,ai Mahmud na jin haka ya wani lashe baki kamar tsohon maye,dan bazai manta dadi da yake sha a wajan basira ba,dan duk da ba doguwa ba ce ba,amma tana da komai tabar kallah, Kuma gashi in sukayi sosai take bashi hadin kai, Mahmud da kai fah nake magana,basira ta kase masa tunanin da y'akeyi Shikenan zan samo miki insha allah,kuma wllhy ki cika min alkawari na,dan kasan ni tsarai,dan wllhy Bashi ne, Shikenan naji kai dai kayi min a bunda nace m'aka ni kuma nayi maka alkawari zan baka hadin kai fiye da na kullun, Shikenan babu damuwa bari na kashe sai na kara k'iran ki,kafin ta ce wani Abu tuni ya kashe wayan, *Bayan wasu a wanni* Wayar ta ce ta shiga kara,saurin da gawa tayi kuma dama a bunda take jira tun d'azu kenan,hello Mahmud!yauwa na samo mik'i Ticket din,yanzu dai a bunda za'ayi ki shiya nan da awa daya jirgin abuja zai tashi dan haka ki sameni a can dan ni zan kai'ku abujan,kinga daga nan sai na samo mana hôtel da zamu dan sh'ana kafin zuwa gobe, Naji maye kawai,tana kai wa nan ta kashe waya, Zuwa tayi ta samo Mahaifiyarta ta fada ma'ta cewa zata je Dubaï a kwai wani abun da zatayi amma bazata wuce sati daya ba zata tawo, Allah ki'yaye hanya mahaifiyarta su tayi mata,babu ko tambaya me zataje ta'yi a can, "Ameen ta amsa"a zuciyarta kuwa ba kara min murna take ba,na ganin cewa zata je ta hadu da mu'radin ranta, Aunty nima na shirya mu tafi tare ne ? naja ta fada, kar'ki fara,da zaki ce zaki jé k'insan ya na samu visan ne ko kuma dai an gaya miki jirgin na u'bammu ne ? allah baki hakuri, "ameen basira ta amsa,sannun ta bar wajan ta koma dakin ta do'min karasa shirye shiryen ta, *Abuja* Bayan sun sauka, hôtel Mahmud ya kama musu suka shiga aikata a bunda suka saba ai'kata wa, Bayan sun samu nitsuwa, Kallon basira Mahmud y'ayi ya soma magana kamar haka...y'auwa baby gobe da karfe sha daya jirginku zai tashi, kuma dana bin'cika ma na gano cewa jirgi daya zaku shiga da Mr h.m.h,waye Mr h.m.h Kuma?"basira ta tambaya,habib Muhammad Habib mana,ohhh, wawww gaskiya naji d'adi, Nifah banga ne miki ba?Wai me k'ike son yi da wannan mutun min ne baby?"soyayya basira ta bashi amsa,k'ina nufin son sa k'ike"kwarai kuwa gashi ma kana ganin yanda na damu da na hadu dashi, Yanzu a gaban nawa k'ike fadar haka... toh sai me dan na fadi haka a gaban ka,naga dai na baka jiki na da k'ake so, Bangane kin bani jikin ki da nake so ba?"eh mana yanzu in n'a ce ka aure ni zaka aure ni ne ?"sosai ma me zai hana, Hummm Mahmud kenan karka maida ni mara hankali mana,nasan ka tsa'rai,dan haka kai dai ka kyaleni kawai, Hummm basira kenan,toh bari na gaya miki wannan mutu min da k'ike cewa kina so ba zaki taba samun sa ba, saboda shi larabawan da yake tare da su ma basa gaban sa ballanta na ke" da ba kowa ba,bakar fada. Yana k'aiwa nan ya bar dakin. Da kallo ta bishi da shi ga kuma jikin ta da y'ayi sanyi sosai akan maganar daya gaya mata, *Kano* Mamace take ta faman yiwa m'asu aiki da security's fada,ta inda take shiga bata nan take fita ba,wai sun san inda Mohseen da afiya suke"sai da suna ranse tukun sannun ta kyale su, Ai shikenan tunda haka suka zaba su je allah bada sa'a,tana kaiwa nan ta koma tayi zamanta taci gaba da shan fruits din ta da take yi, *Abuja* Daddy ne ya kalli su Habib yana fadin....y'auwa muje ko karku makara, Kai suka geda sannun suka mike suka bi bayan shi, Suka fita aka bude musu mota suka shiga sannun aka bude musu get aka jà motar suka bar gidan, motocin da zai musu rak'iya suka mara musu baya suka wuce airport, Tunda d'azu tazo sai kalle -kalle take ta fa man'yi tana jira taga ta inda motocin su zai bullo, Ganin wasu motoci na alfarma sun shigo cik'in airport din ne ya sata saurin mikewa cik'in rawar jiki ta k'araso kusa da wajan da motocin sukayi parking,ta saya daff da motar tana jiran taga ta inda zai fito, Wata matashiyar budurwace da bazata wuce shekaru 23 ba taga ta fara fitowa,sai wani daya fito ta dayan site din, wani Irin y'awu ta hafiye,ta kalli kanta ta kalli afiya,dan itta har ga allah ta dauka itta ma balarabiya ce"......., Pls ku dinga comment, Badan komai ya sa kwana biyu banyi posted ba sai dan rashin comment da ba kwayi min, Dan bai kamata ace na zauna na bata lokacina ina typing ba,kuzo kuki yi min comment, Dan allah ku gyara pls 👏 *Sakeena Ismail Cameroon ce*✍️ intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3UjgUtilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*✍️ (J.W.A) Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✏️ *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske...✍️* Page 35&36 Bismillahi rahmani rahim *********"Wani irin y'awu ta hadiye a lokacin da taga afiya ta fito daga cikin mota,kanta ta kalla sannun ta mai da duban ta kan afiya,dan itta har "ga allah ta dauka itta ma (balarabiya) ce "kasa karasa inda suke" kamar yanda tayi niyar yi tayi, Daddy ne ya fito shi ma,a dayan motar, kallon Habib y'ayi yana fadin..muje ko son,kai Habib ya geda sannun ya juya ya kalli afiya yace...muje beauty!kanta ta geda sannun suka soma tafiya,yana gaba tana binshi a baya har suka karasa ciki,suka zauna kafin lokacin tashinsu"y'ayi, Jiki a sanyaye ta koma inda ta zauna dazu,ta dauk'i a kwatinta,sannun ta soma barin wajan. "Me k'ike shirin aikata wa basira!karki bari wannan damar da kika samu ya kubce miki" (Haka)zuciyarta ta shiga gaya mata a take"ta kara juyowa ta koma ciki. *Bayan minti 15* Shiga jirgi aka somayi,dan haka tashi" Habib y'ayi ya rungume daddyn sa,shafah bayansa ya shigayi,dan "duk da bai leka (fuskarsa) ba amma ya tabbata kuka yake'yi dan tun yana yaro in yaje (Dubaï) daker suke" rabuwa shiyasa abun ya zamam mai jiki,dan kuwa "har yanzu in yaje ko yazo sai yayi kuka idan zasu rabu, Shiru afiya tayi tana kallon su"dan ba karamin burgeta sukayi ba"a take kuwa ta tuna da (Mahaifinta)da kuma irin shakuwan da sukayi dashi"ana cewa shakuwa "uwa yana fi na uba amma itta gaskiya shakuwan da tayi da (Mahaifinta) ko rabinsa basuyi da mama ba, "Tana nan saye ba tare data sani ba"hawaye suka shiga gangaro mata daga kan kuncinta, Tun da'zu daddy ya dago shi yana rarrashin sa" Idon sa ne ya sauka akan ta, tana nan saye da alama bata jikin hayyacinta,dan kallo daya zaka mata ka fahimci cewa wannan abun da Habib yayi ya tuna mata da rayuwarta ta baya. "Jikin daddy ne" y'ayi sanyi sosai,dan haka sakin Habib y'ayi ya nufi inda take"saye,kallon wajan da dad dinshi ya nufah y'ayi,sai yaga wajanta ya nufah,hawayen da yaga Yana zuba akan kuncinta ne yasa shi- shima karasowa inda take da saurin,a lokacin kuma tuni daddy ya karasa inda take"ya d'afata, Firgigit ta dawo cikin haiyacinta,saurin saka hannu tayi tana goge hawayen daya zubo mata,hannunta daddy ya tire daga kan kuncin nata, yana fadin...humm yata kenan ki bar hawayenki dan na riga da nagani. "Sunkuyar da kanta dayi kasa ba tare da tace komai ba" Abba k'ika tuna ko?saurin geda masa kai tayi a lamar eh,hade da kara fashewa da kuka. Beauty mai Haka cewar Habib! "Kyale ta tayi kukanta kila zataji sanyi a ranta,haba daddy taya zata dinga kuka anan wajan,kai ka k'iyaye ni son,yanzu kai ba anan din kayi kukan yanzu ba?tsosa keya yayi yana murmushi, Dole kayi murmuchi ai tunda baka da gaskiya, Yanzu na tabbata kukan naka ne ya tuna mata da (Mahaifinta)da bakayi ba da yanzu lfy lau,kaga y'ata kiyi hakuri ki dinga masa addu'a in kika tuna dashi dan addu'a yake da "bukata ba kuka ba? "Kai kawai ta geda, Yauwa kamata kuje ku shiga jirgi dan kowa ya shiga daddy ya fada yana kallon habib, Kai Habib ya geda sannun ya matso kusa da itta da niyar kamata ta masa kusa da daddy ta shiga yi "masa sallama, Toh daddy mu zamu tafi Allah ya kara lfy da nisan kwana?"Ameen ya allah Daddy ya amsa" "Maza ku tafi,kai ta geda sannun ta wuce"inda jirgin yake" Shima ya kara yiwa daddy sallama yabi bayanta, "Duk a bunda ya faru tagani,ga Kuma bakin ciki daya karu a cikin zuciyarta, Dan ba karamin bakin ciki da haushin afiya taji ba,da taga yanda suke nuna mata so da kuma kulawa. Sai da taga zasu shiga jirgi sannun itta ma ta bi bayan su"dan so take ta zauna kusa da su" "Suna shiga ya nuna mata wata kujera yace" ta zauna,zama tayi shima ya zauna kusa da itta,tana shiga ta tarar inda take" son zama babu waje dan haka a bayansu ta zauna,dan tasan ko babu komai zata dinga ji duk maganar da zasuyi,da Kuma a bunda zasuyi, "Sanar dasu akayi dasu daura b Bell dinsu,dan haka daura mata yayi shima ya daura nasa" Ba'a wani jima ba jirginsu ya tashi" Beautyn yaya Habib ! Na'am ta amsa"meye saki kuka dazu"babu ta bashi amsa"ohhh karya zaki fara min kenan?a'a, toh meyesa kika ce ba komai,bayan kuma dazu kika ce wa daddy saboda kin tuna da abba,ohh yanzu kasan hakane kake tambaya ta"kenan? Gaskiya kin fara rai nani wallahy, Habib ya fada yana hada rai" Sorry tace kawai sannun ta juya tana kallon Window, Shiru basira tayi tana jinsu" Dan juyowan da afiya ta danyi ne" sai taga kamar akwai inda ta taba ganin fuskan, Shiru tayi tana tunani inda ta taba ganin ta lokaci daya kuma tace"yesss tabbas a wayan safna na taba ganinta,toh karfa ace wannan ce mai gidan nata da nake" jin labarin ta,mema sunan ta?".....yauwa afiya! tabbas ina jin safna na cewa aunty afiya,wannan duka a ranta take" fada. Wani irin murmuchi tayi shikenan zan samu ma fita kila daga nan ma sai nayi musu karya da cewa bani da wajan sauka tunda bani da yen uwa a garin kaga shikenan in sun tausaya min sai suce nazo na sauka a gidan su"yesss haka ma zanyi, Sallama ta farayi, (assalamu alaikum)shiru taji ba'a amsa" ba dan haka kara sallam tayi"(assalamu alaikum) Beauty wannan yarinyar fa kamar dake" take" "Magana Habib ya fadi yana kallon afiya data juya, Ni!ta fada tana nuna kanta,eh mn, Juyowa afiya tayi tare da "amsa mata sallamar ta"walaikum salam,sannu sis cewar basira,yauwa sannu afiya ta fada can kasar makoshi kamar ana mata dole yin maganar. Dama tunda muka shiga jirgi nake ta kallon ki,saboda ji nake" kamar akwai inda na taba ganinki"ni kuma?eh wllhy na taba ganin hoton ki a wajan safna,kasan cewa itta din kawar kanwata Naja ce"shiyasa nake yawan jin labarin ki a wajanta, Ayya allah sarki sannunki. Yauwa sannu kema,ashe (Dubaï)zaki tafi,eh afiya tace sannun ta juya ta ci gaba da kallon Window da takeyi"dan tunda tace itta ce yayar kawar safna ta gane itta ce waccata safna ta bata labari tana son habib,shiyasa gaba daya taji ta sane ta, Jik'in basira yayi sanyi sosai dan bata tauka zata mata haka ba, Sai kuma ta tuna safna ta taba ce mata bata da yawan magana,dan ko itta da suka dade tare ma basa magana sosai dan sama -sama kawai sukeyi" *Bayan minti 30* Bacci ne ya dauke" ta akan kujera jin ta kawai yayi ta fada kan kafadunsa, murmuchi kawai yayi sannun ya gyara mata kanta ta yanda zataji dadin yin baccin, Basira kuwa ba karamin na daba zama kusa da su tayi ba, Yanda yake bawa afiya kulawa ji take dama itta ce " *Bayan awa hudu* Jin da tayi yana tashinta ne yasa ta bude idanun ta a hankali ta dorasu" akansa, Sarkin bacci mun iso,zaro ido waje tayi"tana fadin.. gaskiya wasa kake"min yaya Habib,baccin da kikayi ba fah ba kadan bane, Kai yaya baccin da nayi ba fah bai wuce awa daya ba,wani irin hararan wasa yayi mata, Naji tashi mu sauka, kinga kowa ya sauka saura mu kadai, "Kanta ta geda sannun ta mike"ta dauki jakarta, Tun kafin jirgin su ya sauka suka iso airport din,gashi har jirgi ya sauka kowa ya sauka amma basu ga dun fito ba,dan tun dazu suke ta raba idanu, Hangoshi tayi yana saukowa da shi da wata matashiyar budurwa, Tunda ta dora ido a kanta bata dauke idonta ba har suka karasa sauka, Wata mata shiyar budurwa da bazata wuce shekaru 18 zuwa19 ba ya mufoshi,da kallo daya zaka mata ka fahimci itta din balarabiya ce"bin bayanta hajiya Nuria (ammi)tayi suka karasa wajansu"Habib kuwa na ganin mahaifiyar sa abun kaunarsa ya taho ya rungumeta" Ibni barka da dawowa Ammi ta fadi da larabci"ammi mun sameku lfy?lfy lau ibni ta fada tana sakinsa sannun ta rungume afiya "itta ma sannu da zuwa yata,ta fada da hausar ta da bata fita sosai, Sannun ta sake ta,durgusa wa afiya tayi tana gaidata sauri dagota ammi tayi tana fadin...haba yata nifah mahaifiyarki ce"dan haka ya'a bata jin kunyar uwa, "Cikin sanyin murya tace....nagode sosai ammi,kai kawai ammi ta geda mata sannun ta kamo hannun ta suka wuce inda motarsu take" Rungumar Nadra yayi yana sauke ajiyar zuciya,itta ma ajiyar zuciyan ta sauke"tana fadin...nayi missing dinka fah habibi,nima haka habibti! "Sakinta yayi ,Sannun ya kamo hannunta suka nufi mota su ma"......., 😳toh fah jama'a wacece Nadra kuma?" Karfah a ce budurwar Habib ce" Idan Nadra ta kasance budurwar habib toh ya Afiya zatayi?"me habib yake nufi,🤔 Ko dai Habib ba son Afiya yakeyi ba ?" Mu hadu a wani page din domin samo wayen nan amshoshin😊 *Sakeena Ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*✍️ (J.W.A) Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✏️ *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 37&38 Bismillahi rahmani rahim ***********"Sakinta y'ayi ya kamo hannunta suka nufi mota suma,duk a bunda ya faru a kan idon basira ne ya faru... "Kanta gaba daya ya kulle"tun sanda taga nadra da habib,tambayar kanta ta shigayi"wacece Nadra?me a'lakarta da Habib ?"wayen nan tambayoyin ta shiga yi wa kanta amma babu "Mai bata amsa, dan kanda gaba daya Yagama kullle wa" Tana nan tsaye har suka nufi motarsu"sannun itta ma ta fita domin zuwa titi ta samu taxin da zai kaita hôtel din da zata sauka, Kafin su habib su karasa bakin motarsu"tuni ammi ta shiga motar data zo dashi itta da afiya driver Ya ja juka wuce" gida, Suma habib kara sawa suka'yi inda motar nadra take"ta bude sannun ta juya ta kalleshi"hade da cewa...yauwa shiga,kallon ta ya danyi lokaci daya kuma sai ya janye idonsa daga kanta,sannun ya tire hannunta ya rufe mur'fin motar data bude masa"ya zaga ta ma zaunin drive ya shiga,tasan mai yake nufi,dan haka bude dayan site din tayi ta shiga sannun y'ayi wa motar key ya ja ta suka bar wajan.... Tunda suka shiga mota tayi shiru tana kallon titi,dan ba kara min kyau kasar ya'yi mata ba" Dan Dubaï ya hadu iya haduwa, Tana kallon wajan amma hankalinta ba'a wajan take ba?" Dan kuwa tun lokacin da taga wannan yarinyar take tammayar kanta wacece itta, me kuma halakarsu da habib? Kar fah a ce budurwace"karfah a ce ba sona yaya habib yakeyi ba?"k'ai -k'ai ina wllhy yana sona,na tabbata in baya sona ba bazai taba nuna damuwarsa"a kai'na ba"bazai taba nunamin kulawa ba?bazai taba damuwa da damuwata ba"har ma "Yazo ya damu dana kanina ma"tabbas yana sona,kuma duk yanda zanyi sai na gano wacece itta waccan din, Tun dazu ammi take ta Magana amma shiru babu amsa"shiyasa ta tabata,ai kuwa a take"afiya ta dawo cikin Haiyacinta"hade da juyawa tana kirkiro murmuchi,mayar mata da mar'tanin murmuchinta ammi ta'yi hade da cewa...habibti duk kallon ne haka nake ta magana tun dazu baki jini ba?" Wllhy ammi kasar tamin kyau sosai, allah sarki,tunda ta miki kinga sai ki samo mana mijin aure anan na aurar dake sai mu zauna tare ko?"kanta ta sunyar kasa ba tare da tace komai ba ta shiga yin wasa da Ring din azurfan dake en yatsun hannunta har guda biyu, Kallon rings din ammi tayi sannun ta mai da kallonta kan gwala- gwalan rings din dake hannunta, murmuchi ta danyi sannun ta kara mai da dubanta kan afiya,dan gyara zamanta ta danyi sannun ta soma yin magana....habibti afiya ! dagowa tayi tace"na'am ammi,wannan ring din hannun naki nakeso ki bani guda daya ya min kyau,ba tare da bata lokaci ba"afiya ta tiro duka rings din ta mikawa ammi hade da cewa...gashi ammi, a'a habibti nikam guda daya kawai zaki bani,kallon wanda yafi yau a ciki ta'yi sannun ta mikawa ammi...gashi ammi mai ma kon ammi ta karba sai kawai taga ta girgiza mata kai hade da cewa... a'a habibti ni wancan nakeso,ammi ai wannan tafi kyau da sada, Eh nasani habibti amma ni nafi son shi, Shikenan ammi gashi ta fadi tana mika mata waca ta nuna mata,karba ammi tayi hade da yi mata godiya...nagode sosai habibti,naji da'din wanna kyautar dana samo daga habibti na,ina sonki sosai kuma ina so ki daukeni a masayin mahaifiyarki,dan tunda na dora idanuna a kanki naji ina sonki kuma son da nake miki irin sonda uwa takewa yerta,da fatan kema zaki soni sosai kamar yanda nake sonki ammi ta fada hade da tiro daya daga cikin rings din dake cikin en yatsun hannunta... Hannun afiya ta kamo ta saka mata ring din,kasan cewa ammi en yatsunta tsirara ne,kamar na afiyan shiyasa y'ayi mata dai -dai dan in kaga ring din a hannunta zaka zaci nata ne, *Gidan su habib* A wani gida na alfarma naga driver ya'yi hone,mai gadi ya wangakele musu get Driver ya shiga da motar ciki. Wajan parking space naga driver ya nufa yaje ya'yi parking,kafin mai gadi ya rufo get su habib ma sun cilla hancin motarsu ciki, Fito muje habibti,kai afiya ta geda,hade da fitowa,a lokacin suma su habib suka karasa dai -daita parking din motarsu,suka fito. Kallo daya afiya tayi musu ta dauke kai,tabi bayan ammi suka nufi wani part din da taga ta nufa, Kasan cewa part din uku ne amma wacca suka nufi yafi saura kyau da haduwa. "Suna shiga palon suka tarar da wata mata da a shekaru zata iya kai wa 55 haka,kamar ta daya da ammi ko ba'a fadawa mutun ba zaka fahimci itta din mahaifiyartace"wato kakar habib,sai wani dontijo da shima a shekaru zai iya kaiwa 65 haka,shima dai yana dan yin kama da ammin amma kamar yafi yawa da mahaifiyarta,sai wani mutun da kallo daya zaka masa ka fahimci shi din kanin mahaifin ammi ne"saboda yana kama sosai da Abie ,kuma da alama shine mahaifin nadra saboda kama da yake yi da itta"suna ganinsu suka mike"saye,suna yiwa afiya sannu da zuwa tare da karaso inda take"rungumeta ummi tayi tana cewa welcome my dear, thank you sitty, Sitty nifah sukaji habib ya fada a bayansu"wani irin harara sitty da ammi Suka yiwa habib. Zama habib ya'yi a kasan carpet hade da bata fuska kamar mai shirin yin kuka,ya fara magana kamar haka... shikenan nikam tun ba'a je ko ina ba an fara nuna bambanci a sakanina da Beauty,beauty!nadra itta ma ta kira sunan... juyowa habib y'ayi ya kalleta hade da cewa...ke" karki fassarani,sunan da ake" kiranta dashi kenan a can,ya fada hade da kara juyowa ya Kalli jaddah ya fara magana...jaddah kagan su ko?wllhy ammi da sitty tun da beauty tazo na fara ganin canji a wajansu" Kaga taso habibi ni da uncle bazamu canza ba,dan haka taho, abie ya fada hade da bude mai hannu,cikin fara'a ya taso ya taho wajan abie ya rungumeshi. Afiya bata ji mai sukace" ba dan da (larabci)sukayi maganar. Babba!nadra ta kira mahaifinta, na'am binti?zanje gida saboda a kwai wata kawata da zataxo anjima, Okay bari nazo mu wuce" tare,mahaifin nadra ya fada,hade da kallon yayanshi. Abu habib zan tafi sai munyi magana,ya fada yana kallon kakan habib,watoh abie,wanda habib yake kiran shi da jaddah, Bazaku saya muci a binci ba,aa zan tafi da nadra saboda kawarta zataxo anjima kila ma ta zo tunda tun dazu munanan, Shikenan sai anjima abie ya fada yana sakin habib. Habibti sai munyi magana habib ya fada yana kallon nadra,kai kawai nadra ta geda masa sannun ta juya ta bar palon,babba ya bi bayanta shima. Yauwa maza kaje kayi wanka kazo kaci a binci Ammi ya fada tana kallon habib. "Kai habib ya geda sannun ya wuce dakinsa" Muje kema habibti afiya ke" ma na nuna miki dakinki ki samu kiyi wanka kizo kici a binci, Kai ta geda sannun tabi bayan ammi suka wuce" Wani daki mai kyau da sheki,ta kaita,dan kallo daya zakawa dakin ka fahimci ba kara min kudi aka kashe wajan kawata shi ba. Toh habibti ga toilet can ki shiga kiyi wanka sai ki fito kici a binci,toh ammi nagode sosai allah ya kara girma, "ameen ammi ta amsa sannun ta fita ta barta. Haka ma bangaren habib yana shiga dakinsa kayan jikinsa ya rage sannun ya fada toilet, Kallon dakin na shigayi ni kuma kafin ya fito,🤩 Baki da hanci na bude ina kallon dakin,dan ba karamin kyau ya'yi ba, saboda yafi dakinsa na" (Nigeria) kyau sosai, Komai na kanin farine,kama daga labulaye carpet gado wardrobe duk farine,dakin ya hadu iya haduwa. Dan kallo daya zaka wa dakin ka fahimci shi din dan gata ne"gaba da baya. *Bangaren basira* Tana zuwa titi ta samu taxin da zai kaita hotel din da zata sauka. Tana zuwa hotel din, Bayan ta kama daki daya daga cikin ma aikatan yaje ya nuna mata dakin sannun ya barta a bakin kofah shi kuma ya koma, Tana shiga kayan jikinta ta rage ta fada toilet. *Kano Nigeria* Gidan aunty maryam! Kasan cewa makarantar su Mohseen daya ne da Ibrahim,shiyasa yau tare suka je tare suka dawo, Duk da kuwa kwana daya kawai yayi a gidan aunty amma yaji dadin zama gidan sosai, Dan kwata- kwata basa nuna bambanci a saka ninshi da Ibrahim,daga aunty maryam din har ma da mijinta da aisha duka... *Dubaï abu dabi* "Bayan ta fito daga wanka. Shiryawa dayi cikin kaya mara nauyi,kasan cewa sam itta batason kaya masu nau'yi ko kadan. "Yanzu ma dai riga da Wando ne a jikinta"amma rigar na da fadi da kuma tsawo,dan rigar ya dan wuce gwiwarta, mayafi mai dan fadi ta yafah a kanta sannun ta fito zuwa palon gidan. Ammi na hangota ta mike"daga kan kujeran da take zaune ta karasa inda take"tare