[1/1, 2:21 PM] Aunty Usee: *_🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*🤝🏻 ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* _Writing by_📚✍🏻 *_Ameena Musa_* _(GARO)_ *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_Wattapad_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com *_Not edited_*📵 1 Kanta kife yake bisa jakar Kayanta ta Ghana,. Kuka takeyi kamar ranta zai fita duk da a bakin titi take hakan baisa taji wani tsoro ko fargabar kasancewar ta a wajan ba. "Ina ma mutuwa nayi na irin wannan rayuwar, meyasa banbi iyayena ba nake raye har yanzu" saurin istigfari tayi tunawa da tayi da wannan Sabo ne hakan Allah yaso ya ganta amma meyasa ita rayuwar ta kullum cikin jarrabawa take ne,.. Tambayoyin da basu da amsoshi ta dinga yiwa kanta a bakin titin duk da dare ya fara yi amma sam batajin tsoro ko kaɗan dan batama san a wanne gari take ba tasan dai birni ne duba da Yadda yanayin shi yake..... Gudu yake shararawa kamar zai tashi sama dan yasan hankalin mommy yana gareshi tunda yakai dare a waje abinda bai saba ba gashi ita kaɗai ya baro a gida. A hankali yake bin wakar turawan dake tashi Daga cikin motar tashi, amma duk da haka bai rage gudun ba saboda yadda dare yayi masa.... Tsugunne take kamar yadda take tun ɗazu kusan awanta guda a wajan harta fara tunanin tashi taci gaba da jan kafar ta takai koma inane danta samu abincin da zata saka bakinta dan idan bata manta ba rabonta da abinci tun ranar jiya shima ba wani abin kirki taci ba. Tun daga nesa ya hango alamun mutum harya kusa karasowa nan ya tabbatar da zargin shi kuma abin da yafi bashi mamaki macece kuma da alamar tana cikin matsala. Harya wuce saikuma ya reverse ya tsaya saitin ta. Fitowa yayi daga motar ya tsaya yana kare mata kallon, lallai tana cikin damuwa to amma me takeyi a gefen titi tana matsayin mace mai daraja. Waigawa ya fara yi hagu da dama yana kallon titin da motoci suka fara ɗauke wa sai lokaci zuwa lokaci suke wucewa. A hankali ya tako har zuwa kusa da ita sannan ya rankwafo dai dai fuskar ta. "Baiwar Allah, Baiwar Allah..."! A hankali cikin nutsuwa ta ɗago kyakkyawar fuskar ta, yunwar da takeji ne ya hanata sukuni hakan yasa bata nuna firgici akan fuskar taba. Katse mata tunanin ta yayi ta hanyar tambayar ta. "Me kikeyi anan haka, dare fa yayi bai kamata kizo kan titi ki zauna ba" Tunda yafara Magana take kallon shi amma bata fahimtar abinda yake cewa dan ji takeyi kamar ba duniyar takeba. "Pls ki tashi zan kaiki gida idan mota kika rasa" "Ka kyaleni kawai gara mutuwata ta riske ni a nan" tana faɗa ta mayar da kanta kasa taci gaba da kukan ta. Tuni zuciyar shi ta karaya dama shi Sarkin tausayi balle akan mace dayake kallon su masu rauni. Ganin hankalin ta baya tare da ita gashi dare na karayi yasa yace "shikenan dan Allah kizo muje gidanmu idan yaso zuwa safiya saina kawo ki gida.." Abin mamaki ko gama rufe baki baiyi ba ta mike tana kallon shi alamar su tafi ɗin. Cikeda mamakin ta ko tsoron shi bataji duk shidin namiji ne kuma saurayi amma ko ɗar bataji ba. Saida ya ɓude mata ɓangaran mai zaman banza sannan shima ya zagayo ya shiga ya tayar da motar ya fara tafiya. Lokaci zuwa lokaci yana kallonta saidai ita sam bashi take kallo ba hasali ma idanuwanta a rufe suke tanajin yadda cikin ta ke kugi,. "Lallai wasu iyayen dole suci wuta ta hanyar wofantar da amanar da Ubangiji yabasu, ga yarinya kyakkyawar ajin farko amma ta kare a bakin titi kuma ko tsoro bata alamun tanaji, duk yasan mommy bazata yi masa faɗa ba saidai ma taji daɗi". Kallonta ya sakeyi sannan ya mayar da hankalinsa kan driving ɗin dayake yi. Itako ko gezau bataji ba saima daɗi da taji koba komai tasan zata abinci taci ta koshi ko iya hakan ma ta godewa Allah. Wani tafkeken gate light Ash naga yayi horn, da sauri mai gadin ya bude masa, yana shiga ya wuce wajan faka motocin ya aijye. Sam batama San sunzo ba idanuwanta na rufe ta faɗa kogin tunani,. Ganin batasan ma yazo gida ba yasa yace "baiwar Allah munzo" Kamar mai bacci a ɗan firgice ta tashi sannan ya zagayo ya buɗe mata motar. Tunda ta fito take kallon tsaruwar da kyaun gidan kamar a turai, katon gida ne mai shegen kyau da tsari kusan part uku ta iya gani duk da lokacin dare yayi, saidai kyan gidan yasa yanzu tafara tsoro "shikenan yau kuma gidan ƴan shan jini na kawo kaina, Allah ka fitar dani".... "Muje mana." Muryar shi ta katse mata sauran tunanin ta. Jikinta a sanyaye duk lakar jikinta ta saki yunwar tuni ta gudu tsabar tsoro,. Shikam ya saka ta a gaba ganin sai waige waige takeyi, yana bayanta yana dariya kasa ƙasa....... *_comments dinku shine zaisa naci gaba_*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 *_DAGA ALKAMIN FIRST LADY🌹_*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 08112138112 _for adjustment and WhatsApp only_ [1/1, 2:21 PM] Aunty Usee: *_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_* ```{United we stand and succeed: Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* _By_📚✍🏻 *_Ameena Musa_* *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_Wattpad_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com 2 Mommy gaba daya hankalin ta gama tashi dan yaronta bai taɓa kaiwa haka yana waje ba danko dinner baiyi ba gashi wayarshi taƙi shiga , tana cikin zagaye palour taji karar tsayawar motar shi sannan ta saki wata ajiyar zuciya ta zauna... Cikin sanɗa take tafiya kamar ɓarauniya, ganin alamun a tsorace take ne yasa yayi gaba yabarta a baya. Shi mamakin yakeyi dan yaga da farko bata tsorata ba amma tunda suka sauka yaga dukta sauya ta tsorace. "Kana ganin iyayen ka zasu yadda na kwana a nan kuwa "? Yayi mamakin jin Muryar ta dan baiyi tunanin tanada daɗin Murya hakaba,. Saida ya riƙe handle ɗin kofar da zata sada shi da main palour sannan ya jiyo yana kallonta murmushi yayi yace "mommy na zata yarda karki damu" sannan ya Tura palourn ya shiga. "Hibban ina kaje ne hak...!" Maganar mommy cak ta tsaya tana karewa yarinyar da hibban ya shigo da ita, sai boyewa takeyi a bayanshi tana jiran taji abinda mommy zata ce dan tasan shikenan korarta zasuyi. "Haba sweet Mom kinsan ai ina nan dawowa gareki" ya ƙarasa maganar yana jiyowa da kallon shi ga yarinyar da suke tare dan yaga mommy takasa zama tana neman ƙarin bayani danko Amsar daya bata bata saurara ba. "Hibban Ina ka samo kyakkyawar yarinya haka, kuma meya haɗa ka da ita"? "Zauna Mom zanyi Miki bayani daga baya, yanzu dai I'm hungry kuma itama tanajin yunwa" "To shikenan kuje dining room abincin ka yana can har naci nawa dana gaji da jira" "Yauwa mommy nah I love you so much" "Naji nidai jeka ci abinci kuje tareda ita sai kuci tare" mommy tace tana janyo ƙatuwar wayarta. "Muje ko, ki ajiye kayan naki a nan" Bata bashi amsa ba saidai ajiye kayan tayi tabi bayanshi tana tafiya a hankali dan ji takeyi kamar zata faɗi saboda tiles ɗin da aka makaka a palourn. Mommy tana lure da ita har suka shige dining room ɗin sannan ta mayar da hankalinta kan wayarta. "Yau kuma yar ƙauye ya kawo min, Allah yasa dai ba halin nashi ne ya dawo ba." Mommy ta faɗa a zuciyar ta... Hibban saida ya zauna yafara cin abincinsa sannan ya ɗago kai Yana kallanta yadda take ta kalle kalle takasa zama. "Zauna mana" ya katse mata kallanta. Kujerun wajan take kallo sannan tabi dining ɗin da kallo an shaƙe shi da abinci kamar na mutum goma. Kamar mai koyon zama haka ta zauna a kujerar, da kanshi ya tashi yayi zuba mata. Kallan abinci takeyi kamar maisan tuna wani abu, "bazaki iya ci bane" ya tambaye ta. Daga masa kai tayi dan bata taɓa ganin irin abincin ba saidai yau. Tashi yayi yafara buɗe mata cooler abinci duk wanda ya buɗe mata saitace a'a. "To wanne zaki iya ci saina taso kuku ya dafa miki" "Kabarshi zanci wannan ɗin kawai, ngd" ta faɗa tana cire spoon ɗin tafara ci da hannu. Abin har mamaki ya bashi yadda take cin abincin kamar tayi sati bata ciba tsayawa kallanta yayi cikeda da tausayin ta harta gama. "Kin koshi" "Eh" kawai tace dan har Yanzu bata gama sakin jikinta ba. "To tashi muje na nuna Miki inda zaki kwanta naga kamar bacci kikeji" Da sauri ta tashi tace "a'a daka barshi ma kawai, yanzu zan tafi na gode da taimakon ka gareni" Mamaki ne ya kama shi yama rasa mai zaice mata, kallan wrist watch ɗin dake hannun shi yayi sannan ya mayar da kanshi gareta. "Kibari zuwa safiya saina kaki har gida, karfe kusan daya yanzu bai kamata ki fita a matsayin ki na mace ba" ya ƙarasa maganar yana kallan yanayin ta. "Ko biki yarda dani bane, kina ganin zamu Cutar dake ne.."? Ya faɗa yana gyara tsaiwa... "A'a shikenan zan kwana na gode" tace tana wasa da yatsun hannunta. Bakaramin daɗi yakeji ba a duk lokacin da tace ta gode yana ganin hankalin ta ƙarara saidai akwai tarin damuwa a tattare da ita. Baiyi magana ya nufi hanyar fita tana binsa a baya har palour, yadda suka bar mommy haka zo suka sameta itadai tana bayansa a boye. "Mommy zan kaita ɓangaran ma'aikata zata kwana acan" "A'a kabarta anan mana ai kamar bakuwa ce kaita wancan ɗakin" ta nuna masa wani daki dake palourn. Kayanta ya dauka suka nufi ɗakin, tana biye dashi tana jinjina mutumci irin na taddijuwar nan. "Ga ɗakin da zaki kwana idan kina bukatar wani abu ɗakin mommy na upstairs saiki ke ki tambayeta, ki saki jikin ki mommy mutuniyar kirki ce kinji" Daga masa kai kawai tayi dan ta fahimci mutanen arziki ne su duka ga mutumci da karamci. Harzai fita tace "ina ne wajan wanka inaso zanyi wanka" Murmushi yayi yace "I'm sorry mantawa nayi" ya faɗa sannan ya nuna mata bathroom din ya fice. Lallai wannan yanada mutumci ha fara'a sannan ga hakuri. Bathroom ɗin ta shiga wanda ya tsaru kamar bana dakin baƙi ba, a cikin bathroom manne yake da toilet duk waje ɗaya. Ta daɗe tana tsaye dan dakyar ta iya amfani da kayan bathroom ɗin ji takeyi kamar a mafarki take saida ta dade sannan tagama wankan ta tsaya tana karewa banɗakin kallo. "Ikon Allah harda wani madubi (mirror) a bayi ga wani tawuli nidai bazan iya saka wannan na fita ba ai sainaji kunyar kaina ma" ta faɗa a ranta Sannan ta fito. Nan ma gaban madubi ta tsaya tana kallan kanta duk da ba kayan kwalliya dana shafa amma saida ta dade a tsaye a wajan. Komai cikin kauyanci takeyi ta taɓa Wannan ta taɓa wancan kamar wata yarinya. Saida tagama komai sannan ta kwanta kan Italian bed ɗin dake ɗakin, a hankali tafara tunanin iyayenta dakuma rayuwar da tayi. Hibban kuwa yana zuwa palour ya ƙarasa kusada mommy dake zaune har lokacin tana jiran fitowar shi. Saiji tayi ya sako kanshi ta gefen wuyanta "mommy I'm very tied, I want to sleep" "Babu inda zakaje saika yimin bayanin inda kasamo wannan yarinyar" Zagayowa yayi yana dariya "oh mommy! Dama nasan tunda kika ganmu tare zaki fara zargi na kuma nina yi muku alqawarin bazan sake bin wata mace ba ko shan wani ba" "Naji, amma faɗamin inda kasamo ta" Labarin yaɗuwar yabata itama ta tausaya mata sosai kuma take taji yarinyar ta kwanta mata dama Mommy Akwai san yara mata saidai Allah bai bata ba hakan yasa duk sanda hibban ya kawo mata yara take karbar su saidai daga baya su gudu. "Shikenan da safe saimu tambayeta labarinta idan batada kowa ne saimu riketa dan naga da nutsuwa a tareda ita" "A'a fa mommy haryanzu kinasan zama da wata ne bayan kinsan yaya Habibullah ya bayasan wannan kwashe kwashen nawa ko so kike idan ya dawo ya koreni daga gidan Gaba ɗaya" ya tambaye ta cikin sigar tsokana. "Ai kaine da kwashe kwashe kaita tsinto yara marasa hankali saina saba dasu sai suyi min sata su gudu". Dariya sosai hibban yayi sannan yayi mata sallama ya nufi part ɗinsa. Mommy ma tashi tayi ta haye sama dan kwanciya. Hibban saida ya kwanta sannan ya fara tunanin yarinyar, kwarai tanada hankali da nutsuwa sannan daga gani bata kebewa da wani namiji ba dan ya fahimci takasa sakin jikinta ne dan batada sabo da hakan. Yasha gogayya da yammata kala kala kafin yayan shi ya hanashi wannan dabi'ar saidai bai taɓa haɗuwa da mai kamun kai kamar wannan ba Allah yasa ta zauna tare dasu koba komai zai samu abokiyar hira.[1/1, 2:21 PM] Aunty Usee: *_🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*🤝🏻 ```{United we stand and succeed: Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* _By_📚✍🏻 *_Ameena Musa_* *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_Wattpad_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com 3 Cikeda da tunanin yadda zasu kaya da yayan nashi idan ya dawo bacci ya sace. Da asuba ta tashi sam ta manta a ina ma ta kwana, tana buɗe ido tayi saurin tashi tare da addu'ar tashi daga bacci a bakinta. Sake bin dakin da kallo yayi, "wai yau ni JIDDAH ce a irin wannan gidan" ta faɗa a ranta. Tashi tayi ta nufi bathroom tayi alwala. Tana idar da Sallah ya nufi palour dan taya Mommy aiki. Dai dai fitar ta mommy ma tana saukowa daga upstairs. Har ƙasa ta duƙa ta gaida mommy cikeda kunya. Itama mommy da fara'a ta amsa tana tambayar meyasa ta fito Yanzu. "Mommy na fito tayaki aiki ne" Murmushi mommy tayi sannan tace "ayya, bani nakeyi ba ai yan aiki ne Amma muje ki tayani zan haɗa coffee" Ba musu tabi bayan mommy har kichine ɗin, kallan kichine ɗin tayi "lallai su komai nasu na masu kuɗi ne" ya faɗa a ranta. Mommy na haɗa coffee itakuma tana gefe tana kallanta dan batasan ma menene wani coffee ba. Hibban ne ya shiga kichine ɗin sanye da ƙananan kaya da suka amshi jikin shi yayi kyau sosai da hibban ba baya bane wajan kyau da gayu. Saida ya gaida mommy sannan JIDDAH ta gaida shi a kunya ce. "Bakuwa tazama yar gida kenan harda su shigowa kichine" ya faɗa ta sigar tsokana. Murmushi kawai bata tanka masa ba. Kansa ya mayar ga mommy yana kada key ɗin motar sa "mommy nizan fita" "Ka kira kasha coffeen Mana" mommy tace. "No mommy kema kinsan ni wannan bai dameni ba, kema yaya Habibullah ne ya koya miki dan da bahaka kikeba" "Gaskiya kuwa Habib ne ya koya min" "Jiddah ko zaki raka yayan naki ne" "A'a mommy, sannan ta mayar da kanta gareshi daya kafeta da ido. "Nagode da taimakon da kayimin sosai" "Babu komai ki jira na dawo saina kaiki bakin titi" daga haka bai sake magana ba ya fice. Suma fitowar sukayi itada mommy suka nufi dining room. Saida mommy tagama Shan coffeen sannan ta ɗago ta kalli JIDDAH dake zaune kanta a kasa ta kasa shan coffeen tun ɗazu. "jiddah meyasa kika baro gida a irin wannan daran kina matsayin mace..."? Shiru jiddah tayi ma wani lokaci dan bazata iya kin faɗa musu gaskiyar wacece itaba hakan yasa tafara ba mommy labarin cikeda nutsuwa. Iyayena Asalin Fulanin Adamawa ne sana'ar fata ce ta dawo dasu Kano, babana yanada rufin asiri sosai, gida daya suke zaune da kanin sa kawu Audu da matar sa Inna marka. Iyayena sun rasu sanadin rusau ɗin da akayi a wata damina hakan yayi sanadiyyar rayuwar su. Nasha kuka sosai na Rashin iyayena dan Ni kaɗai suka haifa MAHAIFIYATA ta rasu da tsohon ciki. Haka ragamar kula dani ta koma hannun kawuna, kawu Audu. Da farko ya nuna min so kamar yarda ya haifa amma daga baya kuma sai komai ya sauya Sakamakon rashin dacen mata da baiyi ba, sam inna marka ta tsaneni dama can ganin idon iyayena ne. Saida na koma abin tausayi kamar jaka wajan aiki tun ina yarinya ta na iya aikin wahala iri iri duk da babu wani talauci mai tsanani a tareda mu. A haka ta dinga ziga kawuna tanamin sharri tun baya yarda harya koma yana yarda. Talla kuwa saida na koma harda shigowa birni tallan fura. Har girma na tana azabtar dani itada kawu Audu saidai ban taɓa tunanin guduwa ba saidai na tasa hoton iyayena nayi ta kallo ina kukan rashin su danayi. Tun ina da shekaru goma sha Bakwai manema suka fara zuwa wajena, dole inna Marka tasani nake fita wai ai ba jikani zasuyi su sha ba. Ana haka watarana wani Alhj Lawan daga nan birni ya shiga ƙauyen mu ya haɗu dani. Tunda yazo ya samu inna marka shikenan kullum yazo da duka take kora ni sainaje dan kullum yazo saiya bata kuɗi, shikuma kawu Audu baya iya tsawatar mata saidai ma ya ƙaramin. A haka suka tilasta min saina aure shi, babu yadda na iya na amince aka saka rana. A ranar dana gudu kwana biyu kenan da saka rana a matsayin watanni huɗu masu zuwa, na dawo daga aiken da inna marka tayimin na dauko markade naji suna magana kasa ƙasa da Alhj Lawan a zaure yana faɗa mata shifa ba aurena zaiyi ba kawai yazo ne ya lalatamin rayuwa, inna marka kuwa saiji nayi tana fadin wai dama tun tuni tasani amma karya sake ya nuna ya bari ranar da aka daura auran saiya sake Ni a ranar Bayan bukatar shi ta biya. Na razana sosai saidai ina shiga zauran ban nuna naji komai ba. Duk jikinsu yayi sanyi a tsorace inna marka tafara zubamin ashar ma fadi gaskiya kona jisu nikuma fafur na nuna banji komai ba. Dama ba kullum suke bani abinci ba hakan yasa ban damu ba na shirya kayana tsaff bayan uban kukan da naci nayi alkawarin bazan kwana a wannan ƙauyen ba, inna marka na fita makwabta na kwashe yan kuɗin danake tarawa na fito, ban tsaya ko inaba sai tasha daga nan na shigo birni. Kafin nan kusan gida uku naje amma duk wanda naje bana iya zama dan ba gidan zama bane, hakan yasa nafara tunanin ko rayuwata a jarrabawa zata ƙare. Lokacin da yaya hibban ya haɗu dani nan ma gudowa nayi daga gidan wani dan iskan mutum Allah ya kwaceni shine na fito bakin titi yunwar danake ji ne tasa nakasa tare mota ya sameni anan. Takarasa labarin tana goge hawayen da suka maƙale mata tun ɗazu. Ba mommy kaɗai ba har Hibban dake tsaye tun ɗazu yaji komai basu san shigowar shi ba bakaramin tausayin ta sukayi ji ba Musamman mommy mesan Yaya mata. Saijin maganar shi sukayi a kusada dasu "kiyi hakuri JIDDAH dama kowanne dan Adam Akwai tashi jarabawar" Mommy ma cikeda da tausayi dakuma jin wani sabon san yarinyar ya shigar mata zuciya. Ta kamo hannun ta cikin nata "lallai na daɗe rokon Ubangiji yabani ya mace koda ta tsuntuwa ce sai gashi yanzu ya amsa addu'a ta, dan Allah JIDDAH ki zauna tareda mu zamu maye Miki gurbin iyayen ki da kika rasa" Cikeda da karfin guiwa ta daga wa mommy Kai alamu ta amince dan su ta yarda dasu ɗari bisa ɗari. Cikeda farin ciki mommy tace "shikenan yanzu kije ki huta kafin agama breakfast sai hibban ya kaiki ki siyo abubuwan da kike buƙata" "A'a mommy bana bukatar komai" Mommy ce ya katse ta da "banasan musu kuma daga yau banaso kiyi abinda zanji kamar bani na haifeki ba kamar yadda bazan taba nuna bani na haifeki ba" "Shikenan mommy Nagode" sannan ta tashi ta nufi ɗakin ta. "Mommy Amma kina ganin yaya Habibullah zai amince da wannan maganar kuwa" hibban ya tambaye ta. Murmushi yayi "zai yarda Habib yanasan duk abinda nakeso waɗan can ma dan yaga ban damu dasu bane sosai dole yanzu zai yarda" "Tabb yarda yake mugun nan ai wlhy idan ya dawo kila da kanta zata sake guduwa dan wannan koni bai kyale ba Balle yadda ya tsani yaga wata rabe shi, sai anyi magana ya nuna shi mata basu dame shi ba bayan ba wanda yasan me yake aikatawa acan ɗin" Bugu mommy takai masa ya kauce yana dariya. "Saina faɗa masa idan ya dawo, kuma wlhy bai isa ya takurawa yarinya taba saidai shi ya koma inda ya fito kuma dole jiddah ta rabe shi tunda ta zama ya a gidan itama" Hirar Habibullah suka dinga yi sannan hibban ya fice daga gidan Bayan mommy ta jaddada masa Lallai ya dawo da wuri yakai jiddah shopping. [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: *_🌈 KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION🤝🏻_* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 _Story and writing by_📚✍🏻 *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_WATTPAD_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com *_NOT EDITED_*📵 4 Kamar yadda mommy tace Hibban lokacin ma tasowar shi baiyiba ya nufo gida dan kai Jiddah shopping,. Jiddah na zaune a dakinta tayi shiru tana ta tunanin yadda rayuwa ta sauya mata lokaci guda taji an turo kofar ɗakin ta. Idanuwan shi a kanta harya karaso kusa da ita sannan yace "jiddah tunanin me kikeyi haka" "Babu komai ya Hibban" "Ok ki fito ina jiranki mu tafi" ya faɗa yana ficewa. Hijab ɗinta kawai ta dauka tabi bayan shi,. A palour ta sameshi shida mommy a zaune da alamar magana sukeyi. Tashi hibban yayi yace su tafi, sannan tayiwa mommy sai sun dawo suka fice. A hankali hibban yake tafiya dama can baya gudu sosai idan yana driving, tafiya suke suna hirar su cikin nishadi da annashuwa, dama ita sajida akwai saurin sabo. Babban Mall yakaita da kanshi ya jidar mata kaya kamar hauka sannan suka wuce shagon saida drinks nan ma siyo mata kayan kwaɗayi iri iri. Kafin su dawo tuni jiddah ta saki jiki da Hibban musamman data lura bashida wata matsala ga fara'a da iya hira ga ban dariya sosai. A gajiye suka shigo gida su duka biyun tareda kaya niki niki. "Sannu daughter jekiyi wanka kizo muyi lunch" "To mommy nah" jiddah ta faɗa tana tafiya dakinta. saida tayi wanka sannan ta shirya kayanta da suka siyo, kayan kwalliyar kansu ba ƙananan kudi hibban ya kashe mata ba..... acikin sati biyu sabo mai tsanani ya shiga tsakaninsu da hibban dan wani lokacin ko wajan aiki ya tafi ita take kai masa abinci suyi ta hira acan abinsu, mommy kuwa kamar yar cikin ta haka ta dauki jiddah duk Friday saita ɗauke ta sun fita gyaran jiki da kitso wani lokacin har wajan shakatawa mommy ke kaita hakan yasa cikin kankanin lokaci jiddah ta zama kamar yar gida har shagwaba mommy shikuwa Hibban saidai yayi ta dariya yana ce mata yarinya. Yau tunda takaiwa Hibban abinci yagama ci ta ɗauki excuse a wajan aiki ya ɗauke ta suka dinga yawo har gidajan kawayen mommy saida sukaje, sai bayan la'asar suka nufo gida bayan uban siyayyar kayan chocolate da yayo mata. Suna shiga palour suna zauna suna mayar da numfashi kamar waɗan da suka sha aiki, jiddah kuwa kusa da mommy ta zauna tana faman nishi. "Ina kukaje ne haka"? Mommy ta tambaye shi fuska a haɗe. "Mommy Ina office Mana" "Karya kake Hibban na kira layin wajan aikin su ancemin ka ɗauki excuse kun fita ina ku kaje"? Ta maimaita tambayar Tata. Kallon kallo suka farayi da jiddah sun rasa ƙaryar da zasuyi dan tahana su zuwa ko ina bayareda Sanin ta musamman yadda tasan halin dan nata a baya. "Mommy nice nace ya kaini gidan kawar nan taki naje gaida ta kinga rannan tace na sake zuwan mata fa" Jiddah ta faɗa tana taɓe fuska kamar zatayi kuka. Mommy ce ta dawo da kallon ta kan jiddah sannan tace "na kirata na tambaye ta.."? Da sauri suka hada baki sukace "Eh!" DAN sun san sunje ɗin. "Shikenan basaina tambaye taba nasan jiddah bazata yi min karya ba, amma daga Yau karku sake zuwa wani waje baku fadamin ba kuma bazan sake aika ki kai masa abincin ke kaɗai ba saidai na haɗa ki da driver kuje ku dawo tare, ina fatan kina jina" Marairaice murya tayi sannan tace "to mommy" "Jekiyi wanka ki fito zaki gyara min dakina" Da sauri ta tashi tana faɗin to sannan ta wuce dakinta. Sai yanzu ta dawo da kallonta wajan Hibban dake zaune kamar baya magana fuskar nan a haɗe, tunda taga haka tasan ranshi ya ɓaci tunda shi mutum ne da koda yaushe yake cikin fara'a da dariya ba kamar dan uwansa ba. Nuni tayi masa da yazo kusa da ita, babu musu ya ƙarasa ya zauna. Fuskar shi ta kamo ta juyo da ita tana fuskantar Tata, murmushi tayi masa sannan tace "kayi fushi dani ne"? Baisan sanda shima ya mayarwa da mommy murmushin ba yace "mommy tayaya kike tunanin zan iya fushi dake kawai naji zuciya ta tayimin zafi dana fuskanci har yanzu keda yaya Habibullah kuna zargin ina aikata sabo bayan tuni Allah ya shiryi danki, koda zanbi mata ai bazan iya bin jiddah ba dan yanzu na ɗauketa a matsayin yar uwata ta jini" .. Jikin mommy ne yayi sanyi tareda wani farin ciki a zuciyarta kiss tayi masa a goshi sannan ta sake kallan shi tace. "Hibban na daina zargin ka tuni a zuciyarta saidai ina kare mutuncin Jiddah ne saboda sharrin shaidan, amma yanzu na yarda dakai dari bisa.." Kwanciya yayi saman cinyar ta yana murmushin wanda yakara masa kyau. "Yanzu kaima jeka shirya ka fito ku duka mu fita shopping ɗin drinks ya kare na gida" "Mommy kibari naje ni kaɗai Mana" "A'a tare nakeso mu fita" "Shikenan mommy bari naje na shirya" ya faɗa yana ficewa daga palourn. Mommy ma sama ta haye Dakin ta dan shiryawa. ........ wani haɗaɗɗen palour ne wanda faɗar tsaruwar shima kaɗai bata lokaci ne, tafka tafkan kujeru ne zagaye da palour, palourn dana sake hangowa ne yasa na fahimci ashe gidan palour biyu gareshi wanda kowanne kalar kujerun su ya bambanta dana dayan, komai na palourn iri dayane har capet ɗin dake malale kasan floor ɗin tsakar palourn. Idanuwana ne suka kai kan wani gayen saurayi dake kwance saman kujera mai mazaunin mutane uku wato (three sitter). Tsayawa nayi kallon shi, gayan ya haɗu iya haɗuwa sajen fuskar shi ya kwanta luff sai sheki da yakeyi eye lashes ɗinsa kuwa baƙi sidik wanda yayi daidai da yawan gashin girarsa. Doguwar fuskar shi na ƙalla mai dauke kyakkyawan lips ɗinsa Wanda yayi kamar ansa masa Pink lips color,.. Kwance yake yana tunanin yau kwana biyu Kenan bai Kira gida ba gashi yayi matukar kewarsu harda kaninsa wanda yakejin shi har cikin zuciyar shi. A hankali ya buɗe idanuwan shi tarr, Masha Allah sai yanzu naga kyawawan idanuwan nashi farare tarr dasu. Tashi yayi zaune sannan yakai hannun shi kan tafkekiyar wayarshi kirar _iphone11 pro Max_ a hankali yaje latsa wayar kamar bayasan latsawa, lambar mommy yafara Kira saidai shiru yaji ana faɗa masa a kashe take. Sam shi bayasan ya kira waya yaji a kashe amma saboda mommy ce bai damu, kamar karya kira kanin nashi danshi bayasan raini ko kaɗan,saikuma ya tuna bai taɓa kiran sa ba saidai shi hibban ɗin ya kira shi wani lokacin yayi picking wani lokacin kuma yana ganin kiran yake kin dagawa, danshi bayasan surutun nan na Hibban. A haka dai ya dannawa hibban kira..... Dakin mommy jiddah ta shiga tana tambayar ina hibban, mommy tace ya tafi yayi wanka zasu fita, hakan yasa jiddah fitowa dan komawa dakinta. Har zata shiga dakinta taji karar wayar Hibban daya bari kan Centre table,da sauri takarasa bata tsaya duba waye ba ta daga kiran tareda sallama dauke a bakinta. Har zai yanke kiran saboda tsabar bakin ciki wato shine bazai daga kiran ba kenan, baikai da yanke war ba yaji Muryar mace nayi masa sallama. Cikeda mamaki mai tsanani HABIBULLAH ya dauke wayar daga kunnen sa yana sake duba number daya kira, number Hibban dince dai hakan yasa ya sake karata a kunnen sa yayi shiru. "Waye ne"? JIDDAH ta sake faɗa jin anyi shiru kuma mai kiran yana kallan layi. "Me wayar ya shiga wanka idan ya fito za'a faɗa masa ankira" bata tsaya jin wani abu ba ta yanke kiran dai dai shigowar hibban ɗin yana gyara cufflinks din rigar shi. Ganin wayar shi a hannun jiddah ne yasa ya daga mata gira "ya akayi ne ko bincike kike min ne" Taɓe baki tayi tace "Ni ina ruwana da wayarka kiran ka akayi.." "Waye." Ya sake tambayar ta. "Oho nidai na daga naji anyi shiru kuma abin haushi ma mai kiran yana jina yayi banza dani dan rainin wayo" A zabure Hibban ya karaso haryana hadawa da tuntuɓe ya amshi wayar yana duba recieved call dinshi, aikuwa gabanshi ya fadi ganin Sweet bro a kiran karshe. Jiddah na tsaye gefe cike da mamakin yadda yake ta faman barin jiki,. "Me kika ce masa.."? Ya tambaye ta yana kallon ta. "Babu komai kawai nace ka shiga wanka ne amma idan ka fito zaka kira shi.." "Ya Salam shikenan nashiga uku wajan Yaya Habibullah" ya faɗa yana zama kan kujerar kusa dashi. Ita kuwa jiddah ko ajikinta saima taɓe baki ta kuma ta nufi ɗakin ta dan dauko mayafi. .....barin rai tareda wani zafin zuciya ne suka taru suka yiwa Habibullah yawa, waishi yau mace ke masa magana haka kuma ma karuwa. "Wato Hibban bai dana Bin mata ba kenan, harta kai yana mace waya ta amsa masa kira... Wani irin huci ya furzar cikeda haushin Hibban, "lallai dole na ɗauki matakin ladabtar dashi, tunda bazai iya rike marairaicin shiba..." Tashi yayi ya nufi ɗakin dan watsa ruwa,. Ya dade shower na zuba kanshi, dan duk lokacin da ranshi ya ɓaci saiya sakarwa kanshi shower yake jin dadi, saida ya daɗe ruwan na zuba kanshi yaji ya samu sauki kaɗan a zuciyarsa sannan ya shiga bath tub yafara wanka... Tsaye yake a gaban mirror yana gyara sumar kanshi, sannan ya shafa lotion mai daɗin ƙamshi.. Nan ma ya dade yana kalkale jiki sannan ya saka light Ash na wani tsadaddan ya feshe jikinshi da turare mai daɗin da saukin ƙamshi dan bayasan yaji kamshi ya hau masa ka. Ƙatuwar motarshi ya shiga kirar Ferrari New model.sannan ya yakama key zai tayar saikuma ya tsaya yana tunanin. "Har karuwar bazan kyale ba saina nemo ta tagane wa tayiwa iskanci.." ya faɗa yana yiwa motar key ya fice a guje...... Harta dauko mayafinta yana zaune inda tabar shi, har zatayi magana taji Muryar mommy tana fadin su tashi su tafi ta fito. Gaba dayansu suka fice, mommy ke driving jiddah na gefen mommy shikuma Hibban yana baya........ [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: *_KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION_*🤝🏻 https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 _story and writing by_✍🏻 *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_Wattpad_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com *_Yawan comments dinku shine yasa naci gaba da wannan Novel din, Ina godiya sosai dan comments dinku shine yake karamin Kwarin guiwa_*😍😍😍 ```Ban yarda wani ko wata ya juyamin labari na ta wani fanni daban ba kokuma a cire wani abu daga cikin sa batareda neman izinin naba, kuma duk wanda ya siyarmin da Novel din ban yafe ba danni ban siyar dashi ba saboda haka kar wanda ya siyarmin```❗ *_Not edited_*📵 5 _________________________ Babban shagon saida drinks mommy takaisu, sosai suka kwashi lemuka iri iri sannan suka nufi gida dan yamma lokacin tayi. Jiddah tana lure da hibban kamar ranshi a bace yake, mommy ba ta lura da hakan saidai tasan fushin hibban bashida wani tasiri musamman akansu. Horn mommy tayi a tangamemen gate ɗin nasu, cikin kankanin lokaci mai Gadi ya buɗe musu yana musu sannu da dawowa. Kai tsaye Hibban bai kulasu ba ya nufi ɓangaran shi, zuciyar shi kamar yayi kuka haka yake ji. Jikin jiddah duk yayi sanyi sam takasa sakin jikinta, mommy ma ɗakin ta ta wuce dan yin sallar magrib itama zuciyarta nasan sanin abinda ya hada hibban da jiddah duk irin shirin da sukeyi. .....har dare hibban bai sake zuwa part din mommy ba, mommy harta gaji da jira tacewa jiddah dake gefe tana wasa da wayar mommy din. "Jiddah tashi muje muyi dinner naga hibban bashida niyyar dawowa gashi wayar shi a kashe" "Na koshi mommy" jiddah ta faɗa ko dagowa batayi ba. Cikeda mamaki mommy tace "bangane kin koshi ba, meyake faruwa ne keda yayan naki, ko faɗa kukayi".. Jiddah Sarkin hawaye tuni hawaye ya zubo mata sannan ta fadawa mommy abinda ya faru. Murmushi mommy tayi dan sai yanzu tagane matsalar, dama tasan bazai wuce hakan ba dan dazu ta jiyo su. Janyo jiddah tayi jikinta tana lallashin ta, "kiyi hakuri kiyi shiru, yanzu ki tashi kici abinci saiki kai masa nashi ɓangaran shi sannan kibashi hakuri kuma daga yau kidena daga masa waya". Jiddah batayi musu ta tashi mommy na rike da hannun ta suka nufi dining room. Saida suka gama tsaff mommy na kallan yadda take tsakurar abinci duk ta wani damu, itadai mommy murmushi kawai takeyi, suna gamawa ta haɗa mata nashi ta bata. Yauce rana ta farko da jiddah ta taɓa shiga ɓangaran Hibban, tana yin nocking ya buɗe mata yana ganin itace ya saki handle ɗin kofar ya koma ya zauna. Kallon palourn nashi take wanda yafi nasu haduwa kuma ba laifi Hibban yanada tsafta ga ƙamshi tako ina yana tashi, daya daga cikin manyan kujerun dake palourn ta zauna tana wasa da yatsun hannunta. Hibban idanshi na kanta danjin abinda ya kawo ta dan yaga alamar magana a bakinta. "Lafiya naga Kamar kinasan yin magana" ya faɗa yana kare mata kallo. "Dan Allah yaya Hibban kayi hakuri, bazan sake daga maka waya ba nayi alkawari" Har zuciyar shi yaji tausayinta Musamman daya lura duk ta wani daburce kamar zatayi kuka. Murmushi ne ya suɓuce masa harta jiyo sautin fitar shi. Ɗago kai tayi, sai taga yana murmushi. "Ni bakiyi min laifin komai ba jiddah saboda haka ki daina damuwa" Mamaki ne ya cikata "to kodai yayanta yanada aljanu ne, mutum kamar mai iskokai yanzu fa yaketa faman cin magani amma kiji wai banyi masa laifi ba" "To amma naga kanata fushi dani tunda na daga wayarka dazu"... Gyara zaman shi sannan yace "jiddah abinda yasa kika ga na nuna banji daɗi ba saboda nasan yaya Habibullah ranshi zai bashi fiyeda tunanin ki, bashida uzuri ko kaɗan sannan bashida hakuri mutum ne wanda kanshi kawai ya sani, nikuma banasan bata masa rai saboda ina sanshi fiyeda yadda nake san kaina...." Sai yanzu jiddah tagano dalilin dayasa yake fushi da ita tun ɗazu wato saboda yayan shine. "Amma ai naji bai damu ba" ta faɗa with full confidence. Murmushi kawai hibban yayi sannan ya jawo abincin data kawo masa. "Mugama cin abincin saina faɗa miki waye yayana dan naga alamar kema baki ciba" Batayi musu ba suka fara cin abincin dama dazu damuwarsa ce tasa takasa ci din. Saida suka gama sannan yace su tafi part din mommy suyi hirar acan dan yasan hankalin mommy yana kansu.... Aikuwa suna shiga palourn suka samu Mommy na jiran dawowar jiddah, tana Ganin su tare tace "dama nasan fushin naku hutu ne shiyasa ban shiga ba balle naji kunya" ta faɗa tana hayewa upstairs dakinta.... Cikeda da nutsuwa hibban yafara bata Labarin Habibullah. Mahaifin mu Alhj Nasir mutum ne mai arziki da mutane, ya taka mataki iri iri a gwamnati, yayi minister bangare daban daban sannan yana da kamfanoni biyu a Russia, hakan yasa muka tashi cikin gata da wadata da arziki wanda bazan iya kayyade Miki irin tarin dukiyar da mahaifin mu ya mallaba. Abuja Maitama anan gidan mu yake, shekarar iyayen mu shida sannan Allah yabasu haihuwa. Ranar suna aka sawa Yaro suna HABIBULLAH wanda ya gata iya gata wajan abokan Papa, anyi shagali iya yi a wajan lunch din da akayi na murnar haihuwar yaya Habibullah. Cikin kauna da tarairaya yaya Ya tashi, lokacin daya fara wayo halayen shi suka fara bayyana wanda hakan yasa Papa tura shi Russia karatu tun yana yaro.... Da farko yaya Habib mutum miskili ko su mommy maganar shi tsada take musu bayashi da fara'a ko kaɗan ga saurin fushi sannan bayasan wasa a al'amuran shi.. Bashida wani abokin hira dan koda yaushe yana zaune shi kadai da zarar mutane sun wuce biyu to bazai iya zaman waje ba... Yaya Habibullah kyakkyawan ne ajin farko dan mutane da yawa suna mamakin irin kyan da yaya Habib yake dashi, Papa kam abin har mamaki yake bashi da irin halayen shi kamar kurma wanda bayaji baya gani, dole yasa Papa yakai shi Russia duk irin san da suke masa, amma haka suka tura shi a cewar su kila bai samu abokan hira bane amma acan tunda abokin papan yanada yara dai dai shi ya saba dasu ya saki jikinshi... Tun yana yaro ya tafi Russia acan ya fara karatun shi tunda matakin yarinta, a wannan lokacin aka haifeni kowa yayi murna amma banda yaya Habibullah danshi baka gane farin cikin shi balle bakin ciki saboda koda yaushe fuskar nan tashi yadda take haka take.... Ni inada barkwanci da surutu da saurin sabo hakan yasa lokaci guda nayi mutane kuma tun ina yaro nayi abokai sosai.. Papa da mommy suna nuna min so fiyeda yadda kike tunani saboda Ni a gabansu na tashi koda yaushe ina tareda su hakan yasa nafi shakuwa dasu sosai kamar yadda suma suka fi shakuwa dani.. Saidai duk da haka soyayyar yayana tana cikin raina koda yaushe magana akansa ne, saidai shi bazaka taɓa tunanin yana damuwa akaina ba.. Lokaci guda mahaifin mu ya tashi da cutar ajali, wanda yayi sanadiyar tashin hankali na nakasa jurewa, yaya Habibullah ma saida yazo cikin ikon Allah kwana biyu da zuwan shi Allah yayiwa Papa rasuwa, wadda ta girgiza jama'a da yawa ciki harda ni da mommy. Shi kanshi yaya Habibullah wannan lokacin saika tausaya masa yadda yakara shiga cikin wani yanayi na rashin Papa, abinda yabani mamaki sai a lokacin naga irin soyayyar da yaya Habib yakemin, baya bacci saiya nayi baya iya cin komai saiyaga naci, baya nuna damuwarsa a gabana saboda kwantar min da hankali lokaci da dama yakan shigo dakina ya tsaya yana kallo na ma tsawon wani lokaci yana tausaya min saboda yasan sainafi kowa jin rashin Papa a lokacin.... Saida komai ya wuce yaya ya koma Russia dan karashe karatun sa na likita kamar yadda yakeda buri tun yana yaro, sannan nafara shiga wani yanayi wanda har mommy bataso hakan. Nakasa rike maraicina nakasa hakuri da mantawa da rashin papa, nafara bin abokaina zuwa club.. Duk wani babban club da garin Abuja keji dashi nasan da zaman shi, a hankali nafara bin mata,kuɗi da kyau da aji tareda ilimina yasa mata kebi na, mommy tayi fadan harta gaji, saidaga baya sannan ta sanar da yaya Habib.... Duk da lokacin yaya Habibullah yana tsaka da karatu haka ya biyo jirgi yazo Nigeria, Tunda naganshi jiki na yabani mommy ta faɗa masa komai dan yadda naga fuskar shi kamar baisan menene Dariya.... Nasha bakar wahala sosai sannan mommy tabani tausayi hakan yasa nayi musu alkawarin bazan sake shan komai ba kuma bazan kara bin mace ba,. Cikin ikon Allah a sati biyu da yaya Habib yayi na daina komai, kuma lokacin lauyan Papa yazo da shaidar dukiyar da Papa ya yabari tareda takardun kamfanonin shi biyu... A lokacin na daɗe yadda da irin san da yaya Habib yakemin dan kuwa cewa. Yayi ya barmin duk wani abu nashi na daga dukiyar Papa Dan shi Russia zai koma... Mommy taji daɗi sosai tasa masa albarka, sannan ya tsayar da ranar komarsa... Duk irin wannan halin nawa danayi inajin tausayin mace kuma ina darajanta ta, suma wadancan su suka zubar da tasu darajar, kamar yadda na sameki sau biyu na taɓa kawo wasu su biyu wadanda mommy ta amshe hannu biyu² amma daga baya suke guduwa,.. Tun daga lokacin yaya Habibullah ya hanani kwashe kwashe Nan danshi a rayuwarsa bayasan damuwa ko ya take.... Na takaice Miki yaya Habibullah ya wuce duk yadda kike tunanin shi, mommy kaɗai yanzu yake iya sarrafa kanshi a gabanta, bayasan raini ko kaɗan.. Yanzu ma da kikaga na damu nasan gamuwa ta dashi, dan yanzu zaiyi tunanin ban daina halina bane............ Wani irin ajiyar zuciya jiddah ta saki, "wannan wanne irin halitta ne kenan, da alamar shine silar barina gidan nan dan bazan jiri wulakancin shiba..." Ta fada a ranta... Murmushi hibban ya sakeyi danya fahimci kamar tafara tsorata dashi.. "Kinga shifa duk irin wannan halin nashi saidai idan ke kika shiga sabgar shi, amma shi ko kallo baki ishe shi ba.." Taɓe baki jiddah tayi abin ma haushi yabata "Ni dama nace zan shiga sabgar tashi ne.." "Atoh dai gyara ma hakan, dan yaran ministoci da commissioners sunyi sun gama amma baibi takansu ba.." Cikeda takaici jiddah ta tashi tana wani yamitsa fuska, "naga alamar wannan yayan naka da alamar shine zai cinye gasar kyakkyawan duniya na wannan shekarar" ta faɗa ta nifar Dakin.. Dariya sosai hibban yakeyi danya fahimci haushi taji shine ta mayar masa da baka... Tana shiga ɗakin ta tayi tsaki "aikin banza saidai yayiwa wani iskancin shi amma badai Ni jiddah ba" Ta haye saman Royal bed dinta bacci mai ya sace ta... Hibban ma part ɗinsa ya nufa ya kwanta cikeda tunanin yayan nashi. *_ALKALAMIN FIRSTLADY 🌹_*✍🏻✍🏻✍🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: *_kainuwa writers association_*🤝🏻 https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 _writing by_* *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_WATTPAD_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com 6 Da sassafe hibban ya shigo palourn mommy, mommy ce kadai Zaune tana shan coffee,. Waige waige yafara Yi yana neman jiddah. "Good morning mommy" "Morning too dear" "Mommy zan wuce office zanyi breakfast acan.." "Shikenan saika dawo" "Ameen mom" ya faɗa. Har zai fita mommy takira sunan shi.. "Hibban"! "Na'am mom" ya dawo ya zauna. "Dama cewa zanyi Yakamata ka nemawa jiddah school zaman gidan bashida wani amfani tunda babu abinda takeyi" Shiru yayi yana tunanin sannan yace "haka ne mommy zanyi wa abokina magana zuwa gobe" "Shikenan Allah yayi albarka" "Ameen Mommy" ya tashi ya fita. Dai dai fitar shi jiddah ta fito daga ɗakin ta. Gaida mommy tayi sannan tace ina yaya hibban. "Yanzu ya fita, yace zaiyi breakfast acan office, sannan yace zai nemo miki school na tambaye ki idan kinaso" Cikeda farin ciki jiddah ta rungume mommy tana ihun murna dama burinta kenan a rayuwa karatu, amma tunda tagama primary school iyayenta suka rasu bata sake tunanin karatu ba. Sai ya yayanta zai nema mata. .... Gudu yake shararawa kamar wanda zai tashi sama tsabar bakin ciki, lokaci zuwa lokaci yakan ciji lebensa na kasa sannan ya fitar da wani huci mai dauke da baƙin ciki. A haka ya isa wata babbar anguwa dake Russia, wani katon gate yayi horn aka ɓude masa gate din, saida ya samu waje yayi Parking sannan ya buɗe mirfin motar tashi. Saida ya kusa mintina goma sannan ya fito fuskar nan tashi fayau mai dauke da kyakkyawan sajen shi. A hankali Kamar wanda bayasan taka ƙasa ya nufi main palour dake kafcecen gidan. Tun Kafin ya ƙarasa ya ciro wayar shi yana kiran abokin nashi. Bugu biyu ya daga yana faɗin "guy ya akayi ne" abokin nashi ya faɗa wanda ke zaune a wani madai daicin daki. "Pls open the door" ya faɗa kawai yana katse wayar shi. Murmushi Sultan yayi yasan halin abokin nashi bayasan yin nocking shiyasa ya kira shi. Yana bude kofar ya ganshi tsaye fuskar nan a haɗe. Kai tsaye dakin Sultan suka nufa sannan ya cire siririn farin Glass ɗin dake idanshi ya zauna kan kujerar dake cikin dakin yana huci. Sun kusa minti biyar babu wanda yayi magana sannan Sultan ya kawo masa ruwa mai sanyi a ajiye masa tareda dogon Glass cup. Bai kula Glass cup ɗin dake gefe ba ya daga ruwan jirkan yana sha. Saida ya kusa shanyewa tass sannan ya ajiye yana maida numfashi a hankali,. Lumshe kyawawan idanuwan shi yayi kamar mai bacci. "Meya faru ne Habib,"? Sultan ya tambaye shi yana mayar da hankali kanshi. Tsaki yayi dan bayasan yawan tambaya gashi Sultan da shegen tambaya kamar dan jarida. "Nothing" kawai yace. "Kaidai wlhy Habib halinka bazai taba sauyawa ba, shikenan mutum kullum cikin dacin rai kamar wani mala'ikan mutuwa". Sultan yaketa faman mita. Cikin takaici Habib ya tashi ya dauki car key dinshi yayi hanyar fita daga ɗakin. Da sauri Sultan ya tare shi yana bashi hakuri, sannan ya sakeyin tsaki ya koma ya zauna. "Habib ka rage fushi dan Allah Ni banga abin fushi a magana taba" Habib bai kula shiba balle yabashi amsa. Saida yayi sallar magrib sannan ya nufi dankareren gidanshi..... ****** Hibban bai dawo gida ba saida ya tabbatar ya samawar gurbin karatu wata private school. Makaranta ce ta yaran masu kuɗi, secondary school ce kawai, jiddah taji daɗi sosai musamman da hibban yakaita taga yanayin makarantar. Saida ya biya komai sannan suka tafi gida, akan zata fara zuwa ranar Monday. Ranar mommy saida tayiwa jiddah faɗa kan ihun mirnar da takeyi.. Hibban kuwa dariya yake ta yimata dan ya gano yarinta ce tasa jiddah ke wannan tsalle tsallen. Ranar Monday kuwa ta fara zuwa makarantar, hibban shike kaita kuma lokacin tasowa nayi zai ajiye ayyukan shi ya dawo da ita gida. Har tausayin shi takeji yadda ya damu da al'amarin ta. Mommy yau ji tayi tanasan jin lafiyar danta, wayarta ta ɗauko tafara neman layin shi. Habib na zaune gefen bed ɗinsa yaji karar wayar shi, jin ring din da sawa mommy kaɗai yasa ya dauki wayar yana dagawa. Dai dai shigowar jiddah dakin mommy taga tana waya tsayawa tayi tagama wayar. "Hello Mom" "My son" Gaida ta yayi cikin ladabi sannan tace "shikenan wannan karatun yaki karewa ka dawo gida Habib" Shiru yayi na wani sakanni sannan yace "very soon zan dawo" "Yaushe kenan zaka dawo kullum maganar kenan zaka dawo" "Inshallah Nanda 3weeks" "Shikenan Allah yakaimu" mom tace. "Ameen mom" "Ina fatan kana waya da hibban" mommy ta sake tambaya. Nan ma "eh" kawai yace,. Mommy tasan karya yake sarai amma saita ce "to Allah yayi maka albarka, good night" "Night too momma" ya katse wayar shi. Jiddah sarai tagane dawa mommy take waya yadda taji suna maganar ba wani armashi "wannan ko mommy ma bai kyaleba nidai zanso naga wannan sarautar" "Jiddah ya akayi ne kin shigo ina waya da first born dina" mommy ta katse mata tunani. "Mommy muna jiranki a downstairs" "Kije Ina nan saukowa" Bata sake magana ba ta fice ta samu Hibban na jiransu. "Ina mom din" "Yanzu zata sauko tagama waya da yaya Habib ne" Yayi mamaki jin ta samu Habib yanzu amma saiya share. "Amma yaya hibban meya dawo daku Kano, kuma" "Yaya Habib ne yasa muka dawo Kano dan ya rabani da abokaina na can" "Tabb" ta faɗa tana taɓe baki. Saida suka gama lunch din sannan hibban ya fice, ita kuma ta fara ba mommy labarin makarantar su. Kwanci tashi yanzu jiddah tana jin karatun ta sosai, har tayi kawaye su biyu khairat da afnan, karatun ta takeyi hankali kwance bata da wata damuwa dan hibban da mommy sun tare mata komai. Yau ta dade tana jiran hibban yazo daukarta, yana zuwa ta shiga motar ta haɗe rai. "Afwa yar kanwata mommy ce ta sani nemo masu aiki" Saida taji uzurin shi sannan ta saki fuska suka fara hira. Tayi mamakin ganin yadda ake ta gyara gidan harda masu saban fenti, gidan kamar za'ayi biki. Da mamaki ta kalli hibban, sai taga hankalin shi baya tareda ita hasali ma yiwa ma'aikatan magana yake yadda zasu tsara wajan. A palour ta samu mommy anata gyaran palourn har kujeru an sauya musu zama. "Mommy lafiya kuwa" "Kalau daughter jeki shirya ki fito" Ba musu ta wuce dakinta wanda taga shima yasha gyara. "Lallai da alamun tambaya, amma ai sanda na tafi school tsaf naga gidan amma yanzu na dawo naga anata gyara harda part ɗin yaya hibban dana yaya Habib Allah yasa dai baki zamuyi" ta fada tana cire socks ɗinta. Angyara ko ina a gidan ya zama kamar saban gida, ya ƙara kyau kamar bashi ba, sai dare sannan kowa ya samu nutsuwa. Zaune suke zasuyi dinner su duka. "Mommy wai yanaga yau anata gyaran gida ne ko baki zamuyi ne" Murmushi mommy tayi tace "a'a Habib ne zai dawo jibi Nima sai dazu ya kirani ya faɗa min" Damm taji gabanta ya fadi batasan dalilin hakan ba,. "Amma shine sai an gyara gidan haka" "To sarkin tambaya, duk lokacin dazai dawo dole sai an gyara gida dan bayasan yaga komai kamar yadda yabari" "Ikon Allah" ta faɗa kawai sannan tafara cin abinci cikeda mamakin irin wannan rayuwa ta Habibullah. "Daughter gobe zaki je ki duba abinda ma'aikatan basu shirya masa ba saiki gyara, dan nasan ba komai zasuyi shi perfectly ba" "To momma Allah ya kaimu" Suka masa da Ameen ... ```Team din HABIBULLAH saiku fara shiryawa dan tarbar shi, saidai kila ya sage muku guiwa😂😂😂 ``` ```pls SHARE, COMMENTS and VOTE``` [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: *_🌈 KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION🤝🏻_* https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 _by_✍🏻 *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_WAATPAD_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com 7 Kamar kullum jiddah da sassafe ta shirya cikin uniform ɗinta da sukaji masifar yi mata kyau, suna breakfast Hibban yace su tafi. Sannan tayiwa mommy sallama suka fice. "Yaya hibban nifa gaskiya yau saika gaisa da su afnan" "Meyasa kanwata" "Kullum sai afnan tacemin ina yayana sainace ka yafi Amma yau ka tsaya ku gaisa plsss" ta marairaice murya. "Ohhh little sis badai rigima ba, shikenan naji zan tsaya, ina fatan shikenan" "Yes that's all," ta faɗa da murnar ta. Har cikin makarantar yakaita sannan yace taje ta kirasu su gaisa ɗin,. Mintina Kadan ya hango su, har suka karaso sannan su khairat da afnan suka gaida shi ya amsa fuskar shi a sake. "Pls ku kularmin da kanwata banaso naki wani abu ya sameta fa" Dariya sukayi su duka har jiddan sanan ya ciro kudi baima san nawa bane ya basu. Kin karba sukayi suka bar wajan sannan jiddah ta amsa tace zata basu. "Shikenan sis idan akwai matsala ki fadamin kafin na tafi" "Babu wata matsala bro nidai kawai ka tafi karkayi letti" Dariya yayi dan yasan korar shi takeyi danta koma wajan kawayen ta. Sallama yayi mata sannan ya shiga motar shi kirar zenvo Ts1,. Saida taga ficewar shi sannan ta juya ta koma wajansu afnan..... Russia, Moscow. Azimut hoyel:- Fitowar shi kenan daga swimming pool, farar vest da swimsuit, Zaune yake yana karanta jarida, sam baiji zuwan Sultan ba saida ya matso ya mashe jaridar sannan ya tashi yana kallon shi da sleepiness eyes ɗinsa Kamar wanda baya samun bacci. "Ya akayi guy wannan irin tunanin haka" "Babu" "Naji dama nasan ba fadamin zakayi ba, yaushe tafiyar taka 9ja ne" Wani siririn numfashi Habib yaja sannan yace. "Tomorrow"! "Nima da nayi tunanin na bika amma bazai yiyu ba inasan saina gama da wannan zancen sannan..." Kallan neman karin bayani yayiwa Sultan batareda yace kala ba.. Ganin irin kallan da yake masa ne yasa Sultan cewa "kaifa Kanada matsala wlhy yanzu harka manta da magana Angelina din.." Cikeda takaici Habibullah yayi tsaki wanda yasa Sultan sakin baki yana kallanshi. "Kana nufin wai haryanzu kai bakasan soyayya ta da ita ne."? "Eh haka nake nufi" Habibullah yace yana barin Wajan. Da sauri Sultan yabi bayanshi har zuwa cikin kayataccen palournshi, zama sukayi kujera daya. Sultan kam kasa shiru yayi dan yafara tunanin Habib yanada matsala yadda yaran turawa kyawawa masu kuɗi da aji keta faman binshi amma yaki sauraran su sai gashi yanaso shima ya raba shi da Angelina ɗinsa . "Kadai kaje kaita zama haka, Nan gaba da kanka zaka fadamin ga wacce kakeso...." Cikin jin haushin Sultan, Habib ya tashi yana nuna masa hanyar fita "pls fitar min a gida plss" Sultan daya saba da halin Habib ko damuwa baiyi ba saima murmushi yayi yace "zan fita dama ko baka ceba, ka gaida min da mommy idan kaje" yana kaiwa karshen maganar shi ya fice abinsa. Jagwab ya zauna kan kujerar yana maida huci "meyasa wai samarin yanzu basuda aiki sainayin aure da wuri su tarawa kansu damuwa ne, nasan zanyi aure amma har yanzu banga wacce tayimin da sunan wani abu waishi soyayya ba infact ma bansan menene soyayyar da suke hauka akanta ba.." ya faɗa a ransa tareda jan wani karamin tsaki ya nufi ɗakinsa dan shirya kayansa. ....... Yau da wuri hibban yaje ya dauko jiddah, suna zuwa gida kan abinci tayi birki dan wata irin yunwa dama take ji. Saida ta gama da Cikinta sannan ta shiga dakinta, wanka tayi ta shirya sannan ta fito. Mommy na zaune ita da hibban dake danna computer, tana zama mommy tace "jiddah ba zama zakiyi ba jeki gyara ɓangaran Habibullah" "Oh sorry momma na manta ne jiya kin fadamin" sannan ta tashi . "Yaya hibban ka rakani plss" Wata harara ya maka mata yace "saboda ni sa'anki ne ba, shine saina raka ki duk inda zaki ko.." Dai dai mommy ta Miko mata key ɗin tace "sorry yayana da wasa nake fa."? Bai sake kulata ba itama ba sake cewa komai ba ta fice. Saida Tasha wahala kafin ta bude palourn nashi... Cikeda mamaki ta tsaya tana karewa palourn kallo, komai iri dayane a palourn yasha gyara an canja komai har Chinese capet ɗin dake malale a kasa, . Kujerun kansu saida ta tsaya tana kallo ikon Allah wannan palourn aka narkawa kudi ba namu ba Kenan. Ta daɗe tana surutu ita kadai sannan tafara gyare gyaran wurin,. Duk dakunan a gyare suke sai guda daya da taga a rufe yake. Keys din hannunta tafara gwadawa harta samu nashi ta bude. Tana sako kafarta cikin dakin idanuwanta suka sauka kan wani picture Wanda yasa ta ɗauke numfashin ta na wani sakanni. "Ya Allah badai wannan ne Habibullah ba" ta faɗa yana karasa kusa da hoton. Ta kusa mintina shida tana kallan picture din, bakaramin kyau Habibullah yayi ba ji tayi duk irin kwadawar da hibban yayi mata saitaji kamar ma bashi ya siffanta mata ba dan wannan yafi wancan kyau,.. Jin kamar alamun tafiya tayi saurin ajiye wa tafara gyara katon bed ɗinsa. Ɗaki Kamar na mace ya sha alatu saikace a gidan ba . Saida tagama sannan ta shiga bathroom ɗinsa, nanma saida ta daɗe a tsaye sannan ta fito dan ita bataga abin gyarawa anan ba. A palour ta samu Hibban zaune, yana jiran fitowar ta. Tana fitowa ya tashi yace su tafi. "Yaya hibban ya kuma naga ka biyo NI" Murmushi yayi yace "shi ne nima ban sani ba ganina kawai nayi anan" Dariya sosai jiddah tayi danta gane waskewa yayi. Bin bayanshi tayi har gaden ɗin dake bayan part ɗin Habibullah, waje ne babban sai shuke shuke wadanda suka wajan yayi sanyi, har swimming pool din dake gefe kadan yayi matukar birge jiddah. Lallai ashe sune a ƙauye a cikin gidan... Sun daɗe anan sannan suka koma part ɗinsu. Itadai jiddah yau taga ikon Allah, dole Habib yaji kanshi shi wani ne.... Har dare jiddah na tunanin picture din da tagani a part ɗinsa, duk lokacin data tuna sai taji murmushi ya suɓuce mata. ....yau jiddah da wuri ta shirya ta fito dan zasuyi submitting wani assignment, hibban ma tuni ya shirya, yana ganin fitowar ta ya tashi. "Jiddah ki tabbatar kinyi breakfast banaso ki zauna da yunwa dan nasan halin ki" "Rungume mommy tayi "inshallahu zanyi mommy naaa" ta faɗa tana sakin mommyn ta fice da gudu. Dariya mommy tayi "Allah ya shirya minke jiddah," sannan ta kalli hibban. "Kasan yau Habibullah zai dawo saika dawo da wuri". "To momma, Amma ke zaki dauko shi ko."? "Eh Ni zanje da kaina" "Shikenan saina dawo mommy tace to A dawo lafiya Allah ya kiyaye" "Ameen" yace yana ficewa dan yasan jiddah nacan na jiran shi... Tunda suka fita mommy tafara Shirin tarbar Habib, wanda sai 2:00pm jirgin su zai sauka..... Yau gidan kowa saida yasan Habibullah zai dawo, dan aiki sukeyi sosai, kuku kuwa saida sukayi kala kala kamar wanda mutane da yawa ne za suci. Ko ina na gidan ƙamshi yake 1:30pm mommy ta shirya cikin shiga ta Alfarma sannan ta dauki car key ɗinta ta nufi airport... 2:00pm jirginsu Habibullah ya sauka, A hankali mutanan jirgin suka fara fitowa,. Idanuwan mommy ne ya sauka kan dan nata dayake saukowa a hankali kamar bayasan saukowar. "Masha Allah" mommy ta furta ganin yadda dan nata ya sake zama cikakken namiji kyaun shi da haibar shi suka sake bayyana. Sanye yake cikin light blue din suit wacce ta amshi fatar jikin shi. Fara rarraba fararn idanuwan shi yayi dan ganin wanda yazo daukarshi, akan mommyn shi idanuwan shi suka sauka, murmushi daya kara masa kyau yayi sannan ya nufo ta. Itama da murnar ta fal ciki ta tarbe shi tana rungume shi. "Welcome back my son" "Thanks momma" Hannuwanshi ta kama suka nufi motar Tata, ba bata lokaci mommy tafara driving suka tafi gida. "Hibban fa mommy," "Yana wajan aiki shiyasa nazo Ni kaɗai" "Amma mom ina drivern ki" Murmushi tayi danta gane me yake nufi. "Nina sallame shi saboda nafi san driving da kaina" Bai sake magana ba ya kwantar da kanshi kawai yana lumshe ido.... Sai 2:30 sannan hibban yaje dauko jiddah dan aiki ne ya riƙe shi yanzun ma excuse ya dauka ya fito dan yasan tana jiran shi... .... ma'aikatan sai kwasar gaisuwa sukeyi ko kallo basu ishe shiba saima komawa yayi yana dakatar dasu da hannu kawai yakeyi. Palourn mommy ya sauka, saida ya kusa mintina shida sannan yace zai je part ɗinsa yadan huta. "Shikenan dear, jiddah ta gyara maka dama" Sam ba kawo watace jiddah ba yayi tunanin cikin yan aiki duk da bayasan yan aikin ma'aikata shiyasa lokaci da dama hibban ke gyara masa. Amma baice komai ba ya fice hannun shi dauke da suit din daya cire. Kallan palourn nashi yayi ba laifi yayi masa kaɗan dan babu wani dirty sosai. Ɗakinsa ya shiga, sannan yafara bin ko ina da kallo Kamar maisan ganin wani abu,. Mamaki ne ya cika shi ganin picture ɗinsa ba inda yasaba ajiye shiba, tsaki yayi sannan ya mayar dashi mazaunin shi. Bathrobe ya dauka kawai ya shiga wanka. Saida ya nitsa sannan yasa kaya marasa nauyi ya nufi part din mommy sai zuba ƙamshi yake. Mita sosai jiddah tayiwa hibban kamar zatayi kuka, sai hakuri yake bata tana zuba masa shagwaba har suka karaso gida tana saita faɗawa mommy.. Da gudu ta shiga palourn tana kwadawa mommy Kira,.. Kam ta tsaya kamar wacce aka dasa, kallon shi takeyi kamar wacce taga dodo tsoron shi da kwarjinin shine suka sa takasa koda motsa kafarta. Shima Habibullah kallo daya yayi mata ya dauke kai cikeda tunanin wacece ita haka ta shigo kai tsaye tareda kiran mommy. Tunawa yayi da mommy ta bashi labarin wata yarinya da suka tsinto may be itace wannan ya faɗa a ranshi yana jin haushi dan dazu bakin ciki ne yasa ya amsawa mommy kawai.... Jiki a sanyaye ta shige dakinta, tana shiga ta cillar da hijjabin ta gefe ta zauna ta zuba uban tagumi. "Gaskiya Allah yayi halitta anan wannan hoton ma rage masa kyau yayi," "Na yarda da maganar yaya hibban, wannan mutumin daga gani bashida mutumci ko kaɗan" Ta dinga sake sake a ranta sannan ta shige bathroom danyin wanka da alwala.... ````ku biyoni A sannu zakuji yadda zata kaya tsakaninsu DAGA``` *_ALKALAMIN FIRSTLADY 🌹_*✍🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: *_🌈KAINUWAWRITERSASSOCIATION_* https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 _By_✍🏻 *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_WATTPAD_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com 8 Tana idar sallar taji ana nocking din dakinta. Hibban ne tsaye ɗauke da murmushi fuskar shi,. "Sweet sis, meyasa baki fito ba munata jiranki.." "Babu komai yaya hibban" "Muje to" ya faɗa yana bata hanya. Tana gaba yana Binta a baya suka shigo palourn, kamar fadi idanuwanta ya sauka kan na Habibullah wanda ke zaune bashida alamun tashi a wajan. Harara ya maka mata yana wani kankance ido, cikeda da tsana danshi Gaba daya jiyayi ya tsaneta dan suffar munafukai gareta. Ganin irin hararar da yayi mata yasa ita kuma ta taɓe baki a zuciyarta tace "nidai ba abokiyar yinka..." Kafin ta gama zancan zuci taji saukar wani gigitaccen mari Wanda yasa ta juyo a firgice. Habib ne tsaye yana huci kamar wani zaki idanuwannan nashi yayi ja kamar garwashin wuta. Daga hannu yayi zai kuma marinta mommy tayi saurin janyeta jikinta,. "Meye haka Habib, daga dawowarka zaka takurawa yarinya me tayi maka da zaka yi mata irin wannan marin..." Mommy ce ke ta faman yiwa Habib faɗa kamar zata ari baki. Cikin wani irin yanayi Habib ya fice baice komaiba, kai tsaye part ɗinsa ya wuce, bathroom ya shiga ya sakarwa kanshi shower yana huci mai cikeda bakin ciki da bacin rai.... Hibban kuwa dake zaune kamar an dasa shi, ji yayi kamar ya zubar da hawaye dan bakin ciki, shima tashi yayi ya fice kamar zai tashi sama. Jiddah kuwa na jikin mommy tana kuka dan bakaramin zafin marin taji ba, "dole ta fita harkar wannan mutumin dan kuwa nan gaba babu abinda bazai iya yi mata ba".. "Kiyi hakuri JIDDAH dama nasan haka zata faru Habib yanada zafin zuciya saidai ki fita harkar shi kidaina shiga sabgar shi kinji ko" Jiddah kai kawai ta dagawa mommy sannan mommy tace ta tashi suci abincin saita kaiwa hibban nashi dan shima ranshi ya ɓaci. Saida ya kusan 20mnt sannan ya fito ɗaure da towel jikinshi, ya daɗe yana gyara jikinshi sannan ya jura sleeveless shirt, car key ɗinsa kawai ya dauka ya fice dan bazai iya cin komai a gidan ba gyara yaje restaurant ya nemi wani abun yace. Dakyar jiddah ta iya cin wani abu, sannan ta dauki na hibban ta wuce part ɗinsa. Kwance ta same shi yana ganinta ya tashi ya amshi kayan hannunta. Fuskar ta yabi da kallo yadda yaga harta dan tasa, murmushi jiddah ta ƙaƙalo sannan ta zauna kujerar kusa dashi. Hibban abincin yake ci amma lokaci zuwa lokaci yana satar kallon jiddah, har ya gama. A hankali yafara janta da hira har saida tadan sake sannan ya tashi ya raka ta... Habib babban restaurant yaje ya cika cikinsa sannan ya shiga motarshi yayi hanyar gida cikeda sake sake a ranshi akan wannan yarinyar.... Ganin dare yayi lokacin yasa ya nufi ɓangaran mommy yayi mata saida safe kamar yadda ya saba. Babu kowa palourn hakan yasa kai tsaye ya haura upstairs. Fuskar mommy ba yabo ba fallasa ta amsa masa, har yayi hanyar fita ta kira sunan shi a nitse. Amsawa yayi sannan ya koma ya zauna yana sauraran ta fuskar tashi a haɗe. "Habib meyasa baka iya rike fushi ka akan komai, yarinya daga zuwanka zaka fara damun rayuwar ta harta gaza zama damu itama ta gudu kamar yadda kayiwa wadancan, to wlhy daga yau banaso na kara jin kayi mata wani abu da zai sa taji ba dadi harnaji kaji na faɗa maka.." Daga kai kawai yayi sannan ya tashi ya fice yana zayyana abubuwa a ranshi. Kai tsaye part ɗinsa yaje ya kwanta cikeda bacin rai lallai wannan yarinyar tasamu matsayi da yawa" ya faɗa a ransa sannan yayi wani murmushin mugunta yana gyara kwanciyar shi.... Saida hibban ya tabbatar ta saki ranta sannan yayi mata sallama ya wuce ɗakin shi danyin bacci... Jiddah kuwa ta dade bacci bai sace taba tana tunanin yadda zata saba da wulakancin Habib sannan bacci yayi awon gaba da ita....... ************* Kwana biyar kenan da dawowar Habib babu abinda ya sake shiga tsakaninsu, saidai ko gaida shi tayi baya amsawa sai idan mommy na wajan zai amsa a dakile,. Kullum kuma Hibban ke kaita school sabo kuwa sai abinda yayi gaba dan ko abinci daya baya iya ci idan babu ɗaya.... Yau suna gama breakfast yace taje ta gyara masa ɗakinsa, cikeda mamaki ta kalli fuskar shi babu alamun dariya fuskar tashi amsa masa tayi da "to". Har zuciyar Hibban baiso haka ba dan yasan kila wata muguntar ya shirya mata amma sai yayi shiru abinsa baice komai ba. Fita yayi dan bai fiye zama cikin palourn ba, yana fita itama ta nufi part ɗinshi da sauri kafin ya dawo yace ta bata masa lokaci. Buɗe palourn tayi tana bi da kallo dan ita bataga abin gyarawa a wajan ba, ɗakinsa ta nufa tana shiga ta taɓe baki,. "Niban ga abin gyarawa anan ba, kawai dai so yake ya batamin lokaci har malamina yazo yayita jira..." Faɗa tana karasa kusada gadon,. Kallon picture dinnan tayi wanda ya sauyawa wajan ajiya,. "A haka kamar babu ruwan shi amma mugun sai cin zali kamar..." Jin an fizgo hannunta da karfi an murde ne yasa tayi saurin sakin kara. Habib ne tsaye kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa, a hankali ya lumshe idanunsa sannan ya buɗe su jajir yana wani huci cikin bacin rai. Kuka sosai takeyi wanda ya kara hassala shi ya jefata jikin wardrobe din dake gefe. Kyawawan mari biyu ya bata, tuni ta fara bashi hakuri tana kuka kamar ranta zai fita. Wata iska ya fesar dan kukan nata dada bashi haushi yakeyi, "Waye mugu..." Ya faɗa yana kafeta da sexy eyes ɗinsa. "Wlhy bada kai nake ba, plss I'm sorry Yaya Habib.." Murmushi yayi jin yadda take rantsuwa bada shi take ba, can kuma ya sake bude baki zaiyi magana sai kuma ya fasa yayi mata nuni data fice. Da sauri tayi hanyar fita,. "Keeh"! Taji ya dako mata tsawa wanda yasa tayi saurin dawowa tana dukawa kusa dashi. "Share wannan hawayen.." yace yana yi mata wani wulakantaccen kallo. Share hawayen tayi sannan yace "oya smile" Ba shiri ta sake ƙaƙalo murmushin dole tayi sannan yace ta fice da wannan mummunan fuskar Tata. Kamar zata faɗi ta fice da gudu gudu sauri sauri, tana fita ta nufi part din hibba. Dai dai hibban zai fito yaga shigowar ta kamar an jefo ta. "Lpy jiddah, meya faru waya taba ki" "Yaya Habib ne" ta bashi amsa a takaice. Shiru hibban yayi sannan ya nuna mata waje ta zauna. Hakuri sosai ya bata sannan su nufi part din mommy... Habib kuwa tana fita yayi tsaki dan harta sa kanshi yafara yi masa ciwo da wannan shegen kukan nata, kwanciya yayi saman bed ɗinsa sannan ya lumshe idanuwan shi yana tsaki lokaci zuwa lokaci. Sam Habib yaki fara aiki dan tuni angama gina private hospital din dazai fara aiki, a cewar shi hutawa yake dada yi. Sultan ma tuni ya dawo Nigeria bayan ya gama saita maganar auran shi da Angelina. Sosai Habib yake jin haushin yadda mommy ke nunawa jiddah so, wani lokacin har mamaki yakeyi saidai yanzu ko inda jiddah take baya kallo, kuma ko yaya kuskure yake bakaramin wahala yake bata, harta fara sabawa da cin mutuncin shi. Palourn mommy ya shigo sanye da ƙananan kaya Wanda suka amshi fatar jikin shi, ita kadaice a palourn tunda ya shigo ta kalle shi tayi ƙasa dakai. "Mutum har mutum amma zuciyar shaidanu ne dashi" ta faɗa a ranta tana taɓe fuska. Ko inda take bai kalla ba ya wuce sama wajan mommy danya sanar da yau zai fara fita aiki. Mommy na ganin shi tayi murmushi, "Habib ka fito" "Eh maa" "Ina zakake ne haka." "Mommy zan fara fita aiki yau".... "Aiki" mommy ta maimaita. "Allah to ya taimaka, ka tafi da jiddah ka ajiye ta a gidansu kawarta tun ɗazu takesan zuwa nace ta bari hibban ya dawo amma tunda fita zakayi saika ajiye ta acan" Habib ji yayi wani abu ya tsaya masa a wuya tsabar takaici. Mommy kuwa bata bi ta kanshi ba ta fice tana kiran jiddah. "Na'am mommy" "Tashi ki shirya Habib ya ajiye ki gidan su afnan ɗin" Da sauri tace "a'a mommy na fasa ma ai.." Kallon tuhuma mommy tayi mata sannan tace "banasan shashancin banza tashi ku tafi" Badan taso ba ta tashi ta shige ɗakinta dan dauko hijjabin ta. Shikuwa Habib yana saukowa ya fice yana jiranta cikin mota. Kamar munafuka ta shiga baya ta zauna,. Kusan mintina shida yaki tayar da motar, can kuma yayi wani tsaki sannan ya fito ya bude bayan ta dake zaune ya fizgo ta da karfi har tana bigewa, sannan ya mayar da ita gaba ya zagaya ya tayar da motar ya figeta a guje. *_pls kuyi manage da wannan_*👈 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: *_🌈 KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION🤝🏻_* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` *https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 _By_✍🏻 *_🌹 Ameena firstlady 🌹_* *_WATTPAD_* @Ameenafirstladyy ameenamusa881@gmail.com 9 .....gudu yake shararawa kamar zai tashi sama, lokaci zuwa lokaci yake jan wani siririn tsakin takaici. Jiddah kuwa kasa tayi da kanta tana addu'ar Allah ya sauke su lafiya dan a yadda yake gudun nan saidai fatan sauka lafiyan, driving ɗinsa kawai yakeyi ko kallan gefenta baiyi ba... Tun fitarsu mommy ta daɗe tana saka da warwara, sannan ta koma dakinta ta kwanta cikeda kwarin guiwarta... A kofar gidansu afnan Habib ya sauke ta, harta fita zata shiga taji ya dako mata tsawa. A firgice ta juyo tana zaro dara daran fararan idanuwanta da suka nuna tsoro karara a cikinsu, fuskar nan tashi babu fara'a yace "zan dawo mutafi saura idan kinga dama kuma ki tafin".. bai jira amsar taba ya tayar da kura yabarta nan a tsaye kamar an dasa ta... "Ikon Allah kamar wanda zaibar kasar nidai tunda ka sauke ni can ka karata..." Ta shige gidan tana buga uban tsaki... Afnan taji dadin ganinta, hirar sosai sukeyi har yayan afnan ɗin ya shigo yana faɗin "zan iya zama ayi dani.." Afnan ce tace eh mana yaya Kabir, jiddah bataso hakan ba dan yadda ya kafeta da ido kamar zai cinye ta. Kabir Mutum ne wanda babu ruwan shi yana da saurin sabo ga fara'a aikuwa tuni jiddah ta saki jiki suna hira kamar sun saba,, sam Kabir baiyi wasa da damar shi wajan baiyana wa jiddah abinda ke ranshi ba,.... Ba bata lokaci jiddah ta amshi soyayyar shi danta fahimci Kabir gwani ne wajan iya soyayya...... Babban hospital ne wanda yaji kayan aiki, an kayata shi sosai da manyan ma'aikata masu sanin makamar aiki, Habib yaji dadin ganin yadda asibitin yake dan komai yadda yaso haka ya kasance, saida yagama shirya komai sannan ya wuce gidansu Sultan wanda ya dameshi da kira akan yazo ya taya shi tsara yadda auran nashi zai kayatar.... Habib yana zuwa Mama (mahaifiyar Sultan) ita kaɗai ya samu a palour. Gaida ta yayi sannan ya tashi zai nufi ɗakin Sultan. "Wato Habibullah saida bikin abokinka yazo sannan kasan kazo gidan ko, ina fatan dai kaima naka na hanya" Mama ta faɗa tana dariya. Murmushi kawai Habib yayi sannan ya nufi ɗakin Sultan ɗin baice komai ba dan yasan yanzu Mama faɗa zata farayi masa.. Zaune yake saijin shirmen Sultan yake yi harya gama sannan yayi gyaran Murya yace "kaga Malam kabar duk wani abubuwan daka Jero kayi dinner kawai is enough for you..." Ya faɗa yana ci-gaba da kallan wayarshi. "Nifa daman nasan wlhy shawara dakai sainaji haushi ka tsaya muyi magana yadda zan fahimta saika dinga wani abu kamar wanda bayasan bani shawarar..." Murmushi Habib yayi yace "shikenan kaje kayi duk abinda zakayi ba saika nemi shawarata ba" ya tashi ya nufi hanyar fita. Sultan ma tashi yayi yabi bayanshi yana faɗin muje nima na gaida mommy kwana biyu bana zuwa, kaima Mama tayi fushi wai baka zuwa saida bakina yazo... "Ai naji zata farayi min faɗa ɗazu" Daga haka suka shiga motar Habib suka fice. Kai tsaye gidan daya sauke jiddah ya nufa, cikin Sa'a ya gane gidan batareda yasha wata wahala ba, Sultan dai na gefe yana mamakin abinda yasa Habib zuwa gidan. Mai Gadi ne ya fito jin anata horn kuma motar taki shigowa, "ya akayi ne ko wani ake nema?" "Amm... Baba dan Allah bakuwar dana kawo za'a kiramin.." "To shikenan bari naje saina sanar mata" mai gadin ya faɗa yana shigewa gidan.. Lokacin jiddah na zaune itada Kabir suna zuba soyayyar su, dan tuni afnan tabasu wuri. Ganin mai Gadi ne yasa Kabir yace "ya akayi baba". "Wai jiddah ta fito ana jiranta a waje" Ai kafin ya ƙarasa jiddah ta tashi tana ɗaukar hand bag ɗinta. Sallama tayi masa zata fice "ki bari na raka ki Compound Mana" "A'a Nagode, ka fadawa mamee da afnan na wuce" bata sake magana ba ta fice. Habib harya fara kuluwa jin shiru cikeda fushi ya buɗe motar zai fice saiyaga ta fito,. Sultan da mamaki ya kafe shi dan baiyi tunanin jiddah suka zo ɗauka ba, tunda yasan bawani shiri takeyi da Habib ɗin ba. Tana shiga motar ya tayar suka tafi kamar kurame ita kuwa a tsorace take yadda ya haɗe rai tasan ta shiga uku dan cewa zaiyi ta bata masa lokaci. Suna zuwa gida shida Sultan suka wuce part ɗinsa, ita kuma ta nufi part ɗinsu tana sauke ajiyar zuciya dan ta kubuta Allah ya taimake ta dan jarabar baiyi mata kome ba. Tana shiga mommy tayi mamaki dan batayi tunanin Habib zai dawo da ita ba, hibban kuwa da murmushi yace "kanwata yanzu mommy take cewa naje dauko ki" Dariya tayi tace "dama nasan yayana da mommy na hankalin su na kaina" ta faɗa tana kwanciya gefen mommy daketa faman murmushi. "Waya faɗa Miki na damu, kawai banaso naga abokiyar tsokanata bata kusa ne" ya faɗa yana makewa.. Gwalo tayi masa tana fadin "nadai gano" Tsuke fuska yayi sannan ya tashi yana yin hanya fita "nama fasa baki wayar dana siyo Miki" Aida gudu jiddah tabi bayanshi tana bashi hakuri, amma yayi fuska yace saita durkusa. Haka dai hibban ya dinga tsokanarta sannan ya ciro sabuwar ƙatuwar waya ya bata. Tsalle tsalle tafara yi tana ihu a bakin palourn,. Sam batasan Habib ya taho shida Sultan ba saiji tayi ta bige mutum a bayanta... A firgice ta waigo idanuwan nan nata kamar su fito tsabar kaduwa tuni hawaye ya wanke mata fuska, wanda yaba kowa mamaki. Banda mommy da tabar palourn tun dazu. Habib kuwa duk da tuni ranshi ya ɓaci mamaki ne ya kamashi ganin tun kafin ya taba tafara kuka. Sultan kuwa samun waje yayi ya zauna yana kallan yadda take kuka wiwi. Cikeda takaici da bacin rai Habib yakai mata wani wawan marin dayasa ta zauna bata sani ba tana dafe da wajan. "Sharri zakiyi min ehh! " Ya faɗa yana kara bata wani marin tareda riko kunnen ta ta miƙar da ita tsaye. Azaba ce tasa ta saki wani kara wanda yasa Habib saurin toshe kunne tareda rinste ido. Yana sakin ta tayi sama da gudu wajan mommy tana kuka.. Mommy na ganinta tasan itada Habib ne shiyasa batayi Magana ba. Gadon mommyn ta faɗa tana kuka rike da wayar da hibban ya bata... Habib jinjina kai kawai yayi sannan ya fice yana huci kanshi na sara masa Saboda ihun har cikin kanshi yaji shi. Hibban kuwa sam ji yayi baiji daɗi ba a haka mommy take faɗin suyi zaman tare wanda yasan jiddah ce zata cutu karshe ma ta sake guduwa batareda sanin su ba ina wannan baizai yiyu ba yafice shima daga palourn. Sosai Sultan ya bashi hakuri sannan ya bashi magani ya tafi.... "Kema jiddah meyasa bakyajin magana ne sau nawa nake faɗa miki ki daina tsalle tsalle amma shine yau ma kikayi ai gashi nan yau kin jama kanki.." mommy tace. Idanuwanta duk sunyi ja tsabar kuka, "mommy wlhy mommy bazan karaba Amma kiba Yaya Habib hakuri karya dokeni plsss" "Naji yanzu tashi kije kiyi wanka ki huta to" Batayi musu ba tanufi dakinta, wanka tayi sannan ta shirya cikin wata goguwar riga baka wacce ta tafi da shape din jikinta ta amsheta sosai. Wayar da hibban ya siyo mata ta kunna, number shi ce saita mommy da Habib kawai a ciki. Tsaki tayi tace "me zanyi da numban wannan mugun" har zata goge sai kuma ta barta tana kuma yin tsaki.... Har lokacin dinner yayi sannan mommy tace ta Kira Hibban yazo suci abinci, cikin Sa'a ta taji wayar da kuɗi. Yana daga wayar tace "yaya hibban muna jiranka fa".. "Ok gani nan" Ta katse kiran sannan tace "mommy Yaya Habib fa...." Kallan mamaki mommy tayi mata "wato bakiyi zuciya ba" Shiru tayi batace komai ba dan itama batasan meyasa tayi maganar shina . "Ki kyale shi ko ankira shima yanzu yana cikin fushi bazai zoba" mommy tace... godiya sosai tayiwa hibban sannan ta amshi number mamansu afnan ta wuce dakinta.. Saida suka gama waya da afnan sannan afnan ɗin tace zata ba yaya Kabir number wayanta Dan ya dameta da maganar jiddan. "Ba matsala ki bashi, kawai" sannan sukayi sallama ta kashe.. Ciwan kan dakyar yabar yayi wanka yayi Sallah sannan ya kwanta yana lumshe idanuwan shi, dan sosai yakejin ciwan kan, magani ya kuma sha sannan ya kwanta amma yakasa baccin. Mommy kuwa tana shiga ɗakinta ta dauki wayarta ta kirashi. Jin Muryar shine yasa tace "meyake damunka Habib," ta faɗa a dan firgice. "Babu komai mommy ciwan Kaine kawai kuma nadan samu sauki.." A'a Habib bari nasa hibban ya kaika hospital. Bata jira amsar shiba takashe wayarta. Tana fadawa hibban yasan dama hakan saita faru sam Habib kamar mai cuta a ƙwaƙwalwa bayasan ihu ko kaɗan hakan na iya samai ciwan kai tun yana yaro. Da sauri ya tashi ya nufi ɗakin jiddah yace ta kawo masa abinci. ✍🏻✍🏻✍🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 *Writing by* *_🌹 first lady 🌹_* *WATTPAD* @Ameenafirstladyy *Kainuwawritersassociation* 10 ..... jikin jiddah duk yayi sanyi dan taji dalilinta ne yanzu bashida lafiya, ga hibban duk ya rude. A haka ta fita palour ta haɗa masa abinci sannan tabi bayan Hibban zuwa part ɗinsa. Kwance yake idanuwan shi a rufe ya riƙe kanshi da hannu. Jin an bude kofar ɗakinsa ne yasa ya dan buɗe ido a hankali sannan ya mayar ya rufe. "Yaya muje hospital pls karka ce a'a" hibban yace cikin tausayin yayan nashi. A hankali ya sake bude idon nashi, sannan yayi murmushi dan kwantar da hankalin kanin nashi. "Karka damu Hibban I'm feeling better now" Sosai Hibban ya takura daga karshe Habib ya rubuta masa magunguna yace yaje ya siyo masa yanzu ya kawo... Sai yanzu hibban yakai dubansa kan jiddah dake labe a gefe kamar munafuka dauke tiran abinci jikinta a sanyaye. "Kiyi saving ɗinsa jiddah kafin na dawo" hibban yace yana ficewa. Yana fita jiddah ta zauna gefen stool ɗin dake kusa dashi sannan tafara zuba masa abincin. Tura masa gabansa tayi sannan tace "pls Yaya Habib kaci abincin.." Dauke kai yayi yana daɗa lumshe ido baice komai ba. Duk yadda taso yaci abincin ki yayi karshe ma yace ta fice mai a ɗaki. Ba shiri ta fice daga ɗakin sannan tayi tsaki tace "mutum bashi da lafiya ma saiya yi faɗa.." ta wuce ɗakinta ta kwanta sannan ta kira sahibinta wato Kabir suka fara wayar soyayya. Hibban daya dawo dakyar ya samu yayan nashi yaci abincin kaɗan sannan ya bashi magani yayi masa sallama ya wuce part ɗinsa...... Da sassafe jiddah ta shirya cikin uniform ɗinta, ta fito da ainihin kyaun ta. Sam batayi tunanin ganin Habib a palourn ba a wannan lokacin ganin wani lokacin sai 11am yake shigowa sometimes. Gaida shi tayi amma bai kalli inda takeba balle ma tasa ran zai amsa mata. Itama ko ajikinta tunda ta saba,. "Jiddah yau amma saikin yi breakfast ko" mommy ta tambaye ta. "Mommy zan makara fa" ta faɗa cikin shagwaba. Habib yana jinsu saidai hankalin shi yana kan waya, kallon gefen ido yayi mata sannan ya taɓe baki dan shi yarinyar har mamaki take bashi ga shagwaba ga saurin kuka ga kuma shegen tsoron tsiya amma sai taurin zuciya bala'i. Tareda hibban suka tafi a jiye ta a school sannan ya wuce office bayan ya gaisa dasu afnan,. Afnan ce take tayi mata tsiya wai jiya soyayyar tasa ta tafi bata sani ba. "Ke yaya Habib ne yazo dauka ta, kinsan halin shi dana tsaya yi miki sallama dana shiga uku ai" dariya sukayi mata su suka "lallai wannan yaya Habib ɗin naki ko mu tsoron shi mukeji mutum ba fara'a" inji afnan. "Kai amfa guy ɗin ya haɗu, ni wlhy dazai soni da bazan damu da halin shiba ko kadan" khairat ta faɗa cikin serious ɗin nan. Sororo jiddah tayi tana kallanta cikeda takaici da wani irin bakin ciki tace "to Bama zai soki ba gyara ma kiyi hakuri" Dariya suka sakeyi sannan suka wuce aji... Habib zaune a gaden ɗinsa, A hankali yake shan coffeen shi, lokaci zuwa lokaci yakan yi murmushi idan ya tuna jiddah yadda take zaro idanuwanta cikin tsoro, sam baiji shigowar Sultan ba, saijin maganar shi yayi a kanshi. "Me kake tunani ne haka Habibullah." "Babu" kawai yace yaci gaba da shan coffeen shi. "Shikenan, next week za'a yi dinner na gama komai lokaci kawai ake jira.." Sultan yace yana zama kusa dashi. "Hakan yayi" shima ya mayar masa da amsa...... Kwana biyu kenan hibban baya samun dauko jiddah saidai Kabir ya kawota babu wanda ya sani dan ko mommy Bata sani ba,. Yau lokacin tasowar su nayi mommy tace Habib yaje ya dauko ta daga school,. Shi kaɗai ya tafi yana zuwa ya tsaya bakin gate din bai shiga ba, jiddah kuwa suna tafe tare da su khairat suna hira suka nufi bakin gate dan bazasu iya school Bus ba, suna fita daga gate din jiddah gabanta ya fadi ganin Habib zaune saman motar shi da alama turawa yayi a nemo ta gashi tasan yanzu Kabir yana kan hanyar zuwa daukar su itada afnan. Ganin tana kallan waje guda ne yasa su khairat kallan wajan suma sunyi mamakin ganin shiya zo daukar ta. Tun fitowarsu Habib ya gansu tsaff ya kalle su sannan ya mayar da kanshi kasa kamar bai gansu ba, jiki ba Kwari ta karasa tace "sannu yaya Habib ashe yau kaine kazo..." Bata karasa ba ya balla mata harara sannan ya sauko daga saman motar. Yanaji kawayen jiddan na gaida shi amma ko kallan inda suke baiyi ba ya shige motarshi. Sallama tayi musu da sauri ta shiga gaban motar dan ta hango motar Kabir tana zuwa. Iya mamaki Habib yayi dan sarai yagane motar data tsaya ne yasa take wani sauri sauri, take ranshi yafara ɓaci "lallai kuwa ranki zai ɓaci idan ma samari kika fara kulawa yarinya" ya faɗa a ransa.. Har sukaje gida babu wanda yace komai, yana jinta ta saki ajiyar zuciya ganin sun wuce motar.. Suna zuwa gida ta fice shikuma yaja motarshi a guje ya fice... Kofar school tasu ya koma saidai Baiga motar ba, kwafa yayi sannan ya koma motar tashi cikeda takaicin rashin Ganin mai motar "waye a cikin motar, meyasa take sauri tabar wajan..." Ya jerowa kanshi tambayoyin da basu da amsa. Shi sam zuciyar shi bata yadda da kawayen nan nata ba shegu yara kamar munafukai gashi ya fahimci kwana biyu tana yawan zuwa gidansu kawayen nata ko menene dalili...? Habib cikeda damuwa fal cikin shi yaketa faman tunanin ji yayi kanshi harya fara ciwo sannan ya fara driving ɗinsa tareda Jan wani tsaki "akan me ma nake damuwa" ya sake yin wani tsaki yana dukan steering motar.... Yana gama yin Parking ya wuce part ɗinsa, kwanciya kawai yayi sannan ya lumshe idanunsa yafara tunani kamar yadda ya saba..... ***** ***** ****** Yanzu bikin Sultan ya matso, amma dole ya kale Habib Dan yasan bayasan hayaniya sosai, amma saidai yace dole gobe ya halarci dinner da za'ayi, Habib bai Musa ba ya amince yace zaizo. "Nifa gaskiya afnan bazani bikin nan ba ina tsoro kar yaya Habib ya sani.." jiddah ta faɗa kamar zatayi kuka. "Dilla can Yaya Kabir fa kinsan bazaiji daɗi ba tunda shiyace mu raka shi, kuma harda ke yasa akayi mana ankon dinner din ki tambayi mommy zaki kwana anan saimu je bafa dadewa zamuyi ba". Shiru jiddah tayi sannan tace to bari na kirata. Wayar mommy ta Kira ta faɗa mata zata kwana gidansu afnan. Dakyar mommy ta bari,. Cikeda murna tace "Amma pls mommy karki bari yaya Habib ya sani" "Shikenan naji ki kula sosai jiddah kuma da sassafe zan turo hibban ya dauke ki". "To momma byeee" ta kashe wayar... Murna sosai sukayi, sannan suka fara shirin ganin lokaci ya gabato... Hibban baiso jiddah zata kwana acan ba, amma dole ya hakura ya kirata yayi mata nasiha akan ta kula da kanta sannan sukayi sallama ya kashe wayarshi. Fitowar shi kenan daga wanka jikin shi sanye da bathrobe ya nufi mirror yafara kalkale jiki. Sosai ya shirya cikin wani blue ɗin suit sai faman zuba ƙamshi yakeyi,. Sumar kanshi ta kwanta luf sai zuba sheki takeyi, sajen nan nashi masha Allah, Habib yayi kyau kamar wani Balaraben Sudan, (Aeisher initial lady, anga saurayi sai tsuma akeyi😂😝) Dai dai yana daura wrist watch dinshi na gold Wanda ya saje da fatar hannun shi wacce gashi yake kwance luff, kiran Sultan ya shigo. Tsaki yayi sannan ya daga yayi shiru. "Waje da ya cika Malam ga yammata tako ina kyawawa kayi maza kazo mana" Tsaki ya sake yi yace "Kanada damuwa Sultan,". "Ohhh na manta dawa nake waya fa I'm sorry Habibullah na manta kai ba yammata a gabanka amma pls kayi sauri mana nasan mata da yawa zasu rude wlhy" kafin ya gama yaji kit Habib ya katse kiran. Sam bayasan zuwan dan dai shi bai iya karya alkawari bane, dan dole yayiwa mommy sallama ya tafi.. Cikin takun shi irin na isa ya shiga motarshi ya kwasheta kamar wanda ake jira.. Jiddah ansha make-up kamar ba itaba da ta saba da light makeup, tayi kyau iya kyau kamar yar tsana, wasu hadaddun gown suka saka itada afnan sannan suka fice dan tuni Kabir ke jiransu... Suna shiga motar yaja suka fice, jiddah dake gaba sai hirarsu suke yi da Kabir hankali kwance dan yauce rana ta farko da zata taɓa zuwa wani taro....[1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _writin by_📚✍🏻 *_🌹 Firstlady🌹_* *WATTPAD* @Ameenafirstladyy *_🌈Kainuwa writers Association_* 11 Motarsu na Parking afnan ta wuce batareda data jirasu ba, da kanshi ya zagayo ya ɓude mata motar. Jiki a sanyaye Jiddah ta fito, Kabir yace "muje ciki" harya juya zai tafi yaga takasa daga ƙafa. Ji takeyi sam batasan ƙarasawa ciki batayiwa mommy adalci ba data zabga mata karya. Wani kallo Kabir yabi ta dashi na tsantsan soyayya sannan ya gyara tsaiwa yace "jiddah ko bakyasan zuwan ne na takura miki"? Girgiza kai kawai tayi batareda tace komai ba... Habibullah kuwa da shigowar shi kenan fitowa yayi daga cikin lafiyayyar motarshi, rufewa yayi tareda juyowa dan shiga cikin hall din. Dumm yaji kanshi tareda saurin cire siririn farin glass dinshi. Tabbas jiddah ce tareda wani wanda baisan waye ba, hasken fitilar dake haskaka wajan ne yasa ya gane jiddan ce dai tsaye duk da kanta a kasa yake... "Jiddah ki ɗago idanuwanki ki kalle ni kiyi min magana idan bakyasan zuwan ne saina mayar dake gida..." A hankali ta ɗago kai ta sauke idanuwanta kan nashi, da sauri ta janye su tana kawar da kai dai² saukar idanuwanta cikin na Habibullah. Lokaci guda gumi ya fara jika mata fuska nutsuwar ta fara kaucewa dan yadda taga ya ɗaure fuska yana jingine jikin motar shi amma idanshi na kansu... Saida ya gama kallesu sannan a zafafe ya koma motarshi yaja ta da gudun tsiya kamar zai tashi sama.. Tana ganin tafiyar shi ta dawo da kanta wajan Kabir wanda yaketa faman magana tun ɗazu daya fahimci hankalin baya tareda ita. "Pls Kabir ka mayar dani gida yanzu" Da mamaki ya kalle ta "lafiya jiddah lokaci guda kin rude haka" "Pls nidai muje ka mayar dani dan Allah" ta marairaice mai Murya. Ganin hankalin ta ya tashi yasa Kabir yace ta shiga su tafi,,,, ba bata lokaci ta shige tana jin gabanta na faduwa... Gudu sosai yake shararawa tuni kanshi ya fara ciwo dan baya daukar pressure sosai, lokaci zuwa lokaci yakan yi ajiyar zuciya tareda wani huci mai zafi. Kai tsaye part ɗinsa ya wuce ya sakarwa kanshi shower, ya daɗe sannan ya fito. Saman bed ya faɗa tareda rintse ido yanajin wani zafi a cikinsu musamman idan ya tuna fuskar saurayin dake dauke da murmushi... Kabir har gida ya kawo jiddah motar na tsawa ta fice bayan tayi masa godiya, jikinta sai tsima yakeyi tana buga gate din mai Gadi ya buɗe. Ko juyowa batayi ba ta shige sannan Kabir ya tayar da motar shi ya bar wajan zuwa dinner... Tana shiga ɗakinta ta wuce, wanka tayi sannan ta kwanta hawaye na zubo mata "meyasa nayiwa su mommy karya gashi nan najawa kaina yaya Habib ya ganni" ta faɗa hawayen na sake zuba.. Mommy da batayi bacci ba tayi mamakin jin dawowar jiddah tunda taji bude dakinta da sauri mommyn ta fito dan jin ko lafiya ta dawo. Jiddah na kwance taji bude dakinta, a firgice ta tashi ganin mommy ce yasa da gudu ta taso ta faɗa jikinta. "Lafiya jiddah meya faru meya dawo dake yanzu". "Mommy Dan Allah kiyi hakuri nayi kuskure" Cikeda mamaki mommy tace "fadamin meya faru".? Tana kuka ta fadawa mommy gaskiya sannan ta faɗa mata ganin da Habib yayi Mata. Murmushi mommy tayi sannan tace "kinyi kuskure jiddah meyasa kika yimin karya, dakin fadi gaskiya ma da kaina xansa Hibban ya kaiki ki bari kwanta yanzu bari nake gun Habib ɗin" mommy tace tana kwantar da ita.. A kwance ta samu Habib idanuwan shi a rufe jin alamun shigowar Mutum baisa ya buɗe ido ba. Zama mommy tayi gefensa sannan ta kamo hannunsa cikin nata. "Habib" ta kira sunanshi a hankali.. Shima a hankali ya buɗe idanuwan shi tar a kanta amma bai amsa ba.. Murmushi mommy tayi dan yau ta tabbatar da zargin ta akan Habib duk tasan abin mai wuya ne. "Habib jiddah ta faɗa min komai banaso naji kayi mata wani abin kayi hakuri ka kyaleta dan akwai yarinta a kanta" Rufe idanuwan nashi ya sake yi gam sannan ya gyada kai kawai baice komai ba. Mommy kuwa tashi tayi ta nufi ɗakin jiddah wadda tayi bacci tun fitar mommy. Da sassafe Sultan ya kirashi ya karaci masifar shi Habib bai saurare shiba saima kashe wayar shi dayayi. Jiddah na ganin shigowar shi sum sum tabar palourn yana lure da ita, taɓe baki yayi tare jan tsaki dan haushin ta yake ji jira yake wani abu ya sake shiga tsakaninsu taga yadda ake ramuwar hukunci. "Mugu badai shiga sabgar ka zanyi ba Balle ka samu tamari" jiddah tace tana shiga daki. Hibban kuwa yau da kanshi ya dauke ta suka fice shopping, sun sha yawo sannan ya jibgo mata siyayya, suna zuwa gida mommy tace " waiku bakwa gajiya da yawo ne da zarar kaga bakada aiki sosai saika kwashe ta ku fita.." "Mommy ita kadai gareni fa kanwata" hibban ya faɗa yana ficewa. Itama jiddah suna gama Magana. da mommy ta wuce dakinta tanawa mommy dariya wai zatayi bayani ne idan ta auri miji mara fitar.. Sakamakon yau ba makaranta jiddah na zaune itada mommy mai Gadi ya shigo. "Ya akayi malam isya" mommy ta tambaya. "Ana kiran jiddah ne Hajiya" Jiddah gabanta ne ya fadi jin mommy batace komaiba. Jiki a sanyaye Jiddah tace "to baba" sannan ta nufi ɗakin ta dan dauko mayafinta. Mommy na zaune ta wuce ta,,. Part ɗin Habib ta hango alamun baya nan da sauri nufi inda saurayin yake. Saurayi ne babu laifi kyakkyawan ne dai² misali, sallama tayi masa ya amsa sannan ta gaida ya amsa a sake. Saida ya gama gabatar da kanshi sannan ta bude baki zata bashi hakuri saidai ina tuni ta zato idanuwanta ganin Habib yayo wajanta kai tsaye fuskar nan har wani ja tayi. Kafin ya karaso da gudu ta nufi palourn su tana shiga ɗakinta ta wuce ta rufo kanta. Shima saurayin mamaki yayi ganin Habib yasa tabar wajan, Habib na karasowa saurayin ya mika hannu su gaisa saiya ga Habib ɗin ya sake tsuke fuska nan. A hankali Habib ya fitar da wani huci daga bakinsa sannan ya sake kallan saurayin a lalace a wulakance. "Malam karna sake ganinka a gidan nan," har zai wuce yaji saurayin yace "koza iya fadamin meyasa." "Saboda tanada wanda zata aura" Habib ya fadi maganar bayareda wani tunani ba. "Amma ai banji labari ba kafin zuwana" ya sake jefawa Habib maganar. Wani murmushi wanda yafi kuka ciwo Habib yayi sannan ya juyo yana karewa saurayin kallo "ai gashi yanzu kaji" Habib ya faɗa yana barin Wajan. Yanajin tashin motar saurayin wanda ya tafi cikeda mamaki. A zuciye Habib ya shiga palourn, idanuwan shi sun kankance sunyi ja, kai tsaye ɗakin ta ya nufa ,. Kiran mommy ne yasa ya tsaya yana rintse ido sannan ya juyo yana huci. "Habib waikai wanne irin mutum ne, meyasa bazaka iya boye fushin ka na wani lokaci ba kullum kai a zafin kai kake" Idanuwan shi ya buɗe jin fadan mommy,,. Dakyar ya iya magana a hankali. "Mommy jiddah harta San tafara kula samari... Yayi shiru yakasa ƙarasawa. "Ikon Allah to sai yaushe kakeso ta fara kula samarin tunda naga kaine uban nata yau kuma" mommy ta faɗa tana tsare shi da kallo. "Jiddah fa yanzu saura wata biyu kacal tagama makarantar to yaushe kakeso ta tsayar da wanda zata aura Sarkin fushi,,,, to wlhy ka kyalemin ya ta zabi wanda takeso tun wuri duk kabi ka gama tsorata yarinya data ganka zata fara cin gudu tana buya kokuma tafara kuka Habib ka fita ido na na rufe fa.." mommy taci gaba da fadanta... Saida ta gama sannan Habib ya fice zuciyar shi na suya har wani juwa yake gani a haka ya shiga part ɗinsa. "Meyasa nake jin zafi ne akan wannan yarinyar, meyasa banaso na ganta da wani..,,""? Ya jerowa kanshi tambayoyin da basu da amsa... Jiddah kuwa har akayi magrib bata fitoba tana tsoron karsu hadu a palour. Saida akayi isha sannan ta fito tayi dinner, mommy kuwa batace komaiba akan maganar. Tana gama dinner ta koma ɗakinta ta kwanta. Habib ma badan yaso ba saidan mommy ta takura yazo yayi dinner, coffee kawai yasha yana wani yamitsa fuska da jan tsaki kasa ƙasa wanda baisan dalilin yinsa ba, yanaji hibban yana magana amma ko kallan shi baiyi ba ya fice. Murmushi mommy tayi danta fahimci abinda Habib ke nufi saidai tasan yadda zatayi dashi.... Ɗakinsa mommy ta nufa dauke flask Wanda ta zuba masa coffeen shi na dare aciki. Zaune yake da computer a gabansa, ɗago kai yayi yana kallan mommy sannan yayi murmushi ganinta da flask.. A kan Centre table ta ajiye sannan ta dawo gefen shi ta zauna tana kiran sunan shi. "Na'am mommy". Ya amsa dai² yakai coffee bakinsa. "Habib ina san ka auri Jiddah.....";! Wani irin faduwar gaba tareda razana yasa Habib kwarewa da coffee take yafara tari. Da sauri mommy ta amshi cup din hannunshi ta ajiye sannan takama tafara shafa kanshi a hankali. Saida ya tsagaita sannan ya kalli mommy cikin murya mai rauni "mommy bazan iya auran...." Kafin ya ƙarasa yaji mommy tace "umarni nane wannan ba shawarar ka nake nema ba". Gaba daya ji yayi kanshi ya fara ciwo a haka ya ɗago jajayan idanuwan shi da suka fara rufewa yace "shikenan mommy" daga haka bai sake cewa komai ba. "Allah yayi maka albarka my son, ka kwanta ka huta" ta faɗa tana tashi ta fice. Tana fita Habib ya kwanta, yakasa tantance wanne irin yanayi zai fassara hakan dashi yakasa tabbatar da yadda yakeji a ranshi. "Ya Allah" ya furta a hankali yana rintse idanuwanshi.... Mommy Kai tsaye dakin jiddah ta wuce zuciyarta cikeda farin ciki dan tasan jiddah bazata ki amincewa da zancan taba. Jiddah na kwance taji bude dakinta, murmushi tayi ganin mommy ce. "Jiddah tashi zamuyi magana" mommy tace da ita. Babu musu jiddah ta tashi dan yauce rana ta farko da mommy tace zata magana da ita. Kamo hannunta mommy tayi sannan tace "jiddah inaso ki auri Habib duk na nasan hakan zai zama kamar takura a wajanki..." A hanzar ce jiddah ta ɗago tana rufe bakin mommy duk da irin yanayin data tsinci kanta wanda bazata fassara shiba. "Haba mommy ya kikeso ki banbanta ni da yar da kika haifa da kanki, umarni kawai zaki bani dole zanbi tunda na ɗauke ki kamar *MAHAIFIYATA* wacce na rasa.." ta faɗa Muryar ta na rawa. "Jiddah idan bakyasan shi bazan yi miki dole ba, ki fadamin yanzu" "Ina sanshi mommy" ta faɗa amma a zuciyarta kamar ta face da kuka haka takeji. "Amma saidai shi yaya Habib ba lallai ya..." "A'a jiddah shima Habib yana sanki, saidai bazai iya faɗa miki bane nice na gano hakan, kuma yanzu da kanshi yace na tuntubae ki naji idan zaki amince".. Tsananin mamaki ne yakama jiddah, jin Habib da kanshi ya amince harya turo mommy me hakan ke nufi Kenan dama can yana santa kishi ne yasa yake azabtar da ita idan yaganta da wani.. Muryar mommy ce ta katse mata tunanin "kiyi tunani jiddah zuwa wani lokaci idan kinga zaki iya auran nashi sai a tsayar da lokaci da zarar kin gama makaranta sai ayi auran"... Mommy ta faɗa tana tashi ta fice... Sam jiddah takasa wani tunani, cikin kankanin lokaci bacci ya sace ta cikeda mafarki kala kala... Habib kuwa ya dade baiyi bacci ba, shikenan yasan raini dole zai shiga tsakaninsu da yarinyar wanda shi bazai dau hakan ba, dole ma yasa yarinyar ta gane tayi kuskure data nuna tana sanshi....... Mommy kuwa cikeda farin ciki tayi bacci dan tasan shikenan lokacin sauyawar Habib tayi sannan bacci ya sace ta. Kuyi manage da wannan👈 *_🌹 FIRSTLADY CE🌹_*✍🏻 ```VOTE COMMENTS & FOLLOW```🤝🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 *_Writing by_*📚✍🏻 *_🌹 FIRSTLADY🌹_* *WATTPAD* @Ameenafirstladyy *_🌈 KAINUWAWRITERSASSOCIATION_* *https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation* 12 .....yau da wuri jiddah ta tashi, ko breakfast batayi ba ta shirya tafiya school saboda exam din da zasu fara kwana nan. School bag ɗinta ta dauka sannan ta fice jin hibban nayo mata alamun ta fito. Tana shiga hibban ya tada motar suka fice,. Akan idon Habib suka fice taɓe baki yayi sannan ya nufi wajan mommy. Hibban Yana lure da jiddah duk jikinta a sanyaye yake tun safiyar Yau. "Jiddah akwai matsala ne"..? Girgiza kai tayi sannan taci gaba da wasa da yatsun hannunta. Saida Hibban yayi murmushi sannan yace "bakya sanshi ne, saboda halin shi ko dakuma abinda yake miki"? Yasake jeho mata tambayar. Cikin tsananin mamaki jiddah ta kalle shi jin yasan maganar,. Waigowa yayi yana kallanta dauke wani murmushi sannan ya daga mata gira yace "Yes kina mamaki ne ya akayi nasan zancan,. Tuni na sani ai tun dawowar yaya Habib shawarata kawai ki amince nan gaba zakiji dadin rayuwa dashi dama na faɗa miki shi yaya Habibullah duk yadda kika dauke shi haka zaki fahimce shi..." Sosai hibban yaci gaba da kwantar mata da hankali sannan ya sauke ta a school batareda ta furta komai ba saidai tarin tunanin yadda zata iya soyayya da Habib... Habib kuwa saida yayi breakfast sannan mommy tace "Habib na bawa jiddah kwana biyu tayi tunani akan maganar banaso naji wani abu ya biyo baya dazata ki amincewa.." "Inshallahu mommy" Habib yace yana jin wani farin ciki sannan yayi mata sallama ya nufi hospital. "Tabbas saiya san yadda yayi ya janye maganar nan, to amma ta yaya..'? Murmushi yayi sannan ya ciro wayar ya fara kiran layin hibban wanda lokacin yana zaune a office ɗinsa. "Hello yaya.." "Wanne lokaci ake tashin su"? "Wa fa"? Hibban ya tambaya cikin rashin sani. Tsaki Habib yayi cikeda takaici, jin haka hibban yayi saurin faɗa masa lokacin. "Ok" Habib yace yana katse kiran. Hibban ya dade yana mamaki amma saiya make yaci gaba da aikin shi. Jiddah kuwa jiki a sanyaye take komai, lokaci zuwa lokaci takan yi murmushi idan ta tuna Habib tabbas tasan Habib dole kowacce mace tayi fatan samun miji kamar shi saidai bazata iya rayuwa cikin yanayin dayake nuna mata ba, kuma sam bazata iya kin yarda da tayin mommy ba ga hibban wanda ya dauke ta kamar kanwar shi ciki daya. Haka jiddah taci gaba da tunanin karshe dole ta yanke shawarar amincewa koda kuwa hakan na nufin sallama farin cikin ta a gidan Habib..... Bata taɓa kawo Habib ne zaizo ɗaukan taba, hakan yasa bata ji komaiba lokacin data ga Kabir yazo daukan su. Lokaci zuwa lokaci Habib na kallon gold watch dake daure a wrist ɗinsa, lokaci nayi ya fito dauke da jacket dinshi a hannu,. Wata nurse ce ta fito tana fadin yallabai akwai wadanda suka kawo emergency yanzu.. Wani Banzan kallo yayi mata a dakile yace "ku nemi Ameenu I want do something at home" ya faɗa yana ficewa batareda ya waigo ba. Da gudu yaja motarshi dan ganin lokaci yana kurewa, cikin wani irin yanayi yake binsu da kallo, kamar yaso gane guy din kamar shine wanda ya gansu a dinner tare. Jiddah sam batasan yazo ba fara'ar ta kawai takeyi suna jiran fitowar afnan da khairat,. "Waye wancan naga alamar kamar ke yazo ɗauka" Kabir yace yana yi mata nuni da motar Habib wanda yake danna wayarsa amma sam hankalin shi baya kai tsananin bacin rai ne kwance a zuciyarsa. "Innalillahi.."! Jiddah ta faɗa tana zaro manyan idanuwanta da suka nuna tsoro karara. "Lafiya jiddah" Kabir ya tambaye ta. Ko sauraran shi bata yiba jiki a sanyaye kamar munafuka ta zagaya ta shiga motar. Habib wanda baka iya tantance damuwarsa da farin cikin sa sam bai nuna yasan ta shigo motar ba, saida ya dau kusan mintina goma sannan ya tayar da motar batareda ya kalli inda take zaune ba.. Yanayin gudun dayake kaɗai ya isa ya tabbatar da cikin bacin rai yake,,, jiddah kuwa kasa ɗago kanta tayi tsabar tsorata da yanayin sa. Yanayin Parking jiddah ta fice da sauri harda haɗawa da gudunta, wuf ta shiga palour ko sallama babu,,, mommy dake zaune a palourn da mamaki tace "kalau kike gudu haka jiddah keda waye"? Kofar shigowa ta nunawa mommy saidai mommy bataga kowaba tasan dai baya wuce Habib ne. "Habib ne"!? Mommy ta tambaye ta. Daga kai tayi kamar zatayi kuka. "Ke dalla can shine kike wannan numfashi kamar wadda batada gaskiya.."! Tsuru tsuru jiddah tayi tareda share hawayen ta da suka zubo mata. Ganin haka mommy ta sassauta Muryar ta sannan tace "jiddah bafa dole zamuyi miki ba kema yata ce kamar su saboda haka idan bakyasan Habib ki fadamin zan janye maganar.." Girgiza kai Jiddah tayi dan bata da bakin da zatace batasan dan mommy dole ta amince "mommy Ina sanshi.." ta faɗa tana kara share hawayen. Alhammdlilh mommy ta furta a zuciyarta sannan tace jeki shirya ki fito sai muyi maganar karki damu babu abinda zaiyi miki.. Kafin mommy ta rufe baki tuni jiddah ta wuce dakinta da sauri.. Habib ya dade a zaune baisan inda kanshi yakeba tsabar ciwan kai, har duka zuciyarsa keyi gashi mommy bazata barshi yayi wani hukunci ba koda da baki. "Ohhh! Ya Allah" ya furta a hankali sannan ya buɗe motar ya fice. Wanka yayi sannan ya kwanta dai² shigowar mommy ɗakin. "Habib me jiddah tayi maka naga ta shigo a rude". Taɓe baki yayi yace "babu mommy sharrinta ne kawai". Ya faɗa yana lumshe idanunsa. Kamar maisan gano wani abu mommy ta tsaya sannan tace "kayi lunch acan ne"? "No I'm full"?yace kawai. Saidai kisa ta kawomin coffee Yanzu mommy. Batace komaiba ta fice daga ɗakin. Kusan mintina shida jiddah tayi dauke da coffee tarasa tayaya zata shiga ɗakin, cikeda tsoro tayi nocking Kamar yasan itace yaki magana saida tagaji sannan ta shiga cikin sanɗa. Kwance ta ganshi idanuwan shi a rufe yake kamar mai bacci. Cikin sanda ta shiga ta ajiye cup din zata fice. "Waye shi..."