da kamo hannunta suka nufi kan dinning table din, Su sitty da jaddah tuni sun ci nasu a bincin sun koma dakin su"a lokacin, Habib ne kadai a kan dinning,dan haka suna zuwa ammi ta ja mata kujera ta zauna sannun ta dau plate zatayi servin dinta afiya ta rike hannunta tare da mikewa, Ammi ki barshi zan zuba da kaina ki zauna ke"ma na zuba miki, A'a Habibti ni kafin ki fito naci a binci. Shikenan ammi bari na zuba nawa toh,kedai kije ki kwanta ki wuta, Shikenan habinti na allah ya'yi muku albarka "ameen habib da afiya suka amsa a tare". Shafa kansu tayi sannun ta juya ta koma ciki ta barsu suci a binci. Zuba macaronin da miyar vegetable da yaji kayan lambu da taman kaza tayi, sannun ta zauna ta soma cin a bincin....... *Sakeena Ismail Cameroon ce*✍️ [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*✍️ (J.W.A) Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✏️ *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijint attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 39&40 Bismillahi rahmani rahim *********"Zuba macaronin da miyar vegetable da yaji kayan lambu da naman kaza tayi,sannun ta soma ci"beauty yau kuma ba magana?"dagowa ta'yi kallo daya ta'yi mai ta dauke" kai taci gaba da cin a bincin ta... Kafarsa y'ayi anfani dashi ya taka tata kafar ta kasan teburin,washhh ta fadi,sannun ta dago fuskarta ta dora akan Shi,suna hada ido ta fashe da kukan da take" rikewa tun dazu. Subhanallah ya allah ya fadi hade da rike" goshin sa"a'lamar baya son kukan nata" Mai haka ne" beauty,wai ba kin ce min bazaki kara kuka ba,shine yau kika'yi har sau biyu. Ba tare data tanka mai ba,ta ture plate din dake" gabanta ta mike" ta bar wajan,baki sake"yake" kallonta har ta bace" mai. Ruwa dake cikin glass cup din ya dauka ya dan kurba kadan sannun ya mike"ya bi bayan ta, Yana zuwa dakin ya tura kofar, ya'yi sa'a kuwa ta budu bata saka key ba,shigo wa ya'yi ya mai da kofar ya rufe, ganinta ya'yi zaune sai faman zub'da kwalla dake"kai in ka ganta zakayi tunani mutuwa aka'yi mata. Beauty tun a dinning nake"tambayarki mai ye faru amma K'ikayi min banza,ko nan din ne makiya so?saurin girgiza masa kai ta'yi a'lamar a'a,toh in ba haka ba toh meye saki kuka?"dan ni dai lfy lau muka zo har muka sauka daga cikin jirgi ma babu wata mas'ala,ko kuma dai maganar da nayi dazu a palo wansa nace wa su" Ammi sun shanza tunda kika zo?"eh shi ta bashi amsa",amma a zuciyarta kwata -kwata ba wannan Maganar ne ya sata kuka ba,asalima itta bazata ce" ga taka man- man a buda ya sata kuka ba. Toh shikenan kiyi hakuri bazan kara ba,amma dan (Allah dan annabi)karki kara wannan kukan,duk a bunda kinka san ya bata miki rai ki fada min,zanyi miki maganin shi da yar dan allah, a masayi na- na yayanki"kinji,kanta ta geda masa a'lamar toh... Murmuchi ya danyi mata cikin yake"itta ma ta mayar masa da martanin.. Yauwa ko ke" fah yanzu dai a bunda za'ayi ki tashi muje ki karasa cin a bincinki, a'a na koshi,babu wani a bincin da kikaci kice min kin koshi,ko dai dan danon ba irin na nigeria ba,dan dai naga dai akwai macaroni a can ma kuma ana defata da miya a can din ma. A'a kawai dai y'ayi sheni anjima naci, shikenan amma kina son coffee saurin geda masa kai tayi,sarkin coffee kenan bari na kira nashma ta kawo miki ya fadi yana tiro wayarsa daga cikin aljihun... Sannun y'ayi dialing number nashma din,bugu daya aka dauka,yauwa nasham ki kawo coffee guda biyu,yana kaiwa nan bai jira yaji mai zata ce ba ya kashe wayan... Sannun ya juya ya kalli afiya hade da fadin....yauwa yanzu za'a kawo mana kinga sai mu sha tare, Murmuchi kawai ta sake" masa"ba'a wani jima sosai ba a kayi musu nocking, mikewa y'ayi ya bude kofar sannun ya karbi coffee din hade da hi mata godiya ya koma ciki ya mika mata duka cup din sannun ya koma ya rufe kofar ya dawo dakin,ya zauna hade da karbo nashi cup din suka fara shan coffee din... *Bari mu leka bangaren nadra da iyayenta* Kasan cewa ba mota daya suka hau da Mahaifinta ba, saboda shima da motarsa ya zo,kasan cewa daga wajan aiki yake" Tuki take" amma hankalinta ba'a kan tukin yake ba,dan kuwa tunani take'yi akan afiya,wacece itta, saboda itta sanda suka tashi zuwa airport din ammi bata ce mata da wata habib ya zo ba?" Da taga abun na neman damun kwakwalwar ta sai kawai ta share zancen..hade da fadin toh wai ni ina ruwana meye damuwa ta,babu a bunda ya dameni suje Can su karata,in sonta yake ma ai ba aurenta zaiyi ba,tunda ansa mana rana,kuma da zaran munyi aure shikenan...da wannan tunanin dai ta samu hankalinta ya dan kwanta ta karasa gida ranta fari tass... *Bangaren basira* Wannka tayi ta fito,a kwatin ta- ta bude ta dauko man shafawa da turare sannun ta samu wuri gefen gadon ta zauna ta shiga shafah man.. Man take" shafa wa amma hankalinta ya tafi tunani. Tunani take yi kamar haka...dole nayi duk yanda zanyi na gano inda gidan su habib yake"toh amma wa zai tai maka min tunda ni bansan kowa ba a nan garin? Shiru tayi tana tunani,ko tunanin me tayi naga ta saki murmushi hade da cewa...yess na samo mafita,ko babu komai ai balatabe ne" kuma yana da kyau. Wayar telephone dake" cikin dakin ta dauka ta danna kira,ana dagawa,tace yau wa a kawo min a binci da lemo,can cikin wayan akayi magana kamar haka...toh amma madam baki fadi kalan a bincin da kike so ba,kaga a kawo min ko wana iri,amma ku bawa wannan mutumin daya nuna min daki dazu ya kawo min, Okay ya amsa sannun ya kashe wayan... *5 minute* Nicking taji anayi,wani irin murmushi tayi da itta kadai tasan ma'anarshi,sannun ta kara sa saka rigar bacci mai shara-shara wanda komai nata yake"a waje dan rigar da akwai da babu duk daya ne"... Tana karasa sakawa ta tauki wani turarenta wanda in ta shafa take" rikita maza dashi,amma bata san ta ya akayi takasa shawo kan habib dashi ba,a lokacin da suka hadu,dan ta shafa kafin ta shiga jirgi... fesa turaren tayi sannun ta nufi bakin kofar domin budewa, Najib kuwa har ya gaji zai juya ya koma sai yaji an bude kofar,kallon ta ya shigayi daga sama har kasa.... Lokaci daya ya hadiye wani irin yawu,sannun ya hada rai kamar bashi ba.. Najib na da kyau sosai,dan duk cikin ma'aikatan hôtel din yafi su kyau da gayu shiyasa yawancin matan da suke" zuwa Hotel din cewa suke suna sonshi wasu kuma suna masa so na sha'awa kawai da zarar ya'yi musu a bunda sukeso shikenan, Amma yawan cin su in ya kwanta da su dawowa sukeyi saboda yana gamsar da su sosai... Dan allah ka kai mun ciki,kai kawai ya geda sannun ya shiga ciki,dan yasan mai zai faru tunda shima ya na cikin bukata bazai ki bawa abunsa a binci ba... Maida kofar tayi ta rufe sannun ta karasa cikin dakin,lokacin kuma tuni ya a jiye a bincin da niyar ficewa sai yaji ta rungumeshi ta baya tana shinshina wuyanshi da kuma wani turarensa mai d'adin kam shi,a zafafe ya juya ya rungumeta,hade da cafke bakinta ya shiga kissing dinta da sauri da sauri Kamar ma yinwaci daya samu a binci.... Ni dai sakina nace allah ya shiyeku,sannun na fita na ja musu kofah na kara gaba🚶‍♀️ *Bayan kwata uku* Basira ta saba da najib sosai,kai in ka gansu sai ka ranse sunyi shekara da haduwa,nan ko kwana uku ne" kawai.. Tunda basira ta kwanta da najib taji duk duniya babu wanda take so sama dashi,dan tunda take"da mahmud bai taba gamsar da itta kamar yanda najib ya gamsar da itta ba" Da farko tayi anfani da najib ne wajan gano inda zata samo habib,amma daga baya da najib ya dan dana mata a bunda bata taba ji ba tunda take saduwa da miji,sai taga bata lokacinta ne kawai zatayi in tace lallai sai habib ne zai aure ta,kuma uwa uba ta gansa da yemmata har guda biyu dan haka yanke"shawara tayi kawai da ta rungumi najib dinta, Haka bangaren najib shima,dan tun da yake" bai taba jin mace yanda yake"so ba Kamar yanda yaji basira,shiyasa tun ranar da wani abu ya shiga sakaninsu"yaji yana sonta,kuma zai iya aurenta... Shiyasa tun lokacin suke"makale da juna a yanzu haka ma ya canza mata hôtel,saboda wancan hôtel din,a can yake aiki kar wata rana su gansu,a koreshi daga wajan aiki.. My dear saura kwana uhu na koma,zanyi missing dinka sosai cewar basira, Kiss ya danyi mata a baki kagan sannun ya saketa,ya shiga shafah gashin go'okin data kara a kanta, Har ta fudda rai zaiyi magana sai taji yace...nima zanyi missing dinki sosai my baby. Toh mai zai hana ka bini mutafi tare, a'a ina aiki ba yanzu ba,amma ke mai zai hana ki kara min kwana biyu... Wani irin harara ta dalla masa"sannun ta mike ta nufi toilet domin yin wanka,har ta kai bakin kofa sannun ta juya tace....bazan zauna ba nima tunda bazaka biyoni mutafi tare ba?" yanzu kam na tabbata ba sona kake'yi ba, Haba ta yaya zaki ce" ba sonki nake yi ba,ko so k'ike a koreni daga wajan aiki ne?"toh in an koreka sai me?ni zan samo maka aiki a nigeria in har zaka iya zama a can, Gaskiya a'a bazan iya zama a nigeria ba ,dan ina ji ana cewa ba'a samun wuta sosai ga kuma zafin bala'yi, Kai waye gaya maka duk wayennan, bayan kuma ba taba zuwa kayi ba... Wa yace miki ban taba zuwa nigeria ba?" Ni nagano haka,toh karya ne na taba zuwa, saboda hanya yabi damu,lokacin da zanje (Sudan)na saya a airport din ku mun shanza jirgin da zai kaimu can. Toh yanzu me mara barka da wanda bai taba zuwa ba?"toh bari na gaya maka baka da maraba da su"shikenan naji kiyi gaba zanxo daga baya, murmuchi kawai ta dan yi sannun ta karasa shiga toilet din... Kai kawai ya girgiza sannun ya koma ya kwanta... *Bayan kwana uhu* Yau ne basira ta koma Nigeria,inda najib y'ayi mata alkawari akan cewa insha allah shima zaixo,da haka dai suka rabu cikin so da kaunar juna,da suka tashi rabuwa kamar kar su"rabu dan har sun fara kewar juna... *Gidan su habib* Alhamdulillah yanzu kam afiya ta saba sosai da yan gida,kama daga ammi!sitty!abie!wacca ake"kira da jaddah! Haka ma bangaren nadra yanzu kam sun dan saba da afiya,saboda tana yawan zuwa gidan.. Afiya yanzu kam ta bar abubuwan da habib da nadra sukeyi a masayin shakuwa da kuma soyayan yen uwan uwantaka ne kawai... Kuma uwa uba itta bataga wani abu da habib din yake yiwa nadra a masayin soyayya ba,dan tafi ganin nata ne"a masayin soyayya... Yanzu ma dai nadran ce" ta zo tana zaune suna dan yin hira,duk da kuwa itta afiya a da hira ba ta dame ta ba"amma takan danyi yanzu ba laifi..... *Sakeena Ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*✍️ (J.W.A) Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✏️ *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 41&42 Bismillahi rahmani rahim **********Yanzu ma dai Nadra ce"ta zo suna z'aune suna dan taba hira,duk da kuwa itta afiya a da hira ba ta dame ta ba"amma yanzu kam ta kan danyi ba laifi... Wai ni kam ina habibi ne"dan tunda nazo bangansa ba ?"nadra ta fada da harshen turanci dan itta ba iya hausa tayi ba"itta kuma afiya bata iya larabci ba"sai dad daya kawai ta i'ya... Wllhy har yanzu bai dawo daga wajan aiki ba"afiya ta bata amsa"hade da cewa amma bari na kira shi dan yau naga ya yi yamma sosai,ta fada hade da dauko wayarta dake" kusa da itta.. A'a ki bar shi bari na kira shi nadra itta ma ta fada,kafin afiya ta ce wani abu tuni nadra ta yi dialing number habib har ta fara ringing... Z'aune yake"a cikin katafaran ofishin nashi,babba ne sosai, office din d'auke ya ke da k'aton teburi,sai kujeru guda biyu da in ya yi baki suke"zama a kai,sai kujera guda daya wadda yafi na baki kyau guda daya,wato na ma- mallakin office din kenan. Sai set din kujeru,da aka saka a can nisa kadan in ka wuce inda mai office din ya ke zama.. Z'aune ya ke"a kan kujerar ya kurawa hoton iyayensa ido. Ammi ce" da daddy sai shi da aka saka shi a saki ya, sun yi kyau sosai har sun gaji,ammi sanye take da bakar abaya mai masifar kyau,sai sarkan kwal dake" wiyanta da kuma kunnenta... Daddy da habib kuwa suna sanye da maroon din suit iri daya,sunyi kyau har sun gaji... A lokacin da za'a bude companyn ne sukayi hoton... Lokacin bai wani yin girma sosai ba,dan a lokacin bazai wuce" shekaru 25 ba,in har bai manta ba yan zu kusan shekara 8 da bude wannan companyn amma in anga yanda companyn yaci gaba za'a d'auka anyi shekara 20 da bude ta... Jin daya daga cikin wayoyinsa mai kira Samsung Galaxy S10 da ke"ringing ne"ya sashi mika hannu ya dauki wayan,kallon screen din wayan yayi ya shiga jujjuya wayan,sai daya dau kusan 2 second sannun ya daga ya kara a kunne,shiru ya yi ba tare da ya yi magana ba,itta ma bangaren nadra bata ce komai ba,jin shirun ta yi yawa ne" kuma tasan halinsa sarai in har ba tayi magana ba toh fah zasu zauna a haka,karshe ma in ya gaji ya kashe wayan. Sallama tayi masa"sai da aka d'au kusan 5 second sannun ya amsa" sallamar tata. Habibi ! nadra ta kisa sunan shi, na'am ya k'ike ya su babba ?suna lfy ina gidan ku, munji shiru ne ni da beauty,baka dawo ba shiyasa nace"bari na kira naji ko lfy,dan naga yamma tayi kuma gashi lokacin dawowarka gida har ta dan wuce". Eh wllhy aiki ne ya min yewa amma anjima kadan zan dawo ke dai in kin gama ki wuce" gida kawai saboda dare ya kusa yi, bai kamata ki dinga fita da daddare ba,cikin sanyin murya tace" toh habibi. Yauwa ina beautyn bani itta mu gaisa,mikawa afiya waya tayi,afiya ta karba ta sa'a a kunne tayi shiru, tana nan zaune har 10 second ba wanda ya yi magana,kinga beauty kiyi magana kar'ya kashe nadra ta fada. Mai makon ta yi magana kamar yanda tace"sai kawai tayi murmuchi ba tare da ta yi maganar ba. Habib kuwa da far'ko ya dauka nadra bata bawa afiya waya ba,sai da yaji tana cewa...kiyi magana kar'ya kashe sannun ya fahimci cewa ta bata magana ne kawai bata'yi ba.. Hummm mus'kilancin naki ne ta motsa yau kuma kenan habib ya fada hade da lumshe sexy eyes d'inshi masu shek'i,ai na dauka k'aima baza kayi maganar ba ?"afiya ta fadi hade da turo baki gaba kamar yana ganint'a. Bak'i sake nadra take kallon afiya hade da sansar mamaki,humm yanzu nice habib zaiy'i wa haka,ashe magana da ni ne baya so shiyasa in na kira shi idan banyi magana da wuri ba yake kashe wa,ai shikenan zanyi maganin abun,ta fada a cik'in zuciyarta hade da mika hannu ta karbi wayarta,sannun ta kara a kunne hade da fadin....yauwa habibi ka kirata da wayarta ni zan wuce" gida,tana kai wa nan ta kashe waya,hade da kallon afiya,yauwa ni zan wuce gida yamma tayi sosai tunda ba yanzu zai d'awo...ba ta k'arasa maganar ta ba ta ji wayar afiya na ringing,dauka ta yi ta kara kunne ta kara yin shiru irin na d'azu.. Kafin ka ce"mai narda ta dauki kajar ta-ta bar palon. Yau kam ko saya wa tayi wa su ammi sallama ma ba ta yi ba,dan kuwa tana barin palon ba ta saya ko i'na ba sai wa jan motar ta,tana zuwa ta bude ta shiga ta kunna ta,ta ja ta -ta bar gidan. Ammi da ta fido daga part din i'yayen ta kenan zata koma part din ta -ta hango ta- ta fito,sauri ta yi ta samu ta kara sa inda take amma kafin ta K'arasa har ta ja motar ta- ta bar gidan. Humm daga ganin a kwai mas'ala cewar ammi, cik'in sauri ta karasa palon, tarar da afiya z'aune ta yi,ta na waya da habib, afiya na ganin ammi ta shigo,ta cewa habib sai an jima. Sai ka tawo ga ammi na ta zo,bata jira taji mai zai ce ba ta kashe wayan. Ammi dai kallon ta kawai tak'e,tashi ta yi ta dawo kan kujeran da ammi ta ke z'aune ta zauna hade da cewa...ammi na ya dai?"meye samu nadra naga ta fito a fusa ce"? wallahy ni ammi lfy lau muka rabu da itta,muna nan zaune ma ta ce min tunda tazo bata ga yaya habib ba,nace"mata bai dawo daga wajan aik'i ba har yan zu,amma bari na kira shi, shine na d'auki waya ta zan kira tace" na bar shi bari itta ta kira shi,shine na kyale ta -ta kira shi,bayan ta kira shi ne ya suka yi magana bayan sun gama ya ce" mata ta bani waya shi ne" fah ta ba ni,muna cikin magana da shi ta fusge wayar ta daga kunne na ta ce masa"itta tafiya zata yi ya kira ni a waya na muci ga ba da magana,shine fah ya kira a waya ta ina daga wa naga ta bar palon,ni wllhy ban kula cewa ranta ya ba ci ba"dan ni bamma ga abun bacin rai anan ba"afiya ta yi maganar da iya gaskiyar ta. Bayan ammi ta gama saura'ron afiya ne"ta saki murmuchi,hade da fadin... kar'ki damu na fahimci komai kuma baki da laifi,habib ne"mai laifi kuma in sha allah zan yi masa"magana i'dan ya dawo.. Toh ammi amma ni ban ga abun da ya yi a nan ba"kar'ki damu beauty. K'an ta kwai ta geda, *Bayan wata biyu* *Kano Nigeria* Washhh mommy ya fadi hade da dan kwan ciya a kan cinyar ta,ya dai my boy,wllhy mommy na gaji sosai,washhh wllhy nima Mommy na gaji Ibrahim shima ya fada hade da kwanciya a gefen mohseen. Dan Allah ni ku daga ni karku kar ya min ka fah aunty ta fada hade da janye k'afarta... Gaskiya kin yi dai- dai Mommy na shiyasa nake" sonki,aisha ta fada hade da yi musu gwalo.. Mommy k'inganta ko, Ibrahim ya fada hade da turo baki gaba. Wai me a ke yi ne nake"ta ji tun daga bakin kofah.. Kallon inda sukaji maganar suka'yi lah yaya safwan ashe kai ne"aisha ta fada.. a'a bani ba ne"ke ce"ya bata amsa"a lokacin dariya ta danyi sannun ta gaisheshi,ina wuni yaya safwa ,lfy ya amsa"a takai ce"sannun ya karaso cik'in palon,ya zauna daya daga cikin kujerun gidan... Mommy ina wuni,lfy lau safwan ina takwara ta,wllhy tana dawowa daga makaranta tayi bacci, Allah sarki ta gaji shiyasa,eh wllhy ai wannan yinin da suk'eyin ne shi yasa ni ina ga wata zan nemo musu in ya so sai su dinga zuwa islamiya da ban, a'a gwara dai ka barsu a can din tunda hade take"da islamiya, shikenan tunda kin ce" a barsu na bar su"din. Y'auwa gwara dai... murmuchi kawai ya yi sannun ya mike ya ce"bari na dan je wajan Aliyu yanzu zan dawo,okay shikenan sai ka dawo ka gai she min da hajiyarsa,okay zata ji in sha allah sannun ya mik'e,kallon Inda su Mohseen suke zaune ya yi yace"..toh mai kuma ya samu su wayen nan naga sai faman cin magani suke yi?"wai saboda mommy tace"su ta shi daga kan cinyar ta shiyasa suke fushi mtsiii ya ja saki hade da cewa humm ba ku da abun yi ne shiyasa ni kunga tafi ya ta......, *Sakeena Ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena IsmailCameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*✍️ (J.W.A) Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✏️ *Marubuciyar* *bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing...✍️* Page 43&44 Bismillahi rahmani rahim **********"Kallon inda su Mohseen suke"z'aune ya yi yace"toh mai kuma ya samu wayen nan naga sai faman cin magani Suke yi?"wai saboda Mommy tace"su tasar mata daga kan cinya shiyasa suke ta fushi, mtsiiii ya ja tsaki hade da cewa...humm ba ku da a bun yi ne"shiyasa ni ina dashi kun gama tafiya ta,ya fadi hade da barin palon... Kunga ku yi hak'uri kunji?"maza ku tashi muje ku yi wanka ku sauko ku zo ku ci a binci,kunga itta nan da wata daya ma bar muku gidan zata yi badan an kara wata daya ba ma da yanzu shirye shiryen bikin ake yi...yanzu dai maza ku tashi kuje ku yi a bunda nace,toh mommy suka ce a tare sannun suka mike suka nufi ciki domin yin a bunda aka sa su.. Me haka mommy aisha ta fada,me haka kamar ya?daga f'adar gaskiya,ni wllhy duk baby ne ya ja min da yanzu anyi auren kun dena ganina, da yanzu shikenan tunda kun gaji dani,ta fada hade da mikewa... Toh mara kunya ba dai aure ba,zaki ne"ina matsayin uwarki bazan miki baki ba. Allah dai ya sa za'a yi damu ya kuma nuna ma na lokacin ya baku zaman lfy, "ameen ya Allah mommy na,aisha ta fadi a lokacin da take" dawowa cik'in palon. Mommy na ki yi hak'uri wllhy wasa nake yi,ina sonki deyewa ne shiyasa nake kishi in na gansu a kan cinyar ki gashi kuma zan tafi,ta fadi hade da rushewa da kuka,kwantar da kanta tayi a kan cinyar Mommy,sha fah kanta Mommy ta yi hade da cewa...na sani mamana kuma nasan kishi k'ike da su"nafi kowa sanin halinki mama na,amma dan Allah ki dena musu" haka ke da zaki dinga ja su a jiki ma sosai yanda in kin tafi zasu yi missing d'inki,amma yanzu yanda k'ike musu zasu fi kowa son ki bar gidan. Yanzu mohseen da dan auta sunfi son na bar gida ?"toh in dai haka ne kuwa dole na gyara kafin na bar gindan, yanda in na bar gidan zasu dinga zuwa waje na,ta fadi hade da mik'ewa ta dauk'i gelen ta dake"kan kujera ta ya fa,sannun ta kalli Mommy tace"y'auwa Mommy bari naje wajan bestie,yanzu zan dawo. Matar safwan ce take kira da bestie saboda kawarta ce"safwan ya aura. Shikenan sai kin dawo,amma karki dade saboda hajiya Sudan takusa karasowa,dan dazun nan muka yi waya da itta,da toh mommy ta amsa"sannun ta bar palon. *Gidan su afiya* Mama ce" kwance a kan kujerar dake"cikin palon,ta rame ta yi baki. Yanzu kusan sati biyu kenan da gama cinye kudaden da afiya ta bar mata a cik'in jaka. A yanzu haka ko kudin siyon a binci bata da shi ballanta na -na man shafawa. Dalilin daya sa cikin sati biyu ta rame tayi bak'i kenan... Sallamar da taji a palo ne yasa ta-tashi zaune daga kwancen da take yi... Yusuf ne ya shigo palon hannunsa rike da bakar leda,karasowa ya yi ya zauna a kasan carpet din,hade da mika mata ledan dake hannunsa yana cewa.... hajiya ga taliya da mai da magi na siyo miki ya fadi hade da zazzago a bunda ke cikin ledan.. Sai ga taliya guda biyu da manja da magi guda uhu ya baiyana... Yauwa yanzu kinga hajiya wannan zata i'shemu yau da gobe,tunda akwai yaji sai ki defa mana muci ko?" Ohhh ni fatima yanzu nice nake siyon a binci a waje,ikon Allah duniya juyi -juyi Allah sarki afiya ko tana ina, kullun sai ta min magana akan a bincin da nake tarawa a gaba na ina ci... Gashi in nagama ci zubarwa nake yi bana bawa kowa, Allah na t'uba Allah ka yafe min ya Allah ina son yaya na kawai girman kai da son a bun duniya ne ya ja min har bana iya kula da su"Allah gani gareka na tuba... Allah ka yafe min badan halina ba... Allah nasan ban kyau tawa yayana ba,amma nayi alkawari yanzu in sun dawo ko bani da komai,zanyi farincikin idan naga yaya na,zanyi murna kuma in rungumesu hannu bibbiyu na nuna musu k'auna da kuma soyayya da bam musu" ba a da... Shiru Yusuf ya yi yana kallon yanda take kuka tana nemon yafiyar Ubangiji dana yayan ta,bata ma san yana mata vidéo ba,dan kanta na kasa... Ganin zata dago ne yasa shi yin sevin da sauri,hade da a jiye wayan a kan carpet... Hajiya ki yi hak'uri zan shiga ko ina na nemo miki su... Dan Allah da gaske k'ake Yusuf zaka nemo min yaya na?"in sha Allah zan nemo miki su,a duk inda suke"cikin kuka ta shiga yiwa yusuf godiya....nagode nagode sosai yusuf Allah ya saka maka da alkairi ya jikan iyayen ka, kai ka dai baka tafi ka barni ba duk masu aikin sun gudu saboda kudi na ya kare... Ameen ya Allah mama. Mun zauna da afiya lfy,dan na tabbata su din ma dinya ce ya sa su tafiya,ni dai ina nan bazan tafi ba,yanzu dai ki tashi kije ki dafa a binci kici,kai mama ta geda sannun ta mike,ta dauki ledan ta nufi kitchen. Da kallon t'ausayi yusuf ya bita da shi"a zuciyarsa kuwa fadi yake ai itta ta jawa kanta,mikewa ya yi ya fita ya koma dakin sa... Yana zuwa dakinsa ya shiga ya ja kofar ya rufe da Key sannun ya karasa Cikin dakin ya zauna kan katifar shi"sai ya yi dialing number habib... *Dubaï* Kasan cewa yau Friday shi'yasa yau bai je wajan aiki ba,saboda baya zuwa ranar Friday.. Yanzu ma dai dawowarshi daga sallar Jumma'a kenan,ya shiga daki ya dan samu ya danyi bacci sai yaji wayarsa ta fara ringing,yana dubawa yaga sunan yusuf ne yake"yawo a kan screen din... Kashe kiran ya yi ya kira shi da katinsa,bugu daya Yusuf ya dauka... Assalamu alaikum ranka ya dade, walaikum salam Yusuf ya kake ya gida,da Mama?wllhy lfy lau alhamdulillah ranka ya dade,ma sha Allah,ya ake ciki ne toh? Da alama munyi nasara ranka ya dade.. Allah ko yusuf?kwarai kuwa ranka ya dade yanzu ma na tura maka wani video a WhatsApp, okay rike wayan bari na duba,da toh yusuf ya amsa... Shiga cikin Whatsapp habib ya yi ya bude video ya shiga kallo,wani irin murmuchi farinciki ya yi har fararen hakoran sa suka baiya na... Ma sha Allah ya furta hade da kashe video... Gaskiya naji d'adi sosai yusuf kuma na gode da wannan shawaran daka bani kwana kin baya akan cewa mu kwashe sauran kayan a bincin muce masu aiki ne suka sace suka gudu dashi.. Gaskiya naji dadi sosai kuma ina godiya sosai da sosai,in sha Allah in har nazo nigeria ina da k'yauta na mu samman da zan baka... Yanzu dai kaci gaba da aikin ka,dan a bunda ya rage mana kadan ne. Toh ranka ya dade amma fah ni ina gani gwara mu barta a haka,dan ta yi na d'ama sosai... A'a yusuf mu kara mata sati biyu,dan zan zo nan da sati biyu in sha Allah,kuma kaci gaba da zuwa kana duba Mohseen ma,duk da kuwa na san aunty na kula da shi sosai amma dai in yana dan ganin ka zai fi jin d'adi,kuma zai tabbatar ba'a manta da shi ba,saba nin in baka zuwa... Shikenan ranka ya dade Allah ya kawo ka lfy, "Ameen na gode yusuf bari na barka,sai munyi Magana,toh ranka ya dade sai anjima... Okay habib ya fadi sannun ya kashe wayan. Mikewa ya yi ya nufi dakin ammi domin bata wannan dadda dan labarin... Kwance take"ta yi ruf da ciki,fuskarta duk ya kumfura,duk da idon ta a rufe suke amma zaka iya fahimta cewa kuka ta yi.. Tunani take yanda suka yi da ammi kwaki uku da suka wuce... *Kwana uku da suka wuce* Ammi shirye shiryen me kuke ta yi ne,dan naga kwana biyun nan kunyi buzi deyewa afiya dake kwace akan cinyar ammi ta tambaya,daka tar da shafa kan afiya da ammi take yi ta yi... Sannun ta dagota ta tashi zaune"cikin mamaki ammi take"kallon afiya hade da cewa wai beauty kina nufin duk yanda k'ike da yaya habib d'inki amma bai fada miki zaiy'i aure ba?"cikin firgici da mamaki daya kasa boyuwa akan fuskarta take kallon ammi,dan bata ga alamar wasa akan fuskarta ba,ko kadan,da sai tace"wasa take"mata, Dagewa tayi ta seta kanta sannun ta ce ammi aure fah kika ce? Kwarai kuwa beauty dan tun kafin ya je nigeria ma aka saka musu rana,a yanzun haka,ana dawowa daga bikin aisha da sati daya za'ayi na habib... Toh ammi amma wa zai aura?narda mana beauty,nifah abun ya daure min kai sosai saboda naga kun dan saba da itta... Murmuchin y'ake ta yi hade da cewa Allah ya sanya alkhairi ya basu zaman lfy,da "ameen ammi ta amsa"sannun ta mike"yauwa habibty bari naje nayi sallahr la'asar,kema ki tashi ki yi, toh ammi,ta fadi... Barin dakin ammi ta yi.. Ammi na fita ta jingina da jikin kofar,babu a bunda taji sai kukan da Afiya ta saki... Cikin t'ausayi ammi ta juya ta bar bakin kofar... Tun ranar take wasan buya da habib,tana ganin lokacin dawowar shi"ya yi sai ta koma dakin ta kulle kofah... Duk sanda ya dawo bai ganta a palo ba, yakan je dakin ta amma in ya taba sai yaji a kulle... A haka dai yake juyawa ya koma palo jiki babu kwari,ya ke zuwa palon ya tambayi su ammi ko bata nan ta tafi wajan nadra ne ?sai su ce masa tana nan.... Tun abun baya damun sa har ya zo ya fara damun sa... A kwana kin kadan da ya yi bai ganta ba har ya dan fada... Duk wanda ya ganshi dauka yake saboda auransa ya kusa ne shiyasa ya rame.. *Cigaba* Share guntun kwallan da ya zubo mata ta yi,sannun ta mike ta nufi toilet domin watsa ruwa... Yana zuwa dakin mahaifiyar sa, nocking ya yi ta bashi izinin shiga,sannun ya turo k'ofar ya shigo,tarar da itta ya yi zaune itta da sitti ko mai suke tattaunawa oho.. Habibi kai ne,eh sitti nine amma ba wajanki na zo ba wajan ammi na nazo,ronkoshi ta kai mai a kai ya kauce yana murmushi.. Ammi dai babu a bunda tace sai murmuchi da itta ma ta danyi,tana kallon dan nata da ya dan rame,cikin sanyin murya tace"ya dai habibi mai muka samu kake nema na,ai ko kaman jira ya ke dama ta yi magana,a take ya kunna mata video da mama take kuka hade da nemon y'afiyar su"afiya.. Duk da ammi ba wai i'ya hausa tayi sosai ba amma ta fahimci komai.. Alhamdulillah gaskiya naji d'adi sosai na taya habibti na murna,d'ama mu baki daya, naji d'adi sosai habibi na,ina al'fahari da kai, Allah ya yi maka albarka "Ameen ya amsa"sannun ya karbi wayarsa da ammi take mika masa. Hannu ya sa ya karba,sannun yace...bari naje na nunawa beauty. A'a habibi ba yanzu ba ka dan bari sai kaje kagani da idanunka tukun sai kazo ka gaya mata.. Shikenan ammi. Ni bari naje na dan kwanta kadan k'afin la'asar ta yi, shikenan habibi sai anjima,da toh ya amsa"sannun ya bar dakin....., *Sakeena Ismail Cameroon ce✍️* [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*✍️ (J.W.A) Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi.✏️ Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske* Page 45&46 Bismillahi rahmani rahim **********Ni bari naje na dan kwanta kafin la'asar Tayi, shikenan habibi sai anjima ko.da toh ya amsa sannun ya bar dakin,ta bakin k'ofar dakinta ya zo zai wuce sai kuma ya tsaya,kara sowa ya yi bakin kofar nata ya rike hannun kofar da niyar mur'data.ko mai ya tuna naga ya fasa. Sakin hannun k'ofar ya yi ya bar bakin k'ofar ya nufi part dinsa" *Bayan sati daya* Kano Nigeria Okay babu damuwa Allah ya kawo ku lfy aunty Maryam ta fada,ta cikin waya Ammi ta amsa da Ameen,shikenan bari na barki ki gama shiyawa Aunty Nuri, murmuchi kawai Ammi tayi,kai kawai Aunty Maryam ta girgiza sannun ta kashe wayan.kallon inda aisha take zaune Aunty Maryam tayi..zaune take" sai kyalli da sheki take tayi da kaganta kaga Amarya, saboda ko ba'a fadawa mutun ba in ya ganta zai fahimci itta din Amarya ce"saboda irin sheki da kamshi da take'yi.. Ya dai Amarya ke da na barki a d'akin gyaran jiki taya kika biyoni a nan kuma?"haba Mummy yanzu shikenan dan na biyo ki shine zaki Magana, Aisha ta fadi hade da share guntun kwallan daya zubo mata. Tashi daga kan kujera mai zaman mutun biyu dake cikin dakin Aunty Maryam tayi ta karasa kusa da gadon,ta zauna Gefenta, hade da kamo Duka hanna yenta biyu ta hada da nata,sannun ta fara magana kamar haka..haba Mama na! haba indo na!sai kace"karamar yarinya,haba Mummy yanzu ni ba karamin yarinya ba ne?kici gaba da kiran kanki da kara min yarinya,idan auta da Mohseen suka jiki babu ruwana. Mummy toh ai ko nayi girma amma ai a wajanki ni kara min yarinya ce" Shafah kanta Aunty Maryam tayi hade sakin murmushi. Haka ne,ke yarinya ce a waje na amma ki dena bina kamar jela. Dazu ba na bar hajiya Sudan ta hada miki ruwan wanka da turaruka ba,toh meyesa kika biyoni baki saya kin yi wanka da ruwan data hada miki ba.bayan kinsan sarai irin kudaden dana kashe wajan hada miki a bubuwan da kuma irin wahalan dana sha kafin ta amince tazo ? Nasani Mummy yanzu zan je na yi,amma d'azu naji kamar kina waya da Ammi,eh itta ce"Aunty Maryam ta bata amsa"amma dai tare da beauty zata xo ko? a'a ba tare zasu xo ba,itta sai bayan biki Habib zai je ya dauko ta. Haba Mummy dan meyesa baza a zo da itta ba, Dan Allah malama rufe min baki yaushe ma k'ike santa,ba nace miki zata zo daga baya ba. Shikenan Mummy Allah ya kawota lfy, Amma pls "ki ban number dinta in "kina dashi. Bani dashi ki tashi kije "Dan Allah Hajiya na can na jiranki. "Yanzu shine na hada miki ruwa k'ika gudu ko? cewa Hajiya Sudan d'ake saye a bakin k'ofar, Kallon inda take suk'ayi wata mata ce" fara mai dan jiki,kallo daya zaka mata ka fahimci itta din balarabiya kasar Sudan "Ce,duk da tazarar su amma kana iya jiyo kamshin humra da turaren wuta dake tashi daga jik'in ta. Murmuchi Aunty Maryam tayi hade da cewa.. "Hajiya kamar kin sani kuwa tun d'azu nak'e ta "faman yi mata Fada,amma taki tashi. gaskiya gwara da k'ika zo, murmushi kawai Hajiya Sudan dayi. Sannun ta maida duban ta kan aisha. Yauwa tashi "Mu tafi, baki aisha ta turo gaba hade da mik'ewa. Lokacin tuni. Hajiya Sudan ta dade da barin bakin kofar. Bin bayanta tayi, kai kawai aunty maryam ta Girgiza, sannun ta mike Ta shiga toilet. *Dubaï* "Zaune take" a dakin Ammi, tun lokacin da Akace ba da itta za'a tafi nigeria ba jikin ta ya ke a "Sannye, sai bin Ammi kawai take da kallo. Dan har ga Allah tana son zuwa nigeria taga kanninta, uwa uba dayi Kiwar kasarta sosai. Har Ammi ta gama shiryawa bata sani ba. "Cikin t'auyawa Ammi ta karaso kusa da itta ta zaune gefen gadon, sai a lokacin Afiya ta d'ago ta kalleta, batayi wata _wata ba ta fada jikinta, Hade da fashewa da kuka, Ammi zanyi kiwarki sosai ta fadi. Safa bayanta Ammi ta "Shigayi tana yi tana danyin murmushi, dan tasan tsaran kiwar kaninta da kasarta take yi. "Kiyi hakuri habibty ba "Zamu dade ba "zamu dawo, muna dawowa sai habib ya kai ki kije kiga kanin naki kinji, dan nasan ba kiyata da zaki ne ya saki kuka ba. Ammi ta fada hade da sakinta tana murmushi. Rufe fuska Afiya tayi Tana murmushi, oya tashi muje mun kusa makara dan jirgin mu ya kusa tashi, kai Afiya ta "Geda sannun ta mike, gyara mayafin dake kanta tayi ta sa hannu ta dauki yer karamin akwatin kayan Ammi dake wajan. Rataye jakarta Ammi tayi, sannun suka nufi kufar dakin,hannu Afiya ta sa ta murda hannun kofar,murdawarta ya yi dai _dai da murdawar da habib ya yi, dan haka a take kofar ya bude suka bugi goshin juna, washhh "Suka fada a tare, lokaci daya ya rikice yana fadin sorry beauty, bansan kina wajan ba wallahi,dan Allah kiyi hakuri muga waja dana buge ki. Duk a lokaci daya ya fadi Maganar Afiya kam rasa mai zatace ma "tayi. Ammi kuwa cikin al'ajabi Take kallon habib dan kana ganin goshin sa kasan yafi Afiya jin zafi, dan wajan har ya danyi ja ga kuma kumbura da ya danyi. Amma mamaki ya hanata magana. Yaya habib nice fah na bugeka, ba kai ba. Dan ban wani jin zafi sosai ba, kai kuwa goshinka har ya dan kumbura, dan Allah "kayi hakuri, bai kula ta ba sai ma matsowa da ya karayi sosai kusa da Itta, har "Suna jin Numfashin juna. Goshin nata ya shiga dubawa sai daya tabbatar babu ko mai sannun ya sauke ajiyar zuciya,sakin akwatin hannunta tayi ta saka tattausan hannunta a kan wajan daya dan kumbura ta shiga mulmula wajan, washhhh good ya fadi da dan karfi, ai batayi wata wata ba ta saka bakinta a kusa da wajan ta shiga hura masa wajan, wani irin lumshe ido ya yi hade da sauke ajiyar zuciya. Uhummm sukaji a bayan su, suna dagowa suka ga Ammi saye, kai kawai Ammi ta girgiza hade da jawo akwatin ta dake kusan da afiya, ta fita ta barsu" cikin jin kunya Afiya ta bi bayan ta. Shima dai habib mara "Musu baya baya ya yi. "Suna zuwa babban palon gidan suka tarar da Su ummi da Abie har ma da Najwa suna jiransu" Suna ganin su suka mike, wai tun d'azu mai kuke yi ne a dakin? Gashi har "Kun kusa makara Abie ya fadi. Ammi bata ce komai ba sai ma jan akwatinta da taci gaba da yi ta bar palon, dan tasan ko ta saya ma bata san wacca Amsa zata ba su ba. Abie ma dai bai sake cewa komai ba ya bi bayanta ya fita, sauran ma suka mara mishi baya. Amma ban da najwa, Kara sowa tayi gaban habib tasa hannu ta taba goshin sa, hade da cewa.. Subhanallah Habibi mai ya same ka a goshi kuma, bayan lafiya lau ka bar palon nan? "Tire hannunta ya yi daga Kan goshin sa" Ya bude baki da niyar yin magana Afiya ta riga shi cewa... Wallahi kofah na zo budewa ban san yana wanja ba na bugeshi. Haba beauty mai yasa bakiya kula ne? Najwa ta fada cikin masifah, sorry ban sani ba Afiya ta bata amsa hade da jiyowa zata bar wajan ya dakatar da itta ta hanyar rike mata hannu. Juyowa tayi ta kalli hallonta daya rike ta kallesa. Sake ni zan je wajan su Ammi suna jira. Bai sake ta ba sai ma mai da kallon sa da ya yi kan Najwa, hade da cewa karki kara daga mata murya, dan ba sa'arki ba ce, kuma da kike cewa ba kula, nice nan na bugeda ba itta ta bugeni ba, toh amma meyesa nata bai kumbura haka kamar yanda naka ya kumbura ba? Kin ga dan Allah najwa ki dena wannan maganar, ni kin sani na kusa makara ma, yana kai wa nan ya ja hannun Afiya, suka bar wajan, kamar soko haka Afiya take binsa. Duk a bunda ya faru a kan idon Ammi, ya faru, dan haka bata ji dadi a bunda Habib ya yi wa Najwa ba, dan haka su habib na barin wajan ta karaso inda najwa take saye,hade da riko hannunta. Dagowa najwa tayi ta zuba wa Ammi ido,kukan da take rike wa tun dazu ne ta saki. Rugumota Ammi tayi ta shiga bubbuga bayanta. Yi hakuri Najwa, naji duk a bunda ya faru kuma insha Allah zanyi masa" "Magana. Yanzu dai zo mu" tafi kar "Mu makara, a'a Ammi kuje ni dama ba zuwa aireport zanyi ba, nazo ne kawai nayi muku sallama ta fadi hade da dauko jakarta dake ajiye akan kujera. Allah kiyaye hanya ya dawo daku lafiya, ta fadi hade da juyowa ta bar wajan. Kai kawai Ammi ta girgiza. Cikin mutuwar jiki Ammi ta juya ta bar palo. "Su habib kuwa har suka zo suka wuce"Ammi ba "Su ganta ba, haka ma Afiya. Wai ni ina Nurian take" ne. Ko so k'uke ku rasa jirgin ne. Abie ya fada, bari naje na dubata Afiya ta fadi hade da juyowa, da niyar zuwa kiranta, sai suka ga Ammi. Motar najwa data wuce yanzu ta fita suka bi da kallo, hade da kallo. Ammi na dauka najwa zataje aireport, Afiya ta fada, a'a tace d'ama tazo tayi mana sallama ne kawai. Shiga motocin su_suka yi ba tare da sun sake cewa koma. Draver ya ja motar suka bar gidan. Kasan cewa sun kusa makara, shiyasa suna "Zuwa aireport basu fi mintuna 10 ba jirginsu" ya daga zuwa kasar Nigeria. Sanda jirginsu"Ammi zai tashi ji take kamar ta bisu amma ba hali, tana ji tana gani jirginsu Ammi ya daga. Sai da jirgisu Ammi ya daga sannun suka shiga mota suka nufi gida. *Kano Nigeria* Tunda akan tashi da safe ake ta shirye _shirye a gidan, kallo daya zaka wa (Alhaji muhammad habib ibrahim) ka gane cewa yana cikin farinciki. Hajiya Maimuna kam ba karamin haushi abun yake bata ba, tana dai denne wa ne kawai saboda kar ya gane suzo suyi fada ya koma wajan Hajiya Nuria ya barta. "Wasu yemmata ne guda biyu suka shigo palon da ledoji niki_niki a hannunsu" Sallama suka yi daddy ya amsa musu"amma banda uwar gaiyar. Yen albarka kun dawo. Eh mun dawo daddy mufeeda da aisha suka hada baki wajan fadi. Washhh wallahi mun gaji sosai daddy mufeeda ta fada hade da ajiye ledojin dake hannunda ta zauna akan kujeran mai zaman mutun biyu. ayya sorry ku dan wuta sai kuje ku dan samu ku dan watsa ruwa. Toh daddy aisha ta fada itta ma hade da zama akan carpet din dake malale sakiyar palon. Wallahi uwata ke raguwa ce" Haba daddy siyayyan fah na deyewa, kuma ga rana. Ni wallahi badan anfi samun komai a kasuwa ba ma, da super market muka je. Ni wallahi shiyasa nake jin dadin kasar waje, duk kayan girkin da kake so zaka samu a super market, amma banda nan. Aisha ta karashe magana hade da mikewa. Ai laifinka ne Alhaji gasu"chuchu na nan, amma kace"sai su zasu je suyi chefene, Hajiya Maimuna ta fada, ci kanki daddy bai ce da itta ba, sai ma kallon Aisha data nufi dakinsu"ya yi hade da cewa, yauwa mamana fara zuwa ki kira su chuchu "Suzo su kwashe wayennan kayan. Da toh aisha ta amma, hade da dawowa palon, ta zo ta wuce su ta nufi kitchen. Batafi minti daya ba ta dawo tare da wata matashiyar muturwa da bazai wuce sa'ar ta ba. Yauwa chuchu kizo ki kwashe kayan aje ayi sauri a fara aiki dan nasan sun kusa isowa, toh Alhaji cewar chuchu, sannun ta sukunya ta fara kwashe kayan. Mikewa mufeeda tayi itta ma tabi bayan Aisha ta wuce"daki...... Fulanin jajirtattu ce✍️ [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/FJyfKf65hJQApnYM0DV2BU 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *bazan zauna da kishiya ba,* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske...Typing*✍️ https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page47&48 Free book Bismillahi rahmani rahim ******* "Mikewa itta ma Mufeeda tayi tabi bayan Aisha suka nufi dakinsu" "A palo kuwa Mummy ce"ta kalli Daddy ta fara "Magana kamar haka... A gaskiya Alhaji bai kamata ka dinka aikan yaran nan cikin rana ba" Kafi kowa sanin cewa basu"saba da rana ba"amma ka dage lallain Sai sunje sunyi cefene girkin da za'ayiwa yan "Gwal. "Ci kanki Daddy bai ce da itta ba". "Sai ma mikewa da ya yi ya nufi bakin kofar fita, "Yana duba agogon dake daure a kan tsintsiyar Hannunshi. " Yana zuwa kofar bakin gate ya umarci mai gadi dama sauran ma aikatan mazan da suyi alwala su tafi Masallaci, dan an soma kiraye kirayen Sallar Azahar. "Da toh suka amsa mishi sannun suka soma yin alwala, a lokacin kuwa tuni ya dade da fita. A palo kuwa,cikin takaici "Da jin haushi na rashin kulata da Daddy bai ba, ta mike ta nufi sama" "A kitchen kuwa su chuchu ne suke ta faman aikin girki, su sauke wannan " Su dora wancan"itta da baba Safiya. *Bayan awa uku* Tun daga nisa suka hangosu"suna saukowa, kallo daya zaka musu"ka gane su din d'a da uwa ne"saboda babu a bunda Habib Ya barwa Hajiya Nuria, kama daga hasken fata hanci baki, duk iri daya dana Habib, ido ne kadai na Mahaifinsa" Tun daga nisa yake sakar musu kyekkyawar murmushi, har suka karaso inda su Daddy da Hajiya Maimuna da su Mufeeda suke" Welcom my bro cewar Mufeeda hade da rungume Habib din. Thank you sis, amma ki sakeni kefah yanzu ba yarinya bace"kin yi girma. Ya fada hade da janye jikinsa" "Taho yer tsohuwata ki bar wannan fitinenniyar, Habib ya fadi hade da "budewa Aisha hannu. Baki Aisha ta turo gaba hade da fadin "haba bro yanzu ni ce" Ma tsohuwa. Okay bake bace sorry. Nima dai bari naje naji dumin Nuri ta. Daddy ya fada hade da karasowa kusa da Ammi ya bude hannayensa da niyar ya rungumeta, Ammi ta wurga mai harara hade da sakin murmushi. "Kaga hubby nifah sis dita zan runguma ba kai ba. Ammi ta fadi, hade da karaso inda Hajiya Maimuna take tsaye ta cika fam kamar zata fashe, har tayi na damar binsu" Da tayi. Ammi kuwa bata ma lura da fuskar Hajiya Maimuna ba ma, ballantana ta tantance farinciki take ko akacin haka. Rungume Hajiya Maimuna Ammi tayi tana fadin sannu sis ya Nigeria?" Wllhi alhamdulillah, ya k'ika barosu" Ummi da Abie? "Wallahi suna lafiya" Ammi ta amsa"a lokacin da take sakin Mummy. Kallon Daddy tayi tana cewa yauwa Hubby muje naje na samu na huta dan wallahi na gaji sosai wallahi na kwana biyu banyi tafiya ba. Kefah taruwa ce"wallahi, naji muje Ammi ta fada tana kara sakin wani murmushi, da yake kara rikita Daddy. Dan ba karamin so yakewa Ammi ba, har baya iya boyewa. "Shiga mota dukansu sukayi, inda Daddy ya shiga da matansa a mota daya, shi kuma Habib ya shiga motar da su mufeeda suka zo dashi suka wuce" gida. *Bayan Sallar Magariba* Fitowa ya yi daga bangarnsa"sai faman kamshi yake, yasha mlik gesna, wanda aka masa dinkin jomfa dashi, kansa babu wula, gashin nan sai sheki yake" Kai in kaga yanda ya yi kyau zaga dauka biki zashi, nan ko ba ko ina zai je ba illa gidansu"Afiya. Dama ya fadawa Daddy d'azu da suka dawo daga Masallaci, dan yau ya bishi sun je tare". *Gidan su Afiya* Mamace kwance"akan kujerar palo na mai zaman mutun uku"ba lafiya tun dazu zazzabi mai zafi ya rufeta. Gefe guda kuma Yusuf ne zaune a kasar carpet