!? A firgice ta juyo dan bata taɓa tunanin idanshi biyu ba sai maganar shi taji. Tashi yayi fuskar nan a haɗe idanuwan shi farare tarr dasu saidai ya kankance ya tattare fuskar nan babu alamar wasa. "Bana maimaita tambaya kuma nasan kinji Ni" ya fada yana daɗa haɗe fuska. "Yaya Habib nima bansan shiba tambaya ta yakeyi.." ta bashi amsa a takaice. Wani malalacin murmushi yayi wanda jiddah tasan na mugunta ne. "Ni zakiyiwa karya eyy" ya faɗa yana tashi tsaye. Matsawa tafara yi ganin yana nufo ta. Cikin hawaye tafara magana "dan Allah yaya Habib kayi hakuri wlhy yayan afnan ne kuma mun dade muna tareda shi"ta faɗa tana cigaba da kukan. Habib jin ta ambaci sun dade tare tuni yaji zuciyarsa tayi wani baki da zafi,.. Ganin yanayin shi ya sauya ne yasa jiddah tafara tsorata tana yin baya. "Kina sanshi kenan..."? Kafin ya ƙarasa tayi saurin girgiza kai "a'a wlhy banasan shi yaya Habib" ta faɗa batareda tayi wani tunani ba Dan fitar da kanta. Taɓe baki yayi sannan yace "ficemin a daki". Da sauri tayi hanyar fita tsayar da ita yayi cikin tsawa "share wannan hawayen kafin ranki ya ɓaci" ya faɗa ko jiyowa baiyiba. Sharewa tayi sannan ta fice da gudu ta nufi part ɗinsu,Kai tsaye ɗakinta ta faɗa tafara kuka mai tsuma zuciya.... Habib kuwa murmushin mugunta yayi sannan yasha coffeen yana wani lumshe ido koba komai dai yayi maganinta ai.... I'm sorry my Fans I have lots of things that's why manage this👈 *_FIRSTLADY🌹_*✍🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _writing by_📚✍🏻 *_🌹 Ameena firstlady🌹_* *WATTPAD* @Ameenafirstladyy *🌈 Kainuwawritersassociation* https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation *_(This page is yours my sweet sisters Husaina sunusi ibadan thank you so much I'm so proud of you)_*💓💓 ```I can't forget you my daughter NEESHER JAY```🌹🌹 13 _________________________ Jiddah saida taci kukanta Sannan ta share hawayenta ta shiga wanka. Tana fitowa kiran hibban ya shigo ta daga fara'a. "Yaya hibban ya aiki.."? "Kalau kanwata, badai wata matsala ko? "Eh babu" tace. Murmushin jin dadi yayi sannan yayi mata sallama yaci gaba da aikinsa. Cikin Wata ash color din atamfa docuwar riga ta shirya, bakaramin kyau tayi ba,, har zata fita kiran Kabir ya shigo wayarta. A sanyaye ta daga tareda sallama dauke a bakinta. Amsa mata yayi sannan yace "jiddah waye wannan wanda yazo ɗaukar ki".. ya jeho mata tambayar. "Yayana mana" "A'a jiddah bayan wannan fa"? "Kabir bazan boye maka ba amma kayi hakuri zakaji bayani a daga afnan amma karka ga laifi na dan Allah". Kabir kasa fahimtar bayananta yayi hakan yasa ya katse kiran kawai dan hankalin shi ya fara tashi.. Jiddah kuwa jagwab ta zauna kan katifar ta tana rintse ido, sam bazata iya misalta yadda takesan Kabir ba shi kadai ta bawa soyayyar ta gashi ƙaddara tasa zata rabu dashi ta auri wanda babu soyayyar shi ko kadan a zuciyarta. Palour ta fita ta zauna tana jiran a kirawo sallar la'asar sannan ta tashi. Habib yana gama shan coffeen shi ya sake shiga ya sheka wanka sannan ya fito ya kwanta bisa three sitter dake ɗakin kanshi na kallan silling.. "Meyasa nake damuwa da ganinta da wani danayi, mezai sa na damu bayan sam babu soyayyar ta a ranshi infact ma shi tsanarta ce a ransa dan Baiga abin so a jikinta ba..." Tunanin shi ne ya tsaya tunawa da yayi ta amsa zata aure shi cewar mommy, rintse idanuwanshi yayi da sukayi masa zafi da nauyi. "Zaki gane kuskurenki very soon,," ya faɗa ko bude ido baiyiba. Jin ana kiran sallah ne yasa ya fice dan zuwa masallaci.... Suna idar da Sallah tareda hibban suka shigo gidan,, tana zaune a palour taji sallamar su sannan ta amsa tana kasa dakanta dan batasan su hada ido da Habib. "Kanwata" hibban ya kirata cikin fara'a. Ɗago kanta tayi da murmushi tace "yaya hibban sannu da dawowa" "Yauwa jiddah, tashi muje ki tayani gyara dakina" .. Tashi tayi da sauri dan dama a kuntace take a palourn. Kallon gefen da Habib yake tayi yana zaune cikin wani tsadaddan farin yadi wanda ya amshe shi sosai ya fito da ainihin farar fatar shi saidai fuskar nan a haɗe kamar kullum,,. Taɓe baki jiddah tayi tace "mutum a cikin gida ma bazaiyi fara'a kamar sauran mutane ba" ta faɗa tana bin bayan Hibban. Sarai Habib ya ganta wanda tuni zuciyarshi tafara zafi da tafasa saidai bai nuna ba duk da shi kadai ne a palourn lebensa ya ciza sannan ya wani hura baki ya fitar da iska cikeda bacin rai... Hibban da jiddah kuwa hirar su sukeyi harda dariya "yaya hibban nifa nayi maka mata kawai kai nakeso ka motsa" "Uhmm wacece fadamin" "Afnan na baka kuma na yarda da ita sosai.." Dariya yayi yace "angama kanwata jeki shirya ki raka ni" Cikeda mamaki ta kalle shi "da gaske kake yaya hibban ka amince" Kautar da kanshi yayi yana barin wajan zuwa bathroom danyin wanka sannan yace "naki wasa ne yar nan Ni kingama wanka zanyi ke kawai zan jira" ya shige batareda ya kuma cewa komaiba. Abin ya ba jiddah mamaki sosai, part ɗinsu ta koma lokacin Habib bayanan kai tsaye ɗakinta ta wuce ta dauko mayafinta sannan ta haifa sama wajan mommy. "Mommy zamu fita nida yaya hibban" "Ina kuma zakuje sarakan yawo"? "Da alamar dai yau suruka zamo samo miki" jiddah tace tana dariya. "Aaa toku je maza a zabo mai kyawawan halaye dai" mommy tace. Da gudu jiddah tayi hanyar fita tana dariya "aima mommy tanada kyawawan halayen ma" ta faɗa tana ficewa. Motarsu na tsayawa jiddah zata fice hibban ya dakatar da ita. "Let's me call her" yace yana zaro wayarshi. Jiddah sakin baki tayi cikeda mamaki wato ma har waya sunayi kenan. "Hello My dear, ki fito ina waje". Daga can ɓangaran afnan tace to gani nan. Jiddah kasa cewa komai tayi mamaki ya gama kasheta a tsaye,, tun daga nesa ta hango afnan taci uwar kwalliya. Tana karasowa tayi dariya cikeda farin cikin ganin shi tareda jiddah. "Jiddah yau kuma harda ke"? Harara jiddah ta maka mata sannan ta nufi cikin gidan dan gaida Mama. Sun dade suna soyewar su sannan yace ta shiga tace jiddah ta fito yana jiranta. "I'm sorry jiddah shiyace karna sanar miki soyake yayi suprise dinki" afnan tace tana nuna alamun damuwa. "To ai kun kyauta gashi kuma yayi". Ta faɗa suna ficewa.. A mota jiddah shagwaba ta dingayiwa hibban wai tayi fushi ace yana soyayya da Aminiyarta amma bata sani ba sai yau. "To yar rigima ta dalilinki nasan ta ai idan bakyaso saina kyaleta ai na nemi wata". "A'a inaso mana kaga kuwa yadda kuka dace da ita" "Bangani ba sai yanzu da kika faɗa" "Kuma auranta zakayi da gaske yaya hibban" ta sake tambayar shi. "Eh mana so nakeyi a saita bikin da naku keda yaya Habib..."! Tsit tayi bata sake magana ba dan gaba daya jikinta sanyi yayi. Hibban kunshe dariyar shi yayi ganin harta nutsu kamar ba itace take faman zuba surutu ba. "Yadai jiddah akwai wani abu ne"! "A'a babu komai" tace kawai. Murmushin hibban yayi sannan yaci gaba da driving ɗinsa..... Yanzu su jiddah tuni sun fara exam ɗinsu sosai suke shan wuya,,,tuni Kabir ya hakura saidai bakaramin jinyar zuciyarshi yayi ba akan soyayyar jiddah hakan yasa lokaci zuwa lokaci yake kiranta su gaisa.. Kullum hibban ke kaita school ya dauko ta dan fafur Habib yace bai yarda akawo wani kato wai driver ba gara hibban ya dinga zuwa ɗaukar ta... Har yanzu babu wata jituwa tsakaninta da Habib yanzu ko gaisuwa saidai idan mommy na wajan yake amsawa,,, duk wata hanya dazai bi wajan ganin ya warware maganar abin yaki yiyuwa.. Yauma kamar kullum jiddah dawowarta kenan daga school a gajiye saboda yanayin exam,,, ko abinci bataci ba Habib ya shigo palourn.. Har zata shige ɗakinta taji yake kee kamar yadda yake kiranta koda yaushe. Jiyowa tayi bata amsa ba dan itama abin yafara bata haushi. "Ki gyaramin dakina Yanzu" yace yana hanyar fita. "Kabarta ta huta ai ko baba Sarkin saka aiki" Baice komai ba ya fice ya nufi part ɗinsa. Jiddah kuwa kaya kawai ta sake ta fito zata wuce part ɗin nasa. Mommy dake zaune gefe ta tsayar da ita. "Ina zakije bikici abinci ba"! "Mommy zanje na gyara masa dakin ne yanzu zan dawo kinsan halinshi yanzu sainayi laifi". Mommy batace komaiba Dan Yanzu abin har haushi yake bata yadda jiddah ke tsoron Habib kamar wani aljani... Jiddah kuwa ganin mommy batace komaiba yasa tayi saurin ficewa.. A hankali ta tura kofar palourn nashi,wani daddan ƙamshi ne ya ziyarci hancinta tareda sanyin a.c mai ratsa jiki.. Lumshe ido tayi yadda taji ƙamshin yayi mata daɗi ga palourn tsaff kamar ba'a shiga cikin sa. Kallan palourn tayi babu wani abin gyarawa kuma shima baya palourn, dole ta nufi ɗakin shi dan sanin inda zata gyara. Zaune yake hannun shi rikeda da ƙatuwar wayarshi da alamu wani abu yake dubawa... A hankali ta shigo dakin sannan tayi dauriyar cewa "gani yaya Habib"... Ko kallan inda take baiyiba ba kamar ma baisan da wata halitta a wajan ba.. Jiddah ta dade a tsaye har kafafunta suka fara gajiya bashi da alamun ɗago kai yayi mata magana gashi babu damar fita ta shiga Uku wajanshi. Takaici ne ya kamata ganin bashida bashida alamar yin Magana... Saida ya Kara dadewa sannan ya ɗago fuskar nan tashi kamar haduwar hadari yana kallanta kallan wulakanci. "Meyasa kika amsawa mommy zaki aure ni" ya jeho mata tambayar babu alamar wasa sai zallar bacin rai. Cikinta ne ya wani juya jin tambayar da batasan amsar da zata bashi ba hakan yasa tayi shiru. Taɓe baki yayi yaci gaba da danna wayarshi a zuciyarshi yace baki gaji ba kenan. Jiddah tasan ko kwana zasuyi indai bata bashi amsa ba saidai su kwana a haka ga yunwa tanaji. "Babu komai" Har zuciyarshi yaji haushin Maganar Tata amma saiya make tareda yin wani shu'umin murmushi sannan ya sake haɗe fuska. "Jiddah bana sanki dan banga abin so a tareda keba sam baki kala da irin matan da zan iya koda soyayya dasu ba," ya faɗa yana yi mata wani irin kallo kamar yaga kashi. Har zuciyarta taji haushin Maganar tuni hawaye suka zubo mata tafara sharewa. "Saboda haka ki samu mommy kice bakya Sona idan ba hakaba kuwa,, should you be a trouble"""" yace yana wani sakeyin murmushin wulakanci. Yana jinta tana alamar kuka dama haka yaso sannan yace ta fice mai a daki,, aikuwa da gudu ta fice tana kuka. Murmushin ya sakeyi "yanzu ma kika fara kuka.." Jiddah tasha kuka amma ko mommy Bata fadawa komai ba sai hibban kawai ta sanarwa shima baiji daɗi ba amma sai hakuri ya bata tareda kwarin guiwan tayi hakuri dole watarana zai sota.... Habib kuwa kullum saiya kasa kunne yaji mommy tace jiddah tace batasan shi saidai ina baiji komaiba gashi gu sai kurewa yakeyi sun kusa gama exam.. Jiddah kuwa bata sake bi ta kanshi ba da sassafe kafin ya shigo sun fice itada hibban zuwa school kuma idan ta dawo bata fitowa saita tabbatar baya nan. Sam itama yanzu wani haushin shi takeji musamman idan ta tuna irin maganganun daya faɗa mata "kowa ya faɗa masa Nima Ina sanshi oho" ... Wasan yar buya yanzu sukeyi sosai sai wajan cin abinci kawai suke haɗuwa nan ma bata bari su hada ido kuma tana gamawa zata bar palourn ya Karaci hucin shi ya fice danta dana masa tarko tunda yaci mata mutumci kodan ta bakanta masa bazata ce batasan shiba kodan Mommy.. Habib yakasa tantance irin yanayin dayake ciki,,, mommy kuwa batasan abinda ke faruwa ba kota tambayi jiddah saitace baya mata komai... Habib Zaune a makeken office ɗinsa, hankali kwance yake aikinsa saidai cikin zuciyarshi ranshi ya ɓace yake.. Wata farar takarda ce a hannun shi yana dubawa. Tsaki yayi sannan ya danna wani abu yayi ƙara. Cikin sakanni wata nurse ta shigo jiki na rawa. "Yallabai gani" "Ina Ameenu? "Yallabai saidai a kirawo shi" tace tana kallan fuskar shi. Bai bata amsa ba kusan second goma sannan ya dago fararan idanuwanshi yace "Are You mad, bakisan aikin bane" Da sauri ta fice daga office din Dan Kiran Ameenu. Tare suka shigo tace "gashi yallabai zan iya tafiya" shiru yayi baice komai ba hakan yasa ta gane ba sauran wani abu sannan ta fice tana rufo Kofar. Saida suka kusan mintina shida sannan ya ɗago sexy eyes ɗinsa ya karewa Ameenu kallo. A dakile yace "zaka cigaba da kulada komai zanbar asibitin nan a hannunka"" "Meyasa Dr. Habibullah" Ameenu ya tambaya cikeda mamaki. "Wannan ba matsalar ka bace". Ya bashi amsa a takaice. "Shikenan Dr. Zanyi iya kokarina akan haka". "Ok you can go" Habibullah yace yana maida hankali kan aikinsa... Lokacin daya dawo gida tuni su jiddah sun dawo,,, Kai tsaye part ɗinsa ya nufa ya sheka wanka sannan ya fito ya shirya ya nufi part ɗin mommy yana fatan Allah yasa ta amince da buƙatar sa.... ```vote Share & Comment``` *_FIRSTLADY🌹_*✍🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _writing by_📚✍🏻 *_🌹 firstlady🌹_* *_WATTPAD_* @Ameenafirstladyy __________________________ *_🌈 KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION🤝🏻_* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` *https://www.Facwbook.com/Kainuwawritersassociation* ___________________________ 14 ... Kai tsaye upstairs ya haye ɗakin mommy ya shiga dauke da sallama a bakinsa. Jiddah dake kwance saman bed din mommy tana jin sallamar shi ya boyewarta ta rufe ido kamar mai baccin gaske. Mommy ce ta amsa masa sallamar tana zaune gefen mirror ɗinta,. Kallan jiddah dake kwance yayi sannan ya taɓe baki ya zauna gefen gadon yana yiwa mommy sannu da gida. "Yauwa, harka dawo daga wajan aikin kenan"? "Eh mommy" yayi shiru yarasa ta yaya zai faɗa mata yana san komawa Russia ba. Ƙarfin hali yayi yace" Amm., Dama mommy inaso zan koma Russia ne"!! Juyowa mommy tayi tana yimasa Wani kallo wanda yasa gaban Habib faduwa dan ya gano kamar ranta ya ɓaci. "Me zakayo a Russia kuma, ina ka gama course din daya kaika"? Mommy ta tambaya tana cigaba da kallonsa. "Eh mommy na gama" ya faɗa a takaice. "To kuma mezakaje kayi?" Sam Habib bayasan maganar sosai amma ya fahimci idan baiyiwa mommy bayani ba bazata barshi ya tafi ba, dan saita gano tserewa maganar auran nashi yakeyi. Numfashi yaja sannan yace "mommy inaso zan koma nayi ɓangaran mata"! "Bangane ba Habib banasan maganar wai gynaecology kake san ka koma kayi"? Mommy ta tambaye kai tsaye. "Eh mommy Dan Allah karki hanani komawa likitocin mata sunyi mana karanci kuma shi nakeso yanzu na karanta saboda asibitina....." Katse mommy tayi da fadin "to maganar auran naka kuma fa"?. "Saina dawo sai ayi" ya bata amsa. "To ban yarda ba Habib, saura sati biyu ta gama makaranta kuma so nake data gama muje can kauyan nasu mu nemo auran dan banaso bikin ya wuce wata biyu masu zuwa tunda Hibban ma ya samo wacce zai aura sai a hada kawai.." mommy ta faɗa tana tashi daga gaban mirror ɗin zata fice... Da sauri yace "plsss mommy Dan Allah karki hanani tafiyar nan ki san burina kenan a rayuwa" ya marairaice murya kamar karamin yaro... Murmushin mommy tayi dan tasan halin dan nata amma bazata iya bari ya tafi ba'a yi auran nan ba danta gano hakan ne yasa yakesan tafiyar wato sai an ganshi kenan. Zama ta kumayi sannan ta kamo hannunsa cikin nata. "Naji Habib zan Barka ka tafi.." Wani irin farin cikine ya rufe shi har saida yayi murmushi.. "Amma sai bayan anyi auran tukun saika tafi kabarta a wajena itama saita ci gaba da karatunta kafin ka dawo"... Cikin wani irin yanayi wanda yakasa tantance wanne iri ne yake kallan mommy Sam bashi da bakin kin amincewa dole ya daga bakinsa dakyar yace. "Shikenan mommy yayi" Murmushin ta sakeyi cikeda farin ciki "yauwa Allah yayi maka albarka, Habib" ta faɗa tana ficewa daga ɗakin zuwa palour. Kanshi yaji yafara ciwo hakan yasa ya tashi shima ya fice cikeda bacin da kissima abubuwa da yawa a ranshi... Jiddah kuwa taji komai tuni jikinta yayi sanyi jin maganar mommy bataso ko kaɗan wani abu ya sake hadata da inna marka, saidai babu yadda zatayi dole ta hakura farin cikin ta daya jin zataci gaba da karatu burin mahaifin ta zai cika kenan.. Mommy da kanta ta nemi yan uwan mahaifinsu Habib sukaje neman auran afnan, saboda sanayya yasa aka amince tareda saka rana wata biyu kacal,,. Hibban yaji dadin hakan saidai yana tausayin jiddah dan yanzu kana ganinta kasan tana cikin damuwa har wata yar rama tayi ta tunanin auran Habib wanda ko yaushe yana faɗin bayasan ta duk da itama ba sanshi takeyi ba amma tanajin yadda auran nasu zai kasance... Su duka suka shirya zuwa kauyen saidai Habib cewa yayi yanada aiki bazai samu zuwa ba dole saida Hibban suka tafi jiddah jikinta a sanyaye. Suna shiga kauyan aka fara bin motarsu da kallo yara nata ihu kamar basu taba ganin motaba,,,. A kofar gidan kawun nata aka tsaya sannan hibban ya fito ya buɗe musu motar. "Jiddah ki saki jikin ki zasu yarda kuma bazasu hanamu komawa dake ba kinji" mommy tace dan kwantar mata da hankali. Ƙaƙalo murmushi jiddah tayi tana daga kai sannan suka fito suka shige gidan..... Inna marka kamar a mafarki taga jiddah dakyar ta ganeta ganin yadda tayi wani kyau suffar Fulani sak daga ganinta,, cikin murna ta taresu tana kawo musu ruwa sannan ta aika aka kira kawun jiddah,, wato kawu Audu.. Shima yayi farin ciki ganinta sosai musamman dayaji neman auranta aka zo ba bata lokaci ya amince musu tareda yi musu da neman tafiyar jiddah. "saidai kuma auran yayi kusa da yawa.." Mommy ta fahimci meyake nufi hakan yasa tayi murmushin manya "karka damu jiddah yanzu ai yaya ce dama kawai yardar Ka muke nema ganin kaine mahaifi a gareta yanzu.." "To Nagode Allah yakara arziki,, ince wannan ne siririn namu ko" kawu Audu ya faɗa yana kallan Hibban. Mommy ce tace "aa shi sirikin naku aiki ne ya tsayar dashi shiyasa wannan kanin sa ne"! "Masha Allah Allah ya kaimu lokacin babu komai" kawu Audu ya faɗa.. Inna marka ta kawo musu fura da nono wacce aka dama da dabino saiga Hibban yasha sosai suka dinga yi masa dariya shikuwa bai kulasu ba.. Sai yamma sannan sukayi sallama suka hau motarsu suka wuce,, jiddah har hawayen farin ciki tayi ganin yadda su kawu Audu suketa faman rawar kan ganinta koba komai yanzu tasan batada sauran matsala a wajansu. Kiran Habib mommy tayi a waya bugu biyu ya daga tareda yin sallama "Habib sun amince gamu nan hanyar dawowa". Cikin wani takaici yace "alhammdlilh" ya dakile. Katse kiran mommy tayi tana murmushi jiddah kwance a cinyarta. Cikeda tsokana hibban ya waigo "sarkin san jiki idan anyi auran ya Habib dai bazai dauki wannan halin ba". Shiru tayi bata bashi amsa ba ganin mommy a wajan. "Hibban banasan tsokana ka mayar da hankali kan abinda kake yi" mommy tace.. Sun isa gida lafiya Habib yaji dawowar su saidai bai kula inda suke ba saima wani huci yayi cikin bakin ciki......... Tunda suka dawo mommy tafara Shirin bikin ko su hibban ɗin basu sani ba,, jiddah kuwa hankalin ta mayar kan exam din da suka kusa kammalawa. Yau da sassafe Habib ya shigo palourn nasu,, mommy na kichine yada coffee,, har kichine din ya shigo ya gaida ta. "Nasan coffee ne ya shigo dakai Yanzu" "Eh momma" "Nagama ai har breakfast din anyi" ta faɗa tana Miko masa kayana "tayani fitar da su" Babu musu ya amsa yana tayata fiyarwa zuwa dining room. Saida suka gama suka fito dai dai shigowar hibban. Shima mommy ya fara gaisawa sannan yace "good morning bro" "Morning too" kawai yace yana matsawa jikin table din. "Yauwa Habib jeka kira jiddah muyi breakfast din"! Dumm yaji maganar wani iri, ko konto yakeyi kodai bada shi mommy take ba shidin ne zaije ya taso ta kenan lallai akwai matsala shikenan raini zai fara shiga tsakaninsu daga yau kenan... "Habib dakai nake fa koni zan tashi ne" "No mommy " ya faɗa yana barin ɗakin.. A palour ya tsaya yana tunanin wanne ne dakin nata,, dakin dayaji kamar ana magana kasa kasa ya nufa cikin zuciyarshi kuwa tab da bakin ciki. Ya dade a tsaye kofar dakin sannan ya tura a hankali ya shiga. Sam jiddah batasan shigowar shiba ta juya baya tana waya da Kabir cikin shagwaba take magana harda lankwasa Murya... Jin a fizge wayar ne yasa tayi saurin tashi,. Wani wawan mari Habib ya dauke ta dashi wanda yasa ta ganin taurari sun gifta,, tsoro ne ya kamata ganin yadda idanuwan shi suka kankance fuskar nan tayi ja kamar wuta .. Wayar aka sake kira, jiddah gabanta ya sake faduwa shikenan yau mutuwa tazo. Daga wayar yayi ya kara a kunnen shi.. "Hello sweetheart" Kabir ya faɗa daga can ɓangaran. Rintse idanuwanshi yayi yana jin wani zafi a ciki,, karar tarwatsewar wayar ne yasa jiddah zaro idanuwanta. Hanyar fita tayi da gudu,, taku biyu yayi yasha gabanta cikeda bacin rai. "Waye shi"? Ya fizgo dakyar ya tambaya. Jiki na rawa tana yarfar da hannu tace "wlhy saurayina ne amm.." Hannu ya daga cikin zafin rai zai sake marinta. Wani gigitaccen kara ta saki, wanda ya jawo hankalin su mommy da hibban da gudu suka shigo ɗakin. Habibullah kuwa jin karar da sauri ya toshe kunne saidai ina, kanshi ne yayi masa nauyi sosai tareda wani irin zafi, tuni yafara fita hayyacin sa. Su mommy kuwa kan jiddah dake kuka sosai suka nufa suna tambayar lafiya. Kin faɗa tayi saidai mommy taga zanan yatsun mari kwance fuskarta hakan yasa ranta ya ɓaci ta juyo ɓangaran ganin daya riƙe kai. Sam Habib baya jin komai dan gaba daya jiwa yake ji. Ƙafafuwan shi ne suka gaza ɗaukar shi yadda zuciyarshi ke harbawa da sauri da sauri,. Dai dai matsowar mommy Habib ya sulale a Ƙasa a sume. Da sauri hibban da mommy harma da jiddan sukayo kanshi suna jijjiga shi saidai ina tuni numfashi sa yayi nisa... Babu shiri mommy ta dauki car key,, da taimakon gateman suka fitar dashi zuwa Mota. Su duka suka shiga motar hibban ya figeta a guje zuwa babban hospital dake kusa..... *Waiting next page*✍🏻✍🏻 ````AMEENA MUSA``` *_🌹 firstlady 🌹_*✍🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _by_✍🏻 *_🌹 firstlady🌹_* *_WATTPAD_* @Ameenafirstladyy *_🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*✍🏻 15 Cikin gaggawa aka amshe shi sanin shi a matsayin consultant doctor. Kusan mintina 40 likitocin sukayi basu fito ba,, mommy da hibban duk hankalin su a tashe. Jiddah ma duk sai taji babu daɗi jikinta yayi sanyi. Likitan yana fitowa mommy tayi saurin tashi tana tambayar lafiyar danta. "Karku damu ku same ni a office" doctor Ahmad yace yana barin Wajan.. Hibban da mommy ne suka bishi office din, jiddah kuma ta shiga dakin da aka kwantar da Habib. Sambal yake kwance a saman gadon idanuwan shi a rufe an rufe shi da wani katon bargo sannan ga drip a hannun shi. A hankali yake fitar da numfashi, jiddah kura mai ido tayi kamar mai san ganin wani abu,,. Wani murmushi ne ya suɓuce mata "gaskiya Habib ba karamin kyakkyawa bane dole yace baya santa ita ba class ɗinsa bace" a hankali ya lumshe idanuwan ta tareda sakin wani murmushin. "Ba wani abu bane akwai mutanen da ake haifar su a haka kwakwalwar su bata ɗaukar kara ko wani ihu, hakan zaisa tayi nauyi harta girgiza sannan ta sakar musu da ciwan kai mai tsanani,, to wannan shine ya faru da doctor Habibullah sai kuma bacin rai wanda yasa zuciyarshi harbawa da sauri, idan harbawarta ya wuce haka za'a iya samun matsala" Ba mommy kaɗai ba har Hibban saida yaji gabansa ya fadi duk da sunsan dama ba san kara yake ba ko kadan amma sam basu taba tunanin hakan ne dalili ba. "Amma doctor babu yadda za'a yi.." Dariya yayi yace "kiyi hakuri mommy gaskiya babu tunda haka aka haifeshi ba samu yayi daga baya ba,, saidai zamu rubuta magunguna saiya dage da sha" "Babu matsala Ahmad mun gode" mommy tace tana miƙewa. Tare suka fita da hibban ya wuce siyo maganin ita kuma ta wuce ɗakin da aka kwantar dashi. Jiddah na tsaye mommy ta shigo ta zauna gefen sa tana kare masa kallo cikeda da tausayin dan nata. "Jiddah bai tashi bane tunda muka fita" "Eh mommy bai tashi ba"! "Amma meya hadaki dashi"? Mommy ta sake tambaya. Labari jiddah ta bata,, mommy ta sauke ajiyar zuciya,, tasan Habib yana saurin fushi da zuciya saidai batayi tunanin yanada zafin kishi haka ba. Suna nan zaune Habib ya fara motsi da idanshi. Tar ya budesu kan jiddah dake zaune facing dinshi. A hankali ya sake lumshe ido tareda tuna abinda ya faru. "Sannu Habib" mommy ta karaso da sauri kusa dashi. Jiddah ma matsowa tayi kusa dashi "sannu yaya Habib" tace. Kallanta yayi da sexy eyes ɗinsa sannan ya kawar da kanshi gefe. Tashi yayi niyyar yi mommy tayi saurin taimaka masa ya jingina da pillow dake bayansa. Dai dai shigowar hibban dauke da ledar magungunan a hannu. "Yauwa hibban kira doctor kace ya tashi" har Hibban zai fita yaji Muryar Habib ya tsayar dashi. "I will do myself" ya faɗa yana cire drip din. "Mommy ga maganin saiya sha ai" hibban yace yana miƙa mata ledar. Idanuwan shi dake rufe ya bude yana kallansu saidai baice komai ba. Kallan shi mommy tayi alamun tana jiran yace wani abu. Da kyar kamar mai koyon magana yace "I need to eat something before.." shiru yayi bai karasaba yana wani yamitsa fuska. "Ohhh haka fa bakaci komaiba,," mommy ta faɗa tana kallan jiddah. "Jiddah jeki hau napepki koma gida kiyowa Habib girki pls". "No mommy coffee kawai" Habib yace. "Coffee Habib kaida bakada lafiya tun jiya fa bakaci komaiba" Nodding kansa kawai yayi. "Shikenan jiddah kinji, saiki zauna kiyi karatun ki kawai kibar driver ya kawo" "Langabe kai Jiddah tayi alamun shagwaba "gaskiya nidai mommy zan dawo da kaina plss"! Rintse ido ya sakeyi tuna yadda take yiwa saurayin nan shagwaba kenan wannan halinta ne kowa ma zata iya yiwa" Habib ya faɗa a ransa yana jin wani daci a ransa. "Naji jeki dawo ɗin" mommy tace kawai. Harta fita Habib ya bude ido tunawa da yayi mommy tace ta hau napep. "Hibban ka kaita mana" "Yaya banaso nayi nisa ko akwai Wani abin da..." Wani mugun kallo Habib yayi masa dayasa yayi saurin hadiye maganar tasa sannan ya fice da sauri. Jiddah harta fita gate taga hibban ya fito da motar sa,, motar ya bude yace "shigo na kaiki" "Amma yaya hibban za'a iya neman wani abu fa..." "To ya zanyi Sarkin kishi bai yarda ki hau napep ba" ya faɗa yana dariya kasa ƙasa. Dariya jiddah ma tayi kawai ta shiga motar... Suna fita mommy ta dawo da kanta wajan Habib,, daya rufe ido. "Habib"! Ta kira sunan shi a hankali. Bai amsa saboda har lokacin yana jin jiki dan zuciyarshi bata daina harbawa da sauri ba,, kallan mommy yayi da kyawawan idanuwanshi. "Dan Allah Habib ka rage saurin fushi da zuciya, banaso wani abu ya sameka ta dalilin haka.." Kafeta yayi da idanuwan shi kamar mai tuna wani abu. "Meya haɗaka da ita" Nanma shiru yayi yana kallanta sannan ya rufe idanuwan nasa yanajin wani abu a zuciyarsa mai zafi. "Babu" kawai yace yana rike kansa da yafara ciwo. "Shikenan shikenan bari na kira doctor ya sake duba ka" mommy ta faɗa a tsorace ganin yadda ya rike kai yana cike lips ɗinsa. Tare suka shigo da doctor din, dubashi ya sakeyi sannan yace "haba doctor Habib ka daina yawan damuwa mana saikace bakasan hadarin haka ba," docton ya faɗa cikin yanayin nasiha. Drip yakara daura masa sannan yace lallaifa yasha maganin sa sai zuwa dare za'a sallame su idan jikin yayi kyau. Shidai Habib baice komaiba sai rufe idanuwan shi yayi kamar mai bacci yana jin doctor Ahmad din. Jiddah na zuwa gida da sauri da sauri ta haɗama mommy breakfast sannan ta haɗa coffeen ta zufa a flask sannan ta sakeyin wanka ta fito. Light makeup tayi dan lipstick kawai tasa sannan ta dau mayafinta ta fito palour. Shima hibban saida yayi wanka sannan ya fito suka taho,.. Hibban sai tsokanar yakeyi wai dan miji ba lpy duk ta rude. "Da afnan ce ba lafiya da yanzu bamu gane kanka ba kaima ai" Dariya sosai hibban yayi har zuciyarshi yaji dadin yadda take nuna san yayan nashi a gabansa. Saida suka biya suka siyi snacks sannan suka shiga hospital din. Lokacin da suka shigo an cire drip din sai Mommy na zaune suka shigo, Habib dan buɗe ido yayi jin sallamar ta,, tayi masa kyau sosai hakan yasa ya buɗe ido gaba daya saidai bai kalli ta kai tsaye ba sai satar kallanta yakeyi. "Tashi kasha coffeen Habib" Hibban tayar dashi cikin dabara... "Zubo masa jiddah"hibban yace. Da hanzari jiddah ta dauki cup din ta zuba masa. Yana kallanta yadda kayan suka amshi jikinta tsaki yayi kasa ƙasa "wannan yarinyar bataji" ya faɗa a ransa. "Lafiya Habib" "Kalau mommy" yace yana murmushi dole. Itama murmushi tayi sannan tace jiddah ta mika masa cup ɗin. Kusa dashi ta tsaya sannan ta mika masa cup din, kallanta yayi idanuwan su suka haɗu, saurin tsuke fuska yayi sannan ya amshi cup din yafara sipping a hankali. Dakyar ya shanye cup guda sannan mommy ta bashi magungunan nan ma dakyar yasha dan bayasan magani ko kaɗan. "Kana doctor Amma bansan meyasa bakasan magani ba" mommy tace. Sai dare sannan doctor Ahmad ya shigo ya basu sallama tareda nasiha akan ya rage shiga damuwa tunda yasan matsalar hakan.. "I will take care inshallah" Habib yace. Su duka suka tafi gida, suna zuwa hibban ya taimaka masa ya wuce part ɗinsa. Wanka yayi ya dade a bathtub sannan ya fito ya kwanta. Mommy saida ta sake dubo jikin nashi sannan taje ta kwanta. Sai yanzu jiddah ta tuna da Habib ya fasa wayarta Allah yaso sim card din na wajanta tun dawowar ta ta ɗauke abinta ta boye,, sam bataji dadi ba ta saba kullum sai tayi waya da Kabir kafin ta kwanta gashi yau babu damar yin wayar. "Allah ya sakamin wlhy" ta faɗa a ranta.... Da sassafe jiddah ta shirya tafiya school, tana fitowa palour ta samu Habib zaune kan kujera. Mamaki ne ya kamata abinda bata taɓa ganiba kome ya kawo shi da safe haka kuma oho ta faɗa tana taɓe baki. Kai tsaye upstairs ta wuce yiwa mommy sallama. Tare suka fito da mommyn har palour, dai dai shigowar hibban. Mommy ce tace "hibban yau ku jira kuyi breakfast" "A'a mommy zan iya makara fa saidai na tafi tabi taxi ko napep" "Gaskiya tafi dan yarinya ta bazata tafi batayi breakfast ba" mommy ta faɗa tana kama hannun jiddah. Hibban ficewa yayi dama haka yaso dan yau makara zaiyi idan yace saiya kaita.. Dakyar mommy tasa habib yaci wani abu dan bayasan cin abinci koda can balle yanzu daba lpy. Suna gamawa jiddah ta mike zata fita,. Habib car key ɗinsa ya dauka sannan ya kalli jiddah yace "ki same ni a mota" ya faɗa yana ficewa. "Mommy zai iya zuwa kuwa" "Oho masa muje naji koni zan kaiki" Tare suka fita itada mommy har wajan motar da yake ciki. Fitowa yayi yana shafa sajan shi daya kwanta luff. "Habib zaka iya zuwa kuwa, ka bari mana ta hau napep din" Da sauri yace "a'a zan iya" dan har zuciyarshi bayasan yaji an ambaci napep ko taxi ɗin nan. "Shikenan ka kula sosai" "Ok Mom" yace yana komawa cikin motar. Zagayowa jiddah tayi ta shiga sannan suka fice daga Compound din.. A mota kuwa jiddah sai raba ido takeyi dan ta saba idan shine yake driving gudu yakeyi sosai. Ko kallan inda take baiyi ba, saida ya tsaya ya siyo drinks da snacks sannan ya dawo yaci gaba da driving ɗinsa. A bakin gate ya sauke ta sannan ya dauko ledar ya mika mata baice komai ba. "Nagode yaya Habib" tace kawai. Bai jira komaiba yayiwa motar key yabar wajan. Kai tsaye gidan Sultan ya wuce,, yana shiga yayi Parking sannan ya kira Sultan yace gashi a gidan. Angelina ta amshe shi hannu biyu² sama sama yake tayasu hirar,,. "Wanne irin gagarumin taro ka shirya mana ne" Tsaf Habib ya gane me yake nufi aikuwa ya tsuke fuska "bansaniba ba kaida abin ya dameka saika shirya ai" Dariya Sultan yayi "lallai yau na yarda bakasan auran, nima na shirya idan zaka koma Russia tare zamu tafi kawai" Shiru Habib yayi kawai dan ji yayi maganar auran da Sultan yayi masa ta bata masa rai. Lokaci zuwa lokaci yake duban wrist watch ɗinsa kirar vertex, tun safe har lokacin tashin su jiddah yayi.. Sallama yayi musu sannan ya wuce makarantar. ...."gaskiya jiddah saidai kiyi hakuri da wannan yayan naki mutum kullum ba fara'a" afnan ta faɗa tana dariya. Harara jiddah tayi mata tace "toshi yaya hibban ɗin aka faɗa miki yanada fara'a ne"? Bata rai afnan tayi "kinga Malama karki zagarmin miji na ehe" ta faɗa cikin sigar wasa.. Dariya sukayi su duka ukun har khairat dake faman shan sweet ɗinta. "Ni kuwa jiddah kinjin dadin soyayya da ya Habib ɗin nan kuwa" khairat ta tambaya. "Bansaniba kedai sha zakin ki yar nan" Dariya suka sakeyi su duka suna fitowa daga school ɗin. Zaune yake saman motar, yana jiran fitowar