ga magani daya bare a hannunsa, sai kuma ruwa daya debo a cup ne yake mika mata, dan Allah Mama ki daure ki tashi kisha maganin kafin zuwa gobe muje a Sibiti,mikewa Mama tayi daker ta zauna, duk ta kara ramewa ga duhu data karayi, kamar ba Mama da aka sani a baya ba. Maganin da ruwa Yusuf ta mikawa Mama, karba tayi ta sha ta mika masa cup din ya ajiye. Kwanciya zatayi sukaji ana Sallama A bakin kofar palon. "Habib ne ya shigo, cikin palon jikinsa duk ya yi sanyi da yaga yanda Mama ta koma, duk da bai taba ganinta a fili ba"amma ya taba ganin ta a wayar Afiya, kuma Yusuf ma ya tura masa" Kafi ta koma haka kwanakin baya da Yusuf ya tura masa"videonta a lokacin da take kukan na dama da kuma neman yafiyar yayanta ma bata yi baki haka ba. "Cikin tsoro Mama take" kallon Habib,suna hada ido dashi tayi tsaurin kauda kanta kefah. Yusuf wannan Balaraben kuma daga ina, dan ko sanda muke da kudi ma ba'azo wajanmu ba, dan haka nasan ba haka kawai yazo ba? " "Bata saya jin waca amsa Yusuf zai bata ba, ta rushe da kuka, kallon Habib tayi tace".. Dan Allah balarabe karkamin komai ka taimaka ka barni, na jira naga yayana na nemi gafararsu" Na kuma nuna musu"soyayyan da ban nuna musu"a baya ba, kafin na mutu"ta karashe magana hade da hada hannayenta biyu alamar koro. Wani irin murmushin jin dadi Habib ya yi, a lokacin da yaji kalaman da suke fitowa daga bakin Mama, hamdala dayi(Alhamdulillah) Allah mungode maka. "Sannu da tuwa rankashi dade, thank you Yusuf, sorry na shigan muku gida kai saye, nayi Sallama naji shiru ne shiyasa na shigo ciki. L'a ba komai ai rankashi dade kai ma gidanku ne ai, haka ne kam, gidan su beauty gidanmu ne, Habib shima ya fada yana murmushi. Ai Mama najin haka tace...naji kace beauty? Kana nufin Afiya ta, ko kuma dai kaima kana da kanwa mai suna beauty din?" Habib bai amsa mata ba" sai ma waje daya samu akan daya daga cikin kujerun palon ya zauna. Wai Yusuf Mama bata da lafiya ne? "Eh wallahi rankashi dade" Toh amma meyesa baka fadamin ba, ai ya kamata a kaita a sibiti. D'azun nan zazzabin ya rufeta, shine naje na siyo mata maganin zazzabin kafin zuwa gobe muje a sibiti. Kira kuma dama tun safe yau nake gwada number dinka amma ban same ka ba. Yusuf ya karashe magana cikin ladabi. Ohhh wallahi na kashe wayana ne jiya da zan kwanta bacci, kuma dana tashi da safe shirye shiryen zuwa nigeria nake tayi. Na manta shaff ban fada maka shekaran jiya ba. Okay ba komai, rankashi dade,ya hanya? Alhamdulillah. Wayarsa da bai dade da kunnata ba ya bude, ya shiga galeri, sai ga hotunan shi dashi da Afiya sun bayyana. "In kaga yawan hotunan Afiya a ciki zaka dauka sunyi shekara goma tare" Nan kuwa ko shekara basuyi tare ba. Mikawa Yusuf wayan ya yi yace"mikawa Mama wayan nan. Karba Yusuf ya yi ya mikawa Mama hannu na rawa Mama tasa ta karbi wayan. Idonta ne ya sauka akan hotunan Afiya. Kalla ta shigayi, daya itta da Habib ne a lokacin da zasu bar Nigeria sunyi kyau sosai a hoton, sai daya da ya yi musu"a lokacin da take kwance akan cinyar Ammi tana zuba mata shogoba gwanin ban sha'awa, kai in kagansu sai ka dauka ya da uwa ne. Wani irin kuka mai ban tausayi Mama ta saki tanayi tana taba fuskar Afiya da aka mata hoton itta kadai. Mikewa Mama tayi daker ta karasa gaban Habib hade da durkusawa kan guiwarta ta rushe ta kuka ta hada hannayenta biyo ta shiga rokonsa. "Dan Allah dan Annabi ka taimaka ka kai ni wajan Afiya ta, wallahi ina son yayana sosai, wallahi son kudi nane ya ja min, dan Allah nayi na dama ka tausaya min ka hadani da yayata. Naji zan dawo miki da yayanki amma dole kimin alkawari bazaki kara musu a bunda k'ike musu" ba. Wallahi bazan kara ba, wallahi ni yanzu babu a bunda nakeso sama da yayana,wai Mama kina nufi har da kudi? Habib ya tambaya. Sosai ma har kudi, nake nufi Alhaji balarabe. Haba Mama kar kiji kunya indai kina son kudi zan baki gasu sai ki barmin su Afiya. Habib ya fada yana bude wata bakar jaka daya zo dashi. Sai ga daloli sun bayyana. Mama! Ya kira sunanta" Na'am Alhaji. "Kinsan nawane anan? Kai Mama ta girgiza alamar a'a. Million 10 ne anan Mama in dai kin yedda kin amince zaki barmin su Afiya, toh nima yanzun nan zan mallaka miki shi halak malak. A'a bana so ni kam yayana kawai nake so su dawo. Alhamdulillah, Allah mungode maka. Tashi kije ki zauna Mama nayi miki alkawa insha Allah ina komawa kasar Dubaï zan kawo miki Beaunty. Yanzu Alhaji Balarabe kana nufin Afiya bata gasar nan? Eh tun lokacin da kika mareta ta bar gidan nan, na dauketa na kaita wajan mahaifiyata, amma shi mohseen yana kasar nan, yana gidan aunty na, gobe insha Allah zan kaiki wajansu" Wani irin murmushi Mama tayi a lokacin da taji za'a kawo mata yayanta. Bari na wuce gidan ankira sallar I'sha sai nazo goben ki shirya da wuri, zanxo na daukeki na kaiki a sibiti a dubaki daga nan sai na kaiki wajansu, kara washe baki Mama tayi hade da kara masa godiya. T'ashi Habib ya yi ya kalli Yusuf hade da cewa yauwa Yusuf biyoni da jakar nan, toh rankashi dade, Yusuf ya fada hade da dauko jakar. Sallama ya yi wa Mama sannun suka bar palon. Suna fita Habib ya kalli Yusuf baiyi wata wata ba ya rungumeshi. "Yusuf kam sai kokarin janye jikinsa yake" Dan gani yake bai kamata ya hada jikinsa da babban mutun irin Habib ba. Sakinsa ya yi, sannun tace... Gaskiya nagode sosai Yusuf, gaskiya kamin a bunda bazan taba mantawa dashi a rayuwata ba, dan haka wannan kudin dake hannunka nakane dama na kawo baka, badan komai yasa nacewa Mama zan mallaka mata kudin nan ba, sai dan ina so na tabbatar shin da gaske ta shiryu ko kuma dai a'a, sai kuma akayi sa'a da gaske ne. Naji dadi sosai da sosai, ba karamin kokari kayi ba, dan haka komai nayi maka ban fadi ba. Yusuf kam rasa ma bakin magana ya yi sai kuka kawai da yakeyi. Durkusawa yake kokarin yi amma Habiba ya hanashi, yauwa kaji so nake kaima ka bar karkashin wani kaje ka nemo aikin yi, in komai ya yi normal sai kazo ka sameni akwai wata magana da nakeso mu tattauna, bayan ka kammala duk a bunda nace maka. "Godiya sosai Yusuf ya yi wa Habib sannun suka yi sallama ya wuce"gida..... Yauwa ina mai baku hakuri, a wancan page din na manta na sakawa budurwar Habib Najwa, maima kon na saka Nadra. Nagode sai mun hadu a wani page din.🥰 *Fulanin jajirtattu ce*✍️ [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/FJyfKf65hJQApnYM0DV2BU 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Isma'il Cameroon* *(Mom Muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Maruburiyar* *Bazan zauna da kishiya ba,* *Mijin Attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske...Typing*✍️ https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page49&50 Free book Bismillahi rahmani rahim Godiya sosai Yusuf ya yi wa Habib sannun suka yi Sallama ya wuce gida. Yana barin gidansu Afiya gida ya koma. Part ɗinsa ya wuce direct ba tare da ya je wajan Iyayensa ba. Dan baya son takura musuduk da kuwa ya san yanzu yana Masallaci. Yana shiga ɗakinsa kayan jikinsa ya rage sannan ya faɗa toilet domin kara watsa ruwa. "Wanka da alwala ya yi sannun ya fito d'aure da tawul, sai dan karamin tawul da yak'e tsane kansa da shi. Gaban mirror ya je, kujerar dake gaban mirror ya ja ya zauna, mai ya d'auka ya shafa kaɗan da turare ya mik'e. Gaban wardrobe yaje, ya bud'e ya turo mlik din jallabiya da gajeran wando, ya saka, sannun ya d'au Sallaya ya shimfiɗa ya t'ada sallar i'sha. "Yana idar da sallah, bayan ya yi addu'a ya mike ya nad'e sallayar, sannun ya cire jallabiya ya canza kaya zuwa kayan bacci. Sannun ya hau gabon, bayan ya yi addu'ar bacci sai ya kwanta. A part din Mami kuwa Mami ce"mkwamce Akan gado bayan ta itar da sallahr i'sha. Sai Alhaji Muhammad ya shigo ɗakin da sallama a bakinsa. "Assalamu alaikum?" "Walaikum salam" Mami ta amsa daga k'wancen da take. Ƙarasowa ɗakin Alhaji Muhammad ya yi, ya rage kayan jikinsa shima ya hau kan gadon ya ja Matarsa ya runguma. "Shine kika barni tun d'azu a part dina ina ta jiranki ko? " "Haba hubby! ni wallahi kunyar zuwa nakeyi". "Kaga dai muna da yara, bai kamata daga zuwana nazo na wucena tafi dakinka ba." Toh ai nikam bana jin kunyar kowa saboda ina ganinki bazan iya hakura ko na minti goma ba, wallahi, dan haka na kawo kaina a taimaka a agaza min. Ya faɗa cikin marairaice fuska, kai in ka gansa sa ka zaci Saurayi ne yake yiwa buzurwarsa magana. Murmushi kawai Ammi tayiba tare da tayi magana ba" Saboda itta kanta tayi missind din mijin nata sosai. Jikinsa ta kara shiga kamar wata yer baby,murmushi Alhaji Muhammad ya yi ya kara rungumeta sosai a jikinsa. Hannusa daya ya sa ya tire dan karamin wular dake kanta data rufe gashinta dashillloo LYa shiga lshafa gashin nata a hankali, ture hannunta daga rungumar da tayi masa tayi ta kama bakinsa ta shiga bashi zazzafar kiss a baki. Alhaji Muhammad duk ya rikice. Masu karatu dama kunsan yanda fararen fata suka iya kiss😘in sun kama bakin namiji basa bari har sai sunga lips din yayi ja ta fara kumbura sannun suke bakinka🤣 Humm bari dai nayi shiru🤐 A daren dai sun ciyar da Juna dadi. Saboda Mami kullun kamar Budurwa haka take. Bangaren Maman su Afiya. Cikin farinciki ta kwana. Tunda taji za'a hada ta da 'Yyanta Zazzabin dak'e jikinta ya sauka, ko ma ince ta warke, dan lafiya lau ta kwana". *Washe gari* Zaune suk’e a kan teburin cin a bincin, gaba dayansu suna cin a binci. Ya shigo palon" Kara sowa gaban teburin ya yi, ya gurkusa ya gaida Daddy. "Good morning my Dad?" Morning my son, ya ka kuwa? "(Alhamdulillah ) Daddy! Mikewa ya yi ya rungume Ammi ta baya ya yi mata kiss a kumatu, kana yace... (Sabahul khair) Ammi? "Sabahul Nurr Habibi, ya gajiya? " "Wallahi gajiya (Alhamdulillah ) masha Allah, Ammi ta fada. Sai a lokacin ya kalli Mummy. Wato (Hajiya Maimuna) yace" Barka da safiya Mummy? "Barka dai ta amsa a takaice"sannun taci gaba da cin din da take ci. Dan gidan Ammi ni baza ayi min kiss din ba sai Ammi ko? "Haba Daddy Yanzu kishi kakeyi da Ammi. Wani irin hararan watsa Daddy ya yiwa Habib. Ammi ce ta karbi zancewajan cewa... kamar kasani"kuwa Habibi, kishi yake"haba har dake"Nuri! Ammi bata ce Komai ba sai ma jawowa Habib kujera dake kusa da itta tayi tace. "Oya maza zauna ka karya". Murmushi Habib ya yi sannun ya zauna. "Ya dai kannena?" "Me kuma ya faru?" "Ya kara jefah musu tambaya dan yaga duk sun hada rai. Mufeeda da bata iya fushi ba tace.. Bro ba kai bane tun d'azu muk'e ta faman gaisheka amma ka sharemu ba" Ayya Sorry my sisters wallahi banji bane"yanzu dai ba wannan ba, k'uyi sauri ku gama cin a binci ku sai ku rakani wani waje. Cikin murna suka geda masa kai sannun suka ci gaba da cin a binci su". *Dubaï Kwana ta yi batayi wani baccin kirki ba" Saboda kwana tayi tana gwada number wayar sa amma a kashe". Haka ma na Ammi Shi ya sa kwana tayi tana tunaninsa, saboda a kwana daya da bata ji muryarsa a gidan ba"jinta take" kamar shekara tayi ba taji muryarsa ba. Duk da ba wani abu yak’e hada su ba amma ba karamin kewarsa tayi ba. Kiran Safna tayi dan taji ya kanfaninta yake ciki, saboda kusan kwanan su uku basuyi waya ba. Dan tun ranar da jirginsu zai tashi ta kirata ta damka amanar kanfani a hannunta, Duk a bunda ya faru a kanfanin takan kirata ta fada mata, dama yanda suke tafiyar da komai. Suk tana fada mata. Hello Aunty Afiya "Naam Safna!ya k'ike ya gida, ya kuma kanfanina? " Wallahi babu lafiya Aunty, gaskiya ya kamata ki dawo, dan da bakiya nan sai almubazzaranci akeyi da kudin kanfani, kuma abun takaici ma da taimakon Manaja! "suke aikata komai. "Whattt! "Wai kina nufin da hadin kan Manaja suke min barna a kanfani?". "Eh sosai ma kuwa Aunty, jiya na gwada number dinki amma bata shiga dan kwana biyu muna samun mas'alar nertwok a nan" "Shikenan bari na kira Y'aya Habib tunda yana gari, dan yaxyo jiya". Tana kaiwa nan ta kashe wayan, ba tare da ta saya jin mai Safna zata ce ba. *Fulanin jajirtattu ce*✍️ [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/FJyfKf65hJQApnYM0DV2BU 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena isma'il Cameroon* *(Mom Muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba.* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske... Typing✍️* Page51&52 Bismillahi rahmani rahim ******* Tana kai wa nan ta katse wayan, ba tare da ta tsaya jin mai Safna zata ce ba. Kano(Nigeria) Kasancewar sun riga shi, fara cin abinci, shi ya sa suka riga shi kammalawa, "Toh yaya bari muje mu shirya kafin ka kammala cin a bincin." Kai kawai ya gyd'a musu, kasancewa sun san halin shi tsarai in miskilancin nashi ya motsa, shi ya sa basu damu da rashin amsawarshi ba suka wuce d'akinsu. Miƙe wa su Ammi da Daddy suka yi suka nufi palo, kuma dama itta Hajiya Maimuna ta dade da hawa sama, tayi musu karya akan cewa kanta ciwo yake mata, dan ta san in ba haka ta fada musu ba, baza su yadda ba. Ya kammala cin a binci kenan yana goge bakinsa yaji wayarsa da ya dora kan teburin cin a binci ta fara ringing. Can bangaren kuwa ajiyar zuciya ta sauke, a lokacin da taji wayan na ringing, sannun ta gyara kwanciyarta, ɗaukar wayar ya yi ya duba ya ga sunan my Beauty ce ta ke yawo akan screen din wayar. Dafe kansa ya yi daga nan ya furta "Sorry my beauty". Sai da kiran ya katse sannun ya kirata. Bugu ɗaya ta ɗauka. "Hello yaya" my Beauty , ya kike? " "Ina lafiya lau". "Amma me ya sa baka kira;ni ba?" "Sorry Beauty,na gaji ne shi ya sa ban kunna wayata ba." "Amma shine daga kai "har Ammi ba wanda ya kirani? " "Sorry ba zamu sake ba, kinsa itta Ammi tama fini jin gajiyar amma na tabbata zuwa anjima Zata kiraki". "Shi kenan Allah ya sa. Ameen ya amsa". "Yauwa yanzu muka gama yin magana da Safna take bani labarin cewa wai Manaja ya hada baki da wasu Ma'aikatan! suna ta min barna da kudin kanfani". "Subhanallah." "Ni bamma san ya akayi kika bawa amanar kanfani a hannun mace ba wallahi". "Ga maza rututu a kanfani, amma. Ki rasa wa zaki bawa sai Mace?" "Toh ai nafi yanda da itta ne" Shi ya sa na bata." "Shi kenan bari zanje na duba, duk a bunda ake ciki zan sanar miki, tunda nan da sati daya in sha Allah zaki dawo kasarki". Cikin murna da farinciki nace, " Wai da gaske nan da sati daya zan koma. gidanmu? " "Eh Ko bakiya so?" Shiru nayi ba tare dana bashi amsa ba. Dan babu a bunda na tuna sai halin Mamana. Kamar Habib ya san tunanin da na ke yi, sai yace" Kinga beauty ki kwantar da hankaliki. "Ai kina da data ko?" "Eh ina da shi". Okay toh maza- maza kunna datan zan tura miki wani abu". Kai ta gyd'a sannan ta kunna data, ai kuwa yana online shima, babu bata lokaci ya tura mata bidiyon Mama wanda akayi mata kwanakin baya da suka wuce, wanda take cewa tana son 'yayanta su dawo tayi na dama bazata sake ba. Dan lokacin bata wani canza sosai ba. Dan yasan tsarai in ya ce zai tura mata na jiyan nan zata iya yin kuka, shi kuma ya tsani kukanta sosai, dan jin kukan nata yake har cikin ransa, gashi kuma baya ma. Kusa ballantana ya rarrasheta. Buɗe bidiyon daya tura mata tayi, sai taga bidiyon Mama ce Tashi daga kwancen da ta ke tayi, ta shiga kallo, Ta nitso sosai wajan kallon bidiyon. Tun kafin ta karasa ganin bidiyon. Wayayen farinciki suka soma silalo mata daga cikin idanu. Dama bai kashe kiran ba. Dan haka yaji sautin kukan nata. "My Beauty me haka? Allah da na san zaki kuka da ban turo miki bidiyon nan ba." "Ka yi hakuri, Kukan murna na ke yi 'ya Habib." Ajiyar zuciya ya sauke a lokacin da yaji ta ce masa ba kukan data saba takeyi ba. "Duk da haka ba kuka ne ya ka ma ta kiyi ba ya Kamata ne ki daga hannunki sama kiwa Allah godiya daya nuna mana wannan ranar". Murmushi tayi. Kana ta shiga share hawayen daya zubo mata. Sai da ta tabbata babu ko d'igon hawaye akan idanunta, sannun tace. "Yauwa yaya na share hawayen nawa". "Okay good" "Yanzu dai bari naje kanfanin naga mai abun yi, kafin ki dawo." "Toh shikenan Yaya Habib na gode, Sai ka dawo". "Okay bye, sai na dawo zan kiraki." "Okay" ta faɗa Sannan ta katse wayan. D'agowa ya yi yaga 'kannensa tsaye akansa. Hade rai ya yi kana ya ce, "Kallon me kuke min haka, Kamar mayu". "Haba Bro Yanzu mune mayu? " "Toh ba dole na kira ku da mayu ba, "kun wani kura min ido sai kace ba wayeyyo ba". "Toh ai Bro tun dazu muka shirya muna ta maka magana bakaji ba. Sai faman waya kakeyi." "Toh sai kuma a kace ku saya ku kura min ido? " "A'a Bro"kayi hakuri." "Naji mu tafi" Murmushi sukayi sannun suka wuce tsakiyar palon. Sai da suka saya suka yiwa su, Daddy sallama sannun suka wuce. Suna shiga mota, maigadi ya bude musu gate suka fita, ya nufi kanfani, dan so yake ya fara zuwa kanfanin tukun, kafin ya dawo ya dauki Mama. Comments and share pls😍👏 *Fulanin jajirtattu ce*✍️ [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/BoEGaUYscLHDtLr41wYFFI 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU Da HASKE* *By* *Sakeena isma'il Cameeron* *(Mom Muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ *marubuciyar* *Bazan zauna da kiya ba,* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing... ✍️* Page 53&54 Free book Bismillahi rahmani rahim **********Su na shiga mota, maigadi ya buɗe mu su gate ya ja motar, su ka fita su ka nufi kanfani, don so ya ke ya fara zuwa kanfanin kafin ya dawo ya ɗauki Mama, Kasan cewa ba bu go'slow a hanya shi ya sa nan da nan suka isa kanfanin, Kasancewar ba bu wanda bai san Habib Muhammad Habib ba, shi ya sa su na ganinsa su ku sauka cikin mota da shi da 'kannensa, maaikatan dake wajan su ka ƙara so in da su ke, sannun su ka durƙusa su ka gaishe su, hannu kawai ya ɗaga mu su sannin ya wuce ciki, su ma su Ai'sha su na gama amsa gaisuwar su su ka mara mishi baya su ka nufi cikin kanfani Su na shiga su ka tarar da wani Saurayi da bazai wuce shekaru 23 ba zaune a inda ya saba ganin Safna da alama shine a matsayin saketare a yanzu, Safna kuma ta koma Offince ɗin Afiya tun da ita Afiya ta damƙawa amanar kanfaninta kafin Allah ya dawo da Ita Saurayin na ganin Habib ya miƙe ta re da rusunawa ya gaisheshi "Sannu da zuwa Sir." "Y'auwa sannun ka dai." "Bismillah Sir da ma Safna ta fadya min zuwanka." Saurayin ya faɗa Juyowa Habib ya yi ya kalli k'annensa ya ce"yauwa Mufeeda ku zauna ku jirani yanzu zan fito." "Toh Bro sai ka fito." Mufeeda ta faɗa haɗe da jawo ɗaya da ga cikin kujerun da ke wajan ta zauna, "NI dai binka ciki zan yi dan ban san lokacin da za ka fito ba." Ai'sha ta faɗa ha ɗe da marawa Habib da ya fara tafiya da niyar shiga office ɗinn baya, jin abinda Ai'sha ta ke cewa ne ya sa shi tsai da tafiyar da ya ke yi ha ɗe juyowa, wani irin kallo ya yi mata da har ya sa hanjin cikinta kaɗawa, ba shiri ta ja kujeran da ke kusa da ita ta zauna, Juyowa ya yi ya karasa office ɗin,ba tare da ya tsaya kwankwasa wa ba ya tura ƙofar ya shiga, ya mai da shi ya rufe, tun da ya shigo su ke kallon sa har ya ƙara so gaban su, Habib kuwa kallo ɗaya ya yi mu su ya ɗauke kai, "Sannu da zuwa yellabaï." Safna ta faɗa ha ɗe da miƙewa tsaye, sannan ta ci gaba da cewa "bismillah ga kujera ka zauna." ta faɗa ta na nuna mai kujerar da ta miƙe akai, Habib bai zauna ba, sai ma kallon Basira da ke zaune a dayan kujerar ya yi sannan ya mai da kallonsa kan Safna ya ce "Waye wannan Ko ita ma Ma'aikaciyar ku ce?." kafin Safna ta buɗe baki ta yi magana Basira ta rigata cewa "hy Sir ka mantani ne.?" ta faɗa ta na turo ƙirji gaba ha ɗe da kashe mai ido ɗaya " Tambayar ki ni ke kin yi shiru." Habib ya faɗa fuskar nan kamar bai taɓa dariya ba, "Yellabaï Yayar k'awata ce ta kawo min ziyara." "Nan gidanku ne da za ta kawo miki ziyara,?" "A'a Yallaɓai ba gidanmu bane." "Toh da ga y'au kar na ƙara ganin wata ta zo miki nan da sunan ziyara, duk wadda ta ke son je miki ziyara taje gidanku Kinji ni.?" "Eh naj.i" "Good!. " Mai da dubansa ya yi kan Basira kana ya ce"ke malama tashi kifita kuma in kin fita karki sake dawowa nan wajan da sunan ziyara." da sauri Basira ta geyɗa kai ha ɗe da miƙewa har ta na tuntube, Aguje ta zo ta wuce su Mufeeda ta bar wajan, "Sis kinga wata ta fito a soro ce da alama Bro ne ya yi mata wannan fadan nashi." Mufeeda tayi maganar ta na dariya Taɓe baki Ai'sha ta yi ba ta re da ta ce komai ba, A cikin office kuwa ƙara sowa Habib ya yi ya zauna akan kujerar da Safna ta nu na mai d'azu, sannun ya nu na mata ita ma kujerar da Basira ta ta shi akai da hannu alamun ta zauna. Ai ba shiri ta ƙarasa ta zauna, Sai da su ka ɗau kusan 3 minunt a haka sannun ya fara magana kamar haka "d'azu Afiya ta faɗa min kin kirata kin faɗa mata cewa ana barnan kuɗi a cikin kanfanin nan." "Eh haka ne Yallaɓaï." "Saboda mi ba ta d'au amanar kanfanin ta bawa kowa ba sai ke.?" "Saboda ta Yadda dani kuma ta tabbata zan kulan mata da kanfanin shi ya sa ta bani." "Good." "Toh amma me ya sa kikaci amanarta.?" "N.. N... N... Ni kuma Yallll... La ɓaï?"Safna ta ha ɗa kalmar nu ɗin da kyar wajan furtawa, don yanzu kam ta fara tsorata da Habib mutun kamar mai aljanu, "Mu nawa ne a nan da za ki tambayen.? " "Mu kadai ne." "Toh amsa min tambaya ta." "Toh.toh.toh zan amsa." "Ina jinki." "Dama........ Toh fah safna dama me? 🤔 Fulanin jajirtattu ce✍️ Comments and sharee pls👏 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena isma'il Cameeron* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske typing... ✍️* tilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/BoEGaUYscLHDtLr41wYFFI https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauki. ✏️ Page 55&56 Free book Bismillahi rahmani rahim **********"Mu ka d'ai ne". "Toh amsa min tambaya ta. " Toh Toh Toh zan amsa" "Ina jinki? " "Dama Manaja ne ya min bara zana cewa in har ban ba shi had'in kai ba sai ya min a bunda bazan ta'ba mantawa da shi a rayuwata ba" "Hadin kai na me zaki bashi?" "Dama...." Magana Safna ta fara yi ya dakatar da ita ta hanyar d'aga mata hannu, wayarsa ya d'auka ya danna recoding sannun ya ya:ce" Zaki iya ci gaba ina jinki". "Dama a kwai wata rana da na tashi yin lissafin abubuwan da a ka siya sai na ga kaya dayawa ya 'bata, dan kusan a tampofi guta dari da ashirin da lesis guda amsin da nayi bincike na gano cewa ashe ma da sa hannunsa kayan suka 'bata, shine na je nayi masa magana na kuma k'ara da cewa in har bai sa an dawo da kayan nan ba sai na fadawa Aunty Afiya.Da farko ya fadamin cewa kar na fada in sha Allah zai biya kud'in kayan tun da ya riga da ya siyar da kayan Da haka dai muka bar zancen akan cewa zai biya kud'in kayan da suka 'bata". "A haka na koma office d'ina, watoh office Aunty. Bayan an tashi ne na fito da niyar in samu abun hawa sai muka had'u da shi_shima zai shiga motarsa ya wuce gida shi ne ya ce in baza na damu ba mai zai hana in shiga ya ajiye ni a gidan daga nan ma sai ya je banki ya ciro kud'i ya mayer wa kanfani". Jin cewa zai mayar da kud'in kanfani ne ya sa ni amince wa na shiga muka wuce". "A bunda ban sa ni ba shi ne a she ba haka ne a ransa ba.Muna hawa titi ya kalleni ya ce min "Bismillah ga ice cream, kasan cewa ina son ice cream sosai a rayuwa ta shi ya sa ba musu na kar'ba na fara sha. Shan ice cream ne ke da wahala sai kawai na ji ina jin wani irin baccin da ban taba ji irinsa ba" "Babu 'bata lokaci kuwa na bingire a wajan sai bacci.Daga nan kuma ba san a bunda ya faru badan lokacin da na farka gani na nayi a wani d'aki Kalle-kalle na shiga yi Sannan na ce wai waye kamo ni nan gidan?" "Na tambayi kai na a lokacin dana farka na ganni a wani d'aki. "Shiru nayi ina tuna lokacin da yace min na shiga mota ya kai ni gida Ina cikin wanan tunanin ne ya fito daga wanka daga shi sai tawol a kan k'ugunsa, ina gani haka jikina ya d'auki rawa dan tuna nake ban taba ganin na Miji a haka ba. "K'arasowa ya yi gabana yana dariya sannan ya hau gadon ya finciki hijabin dake cikina da karfi, sai na fada jikinsa, k'ok'arin kwace kai na na shiga yi amma na kasa, dan ba karamin riko ya min ba, magana ya fara min kamar haka." "Ke ki tsaya ki saurare ni in kuma ba haka ba...." Bai k'arasa maganar ba na ga ya fara l'alubata, wani irin riko ya yi wa k'irjina nan da nan kuwa na fahimci mai yake nufi wato yana nufin in har ban saya na saurare shi ba zai min fiyad'e!" Ba shiri na ce "Ina jinka ka fad'i koma mene ne zan yi in har zaka bar ni da mutunci na" Wani irin dariya ya kara shekewa da shi sannan ya gyara zama ya fara magana kamar haka; " Dama so na ke ki janye maganar nan". "Waca magana kake magana akai?" "Maganar da muka yi d'azu na cewa lallai sai na biya kud'in kayan nan da na sata" "Toh ai ni a tunani na mun riga da mun gama wannan maganar, tun da har kace zaka je ka ture kud'in a Banki ka mayar musu" " Ke a tunaninki zan bayar?"."toh bari kiji ko sisi bazan bayar ba Dan haka kar ki kuskura ki cewa Afiya ni ne na d'auki kayan nan in ba haka ba kuma, sai na zubar miki da mutuncin ki da kike tak'ama da shi in ya so sai muga ya zaki yi, ko Afiyan ce zata dawo miki da budurcin" "Wallahi in dai zaka barni da mutuncina na tafi gida Allah bazan fad'i ba "Kuma dama ni ka d'ai na sani dan haka na jan ye komai ba zan fada ba" Shi ke nan bari na shirya sai na mai da ke gidan ku, amma zan rufe miki fuska" Kai na kawai na gyad'a masa sannan ya mik'e ya d'auki kayan sa,ya koma toilet ya shirya ya dawo d'akin ya d'auki key d'in motarsa da wani kelle ya rufe min fuska muka fito ya bude min mota ya taimaka min na shiga sannan ya ja motar muka bar gidan. Can nisa da layin mu ya yi parking sannan ya bud'e min fuska , sai daya kara jadda da min cewa in har na tona masa a siri shi ma sai ya lalata min rayuwa. Sannan ya bar ni na fita ya ja motarsa a guje ya bar layin Ni kuma na k'ara sa gida" "Da na je gida,da Mama ta ga ba kamar yanda ta saba gani na kullun in na dawo daga wajan aiki ba shi ne ta tambaye ni lafiya? Nace mata kai na ne yake min ciwo, shi ne ta ce na je na samu magani na sha sai na kwan ta, na amsa mata da toh sannun na mike na shiga daki". "Tun ranar ban kara yiwa Manaja maganar biyan kudi ba" "Amma kuma duk lokacin da na tunani cewa ga a bunda Manaja ya yi kuma ban gayawa Aunty ba,sai in ji kamar amanar ta naci" "Kullun Ummana na lura da ni, dan haka wata rana ta tambaye ni me ya ke damu na, kasan cewa ban iya k'arya ba shi ya sa na kwashe komai na fad'a mata amma abu d'aya na boye mata shi ne d'auka na da Manaja ya yi ya kai ni gidansa ya yi min bara zana da in har na tona masa asiri zan rasa budurci na, shi ka dai na boye mata saboda na san in na fad'a mata ba kara min fada zan sha ba,na rashin gaya mata da wuri da ban yi ba". "Ummata ce ta bani shawara cewa na fada wa Aunty Afiya komai, dan shiru da nayi zai iya j'awo min babbargas'ala". "Shi ya sa yau ina zuwa kanfani na kira Aunty na fad'a mata komai" Ajiyar zuciya Habib ya sauke sannun ya koma ya zauna, dan tun d'azu ya ke saye, saboda abun ba kara min bata masa rai ya yi ba. "Y'auwa kina ji na?" "Eh ina jinka Yellabaï!" "In mun fita kar kiyi a bunda zai sa ya gano cewa kin fada min wannan maganar". " Toh Yellabaï! " "Saboda a kwai wani shiri da nake son yi kafin gobe". "Ni na wuce in lokacin tashi ya yi ki wuce gida ke ma" "Toh yallabï!" Shi kuma Habib na gama fad'ar haka ya sa hannu ya d'auki wayoyin sa daya ajiye kan teburin sannun ya bar offince din. *Fulanin jajirtattu ce✍️* Comments and share pls👏 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena isma'il Cameeron* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske typing... ✍️* tilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/BoEGaUYscLHDtLr41wYFFI https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauki. ✏️ Page 57&58 Free book Bismillahi rahmani rahim ********** Habib na gama fad'ar haka ya sa hannu ya d'auki wayoyin sa daya a jiye akan teburin sannun ya bar office din. Bude kofar ya yi ya fita ya bar office din, " Ni wallahi sister in ba zaki tafi gida ba ni zan tafi"Ai'sha ta yi maganar,dan ba karamin haushi taji ba da Habib ya shiga ciki tun dazu ya barsu zaune. "Wallahi nima na gaji.amma mu dan kara ko da minti goma ne in bai fito ba sai mu fati"Mufeeda ita ma ta fada,dan ita ma harga Allah ta gaji, "Ni wallahi da ya sani gidan Aunty Maryam ya kai mu" Mufeeda ta kara fada. "Ƙe kuwa sister me zaki yi a gidan Aunty Maryam tunda baki da sa'arki a can da zaki ce zaki je wajanta" "Wajan Aunty Maryam zan je mana.kuma da ki ke cewa babu sa'a ta a gidan Aunty Maryam,ita Ai'sha ba sa'ata bace ba ne?". "Jiki tsoron Allah sis.yanzu dan Allah Ai'sha sa'arki ce?"ke yanzu har kina sha'awa Zama sa'ar Aunty Ai'sha ?" "Toh me a ciki ita ba mutun bane?". "Kin ga karki fassa'rani,gani nayi kin fita yarinta da komai,ba dan wannan abokin Oncle Safwan yace yana sonta bama da har yanzu bata samu mijin aure ba,dan wallahi ta fara sufa,kin ga fah ta kusa 30 dan yanzu tana 27!" Ai'sha ta kare magana. Wallahi Ai'sha ki dena "wannan halin naki,yanzu dan Allah ya dace ki dinga fadar haka?"ai ko ba komai yanzu kam ta samu Kuma zata yi aure" "Kuma da ki ke cewa bata samu mijin aure da wuri ba,mu mun samu ne?". "Kinga sister karki hada ni da ƙe dan kin san sarai na fiki kyau da komai,kuma da ki ke cewa mu ma bamu samu ba,ni kinfi kowa sanin ina da shi kuma in sha Allah kwa nan _nan zai turo kuma dama can nice ban bashi dama ba". Tabe baki Mufeeda ta yi hawayen da take rikewa tun dazu suka samu damar zubowa,dan ita abu kadan yake sata Ku ka, Tun ɗazu Habib ya karasa wajan su ya ji suna magana,Shi ya sa bai yi magana ba,sai ma hannunsa da ya zuba jikin aljiwu,kasan cewa dama ɗabiyar sa ce yin hakan. Gyaran murya ya yi duka suka dago suka zuba masa ido. Saurin goge hawaye Mufeena ta yi dan ta san sarai in yaga hawayen sai ya tabbayeta me ya sa ta ku ka. “Sorry na barku kuna ta jira na.ku tashi mu tafi ina so na kammala duk a bunda zan yi kafin 1 na rana". Miƙewa suka yi,suka soma barin offince din Saketara sai suka ji muryarsa ya yi magana "ke Ai'sha juyowa Ai'sha ta yi tace"na'am Bro Mufeeda sa'ar kice ?"a'a ba sa'ata bace.toh me ya sa ki ke mata wani abu kamar kin samu sa'ar ki?" "Ba komai Ai'sha ta kara cewa. "Toh bata haƙuri, haƙuri fah kace Bro?"eh haƙuri nace.ko ba zaki bata ba ?" "Ban ce ba, amma fah da shekara ɗaya fah kawai ta girme ni,ko da wata daya ta girmeki Ƴayar kice dan haka ki bata haƙuri" Turo baki gaba Ai'sha ta yi sannun tace "ki yi haƙuri" "Ba komai ya wuce" “Mu tafi toh mara kunya" Sumsum tabi ta kefan su ta fita kamar mutafiki. Suma fita suka yi. bayan ya yi sallama da sakatare. Suna barin kanfanin ya wuce gidansu,a gaban gate din gidansu ya yi parking ya juya ya kalli Ai'sha dake zaune a bayan mota "ƙe Ai'sha"ɗagowa Ai'sha ta yi ta amsa da "na'am Bro" "Sauka ki wuce gida". "Toh Bro ku kuma ina zaku je?"."ina ruwanki fita nace " Tabe baki Ai'sha ta yi sannun ta fita ta shiga gida ta karamin gate. Shi kuma Habib ya yi ravas suka kuya ya bar wajan ya nufi gidan su Afiya. "Bro ina zamu ?"Mufeeda ta tambaya cikin sanyin murya. "Ina so zan dauko wata yer uwar mu anan sai ki kai ta salon da kuma gyaran jiki,dan ta sha jinya kwana biyu tana kwance ba ta da lafiya,duk ta canza,kuma kinga ta kwana biyu bata hadu da yan uwa ba,bai kamata su ganta haka ba" "Haka ne kam Bro". "Amma me ya sa baka taba kawo mu wajan ta ba?". "Ina na ganki da zan kawo ki dududu yaushe ma ku ka dawo Nigeria!" "Haka ne Bro " "Bari na kira Yusuf ya gaya mata ta fito mu tafi dan nasan ta dade da gama shiryawa"ya fada yana dauko wayarsa daya ajiye a gefen sa, Kiran Yusuf ya yi yana dagawa yace "y'auwa Yusuf ki faɗawa Mama ina kofar gida ta fito mu tafi"ta can bangaren Yusuf ya amsa da"toh yellabaï!" Kashe wayan ya yi ya jingina bayansa da jikin kujeran ya lumshe kyawawan idanunsa. Tunani ne kala _kala a ransa kuma gaskiya ya na nemon ma fita. *Cikin gidan su Afiya* Yusuf ne ya shigo cikin palon da "salama"kana ya kalli Mama dake zaune kan kujera tun ɗazu ta shirya ta na jiran Habib ya zo ya kai ta wajan dan autanta, Kallon Mama Yusuf ya yi yace "Mama ga yellabaï ya zo yana bakin gate ya ce na fada miki ki fito". Ai Mama na jin haka ta miƙe tana cewa "mu je toh Yusuf"!kai Yusuf ya geɗa sannun ya bi bayan Mama suka fita. Kasan cewa Mama na da kaya masu sada da Afiya take siyo mata Shi ya sa ta fito fess kamar masu kudi,se dai kawai raman da kuma baƙi da ta yi ne kawai ya dan kwaf sa mata. Fitowa suka yi Habib na ganin su ya fito daga mota, rusunawa ya yi ya fara gaida Mama "Mama ina kwana?"."lafiya lau yellabaï"dan Allah Mama ki dena kirana da yellabaï ki kira ni da sunana Habib in har kina so naji dadi" Mama zata yi magana Habib ya yi surin Katse ta ta hanyar cewa"Mufeeda ga Mama ki fito ku gai sa "kai Mufeeda ta geda sannun ta sauko daga cikin mota ta shiga gaida Mama,"Mama ina wuni lafiya lau alhamdulillah ƴata ". "Habib kanwarka ce ?" "Eh Mama kanwata ce" "Ma sha Allah" "Bismillahi!Mama shiga mota mutafi " "Toh ɗana"Mama tace sannun ta shiga bayan mota da Habib ya bude mata ta shiga,ya rufe ya zaga zai shiga ta ma zaunin dreve sai Yusuf ya riga shi shiga"kaga Yusuf koma ɗayan sit din ka zauna ka bani na tuƙa". "Gaskiya yellabaï ka yi haƙuri amma ni zan tuka dan bazan taba barin ka tuƙa mu ba, bayan muna tare " Habib bai sake magana ba ya koma dayan sit ɗin ya shiga Yusuf ya ja mota suka bar layin.... *Fulanin Jajirtattu ce* Comments & share pls👏 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Isma'il Cameroon* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske typing...✍️* Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/BoEGaUYscLHDtLr41wYFFI https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 59&60 Free Book Bismillahi rahmani rahim **********Habib bai sake cewa komai ba ya koma dayan sit din ya shiga ya zauna Yusuf ya ja mota suka bar layin, A wani ƙaton shagon da aka rubuta a samansa beauty Salon and gyaran jiki ne Yusuf ya yi barking ,dan tun jiya da daddare ya faɗa masa in da zasu fara zuwa kafin a je gidan Aunty Maryam, Wata jaka daya fito da shi daga gida ne,ya buɗe,tattausan hannunsa ya saka ya d'au banɗir ƙuɗi guda biyar a ciki,in da a ce za'a irga zasu iya kai rabin million,wata leda mai kyau ya ɗauka a cikin motar ya saka ƙidin a cikin sannun ya juya bayan shi,yace "tek sister"!karɓa Mufeeda ta yi sannun ya ci gaba da cewa "y'auwa kuje ayi duk abunda ya ɗace"."okay Bro Mufeeda ta faɗi haɗe da juyowa ta kalli Mama gake gefan ta ta ce "sauko muje Mama"kallon ta Mama ta yi sannun ta ce"ƴata nan ne Mohseen nawa ya.....bata karasa ba Habib ya kase ta ta hanyan cewa"Mama kawai ki bita ku shiga kuma dan Allah ki bari ayi miki duk a bunda ya ɗa ce in har kina so na cika miki alkawarin da nayi miki jiya kuma muna gama da nan ma a sibiti zan kai ki a kara duba jikin ki da kyau a baki magani"."Toh na amince zan bita mu shiga cikin amma dan Allah ba sai ka kai ni a sibiti ba,dan wallahi na warke" "Shi ke nan Mama naji Amma sauka ku je anjima kaɗan zan dawo, kallon Mufeeda ya yi sannun ya ce yauwa sister in kun kusa gama wa ki yi min waya " "Toh Bro"Mufeeda ta amsa sannun suka fita suka nufi cikin wajan. Jinginar da kansa ya yi da jikin kujerar motar ya lumshe ido,ganin da Yusuf ya yi ba magana zai yi ba ne ya sa shi buɗe baki yace "yellabaï anan zamu jira su ne ?" A'a ya faɗa a takai ce,taɗa mota Yusuf ya yi,ya bar wajan a zuciyarsa kuwa faɗi yake'yau kuma muskilancin ya motsa ke nan Sai da suka hau titi sannun ya juya ya kalli Yusuf kana ya ce "kanfanin mu zaka kai ni" "Toh yallabai amma kasan ban san kanfanin ba" "Muje zan nuna maka" "Toh yellabaï" Kotan ce ya shiga yi masa har suka kara sa kanfanin na su. A wani babban gini naga Yusuf ya yi barking,kallon ginin Yusuf ya shiga yi dan tun ylda yake bai taba ganin kanfanin irin sa ba a (Kano) Ma aikatan wajan na ganin shigowar motar suka tawo dan sun san dan Alhaji Muhammad Habib Ibrahim ne ya zo, Kowa sai zuwa ya ke yana kwasar gaisuwa,shi kam Habib hannu kawai yake ɗaga musu sannun ya juya ya kalli gefen sa inda Yusuf ya ke saye kana ya ce "mu je" Kai Yusuf ya geɗa masa sannun suka wuce ciki,sama suka hau kasan cewa sai an wuce office din sakatare kafin a karasa office din sa shi ya sa suna shiga office din saketare ya miƙe saye haɗe da rusunawa ya shiga yi musu sannu da zuwa "Welcome Sir" "Thank you"ya amsa a takai ce "Sannu da zuwa"saketare ya yi wa Yusuf ma"amsa wa Yusuf ya yi cikin sakin fuska sannu ya ce "ya aiki?"da alhamdulillah sakerate ya amsa. "Muje Sir" Kai Habib ya geɗa sannun ya bi bayan sakerate, Yusuf ma bin bayan su ya yi,suka shiga ciki Ina yin ido huɗu da office din babu a bunda nake furkawa sai "wow da ma sha Allah" Kaɗai nake furtawa,dan ba kara min kyau office din ya yi min ba. Duk da bai kai office dinsa dake (Dubaï)ba amma shima wannan din na da kyau sosai, Zama Yusuf ya yi akan kujerar dake fuskantar na Habib, Sannun shima ya karasa kan nashi kujerar sai daya saka hannun shi ya shafa wajan don ya tabbatar an goge masa yanda ya ke so,dan wannan ɗabiyar sa ce nayin hakan. Yana shafawa ya dago ya kalli saketare dake saye cikin bacin rai ya fara magana "wai dama baka sa an share min office din nan ba ka bar ni na shig a haka har ka ke kallo na_ na bar baƙo na ya zauna akai?" "Sorry Sir an share jiya ganin da nayi ba anfani aka yi da office din ba ne ya sa ban sa an share y'au ba". "Kalle ni da kyau Paisal kafi kowa sanin bana son kazan ta,kai nifah in dai akan kazan ta ne zan iya bata wa da mutu kai Yusuf ka tashi mu tafi ka kuma yi hakuri da ɓata maka kayan da ya yi"yana kaiwa nan ya juya ya bar wajan Baki sake Yusuf ya ke kallon Habib dan tunda ya ke dashi bai taba ganin ya yiwa wani faɗa ba. Shi a bunda yafi komai bashi mamaki ma bai ga datin da office din ya yi ba ballanta na ya ce zai ɓata masa kaya. Shanye mamakin sa ya yi ya miƙe ya bi bayan sa dan shi Habib har ya ma bar office din,haka ma saketare Dan ya bi bayan sa yana bashi hakuri "Shi ke nan naji amma karka sake min haka,ka saka a share min gobe da safe kafin na shigo office"toh Sir in sha Allah bazan sake ba" "Good" Habib ya faɗi sannun ya juya ya kalli Yusuf daya karasa wajan yanzu sannun ya ye "mu je Yusuf"! "Toh yellabaï" Suna barin kanfani ya umarci Yusuf da in ya ga supermarket ya saya Yusuf na ganin katon supermarket ya yi barking sannun ya juya ya ce "yellabaï wani abu zan siyo maka ne?" Ba tare daya bawa Yusuf amsa ba ya balla murfin motar ya fita sannun ya ce"biyo ni" Kai Yusuf ya geɗa sannun ya fito daga cikin motar ya bi bayan shi suka shiga ciki. Bangaren kayan maza ya nufa,wasu riga da wando ne mai masifar kyau da sada ya tiro ya miƙawa Yusuf karɓa Yusuf ya yi kana yace "shiga ciki ka goda"ya faɗa hade da nuna masa wani dan karamin daki da ake shiga ana goda kaya Baki Yusuf ya buɗe da niyar yin magana ya daga mata hannu sannun ya kara nuna masa dakin, Ba yanda Yusuf ya iya haka ya wuce ya shiga dakin,babu jima wa Yusuf ya fito ya yi kyau sosai dan in kagan sa zaka d'auka shima dan gidan masu ƙuɗi ne,sai in ka kalli fuskarsa ne zaka fahimci shi ba dan gidan masu ƙuɗi ba ne ,amma bayan wannan babu komai,dan Yusuf kyakkyawa ne,yana da kyau dai dai gwargwado,duk da kuwa baƙi ne amma ba can_ can ba, Murmushi mai kyau Habib ya yi sannun ya furta "ma sha Allah ka yi kyau sosai Yusuf" "Na gode yellabaï amma banga mai kayan nawa ya yi ba da har zaka sai min wannan" Habib bai ce komai ba sai ma barin wajan daya soma yi,ganin hakan da Yusuf ya yi ne shima ya yi saurin bin bayan sa da wayen nan kayan daya tire. Wajan biya ya je ya biya sannun ya mikawa Yusuf sauran ledan suka bar wajan Suna fita yaga wasu ma barata ya am shi soffin kayan da Yusuf ya tire ya mika musu, godiya suka shiga yi masa shi kam bai saya amsa musu ba ya yi gaba abun shi, Baki sake Yusuf ya bi bayan Habib da kallo,dan shi bai ga a bunda kayan ya yi ba da har zai bawa mabarata. A wajan Salon kuwa,gyaran jiki aka yiwa Mama sai wanki kai da kitso, ba kara min kyau Mama ta yi ba,ga kuma wani irin kamshi da take yi,kasan cewa Mama ba wani babba bane sosai ba, shi ya sa in ka ganta sai ka dauka amarya ce, Dan ko Ammi da Mommy da Aunty Maryam zasu girme ta, Da Mufeeda ta ga an kusa kamma lawa Mama kitso ne ta d'auri waya ta kira Habib domin ta sheda masa cewa sun kusa gaba wa, Kara sowar su Habib ke nan daga wajan ya d'auki wayan zai kira Mufeeda sai yaga kiranta ya shigo cikin wayarsa,yana ɗaga wa ta ce "Bro mun kusa gama wa" "Okay ina waje" "Toh Bro sai mun fito" Bai amsa ba ya kashe waya. Bai fi minti 5 ba suka gama Mufeeda ta biya mai Salon ƙuɗin ta sannun suka fito, Suna fita kuwa suka hango motarsa Kara sowa suka yi ta buɗewa Mama bayan mota ta shiga sannun ita ma ta buɗe ɗayan sit ɗin ta shiga sannun Yusuf ya ja motar suka bar wajan...... *Fulanin Jajirtattu ce* *Comments & share fisabilillah*👏 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Isma'il Cameroon* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske typing...