su,. Jiddah na ganin shi tayi saurin yi musu sallama ta matsa jikin motar. Ya dade zaune bai ɗago kai ba kuma yasan zuwanta wajan,, jiddah kuwa takaici ne yasa tayi shiru dan tasan yaga zuwanta wajan.. Saida ya daɗe sannan ya sauko ya wuce cikin motar tana biye da shi. Tana shiga ya figi motar suka bar wajan..... FIRSTLADY✍🏻 [1/1, 2:24 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _By_✍🏻 *_🌹 FIRSTLADY🌹_* *_Wattpad_* @Ameenafirstladyy __________________________ *_🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*✍🏻 ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation ____________________________ 16 Tafiya sukeyi babu wanda yayi magana a cikinsu sai jiddah dake duba littafin ta. Suna zuwa gida yayi Parking, da sauri ta fice zata shige ciki. Dakatar da ita tayi yana mata wani kallo dayasa tayi kasa da kanta. "Saurin na menene haka" "Babu komai"! Tace kanta na ƙasa. Bai sake Magana ba ya wuce yabarta ya nufi part ɗinsa. Tsaki jiddah tayi kasa kasa sannan itama ta nufi nasu part din. Mommy na zaune palour taga shigowar jiddah. "Waya dawo dake"? "Yaya Habib ne" Shiru mommy tayi cikin zuciyarta kuwa daɗi taji... Hibban bai samu dawowa da wuri ba hakan yasa su uku kawai sukayi lunch, mommy nagama cin abincin ta ta wuce dakinta dan ta kwanta. Shima Habib barin palourn yayi cikin dakewar fuska yana fita jiddah ta taɓe baki "kaji dashi kai kaɗai" ta faɗa tana barin palourn itama... Yanzu kullum Habib ke kaita school kuma ya dauko ta jiddah harta saba da zuwa ɗaukar ta dayake yi saidai har yanzu bata sakin jiki dashi dan sam bata ganin fara'ar shi ko kodan. Tuni mommy tafara gyarata ita dai jiddah duk abinda mommy ta Bata sha takeyi dan ko tayi gaddama mommy cewa takeyi zata hada ta da Habib aikuwa nan da nan zata shanye shi tass. Ita kanta jiddah taji sauyi a jikinta saidai yanzu hankalin ta yana kan final exam ɗinsu.... Ranar da sukayi final anyi shagali sosai dan har taro akayi na iyayen yara akaci aka sha tareda bawa yara kyaututtuka daban daban ciki harda jiddah ta samu kyaututtuka har kusan kala huɗu... Duk da Habib baije wajan ba yaji daɗi sosai saidai bai nuna hakan ba koda mommy ta nuna masa kyaututtukan taɓe baki kawai yayi baice komai ba. Biki sati Uku kawai ya rage mommy yanzu batada hutu tako ina. Hibban ma kazar kazar yake yi sosai amma Habib ko a kanshi bai damu ba saima daina wunin gidan yayi ya koma hotel dan samun hutu.. Jiddah kuwa shan gyaran jiki takeyi kamar hauka harta fara gajiya,, kullum da kalar abinda za'ai mata musamman mommy ta dauko masu gyaran jiki,,... Yauma kamar kullum wajan azhar Habib ya shigo gidan cikin tamfatsetsiyar motar shi yana gama Parking hibban ma ya shigo yayi Parking. "Yaya Habib sannu" Baice masa komai ba suka nufi palourn mommy. Tun a bakin shiga sukaji mommy nawa jiddah faɗa. "Karki sha kiyi ta zama a wajan ke kullum sai anyi fama dake wajan shan magani kamar karamar yarinya kanki zakiyiwa ai".. Sallamar su ce tasa mommy yin shiru tana fadin "yauwa aiga maisa ki sha nan yazo" Jiddah najin haka ta daga maganin kamar zatayi kuka ta shanye tass. Hibban ne yafara yi mata dariya cikin tsokana "yanzu maganin kikewa wannan yamitsa fuska kamar zakiyi kuka"... Wani kallo Habib yayi masa mai tattare da gargadi wanda yasa hibban saurin yin shiru ya zauna yana dariya kasa ƙasa.. Habib kuwa ficewa yayi baiyi magana ba dan yasan yanzu ranshi zai iya ɓaci idan yace zai zauna a palourn... Biki ya matso mommy ta kashe kudi har ba'a magana, jiddah tayi kyau kamar ba itaba dan fatar jikin ta kaɗai ya isa ya tabbatar data sha gyaran jiki. Sam yanzu Habib bai fiye zuwa gidan ba shiyasa babu wani abu daya sake shiga tsakaninsu... Yau tun safe Habib ya shigo gidan saidai Baiga alamar jiddah na gidan ba yana gaida mommy ya fice yana faɗin a kawo masa coffee part ɗinsa.. Kusan mintina goma ya ɗauka shiru babu wanda yazo kawo masa.,, Cikeda takaici Habib keta faman tsaki. Shigowar jiddah kenan daga gidansu afnan tun safe hibban ya kaita dansu tsara abinda suke bukata hira ce tayi daɗi ganin harda khairat yasa jiddah dadewa sai yanzu ta dawo.. Harara mommy tayi mata sannan tace "sai yanzu kika ga damar dawowa" "I'm sorry momma mun tsara abinda muke so ne nida su khairat" "Amma kinsan yayanki bazai yadda da wannan tsarin ba ko" Shiru jiddah tayi tunawa da dan rigimar ta datayi . "Na manta yace akai masa coffee jeki kaimasa part ɗinsa" mommy tace tana barin palourn. Gaban jiddah ne ya fadi shikenan tasan saiya ci mata mutunci yanzu,, jiki ba kwari ta nufi kichine ta dauko flaks din ta wuce part ɗinsa. Ta daɗe a tsaye tana tunanin yadda zasu kaya dashi,, a haka jiki a sanyaye ta tura kofar palourn ta shiga da sallama a bakinta. Tunda ta shigo Habib ya kureta da ido bakaramin yi masa kyau tayi ba dan wata doguwar riga ce ta shadda a jikinta tayi mata das kamar a jikinta aka dinka. Ya shagala da kallanta yakasa ɗauke ido daga kanta,, jin shiru yasa jiddah ɗago kanta. Karaf idanuwan su suka haɗu, tsuke fuska yayi saurin yi tareda tsaki sannan ya kawar da kai gefe. "Ikon Allah na kama ka kana kallo na kuma kabini da tsaki" jiddah ta faɗa a ranta. A saman Centre table ta ajiye flask din "ga coffeen Yaya Habib" tace masa cikin sanyin Murya. Jin Muryar ta ne yasa ya lumshe idanunsa a hankali yadda yaji tayi maganar kamar ba Muryar taba.... Buɗe idanuwan nashi yayi yana wani yamitsa fuska yace ta dauko masa cup a kichine ɗinsa. Babu musu ta dauko ta ajiye sannan tayi hanyar fita. "Jiddah..!!!!? Cak ta tsaya takasa jiyowa dan wani abu taji har cikin zuciyarta yadda ya ambaci sunanta karo na farko a rayuwarta sai taji kamar babu wanda ya iya furta sunanta kamar shi. A dan tsorace ta juyo jin yayi tsaki,, "na'am yaya Habib" "Ina kikaje"? Ya jeho mata tambayar. Cikin in Ina tace "babu inda naje ina ɗaki".. Fuska a haɗe ya ɗago kai cikin bacin rai baice komaiba. Ganin irin kallan dayake mata ne yasa tagane gargadi yake mata akan ƙaryar da tayi masa. "Kayi hakuri yaya Habib wajan afnan naje saboda mu shirya..." Kafin ta karasa taji yace "A haka kika fita" Bata kawo komaiba tace "eh" Cikin zafin rai ya taso ganin a yadda ya taso yasa jiddah ficewa da gudu kamar wacce taga dodo. Wani zazzafan huci ya fitar tareda saurin rike kansa yana zama saman kujerarsa... Jiddah kuwa dakinta ta shige ta rufo kofa "wlhy na daina zama kana Marina kamar ka samu jaka" ta murguda baki kamar yana ganinta. Habib kuwa saida ya daɗe a zaune sannan ya tashi ya dauki car key ɗinsa ya nufi wajan mommy. Yana shiga daidai mommy ta ajiye wayar hannunta "yauwa Habib kaya sun karaso yanzu zan aika driver ya ɗauko" Taɓe baki yayi duk da baisan kayan me mommy take nufi ba,. "Lafiya kuwa naga alamar ranka a bace yake" mommy ta tambaye shi.. Shiru yayi na wani lokaci sannan yace "mommy karta sake fita" Da mamaki ta kalle shi tagane me yake nufi saidai ta waske tace "wa Kenan kake nufi" Shiru yayi bai bata amsa ba dan baisan me zaice mata ba. "Naji bazata sake fita ba, amma kasan yanzu dole ne fitar kokuma ka sai mata waya ta dinga maganar ta waya" Nan ma shiru sannan ya fice batareda yace komai ba. Kai tsaye motarshi ya shiga ya fice daga gidan. Yana fita jiddah ta fito palourn. Kallan mommy tayi tace "laifin me kikayi masa"? Jiddah ta gane wanda mommy ke nufi hakan yasa ta marairaice murya tareda langabe kai "mommy kawai dan naje gidansu afnan" "To yace karki sake fita kin jawa kanki". "Karna sake fita kuma mommy" "Eh haka yace saiki jira ya dawo saiki tambaye shi karin bayani"... Kamar tayi kuka haka jiddah taji amma dole ta hakura ta koma ɗakinta... ✍🏻✍🏻✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _By_✍🏻 *_🌹Ameena firstlady🌹_* *_Wattpad_* @Ameenafirstladyy *_🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*🤝🏻 *(Ina ganin sakonnin ku kuma inajin dadi hakan yake karamin Kwarin guiwa I so much love you my Fans Ina yinku irin 💯💯💯 dinnan)*💗💗💗 17 Habib kai tsaye wajan saida waya ya nufa,, yana gama siyan ya biya kudi yabar wajan ya nufi komawa gida har lokacin ransa a dan ɓace yake. Mommy ya bawa wayar ya fice bai nemi inda take ba,, Ganin wayar ce yasa jiddah murna harda su tsalle tsallen murna tana komawa daki tasa sim ɗinta ta kira afnan.... Tun daga lokacin basu sake haduwa ba kuma bata sake fita ba kamar yadda yace,, afnan ce da tazo yaji labarin ya hanata fita tsaki tayi "ke dai wlhy sokuwa ce dole ma ya rainaki kuma nan gaba saikin zubar da hawaye akan wannan tsoron nashi da kikeji, garama ki daina jin tsoro dan zaman aure bazai yiyu a haka ba wahala zaki sha" afnan ta karasa maganar cikeda takaici.. "Dama waya faɗa miki zanji dadin zaman auran nashi bayan da kanshi ya furta cewa ya tsaneni baya kaunata niba class ɗinsa bace".. "To sai me kema ai basan shi kike ba, saiki nuna masa hakan dan kwatowa kanki yanci" afnan tace mata.. Shiru jiddah tayi da alamun Maganganun sun shige,, Afnan ce ta sake katse mata tunanin "Malama dole fa ki fita dan tare zamu raba invitation card dan bazanyi ni daya ba" "Shikenan naji sai muyi tare ɗin" Daga nan suka faɗa wata hirar sai yamma hibban ya maida ta gida... Jiddah kuwa fitar ta kawai takeyi suna sha'anin biki, dan yanzu 6days ya rage tuni danginta na ƙauye su inna marka da sauran Yan uwa duk sun zo har kawu Audu. Shagali sosai akeyi koda yaushe gida a cike yake da jama'a,, mommy tayi rawar gani wajan akwatuna dan kowacce dozin aka yi mata kuma oda mommy Tayo musamman har kayan fitar biki da tayiwa jiddan. Habib kuwa sam baya zuwa gidan saboda hayaniya mutane, koda mommy tayi masa zancan dinner cewa yayi babu inda zaije dan ciwan kai za'a sashi a wajan. Jiddah bataso hakan ba dan zai barmata abin magana wajan kawayen ta. Ranar har kuka tayi jin abinda yace mommy data matsan ta masa akan ya daure yaje karshe cewa yayi tayi hakuri da magana dinner tunda ba yanzu zasu tare ba sai bayan ya dawo daga Russia,,, dole suka kyale shi dan sunsan halin shi sarai.... Ɓangaran Habib kuwa sam baisan meyasa har yanzu bayasan yarinyar ba kodan baisan menene soba shiyasa, tabbas bazai ce bayasan yin aure ba dan zuwa yanzu yana bukatar mace a tareda shi lokuta da dama yakan tsinci kanshi a wani yanayi na bukatar mace amma sam baya murna da wannan auran. Cikin tunanin nasa ne yaji ring din wayarsa dakyar yakai hannu ya daga ganin mommy ce ke kiran.. "Habib meyasa kake haka ne, umarnin nawa ne yazama na banza kome dangin yarinyar nan har sai sun gane wani abu kowa tambayar ina sirikin nasu yakeyi amma kaki zuwa ka gaida su gashi har gobe daurin aure,,, na yarda da cewa ba yanzu zata tare ba sannan na yarda ba saika ke kowanne event ba duk dan hankalin ka ya kwanta amma a duk a banza.." mommy ta karasa faɗa sosai. Iya mamaki Habib yayi dan yauce rana ta farko da mommy tayi masa faɗa har haka. Da kyar ya iya motsa bakinsa kamar mai ciwan baki yace "I'm sorry mom zanzo yau inshallahu" "Karma kazo idan kanasan ganin bacin raina" ta katse wayar batareda ta tsaya jin wani abu ba. Ya dade a kwance kafin ya tashi ya shiga bathroom din dake cikin dakin,. "Pls jiddah kije ki karasa rabawa kinga yayanki ne zaizo ,,daga yau fa shikenan kuma ita kadaice ba'a kaiwa ba wayarta kuma bata shiga" Kallanta jiddah tayi tace "kinsan fa Mommy batasan na fito ba yau," "Nasani aiba dadewa zakiyi,, bari ma nasa yaya kabir ya kaiki ai naji shigowar shi" Kafin jiddah tayi magana afnan ta saurin ficewa daga palourn. Tana nan tsaye suka shigo tareda Kabir ɗin murmushi sukayi wa juna sannan Kabir yace "amayar gobe ce a waje haka" Kasa tayi da kanta kawai batace komaiba. "Shikenan tunda kunyar magana kikeyi, muke na kaiki ɗin kafin ango ya rude Baiga amayar Saba" Nanma shiru tayi sai afnan ce take ta dariya. Kai tsaye motar shi suka shiga sannan suka fice daga Compound din.. Fitowar Habib daga wanka kenan ya shirya cikin wani tsadaddan farin yadi mai taushi wanda tsadar shi ta bayyana tun daga kallansa,, gyara sumar kanshi yayi tareda daura Watch ɗinsa sannan ya feshe jikinsa da wani daddan turare. Bakaramin kyau Habib Yayi ba, car key ɗinsa ya dauka sannan ya fice. kirar Mercedes Benz ya hau tareda yi mata key ya fice daga hotel din. Tafiya sukeyi jefi jefi sukeyin hira saidai jiddah bata saki sosai ba, ganin ya gangara ya tsaya ne yasa ta kalle sa. "Yadai lafiya kuwa" ta tambaya. "Sorry zan sha mai ne " "Ok" tace. Fita yayi daga motar ita kuma ta zuge glass din motar dan ganin gari. Habib daya tsaya shopping dan kaiwa yan uwan jiddan, fitowar shi kenan ya shiga Mota. Har zai tayar idanuwan sa suka sauka kan jiddah dake cikin mota. A hankali ya sauke Glass din motar shi dan tabbatar da zargin shi,tuni idanuwan shi suka sauya launi zuciyarshi tafara tafasa. Jiddah kuwa kallan Kabir tayi daya shigo yanzu yana faɗin "sorry amarya na makara ko" Maganar tasa ce tasa ta yin dariya tareda waigar da kanta gefe. Idanuwanta ne ya sauka kan Habib daya zubo musu ido cikin wani irin kallo, fuskar tashi tayi jajir idanuwan shi sun bayyanar da tsantsan bacin rai. Da gudu taga ya figi motar shi hakan ya tabbatar mata da bakaramin fushi da zuciyar yayi ba. A firgice ta waigo cikin tsoro tace "yaya Habib" "Yana ina" Kabir ya tambaye ta dan yasan wanda zata aura take nufi. Nuni tayi masa da motarshi datayi musu nisa tana fadin "dan Allah Kabir kabi bayanshi pls karya samu matsala kaga fa gudun dayake yi" ta faɗa Muryar ta na cracking.. Kabir shima bayan Habib yabi saidai ina ko kurarsa basa hangowa yayi nisa. Gudu yake sosai saidai yadda kanshi ke ciwo zuciyarshi tayi masa nauyi yana dafe da wajan baisan ina yake yiba shidai driving kawai yakeyi,,,,,, Lokaci zuwa lokaci yake lumshe ido tareda cizan lower lips ɗinsa "meye hadinta dashi meyasa ta fita bayan na hanata" ya faɗa a zuciyarshi tareda sake lumshe idanuwanshi,,, Daidai zai shiga layinsu wata mota ta bige motar shi mutanen wajan sukayo wajan tareda salati.... Hankalin jiddah yagama tashi a haka suka karaso wajan da mutane suke tsaye. "Jiddah hawaye ne suka zubo mata,, tareda saurin buɗe motar ta fita. Habib kuwa tuni ya suma baisan abinda ke faruwa ba,,,, da taimakon Kabir aka sashi a motarsa suka nufi hospital din Dr Ahmad.. Saida aka shiga dashi wani daki sannan jiddah ta kira hibban ta fada masa. "Whattt kuna ina yanzu"" Cikin murya mai sanyi jiddah ta faɗa masa suna hospital din Ahmad. Hankalin mommy ya tashi sosai tareda mutanen da suka zo biki saidai mommy da hibban ne kaɗai suka tafi hospital ɗin.. Kusan awa daya sannan aka kaishi dakin hutu, mommy Bata tambayi jiddah komaiba dan hankalin ta a tashe yake.. "Mommy gaskiya Habib yana wasa da lafiyar shi bansan damuwarsa ba saidai ku bari idan ya tashi saiya yi muku bayani" Dr Ahmad ya faɗa yana ci-gaba da basu bayani akan maganar. "Amma baiji ciwo sosaiba ko"? Mommy ta tambaya. "Eh babu wani ciwo sosai a hannu ne kawai shima bugawar kashi ne very soon zai dawo nrml" Mommy da hibban harma jiddah sauke ajiyar zuciya sukayi sannan suka bar office din zuwa dakin da aka kwantar dashi. Kabir kuwa tuni yabar hospital din ya koma gida,, shima hibban ganin yamma ta gabato yasa ya nufi gida dan tarbar manyan bakin da zasu zo yau. Da kyar mommy ta lallabi jiddah akan ta koma gida saboda baki idan yaso zuwa dare saita dawo. Haka jiddah ta tafi cikeda tsoron farkawar Habibullah yadda zata kasance abu daya take tunani bazai wuce yace ya fasa auran ba wanda ita kuma a daɗin ta haka zata so...... 😍😍Mush love you my Fans💗💗🤝🏻🤝🏻 Yar mutan garo✍🏻 Ameena firstlady [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _By_✍🏻 *_🌹 Firstlady🌹_* *_Wattpad_* @Ameenafirstladyy _____________________________ *_🌈 KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION🤝🏻_* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` *https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation* _____________________________ 18 Jiddah na zuwan gida tayi wanka taci abincinta sannan ta wuce wajan ƴan uwanta dan tayasu hira duk da hankalin ta na wajan Habib.. Zuwa dare gida yagama cika itama shiryawa tayi sannan ta haɗawa Habib coffee Dan tasan zai bukata da zarar ya farfaɗo, tana gamawa hibban ya shigo kichine ɗin. "Yauwa ki same ni a mota mu wuce" yana gama faɗin haka ya fice. A mota ta sameshi tana shiga ya tayar suka fice daga Compound din, tunda suka fara tafiya yake waya da Afnan ita kuwa kanta ta waigar window tana kallan gari. Sai bayan magrib sannan Habib ya farko daga sumar da yayi, da sauri mommy ta Kira Dr Ahmad suka shigo tare lokacin harya cire karin jinin da ake masa ya rufe idanuwan sa. Shigowar su ce tasa ya dan buɗe ido yana kallan su, allura uku akayi masa sannan Dr Ahmad ya fice yace yanzu zai dawo mommy ta kula da shi. Habib na jin jiki sosai dan kanshi bakaramin ciwo yake masa ba ga zuciyarshi na zafi ido kawai yake binsu dashi lokaci zuwa lokaci yake rintse idanuwanshi da sukayi masa zafi.. Motar su jiddah na tsayawa ta nufi room tabar hibban a wajan yana wayarsa. Tura kofar dakin tayi tareda sallama a bakinta,,, mommy ce ta amsa mata tana kallan shigowar ta. "Kin dawo" Jiki a sanyaye Jiddah tace "eh mommy ya jikin yayan" "To gashi nan dai da sauki" Jiddah bata sake cewa komaiba ta ajiye flask din hannunta ta zauna. Habib yana jinsu tun shigowar ta saidai tsananin haushin ta tareda zargi zuciyarshi yasa yakasa bude ido balle ya kalleta dan ko ganinta bayasan yi a Yanzu. Sun dade a haka sannan Dr Ahmad ya shigo yana faɗin.. "mommy a bar sallamar taku sai gobe muga yadda jikin nashi zaiyi". A hankali Habib ya motsa bakinsa cikin yanayin cuta yace "no I can't sleep here,"! Duk yadda mommy taso ya bari zuwa safiya ki yayi yace bazai iya bacci a wajan ba dole aka sallame su kuma da kanshi yaje har wajan Mota. Yadda jiddah taga ko inda take baya kallo ya tabbatar mata tashiga uku wajan shi ala bashi yaga gobe za'a daura auren su. A haka har suka je gida mommy kadai ke Jero masa sannu jiddah kuwa tunda tace sannu taga irin kallan tsanar da yayi mata tayi shiru bata sake magana ba. Part ɗin mommy suka sauka saboda yan bikin part guda aka ware musu shiyasa babu yawan hayaniya a Wajan. Kai tsaye jiddah dakinta ta wuce,, hibban ma part ɗinsa ya je ya shirya... Mommy dake zuba masa coffee kallan shi tayi taga yana rike da kansa. "Habib yadai" Shiru yayi baice komai ba can yace "Dan Allah mommy Kar a daura auran nan gobe banasan ta ku....." Kallan zallar bacin rai mommy tayi masa sannan ta ajiye coffeen tabar palourn cikin bacin rai.. "Ohh help me God" Habib ya faɗa yana rintse idanuwanshi,, sannan ya bi bayanta. Kayan fitar bikin jiddah take linkewa taga shigowar shi yana tafiya a hankali saidai bata da daga kai ta dubeshi ba. "I'm sorry momma plss"! Yadda yayi maganar ne yasa ta kalleshi zuciyarta ta karaya. "Habib narasa meyake damunka jiddah ce bakaso ko kuma auran ne bakaso nasan cutar dake damunka saina fara nema maka magani" Shiru yayi nan ma dan ya gane me mommy ke nufi. "Shikenan na fahimci jiddah ce bakaso to wlhy akan maganar nan Habib saidai ka canja mahaifiya ..." A gigice ya ɗago kai yana kallanta cikin wani iri yanayi wanda yasa kanshi yafara mugun yi masa ciwo yafara magiyar bata hakuri. Saida ya tabbatar mata bazai sake irin maganar Bama sannan ya tashi zai fice. "Coffeen fa"? Mommy ta tambaye shi. Shiru taji yayi hakan yasa tace "jeka jiddah zata kawo maka"! Ji yayi sam coffeen ma ya fice masa a rai amma babu yadda zaiyi "shikenan mommy" yace yana ficewa. Yana zuwa ɗakinsa ya shiga wanka ya dade shower na zuba a kansa sannan yayi wanka ya fito yana wani hucin bakin ciki. "Very soon zata gane kuranta"! Ya faɗa yana kwanciya batareda ya sa kaya ba. Tunda mommy tace takai masa coffee gabanta ya fadi, hatta je bakin ɗakinsa ta dade a tsaye sai ta tuna shawarar da Afnan ta bata akan ta rage tsoron shi hakan yasa ta aro jarumta ta tura kofar dakin ta shiga. Yana jin bude ɗakinsa ya tashi yana kallanta cikeda bacin rai,,, Ganin shi da towel ɗaure a kugunsa yasa jiddah gabanta ya sake faduwa dan sai yau taga cikar haibar shi gaskiya Habib cikakken namiji ne ga faffaɗan ƙirjin shi daya yalwatu da gashi sun kwanta luff,,. Kallanta tsana Habib yayi mata sannan yayi tsaki a zuciyarshi yace "dole ki tsaya mana tunda kin saba ganin maza haka" Jiddah kuwa tunda tayi kasa da kanta ko motsi ta kasa ji tayi kamar kasa ta tsage ta shige dan kunya saidai shi taga ko a jikinsa. "Basai kin nuna kin saba ganin maza a haka ba,,, saiki ajiye ki ficemin a ɗaki" ya faɗa yana kare mata wani mugun kallo. Har zuciyarta taji haushin abinda ya faɗa kenan yana nufin tana bin maza kome yake nufi. Dan ta bashi haushi tabe baki tayi tace "ai shiyasa yau ban tsorata ba".. Mamaki ne ya cika Habib tareda wani baƙin ciki,, cikin fushi yayo kanta ai da gudu ta fice daga ɗakin zuwa part ɗinsu. Garam ya rufe kofar sa sannan ya kaiwa bango duka tareda fitar da wani huci. "Me Kenan"? Ya tambayi kanshi wata zuciyar tashi ta bashi amsa da "raini kenan".. Wani huci ya sakeyi sannan ya zauna yana dafe da kanshi "zaki gane matsayin kowanne namiji very soon" ya faɗa sannan ya nufi wardrobe ɗinsa dan shiryawa. A tsorace ta shiga palourn,, mommy dake zaune ta kalle ta "lafiya kike wannan gudun cikin dare ko wani abu yayi miki" "A'a mommy tsoro naji ganin Compound din babu kowa" Tsaki mommy tayi sannan tace "kedai naga lokacin da zaki girma wlhy" tabar palourn ta nufi upstairs. Itama jiddah dakinta ta wuce ta kwanta luf "daga yau na daina jin tsoron naka tunda abin haka ne" ta faɗa tana juya kwanciyar ta. Habib bai samu wani bacci sosaiba har safiya, mommy da kanta tazo duba jikin nasa da safe. Da sauki yace mata sannan yace zai koma hotel saboda hayaniya mutane daya dameshi. "Shikenan amma ka tabbatar ka dawo before a daura auran" Dumm yayi sannan yace"to" Saida ya biya ya gaida yan uwan jiddan kamar yadda mommy tace sannan ya shiga motar shi yabar gidan ya koma hotel. Yau jiddah da wuri ta tashi saboda zuwan kawayen ta,, a ranar mommy ta dauko makeover,,,.. Habib kuwa yana zuwa hotel ya kwanta tunani fal zuciyarshi sam shi har Yanzu bai yarda yau zaiyi aure ba,, tsaki yayi sannan ya ciro wayar shi ya kira Sultan. "Ango kana ina ne"? Tsaki yayi sannan yace "kafara shirin komawar mu Russia banasan kuma a samu Matsala' "Shikenan Amma pls kana ina" Faɗa masa inda yake yayi sannan ya kashe wayar tashi ya kwanta. Mintina kadan Sultan yazo,, yayi mamakin ganin shi a hotel amma saboda sanin halin abokin nasa yayi shiru bai tambaye shiba. Sai 2 daurin auran shiyasa tun 1 mommy take kiransa akan lallai ya shirya batasan yabata lokaci. Sultan ne ya kawo masa kayansa wata bugaggiyar shadda ce gezna wacce ta amsa sunan kuɗin da aka siyeta. 1:30 Habib ya gama shirinsa tsaff. Masha Allah,, Habibullah bakaramin kyau yayi ba kamar jinsin larabawa ya fito da asalin kyaun sa sak sai zuba ƙamshi yake yi,, sumar kan nan nashi kamar ta larabawa. Yana cikin daura gold Watch ɗinsa yaji kiran mommy. Yana dagawa tace "mutane fa su taru me kakeyi har Yanzu" "I'm sorry momma on my way now" ya faɗa yana ajiye wayar hannunshi... 2:00 dai dai daruruwan jama'a suka shaida daurin auran Dr Habibullah da jiddah sannan aka daura nasu hibban da Afnan,, duk mutane kowa fuskar shi dauke da farin ciki,,,. Habib kuwa ana gama daurin auran yabar taron mutane dan hayaniyar tayi yawa,,, sai neman shi akayi baya wajan Hibban baiji daɗi ba shida Sultan ganin abokansu sai neman shi sukeyi. "Habib badai komawa hotel din kayi ba, ga friends sai neman ka sukeyi" "Eh na koma kuma bana bukatar kowa yasan ina nan" ya katse wayar tashi tareda shan magani ya kwanta... ✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 _By_📚✍🏻 *_🌹 Ameena firstlady🌹_* *_Wattpad_* @Ameenafirstladyy *_🌈 Kainuwa writers association_* 19 A ranar ansha shagali sosai Hibban ji yakeyi kamar yafi kowa farin ciki a Yau.. Sai yamma sannan amare suka fara shirin zuwa dinner,,sosai aka bata lokaci wajan tsara musu tsantsararriyar kwalliya ta gani ta faɗa. Jiddah kamar ba itaba tayi masifar kyau cikin English weeding gown Wanda mommy Tayo mata odarta daga waje.. Saida suka gama shirin sannan mommy tace "jiddah ki kirashi ki tambaye shi kinsan halin Habib sarai" Taɓe fuska tayi kamar zatayi kuka tace "mommy bazan daɗe bafa kinga idan banje lokacin nawa shagalin babu mai zuwa" Kallanta mommy tayi tace "babu ruwana nidai kinsan yanzu dole saida izinin shi zaki fita" Jiddah batace komaiba ta fice ta nufi ɗakinta. Yauce rana ta farko da zata kira Habib da wayarta,, bata ma sani ma ko yanada number nata Saidai tasan zata sha wulakanci... Habib kuwa lokacin yana kwance daga shi sai wata farar jallabiya mai shegen kyau,, hankali kwance yake danna wayarsa yana dube duben sa. Dakyar jiddah ta iya danna number tafara Ring. Ya daɗe yana kallan number duk baisan number ba hakan yasa harta katse bai daga ba. Tsaki tayi tana fadin "na hakura dan bazan juri wulakanci ba" Tunawa tayi ita zata cutu hakan yasa ta sake danna masa kira. Wani siririn tsaki yayi sannan ya daga wayar yayi shiru. Tattara nutsuwar tayi sannan tace "yaya Habib zamu dinner" Tsintar kanshi yayi da yin murmushi sannan yace "to mene nawa aciki"? Shiru tayi cikeda baƙin ciki wato ma mene nashi a ciki. Jin tayi shiru yasa Habib yin tsaki zai kashe wayar,, da sauri ta marairaice murya tace "pls Yaya Dan Allah kabarni" Shiru yayi yana tunanin yadda maza da mata ke zuwa irin wannan wajan cikeda izza yace "ban amince ba" ya faɗa yana katse wayar shi,,,. Har zuciyar jiddah bataji dadi ba,, tasan babu ta yadda za'ayi ta fita dan mommy bazata barta ba gashi bazata dauki wulakanci ba balle ta sake kiranshi... Tanaji tana gani motocin daukar su tazo aka tafi aka barta sai dariya suke mata duk irin kwalliyar data ci dole ta hakura.. Daki ta koma tasha kukanta sosai a zuciyarta tana fadin wannan wanne irin aure ne ace dan baza'ayi tarewa yanzu ba shikenan komai ma baza'ayi ba Kenan... Mommy kuwa batasan banda jiddah aka tafi ba harkan jama'a kawai takeyi... Murmushin mugunta Habib yayi dan yasan bakaramin bata mata rai yayi ba "kaɗan ma kika gani yarinya" ya faɗa yana cizan lips ɗinsa tareda sakeyin wani shu'umin murmushin.... Hibban ma sam baiso hakan ba daya kira jiddah ta faɗa masa amma babu yanda zaiyi sai hakuri ya bata... Kashe gari aka kai Afnan gidan hibban dake cikin anguwar wanda ya gama tuntuni basu da wata tazara sosai sun sha nasiha sosai a wajan mommy sannan ta sake yiwa hibban nasiha akan hakuri.. Next day baki kowa ya watse har mutanan ƙauye jiddah kamar tabisu haka taji dan yanzu soyayya suke nuna mata sosai dakyar mommy ta Bata hakurin watarana Habib ya kaita taje da dade musu..... Haka tabarsu suka tafi aka bari daga ita sai mommy a gidan. Jiddah ji takeyi kamar ita ɗin ba matar aure bace takasa yarda da hakan shiyasa yau tun safe take bacci abinta dan huta gajiyar biki.. Sai yamma mommy ta Kira Habib tace Lallai yau ya dawo tunda taro ya tashi lafiya. "To mommy zan dawo" yace kawai. Sai dare sannan ya shirya ya nufi gidan nasu cikin jibgegiyar motarshi,, yanayin horn mai Gadi ya wangale masa gate ya danna hancin motarsa. Ya dade a cikin motar kamar bazai fito ba saida ya dau lokaci sannan ya fito sanye da siririn farin glass ɗinsa. Jiddah na zaune a palour Tasha light makeup tayi kyau sosai kana ganinta kaga amarya. A hankali ya tura kofar main palourn nasu tareda yin sallama wanda sai mutum ya kasa kunne zai iya ji. Bataji sallamar tashi ba sai ƙamshin turaren sane ya sanar da ita zuwanshi palourn hakan yasa ta dan ɗago kanta tana satar kallan shi,. Yayi mata masifar kyau sosai shiyasa takasa ɗauke kanta daga kallansa. Shima a sace ya kalleta kamar baisan da da mutum a palourn ba yayi hanye upstairs.. Taɓe baki tayi a zuciyarta tace "sarkin izza kamar wani jinin sarauta" ta faɗa yana mayar da hankali kan charting din da takeyi.. A zaune ya samu mommy tana waya da alamar yan uwan jidda ta kira tana musu ya gajiya tunda yaji ta ambaci sunan Inna marka.. Saida tagama sannan ya gaida ta amsa masa sannan ya tashi zai fice.. "Habib" "Na'am"!!!! "Idan kayi sallar isha kazo inasan ganinku" Maimaita zancan yayi a zuciyarshi "ganin mu kuma" Kamar tasan me yake tunani tace "ina nufin kaida jiddah"! Da kyar ya iya cewa "to momma" ya fice daga ɗakin nata. Kamar yadda ya barta a zaune haka ya dawo ya sameta har zai fita yaji tace "a dawo lafiya".. Dan tsayawa yayi cikeda mamaki saidai ko jiyowa baiyi ba yasa kai ya fice tareda taɓe baki yana faɗin "da alamun wannan ta zata fiye zakewa da yawa"..!! A zuciyarsa. Kamar yadda mommy tace yanayin sallah ya dawo gida lokacin har sun zauna yin dinner itada jiddah. Zama shima yayi kujerar kusa da mommy yana fuskantar jiddah dake cin abincinta hankali kwance.. Saida suka gama cin abincin suna zaune a palourn mommy ta kalli Habib da yake zaune fuskar nan kamar bai taɓa dariya ba. Nasiha tafara yi musu mai ratsa jiki sannan ta sake kallan Habib ɗin. "Dan Allah Habib ka kula da jiddah dan kamar amana ce a hannun mu saboda haka banasan naji wata matsala ta biyo baya".. sannan ta koma yiwa jiddah nasiha sosai har saida jiddah ta zubar da kwalla tareda sake jin soyayyar mommy har cikin ranta. Saida mommy ta gama yi musu nasihar sannan tace jiddah tabishi part ɗinsa kafin komawar tashi saita dawo wajanta,,. Gaban jiddah bakaramin faduwa yayi ba dan tasan shikenan tashiga wani hali muddin aka barsu tare ita zata sha wahala. Habib kuwa zuciyarshi baƙiƙƙirin tayi tareda wani takaici amma saiya make bai nuna ba. Badan jiddah taso ba dole tabi bayanshi saidai zuciyarta cikeda fargaban abinda zai biyo baya dan ita bazata taɓa yarda wani abu ya shiga tsakaninsu ba tunda ba yanzu zata tare ba. Har sukaje part ɗinsa bai jiyo ya kalleta ba,, suna shiga ta zauna kan kujerar dake palourn. Wani wulakantaccen kallo yayi mata sannan ya nufi ɗakinsa cikeda takaici dan shi bai saba kwana da wani a part ɗinsa ba. "Wane daki zan kwanta" ta tambaye shi tana miƙewa kanta a kasa. Cak ya tsaya sannan ya juyo yafara takowa inda take,,,,, gab da ita ya tsaya har suna jiyo numfashin juna, Jikin jiddah har rawa yakeyi dan ta tsorata sosai,, "Ki kwanta duk a inda kika ga dama saidai karki sake zomin ɗaki na dan naga alamar kinyi sabo da kwana da maza sosai".. Jiddah shiru tayi batace komaiba sai tarin bakin ciki dayasa takasa yin magana. Tsaki yayi sannan yabara palourn ya nufi ɗakin sa batareda ya sake jiyowa ba. Jiki babu Kwari ta nufi ɗakin dake gefen nasa,, bata sha wahalar guarashi ba dan baiyi wani datti ba sannan ta kwanta tareda share hawayen da suka zubo mata na bakin ciki.... Da sassafe tagama shirinta tsaff ta fito zuwa wajan mommy shima dai dai fitowar shi yana waya da Sultan kan maganar tafiyar su. Hararar ta yayi ya kawar da fuska gefe,,, hartayi hanyar fita yace keeee. Bata juyo ba saidai ta tsaya a inda take. Yana karasowa ya wuce ya barta,, bin bayanshi tayi danta gane me yake nufi wato su jera tare.. Mommy taji dadin ganinsu tare sosai saidai ta fahimci babu abinda ya faru tsakaninsu bata so hakan ba dan so tayi da kanshi yafasa tafiya kamar yadda ya kudurta... *🌹FIRSTLADY CE*✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 _*DR. HABIBULLAH*_ ɳɑ *🌹ᴀᴍʀᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛʟᴀᴅʏ🌹* ⓒ ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wαttpαd* @Ameenafirstladyy *🌈Kᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀs ᴀssᴏᴄɪᴀᴏɴ* 20 Tare sukayi breakfast sannan Habib ya fice yabar gidan gaba daya.. A ranar hibban da Afnan a gidan suka wuni Gwanin sha'awa jiddah take kallan su abin har birgeta yayi suna kula da junansu sosai. Sai yamma sannan mommy tace suzo su tafi gida kar dare yayi musu duk da a kusa suke. Lokacin jiddah da Afnan suna tsohon dakin jiddah suna hira a tsakanin su. Hibban ne ya shigo yana faɗin "dear tashi mu wuce ita wannan a gida take"! Ya kalli jiddah yana mata dariya. Hararan wasa jiddah tayi masa tace "haba yaya hibban tun yanzu zaku tafi" "Eh mana ko so kike wancan mijin naki ya dawo ya fara hade mana fuska.." "A'a ba haka nake nufi ba" tayi saurin kawar da zancen. Tare suka fita su duka suka yiwa mommy sallama sannan jiddah ta raka su,,, suna fita motar Habib na shigowa. Baiyi mamakin ganinta a wajan ba,, yana gama Parking ya fito ba yabo ba fallasa,,. Har fara tafiya taji yace "meya fito dake yanzu ko baki kula mai Gadi na Compound din ba"? "Su yaya hibban na rako suka tafi" "Saboda basusan hanya ba ko"..? Ya sake tambayar ta.. Shiru tayi dan bata da amsar bashi. Tsaki yayi sannan ya wuce gaba tana bayansa cikeda takaicin wannan isar. Tare suka shigo palourn mommy na zaune taga shigowar su. "Ina