✍️* Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/BoEGaUYscLHDtLr41wYFFI https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 61&62 Free Book Bismillahi rahmani rahim ***********K'arasowa suka yi ta buɗe wa Mama bayan mota ta shiga sannun ita ma ta buɗe ɗayan sit din ta shiga Yusuf ya ja motar suka bar wajan. Ba su tsaya ko ina ba sai kofar gidan Aunty Maryam fitowa duk suka yi daga cikin motar,kallon Mama Mufeeda ta yi kana ta ce "Mama kizo mu shiga ciki". "Toh mu je" Mama ta fadi cikin zumuɗi dan babu a bun da take son gani a yan zu sama da Muhsin dan ta yi kewarsu sosai daga shi har Afiya. Kara min gate din suka nufah sai Habib ya dakatar da su ta hanyar fadin "ku dan tsaya sister"! Dakatar da tafiyan suka yi ya ciro waya daga cikin aljiwun shi ya shiga nemo number "Aunty Maryam yana ganin number d'in ya ya danna mata kira amma har ta tsinƙe ba ta ɗaga ba. Ita ko Aunty Maryam tana nan tare da baƙi shi ya sa gaba ɗaya bata ji kiran ba, saboda bata ma san inda ta ajiye wayan ba ma. Shi kuwa Habib ganin da ya yi har 2 miss call ya yi mata bata d'auka ba ne ya sa shi mai da wayarsa cikin aljiwu Muhsen ne ya shigo ɗakin da gubu ya na faɗin "Mommy ana ta kiran ki tun ɗazu".Mommy da take ta faman shirye- shirye yan da za'a gudanar da Kamu gobe ne ta juyo ta ce "Wa ya ke kira na Boy?" "Mommy my Son naga ni" "Maza bani wayan na kira shi dan Habib bai cika kirana haka Kawai ba sai da dalili" Mik'a wa Aunty Maryam waya Muhsen ya yi ya juya zai tafi sai kuma ya tsinci kansa da dakatar da tafiyan saya wa ya yi ya na kallon Aunty data fara magana a waya"Sorry Son abubuwa ne suka min yawa shi ya sa ban ji kiran da ka min ba". "Okay dama muna tare da Maman Muhsen ne shi ya sa na ce bari na kira ki kafin mu shigo ciki". Okay ka yi kyan kai,bari na d'auko key din bangaren Abban Safwan sai na buɗe mana can dan nan part dina akwai muta ne sosai kuma na san baka son muta ne ga shi kuma kana tare da Maman Muhsen" Lumshe ido ya yi ya buɗe su dan har ga Allah baya nin da take masa sun ishe shi gaba ɗaya. "Okay" ya faɗa haɗe da kashe wayan dan ya san part din Abban su Safwan d'in shi ya sa ya kalli Mufeeda "ya ce ku zo mu shiga" Ya juya ya kalli Yusuf ya ce "y'auwa Yusuf ka d'an jira ni yan zu zan fito mu tafi" "Toh yellabaï a fito lafiya" Kai kawai ya geɗa sannun ya wuce ciki ya bi bayan su Mufeeda da tuni sun shiga. "Ke Mufeeda kuxo mu je ba a nan ta ke ba" Kai Mufeeda ta gyaɗa kana suka bi bayan shi suka nufi part din Abban Safwan. Suna zuwa suka tarar da Aunty Maryam na ciki dan shigowar ta part din ke nan tare da Muhsen Dan bayan ta gama waya da Habib ne ta ce wa Muhsen ya zo su je part din Abban ya taya ta d'auko wani abu ya ce "toh" Sannun ya bi bayanta suka zo. K'arasowa Aunty Maryam ta yi baƙin kofar shiga palon ta shiga yi wa Mama sannun da zuwa "sannu da zuwa Maman Afiya dan ba zan ce miki Maman Muhsen ba tun da yan zu Muhsen ya za ma nawa"Aunty Maryam ta faɗi tana dariya. Mohsen dake z'aune sakiyar palon ya na dadda waya ne ya dago ya zuba wa Mama idanu,sanun ya miƙe cikin farinciki ya nufo ta da guɗu har ya k'arasa gabanta ya buɗe hannayensa biyu da niyar yi mata oyoyo sai ya tuna lokacin da ya ke gida in ya dawo daga makaranta in ya zo zai rungumeta ta ke hana shi din nan,sai kawai ya ja baya yana murmushi haɗe da cewa "Mama sannu da zuwa" Jikin Mama ne ya yi san yi sosai tabbas ta san dalilin daya sa Muhsen yaƙi rungumarta, cikin zuciyarta ta furta ya Allah ka ya fe min na tuba' Mufeeda kam gaba ɗaya ta cika da mamaki, tambayoyi ne kala _kala a zuciyarta amma babu mai amsa mata shi. Mama kam hawayen na dama ne ya shiga sauko mata daga kan kumatunta. Habib da Aunty Maryam kuwa tausa yin Mama da Muhsen ne ya kama su,sun san cewa ta yi na dama sosai. Kallon Muhsen Habib ya yi kana ya ce "Muhsen ba kaga Uncle ba ne ?" "Sorry Uncle ina wuni ina Aunty Afiya ta ke me ya sa baka zo da ita ba?". "Sorry zata xo kwa nan_ nan" "Amma kafin nan ina so ka je ka rungumi Mama dan na san ita ma ka yi kewarta sosai" "Toh Uncle ina son rungumarta amma bata so" "A'a ita ma tana so ka je ka gwada zaka gani" "Da gaske ita ma tana so?" "Eh tana so je ka kawai" Karasowa Mohsen ya yi ya tsaya gaban Mama amma ya kasa rungumar ta, Hannu Mama ta buɗe wa Muhsen tana murmushi shi ma Mohsen murmushi ya yi haɗe da faɗa wa jikin Mama. A tare suka s'auke a jiyar zuciya. Allan sarki saka nin ɗa da uwa sai Allah 😢 "Aunty ina wuni "Mufeeda ta faɗi lafiya lau Mufeeda ya gida?" da"alhamdulillah"Mufeeda ta amsa, Aunty ina Aunty Ai'sha Amarya?" "Tana ciki ta yi fushi daku daga ke har Mamana ba wanda ya zo". "Ayya Aunty ku yi haƙuri" "Bani zaki ba wa haƙuri ba.yer Uwarki zaki je ki ba wa tun da ku ba kwa son zumunci" "Toh tana ina na je na ba ta?". Kwatan tawa Mufeeda taƙin da Amarya ta ke ta yi Juyowa Mufeeda ta yi ta nufi cikin gidan. "Toh ku shiga ciki mana Maman Afiya"! "A'a ni kam ba shiga zan yi ba akwai wani abu da nake so na je na yi" "Kai dama aikin ka ke nan" "Allah!ya kyauta ya kuma nuna min ranar da zaka dinga zama cikin muta ne ana hira da kai kamar kowa" Ɗan guntun murmushi ya saƙi da ya saya iya labensa,kana ya kalli Mama ya ce"y'auwa Mama Yusuf zai xo ya d'auke ku anjima" Baki Mama ta buɗe da niyar yin magana sai Aunty ta riga ta cewa "ai baka isa ba, babu inda Mama zata je har sai an kammala biki dan haka in Yusuf ɗin ya zo sai dai ya d'auki Mufeeda amma Mama kam tana nan" Okay ai shi ke nan Aunty duk a bun da ki ka ce shi za'a yi, Mufeeda ma dan bata faɗa wa Mommy ba da har ita zan bar ta ta kwana tun da tare suka zo" *Bayan kwana uku* Washe gari Ammi ita ma ta je gidan Aunty Maryam anan ne suka haɗu da Mama.Mama ta ji dad'i haɗu wa da Ammi sosai kuma ta yi mata godiya sosai akan irin a bubuwan alkhairi da ta yi musu da ita da dan ta. Ammi ba ta kwana a gidan Aunty Maryam amma kullun tana zuwa wuni sai dare take koma wa gida. Ita kam Mommy in ta zo ma ba ta wuni take tafiya gida,kuma bai fi sau biyu ta je ba tun da aka fara biki. Anyi biki lafiya an watse inda Amarya Ai'sha ta tare a gidan Mijinta Aliyu da ke (Kabuga) Mohsen kuwa d'a Aunty Maryam ta ce baza ta ba wa Mama shi ba amma da suka zauna suka tattauna da Ammi da Daddy sai ya ce a barta ta tafi da shi ta yan da zai samu ya shaku da mahaifiyarsa sosai,tun da wan can zaman da suka yi ba wata shakura a saka nin su na sakanin uwa da ɗa. Wannan shi ne dalilin da ya sa Aunty ta bar Mama ta tafi da Mohsen, Amma fah Ibrahim ma ya ce ba zai z'auna ba sai ya bisu,a haka dai duk suka bi Mama suka tafi. A kwana ki kaɗan aka dawowa da Mama komai nata har ma da yer aikin ta Husna! Habib ya so ya dawo mata da dukkan 'yen aikinta amma ta ce ita bata so yer aiki ko ɗaya, wai ita ma zata iya yin aikin ta da kanta ba sai masu aiki sun mata ba. Habib ya ji daɗin hakan sosai kuma ya kara tabbatar da cewa lallaï Mama ta shiryu. Sai da Habib ya sa baki kafin Mama ya amince aka dawo mata da Husna. *Bayan kwana ɓiyu* Gobe ne su Habib za su koma ( Dubaï)kuma a goben zasu cika sati ɗaya a (Kano) Dan so suke su koma saboda bikin Habib da Nadra saura sati uku,shi ya sa ma tare da Daddy da kuma su Mufeeda za su tafi. Ammi ce ta je gidan su Mama dan tun da ta zo bata je ba, Ammi ta jima sosai a gidan Mama sun yi hira sosai sai da yamma Habib ya zo ya maida ita gida..... *Fulanin Jajirtattu ce*✍️ Comments and share fisabilillah 👏 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Isma'il Cameroon* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske typing...✍️* Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/BoEGaUYscLHDtLr41wYFFI https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 63&64 Free Book Bismillahi rahmani rahim ***********Ammi ta jima sosai a gidan Mama sun yi hira sosai da yamma Habib ya zo ya maida ita gida, *Bari mu leƙa gidan su Basira* Kwan ce ta ke a gidan su kusan wata biyu ke nan bata da lafiya,shiru ta yi kanta na sama ga hawayen da suke ta faman ambaliya da ga kan kuncinta, ta shiga magana ita Kaɗai "Najib me ya sa zaka min haka?tun da na ke ban taɓa jin ina son mutun sosai kamar ka ba,duk da kuwa ba yau ne na fara soyayya ba,na yi soyayya da mutane daban _ daban amma ban taɓa haɗuwa da wanda ya kwanta min a rai sosai na ji ina so na aure shi ba sai kai,sai kuma Habib Muhammad Habib,shi ƙad'ai na ji ina so kuma so na aure na ke masa,a lokacin da nagansa da wata na ji babu dad'i amma da na haɗu da kai Najib!a kwana ki kaɗan da na yi ta re da kai sai na nemi soyayyan da na ke yiwa Habib na rasa, amma shi ne zaka min haka?ka ce zaka zo baka zo ba har yan zu gashi wayan da muke yi yan zu ko shima babu me ya sa _me ya sa zaka min haka,dan Allah ka taimaka ka dawo gare ni "Ta kara she maganar haɗe da sakin kuka mai ban tausaya yi, Wani irin tsawa Basira ta ji an ɗaga mata ɗago wa ta yi da s'auri mahaifinta taga ni tsaye a bakin ƙofar shiga ɗ'akin nata,hannu ta saka akan fuskarta ta shiga go ge hawanyen da ta ke zubuwa da ga kan kuncinta haɗe da k'irk'iro murmushi, "Daddy sannu da dawo wa"?mai ma kon mahaifinta ya amsa mata sai ma binta da kallo daya shiga yi,takowa ya soma yi har ya ƙara so inda ta ke zaune,hannu ya sa ya wanke ta da mari lafi'yayyu har guda ɓiyu akan kuncinta,dafa wajan ta yi haɗe da miƙe wa tsaye, "To marar kunya ko zaki rama ne.?" "A'a Daddy ba zan rama ba amma na yi mamaki sosai da marin da ka yi min dan ni kwata _kwata ban san mai ma yi ba.?" Murmushi tak'aici mahaifin Basira ya yi kana ya ce "Ubanki ki ka yi na ce Ubanki ki ka yi yanzu ke baki ji kun ya yi min wannan tambayar ba?ni bazan miki baki ki kara lalacewa ba amma abu guda ɗaya da zan gaya miki shi ne ki g'agg'auta nemo wanda ya yi miki wannan ciki in ba haka ba zan d'auki mummunar mata ki a kank'i,kuma ko da wasa kar na ga k'afarki ta taka ko ƙofar gida ne".Ya na kaiwa nan ya juya ya bar ɗakin Cikin mutuwar jiki Basira ta koma ta zauna gefan gadonta ta yi shiru ta na tunani mafita *Mufeeda 9h na dare* Kwance ta ke akan gadonta Ai'sha kuma ta na wanka, Waya ta ke ta na cewa "humm Yaya Yusuf tun lokacin da ka dawo dani da ga gidan Aunty Maryam na baka number d'ina na ce in ka je gida ka kirani baka kira ni ba, yau ma saboda ni na kiraka da bansan san da zaka kira ni ba,k'ila ma tun ranar dana baka number d'in ka y'edda ita" "A'a wallahi ba haka ba ne Ranki ya daɗe kawai dai tsoron kiran ki na ke" "Tsoro kumaYayaYusuf"?."Ehwallahi""Toh tsoron me?""Kinfi kar'fi na Ranki ya daɗe ta ya zan kira ki bayan ni ba kowa bane""Gaskiya Yaya Yusuf ban ji dad'i wannan maganar ba" "Sorry in na ɓata miki rai amma gaskiya na faɗa ni dan Allah ki de na kirana ma dan in yayanki ya ji bazai ji dad'i ba" Yusuf na kaiwa nan ya katse kiran. "Hello! Hello!" Mufeeda ta shiga fadi amma ta ji shuru ta na duba wa ta ga ya katse kiran,jiki babu kwari ta miƙe dan ta na so ta je wajan Habib su yi magana saboda gobe in sun tafi Dubaï ba lallaï ne ta ganshi ba. Mayafinta ta d'auka ta yafa har ta saka hannu zata buɗe kofa ta ji Ai'sha na mata magana juyowa ta yi ta kalle ta,ta na nan tsaye bakin ƙofar fita toilet ɗin da ga ita sai wata ƙaramin tawol da ko ciny'oyinta bai gama rufe wa ba "Me ki ke kallo na?" cewar Ai'sha Tsakii Mufeeda ta saƙi haɗe da buɗe Ƙofa ta fita ta maida ta rufe ta nufi bangaren Habib ta na addu'a Allah ya sa bai yi bacci ba Kwan ce ya ke akan gado ya yi ruf'da ciki ya na waya,kallo ɗaya zaka masa ka fahimci cewa wayan da ya ke yi ba kara min dad'i ya ke masa ba,dan ko ya na yin yan da yake rufe idonsa ma zai tabbatar maka da hakan. "Wallahi na yi missed dinku sosai Yayana baka ji yanda na matsu safiyan nan ta yi na ganku kun dawo ba" "Hummm really my Beauty!"? "Yeah" "Nima haka amma ta ya zan yadda kin yi missind d'ina?" "Ka bari in ka dawo zaka ga yan da na rame" "Rame wa kuma ?" "Eh mana" "Toh ni dai gaskiya in har na dawo na tarar kin rame ba zan ji dad'i ba" "Toh kaga ni,shi ya sa na ce maka kai baka yi missind d'ina ba" "Na yi mana sosai _sosai" "Ban yadda ba" "Na san missind d'in Nadra kawai ka yi baka yi na kanwarka ba" Jin ta ambaci sunan Nadra ne ya sa lokaci ɗaya mod d'insa ya canza,haka ma murmushin da ya ke yi "Hello! Yaya kana ji na kuwa?" "Eh ina jin ki" Ya faɗa sai kuma ya ji ana mai nocking "Beauty ina zuwa nocking ake min" Bai jira amsar ta ba ya katse Kiran ya miƙe ya nufi bakin ƙofar dan ganin wa ya ke masa nocking kofa a wannan lokacin. Yana zuwa bakin kofah ya sa hannunsa ya buɗe kofar, Mufeeda ya gani saye a bakin kofah, Haɗe rai ya yi ya shiga tambayar ta "Ke kuma lafiya zaki zo min da daɗɗare" "Sorry brother magana zamu yi please " Mufeeda ta faɗa haɗe da mar'air'ai ce fuska Matsa mata ta yi ta shiga ciki ya rufo kofar ya koma ya z'auna gefen gadon,ita kuma ya nuna mata kujera ya ce ta "z'auna". "Ina jin ki mene ne ?". Magana Mufeeda ta fara yi kamar haka...... *Fulanin Jajirtattu ce* Comments and share fisabilillah👏😍 [6/21, 15:24] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Isma'il Cameroon* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske typing...✍️* Utilise ce lien pour intégrer mon groupe WhatsApp : https://chat.whatsapp.com/BoEGaUYscLHDtLr41wYFFI https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 65&66 Free Book Bismillahi rahmani rahim **********Magana Mufeeda ta fara yi kamar haka "Bro da ma akan Yusuf ne..." Ta faɗa sai kuma ta yi shiru ba tare da taci gaba ba Tun da yaji ta ambaci Sunan Yusuf ya kafe ta da da ido,lokaci ɗaya kuma ya saki guntun murmushi, sai kuma ya tamke fuska kamar ba shi ne wanda ya yi murmushi a yan zu ba. "Ke in ba zaki magana ba ki tashi ki tafi ni bacci nake ji" Taji ya faɗa,tana son ci gaba da yi masa baya ni amma tana jin kunya, kai bata ma san ta ina zata fara ba. Wani tunani ne ya zo mata a kai dan haka wayarta dake hannunta ta kunna haɗe dayin dealing number Yusuf, Yusuf da ke kwance bacci har ya soma d'aukarsa yaji wayarsa na ringing, dan guntun tsaki ya ja sannan ya daga wayan ba tare daya tsaya duba mai kiranshi ba, ya saka a kun ne ya yi shiru ba tare da ya yi magana ba. "Yaya Yusuf ni ce." Mufeeda ta faɗa buɗe ido Yusuf ya yi sosai ya ta shi daga K'wacen da yake ya z'auna kana ya soma magana "Haba ranki ya daɗe daya zaki min haka dan Allah dan annabi ki kyaleni,ki baki mu dinga gaisawa in na zo wajan yayanki dan wallahi kinfi karfina bai kamata ki dinga waya da mutun iri na ba wanda bashi da komai" Ya kara she maganar. Kasancewa a handprin Mufeeda ta saka wayan shi ya sa Habib ya ji duk a bunda ya fada,kashe wayan Mufeeda ta yi dama a bunda take so ya fada ke nan kuma ya fad'a. "Bro zan tafi yanzu tunda ka ji mai ya kawo ni wajanka"Ta faɗa ba tare data tsaya jin mai zai ce ba ta fita ta bar ɗak'in. "Ma sha Allah!" Ya furta had'e da sakin murmushi,kana ya miƙe ya je kashe duka fiti'lun dake ɗakin sannun ya hau gado, bayan ya yi addu'a ya k'wanta ya ja bargo ya rufe cikinsa da shi,babu jimawa bacci ya d'auke shi. *Washe gari* Tun da ya yi Sallah a subaha bai koma ba, k'arasa shirya kayan sa ya yi,bayan ya kamma'la wanka ya shiga bayan ya fito ya shirya cikin farar jallabiya ya naɗa wannan rawanin da (larabawa ( suke nadawa a ka sosai ya yi kyau ya fito a (Balaraben) sak! Fita ya yi ya nufi cikin gida domin yin breakfast, Bayan sun gama breakfast suka ɗunguma zuwa airport, Basu wani jima sosai a airport ba jirginsu ya ɗaga zuwa kasar (Dubaï) Kasancewa ita Hajiya Maimuna(Mommy)bata je ba dan ko airport ma bata raka su ba, ta ce ita sai biki saura kwana uku zata zo, Daddy ta buɗe baki da niyar yin masifa sai Ammi ta hanashi ba yanda ya iya a haka ya gyale ta. *Dubaï Abu Dabi* Tunda na tashi da safe ban koma ba sai shirye_ shiryen dawowar su Ammi nake ta fama yi,dan y'au duk wanda ya ganni zai gane cewa ina cikin farinciki Su Ummi da Abe sai dariya suke min, Bayan na taya masu aiki girin mun yi mun gama ne na koma dakina na je na yi wanka, da sallahr azahar,dan har an kira. Palo na koma ina zuwa na tarar da Nadra da mahaifiyarta sun zo,gaida mahaifiyar Nadra na yi sannun muka gaisa da Nadra Kallon mu Abie ya yi kana ya ce"ku tashi mu tafi lokaci ya kusa" Baki muka had'a muka ce "Toh" Sannan muka mike muka nufi wajan ajiye motoci,mota uku muka d'auka, Na Nadra dana driver sai nawa,dan nima yanzu na iya tuƙi. Bamu jima da zuwa airport ba jirginsu ya sauka. *Bayan minti 10* Hango su muka yi suna saukowa daga cikin jirgi, Mikewa dukan mu muka yi muka nufosu muna murmushi,suma murmushin suke yi. Muna zuwa kafin na je wajan shi Nadra ta rigani zuwa ta rungumeshi, Dan haka wajan Ammi na je na runguma,shafa kaina Ammi ta yi tana murmushi,"Ammi na yi kewarki sosai""nima na yi kiwarki habibti" Kafin ka ce me Shima ya haɗa daga ni har Ammi ya runguma,a tare muka sauke a jiyar zuciya Shafa kanmu Ammi ta yi sannun ta shiga daga Habib daga rungumar da ya yi mana. "Beauty a hakan ne ki ke cewa kin yi missind d'ina?". "Watoh mu baza'a kulamu ba ke nan?" Mufeeda ta faɗa. Ai'sha kam saboda takaici ma kasa magana ta yi,dan ita bata raina abu ko kaɗan Jin hakan da Nadra ta yi ya sa ta fadin "hey!ya kuke ya anya?". Cikin sanyin murya Mufeeda ta amsa,da "Alhamdulillah"! Ai'sha kam tsaki ma ta ja haɗe da barin wajan ta nufi wajan su Ummi da Abie domin gaishe su, Dan duk iskancinta tana girmama manya. Saboda dama Daddy tunda suka s'auka daga cikin jirgi ya wuce wajan su Abie domin kwaso gaisuwan sirkai. Dan murmushi na yi sannun na karasa inda Mufeeda ta ke saye kafin ka ce mai na faɗa jikinta na rungumeta sam a jikina, Kai in kaga yanda na yi sai ka d'auka na santa,nan kuwa iya kacina hoto,dan ina ganin hoton su a gidan su Habib da suka yi su duka har ma da Mommy a ciki, shi ya sa kallo ɗaya na yi musu naga ne su ne, Daskarewa Mufeeda ta yi a wajan ba tare data rungume Afiya back ba. Sakin Mufeeda na yi kana na ce "Sorry sis welcome?" Murmushi jin dad'i Mufeeda ta yi kana ta ce "thank you""amma kina da kirki" "Na gode! Amma kema kina da kirkin ai" Murmushi kawai Mufeeda ta yi, Matsowa wajan Maman Nadra Habib ya yi ya gaisheta,ta amsa cikin sakin fuska haɗe da yi masa ya hanya ya ce alhamdulillah"! Bayan angama gaisawa ne suka shiga mota suka dunguma zuwa gida.... *Fulanin Jajirtattu ce*✍️ Comments and share pls😍👏 [6/25, 15:08] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da haske typing...✍️* Bi wannan mahaɗi don shiga guruf ɗin WhatsApp ɗina: https://chat.whatsapp.com/K0ug6sIXtuyFaEI3q27XDx https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 67&68 Free Book Bismillahi rahmani rahim **********Bayan angama gaisawa ne suka shiga mota suka dunguma zuwa gida, Habib ya shiga motarsu Nadra da shi da Ai'sha da ba haka ta so ba,dan kwata_ kwata ita bata shiri sosai da Nadra saboda girman kan da take da shi,wannan din ma saboda Habibi ne ya ce ta shiga shi ya sa ta shiga amma ba a son ranta ta shiga ba. Daddy kuma motarsu Abie ya shiga da shi da kuma Abie,su ɓiyu da dreve uku. Ammi da Mufeeda da Ummi kuma a mortar Afiya suka shiga, Ammi da Ummi na baya Mufeeda na gama sai Afiya dake tuki. Sorry masu karatu na manta a wancan page din na ce Afiya ta koyi tuki,bayan kuma ta riga data iya tuƙi tun tuni.kun san a bubuwa sun yi yawa akan nawa 😹 *Gidan su Habib* Kasan cewa su Mufeeda suna da dakinsu shi ya sa muna zuwa gida suka nufi dakinsu domin watsa ruwa, Wanka suka je suka yi su duka har da Ammi da Daddy, Bayan sun gama suka fito suka ci a binci Ranar hira sosai aka sha sai da yamma Nadra da mahaifiyarta suka tafi gida Ina lura da Yaya Habib yanda ya ke satar kallo na Muna son mu keɓe mu ɓiyu amma ba hali tunda su Mufeeda da Ai'sha suna nan *Bayan sati ɗaya* Shirye _shiryen biki ake sosai babu kama hannun yaro,kana ganin zaka gane bikin 'yen gata ake yi, Dan daga Nadra har Mahaifiyarta gidan suka dawo suka haɗe ana ta shirye _shirye tare kun dai san bikin fararen fata,in ana biki daga iyayen ango har dana Amarya duk haɗuwa suke waje ɗaya Gyaran jiki ake wa Nadra sai naga abun ba kara min burge ni ya yi ba, Ammi na lura da ni sosai ta yan da nake kallon yan da ake wa Narda gyaran jiki ɗin kuma ta fahimci abun ba kara min burge ni ya yi ba.shi ya sa ta ce nima na zauna ayi mun, Zo kaga murna a waje na,su Mufeenda mai zasu min banda dariya, Ana haka ne sai Ammi ta ce suma su Mufeeda su z'auna ayi musu,a haka muka z'auna aka yi mana gyran jiki na bam mamaki, Rana ɗaya aka min amma ba kuga yanda na koma ba dan gyaran cikin ba maramin karbata ya yi ba Su Mufeeda sai ya ba gyaran jikin nawa suk'e ta faman yi,har cewa suke wai mai gyaran jiki na sane ta yi nawa tafi nasu kyau Ni dai babu a bunda nake yi sai murmushi *Kano* *Gidansu Basira* Tun lokacin da mahaifinta ya ce zai d'auki mummunar mataki a kanta in har bata nemo wanda ya yi mata cikin nan ba. Shi ya sa tun ranar ta ke ta faman gwada number Najib amma bata shiga. Bangaren manaja Afiya kuwa tun washegari ranar da Habib ya je company ya kawo 'Yen sanda aka kama Manaja aka kulle a police station ance baza'a sake shi ba har sai ya biya kudin company daya ci sannun za'a sake shi. Sai daya yi kusan Sati ɗaya a kulle sannu ya biya kudin aka sake shi Amma kafin a sake shi sai da aka masa kashesi sosai akan kar ya kara shiga harkan Safna in kuma ya shiga zasu d'auki mummunar mataki akan sa yace in sha Allah bazai shiga ba a haka dai aka kyale shi ha tafi. *Gidan su Mama* Shirye _shirye tafiya kasar(Dubaï)ake ta yi duk wanda ya ga Mama zai gane cewa tana cikin farinciki, Kallo kuma ɗaya zaka mata ka fahinci cewa ta canza ba Kamar wancan Mama da aka sani a baya ba *Dubaï* Gidan cike yake da dangi da kuma 'yen uwa da abokan arziki,sai kai kawo suke a cikin gidan,kowa da abunda yake yi Su Nadra da Afiya ne zaune a dakin da aka wara musu na gyaran jiki,jikin Kowa sai sheƙi da walkiya yeke yi, amma na Afiya yafi nasu yin sheƙin dan gyaran jikin ba kara min karbarta ta yi ba Duk da kuwa Nadra tafi Afiya hasken fata na masayinta na: Balarabiya)amma sakama kon gyaran jiki da aka yiwa Afiya sai ta zo tafita haske. Y'au ne su Mama dasu Aunty Maryam da Hajiya Maimuna( Mommy)zasu diro kasar:Dubaï)kowa yasan da zuwan su amma banda Afiya,dan an ce kar a gaya mata saboda so suke su yi mata bazata shi ya sa ma ba wanda ya je d'auko su a airport sai Daddy kawai da Habib suka tafi *Bayan awa ɗaya* Suna s'auka daga cikin motar ta nufi dakinta dake cikin gidan dan bata son a dame ta,da kallo Daddy da Habib suka bita dashi haɗe da girgiza kai, Mama kuwa tunda suka shiga farfaɗiya gidan take baza ido taga ta inda Afiya zata bullo amma shiru,jikinta ne ya fara san yi,dan tuna ni take ko har yanzun bata haƙura ba?fahimtar hakan da Habib ya yi ne ya sa shi sakin murmushi haɗe da kamo hannunta ya ce "Mama zomu je kiga wani abu".Kafin Mama ta yi magana tuni Habib ya ja hannunta suka nufi cikin gidan,bai saya ko ina ba sai dakin da ake wa su Afiya gyaran jiki,kuma dama shi ma yana son ganinta saboda ya kwana ɓiyu bai sata a ido ba shi ya sa duk ya rame babu a bunda ake fani sai dogon hanci da idonsa da ya kara wani irin haske,shi ya sa yabi ta wannan hanyar saboda shi ma ya samu ya ganta. Suna zuwa ya turo kofar a hankali suka shiga ya mai da kofar ya rufe suka karasa cikin dakin. Matar da take musu gyaran jiki ne ta kalle sa sannun ta fara magana da Larabci)kai kuma Habib ba na hanaka shigo dakin nan ba"?" Sorry wallahi Mama na raka taga Beauty". Ya fada ya shiga kallon dakin kamar yana nemon wani abu,sai ɗaya karewa ɗakin kallo saf amma bai ganta ba. Dan sai su Narda kawai da su Ai'sha da Mufeeda da suke zaune Ai'sha da Nadra wayoyinsu suke danna wa sai Mufeeda da take kwance akan kujera mai zaman mutun uku. Ganin Mama da su ka yi ne ya sa su kallonta suka fara gaishe ta "Mama sannu dazuwa ya anya Ai'sha ta faɗi"."Lafiya lau"Mama ta amsa, Nadra ma gaisheta ta yi sama_ sama taci gaba da dadne dadnen wayan da take yi "Da lafiya" Mama ta amsa, Mufeenda ce kaɗai ta miƙe ta zo ta fada jikin Mama tare da faɗin"Laa Mama a she kun kara so babu ko labari ina Mommy da Aunty Maryam?".Shafa kanta Mama ta yi tana murmushi,"Mommynku tana dakinta ta ce bari ta je ta wuta Aunty Maryam kuma suna Palo da su Mohsin".Ai Mufeeda na jin haka ta saki Mama ta ruga a guje ta fita ta bar dakin ta nufi palo, dariya Mama ta saki, Habib kuwa kai kawai ya girgiza dan ya na son Mufeenda sosai babu ruwanta shi ya sa yake damuwa da damuwarta, Kallon Ai'sha Habib ya yi cikin haɗe fuska ya ce "ina beauty take"?."tana wan.... Ai'sha bata karasa magana ba suka ji na buɗe kofar toilet ɗin na fito d'aure da tawol a irjina gashina sai ɗigan ruwa ya ke,takowa na fara yi na nufi cikin palo ban kula da su ba har sai dana karasa sakiyar palon sannun idanuna ya s'auka akan mahaifiyata wani irin ihon murna na saki haɗe da nufota da s'auri wanna ruwan dake ɗigawa akaina ne na taka zan faɗi ya yi s'aurin riko ni ta faɗa irjinsa,rufe idona nayi ina jiran na jini a kasa sai kawai naji ni akan wani abu mai l'aushi a hankali na shiga buɗe idona har na karasa budesu tar akan kyakkyawar fuskarsa,gyaran murya Ai'sha ta yi ta kalli Nadra da kallo daya ta yiwa su Habib ta d'auke kanta taci gaba da danna wayarta,mikewa ta yi ta karasa gaban mu kara yin gyaran muryan ta yi dan wancan wanda ta yi bamu jiba, s'aurin janye jikina na yi daga na Habib haɗe da yin s'aurin karasa inda hijabina take na d'auka na saka dan tunda naƙe da shi bai taba ganina haka ba sai y'au Juyowa Mama ta yi da niyar barin dakin sai na kira sunan ta "Mamana".Dakatar da bude kofar da Mama ta ke k'oƙ'arin yi ta yi haɗe da juyowa,da guɗu na karasa gabanta haɗe da rungumeta sam a jikina ina sakin kuka "Haba Mamana baki kiwata ba ?".Shafa kaina Mama ta yi haɗe da rungume ni sosai a jikinta da shiga faɗin "na yi kiwarki sosai ma Afiyata dan Allah ki yafe mi"....Bata karasa ba taji Habib ya ce"me haka Kuma Mama ?"Ya yi maganar yana satar kallon su Ai'sha da Nadra ke Ai'sha kimma je kin yiwa su Aunty da Mommy sannu dazuwa kuwa?"A'a Bro ban je ba""Toh Tashi maza jike ki yi musu ki dawo".Kai Ai'sha ta geɗa haɗe da mikewa ta sa takalmin ta ta fice daga ɗakin Mama ta fahimci me ye sa baya son ta yi Magana shi ya sa ita ma bata ci gaba da magana ba sai da Ai'sha ta bar ɗak'in,kasan cewa Nadra da mai gyaran jiki basu iya (Hausa) ba shi ya sa bai damu da su fita ba "Mama ga waje ki z'auna bari na je na dawo ya faɗa haɗe da ficewa ya bar dakin ya ja musu kofah. Bayan fitar Habib ne Hajiya mai gyaran jikin ita ma ta miƙe ta bar dakin dan ta fahimci cewa Habib ya bar dakin ne saboda yana bukatar barin Afiya ta tattauna da Mahaifiyarta, Nadra ce dai taki tafiya dan tana z'aune a dakin Mama bata damu da rashin fitarta ba.ta kamo hannun Afiya ta shiga nemon yafiya a wajan ta,cikin kuka take faɗin"Dan Allah ƴata ki yafe min na yi na damar a bubuwan dana aikata muku a baya dan Allah ki ya fe min Afiya""Haba Mama na yafe miki kuma ni dama can ban riƙe ki ba dan haka dan Allah nima ki yafe min" Ana haka ne Mohsin ya shigo dakin da guɗu yana faɗin "Aunty Afiya oyoyo""Oyoyo ɗan ƙanina ka ce har da kai aka zo?"."eh mana Aunty tare muka zo har ma da Aunty Maryam"Mohsin ya bata amsa haɗe da karasowa kusa da Afiya rungumesu na yi gaba ɗayansu daga shi har Mama muka s'auke ajiyar zuciya a tare. *Bayan kwana ɓiyu* Mama ce da Ammi z'aune a daki sai ni da nake z'aune a gefensu tun dazu suka kirani amma sun ki ce min komai, Sai da aka d'au kusan mintuna biyar kafin Mama ta fara magana,"Afiya!"Mama ta kira sunana"Na'am"na amsa,kinsan yanda a bubuwa suka kasan ce a baya kuma kinsan a bunda ya faru da ke duk da kuwa nice cilar jefaki ciki,dan haka tunda yanzu farincikin mu ya dawo kamar da a lokacin da Abbanku yana raye" "Nasan baki san dalilin daya sa na zo nan Dubaï ba ko?"."Eh Mama ban sani ba amma na d'auka bikin Yaya Habib ki ka zo da kuma ganina""Eh kusan hakan amma babban a bunda ya kawo ni garin nan saboda har da auren ki saboda lokacin da Amminki ta zo :Nigeria)mun z'auna mun tattauna sosai da ita anan ne muka yanke shawara mu haɗa ki da wani dan uwan Mamar Nadra tunda yaron yana da hankali da nitsuwan da kuma sanin ya kamata Amminki ta yaba da halinsa sosai" Wani irn faduwar gaba naji a lokacin da Mama ta furta maganar aure. Sai ta kaina na yi na kirkiro murmushi dan bana so na bata musu rai dole na amince da zabin da suka min saboda bazan taba watsa musu kasa a ido ba, "Baki ce komai ba habibti"Naji Ammi ta faɗa "Haba Ammi ni a ganina bai kamata ku zaunar da ni kan wannan maganar ba ku sani cewa ku fah iyayena ne dan haka duk a bunda kuka yanke a kaina dai_ dai ne""Haka ne habibtina Allah ya miki albarka ya sa ki rabu da mu lafiya".Da ameen na amsa sannun na biƙe na bar daƙin Ina fita ban saya ko ina ba sai daƙina ina shiga na ja kofar na rufe da key na faɗa kan gado na saki wani irin kuka mai ban t'ausa. *Bayan kwana uƙu* An d'aura auren su Nadra sai kuma ni da wannan mutumin da bansan ko waye shi ba,dan s'au ɗaya na taba ganin sa,yana da kyau sosai amma gaskiya ni Yaya Habib yafi min shi. Da daɗɗare aka shirya ni saf Nida Nadra,sai da aka yi mana nasiha sosai sannun aka kaimu gida jen mu, Nadra aka fara kai kafin ni " Bayan an kaini aka barni tare da su Mufeeda da Ai'sha,su din ma daga baya sulalewa suka yi suka tafi suka barni ni ɗaya, Ina ganin haka na saki kuka ina tunani'yanzu shi ke nan anan zanci gaba da zama bazan koma kasata ba?yanzu shi ke nan na rasa Yaya Habib har abadan way Yaya Habib way.me ya sa zaka min ha...ban karasa maganar zuci ba sakama kon kukan dayaci karfina kuka nake mai suma zuciya,jin da na yi an buɗe kofar dakin ne ya sa ni kara s'autin kuka na Takowa ya shiga yi ya nufo inda nake gadan_ gadan... Su Afiya an zama Amarya 🥰💃 *Fulanin Jajirtattu ce✍️* Comments and share fisabilillah 👏😍 [6/26, 20:15] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Ismail Cameroon* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin Attajira* *Muguna Uba* *Duhu da Haske typing...✍️* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K0ug6sIXtuyFaEI3q27XDx https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 69&70 Free Book Bismillahi rahmani rahim Takowa ya shiga yi,ya nufo in da na ke gadan _gadan jin kamshi turaren mutumin da bazan taba iya tire shi a cikin zuciyata da kuma manta wa dashi ne ya sani sai da kukan da na ke yi na dago fararen zara_ zara idanuna wanda sabar kukan da na yi ne ya sa shi janza kala juwa ja,dagowa nayi dan tabbatar wa kaina a bunda na ke ji. Ɗagowan da na yi ya yi dai _dai da karasowar sa in da naƙe,ajiya mamaki na na yi na miƙe zunbur na faɗa cikinsa haɗe da saƙin kuka mai suma zuciya cikin kuka nake cewa Yaya Habib nasan ba za ka bar ni ba na san ba za ka taba barina a wannan gidan ba na san ba za ka taba bari na z'auna da mutumin da bana so ba duk a cikin kuka na yi wannan maganar dan a tunanina na d'auka zuwa kawai ya yi ya ganni ne,shafah baya na ya shiga yi haɗe da runtse idanu,dan bayan son jin kuka na ko kaɗan saboda har cikin rantsa ya ke jin kukan, Bai dena shafah baya na ba har sai da na yi shuru sannun ya dago, haɗa ido muka yi na yi s'aurin sunkuyar da nawa idon kasa hawayen ya shiga share min sai daya share shi tasss sannun ya soma magana "Beautyna me ye sa kika ce haka?me ya sa bakiya son wanda aka aura muku aure tare da shi?"Duk a lokacin ɗaya ya yi min wannan tambayar Shuru na yi ba tare dana bashi amsa ba. Shi kuwa Habib ba dan komai ya sa ya min wanna tambayar ba sai dan so ya ke ya tabbatar ina son shi ko kuwa "Shi ke nan bari na tafi tunda ba za ki faɗa min ba"Ya yi maganar haɗe da juyowa zai tafi Wani irin runguma na yi mishi ta baya,cikin kuka na shiga faɗin"wallahi Yaya Habib bana son wancan mutu min kai nake so dan Allah karka tafi ka barni anan.dan Allah ka tafi dani"Wani ya irin murmushin farinci Habib ya saƙi a lokacin da yaji Afiya na cewa ita shi take so, Juyowa ya yi ya rungumeta sosai kamar akwai wanda zai kwance masa ita "Beauty da gaske ni ki ke so?"Mayafin dake jikina na saka na rufe fuskata da shi ina murmushi,dan har ga Allah bansan ta ya aka yi na faɗi hakan ba Kiss ya sakar min a goshi kana ya kamo hannuna ya yi hanyar toilet da ni,nidai binsa kawai na yi har bakin toilet din, "Shiga ki yi alwala ina zuwa"yana kaiwa nan ya juya zai bar wajan na riƙo hannunsa na fara magana"dan Allah karka tafi ka barni""Ba tafiya zan yi ba Beauty ina nan tare da ke har karshen rayuwata""taya zaka ce kana nan tare da ni har karshen rayuwarka bayan kun riga da kun aura min wannan mutumin?""ni ne nan mijinki Beauty ni aka aura miki"idona na zaro waje ina faɗin da gaske Yaya Habib?""Eh da gaske " Ya faɗi yana lakutan dogon hancina,"Toh amma me ya sa su Mama suka ce wancan zan aura ?"hannunta ya kara kamowa suka dawo cikin dakin,gefen gado ya zaunar da ni shima ya z'auna duka hannayena ya kamo ya hada da nasa ya shiga murzawa a hankali,sai daya d'au kusan mintuna biyar a haka kafin ya fara mani labari. *Satin uku da suka wuce* *(Nigeria)* Mama ce z'aune a palo tare da Ammi suna hira Ammi ta ce "y'auwa Oum Mohsin akwai maganar da nake so mu tatt'auna kafin na wuce (Dubaï)""Toh ina jinki Ammi"?" Mama ta faɗi gyara zama Ammi ta yi kana ta fara magana"Dama akan Beauty da Habib ne saboda na ga suna son junan su sosai duk da kuwa basu taba furtawa juna ba amma na gama fahimtar hakan"."Toh yanzu ya za'a yi dan naga dai an riga da an yiwa Habib baiko da yer uwarta kuma da bakinki kika faɗa min haka kwana kin baya kinga dai bazai yu a bashi mata har guda biyu ya aura a lokaci daya ba""Eh na sani akwai maganar da na yi da su Abie kwana kin baya""Wana irin magana?""Dan gyara zama Ammi ta yi sannun taci gaba da magana "dama Nadra akwai wani dan uwan mamanta da yake sonta kuma ita ma yanzu tana son shi ɗa bata son shi Habib take so saboda akwai shakuwa sosai a sakaninta da Habib toh a lokacin mun d'auka soyayya ce har muka z'auna da iyayenta muka tatt'auna muka yanke shawara muyi musu baiko,anyi baikon su da 'yen watan ni kaɗan sai Habib ya taho da Beauty kasar (Dubaï) irin kulawa da kuma soyayya da Habib ya ke nuna wa Beauty ne da ita kanta Beautyn take nuna masa ko a gaban Nadra nunawa juna suke yi ne ya sa muka sake zama tare da iyayen Nadra dama ita kanta Nadran muka yanke shawara s'auke baikon da muka yi musu,anan ne Nadra take cewa ita ma ɗa ko ba'ayi wannan zaman ba ma ta fasa auran Habib dan a yanzu babu soyayarsa Habib a cikin zuciyata kwata_ kwata a yanzu sai na 'yen uwantaka kawai,anan ne muka yanke shawara bawa wancan dan uwan nata dama turo wa bayan ya turo ne aka saka rana dai _dai da lokacin da za'ayi bikin Habib din da Afiyan shi ya sa na ce in sha Allah in na zo Nigeria zan z'auna dake mu yi magana naji ra'ayinki akan maganar auran na su?".Ammi ta k'are magana ajiyar zuciya Mama ta s'auke kana ta fara magana"Ni dai duk a bunda ku ka yan ke akan Afiya dai _dai ne tunda ku ne iyayenta a yanzu ni dai iya kacina na yi musu addu'a da kuma fatan alkhairi Allah kuma ya sa za'a yi damu" "Ameen ya Allah!Na gode sosai Oum Mohsin" "Ni ce da godiya dan babu a bunda zan iya cewa sai godiya Allah ya saka muku dama fificin alkhairi" "Ameen" Ita ma Ammi ta amsa Dagowa ya yi ya kalleni kana ya ce"kinji yadda aka yi ke nan?""Eh na ji amma ya aka yi kai an gaya maka ni ba'a gaya min ba?"kai Beauty sarkin tambaya toh ni ɗin ma saboda ranar nazo d'aukar Ammi ce na zo zan shiga palon naji suna tatt'auna wa shi ya sa na saya naji komai kinji yanda aka yi naji ke nan?" "Toh da kaji me ya sa baka faɗa min ba" Hancina ya dan ja Kana ya ce"saboda so muƙe muyi miki bazata ne shi ya sa" Baki na buɗe da niyar kara yin magana ya rufe min baki ta hanyar ɗora manuniyar yen yatsunsa akan laɓena ya furta"shiiiiii!...... *Fulanin Jajirtattu ce*✍️ Comments and share fisabilillah 👏😍 [6/29, 23:25] Mom Muwadda🥰: 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena Isma'il Cameroon* *(Mom Muwadda)* *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin Attajira* *Mugun Uba* *Duhu da Haske typing...✍️* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/K0ug6sIXtuyFaEI3q27XDx https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ Page 71&72 🔚🔚🔚🔚 Free Book Bismillahi rahmani rahim *********Baki na buɗe da niyar kara yin magana ya rufe min baki ta hanyar ɗora manuniyar yen yatsunsa akan laɓena ya furta "shiiiiii!" Shiru na yi ina kallon sa "gaskiya Beautyna kin ko yi surutu""ni ɗin?"Na faɗi ina nuna kai na""sosai ma kuwa gaba ɗaya su Ammi sun ɓata ki da suturu yan zu dai ba wannan ba ki tashi ki je ki yi alwalan nan dana sa'aki""Toh"Na faɗi ina miƙewa bina ya yi da kallon so har na shiga toilet, shi ma miƙe wa ya ƴi ya bar ɗak'in, ɗakin daƙe kusa da nawa ya shiga babu jima wa ya dawo dakina lokacin kuma tuni na yi alwala na har na fito ya na shiga ɗ'akin muna haɗa ido ya sakar min murmushi kana ta ce "y'auwa shimfiɗa mana sallaya mu yi sallah"Abun sallah na d'auƙo na shimfiɗa mana sannun ya ja mu sallah! sallah raka'a ɓiƴu muka yi muna itar ya kama kaina ya min addu'a sosai har dana zaman lafiya. *Bayan mintuna arba'in* Munci a binci kala_kala irin nasu na (Larabawa) saboda su ba kaza ake kawowa amarya ba a can,tun da kullun suna cinta a gida jan su, shi ya sa su bazu san kawowa amarya kazan amarci ba Har wanka mun yi amma ba tare ba dan ya ce mu shiga mu yi tare naƙi amin cewa shi ne ya tafi dakinsa ya je ya yi ya dawo, Na tire kaya na ke nan ya rage daga ni sai pand dan har da bra ma na tire saboda ban iya bacci da bra ba,na saka kaina ke nan da niyar saka rigar baccin sai zaren rigar ya makala min a kunne ina ta ƙ'ok'arin tire wa amma ta kasa,ya na shiga cikin ɗakin idonsa ya s'auka akan manya _manya books dina farare tass sai sheƙi suk'e lokaci ɗaya idanunsa suka canza l'auni zuwa ja tabbas shi ma bukaci ne sosai wani lokaci kwana ya ke da ciwon mara amma a haka ya ke d'aure wa, ƴ'emmata deyewa sun sha kawo mai kan su amma bai taba basu fuska ba. Cikin san yin jiki ya shiga takowa a hankali ya nufi in da naƙe Ba zato ba sammani na ji an rikoni ta baya,kamshin turaren sa daya jika min hanci ne ya tabbatar min da shi ne, Wani irin ihu na saki haɗe da faɗin "Haba Yaya Habib babu kyau fah ya zaka min haka dan Allah dan annabi ka sake ni"Na kara rike kunnena daya makale da zaran riga ta "Ki tsaya in tire miki kar ki ji ciwo" Ya faɗi a hankali a cikin kunnena ya na yin yan da ya yi maganar ne ya sa tsigar jikina ta shi,shi ya sa ban kara tanka masa ba har ya tire ya na tire min zaran ya tire ɗan kunnen shi ma ya ajiye su a gaban mirror tun da muna kusa da mirror. Rigar kuwa ya je fah shi a ƙasa sai a lokacin ya karewa jikin nawa kallo sosai dama irjina dan ina da irji sosai tabar kalla,wani irin numfashi ya ja haɗe da saƙina ya zauna kan carpet din ɗak'in,gani da na yi ya saƙe ni ne ya sani s'aurin juyowa na nufi in da ya ajiye min rigata na dur'kusa na d'auki rigar zan na ɗago ke nan da niyar miƙewa naga sai riƙe mararsa ya ke ga idonsa da ya yi wani irin ja,cikin ruɗewa na karasa gaban shi,shi kuwa Habib idonsa ne ya ƙara s'auka kan irjina ba sai kawai naga ya kara jan numfashi ba haɗe da kwamciya a kasa ya na riƙe mararsa, Ni kam kwata kwata ban fahimci komai ba, Kuka na saƙi na shiga jijjiga shi haɗe da kiran sunan shi "Yaya Habib! dan Allah ka de na min haka ka de na min wannan wasan ba na so dan Allah ka dena"Ba tare ɗaya yi min magana ba ya mika min hannunsa babu musu na saka nawa hannu ya saka ragowan karfin da ya ke da shi ya ja ni na faɗa cikinsa hannay'ensa ɓiyu ya haɗa ya rungume ni sosai a jikinsa ya na s'auke ajiyar zuciya. Wasu abubuwan da ba'a taba yi min su ba na ji ya na min,tun da lokacin da oga Jabir ya yi anfani da ni ba'a cikin hankalina naƙe ba tun da magani ya zuba min a lemo na sha Cikin kuka na ke cewa "dan Allah ka bari ba na so da zafi dan Allah kar ka yi""shi ke nan Beauty na bari amma ki sani in har baki bani ba mutuwa zan yi"Ya faɗi haɗe da miƙe wa daƙer ya hau gado ya kwanta ruff da ciki, Cikin tashin hankali na bishi kan gadon ina faɗin dan Allah ka yi haƙuri zan baka a bun da ka ke so amma dan Allah karka mutu ka barni ba zan iya rayuwa babu kai ba.ina jikin DUHU kai ne ka kawoni cikin HASKE dan haka dan Allah karma min haka dan kai HASKE na ne ba'a tafiya cikin DUHU sai da HASKE"Na k'are magana ina sakin kuka mai ban t'ausa yi,kin tabbata zaki bani,kai na kawai na geɗa masa ba tare da na yi magana ba,kara jawo ni ya yi jikinsa, A tak'ai ce dai ranar sai da Habib ya mai da ni matarsa sannun ya kyaleni, Kala mai soyayya kam na shata kala _kala dan a cikin kalamai soyayya babu a bun da ya rage wanda bai gaya min ba. Haka ma albarka shima na shata sosai Ba karamin wahala na sha ba a wajan sa Bangaren Habib kuwa badan Afiya da bakinta ta bashi labarin a bun da ya faru da ita ba da zai ce ita mudurwa ce, Saboda yan da ya samu wajan a rufe Kamar budurwa, Cikin farinciki ya d'auki abarsa sai toilet,ruwan mai zafi ya haɗa ya sata a ciki sai daya tabbatar ta ji s'auƙi abun sannun ya fito ya barta a cikin toilet din ta samu ta yi wankan tsarki, Zanin gadon ya tire ya d'auko wata ya shimfiɗa musu,sannun ya koma toilet din ya t'aimaka mata ta fito. Sai daya tsaya ya t'aimaka mata ta shirya ta k'wanta sannun shi ma ya shiga ya yi wankan ya fito ya shirya bayan ya yi musu addu'a ya kwanta ya ja musu bargo,ya rungumeta sai bacci Ranar dai cikin farinciki da k'aunar juna suka yi bacci *Bayan sati biyu* Su Mama da su Daddy sun koma (Nigeria) Ranar da za su koma ba karamin kuka na sha ba, Ni yan zu shi ke nan na dawo kasar (Dubaï)da zama ba zan sake koma wa (Nigeria) ba sai da Habib da su Daddy suka rarra she ni suka kuma kara da cewa taya zan ce ba zan kara koma wa (Nigeria) ba bayan kuma daga ni har mijina dukan mu 'yen (Nigeria) ne dan haka na kwantar da hankalina,da haka dai suka shawo kaina har na haƙura na dena kuka *Bayan shekara ɓiyu* *Kano Nigeria* *Gidan su Basira* Basira ta haifi cikin shegen da aka yi mata, kana ganin yarinyar kaga ubanta watoh Najib dan farace sosai yarinyar,san da take da cikin kullun cikin fargama take saboda batasan cikin waye daga cikin ba.na Mahmud ne ko na Najib saboda ta saɗu da Mahmud ranar da zata tafi kasar Dubaï,amma tun ranar data haifi yarinyar taga farace sosai yarinyar hankalinta ya dan kwanta, Tana haifar yarinyar da wata biyar Babanta ya ce lallaï sai ta je ta nemo uban yarinyar data haifa musu a gida in ba haka ba kuma sai ya tsine mata in ya so ta bi duniya. Hankalin Maman Basira ya tashi sosai,shine taiwa Baban Basira magana daya janye maganar da ya yi amma tana gama magana ya ce mata ita ma in ta kara magana zai s'auwaƙe mata in ya so ta d'auki Basiran su koma gidan su tare da ita,ai Maman Basira na jin haka ta yi tsit da bakinta bata sake furta komai ba. Haƙuri sosai Basira ta shiga bawa mahaifinta daƙer ya haƙura, Ƙuɗin jirgi zuwa ( Dubaï)ya biya mata ya ce ta je ta nemo duk in da uban ƴerta ya ke ta bashi ƴersa ta dawo tazo ta nemi mijin aure ta yi aure in kuma ba haka ba sai ya koreta daga gidansa,cikin rawar jiki Basira ta amince *Bayan kwana biyu* Bayan kwana ɓiyu Basira ya je Dubaï,kasan cewa bata san gidan su Najib ba shiyasa tana sauka a kasar ta nufi hôtel din da ya ke aiki,ta na zuwa kuwa ta nuna musu hotonsa,anan ne masu hôtel din suke sh'aida mata cewa shekara ɗaya da suka wuce ya bar aiki anan,amma sun yi mata kwatancen gidan shi ta tafi Basira ta je gidan su Najib kuma ta yi sa'a data je ta nuna wa Najib Babyn data haifah ba'a wani sha wahala ba ya karbi yarinyar hannu ɓiyu,kuma data faɗa masa a bun da mahaifinta ya ce in ta dawo zai mata aure shine ya yan ke shawara binta Nigeria a yi musu aure duk da bashi da ƙudi sosai a hannunsa amma gwara ya je a haka,a hakan dai suka yan ke shawara nan zuwa jibi zasu je Nigeria, Basira ta ji dad'i sosai,kuma ta kira mahifinta ta yi masa baya nin komai Bayan kwana ɓiyu Najib da Basira suka je (Nigeria) mahaifin Basira da ya ga Najib jikinsa ya yi san yi sosai,dan ba irin mijin