kaje Habib"? "Naje wajan Sultan ne akan tafiyar mu"! "Yaushe ne tafiyar"? Mommy ta sake tambaya. "Jibi ne inshallahu" Mommy Bata sake cewa komaiba. Tashi hibban yayi yana yiwa mommy saida safe ya fice bai jira jiddah ba,,, Har zata tafi mommy ta tsayar da ita sannan ta nufi ɗakin ta... Wani turare mai shegen ƙamshi mommy ta shafa mata sannan ta bata ragowar sannan tace ta dauki flask din coffee shi ta tafi mai dashi. Ita kanta jiddah turaren ya birgeta sosai batayi musu ba ta ɗauka ta fice zuwa nasu part din,,. Ta daɗe a tsaye bakin kofar shi,, shahada tayi sannan ta tura kofar dakin ta shiga da sallama. A hankali Habib ya lumshe idanuwanshi jin ƙamshin turaren lokaci guda yaji wani irin yanayi tare dashi,,. Buɗe idanuwan shi yayi kamar mai jin bacci sannan ya tashi yana kare mata kallo da sexy eyes ɗinsa da suka fara canja launi. "Yaya Habib ga coffeen..." Kasa karawa tayi ganin yayo kanta fuska a haɗe. "Ficemin a ɗaki" yace yana nuna mata hanyar fitar. "Kabari na zuba.." Wani dogon tsaki yaja wanda baima san ya iya shi ba ganin tana niyyar tasa ya zubar da ajinsa yanzu. "Bana bukata,, kin saba kai kanki shine yau nima kika kawo kanki gare kina tunanin zan yadda""""! Ya karasa yana sakin wani shu'umin murmushi. "To ba haka nake ba, Dr Habibullah yafi karfin haɗa jiki dake saboda haka ki ficemin before I open my eyes" Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa jiddah wanda bata taɓa jin irin suba dan yauce rana ta farko da aka taba ci mata mutumci kamar haka. Jiki babu kwari ta fice ta shiga dakinta ta faɗa saman gado tare da sakin wani marayan kuka. Habib kuwa tana fita ya rufe ɗakinsa sannan ya koma saman bed ɗinsa yana wani irin huci dan wani zazzaɓi ne ya rufe shi lokaci guda,, saida yasha magani sannan wani bacci ya dauke shi mai daɗi.. Jiddah kuwa dakyar bacci ya sace ta dan bakaramin kuka tayi ba ta dade tana zubar da kukan bakin ciki. Da asuba ta tashi tayi sallah, sannan ta koma ta kwanta dan tashi tayi da ciwan kai sosai ga fuskar ta tayi ja idanuwan ta nuna alamun tasha kuka shiyasa taki zuwa Wajan mommy Dan Karta gane abinda ya faru.. Habib kuwa bayan yayi sallar asuba shima bacci ya koma sai kusan 11:39 sannan ya nufi part din mommy su gaisa.. Mamaki yagama kama mommy jinsu shiru saidai tana fatan abinda take tunani ne ya faru hakan yasa ta basar bata nemesu ba. Jin sallamar Habib ne yasa mommy juyowa,, saida ta amsa gaisuwar shi sannan tace "ina jiddan take kuma"? Cikeda mamaki yace "batazo nan ba"? "Banasan iskanci Habib ya ina tambayar ka kana mayar min da tambaya idan batada lafiya ne saika sanar min ai" Shiru yayi dan sai yanzu ya tuna rabuwar su a jiya Allah yasa dai ba wani abu bane ya sameta dan yasan ya shiga Uku wajan mommy.. Jin shiru bai amsa mata bane yasa tace "Habib ba daki daya kuke kwana bane da zakace bakasan halin da take ciki ba"? Da sauri yace "a'a mommy na tashi naga bata dakin ne nayi tunanin nan tazo, sai yanzu na tuna ashe tace yau ita zata hada mana breakfast inaga tana kichine ne".. ya shararo mata karya wadda baisan ma ya iya ta ba sai yau data kama dole.. (O su Habibullah Allah ya shirya an fara karya kuma🤔🤔) Kallan shi mommy tayi kamar maisan gano karya yayi sai kuma tace "shikenan naji, saika koma can kuyi tare ai" "To momma" ya faɗa yana fice tareda sakin wani ajiyar zuciya ganin karyar shi ta amsu.. Kai tsaye motarshi ya hau ya fice daga gidan batareda wani tunani ba. Sai rana sosai jiddah ta tashi cikin wani irin yanayi ga yunwa ga zazzaɓi gashi bazata iya zuwa wajan mommy ba Dan ko gani batayi sosai tsabar yunwa da zazzabin. Da kyar ta iya tashi ta shiga bathroom tayi wanka tadan ji kwarin jikinta sannan ta fito palourn tana tafiya dakyar. Ganin kofar dakin sa a rufe yasa tagane baya nan kenan. Kichine ɗinsa ta shiga ta dade a tsaye tana tunanin mezata dafa. Ji tayi komai ya fice mata a rai sai ruwan Lipton kawai tasha ta koma ɗakinta ta kwanta hawaye na sake zubo mata... Mommy Bata kawo komai a ranta ba tayi tunanin suna tare shiyasa ko kiran jiddah batayi ba, saidai lokaci zuwa lokaci takan yi murmushin irin halin Habib..... Har bayan la'asar jiddah na kwance da kyar take iya tashi tayi sallah sai yanzu take dana sanin amincewa da auran Habib da tayi,, duk lokacin data tuna kalaman da yayi mata wasu hawaye ne ke zubo mata,, amma tana mamakin abinda yasa mommy bata neme ta kodai yaje ya shirya wa mommy wata maganar matanar ne... Tana nan kwance zuwa lokacin duk tagama galabaita ga wayarta ta mutu ko mommy ta kirata bazata sameta ba. Da kyar ta iya tashi ta dauki wayar tasa a caji sannan ta koma ta kwanta. Mommy abin harya fara bata tsoro wayarta ta dauko ta kira layin jiddah amma switch off, wayar Habib kuma busy, hakan yasa mommy ba shiri ta nufi part ɗinsu danta ga lafiyan jiddan. Palour babu kowa kuma wajan tsit, dakin Habib ta shiga nan ma babu kowa hakan yasa ta nufi ɗakin kusa dashi. Kwance ta hango jiddah cikin bargo, da sauri ta karasa tana fadin "jiddah lafiya kuwa." Ta faɗa tana yaye blanket din. Cikeda tsoro mommy ta ɗago jikinta taji jikin zafi,, "Jiddah meya same ki"? "Zazzabi ne mommy da ciwan kai" Da sauri mommy tace "Ina Habib din kuma meyasa bai fadamin ba" "Nima bansan inda yaje ba tun jiya ban sake ganinsa ba" Mommy Bata sake cewa komaiba ta tashi jiddah ta kaita bathroom sannan ta ta fice kichine ta hadi mata tea mai kauri da jellof ɗin taliya da taji kifi. Jiddah na fitowa ta shiga sannan mommy ta Bata tea Tasha sosai. Saida ta tabbatar tea din tsirga mata sannan tasa ta taci abinci sosai.. Cikin kankanin lokaci zazzaɓin da ciwan kan suka gudu jiddah taji dadin jikin saidai babu kwari sosai. Ran mommy yayi matukar ɓaci danta fahimci babu abinda ya shiga tsakaninsu Ashe Habib karya yayi mata kenan. Jiddah dake kwance mommy ta kalla cikeda tausayi tace "jiddah zan tambaye ki ki fadamin gaskiya kuma banasan kiji kunya ta" "To momma" "Kun taba haɗa daki da Habib"? Cikeda kunya jiddah tayi ƙasa dakai tare girgiza kai alamar a'a. Ran mommy ya sake baci Amma Bata nuna ba sai hakuri taba jiddah sannan tace ta kwanta kafin a kira magrib. Kwanciya tayi mommy ta fice zuwa part ɗinta Rai a bace.. Saida Habib ya gama shirin tafiyar sa gobe sannan yayo hanyar gida bayan yayi sallar magrib a hanya.. mommy saida tayi sallah sannan takira Habib cikin Sa'a ta sameshi. "Kana ina Habib"? Yadda yaji Muryar mommy ne yasa gabansa faduwa dan babu shakka yasan tagano karya yayi mata. "Ina kan hanyar gida" "Shikenan ina jiran ka" mommy tace tana yanke wayarta.. Ana kiraye kirayen isha ya shigo anguwar tasu,, saida yayi Sallah a masallacin anguwar sannan ya shiga cikin gidan. Kai tsaye part din mommy ya wuce,, a zaune ya same ta a palour, ita kadai ce babu jiddah yadda ta amsa masa sallamar ne yaji gabansa ya sake faduwa. Zama yayi sannan yace yayi mata ya gida,, banza tayi dashi bata amsa ba. Saida suka dauki lokaci sannan mommy ta fara yi masa cikin faɗa faɗa. "Habib meyasa kayi min karya ɗazu"? Shiru yayi yakasa cewa komai. "Dama nasan ai bazaka iya bani amsa ba,, to kasani koma me kayiwa yarinyar nan Allah bazai Barka ba kodan maraicin ta sannan kaida Allah daka kasa sauke hakkin ta dake kanka bazan sake yi maka magana akan haka ba tunda kaima kasan zunubin hakan".. Mamaki ne da tsabar takaici wato jiddah rashin kunyar tata harya kai ta fadawa mommy bai taɓa kusantarta ba. "Tashi ka bani wuri shashasha kawai" Mommy ta faɗa cikeda bacin rai. Hakuri Habib yabata sosai da kyar ta hakura bayan ya tabbatar mata da zai gyara inshallahu sannan yayi mata sallama ya fice. Ran Habib yayi matukar ɓaci akan jiddah dan saida yasan ta sannan mommy tafara yi masa faɗa a rayuwarsa kuma ta dalilita dole ya nuna mata kuskuren ta kuma yau zataga karshen rashin kunya kuwa... Ya faɗa a ransa yana shiga palourn.. Palourn babu kowa hakan yasa ya shiga ɗakinsa ya faɗa wanka. Ya dade sannan ya fito ya shirya cikeda bacin rai ya nufi ɗakinta. Jiddah na zaune kan capet ta idar da sallam taji anbugo kofar dakin ta. A firgice ta ɗago tana kallan Habib daya haɗe fuska idanuwan nan nashi sun kankance cikin bacin rai. Da sauri ta tashi a tsorace ganin yana matso kusa da Ita. "Yaya Habib dan Allah kayi hakuri.." Wani Banzan kallo yayi mata sannan yaja tsaki "ni zaki haɗa da mommy ko wato har kinsan ki faɗa mata magana ko". Jikin jiddah ne yafara rawa dan sai yanzu ta fahimci abinda yake nufi tuni tafara bashi hakuri wanda shi ko kadan kukanta da hakurin datake bashi kamar Dada tunzura shi takeyi. "Dan Allah kayi hakuri bazan sake faɗa mata ba" Taɓe baki yayi sannan ya make kafada alamun bai dameshi ba. Zata sake magana taji ya fizgo ta cikin mugunta ya haɗe fuskar su waje daya,, "yau zaki sha mamaki na" Kafin tace wani abu tuni ya haɗe bakinsu waje ɗaya.. Yadda yake aika mata da zafafan kisses ne yasa jiddah tafara hawaye tana neman kwatar kanta. Shikam Habib hankalin shi gaba daya baya tareda jikinsa dan har rawa jikinsa keyi,,. Jiddah tun tana hawaye harta fara kuka sosai kamar ranta zai fita saidai ina cikin fitar hayyaci Habib yabi mata ta karfin tsiya wanda yasa jiddah sakin wata kara tareda sumewar azaba... Sam Habib baisan meya aikata ba dan yana gamawa ya mirgina gefe yana fitar da numfashi ga wani zazzaɓi mai zafi daya rufe shi,,. Dakyar ya tattaro sauran karfin da yake dashi ya shiga bathroom ɗinta,, jikinsa shima babu kwari ga wani irin yanayi dayake ji a jikin nashi yayi wanka ya fito,, lokacin aka fara kiran sallar asuba... Sai yanzu Habib ya kalli irin barnar da yayi gabansa ne ya fadi kanshi ya kulle ga zazzaɓi yasa jikinsa duk yayi sanyi,, Yana cikin kallan kyakkyawar fuskar ta dayake ganin sai yau yayi mata kallan tsaff, gani yayi tana motsa ido da sauri yayi kanta. A hankali ta buɗe ido tana ganinsa ta saki wata kara mai karfi dayasa Habib saurin toshe kunne tareda dafe bango dan bai taɓa jin kara haka ba. Kamar taga dodo haka tafara kokarin motsa jiki saidai ina jikinta duk ciwo yake mata ga wata irin azaba da taji ta kasanta wanda yasa ta saurin rintse ido tana cigaba da kukan. Habib kuwa tunda yaji ihun nan kanshi yafara wani azababben ciwo tareda sara mai da sauri da sauri,,, jan ƙafarsa yayi yana rike dakai ya fice yabar dakin ya shiga ɗakinsa ya faɗa saman bed... Jiddah kuwa batasan fitar shiba saboda numfashin tane yafara kokarin daukewa dakyar take janyo shi ta samu ta dauki wayarta ta danna layin mommy saidai kafin a ɗaga numfashin ta ya[1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ɳɑ *🌹ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛʟᴀᴅʏʏ🌹* ⓒ ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wɑttpɑɗ* @ᴀmєєnαfírѕtlαdчч *🌈ᴋᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀs ᴀssᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ*🤝🏻 21 Mommy na zaune kan capet taji karar wayarta, cikeda mamaki ta janyo wayar tata dake saman bed,,. Gabanta ne ya fadi ganin number jiddah da sauri ta danna layin ta kira saida harta katse ba'a daga ba,, hakan yasa mommy ta nufi part ɗin nasu cikeda fargaba.... Kai tsaye dakin jiddah mommy na nufa,, tana tura kofar dakin ta saki salati tareda faduwar gaba ganin halin da jiddah take ciki. Da hanzari ta karasa jikin gadon tana girgiza jiddah saidai ina ko numfashi batayi cikin kidima mommy ta kama jiddah batare da bata lokaci suka fice daga part din.. Da kanta tayi driving zuwa hospital duk garin bai gama waye ba amma sun samu doctors kasancewar private,, emergency room aka wuce da ita kai tsaye tareda Dr Ahmad wanda ya tsayar da mommy yana ta kwantar da hankalin ta... Cikeda tashin hankali mommy take Kai kawo tarasa wanne tunani Yakamata tayi,,, sai zuwa can sannan ta kira layin hibban. "Ka sameni a hospital din Dr Ahmad" tana gama faɗin haka ta kashe wayar.. Shima Hibban cikin tashin hankali ya nufo hospital tareda fargaba fal zuciyarshi.. Abu kamar wasa saiga shi likitocin sun dade cikin emergency room din, babu wanda bai tausayawa jiddah ba musamman Dr Ahmad dayasan wacece ita kuma babu shakka yasan aikin Habib ne tunda yanada labarin komai saidai yaji takaici da tausayin ta musamman dayasa yarintar ta. Kusan 2hrs suka kwashe sannan suka fito daga ɗakin, kallo daya Dr Ahmad yayi musu yaji tausayin su dan kana ganin mommy kasan bata cikin yanayi mai daɗi. Mommy na ganin shi tayi kanshi "meya faru da ita Ahmad" "Calm down mommy, ku same ni a office sainayi muku bayani" ya faɗa yana barin Wajan zuwa office ɗinsa. Zaune sukayi mommy kanta na ƙasa tana jiran bayani daga bakin Dr Ahmad. Saida yayi gyaran Murya sannan yace "karki damu mommy jiddah zata tashi saidai tana bukatar hutu yanzu dan doguwar suna tayi zata jima bata farfaɗo ba..." "Meya sameta Kawai nake san ji" mommy ta sake maimaita tambaya. Shiru ya danyi saboda yadda ya tuna abinda Habib yayi mata "kiyi hakuri mommy nasan jiddah tanada aure sanin haka ne yasa ban nuna damuwata sosaiba,, saidai Habib yabi mata ta karfi ta yadda har saida takai ga munyi mata dinki amma karki damu zata tashi nrml.." Rintse ido mommy tayi cikin bacin rai da tashin hankali sam kasa magana tayi sai zuciyarta datayi mata zafi. Dr Ahmad ne ya kalli hibban da yake tsaye fuskar shi ta nuna tsantsan dimuwa yace "hibban zan rubuta maka magunguna sai aje a siya, sannan ba'a bukatar bata abinci mai nauyi sai bayan 1week".. Daga kai kawai hibban yayi mommy kuwa tashi tayi jiki a sanyaye ta fice zuwa dakin da aka kwantar da jiddah.. Habib sai 11am ya tashi cikin wani irin yanayi na kasala,, a hankali ya buɗe idanuwan shi tareda saurin tashi yana dafe kai da har yanzu yake masa ciwo, cikin hanzari ya shiga dakinta saidai babu alamar ta a dakin har bathroom,, shikenan yasan mommy zuwa Yanzu tasan komai dan yasan waccan yarinyar ta faɗa mata Yanzu. Cikin dakewar zuciya ya nufi part din mommy bayan ya gyara dakin nata tsaff daya ɓaci har bed din saida ya sauya sannan ya fice,,,. Cikeda mamaki ya fito daga part din mommy ya nufi gateman yana tambayar koyaga fitarsu. "Eh yallabai sun fita cikin sauri zuwa asibiti" Da sauri ya maimaita kalmar asibiti kuma? "Eh jiddah ce babu lafiya da alamu ma baya cikin hayyacin ta lokacin..." Bai karasa jin abinda yake cewa ba yabar wajan yana kiran hibban. Lokacin hibban shigowar shi kenan dakin da jiddah take, mommy Zaune ta zubawa jiddah Ido saidai kana ganinta kasan ranta a matukar bace yake,,. Cikin taushin Murya hibban yafara lallabar mommy "pls mommy karki sa kanki a damuwa kinfi kowa sanin halin yaya Habib yanada saurin fushi may be ta ɗanyi masa laifi ne shiyasa ya rama ta haka...." Wayar shi ce tayi kara hakan yasa ya ciro ta daga aljihu yana dubawa. Kallan mommy yayi yaga hankalin ta baya wajan da sauri ya fice yana daga wayar. "Hello yay..." "Kuna ina" Habib ya katse shi da tambayar inda suke. Cikin in Ina yace suna Ahmad City clinic. Batareda ya sake jin wata magana ba ya kashe kiran,,. Hibban kuwa shiru yayi duk da baiji dadin abinda yayan nashi yayi ba saidai babu yadda zaiyi ya nuna hakan,,. Dakin ya koma yace "mommy Afnan zata zo yanzu da abinci". Dakyar mommy tace "to Allah ya kawota Lafiya, saika je ka taho da ita dan bai kamata tahau motar haya yanzu ba" "To momma" ya faɗa yana ficewa daga ɗakin.. Yana fita jiddah tafara buɗe idanuwan ta a hankali tareda zubar hawaye Masu zafi,, da sauri mommy tayo kanta tana jera mata sannu. Itama jiddah tashi tayi niyyar saidai wata irin azaba da taji ta kasanta yasa tayi wata kara tareda saurin komawa ta kwanta tana rinste ido cikin azaba. "Sannu jiddah bari na kira doctor" mommy tace tana ficewa. Habib kuwa motarshi ya hau kai tsaye ya nufi hospital din,Parking yayi sannan ya nufi ɗakin da hibban ya faɗa masa kai tsaye.. A hankali ya tura kofar dakin,, ita ƙadaice a dakin idanuwanta a rufe sam batayi tunanin Habib bane tayi tunanin mommy ce ta dawo dakin.. Kyam Habib ya tsaya yana kare mata kallo tun daga bakin kofa har jikin gadon. Ƙamshin turaren shine yasa jiddah bude fuska a razane tareda kokarin tashi duk irin azabar da take ji. Shikam Habib kallanta yakeyi cikeda mugunta dan da alamar yayi mata hankali kenan. Matsowa yayi saitin fuskar ta kamar zaiyi manna mata kiss. Cikin wani wahalallan kuka jiddah tafara bashi hakuri tana juya fuskar ta gefe. Murmushin mugunta yayi sannan yasa hannu yana juyo da kanta saitin shi. "Ina fatan Yanzu kin gane waye Habib" Shiru tayi tana kokarin kwace kanta saidai bakaramin riko yayiwa kan nata ba. "Ok Bikiyi hankali ba kenan kokuma kin manta, bari na tuna miki.." ya faɗa yana kokarin yaye bargon dake jikinta. Wani ihu tayi wanda yasa Habib saurin toshe kunne tareda rinste ido, dai dai shigowar mommy. Cikin tsananin mamaki take kallansa duk da halin da yake ciki baisa mommy ta raga masa tace "Habib Wannan wanne irin iskanci ne zaka biyo ta har asibiti ka ƙarasa kashe ta wato Burin ka bai cika ba Kenan,, toka ficemin daga gani yanzu kuma jiddah ce tunda bakaso saika sauwake mata ta nemi wanda takeso yake santa" Dumm yaji maganar duk da baya cikin hayyacin sa sosai saidai yaji Maganar tamkar saukar aradu, a kidime ya tashi yana rintse ido dan wata irin juya yaji na ɗaukar. Har zaiyi magana mommy ta dakatar dashi tana fadin ya fice mata kafin ransa yayi mummunan ɓaci. Kallan jiddah yayi wacce ke kuka haikan kamar wacce za'a zarewa rai duk ta fita hayyacin ta. Tsawar da mommy ta sake daka masa ne yasa yayi saurin ficewa daga ɗakin yana layi tareda dake kanshi,. Da sauri Dr Ahmad ya karaso yana saurin taro shi ganin zai fadi tareda kiran nurse.. Kai tsaye ya basu umarni dasu dauko gadon marasa lafiya aka tura Habib zuwa dakin gaggawa. Babu bata lokaci Dr Ahmad yabashi taimakon gaggawa cikin kankanin lokaci Habib ya wuce baccin wahala.. 1 dai dai Habib ya bude ido yana kallan dakin tareda tuna kalaman mommy ta kukan da jiddah keyi, wani zafi yaji a zuciyarshi tareda sarawa da kanshi yayi. Dr Ahmad ne ya shigo dakin yana tambayar ya jin nashi, da sauki kawai yace batareda ya sake cewa komaiba. "Habib zaka jawa kanka wata matsala wacce ba lallai bane ka iya magance ta,, kasani na sani wannan cutar taka bata bukatar hargitsi ko yaya yake kuma kasani zuciyarka na kamuwa da mummunan ciwo wanda zai iya sanadiyyar rayuwar ka, meyasa bazaka yiwa kanka faɗa ba". Kiran wayar shine yasa bai yiwa Dr Ahmad magana ba ya daga kiran ganin Sultan ne. Basu dade suna wayaba ya ajiye yana kallan Dr Ahmad. "Shikenan zan kiyaye" ya faɗa yana tashi. Sosai Dr Ahmad daya kasance abokinsa ne ya bashi shawarwari sannan ya fice dan lokaci Flight ɗinsu ya kusa. Mommy kuwa tunda Habib ya fita ta dawo kan jiddah tana lallashinta dakyar jiddah tayi shiru saidai bata sake magana ba, sai ajiyar zuciya. "Kiyi hakuri jiddah bazai sake yi miki komaiba saida amincewar ki zaki sake zama dashi.." "Wlhy mommy Yaya Habib kashe Ni zaiyi indai na sake zama dashi baya sona baya kaunata bazan iya cigaba da zama dashi ba gara na zauna tareda ko auran ma bazan sake yiba" jiddah ta faɗa cikin zafin ciwo. "Naji jiddah babu mai sake yi miki dole". Hibban da Afnan ne suka shigo duk sun tausaya mata dan harta dan faɗa na rama, dakyar aka samu tasha tea sannan tasha maganinta. Bacci ne mai nauyi ya dauke ta batasan inda kanta yakeba. Cikin karfin hali Habib ya shigo dakin, mommy na ganinsa ta haɗe fuska. Hibban da Afnan kallansu kawai yayi suka fice daga ɗakin, sannan ya dawo kansa wajan mommy. "Mommy zan tafi amma..." "Naji Allah ya kiyaye hanya, bana bukatar wata magana kuma jiddah ce dai bakaso kuma na amince sai ka aiko mata da takardar ta shikenan burinka ya cika" A hankali ya dago kanshi yace "pls mommy Dan Allah kiyi hakuri".. Katse ta sakeyi da cewa "na hakura Habib saidai bada wannan maganar ba kuma banaso ka sake furta wata kalma" Bai sake magana ba ya tashi zai fice sannan ya sake jiyowa yana kallan jiddah dake sauke numfashi a hankali cikin wahala. Ganin kallan da mommy tayi masa ne yasa yayi saurin ficewa daga ɗakin.. Ko kallan inda su hibban baiyi ba ya wuce ya fita. Kai tsaye gida ya wuce ya shirya zuciyarshi fes baisan Dalili ba saidai da zarar ya tuna maganar mommy saiyaji gabanshi ya fadi,, a haka ya shirya cikin yadi sky blue Wanda ya amshi fatar jikin shi yayi masifar kyau ga wani annuri dake fita akan fuskar shi wanda bansan dalilin wannan annuri ba. (Readers ko kun sani?🤔) A haka ya fice cikin takama da izza kamar bashida wata matsala dan wasai yake jinsa, har yaje airport ya samu Sultan a can. 3 dai dai jirginsu Habibullah ya daga zuwa Russia dan karo karatu a bangaren mata.... Sultan da Angelina suna lure dashi lokaci zuwa lokaci yake murmusawa da alamu murmushin gaske yakeyi yau bana mugunta ba. Sultan ne ya kalle shi yace "Mutumi na yadai yai naganka kamar kana cikin farin ciki" Wani tsadaddan murmushi ya sakeyi har kyawawan fararan haƙoransa suka baiyana sannan ya motsa dan karamin bakinsa pink color yace "Sultan nima bansan dalili ba" ya faɗa yana shafa kyakkyawan sajensa tareda sake murmushi tuna irin shagwabar jiddah tareda magiyar da takeyi masa a daran jiya sai kuma a yadda ya baro tana bacci tana sauke numfashi a hankali fuskar nan tata fayau,, a hankali ya lumshe idanuwanshi yana jin wani irin abu a zuciyarsa karo na farko game da jiddah... Waiting New page✍🏻 ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛʟᴀᴅʏ [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 nα *🌹ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛʟᴀᴅʏ*🌹 ⓒ ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wɑttpɑɗ* @ᴀᴍᴇᴇɴᴀғɪʀsᴛʟᴀᴅʏʏ ____________________________ *🌈ᴋᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀs ᴀssᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation ____________________________ ( *_Kuyimin afwa kwana biyu zaku jini shiru hakan ya faru ne dalilin uzuri danake dashi zanci gabada typing da zarar komai ya kammala na gode da kulawarku sosai_*) 22 ...... jiddah kuwa sai yamma ta tashi duk da har lokacin jikinta babu kwari amma taji dadin jikin sosai. Mommy ce ta haɗa mata tea mai kauri kamar yadda Dr Ahmad yace da kyar aka samu tasha kaɗan dan bakinta babu taste sosai,,,, hibban da Afnan ma sai yamma mommy tace ya kamata su tafi kar dare yayi suma zuwa safiya za'a sallame su. Haka suka tafi cikeda tausayinta "gaskiya dear Yaya Habib baiyiwa jiddah adalci ba sam" Hararan wasa hibban yayiwa Afnan yace "to ba matarsa bace koma me yayi mata ai babu wani abu" "Duk da haka dai yayi rashin tausayi". Murmushi kawai hibban yayi dan shima yasan gaskiya ta faɗa yaya Habib baiyi mata adalci ba gashi nan yanzu yaja mata kwanciya a asibiti. Jiddah kuwa tunda ta farka tasha tea Bata sake magana ba dan batajin zata iya surutu a yanayin da take ciki., Lokaci zuwa lokaci dai takanyi hawayen baƙin ciki sai mommy ce kawai ke bata hakuri, a haka Dr Ahmad ya shigo dakin. "Mommy zan wuce gida akwai wani abinda kuke buƙata"? "A'a Ahmad mungode sosai" Shiru yayi yana maida kansa kan jiddah dake kwance "ki lura wajan motsi da tashi saboda gudun matsala" Daga kai kawai tayi dan haushi ma ya bata da maganar tasa. Mommy ce tace shikenan zata kula ai. Sallama yayi musu sannan ya tafi dan sai zuwa gobe zai sallame su. Ko kaka jiddah tayi kyakkyawan motsi saita yi kuka sosai mommy kaɗai ke lallashin ta, har dare bata sake cin komaiba. ʀᴜssɪᴀ:- ᴍᴏsᴄᴏᴡ ᴄɪᴛʏ Azimut hotel. Fitowar shi Kenan daga hadaddan bathroom ɗinsa Yana tsane ruwan daya kwanta jikin kyakkyawar fatar shi, tsaki yayi yana matsawa jikin wani dan karamin table na glass, tafkekiyar wayarshi ya dauka tareda karawa a kunnen shi. "Sultan ina san contact din shugaban makarantar yanzu" Daga can ɓangaran Sultan yace "shikenan zan Turo maka amma kafara duba makarantar idan tayi maka" "Ok" Kawai yace yana kashe wayarshi. Kai tsaye wardrobe ya nufa ya shirya cikin ƙananan kaya wanda suka amshe shi tsaff ya feshe jikinsa da turare mai sanyin ƙamshi. Laptop ɗinsa ya janyo ya yafara binciken makarantar babu bata lokaci yayi apply a RUDN University of Moscow. Bai tashi ba saida ya kammala komai sannan ya tashi ya kira Sultan yace ya gama komai baya bukatar imel address din. "Shikenan dama nasan zata birge ka ai, saika dage nima yanzu na dauki hutu ne saboda Angelina batada lafiya" Habib kashe wayarshi yayi danya gaji dajin fadi ba'a tambaye kaba irin na Sultan. Kwanciya yayi a saman bed ɗinsa yana lumshe ido, ya dauki lokaci kafin ya saki wani kayataccen murmushi yana tashi tareda lalubo wayarshi. Wayar mommy ya Kira saida ta kusa katsewa sannan ta daga Muryar ta babu yabo ba fallasa. Lokacin jiddah na zaune ta jingina da pillow,, tunda taga mommy ta daga waya babu fara'a ta mayar da hankalnta kan mommy. "Mommy barka da dare" Habib yace. "Ka sauka lafiya ko"? Mommy bta Tambaye shi. "Eh mommy alhammdlilh" "Masha Allah, saika dage da abinda kaje yi" Shiru yayi baice komai ba, so yake ya tambayi ya jikin jiddah amma yarasa tayaya zaiyi tambayar. "Akwai wani abu ne kuma" "Ya jikin nata" ya faɗa batareda yayi wani dogon nazari ba. "Da sauki,"! Kawai mommy tace. Sallama yayiwa mommy ganin yadda take bashi amsa yasan har yanzu tana kan bakanta wanda yakejin bazai iya yiyuwa a yanzu yadda yake jinsa. Jiddah kuwa sarai tasan dawa mommy take waya amma saitayi fuska kawai. A hankali Habib ya ajiye wayar yana wani yamitsa fuska na takaici, daya sani ma bai kira ba Balle ranshi ya ɓaci. A haka ya tashi ya fice daga wajan nashi ya shiga Motarshi yaja ta yabar hotel din Gaba ɗaya... Kamar yadda Dr Ahmad yace da sassafe ya basu sallama yace zai dinga zuwa yana ganin yanayin jikin nata saidai a dage da bata magungunan ta sannan banda ɗaukar abu mai nauyi ko tsalle ko gudu har sai bayan 2weeks,, abinci kuma kar taci mai nauyi sai 1week. Mommy ce ta amsa sannan hibban ya dauke su ya mayar dasu gida. Dakinta na da ta koma abinta hankali kwance. Tun daga lokacin jiddah bata sake damuwa ba musanman dataji mommy na yawan yiwa Habib maganar sakinta. Sosai takeso ta koma makaranta saidai takasa yiwa mommy Maganar,. Yau tana dakin mommy Habib ya kira,. Saida suka gama gaisawa sannan mommy tace "Habib Wai meyasa kake daukan magana ta mara amfani ne, sau nawa zance ka sauwake wa jiddah tayi iddah dan ta samu miji tayi aure wanda yake santa" Habib da kanshi yayi masa nauyi sosai ya rintse ido yanajin wani zafi a cikinsu, da kyar ya iya motsa bakinsa yace "I'm sorry momma" "Sorry for what"? Ta Tambaye cikin fada fada. "Kenan bazaka iya sakin nata ba kome"? "A'a mommy" "To Ina jiranka dan bazata ci-gaba da zama haka kawai ba" Bai sake cin ba mommy harta gama fadan ta ta kashe wayar. Ji yayi yarasa dalilin da yasa yake jin bazai iya sakin jiddah ba to akan me zai sake ma bayan yasan koya rabu da ita wani zataje ta aura ina never and impossible Ya faɗa a fili.. Jiddah kuwa yanzu abin yafara damunta kusan 3weeks kenan amma mommy ta hanata fita ko ina gashi tanasan zuwa gidan hibban wajan Aminiyarta sau kusan shida suna zuwa amma mommy ta hanata zuwa yau kuma gashi har khairat zataje susha hirar su sai Kiranta suke suna tazo. Da karfin guiwa ta shiga dakin mommy,. "Mommy pls kubarni naje gidan yaya hibban yau" Shiru mommy tayi mata bata kulata ba, cikin shagwaba jiddah tai aniyar fara kuka dan tasan mommy hakan ce kadai zaisa ta kulata. Cikin sigar lallashi mommy ta jawo ta jikinta tafara bata hakuri. "Banida ikon barinki ki fita jiddah saboda har yanzu kin karkashin ikon Habib ne, gashi kwana biyu baya kira saboda nayi masa maganar rabuwar ku, indai kinsan fita saiki kirashi da kanki ki tambaye shi.." A dan tsorace ta ɗago kai tace "wlhy mommy idan na kira shi nashiga uku" Tsaki mommy tayi tana barin Wajan "saiki ta zama ai, ashe bakya san Zuwan"... Ta fice daga ɗakin.. Zaune yake daga shi sai singlet fara tas sai trouser, gashin jikin shi kwance luf, wasu takardu kawai yake dubawa saidai hankalin shi sam baya kan takardun yana kan maganar mommy,, Dan tsaki yayi yana tashi cikeda jin haushin kansa "meyasa ma nakasa control ɗin kaina a waccan ranar?" Ya tambayi kanshi tsaki ya sakeyi sannan ya bar palourn zuwa ɗakinsa... Jiddah kuwa ganin babu sarki sai Allah tasan mommy bazata taɓa barinta ta fitaba, dole ta dauki wayarta ta fara neman layinsa cikeda da tsoron yadda zasuyi dashi, duk yanzu batajin zata dauki wani wulakancin shi tunda ba sake zama zasuyi a matsayin mata da miji ba. 2times tana kira amma babu answer, tsaki tayi tana sake kiran wayar tashi. Fitowar shi kenan palourn, ya dauki wayar yana kallan numban cikeda tsantsan mamaki. "Tome ta kira tace min, kodai mommy ce tasa ta" Katse kiran yayi sannan shiya kirata,. Jiddah hatta ji haushi sai kuma taga kiran shi. Tayi mamaki ganin katsewa yayi danya kirata, sannan ta daga dauke da sallama a bakinta. Dan rintse ido yayi yadda yaji sautin Muryar Tata har cikin zuciyarshi. Jin bai amsa mata yasa jiddah ta taɓe baki "zan fita ne mommy tace a Kira na sanar maka"? Ta fada kai tsaye. Yaji haushin yadda tayi masa magana batareda wani tunani ba yace "haka ake tambayar miji fita"!? Dumm taji kalmar datasa takasa cewa komai cikeda mamaki shaidai wannan ba'a gane gabansa da bayansa kam. "Idan kin koyo Yadda ake tambayar miji fita saiki kirani" ya katse mata tunanin ta tareda kokarin kashewa. Da sauri ta dakatar dashi ga mamakin ta saitaji bai kashe ba saidai baice komai ba, "pls Yaya Habib bazan daɗe ba kuma gidan yaya hibban zani fa" yadda tayi maganar har saida tsigar jikin shi ta tashi hakan ya saukar masa da wata irin kasala ya lumshe idanuwanshi a hankali tareda cizan lower lip ɗinsa. Kallan wayar jiddah tayi a tunanin ta ya kashe ne saidai ga mamakin ta saitaga yana kan layi amsar ce dai bazai bata ba. "Plss yaya Habib i promise bazan daɗe ba". Tuni idanuwan shi suka fara sauya yanayi ganin zata iya gano halin dayake ciki ne ta raina shi yasa ya buɗe baki dakyar yace "kije" kawai yace yana katse kiran nata.. Sosai jiddah tayi murna dan bata taba tunanin zasuyi haka dashi ya barta cikin sauki ba "kodan baya nan ne"? Ta tambayi kanta,,, taɓe baki tayi tana fadin ina ruwana ma ni karma yayi tunanin nafara sanshi ne kawai danya barni fita ne. Ta faɗa tana shigewa bathroom.. Mommy kuwa batayi mamakin barinta da Habib yayi ba danta gama gano shi sarai saidai dayake shi ba'a gane masa ne sauya wa yakeyi any time. Habib kuwa har dare yarasa abinda ke masa daɗi musamman idan ya tuna kasancewar shi da jiddah yanzu ya gama yadda akwai Abinda yakeso game da jiddah to amma menene wannan shine abinda yakasa tantance wa. Coffee mai zafi ya haɗa yasha sannan ya samu bacci ya dauke shi cikeda mafarki iri iri.. ✍🏻✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ηα *🌹ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛʟᴀᴅʏ🌹* ⓒᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wɑttpɑɗ* @ᴀmeenafirstladyy *🌈ᴋᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀs ᴀssᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ* 23 ...... jiddah kuwa sai yamma sannan ta dawo gida musamman data ga baya nan ba sanin lokacin data dawo zaiyi ba, mommy ce kawai tayi mata fadan kaiwa Yamma da tayi, hakuri taba mommyn sannan mommy tace kyaji dashi idan ya gano kin kai Yamma ai. "Pls mommy karki faɗa masa" Taɓe baki mommy tayi tana haurawa sama batareda tacewa jiddah komaiba.. Habib kuwa da sai yamma ya tashi ya danji jikinsa yayi kwari saidai ba nrml yake jinsa ba, kai tsaye wanda ya sakeyi sannan ya fice daga hotel din gaba daya ya nufi shopping.. Yanzu Habib yakan kira mommy lokaci zuwa lokaci saidai baya bari wayar tasu ta dade yake mata sallama ya kashe, saidai ya mayar da hankalinsa kan karatun dayake ka'in da na'in sosai yake jin dadin karatun nasa saidai zuciyarsa koda yaushe takan lissafo masa jiddah a yanayi da lokuta daban daban saidai kawai ya tsanci kanshi dayin murmushi.. Kusan 1month kenan da tafiyar Habib saidai basu sake waya da jiddah ba, duk lokacin da zasuyi waya da mommy tana wajan saidai bata damu da abata su gaisa ba dan yanzu baya gabanta harkar gabanta kawai takeyi wani lokacin har mantawa takeyi da tanada aure,, shikam Habib Dama kawai yakeso ya samu dan ya koma gida duk baisan dalilin da yasa yakesan komawar ba saidai zuciyarshi ta Dada tunzura da zuwa gidan. Yau jiddah sosai take wa mommy kuka akan makarantar ta duk ta ruda mommy da shagwaba sai faman lallashin ta mommy keyi akan tayi hakuri har Habib ya dawo saitayi karatun nata hankali kwance bayan basa tare amma fafur jiddah taki yarda har su hibban da Afnan suka zo suka tarar da rigimar. "Kwantar da hankalin ki kanwata Ni zan siyo miki form a wannan satin kinji" hibban ya faɗa yana mata dariya. Mommy ma Kai tsaye ta amince da zancan kawai sannan tace ita zatayiwa Habib Maganar a yau dan ta san halinshi sarai. Har yamma su hibban suna gidan, jiddah kuwa ta samu abokiyar hira a hirar tasu ne Afnan ta sanar da ita tana ciki na sati 3,. "Amma fa karki fadawa mommy" Afnan tace. Hararan ta jiddah tayi "dalla can meye na kar a faɗa mata bayan dole ta sani"! "Eh dai naji ta gani amma dai karki faɗa mata da bakin ki" Tsaki jiddah tayi cikeda takaicin wannan sakarci bayan mommy dole tasan maganar, "to meye ma Abin jin kunya tunda har anyin cikin" jiddah ta sake tambayar Afnan. Bugun wasa Afnan tayi mata tana dariya "ke jiddah duk kin zama mara kunya tunda yaya Habib ya gama da shafinki". Murmushi jiddah tayi "waya faɗa miki ya rufe shafina, kuma ku daina ganin laifins..." Kasa ƙarasawa tayi ganin irin kallan da Afnan take mata ta tsanin mamaki. "Jiddah badai har kin saiya ra'ayi ba keda kike cewa a raba auran" Afnan ta tambaye ta. Shiru jiddah kawai tayi dan ita kanta batasan dalilin da yasa kwana biyu takejin Habib a ranta ba ga wani irin mafarkai da takeyi tun abinda ya faru tsakaninsu dashi. Girgiza kai Afnan tayi danta gama gano jiddah kawai shiru tayi bata sake magana ba suka cigaba da hirar su. Sai dare sannan su hibban suka tafi gida,,, Mommy kuwa suna tafiya ta dauki wayarta zata kira Habib.. Jiddah sake gefenta ta kalli mommy tace "mommy wazaki Kira"? Hararan ta mommy tayi tace "yaushe kika fara samin ido ne jiddah, to Habib zan kira akan maganar makarantar ki amma idan kin hakura shikenan"! "Aaa mommy ya haƙuri" Batareda mommy tace komai ta danna layinsa. Lokacin Habib na zaune a haɗaɗɗen palourn shi A.C na Ratsa sassan jikinsa idanuwan shi a rufe kamar mai bacci,, jin karar wayar shine yasa ya dauko wayar tareda karawa a kunnen shi ganin Mommy ce.. A hankali ya gaida ta ta amsa sannan tace "Habib naga bakada niyyar rabuwa da jiddah zan jira har dawowar ka amma yanzu nasa a nema mata makaranta..."? Shiru yayi baice komai ba harta gama jawabin ta Sannan ya sauke numfashi a hankali. "Mommy Ina ganin tabar karatun saina dawo sai a dub.. "Ban yarda da wannan maganar ba, Hibban yace zai nema mata tafara hankali kwance kafin ka dawo kuma karka sake ka hanashi neman mata kaji na faɗa maka"! "To momma," kawai yace. "Sannan kuma Habib karka manta wlhy idan har ba jiddah ce ta amince da sake zama dakai ba to dole saika rubuta mata sakin ta dan naga alamar kamar kanaso ka nuna ka manta"! Rintse idanuwanshi yayi zuciyarshi ta dan harba, a hankali ya sake bude idanuwan nashi farare tarr dasu, saidai yakasa cewa komai, dakyar yace "to mommy" Yanaji ta katse wayar saida ya kusa 10s sannan ya sauke hannun nashi sannan ya tashi ya shige ɗakin sa cikin wani irin yanayi da baisan dalilin shigar shi wannan halin ba. Jiddah kuwa dake gefe sam bataso mommy tabi masa ta haka ba duk da har zuwa yanzu tana jin zafi da radadin abinda yayi mata a zuciyarta amma duk da haka bai kamata mommy tayi masa faɗa har haka ba. "Amma mommy bakya ganin yaya Habib zaisa wannan maganar a ransa harya shafi karatun saba".. Kallanta mommy tayi cikin mamaki "to saime yasa ɗin mana, kedai wlhy Allah ya shirya ki shashasha kawai" mommy tace tana barin palourn. A daran Habib ya kira hibban ya ja kunnen sa akan ya tabbatar bayan jiddah ta samu admission shi zai dinga kaita kuma ya dauko bai yarda a dauki driver ba. Amsa masa hibban yayi sannan yayi masa sallama.. Kamar Yadda hibban yace zai samar mata makaranta, a cikin satin ya sama mata gurbin karatu a jami'ar Bayero University, babu bata lokaci tafara zuwa cikeda farin ciki da murna kuma babu laifi makarantar tayi mata sosai tanajin daɗin karatu a ciki. Kullum hibban ke kaita kuma ya dauko ta, saidai wani lokacin idan aiki yayi masa yawa take hawa napep ta dawo gida batareda sanin Habib ba. Shima Habibullah yanzu karatun sa yayi nisa sosai kuma yana jin dadin jami'ar sosai ya mayar da hankali kan karatun nasa. Jiddah ta rike mutuncin ta a matsayin matar aure duk da har yanzu batajin kanta a wacce zata cigaba da zaman aure da Habib ba, saidai takanyi tunanin lokaci zuwa lokaci wani lokacin taji haushin shi ya sake kamata musamman idan ta tuna irin abubuwan da yayi mata na wulakanci,, Yanzu ta dada wayewa kamar ba itaba tayi kyau ta murje abinta hankali kwance take rayuwarta batada wata matsala ko tunanin data sawa kanta hakan yakara bayyana kwanciyar hankali a tattare da ita wanda yasa fatar ta sauyawa alamun jin dadi da kwanciyar hankali ya ratsa ta.. Habib kuwa yanzu ya tabbatar da yarinyar nan asiri tayi masa Saboda yawan tunanin ta dayake yi a kullum kuma akoda yaushe. Yauma zaune yake yana Watching TV Sam hankalin shi ba akan tv yake ba jiddah ce kawai a ransa,,, tsaki yayi kasa ƙasa yana jin haushin kanshi "wai Meyasa nake yawan tunanin yarinyar nan"? Ya tambayi kanshi,..dan taɓe baki yayi tareda ta tabbatar wa da kansa "Saboda halin daka baro ta mana"! Tsaki ya sakeyi sannan ya tashi yana barin palourn nashi... 3Month kenan da tafiyar Habib saidai yanzu gaba daya hankalin sa yayo gida kuma sam lokacin tafiyar tashi batayi ba dole ya sawa zuciyarshi hakuri duk da dama bashi da wani kwakwaran dalili na san Zuwan nashi gidan.... Jiddah kuwa wata uku kenan da Habib ya mayar da ita cikakkiyar mace, tayi kyau takara haske da ita duk kirjinta ya sake bayyana, duk wata boyayyar halittarta ta bayyana musamman hips ɗinta da suka sake fitowa dasu... Yan kwanakin nan mommy na lure da ita tafiye shegen ciye ciye ga kwadayin kuma bata fiye cin abinci sosai kamar da ba ga bacci yanzu da take yawan yi da shegen san jikin tsiya koda yaushe tana kan cinyar mommy idan tana gida, hankalin mommy ya fara dan tashi duk da bata gama tabbatar da zarginta ba saidai alamomin masu ciki ya gana bayyana ga jiddah,. Yau ta kasance Sunday, jiddah na gida tana dakinta sai faman bacci takeyi takeyi tun safe ta shiga bata sake fitowa ba.. Saida aka gama lunch sannan mommy ta taso ta suka nufi dining room,. Mommy na ɓude abincin jiddah ta tashi da gudu ta nufi bathroom din dake cikin dining room din, ta daɗe tana kyalaya amai har saida ta galabaita mommy na rike da ita, saida ta gama sannan mommy ta kamo ta suka fita, dakinta mommy ta kaita sannan tace me takeso taci. Ruwan Lipton kawai tace mommy ta hado mata tasha sannan bacci ya kwashe ta mommy tabar ɗakin.. Sai yamma ta tashi jikinta duk babu kwari, a palour ta samu mommy Zaune tana zuwa ta kwantar da kanta ka cinyar mommy zata fara shagwaba.. Mommy ce ta katse ta da tambayar "jiddah wata nawa kenan bakiyi menstruation dinki ba" Shiru jiddah tayi tana nazari, sai kuma ta tashi da sauri tana fadin "3month Kenan Mommy, nashiga uku banda lpy ko?! Murmushi mommy tayi danta gane jiddah haryanzu da yarinta kanta sannan bata shiga cikin mutane ballantana tasan irin wannan abubuwan.. "A'a kalau kike jiddah, kwantar da hankalin ki may be wahalar karatun da kikeyi ne yasa bakiyi ba har yanzu"! Wata ajiyar zuciya jiddah ta saki tareda murmushin jin dadi danta yadda da maganar mommyn harga Allah. Mommy kuwa yanzu ta tabbatar da zargin da takeyi na jiddah na ɗauke da cikin Habib harna wata uku tunda tafiyar shi da kwanciyar su a asibiti wata biyu kenan. Wani farin ciki ne ya mamaye zuciyar mommy saidai bata nunawa jiddah ba dan tasan halin jiddah sarai yanzu saita sa mata rigima wadda batasan yadda zatayi da ita ba Gara ta rufe ta har abin ya bayyana saita san yadda zatayi da ita. "Mommy yunwa nake ji" jiddah ta faɗa ta a wani yamitsa fuska. "Me zakici to"? Mommy ta Tambaye ta. "Sinasir zanci amma mara zafi nakeso a basshi saiya huce" ta faɗa tana dada wani yamitsa fuska. Ga mamakin ta saitaga mommy batayi mata mita ba kamar yadda ta saba kullum idan tafara ciye ciyenta da tsirfa sai mommy tayi ta mata mita wai tafiye shirme amma yau sai taga mommy batace komaiba saima murmushi da tayi ta nufi kitchen da alamu da kanta ma zata hada mata. Bata kawo komai a ranta ba ta kwanta a saman kujera tafara game a wayarta hankali kwance.... *ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ* 🌹ғɪʀsᴛʟᴀᴅʏ🌹✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 вч *🌹fírѕt lαdч🌹* *ⓒ* ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wαttpαd* @Ameenafirstladyy *🌈 ᴋᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀs ᴀssᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ* *(This page is yours, my dear sweet sis Maman Hajiya kiyi yadda kikeso dashi naki ne na mallaka miki)*🌹🌹 24 Mommy da kanta ta yi aikin ta gama sannan ta dawo palourn gun jiddah wacce har ta fara lumshe ido zatayi bacci,, da sauri ta tashi da fara'a tana fadin Sannu mommy meyasa baki kirani na tayaki ba. Hararan mommy tayi tace "ai kinaji ina aikin ai shine kika kwanta harma zakiyi bacci"! "Ayya mommy wlhy bansan meyasa nake yawan jin bacci ba yanzu ma duk jikina a mace yake wlhy" ya faɗa kamar zatayi kuka. "Shikenan naji saiki tashi kici aiya huce ɗin" Tashi tayi ta nufi dining room din saidai kadan taci taji duk batasan ci haka ta dawo palour suka ci gaba da hirar su itada mommy.. Da sassafe hibban yazo da hanzari ta shirya dan sai faman azalzalar ta yakeyi tayi sauri, ko breakfast batayi ba haka suka tafi, a mota sai faman zuba mita takewa hibban wai duk yasa jikinta ya gaji. Taɓe baki yayi cikin salan tsokana yace "saika ce wata mai ciki, shikenan daga nasa kinyi sauri dan karmu makara shine zakice wani duk kin gaji" ya faɗa bai kalli inda take ba. "Allah kuwa yaya hibban kwana biyu nima bansan meyasa nake yawan jin gajiya da bacci ba kullum sai mommy tayimin faɗa wai yanzu na fiye san jiki da yawa"! Dan murmushi yayi yace "to kodai yaya Habib ya jefa kwallansa a raga ne" Jiddah bata gane meyake nufi ba shiyasa batace komaiba saima cewa ta kumayi "nima wannan halin yafara takura min saboda banasan ya shafi karatuna" Murmushi hibban ya sakeyi wannan karan yace "kar dai kicemin bakisan kina dauke da cikin yayana ba saboda nasan ɓangaran doctor kike karanta ai" duk da Damm taji gabanta ya fadi me hakan yake nufi kenan hibban yana nufin ciki gareta,,,. Innalillahi ta fara maimaitawa a zuciyarta shikenan tashiga uku idan kuwa hakan ya tabbata ta shiga Uku, to amma meyasa batayi tunanin hakan ba sai yanzu... Jin tayi shiru yasa hibban kallan gefenta yace "yadai jiddah akwai damuwa ne"? Nodding kanta tayi dan tazama speechless bazata iya cewa komai ba. Har suka zo school din babu wanda ya sake magana, jiki a sanyaye ta fice ko sallama batayi masa ba shika murmushi kawai yayi danya fahimci maganar dayayi mata ce tasa duk tayi weak da ita,, murmushi ya sakeyi danshi tsokanar ta yayi har zuciyarshi bawai yasan komai bane,, haka ya tafi yana mata dariya a zuciyarsa.. Jiddah kuwa hankalin ta a tashe yake dan yanzu tagama tabbatar da maganar hibban duk sai yanzu take tunanin alamomin masu ciki duk sun gama bayyana akanta. Sam hankalin ta yakasa kwantawa dole lokacin tashi baiyi yiba ta nufi hospital, sosai doctor ya gwadata sannan ya tabbatar mata da tanada ciki bayan urine test da akayi mata. A firgice ta zaro idanuwanta kamar tasa ihu tace "doctor amm..." "Kinga nasan me zakice, saboda haka kije wani Asibitin a sake dubawa amma duk result din daya ne indai dubawar za'a yi so karma ki batawa kanki time Gara kawai ki yarda" Wani zazzaɓi ne ya rufe ta a take a wajan haka ta sallami doctor ta fice, kai tsaye gida ta nufa tana shiga palourn ta fashe da wani irin kuka. Da sauri mommy ta riƙo ta hankali a tashe tana tambayar ta lpy. Bata amsa ba sai kuka da takeyi kamar ranta zai fita, saida tagaji dan kanta tayi shiru sannan ta mikawa mommy takardar dake hannun ta. Mommy bataji komaiba Dan dama tasan hakan amma a fili saita nuna tashin hankalin ta fili.. "Wlhy mommy banasan cikin nan, yaya Habib basona yake ba tayaya zaiso abinda ke ciki na mommy nashiga uku dan Allah a zubar da cikin nan kafin yaya Habib ya sani.." takarasa cikin kuka sosai. Da sauri mommy ta rufe mata baki tana girgiza mata kai, nasiha sosai mommy tayi mata sannan tace "kema aiba sanshi kikeba nasani saboda haka na bari ya dawo saiya sake ki ki nemai wanda kikeso yake sanki, amma banaso nakara jin kalmar zubar da cikin nan". Jin mommy kawai takeyi amma sam bazata iya barin wannan mummunan abu ya faru ba wai ta haife cikin Habib bayan irin tsanar dayake nuna mata inaga ta haihu dashi "mommy karatu na fa" ta sake tambaya. "Ciki ai baya hana karatu jiddah ki kwantar da hankalin ki" mommy ta Bata amsa. Dakinta kawai ta nufa saidai hankalin ta still a tashe yake dan ta tabbatar wulakanci ne zai biyo baya idan har Habib ya sani... Cikin sati ɗaya kowa yasan jiddah nada ciki musamman kawayen ta da hibban duk sunyi farin ciki saidai yanzu bakaramin wahalar cikin take shaba sau biyu tana kwanciya a asibiti duk ta rame harda tunani ne yasa duk ta zange gashi ba komai take iya ci ba. Mommy na tausaya mata amma a haka take zuwa makaranta kawayen ta na school suyi tayi mata dariya.. Wata cikin hudu kenan saidai bai nuna ba saboda jikin jiddah ga tsayi gata babu kiba saidai kana ganinta kasan tanada ciki saboda yadda takara kyau fatar ta murje sai sheki takeyi,,.. Yau mommy ta yanke fadawa Habib duk tasan ba lallai ne su kwashe ta kalau ba tunda tasan halin shi sarai saidai dole zata faɗa masa dan ya sani koma menene saidai yayi amma dole ya sani.. Sai dare sannan mommy ta kirashi lokacin yana kwance da wayarshi a hannun shi kiran mommy ya shigo. Gabansa ne fadi dan yasan kiran mommy maganar ɗaya ce bata wuce sakin jiddah zatace ba shikam yanzu duk da yanajin jiddah a zuciyarshi bayajin zai dauki damuwa akan maganar sakin ta.. Da sallama ya daga ta amsa masa sannan ta fara sanar dashi maganar cikin jiddah.. Bazaka iya tantance irin yanayin da Habib yake ciki ba saidai za'a iya gane tsantsan farin ciki wanda har saida yasa Habib sakin wani kayataccen murmushi har mommy ta jiyo.. Murmushi itama tayi cikeda da jin dadi yadda ya amshi maganar. "Mommy to akwai wani abu ne ko dole saina dawo" ya faɗa cikin zumudi. "A'a Habib saidai ita jiddan tana shan wahalar cikin sosai amma komai yana tafiya dai dai ka zauna kayi karatun ka kawai," Shiru yayi dan farin ciki ya hanashi sake yin magana,. Sallama mommy tayi masa sannan ta kashe wayan nata.. A ranar Habib kowa ya ganshi yasan yana cikin farin ciki duk mutum ne shi mara nuna condition dinsa saidai yau kowa ya fahimce sa musamman abokan zaman sa dake cikin hotel din wadanda yake mu amalla dasu.. Cikin ikon Allah jarabawar su ta fita suka fara kagara yayi su gama saboda kawai ya koma yaga jiddansa da dansa ko yarsa saidai bai taba kiranta ba saidai ya kira mommy yaji yadda take.. Abin duniya ya ishi jiddah kullum sai tayi kuka sosai saidai Mommy tayi ta Bata baki da hakuri saidai bata sauraran nasihar mommy saboda yanzu haushin cikin kanshi take yadda ya hanata rawan gaban hantsi abinci ma ba sosai takeci ba duk a takure take jinta,,, tuni tagama yanke shawarata a ranta dan bazata iya daukan wannan wulakancin daga Habib ba sannan tanaso tayi karatu yadda ya kamata saboda yau ta shirya tsaf dan tafiya makaranta,. Hibban da yazo daukar ta tace ya tafi zata tafi da kanta saboda zata biya gidan kawarta su tafi tare.. Haka hibban ya tafi batareda ita ba, ita kuwa tana gama shirinta tayiwa mommy sallama ta taci ta tare me napep,,, kai tsaye wani private hospital da wata kawarta (Amra) tayi mata kwatance ta nufa taci Sa'a tana zuwa aka tabbatar mata da likitan da take nema yana nan yazo babu bata lokaci ta nufi office din Nasa... *_pls manage da wannan_*👈 ɪɴᴀ ᴊɪɴ ᴅᴀᴅ ɪɴ ᴄᴏᴍᴍᴇɴᴛ ᴅɪɴᴋᴜ sᴏsᴀɪ ᴋᴜᴍᴀ ɪɴᴀ sᴀɴᴇ ᴅᴀᴋᴜ ᴀʟʟᴀʜ ʏᴀʙᴀʀ ᴋᴀᴜɴᴀ ɪɴᴀ ᴀʟғᴀʜᴀʀɪ ᴅᴀᴋᴜ,, ᴍᴜᴄʜ ʟᴏᴠᴇ ʏᴏᴜ ❤❤❤ *ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛ ʟᴀᴅʏ*✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 вч *🌹fírѕt lαdч🌹* *ⓒ* ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wαttpαd* @Ameenafirstladyy 25 .....Zaune take gaban doctor bayan ya gama koro mata bayanin yanayin yadda abin yake, sannan ta nisa tana kallan dan dattijon wanda jin dadi ya ratsa shi da alamu.. "Pls nidai doctor koma yane ina so a cire shi"! "Gaskiya hajiya akwai haɗari babba saboda cikin ya fara kwari za'a iya samun matsala babba inaga kawai ki hakura" ya karasa maganar yana kallan face ɗinta. Cikin yanayin damuwa tace "Yanzu babu yadda za'a yi kenan"! Make kafada docton yayi sannan yace "akwai mana idan kikace kinaso ayi kin amince zaki dauki kowanne irin matsala idan ta biyo baya"! Da sauri tace eh doctor ayi inshallah babu wata matsala da za'a samu by God grace.. "Shikenan ki dawo next week zanyi Miki allura tareda magani wanda zaki sha" "Ok thank you doctor" tace tana tashi bayan ya faɗa mata payment din... Jiddah cikeda farin ciki ta koma gida hankali kwance babu wanda ta faɗawa saidai mommy ta lura ta dan rage damuwa kwana biyu.. *Russia* Sultan ne dake gefe a zaune cikeda mamaki yake kallan Habib wanda yake hada kaya cikin nutsuwa fuskar tashi wasai,, "wai man da gaske kake yi tafiya zakayi"! Ɗago eye ball dinsa yayi ya kalli Sultan batareda yace komai ba, saida ya gama abinda yake tsaf sannan ya zauna ya fuskanci Sultan ɗin da mamaki ya gama kamashi.. "Sultan bazaka gane yadda nake ji a zuciya taba, Saboda haka dole na koma na nawa matata da yarona kulawa ta.." "Amma karatun naka fa" Kallan Sultan ya sakeyi na tsawon wasu sakanni kamar mai tuna wani abu, sannan yayi ajiyar zuciya yace "nima bansani ba" "Kamar ya baka sani ba kana nufin bazaka dawo ba"? Cikin ƙosawa da tambayoyin da Sultan yake masa ya danyi tsaki yace "banida tabbacin zan dawo ko a'a, koda na dawo ma zan karasa makaranta ta kamar yadda na fara" Jinjina kai Sultan yayi dan yasan tsarin makarantar da Habib keyi ba irin sauran Makarantun gida Nigeria bane shiyasa yakesan ya tafi dan yasan bashida wata matsala ta ɓangaran karatun nashi.. "Shikenan yaushe zakayi tafiyar"? "Next week inshallah" "Amma shine ka hada kaya tun yau" Sultan ya faɗa yana dariya tsokana. Shiru Habib yayi dan ya gaji da ba Sultan amsa kuma yasan ko zasu kwana bazai gaji da tambayar shi abubuwa ba. Sultan ne yaci gaba da surutun shi saidai sam Habib ba kula shi yake ba, cikin jin haushi Sultan ya tashi yana faɗin "nifa kaga abin dayake hadani dakai, kaga nina tafi wajan matata muyi hirar" Sultan ya faɗa yana ficewa.. "Mata"? Habib ya maimaita kamar baisan me kalmar take nufi ba,,, Wani murmushi yayi tareda lumshe sexy eyes ɗinsa Sannan ya lashi lips ɗinsa. "Ohhh next week come quickly"!!! Ya faɗa yana daɗa lumshe ido,,,,,, "Jiddah lunch is ready, tashi muje kici abinci" mommy ta faɗa tana kallan jiddah dake cin biscuit tun ɗazu. Yamitsa fuska ta ɗanyi "a'a mommy I'm full" "Da kika ci me"? Mommy ta Tambaye cikin nuna kulawa. "Biscuit" "Banasan shashanci tashi ki wuce muje kar ranki ya ɓaci" Dariya jiddah tayi tana tashi da sauri ta nufi dining room. "Waike jiddah ko nauyin jikin ki bakyaji ne, bana hanaki irin wannan tashin ba.."! Jiddah da har takai bakin shiga ta tsaya tana langabe kai "sorry momma bazan sake ba" "Kima sake mana".. Tare suka zauna saidai jiddah takasa taba komai a wajan sai mommy ce tayi saving ɗinta cikeda kulawa sannan ta Turo mata plate din abinci" Jiddah kamar tayi kuka dan tasan kotaci ma ba zama zaiyi ba,, kallanta mommy tayi tace "eat Mana" "Allah mommy zuciyata ma harta fara tashi sam banasan wannan abincin" "Shikenan me kikeso sai a dafa miki" "A'a mommy bari na gwada cin wannan ɗin"" A hankali ta fara ci saidai loman ta uku ta tashi da dan gudunta ta nufi bathroom din wajan,, Cikeda tausayinta mommy suka koma palour, dan itama mommyn har abincin ya fita a kanta saboda bakaramin so mommy kewa jiddah ba shiyasa ko zazzaɓi jiddah keyi hankali mommy tashi yake sosai ballantana yanzu da ko abincin kirki bata iya ci duk ta dan rame.. Hawaye ne suka zubowa jiddah masu zafi da tuna irin tsanar da Habib yayi mata harta kai yabi mata ta karfi amma sai gashi dalilin hakan tana dauke da cikin shi,.. Ɗagota daga kan cinyarta mommy tayi tana share mata hawayen, "jiddah banaso naga kina kuka kin sani, yanzu kuma kukan na mene bayan kinsan kowacce mai ciki hakuri takeyi ko kinaso hankalina ya tashi ne" Girgiza kai tayi tana dada zubar da hawaye,, "a'a mommy banaso hankalin ki ya tashi, saidai ina tsoron yaya Habib mommy baya Sona tayaya zai so abinda ke cikina ki duba fa irin abubuwan da tayimin kafin barinshi kasar nan, nasan kashe nine kawai bazaiyi ba idan yaji wannan maganar" Da sauri mommy ta girgiza mata kai "a'a waya faɗa miki Habib yaji dadin Wannan maganar sosai ma kuwa saidai yace ranki zai ɓaci idan bakyacin wani abin kirki"! Dan murmushi tayi kawai danta nunawa mommy ta yarda amma har zuciyarta tasan mommy kawai faɗa tayi dan karta tayar mata da hankali. Tayaya ma zata yarda bayan tasan waye Habibullah mutum mai san zuciyarshi da mugunta da wulakanci iri iri... Suna nan zaune har bacci ya dauke jiddah sannan mommy ta gyara mata kwanciyarta.. Yanzu jiddah tagama Shirin komai kuma ko mommy Bata faɗawa ba, school kuwa yanzu ko fashi batayi kullum saita je,.. Habib da Afnan kuwa sai tattalin nasu cikin sukeyi Gwanin sha'awa haka rayuwar su take tafiya,,. Next week Jibi ne takama jiddah zata koma hospital Kamar yadda doctor yace mata shiyasa tun yau ta tsarawa kanta yadda zataje batareda kowa ya sani ba danta kudurta a ranta dole ma ta rabu da cikin ko zata rasa Rayuwar ta saita zubar data fuskanci wulakancin Habib.. ......... ........ Habib kuwa ya gama shirin tafiyar shi tsaff yau, sai dare sannan ya kira mommy Wanda yake da tabbacin bata tareda jiddah saboda yasan Nigeria yanzu dare ne sosai.. Cikin alamun bacci Mommy ta daga Kiran ganin Habib ne batayi wani mamaki ba tunda tasan halin shi,, shi juyayyan mutum ne.. "Lafiya kuwa Habib"? Mommy ta jefa masa tambaya bayan ta amsa sallamar shi. "I'm sorry momma, gobe zan dawo inshallah that's why I called you" "Cikin mamaki mommy tace gobe kuma Habib"? "Yes mommy pls don't no" "Shikenan wanne lokaci zaka sauka" "By 6pm Flight dinmu zai sauka" "Shikenan Allah ya kaimu" Ameen yace tareda katse wayar tashi.. Suna gama wayar mommy taci gaba da baccin ta, koda safe har jiddah ta fita school mommy Bata fito ba shiyasa jiddah batasan zancan ba,.. Mommy na saukowa down stairs ta Kira Hibban ta sanar masa da dawowar Habib saboda haka ya kawo masu gyara gidan tunda ka'idar Habib dole sai an sauya komai na part ɗinsa kafin ya dawo.. Ba bata lokaci hibban yazo da ma'aikata suka fara aikin su cikin kankanin lokaci... Sai 3pm jiddah ta dawo duk a gajiye, Bata kula da masu aikin ba ta shiga ga palour tana cire mayafinta. "Wash mommy I'm tired" "Sannu da hanya" Kallan mommy tayi da mamaki ganin an sauya musu tsarin palourn nasu. "Mommy badai kece kikayi wannan aikin ba" Murmushi mommy tayi sannan tace "baki kula da masu aiki bane, yau da yamma Flight dinsu Habib zai sauka kinsan halin shi da tsafta bayasan ya dawo ya samu komai yadda ya barshi" Tunda mommy tafara Magana gaban jiddah yayi mummunan faduwa cikinta ya hatsina shikenan tashiga uku gashi gobe ne sukayi da doctor zataje Yaya kenan.. "Yadai jiddah, na faɗa miki wlhy wannan shegen tsoron naki shine yasa Habib yake dada ganin kamar bakida gaskiya akan komai" Murmushi jiddah ta ƙaƙalo sannan tace "to momma zan kiyaye barina shiga na watsa ruwa" bata jira amsar mommy ba ta wuce ciki da sauri.. Tana rufi kofar dakin nata ta jingina tareda sakin wani ajiyar zuciya, "bazan taɓa fasa abinda nayi niyya ba" ta faɗa tana karasawa jikin bed ɗinta.. ғᴏʟʟᴏᴡ ᴏɴ ᴡᴀᴛᴛᴘᴀᴅ ᴘʟs ᴍᴏʀᴇ ᴄᴏᴍᴍᴇɴᴛs ᴍᴏʀᴇ ᴛʏᴘɪɴɢ✍🏻 ᴛᴀᴋᴜ ᴄᴇ *ᶠᴵᴿˢᵀ ᴸᴬᴰᵞ*🌹✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 вч *🌹fírѕt lαdч🌹* *ⓒ* ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wαttpαd* @Ameenafirstladyy ( *_wannan page din gaba daya sadaukarwa ne gareku sweets dears_* _Sha'awanat Auwal Ƴar mutan garo_ _Nusee na'ala_ _Maman Hajiya_ _Ruky gabari_ _Pretty 1_ _Pretty 2_ _My sweet sis Hussaina ibadan_ *_so much love you_*🌹🌹🌹 26 .....kai tsaye wanka jiddah ta shiga ta sheka wankan ta ta fito ɗaure da towel, tsaf ta shirya cikin riga da skirt na atamfa Wanda ya amshi jikinta kallan kanta tayi a mirror sannan ta kalli cikinta, duk sai taji jikinta yayi sanyi sam ita wannan cikin duk lokacin data tuna da dashi saitaji haushin kanta da shi kanshi cikin. Tsaki ta ɗanyi sannan ta dauki mayafinta ta fito palour.. Tana shigowa palourn taji daddan ƙamshim abincin da mommy keyi duk ya cika palourn,, kitchen din ta shiga tana fadin "mommy yau gidan duk ya cika da ƙamshi" Murmushi mommy tayi tana jiyowa tace "kinsan halin Habib ba lallai ma yaci komai ba kila wahalar banza mukeyi" Dan taɓe baki jiddah tayi sannan ta nufi hanyar fita, Muryar mommy taji tana tambayar"zaki bi hibban ne ku taro shi" Da sauri ta girgiza kai "a'a mommy zanyi assignment ne" Daga kai kawai mommy tayi jiddah ta fice da sauri ta koma ɗakinta ta kwanta cikeda da tunanin iri iri tareda fatan Allah yasa ayi komai lpy batareda wata matsala ba cikin kankanin lokaci bacci ya dauke ta hankali kwance tafara baccin ta.. Tun 5:30 Hibban ya isa airport yana jiran lokacin saukar su Habib, 6pm dai dai jirginsu Habibullah ya sauka.. Cikin isa da kasaita yake saukowa daga jirgin, fuskar tashi ba yabo ba fallasa saidai zaka iya hango kwarjini da haibar dake tattare da kyakkyawar fuskar shi, cikin nutsuwa ya sauko yafara waige waige cikin takaici ya fara tsaki tareda zaro tafkekiyar wayarshi daga aljihun rigar shi. Cikin sauri hibban ta karasa kusa dashi dai dai ya daga wayar zuwa kunnen shi. Yana ganin hibban ya sauke wayar fuskar shi a haɗe ya danyi tsaki. "I'm sorry Yaya" hibban yayi saurin bashi hakuri dan ya gane meyake nufi. Amsar jakar hannun shi yayi sannan suka wuce mota Habib yana tafiya kamar bayasan taka ƙasa saidai zuciyarshi a zake take da zuwa gida dan ganin abubuwan alfaharin shi.. Hibban keta faman surutu saidai Habib ko sauraran bayayi,, karshe ma sai hararan hibban ɗin yayi yace"zaka iya min shiru"? "I'm so sorry Yaya" hibban yace yana maida hankali kan tukinsa.. Cikin garage din gidan hibban yayi Parking sannan ya fice ya dauki kayan Habib ɗin ya shige ciki.. Saida Habib ya dauki mintina sannan ya fito cikeda izza ya fara tafiya,, dakatar da ma'aikatan gidan kawai yake da hannu da suke ta faman Miko masa gaisuwar Barka da dawowa. "Mommy Ina jiddan kuma" "Tana daki hibban kasan yanzu ta fiye bacci sosai". "Ai dama duk haka suke itama afnan sai Ni nake mata..." Kasa ƙarasawa yayi tunawa da yayi rashin kunya zaiyi sannan ya kalli dake faman murmushi. "Amm.. ina nufin saini nake abinci".. ya faɗa yana sosa keya.. Dariya mommy dai dai shigowar Habib palourn.. Hugging din juna sukayi "i miss You momma" "Miss you dear" Dan kallan palourn yayi kamar maisan gano wani abu sai kuma ya fiske ya zauna a saman kujera.. Sallama hibban yayi musu akan zasu dawo shida afnan ɗin zuwa gobe sannan ya tafi bayan yayiwa Habib welcome back... Da kyar mommy ta lallabi Habibullah ya Dan ci abinci sai yamitsa fuska yake Kamar wani yaro,,. "Habibullah bakasan cin abinci kamar wani yaro, ga jiddah ma sam batasan cin abinci sosai..." "What, amma shine aka kyaleta.." Habib ya faɗa da dan saurin shi dan ji yayi ranshi ya ɓaci me take nufi kenan tanaso ta wahalar masa da babynsa kenan kome. "Kaga kwantar da hankalin ka kowacce mace haka take fuskanta a lokacin da take dauke da ciki" Shiru kawai yayi sannan ya tashi zai fice.. "Mommy kisa ta kawomin coffee anjima" ya fice batareda ya jira amsar taba.. Kallo mommy tabishi dashi sannan ta tashi ta haye upstairs.. Sai bayan magrib sannan jiddah ta tashi, wanka ta sake yi sannan ta fito palour, babu kowa a palourn kai tsaye kitchen ta shiga ta haɗa ruwan Lipton Kamar yadda ta saba ta fito palour tana sha dai dai saukowar mommy. "Sannu mommy" "Yauwa jiddah kin tashi" "Eh momma" "Yayanki ya dawo, ki haɗa coffee ki Kai masa sannan ki dawo kici abinci" Gabanta ya fadi dan sai yanzu ta tuna da dawowar tashi. "Yadai lafiya"? Murmushi ta ƙaƙalo tace "babu komai mommy, Amma nifa bazan iya cin komai ba" "Shikenan dama na faɗa masa ai, saiki tanadi amsar bashi"! A tsorace ta kalli mommy tareda zaro idanuwanta "nashiga3"! Tashi mommy tayi batace komaiba tabar jiddah a wajan.. Haɗa coffee take saidai zuciyarta a tsinke take "tayaya zata fuskanci Habib da cikin nan, wanne irin wulakanci zata fuskanta daga gareshi, ya Allah"! Harta gama hada coffeen ta fice zuwa part ɗinsa amma zuciyarta harbawa take a hankali.. Saida Habib yayi sallar isha sannan ya shiga bathroom ya fesa wanka ya fito ɗaure da towel jikinshi yana tsane jiki. Ta daɗe a tsaye a palourn sannan ta nufi ɗakin nasa cikin dakewa. Yanajin shigowar ta saidai ya juya baya yana hango ta ta mirror,.tana shigowa taganshi da towel da sauri ta juya zata fice. "Jiddahhhh.."! Wata faduwar gaba taji wanda yasa saida taji kanta ya sara dan yauce rana ta farko daya taɓa kiranta da sunanta. Cak ta tsaya saidai ta kasa juyowa,. Dan taɓe baki yayi sannan ya nufo ta, daf da ita ya tsaya yace "ajiye saiki fitan" Badan taso ba ta juyo ta ajiye sannan ta saci kallanshi, "masha Allah gaskiya yaya Habib karshe ne fagen komai, ta ko ina ya hadu ya cika cikakken namiji maiji da kyau da cikar haiba"! "Zaki iya fita" yace yana haɗe fuska tareda yin dan tsaki.. "Keee" ya sake kiranta. A dan tsorace ta juyo da fararan idanuwanta. "Mommy ta fadamin bakyasan cin abinci"! Shiru tayi tana mazurai da idanuwanta. "Sorry yaya..." Dakatar da ita yayi sannan yace ta fita ta bashi waje kafin ranshi ya sake ɓaci. Babu shiri ta fice da sauri ganin ya fara sauyawa.. Dan murmushi yayi yana lumshe idanuwan shi tunawa da cikin nata da yayi, ya fahimci har wani irin kyau cikin yasa ta gashi takara yar kiba boobs ɗinta sun Kara girma.. Lips ɗinsa ya lasa yana wani kasaitaccen murmushi sannan ya fara sipping coffee ɗinsa a hankali. Da sassafe jiddah ta shirya zuciyarta fes, tana gama shiryawa ta kira hibban. "Yaya hibban ba saika zo daukana ba" "Why" hibban ya Tambaye ta. "Yaya Habib ne yace zai kaini"! "Ohh manta fa, ashe yau zan huta da tawa matar dama duk an takura min" Dariya jiddah tayi tace "saina faɗa masa kuwa" "So what, abinda nasan ko kwakwaran numfashi bakyayi idan yana waje" Dariya ta sakeyi tayi masa sallama ganin zai bata mata lokaci. Da sauri sauri jiddah ta fito palour, mommy kaɗai ta samu a palour. "Mommy zan wuce"! "Bazaki jira hibban ɗin ba" "Yace na same shi a gida" "Ok shikenan saikin dawo" Bata sake magana ba ta fice da sauri dan 8am sukayi da doctor kafin aiki yayi masa yawa yace tazo.. Me napep ta tare tayi masa kwatancen hospital din suka dau hanya.. Tana fita Habib ya shigo, gaida mommy yayi sannan ya fara bin palourn da kallo. Lura da yadda yake waige waige mommy tayi, murmushi ta ɗanyi danta fahimci yanzu Habib bashida kunya akan cikinsa. "Jiddah ta tafi school" "Waye ya kaita"? "Hibban mana bashi kasa ya dinga kaita ba" Shiru ya danyi saboda tunawa da yanzu hibban ɗin ya kira shi ya gaida shi saidai baiji alamun driving yake ba. Ji yayi bai gamsu tafiyar tata ba Amma saiyayi shiri kawai. "Yadai naga kamar ranka ya ɓaci"! "Nothing, kawai dai nasan hibban baya tafiya a hankali ne kuma kinga ba ita kadai bace"! Da mamaki mommy ta kalle shi saidai yayi kasa da kai alamun kunya. "To ai saika dinga kaita da kanka, saiku fita tun 6am saiku kai 8 baku isa ba tsabar tafiya a hankali.."