da ya ke burin aurawa ƴayansa ba. Saboda shi dan gidan mutunci da kuma tarbiya ya ke son bawa ƴayansa,ga shi kuma shi Najib kallo daya zaka masa ka gane ba wani tarbiyan kirki ya ke dashi ba,dan daga yana yin askin kansa ma zai tabbatar maka da hakan,amma ya na yin yan da abun ya zo ne ya sa ba'a wani d'au lokaci ba ya abince Baban Basira ya cewa Najib ya sanar wa da magaba tansa suzo a yi maganar auran nashi,shi ne ya ce mahaifinsa ya daɗe da rasuwa dan tun ya na shekara goma sha ɓiyar Allah ya yir masa rasuwa Mahaifiyarsa ƴar kasar (Sudan)ce mahaifinsa ne balataben kasar (Dubaï)shi ya sa lokacin da Mahifinsa ya rasu da mahaifiyarsa ta ce ya zo su koma kasar (Sudan) yaƙi amince wa,dan shi ya tsaba da kasar (Dubaï)a haka dai mahaifiyarsa ta tattara na ta eh na ta ta koma kasar (Sudan)ta bar shi a (Dubaï) ƙuɗin da mahaifinsa ya bari ne ya shiga yin bushasha da shi har ya cinye su tass daga baya ya z'auna ba shi da ko sisi Wannan shi ne dalilin ɗaya sa ya shiga nemo aiki ke nan Babu in da bai je nemon aiki ba amma bai samu ba sai a wannan hôtel ɗin da suka haɗu da Basira. Najib ya faɗa wa mahaifin Basira labarinsa,amma bai faɗa masa cewa mahaifinsa ya bar dukiya mai yawa ya cinye su ba. Yana gama faɗa wa Baban Basira Baban Basira ya ce "Allah!ya yi masa rahma ya amsa da "ameen kana ya kara da cewa ya kira ɗaya daga cikin kawun nan sa,anan ma dai ya ce bashi da number dinsu Shiru Baban Basira ya yi ya rasa mai zai ce, sai kawai ya ce"toh shi ke nan ka je ka same su ka faɗa musu in ya so sai ku taho tare"Baki Najib ya buɗe da niyar yin magana sai Basira ya yi wa Mahifinta magana da Hausa tun da shi Najib baya jin (Hausa)sai Turanci : da kuma (Larabci)kawai ya ke ji,shi ya sa Basira ta yi wa mahifinta magana da (Hausa)kaga Abba ka zama waliyinsa kawai a yi a d'aura auran dan wallahi in ya tafi ba lallai ne na kara ganinsa ba Dan nisawa Baban Basira ya yi kana ya ce "yan zu in na ce zan zama wakilinka kana so?".Shiru Najib ya yi na y'en mintuna kana ya ce "eh ina so"shi ke nan zan baka daki a nan gidan kafin zuwa kwana shiɗa saboda so na ke a haɗa d'aurin auren dana ƴar uwarta Naja'atu,kai Najib ya geɗa kana Baban Basira ya ce wa Basira ta je da shi ta kai shi ɗaki na musamman da zai z'auna kafin lokacin,kai Basira ta geɗa sannun ta raka Najib ma s'aukinsa. Bayan kwana shiɗa aka d'aura auran Najib da Basira sai kuma Naja da Yayan Safna kawarta aka aura musu aure. Ita ma dai Safna kusan watan ta ɓiyar da aure Bayan an d'aura auransu Basira Najib ya d'auke ta suka wuce Sudan din,amma sai da aka haɗa ta da wata goggonta watoh ƙanwar mahifinta saboda sun ce ba za su barta ta tafi daga ita sai Najib ba. Sai da goggon Basira ta je (Sudan)taga in da gidan su Najib ya ke sannun ta dawo (Nigeria) Ba lefi sun samu tarba sosai a wajan mahaifiyar har dama s'auran y'en uwanta Najib dan tana da kirki sosai,da taga Basira da yarta kamar ta haɗiye su saboda so Najib da Basira sun yiwa Maman Najib karya kan cewa sun daɗe da aure saboda ba sa so su fada mata cewa tun kafin aure suka haihu. Mohsin da Ibrahim dan gidan Aunty Maryam sun kara girma sosai dan s'aura shekara ɗaya ma kacal ya rage musu su kammala makaranta Bangaren Ai'shan Aunty Maryam ma ta na z'aune lafiya da mijinta Aliyu a yan zu haka suna da yaro Huda ɗaya. Bangaren Mufeeda sosayyarsu da Yusuf ya yi nisa sosai har ma manya ya shiga maganar anyi angama har ma an saka rana a yan zun haka s'aura wata ɗaya kacal ya rage ayi bikinsu dan har dana Ai'sha kanwarta za'a haɗa *Dubaï Abu Dhabi* "Habibti zo kiga wani abu"."toh gani nan zuwa"Na faɗi da s'auri na fito daga cikin kitchen din na nufo ɗakin dan a zatoh na_ na d'auka ko barna Zarina ta ke min ne dan ya wanci in ya min wannan kiran toh ba lafiya ba, Abun mamaki ina zuwa na tarar da Zarina bata ɗakin,kara sowa na yi gefen gadon ina cewa Habibi gani"shiru ya yi kamar mai bacci dan a kwance ya ke akan gado ga kuma idonsa dake rufe kamar mai bacci, "Shi ke nan bari na koma naci gaba da girkina tun da bazaka faɗa min dalilin ɗaya sa ka kirani ba"Na faɗi haɗe da juyowa zan tafi ya riko hannuna ya jani na faɗa irjinsa kara ya saƙi "washhh! a lokacin dana faɗa jikinsa"wallahi habibti zaki karya ni"Ya faɗi ya na kara jani a jikinsa,haba yan zu duka_ duka jikin na wa _nawa take da zaka ce zan karya ka"wani irin hararan wasa ya tallamin kana ya ce "ba ki ga yan da ki ka koma ba tabar kallah!"Na ji ni dai faɗa min dalilin ɗaya sa ka kira ni?"."Toh shi ke nan kawo kunnanki na faɗa miki dan bana son kowa ya ji""Haba habibi mu ɓiyu ne fah kawai anan kuma sai na kawo kunnena"."Eh mana ke dai kawo na gaya miki"kwantar da jikina na yi dai_ dai nashi kana na matso da kunnena s'aitin bakinsa na ce"Toh fada min""Toh" ya furta kana sai ya ciji kunnen nawa kaɗan wani irin kukan shogoɓa na saƙi sannun na ce "habibi me haka?".na faɗi ina turo baki gaba,dongon hancina ya ja kana ya shiga yi min wasu abubunwan mai yiwan fassara sai a lokacin na ga ne dalilin kiran da ya min,wani tunani ne ya zo min dan haka na ce "Habibi kasan mene ne kuwa?"Kai ya girgiza min alamar bai sani ba,kwana kin baya da muka je Nigeria na je gidan Ai'shan Aunty Maryam mun haɗu da mijinta ashe ma mijin tsohon saurayina ne"wani irin kishi ne ya taso wa Habib kana ya buɗe baki daƙer ya ce "toh in kin je (Nigeria)kar na saƙe gani kin je gidana su"murmushi na dan yi haɗe da ja hancinsa,kana na ce "tsarkin kishi toh ba saurayina ba ne.ya dai taba cewa ya na sona a lokacin da naje zuwa mutsa jiki,in na muka fara haɗuwa da kai toh acan shima muka haɗu""toh da kuka haɗu mai ya ce miki"?".cewa ya yi ya na so na shi ne na haɗa rai na ce masa ya je zan neme shi tun lokacin bai saƙe ganina ba sai ranar dana je gidan su muka haɗu a can,da muka haɗu ya nuna Kamar bai sanni ba nima na nuna kamar ban taba ganinsa ba""ummm sai yan zu na ji magana"Habib ya faɗi ya na ci gaba da abubun daya fara mim ɗazu "Habibina girkifah na ke yi"Na faɗi.bai tanka min ba sai ma daga ni da ya yi daga jikinsa ya miƙe ya bar ɗak'in babu jimawa ya dawo, "Na je na kashe miki gass din"zan yi magana ya haɗa bakinmu waje ɠuda ya ginda kissing Ni kam fitowa na yi na ja musu kofah na kara gaba dan mu ba mu iya wannan abun ba 🏃‍♀️😂🤌 *Bayan sheraka ɓiyar* An yi bikin Yusuf da Mufeenda haka ma Ai'sha kanwar mufida a yan zu haka Mufeenda na da Yaya ɓiyu mace dana miji,in da Ai'sha kanwar Mufeeda kuma take da ƴah mace ɗaya sai tsowon cikin da take da shi a yan zu Habib ya mallakawa Yusuf companyn Afiya,sai da ya yi da gaske kafin Yusuf ya amince ya karbi companyn Ya budewa Afiya wani katon company a (Dubaï) ya saka maikata sosai a ciki way'en da zasu dinga kullar mata da companyn, saboda ita ba kullun take zuwa ba *Bangaren Basira* Tun lokacin da aka d'aura musu aure tare da Najib soyayya wata daya kawai suka yi,ya dinga kawo mata 'ƴammata kala _kala a gida ya zo ya kwata da su,wani lokaci ma in ya sha giya a gabanta ya ke kwanciya da su din Ana haka ne ya kwanta rashin lafiya ana kaishi a sibiti aka shai da musu cewa Najib na d'auke da cutar mai karya garkuwan jiki,tun da Basira ta ji wannan labarin take kuka sai tsinewa Najib ta ke wai shi ke nan ya lalata mata rayuwa ya sa mata cuta maganganu dai ga su nan kala _kala A haka dai ta dawo gida ta zo ta haɗa kayanta ta wuce tasha ta shiga mota sai garin (Kano) Tana dawowa ta fadawa mahifinta a bun da ya ke faruwa duk suka shiga tashin hankali anan ne mahaifinta ya shiga yin magana kamar haka "kin ga a bunda na ke gaya miki ko amma ki ka ƙi y'edda sai da ki ka je ki ka jajibo mana wannan cikin da kuma wannna mutumin yan zu ga irinta nan. Basira bata yi magana ba a haka ta wuce a sibiti tana zuwa aka mata tess anan ne aka tabbatar mata da cewa ita ma ta kamu da cutar da aka faɗa mata suma ta yi a sibitin sai da aka yayyafa mata ruwa sannun ta farfado bayan an bata maganin da zata dinga sha aka kira mahifinta ya zo ya tafi da ita gida *Bayan wata uƙu* Suka ji labari Allah ya yi wa Najib rasuwa, Ita ma dai Basira duk ta rame ta yi baƙi duk ta fita daga cikin hayyacinta Tana cikin taƙ'aba ita ma Allah ya yi mata rasuwa Iyayenta sun yi kuka har sun gode Allah! *Bayan shekara ɓiyu* *Kano Nigeria* *Aminu Kano international airport* Mama ce da Ammi da'a yan zu sufah ya fara kama su ne suk'e sallama rungume juna suka yi kana Ammi ta ce "Oum Mohsin sai mun sake zuwa sunan ɗan Mohsin Kuma tun da yan zun mun zo biki Murmushi Mama ta yi sannun ta ce "Haba dai in sha Allah kafin nan zaku dawo ko kin manta matar ibarahim ta kusa haihuwa ne"?"Eh haka ne kuma. toh Allah ya s'auke ta lafiya"Da"ameeen Mama ta amsa Zuwa na yi na rungume Mama ina cewa "toh Mama sai mun saƙe zuwa"Shafah kaina Mama ta yi sannun ta ce "Ameen ya Allah!Allah ya kai mu""Ameen nima na amsa. "Sitti!Oum fah ta yi girma ki ce mata ta dena yiwa Mama haka" ƴaron da bai wuce shekaru uƙu ba ya fada, Dan a yan zu Afiya ta na da ƴaƴa uku maza ɓiyu mace ɗaya,a yan zu haka ta bar guda biyu a gida da kara min kawai tazo Dan way'en can sun yi girma dan macen mai suna Nuria(Zarina)a yan zu tana da shekara 8 sai ta biyu mai suna Abubakar (Munif)na da shekara 6 sai wanda aka zo da Shi mai suna Muhammad(Fauzan)wanda aka zo da shi mai shekara huɗu Dariya Ammi ta yi kana ta ce y'auwa gaya mata dai my boy ko zata dena Dariya suka yi su duka sannun suka kara yiwa juna sallama suka nufi in da jirgi da za su hau ya ke, *Cikin jirgi* Ammi da Fauzan na gabam mu_mu kuma muna bayan su shi ya sa basa ganin a bun da muke yi Kwantar da kaina na yi kan kafaɗunsa haɗe da kurawa kyakkyawar duskarsa idanu,shima ni ya ke kallo,murmushi muka sakarwa juna kana ya furta "I love you my wife"Lumshe mai ido na_ na yi sannun na ce "I Love you more H.M.H" murmushi ya saki sai ya tuna lokacin da naƙe kiran sa da sunan ya matso da bakinsa s'aitin kunnena ya furta "Afiiiiiiii! A hankali 🥹❤️ Nima fah Sakina na ce "Afiiiiiiii! 😂Atoh nima baza'a barni a baya ba 😂😂🤌 Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!! Duka_ duka anan na kawo muku karshen Wannan littafin nawa mai suna DUHU DA HASKE 🥹 Abun da na faɗi dai _dai Allah ya sa mu amfana da shi😍 Wanda na faɗi ba dai _dai ba Allah ka yafe min da ni da masu karatu gaba ɗaya, Ina yinku sosai masoyana masoyan❤️😍 littatafai na 📚 Godiya tamu samman ga kungiyarmu ta Jajirtattu💪 Allah ya saka muku da alkhairi ya biyaku da gidan Aljanna Ameen 🥰 Allah ya kara hada kanmu 😍 Sai mun haɗu a wannan sabon Book d'in dana fara mai suna :Ni DA KaNIN MIJINA,karku bari a baku labari dan salonsa shima daban ne dana s'auran🥰 Zan yi missind din su Afiya da ɗana Habib 🥹😩 *Fulanin Jajirtattu ce ✍️* [6/30, 14:29] Mom Muwadda🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KpwDZw5aq7C2Pr2NCZ3Ujg 🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑🌑 *DUHU DA HASKE* *By* *Sakeena ismail Cameroon* *(Mom muwadda)* 🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼 *Marubuciyar* *Bazan zauna da kishiya ba* *Mijin attajira* *Mugun uba* *Duhu da haske typing*...✍️ Page9&10 Free book Bismillahi rahmani rahim ******"Ya fada yana hade rai kamar ba shine dazu yayi magana cikin sakin fuska ba,cikin sanyin murya ta fara magana..kayi hakuri Mr H.M.h!amma wllhy ba haka bane ? Toh in ba haka ba?ya ne ?ya tambaya? yana tsare ta da idanu,sunkuyar da kanta tayi kasa dan bazata iya jure ganin kwayar idanunsa ba, saboda kwarjinin sa yayi yawa, Ke nake sauraro ? Habib ya sake fadi,wllhy lefin seketariya ta ce,bata gaya min,sune suka zo ba, Karfa ki renamin hankali afiiii! Lumshe ido tayi a lokacin da yake kiran sunan nata"dan ji take duk duniya babu wanda ya iya kiran sunanta sama da shi"saboda yanda ya kira sunan nata ba karamin dadi sunan yayi mata"ba, Mutanena sun fada min kingansu a lokacin da kike barin office! Sabota sun tabbatar min da cewa har gabansu"kikazo kika wuce kika fita, Amma shine yanzu zakice lefin seketariyarki ce" Rasa bakin magana afiya tayi dan yanzu kam surutun nasa"ya soma damunta" Mutun sai tsurutun tsiya? Ta fada a kasan makogoro, Abunda bata sani ba shine,habib irin mutanen nan ne masu ji,dan ko maganar zuci kayi yana ganewa, Humm yanzu maganar da nakeyi ne shine tsurutu?"Habib ya fada yana kallon afiya, Dagowa tayi cikin mamaki tana fadin wllhy ban....bata karasa ba,ya daga mata hannu, Karki kuskura ki rantse akan karya,yana kaiwa nan ya mike, Ya fara kokarin barin office din,har ya kai bakin kofah sai ya tsinkari maganarta tana fadin...dan allah Mr H kayi hakuri,ka dawo muyi magana, Karki damu Habib Muhammad Habib in yayi niyar taimako baya janyewa,ya fada ba tare daya juya ba,dan haka hannu yasa ya bude kofar ya fice. Habib Muhammad Habib !haka afiya ta shiga mai maita sunan akasan lebenta" Wai yana nufin shine Habib Muhammad Habib da nakejin lbr,wai dama shine yazo jiya naji samari na magana,ta fada, Tabbas shine,dan sai yanzu na gane dalilin dayasa ya saka HMH, Habib Muhammad Habib !kenan ta fada, hade da mikewa, Kayanta ta fara tattakawa tana saka a jaka, Bayan ta gaba fita tayi,ta samu safna a office dinta,tana aiki a wasu ta kardu. Safna ni zan wuce,ta fada tana kallon safna, Aunty tun yanzu? Eh,bana jin dadi wannan mutumin yazo ya samin ciwon Kai da wannan hayaliyar nashi" Kina nufin wannan balaraben safna ta tambaya, eh shi fah, Ko kin sanshi ne? afiya ta tambayi safna, Zaro ido waje safna tayi tana fadin tabb aunty ni asu wa da zan san babbar mutun kamar wannan, Shikenan,na tafi,toh aunty allah ya kiyaye "Ameen afiya ta fada a lolacin da take kokarin barin office din"har ta zo bakin kofah,kome ta tuna sai ta juya tana fadin...safna kina jin lbrn Habib Muhammad Habib,da sauri safna ta mike tana geda kai,tare da fadin karfa ace wannan shine aunty? Tabbas shine safna, Haba dole yayar kawata ta damemu da sunanshi" Kikace me safna?"afiya ta fada tana dawowa cikin office din. Kina nufin yayar kawarki tasan Habib, Eh aunty,amma fah shi bai santa ba,itta ce dai take haukanta itta kadai,saboda sun taba shiga jirgi tare,toh tun a lokacin take sonshi"shiyasa ma har yanzu batayi aure ba. Ni ba wannan na tambayeki ba safna, Toh aunty kece fah kika tambayeni,toh naji gayamin tasan komai akanshi ne ?"shiru safna tayi kamar mai nazari, Sai kuma tace a'a aunty lbrn sane kawai ta taba bamu ni da Naja kanwarta, Good afiya ta fadi,tana jawo kujerar dake cikin office din ta zauna, Bani lbrn naji,?"yau kuma aunty kece da jin lbr? Dakata safna zaki bani ko bazaki bani ba natashi na tafi?" A'a yi hakuri aunty allah ya wuci zuciyarki,ni na isa ince bazan baki ba,bari ma kigani,safna ta fada itta ma ta koma ta zauna. *Labari* Alhaji Habib Ibrahim babban dan kasuwa ne tako waca fenni, Irin mutanen nan ne da ake kira kome da ruwanka,ya shahara sosai ta fennin kasuwanci, yana da yara guda uku, Muhammad ne babba,sai Nabila,sai Maryam autarsu" Matarsa daya hajiya aisha wacca akafi sani da hajiya indo! Sun bawa yaransu tarbiya dai dai gwargwodo, Ga kuma ilimin da suka samu,daga boko har arabiya, Kasan cewa Muhammad shi kadai ne namiji kuma shine babba a cikin yaransa"shiyasa ya gaji mahaifinsa ta harkan kasuwanci,kasan cewa shima ta fennin kasuwancin ya karanta shiyasa abun yazo mai da sauki,dan tunda ya fara harkan, kasuwanci komai nasu ya karaci gaba,dan duk garin babu wanda bai san alhaji Habib Ibrahim ba, Wani kata faren kanfani seda a tamfofi da lesika suka bude, Akwai wata rana da Muhammad yake zaune da abokinsa"auwal,anan ne auwal yake bawa Muhammad lbrn irin kudaden da yake samu ta harkan seda man petir,ya kuma kara da cewa mezai hana shima bazai gwada ya gani ba,da farko dai Muhammad kin amincewa yayi,saboda a cewarsa suda suke da wayennan kudaden wana kudi kuma suke bukata, Auwal yace haba abokina ta yaya kudi zasuyi yawa, Da Muhammad yaga auwal ya nace,sai yace mai insha allah zaiyi shawara da mahaifnsa duk yanda sukayi zai gaya masa"da haka dai suka rabu, Bayan Muhammad ya gayawa mahaifinsa yanda sukayi da auwal shima yayi na'am da maganar,dan haka yacewa Muhammad yaje ya tambayi auwal in za'a fara sana'ar kamar nawa za'a bukata?" Bayan Muhammad yaje ya gayawa auwal yanda sukayi da mahaifinsa yaji dadi sosai,dan haka ya gaya masa kudin,sannun shima Muhammad yaje ya fadawa mahaifinsa" *Bayan wata biyu* An kammala komai inda Muhammad ya bude gidan mai,yasaka mutane yana mai aikin,shikuma yana kula da kanfanin mahaifinsa" Wasa wasa a cikin shekara uku,sai ga Muhammad ya mallaki gidan mai har guda shiga,dan ba karamin karban sa sana'ar yayi ba, Shiyasa auwal ya fara kishin Muhammad,duk da kuwa shima yana samu amma na Muhammad ya bashi mamaki sosai,har yayi na damar bashi shawaran seda man petir, Muhammad yaga canji sosai wajan auwal,dan abukantakarsu"ya faka ja baya,kuma a duk lokacin da Muhammad zai tambayi auwal dalilin canzawar shi cewa zaiyi babu komai, *Bayan wata biyar* Yanzun kam Muhammad ya fahimci kishi auwal yakeyi dashi"amma har yanzu,bai dena zuwa wajan auwal ba"duk da kuwa shi auwal a yanzu baya zuwa wajan Muhammad,kuma in Muhammad din yaje wajanshi,ba wani kulashi yake ba, Tun Muhammad yana jure wulakancin da auwal yake masa"har ya kasa ya hakura shima ya fita sabgarshi" *Bayan wata biyar* Alhaji Habib Ibrahim ne zaune a palo tare da matarsa hajiya indo" Sai Muhammad dake Zaune a kasan carpet din,yana jiran yaji da lilin dayasa mahaifinsa ya kirashi" Gyaran murya alhaji Habib yayi ya fara magana kamar haka... Muhammad kafi kowa sanin cewa kaine babba kuma kai ka dai namiji,allah ya baka komai na rayuwa ilimin addini dana zamani duk ka samu babu wanda baka samu daga ciki ba" Dan haka ina so ka kawomin matar aure nan da sati biyu, saboda na gaji da ganinka a haka, Alhaji Habib ya karashe maganar, Tunda mahaifinsa ya fara magana kansa yake kasa"bai dago ya kallesa ba har ya kai aya,dan wannan dabiyarsa ce, Shikenan abba insha allah zanyi abunda kace, Masha allah allah yayi maka albarka, Ameen Muhammad ya amsa" Zaka iya tafiya alhaji habib ya fada, Toh nagode abba Allah ya kara girma?"Ameen"abba ya amsa shi kuma Muhammad ya mike ya bar palon. *Bayan kwana shabiyar* Muhammad yau sati biyu har da kwana daya bakace komai ba, Dan haka ina so na sani inda maganarmu ta kwana?" Wllhy abba ban samu ba amma insha allah ina ci gaba da nemowa, Haba Muhammad yanzu so kake kace min har yanzu baka samu ba,wai kai ko kunya ma bakaji?"kannenka duka sunyi aure amma kai har yanzu,kayi hakuri abba,kaga malam ba hakuri zaka saya bani ba,matar aure nace ka nema,dan haka na kara baka sati daya,in har baka kawo ba,ni da kaina zan zabo maka wacca ta dace da kai,dan haka kana dawowa daga tafiya Dubaï da kace zakayi,ka gabatar min ta matar da zaka aura,tashi ka tafi na sallameka, alhaji Habib ya fada, Jiki a sanyaye ya mike ya bar palon, *Bayan kwana biyu* *Dubaï ,habu dabi* Tun lokacin daya shigo supermarket din yaganta tana siyayya,kuma da alama takusa gamawa,dan haka sauri yayi shima ya dauki a bunda yake da bukata"lokacin kuma har ta wuce wajan biya,dan haka shima da sauri saurin sa ya karasa wajan biyan,kudi ta fido dashi da niyar biya ya rigata ajiye magodan kudi a gaban masu biyan hade da cewa....gashi ku hada nawa da nata duka ku dauka anan,in bai isa ba kuma sai a karo,ya fada da harshen larabci,saboda ya iya sosai shima, Da yake yana yawan zuwa"Dubaï, Murmuchi saurayin yayi yana fadin haba yellabai ai wannan kudin tamayi yawa"dan na tabbata kana da ragowar canji ma a ciki, Okay shikenan ka saka mana kayanmu a leda, in yaso ka rike canjin, Muhammad ya fada yana kallon saurayin,godiya saurayin yayi ya shiga hada kayan, Yer matashiyar budurwar da tun da suka fara magana bata saka musu baki ba ?tayi magana..kaga ka dauki iya nasa kudin ni ina da kudin da zan biya ta fada tana mika mai kudin dake hannunta" Hannu biyu Muhammad ya hada yana rokonta,kinga dan allah dan annabi karki maida hannun kyauta baya,kinga babu kyau maida hannun kyauta baya,shiru tayi,bata ce dashi komai ba,kudin data fito dashi ta mayer cikin jakarta,tare da dauko kayan da aka saka a leda, sannun ta fice daga cikin supermarket din, Da sauri sauri ya karbi tasa ledan yabi bayanta" Da yayi niyar yace mata dazo ya rege mata hanya,sai kuma yaganta da mota" Bude bayan mota tayi ta saka kayan data siya a ciki,sannun ta zaga ta mazaunin dreve ta bude murfin da niyar shiga sai taji Muhammad na magana....kinga pretty kisaya dan allah,sayawa tayi cak da shiga motar da tayi niyar yi,har ya karasa wajan da take saye, Sunana Muhammad Habib Ibrahim,ya fada, Badan komai ya gaya mata sunansa ba"sai dan yana so itta ma ta fada masa"nata sunan, Fahimtar da tayi ne yasa ta murmusawa, tare da fadin... Sunana muriya ?woww suna mai dadi, thanks ta fada a yayinda take shiga cikin motarta,hade da jawo murfin motar da niyar rufewa, Saurin rike murfin motar yayi yana fadin dan allah number wayarki,yatsine fuska tayi hade da turo dan karamin bakinta mai ja lebe gaba, Pls ya fada hade da hada hanna yensa biyu alamar roko, Kate dinta"ta dauka a cikin motar ta mika masa"hannu na rawa ya karba,yana godiya,itta dai bata saya ta saurareshi ba tayiwa motarta key ta bar wajan.......... *Sakeena ismail Cameroon ce ✍️* 07049322735