! Mommy ta faɗa tana barin palourn.. Murmushi yayi shima ya koma part ɗinsa Dan ba abinci zaici yanzu ba,.. Zuciyarshi fal da tunanin jiddah da cikin jikinta,,, tabbas lokaci yayi dazai nunawa jiddah kulawa kodan cikin dake jikinta, yanajin soyayyar cikin har zuciyarshi yanaji kamar yafi zaifi kowa farin ciki ranar da aka haife masa cikin da wannan tunanin bacci ya dauke shi.. Har cikin asibitin mai napep ya ajiye jiddah sannan tace ya jira ta fito saiya maida ta sannan ta biya shi. "To Hajiya" mai napep yace. Kai tsaye office din docton ta shiga... ✍🏻✍🏻✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 вч *🌹ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛ ʟᴀᴅʏ 🌹* *ⓒ* ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ *wαttpαd* @Ameenafirstladyy _____________________________ *🌈ᴋᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀs ᴀssᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociatio _____________________________ 27 Zaune docton yake sanye da siririn farin glass, zama tayi a kujerar dake gabansa. "Doctor pls kayi kokarin kar a samu matsala"! "Banida tabbacin samun matsala ko akasin haka, kawai dai zan baki magani wanda zakiyi Amfani dashi zuwa anjima yanzu kuma zanyi miki allura" "Yauwa doctor" tace tana ciro kudin dake jakarta.. Babu bata lokaci doctor yayi mata allurar tareda wasu irin magunguna tablet kananu,, sosai tayi masa Godiya sannan tace "zan iya tafiya yanzu" "Eh mana idan kinji wata matsalar saiki kira Ni" Batareda ta sake cewa komai ba ta fice daga office din.. Habibullah sosai ya samu bacci sai azhar sannan ya tashi yana miƙa tareda addu'ar tashi daga bacci dauke a bakinsa,, kai tsaye wanka ya faɗa sannan ya fito ya shirya zuwa part din mommy,. Babu kowa a palourn hakan yasa yayi zamansa tareda lumshe ido yana mai jin dadin zama a palourn yadda yaji shiru babu wata hayaniya.. Yana nan zaune mommy ta sauko downstairs. "Habib ka shigo Kenan" "Eh mommy" Kujerar dayake zaune ta samu kusa dashi ta zauna sannan ta kamo hannuwanshi cikin nata, ta ɗago kai tana kallan shi taga shima ita yake kallo. Cikin nutsuwa da lallami mommy tafara masa magana. "Habib dan Allah karka nunawa jiddah bakasan cikin nan, takasa sakin jikinta da wannan cikin koda yaushe maganar ta baya wuce yadda zakuyi da ita idan ka dawo,, saboda haka banaso naji kayi mata wani abu dazai sa azo a samu matsala pls" Dan murmushi Habib yayi sannan yace "inshallah mommy babu abinda zan nuna mata" Kiss ta manna masa a saman goshin shi "good my boy" ta faɗa tana barin palourn zuwa kitchen. Tana barin palourn Habib ya saki wani kayataccen murmushi har fararan haƙoran sa suka bayyana sannan ya sake lumshe idanuwanshi cikeda farin ciki yake jin kansa yau Kamar bashi ba. "Allah kasa jiddah ta haife lpy" ya faɗa yana sake zaman shi.. Makaranta jiddah ta wuce sai lokacin tashi sannan ta nufo gida dan batajin dadin jikinta saidai bata wani damu ba tunda tasan dalilin cutar tata.. Hankalin Habib yakasa kwanciya sai faman kai kawo yake a palour jira kawai yake jiddah ta dawo tasha faɗa dan Gani yake kamar yawo kawai ta wuce. "Mommy dama suna kaiwa wannan lokacin"? "Eh mana, dayake bakayi karatu anan ba shiyasa bakasan hakan ba" Wayar shi ya ciro tareda dannawa hibban kira,, bugu daya hibban ya daga cikeda tsoron kiran.. "Wai bakasan lokacin da suke tashi bane"? "Ai.na..yi tunanin zaka koma ka ɗauko ta ne"! Ran Habib ya fara ɓaci da wannan rainin hankalin.. "Ok Nina kaita kenan, ko kuma sa'an ta ne dazanje dauko ta".. A dan tsorace hibban yace "yaya nayi tunanin kai ka kaita ai, nace zan kaita tace kai zaka kaita. .."!!! Katse wayar Habib yayi cikin fushi da bacin rai,.. Jin yana fitar da wata iska mommy ta kalle shi. "Me kuma ya faru"! Shiru yayi mata yakasa bata amsa,, ganin haka yasa mommy ta share shi itama dan tasan ba amsa zai bata ba, karshe ma ta barmasa palourn. Da sauri jiddah ta biya mai napep kudinsa sannan ta shige gidan,, ganin motarshi saida gabanta ya fadi "kenan yana gida bai fita ba,, ya Allah ya tamkeni kar tayimin wani abu"!! Zaune ta same shi a palourn ya ɗan jingina da jikin kujera idanuwan shi a rufe saidai ta hango tsantsan bacin rai a fuskar shi.. Kamar munafuka haka tafara sanɗa zata wuce, wani irin fizgo ta taji anyi har saida ta tsorata,. Tar ya bude idanuwan shi a kanta yana mata wani irin kallo wanda yasa tafara hawaye tana yarfar da hannu. "Daga ina kike"? Kasa Magana tayi dan batasan amsar bashi ba saidai tuni hawaye ya gama wanke mata fuska,, har zuciyarshi yaji zubar hawayen nata..Dan kawar da kanshi yayi gefe saidai yana tsaye gabanta da alamu tunanin matakin da zai dauka yakeyi.... Kasa yi mata komai yayi saidai zuciyarshi kamar ta fito dan bacin rai da bakin ciki.. Ganin haka yasa tayi saurin barin wajan kafin ya sauya ra'ayinsa ya kai ga marinta.. "Habib kaida waye ne" mommy ta tambaya tana saukowa daga upstairs.. Girgiza kanshi kawai yayi sannan ya fice daga palourn.. Dakin jiddah mommy ta shiga, "bai miki komaiba ko"? "Eh mommy" jiddah ta faɗa da kyar tana dan rufe ido yadda taji marar ta na juyawa.. Kallanta mommy tayi tsaff"lpy kike kuwa" Ƙaƙalo murmushi tayi dan kar mommyn tagane halin da take ciki.. "Babu komai fa" "Shikenan ki fito kiyi lunch naga yamma tayi kuma nasan bakici komaiba" "To momma" Mommy ta fice daga ɗakin nata.. Da kyar tayi wanka ta fita palourn, abinci ma kadan taci sannan ta kwanta a palourn kan kujera duk dan kar mommy ta gane.. Ya dade shower na sauka kanshi yana huci a hankali,, da kyar ya samu yaji zuciyarshi ta ɗanyi sanyi sannan ya fito zuwa Masallaci jin ana kiran magrib.. Sai bayan isha ya shigo, ko abinci baici ba ya koma part ɗinsa ya kwanta,,.. Sai 10pm jiddah tayiwa mommy sallama ta nufi ɗakin ta, kwanciya tayi batasha maganin ba danta manta ma,,, bacci mai daɗi ne ya dauke ta duk da batada lafiya saidai ta danji sauki marar Tata... Cikin bacci jiddah taji marar ta na dan karta mata, kamar an tsikareta ta tashi zaune, abu kamar wasa saiga jiddah tafara juye juye tana zuba uban gumi,.. Cikin kankanin lokaci jiddah ta jigata, sunan Allah kawai take ambato,. Jin ana kiran sallar asuba ne yasa jiddah rufe idanuwan ta cikin azabar ciwo,,. Sosai ta godewa Allah da bata sha maganin ba tabar shi a cikin jakarta da shikenan tasan yau mutuwa zatayi.. Wasa farin girki jiddah Kamar ana karo ciwan tun tana iya buɗe ido har takasa motsa bakinta ma, tanaji wani abu mai dumi yana bin kafarta saidai ina batasan ko menene ba juye juye kawai takeyi tana kiran sunan Allah a ranta dan tasan yau mutuwa ce kawai.. Da sassafe mommy ta sauko kamar yadda ta Saba, kafin masu girki su tashi ta shiga kitchen Dan da yunwa ta tashi yau.. Habibullah ma yau da sassafe ya shigo part ɗinsu mommy tayi mamaki sosai ganinshi a irin wannan Lokacin. Sai 7am sannan mommy ta fito daga kitchen din, cikeda mamaki ta kalli Habib"jiddah kuwa lpy naga yau bata fito ba zata makara fa, dama naga jiya kamar batajin daɗi" . Ai Habib a zabure ya tashi ya nufi ɗakin nata, sau biyu yayi nocking saidai babu alamar da mutum a cikin ɗakin.. Cikeda da takaici ya tura kofar dakin, har zai fara nuna fushin sa saidai kuma komai ya tsaya masa cak ganin jiddah cikin jini babu alamar motsi a tareda Ita.. Cikin wani irin sauri Habib ya karasa kusa da ita yana duba numfashin ta saidai ina babu alamar numfashi ko kaɗan.. Kamar wanda ya dauki kara yana Habib ya dauki jiddah ya fita cikin tashin hankali da razana.. Salati mommy tayi itama hankali a tashe tabi bayan Habib zuwa Mota, dakatar da shi mommy tayi ta amshi car key ɗin ganin yanayin dayake bazai iya driving ba duk ya fita hankalin sa... Asibitin Dr Ahmad suka nufa, kai tsaye emergency room suka nufa da ita dan ceto rayuwar ta,.. Sosai mommy ta koma lallashin Habib ganin yadda ya koma jikinsa duk yayi sanyi idanuwan shi sunyi ja sosai alamun tashin hankali da damuwa.. Saida doctor Ahmad suka dauki lokaci sosai sannan ya fito yana share gumin goshinsa.. Zaune suke a office ɗinsa yafara Yi musu bayani. "Alhamdulillah saidai mu godewa Allah cikin bai zube ba sabo.. shiru ya danyi sannan yayi murmushi yace Finally dai Habib ka kwantar da hankalin ka cikin matarka yana nan bai zube ba saidai zai maimaita lokacinsa kamar yadda nasan ka sani".. Ba Habib kaɗai ba har mommy saida taji wata iska mai daɗi ta kada saɓanin ɗazu da sukejin zafin garin.. "Yanzu tana dakin hutu zuwa anjima zaku iya ganinta" ya faɗa yana kallan fuskar Habib da take nuna farin ciki wanda ba kowane zai iya ganewa ba. "Alhamdulillah mungode Allah, saidai ba wani matsalar kodai wani abu taci wanda ba'a so masu ciki suci" mommy ta Tambaya. Dr Ahmad wanda bazai iya faɗa musu gaskiyar abin ba dan yasan matsala hakan zai haifar musamman daga wajan Habib,, shiyasa bai faɗi dalilin dayasa cikin yayi barazanar zubewa ba ya bari ne har saita farfaɗo sannan yayi mata nasiha, sannan yabata shawarwari sosai, wannan ya barshi a matsayin sirri tsakanin su tunda yasan ko mommy bazataji Dadi ba musamman yadda take,san jiddah kuma take daukar ta kamar yar cikinta... "Babu komai mommy saidai Yakamata a lura da abubuwa da take ci" Habib duk ya lura dashi kamar yana boye musu wani abu... Dr Ahmad kuwa Ganin irin kallan da Habib ke masa ne yasa yace " kai tsabar kaduwa ma zaka rasa first born har mantawa kayi da matsayinka na babban likita duk ka wani rude kazama abin tausayi.".. Dariya sukayi su duka saidai banda Habib wanda yayi murmushi wanda iya karsa lips ɗinsa kawai.. sannan suka fice shida mommy zuwa dakin da aka kwantar da jiddan... ```NOT EDITED📵``` ```Follow me on Wattpad``` Comment,, share and vote pls.. [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 *🌈K͎a͎i͎n͎u͎w͎a͎ W͎r͎i͎t͎e͎r͎s͎ A͎s͎s͎o͎c͎i͎a͎t͎i͎o͎n͎* вч *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* *wαttpαd:ameenafirstladyy* {29} Kai tsaye fita yayi ya siyo komai saidai zuciyarshi a cikeda bakin ciki,, palourn mommy ya shiga tana zaune itada jiddah wacce ke kwance cinyar mommyn, tana jin sallamar shi ta tashi zaune tana kasa da kanta dan bataso su hada ido dashi. "Munafuka dole mana ki ƙasa dakai"! Ya faɗa a ransa. "Yadai ka tsaya kazo mana kayi aikin ka" mommy ta faɗa masa.. Kamar mai koyon tafiya haka Habib ya ƙarasa ya ciro alluran,,, saidai yana kawo hannu jiddah tafara kuka tana fadin batasan alluran,. Sai lallashin ta mommy keyi amma ina taki mika hannun Habib kuwa takaici ne ya cika shi tsabar takaici baisan sanda ya fizgo hannunta ba ya caka mata allura fuskar nan a haɗe kamar bai taɓa dariya ba, toshe baki jiddah tayi tana kuka sosai tunda tasan ba san kara yake ba, haka ya gama sannan ya nunawa mommy Maganganun da yadda zata sha sannan ya fice daga palourn dan zuciyarshi tunzura shi takeyi yayi abinda bayasan yi yanzu.. Da kyar jiddah tayi shiru sannan ta wuce dakinta tana ajiyar zuciya tareda jin haushin Habib danta lura harda mugunta ya haɗa Mata.... Kwana takwas jiddah ta kwashe tana jinya bata zuwa school sai ranar Monday ta shirya tsaf ta fito palour da ɗan saurin ta, Habib na zaune yana sipping coffee saidai yana ganinta ya ajiye coffeen yana Binta da ido,. Gaida shi tayi kamar mara gaskiya zata fice duk da bai amsa gaisuwar tataba,, dakatar da ita yayi ta hanyar kiranta da keee. Juyowa tayi tana wasa da kasan mayafinta sannan ta matso kusa dashi tana fadin "gani yaya Habib" Wulakantaccen kallo yabita dashi sannan yace ina zaki a irin wannan shigar"? Kasa bashi amsa tayi, ganin ya mike ne yasa tayi baya da sauri tana zare ido cikin in Ina tace "school zanje" Baice komaiba ya raba ta gefenta zai ya wuce saida ya kai bakin kofa sannu taji yace "ki canza shiga ina jiranki a mota" Da sauri ta koma ɗakin Tata dauko hijab Sannu ta same shi a mota yana jiranta.. Babi wanda yayi magana har ya ajiye ya juya sannan ta shige cikin makarantar.. Zaune suke ita da kawarta Amra suna hira Bayan tagama bata labari me tace.. "Gaskiya Amra na kusa tafka kuskure wanda na kusa shiga Uku wajan yaya Habib" Shekeke Amra ta kalle ta tace "kyaji dashi jiddah, ke kika jama kanki ai asirin ki ya kusa tonuwa meyasa baki neme ni ba, kinsan fa Ni nayi abortion yafi sau biyu"! Da mamaki jiddah ta lalle ta "amma mijinki bai sani ba" "Tayaya zai sani tunda na hada baki da docton, ki bari zan raka ki ayi miki hankali kwance dama yanzu cikin ba wani kwari gareshi ba" Gaban jiddah ne ya fadi ta dafe kirji tana zaro ido harga Allah itama bata tashi haihuwa yanzu ba sannan tana tunanin da zarar ta haihu Habib zai cigaba da wulakanta ta tunda cikin yake so ba itaba amma kuma tayaya zata iya wannan gangancin.. Amra ce ta katse ta da "karki tsaya wani tunanin next week zamu fara exam zakizo kina shiga damuwa dan karatu saiya gagareki da wannan cikin wlhy" "Gaskiya Amra bazan iya ba Ina tsoro wlhy" Tsaki Amra tayi tace "bafa zai gane idan ma zai gane ai bazai dau wani action ba tunda dama ba san juna kuke ba hakan zaisa yaji haushi ya rabu dake" Shiru jiddah tayi tana tunanin maganganun Dr Ahmad na Karta sake kokarin zubar da ciki za'a iya samun matsala... Ji tayi Amra ta dafa tace "jiddah ki kwantar da hankalin ki idan na raka ki yanzu saiki tsare-tsaren da Dr yake dashi wanda asirin ki bazai tonu ba, da zarar kimgama school saiki samu ciki a lokacin ki haihu bakida wata damuwa".. Nan ma jiddah shiru tayi saidai ta yanke bin Amra kodan taji abinda Dr zaice.. Haka suka tashi tabi Amra suka bar makarantar kai tsaye asibitin da Amra tace suka nufa sunci Sa'a likitan na nan yana ganinsu ya fara dariya tareda yiwa Amra kirari da alamu sun saba.. "Ashe ana ganinku ma'am na zaki saina yanki ticket zan samu ganinki ai" Wani irin fari tayi da idanun sannan tace "aikasan Ni ɗin koda yaushe zaka iya ganina saidai idan kaine bakaso ba,, yanzu dai ba wannan ba akwai abinda ya kawo mu" "To inaji fadi yanzu a biya miki bukatar ki" Jiddah dake gefe tayi tsuru tana ganin ikon Allah, ta nuna sannan tayi masa bayanin suna so ne a zubar da cikin dake jikinta saidai 4month ne amma tayi zubar jini wancan satin sanadiyyar yunkurin zubar da Cikin... Murmushi docton yayi sannan yace "babu matsala mu dama ai wannan aikin mun kware a bangaren yaushe kuke so ayi aikin" Kallan jiddah wacce keta faman kallan wayarta tana tsoron karsu dade Habib yaje school bai dame taba.. Tabo ta Amra tayi tace yaushe kike so ayi abortion din.. "Emm...Ina ganin..kamar rana ita yau.." Dan murmushi Dr ya sakeyi ya gane a tsorace take yace "karki damu Hajiya komai zai tafi nrml ranar Monday kenan za'a yi saiku zo da misalin 8:30am Saboda lokacin ne nake Free" Godiya sukayi masa sannan Amra tace ta Dan jirata a waje" Fita jiddah tayi ta tsaya hankalin ta duk a tashe yake, saidai ta kusa 30m sannan Amra ta fito tana gyara head tie dinta... Napep suka tare suka tafi saidai jiddah hankalin ta duk ya tashi tana ki Amra na cewa wai docton yace subar kudin zai musu kyauta,,. Mamaki ne ya kamata hartayi niyyar magana sai kiran wayarta ya katse ta.. Mummunan faduwar gaba ne ya ziyarce ta, kasa daga wayar tayi harta gama ringing sannan tace mai napep ya kara sauri.. Habib ya dade a tsaye cikeda mamaki, meya hanata daukan wayar shi gashi dai yaji har an tashe su to ina taje Kenan.. Tuni ranshi ya gama ɓaci zuciyarshi tafasa kawai takeyi a take ya yanke wa kanshi jiddah tagama makarantar tunda iskanci da zata keyi kenan... A hankali yake bin su da ido itada kawar Tata mai suffar karuwai a cewar shi,, kallo daya jiddah tayi masa taji gabanta ya sake faduwa har suka karaso wajan Amra ta gaida ko kallan inda take baiyi ba ya shige motar.. Sallama sukayi da Amra sannan ta shiga motar a darare ta zauna.. Yadda yaja motar kaɗai ya isa ya tabbatar mata da bakaramin ɓacin rai yake ciki ba.. Dakewa tayi kamar kamar batayi laifi ba ta kawar da kanta gefe kawai.. Yana gama Parking ta fara kokarin buɗe motar saidai jinta tayi a kulle ya rufe ta,, kallanshi tayi tace "yaya Habib zan fita" Shiru yayi bai bata amsa ba kuma bai buɗe motar ba, saida ya dauki mintina sannan yace "daga yau na hana zuwa school dinki" A zabure ta sake kallanshi idanuwanta suka fara kawo ruwa, cikin marairaice murya tace "me nayi, pls Dan Allah kayi hakuri karka hanani zuwa plsss" Batareda ya kalli gefenta ba yace "nine mai baki umarnin fita,, right"!? Daga kai tayi tana zubar da hawaye.. "To nace bazaki sake zuwa ba"! Share hawayenta tayi tayi ta daga kai alamar to sannan ya buɗe motar yace "U can go".. Da sauri ta fita ta nufi palourn tana kuka, mommy dake zaune tana ganin shigowar ta da kuka ta ajiye wayar tana janyota jikin ta.. "Meya faru, wani abu yayi miki" "Mommy Wai bazan Kara zuwa school ba" ta fadi cikin kuka sosai.. "Ina Habib ɗin sam bazan yadda da wannan maganar ba tunda aiba shi ya sakaki ba".. "Ya sake ficewa" jiddah tace kawai tana cigaba da kukan ta.. Tambayar mommy tayi laifin da tayi masa,,. "Wai kawai dan fita dubo wata kasarmu ne nida Amra shine yazo ɗaukana bai sameni a school ɗin ba"".. Shiru mommy tayi dan tasan halin Habib wannan abin bacin da fushi ne a wajansa dole su kyale shi saiya sauko tayi masa maganar dan yanzu zai iya yin iko da matarsa ce ya hana babu kuma yadda zasuyi dole su kyale shi.... "Kinyi laifi jiddah da baki kirashi kin sanar dashi ba, yanzu ki bari zuwa Friday ya sauka a fushin sainayi masa maganar" "Yanzu idan bai yarda ba shikenan narasa karatu na" "A'a waya faɗa miki zaima yarda amma mubari zuwa Friday din, kinga Monday saiki je ko" Daga kai kawai tayi sannan mommy tace ta tashi ta shiga ta shirya ta fito taci abinci... Daki ta shiga dan shiryawa ta fito kamar yadda mommy tace.. Habibullah kuwa fasa fita yayi ya wuce part ɗinsa ya shiga bathroom saida ya daɗe sannan ya fito ya shafa wani tsadaddan mai da turare sannan ya kwanta yana tunanin inda jiddah ta tafi ɗazu.. Ko mommy tasa ya hakura to dole saiya rabata da wannan kawar Tata dan shi sam bai yadda da Ita ba.. Da kyar ya amince ya koma saboda mommy tasa baki saidai zuciyarshi takasa amincewa da komawar tata Amma babu yadda ya iya dole ya bar abin a zuciyarshi kawai.. Jiddah ta sanar da Amra Habib ne yasa kwana biyu bata shigo school ɗin ba, Amra tace shikenan ai tunda ya hana yanzu babu wata maganar zubar da ciki kuma amma kam ya cuceta dan yanzu ilimi shine kan gaba... Yau takama Sunday tun safiya jiddah ke kiran Amra ta faɗa mata Habib ya barta gobe Monday zataci gaba da zuwa makarantar ta, saidai bata same ta, duk jiddah bataji dadi ba dan gobe sukayi da Dr zataje ayi abortion ɗin.. Shigowar ta daki Kenan taji kira tana dubawa taga Amra ce da sauri ta daga "Amra lpy na Kira wayarki tun safe a kashe". "Lpy klau na ajiye ta kawai ta huta" "Ok, gobe zan shigo school saboda ya barni naci gaba da zuwa".. Wani ihu Amra tayi cikin murna tace saidai kuma harna kira Dr nace an fasa wannan maganar" Tsaki jiddah tayi tace "to waye yace ki kirasa kice nafasa, ko munyi dake"? "A'a nayi tunanin kin fasa ne tunda ga dalilin yi kuma yanzu babu wannan dalilin" "Kinga Amra kirashi kice gobe zan zo ayi abortion din nan dan bazan zauna da cikin mugu ba wlhy sai zali na yakeci kuma shiba sona yake ba kamar yadda nima bai san ba sanshi nake ba, sam banaso wannan week din ya fita baayi ba dan asirina zai iya tonuw...." Wayarta ce ta fadi tsabar kaduwa da karar bugo kofar dakin ta da taji.. Habib ta gani wanda yaji duk maganar da takeyi tun fara zancan nasu mommy ce tace yazo ya kirata suyi lunch duk da baiso zuwan ba amma sai gashi yaji abinda ya firgita shi,,, duk ya fita kamannin sa tsabar bacin rai fuskar shi tayi ja har jikin sai tsuma yake idanuwan nan nashi kamar banashi ba,.. jiddah tuni tafara kuka tana matsawa jikin bango yanayin sa kaɗai ya gama tsoratata, kokarin zubewa kasa takeyi saidai tuni Habib ya damko hannun ta cikin wani irin zafin nama ,, da jikin bango Ya haɗe ta tareda zuba mata kyawawan mari har hudu sannan ya wurga ta kan bed, tuni bakinta ya fashe sai jini dake zuba tana kuka wanda bashida sauti tsabar shewar da yayi mata.. Ran Habib ya gama ɓaci fushinsa ya bayyana wanda jiddah bata taɓa ganin a wannan yanayin ba, cikin huci ya dauki littafin dake kan mirror ɗinta da biro ya rubutun shi sannan ya dawo kanta ya sake bata wani kyakkyawan mari ya fice da sauri cikin sassarfa zuciyarshi a matukar dagule... Fitowar shi mommy tagani cikin wani irin yanayi saidai kafin tayi magana harya fice...... ✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 *🌈K͎a͎i͎n͎u͎w͎a͎ W͎r͎i͎t͎e͎r͎s͎ A͎s͎s͎o͎c͎i͎a͎t͎i͎o͎n͎* nα *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* *wαttpαd:-Ameenafirstladyy* 28 A hankali jiddah take sauke numfashi, saidai kana ganinta kasan bakaramar wahala tasha ba duk ta dan rame a fuska kamar wacce tayi jinyar sati guda... A gefenta mommy ta zauna tana kallanta cikeda da tausayi dan jiddah ba yar riko bace a wajanta kamar yar cikinta take jinta,, kallanta ta dawo da shi kan Habib dake tsaye yana kallan fuskar jiddan. "Habib ka koma gida kasa Laraba tayo abinci saboda karta farka babu abinda zataci"! Daga kai yayi sannan ya fice batareda yace komai ba. Yana fita mommy ta Kira Hibban ta sanar masa,, ciki kidima ya amsa da gasu nan tafe.. Cikin nutsuwa Habib yake driving ɗinsa saidai zuciyarshi taf take da sake sake Maganganun Ahmad, sam zuciyarshi takasa yadda da maganar tasa "to kodai yunkurin zubar da cikin tayi da kanta"? Ya tambayi kanshi yana dan dukan steering din motar tareda dan ajiyar zuciya,.. Cikin yan mintina ya karasa gida, a palour ya samu labara ya faɗa mata sakon mommy a takaice sannan ya nufi hanyar barin palourn,, tsayawa yayi sannan ya juyo ya shiga dakin jiddah yana bin dakin da kallo Kamar maisan ganin wani abu.. Ya dade a tsaye sannan ya karasa jikin mirror ɗinta, jakarta ya bude ya fara ciro wayar ta yana dubawa, cikin Sa'a yaga babu security, picture ɗinta ne a screen ɗin wayar hakan ya bashi damar kallan kyakkyawar fuskar ta sosai, tayi masifar kyau a hoton fuskarta dauke da kayataccen murmushi wanda yakara mata kyau sosai,, Habib ya dade yana kallan hoton sannan ya taɓe baki ya ajiye wayar dai dai da saukar idanuwanshi kan wani Tablet din magani,, da sauri ya dauko cikeda fargaban Allah yasa ba zargin sane zai tabbata ba. Tun Kafin yakarasa dubawa yaji zufa na karyo masa, a hankali ya zauna gefen bed ɗinta yana rintse idanuwanshi tareda dafe kanshi cikin matukar bacin rai da bakin ciki.. Ya dade zaune sannan ya tashi zai fice saikuma ya dawo ya dauki maganin ya fice zuwa part ɗinsa.. Bai dade da fita ba jiddah ta farka da kukan kiran mommy tana yunkurin tashi,, riketa mommy tayi tana fadin "gani jiddah ki nutsu kinji zaki samu lpy" Gefen mommy dake rike da hannunta ta kalla wasu zafafan hawaye na zubo mata,.. "Barina kira doctor yanzu" mommy ta faɗa tana ficewa zuwa office din docton. Rintse ido jiddah tayi hawaye suka sake zubo mata tareda tausayin kanta da mommy,,. "Mommy zanyi mata wasu tambayoyi pls" doctor Ahmad yace yana shigewa cikin ɗakin. A waje mommy ta tsaya saidai hankalin ta nakan jiddah gani takeyi kamar wani zai sameta.. Saida ya gama dube duben sa sannan ya kalli jiddah dake ta zubar da hawaye ya Kira sunanta cikin lallashi,, buɗe idanuwanta tayi saidai bashi take kallo ba gefe take kallo cikeda bakin ciki.. "Ki fara godewa Allah cikin da kikayi kokarin zubarwa bai zube ba"! A dan zabure jiddah ta kalle shi tanajin wani sanyi da farin ciki yazo mata koba komai tasan su mommy zasuyi mata afwa.. "Jiddah meyasa kikayi yunkurin zubar da ciki bayan kinsan mai cikin yanasan abinsa"? Ya jefa mata tambayar kai tsaye.. Wannan karan wani kallo tayi masa na neman karin bayani.. "Kwarai kuwa Habib yanasan abinsa, saidai zan baki shawara karki kara kuskuren sake yunkurin zubar da ciki dan zaki iya samun babbar matsala wacce zakizo kina da kin sani"! Kuka ne ya kwacewa jiddah cikin kukan tace "doctor banida wani sauran dana sani wanda ya kai na yanzu danake ciki, bansan da wanne fuskar zan kalli mommy ba kuma bansan irin hukuncin da yaya Habib zai yanke ba".. Hakuri Dr Ahmad ya bata sannan ya faɗa mata bai faɗa musu gaskiyar komai ba saidai bai sani ba ko nan gaba su sani..! Wani sassanyar ajiyar zuciya ta saki tareda yiwa Dr Ahmad godiya sannan tayi masa alkawarin bazata sake maimaita wannan kuskure ba.. Murmushi yayi ya fice zuwa wajan mommy dasu hibban da suka zo yanzu yace zasu iya shiga Yanzu.. "Sannu jiddah" Hawaye ne ya zubo mata na tausayin mommy Dan tasan da mommy tasan maganar nan bazata taɓa jin dadi ba. "Akwai matsala ne"? "A'a mommy"! Sannu suka dinga jera mata harda hibban da Afnan da suka zauna a dakin... Habib ya dade a part ɗinsa sannan ya fito ya amshi abinci ya wuce ransa a matukar bace fuskar nan tayi ja kana ganin sa kasan ransa a bace yake matuƙa sosai.. Kai tsaye asibitin ya koma yana Parking ya nufi ɗakin da aka kwantar da jiddan,, duk su mommy suna zaune ya turo kofar dakin,.. A hankali ya shigo babu wanda yaji sallamar shi dan bai wani bude baki ba, saidai hibban naganin yanayin sa ya tashi shida Afnan suka fice dan sunsan halin sa sarai gashi kuma a yadda ya shigo rai a matukar ɓace.. Jiddah wacce ke kwance batasan shigowar shiba saida taji mommy tace "Habib ka dawo".. A tsorace ta juyo inda taji mommy na Magana,,, karaf idanuwan su suka haɗu gabanta yayi mummunan faduwa dan ko ba'a tambaya ba tasan bakaramin ɓaci ransa yayi ba duk da batasan dalilin bacin ran nasa ba.. Wani kallo yayi mata wanda yasa saida cikin ta ya juya tayi saurin jiyar da kanta gefe tana maida numfashi.. "Akwai Wani abu ne? Mommy ta Tambaye shi ganin yanayin dayake ciki.. Girgiza kai kawai yayi sannan yayi hanyar fita. "Habib kaje ka samu Ahmad ko za'a iya sallamar mu" Baice komai ba ya fice cikin dacin rai da bakin ciki.. Hibban ya aika wajan Dr Ahmad dan haushin sa yake ji Musamman yadda ya iya zuba masa karya baya tunanin shima fa docton ne zai iya sani.. Barin hospital din yayi gaba daya ya koma gida dan yadda kansa ke masa ciwo sosai ga wani irin yanayi dayake jin kansa na tsananin zafin zuciya.. Dr Ahmad yayi dube sannan yace za'a iya sallamar su yanzu idan yaso Habib yasan abubuwan da za'a bukata na allurai da magunguna basai sun neme shiba.. Mommy tayi mamakin rashin Ganin Habib a asibitin saidai batace komaiba hibban ya kwashe zuwa gida.. Habib na kwance saman bed ɗinsa fitowar shi daga wanka kenan saidai har zuwa lokacin zuciyarshi na masa zafi ranshi yakasa kwanciya wani haushi da tsanar jiddah yaji a lokacin, sai lokacin ya tabbatar da jiddah bata sanshi bata kaunar shi tunda hartayi yunkurin zubar masa da cikin shi wanda yakejin tsananin san abinshi da kaunar sa.. Tabbas lokaci yayi da zai rabu da jiddah sannan ya kafa mata dokar karta sake yunkurin zubar masa da ciki idan kuwa ba haka ba saidai kotu ta rabasu dan yanzu yagama yanke zama da ita duk kuwa da irin soyayyar da yake mata,, wayar shi ce tayi kara kamar bazai dauka ba sai kuma ya mika hannu ya dauka batareda ya duba mai kiran ba.. Sultan kuwa jin Muryar Habib kawai ya tabbatar masa da ba lpy yake ba. "Lpy kuwa naji sound dinka haka"? "Sultan jiddah bata sona batasan haihuwa dani I don't know why"!? Ya faɗa cikin wani irin yanayi kamar mai san zubda hawaye.. "Kamar ya, bangane maganar taka ba" Labarin komai Habib ya bashi duk da yanajin zafin abin,,.. "Saki kuma Habib Ashe ma bakaji haushin abin ba"! "Kamar yadda ta nuna maka bata sanka batasan haihuwa dakai saika nuna mata kuskuren ta amma baka sake ta kai tsaye ba" Shiru Habib yayi baice komai ba saidai tuni dama zuciyarshi tagama yanke irin hukuncin da yake tunanin saidai tabbas bazai ci gaba da zama da jiddah ba duk da yanzu yanajn wani abu gameda ita saidai baisan ko menene ba..! Sallama kawai yayiwa Sultan ya kashe wayarshi dan yagama yanke hukunci bazai tsaya sauraran shiba a yanzu yadda yakejin kanshi,,, yanajin dawowar su mommy saidai ba fita daga part ɗin nasa ba saima gyara kwanciya da yayi.. Har dare su Afnan suna gidan itada afnan ɗin suna dakinta har hibban ya shigo yana tsokanar jiddan.. "Hankali ya tashi za'a rasa baby ko kunyar mommy bakuji ba keda yaya Habib"! Dariya sukayi shida afnan jiddah kuwa murmushin kawai tayi tana hararan hibban ɗin dake kallanta yana dariya,, "waya faɗa maka mun damu" "Gashi nan na gani harda su kuka"! Dariya ta ɗanyi tace "kaga laifi nane"!? "A'a ina fa bangani ba ko kadan saima kokarin ku dana gani dan da nine ko kaina bazaku gane ba" Dariya sukayi su duka sannan yace Afnan ta tashi su tafi,, "kai yaya hibban tun yanzu" afnan tace tana langabe kai. "Baku gama gulmar ba kenan ko dear" ya faɗa yana kallan Afnan tareda kashe mata ido. "A'a mun gama muje kar wannan ta tsayar damu danta ga tana tareda nata mijin a gidan so take na manta da nawa" suka fice suna mata dariya tareda sake yi mata sannu.. Suna tafiya ta fito palour duk da batajin dadin jikinta duk ba kwari, saidai mommy Bata palourn sai Laraba kawai dake fito da kayan da aka ci a abinci.. "Laraba ina mommy"? "Ta fita zuwa wajan Habibu wai zai siyo magunguna naji tace" Shiru ta ɗanyi sannan ta koma ɗakin ta ta kwanta tana rufe ido.. "Habib wai lpy kuwa kake naga duk ka sauya kamar bakada lpy" Habib dake kwance ya dan buɗe ido sannan ya tashi zaune "babu komai mommy" "Wani ya bata maka rai ne" ta sake tambayar shi. Baice komai ba sai kallo yabita dashi sannan yayi ƙasa dakai kawai yana jiran yaji me zatace.. Jin yayi shiru yasa mommy tagane miskilancin nashi ya motsa kenan hakan yasa tace "to shikenan ka tashi muje ka duba jikin jiddah saika siyo abubuwan da ake bukata tunda Dr Ahmad yace basai an neme shiba" Tsuke fuska yayi saboda ko ganin jiddah bayasan yi yanzu dan ranshi sake ɓaci zaiyi yanzu da sauri yace "basaina dubata ba, zan siyo komai idan na fita" "Shikenan to amma yanzu Yakamata kaje ka siyo dan kasan tana bukatar alluran da magungunan tunda babu wanda Dr Ahmad ɗin yayi mata" "Ok momma" ya faɗa yana tashi yabi bayanta.. ✍🏻✍🏻✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 *🌈K͎a͎i͎n͎u͎w͎a͎ W͎r͎i͎t͎e͎r͎s͎ A͎s͎s͎o͎c͎i͎a͎t͎i͎o͎n͎* *wαttpαd:- Ameenafirstladyy* nα *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ✍🏻 {30} Ganin yanayin nasa yasa mommy tagane ba lpy ba, da sauri ta nufi ɗakin jiddah saidai yanayin da taga bakaramin tashin hankali ta shiga ba, da gudu ta karasa wajan jiddan saidai ina jiddah bata cikin hayyacin ta ga jini dake zuba daga bakinta da hannunta data ji ciwo a wajan.. A firgice mommy ta fice zuwa dakinta ta dauko Car key ɗinta sannan ta kira Laraba ta taya suka dauki jiddah zuwa motar ta.. Bata kula ba motar Habib ba dan hankalin ta a matukar tashi yake, gudu sosai takeyi da kyar ta iya neman layin hibban tace ya sameta a asibiti ko tambayar dayake mata bata tsaya bashi amsa ba ta kashe kiran tare kallo jiddah ta mirror ɗin motar... Lokacin da hibban yazo tuni an shiga da ita dakin gaggawa,, yana gama Parking ya Kira mommy ta faɗa tana kusa da emergency room, cikin mintina ya karaso wajan,. Kallo daya yayiwa mommy yasan hankalin ta a tashe yake sosai saidai Baiga Habib a wajan ba kuma ba jiddah kenan waye a cikin su ba lpy.. "Mommy waye ba lpy"? "Jiddah ce"! Ta bashi amsa a takaice.. Bai sake magana ba suka hango Dr Ahmad tafe rike da abin lalubo numfashi.. Ita da hibban suna zaune suna jiran jin abinda ke damunta,,. "Mommy kiyi hakuri gaskiya jiddah bakaramin wahala tasha ba, danta bugu a hannun ta sosai sannan tayi rauni a hannun wanda yasa ta zubar da jini sosai, Saboda haka yanzu muna bukatar jini wanda za'a kara Mata nan da 1hrs" Gaban hibban yayi mummunan faduwa meyake shirin faruwa da jiddah ne,.,. Mommy kuwa kasa magana tayi sai hibban ne yayi dauriyar cewa a gwada nasa ko zaiyi dai dai.. Babu bata lokaci Dr Ahmad yaja shi lab aka gwada sannan aka tabbatar babu wata matsala zai iya bata jini,.. Kusan 4hrs sannan aka kai jiddah dakin hutu tareda sa mata Oxygen Dan janyo numfashin ta.. Mommy rasa me zatayi ma tayi dan hawaye yaki zuwa mata a irin halin data samu jiddah, hibban kuwa kasa daurewa yayi saida ya zubar da hawaye dan fuskar ta ta kumbura saboda marin da Habib yayi mata ga sawun yatsun sa nan kwance a kan fuskarta,.. Sun dade babu wanda yayi magana sannan hibban ya share hawayen shi yafara ba mommy hakuri.. "Nayi kuskuren hada jiddah da Habib dama nasan halin su ba daya bane amma nayi tunanin Habib zai sauya idan ya auri Jiddah, soyayyar danake yiwa jiddah ne yasa banaso tayi aure a wani wajan sai a cikin ku, nasan kanasan jiddah a lokacin amma saboda kwadayin canza halin Habib yasa na canja ra'ayin ku,, kai kuma kayi kawaici da hakuri da kuma sadaukar da soyayyar ta ga Habib duk da naji dadin haka amma yau kam nayi dana sani"! Mommy takarasa cikin rauni sosai.. Kwarai naso jiddah kamar yadda naso rayuwa ta saidai banji haushin hada ta da yaya Habib da akayi ba, saidai har yanzu inajin tausayin jiddah marainiya Allah""" hibban ya faɗa a zuciyarshi yana riko hannun mommy.. "dan Allah mommy kiyi hakuri zubar hawayenki bala'i ne ga yaya Habib addu'a kawai zamuyi jiddah ta tashi lpy".. (((Kome ƴaƴa sukayi kada iyaye su zubar musu da hawaye Saboda hawayen su bala'i ne ga ƴaƴansu✍🏻))) Share hawayen ta mommy tayi da sauri tana girgiza "ba Habib nake zubarwa da hawaye ba jiddah nake zubarwa ina santa kamar yadda nake san ku hibban dole na tausaya mata ga ciki a tareda ita" Hakuri ya sake bata sannan yace zai koma gida yasa Afnan ta hado mata abinci.. "A'a ka zauna tareda ita nizan je nayo mata yanzu Afnan tafara nauyi ba'a sata aiki ba".. mommy ta tashi ta fice.. Tsananin gudu Habib keyi saidai yakan sauke ajiyar zuciya lokaci zuwa lokaci,, kai tsaye booking flights yaje yayi ya samu Sa'a kuwa jirgin safiya ya samu zuwa Russia, yana dawowa gida ya wuce part ɗinsa ya shiga bathroom ya daɗe shower na zuba kansa sannan ya shiga bathtub ya salla wanka ya fito ya shirya cikin ƙananan kaya ya kwanta... Tunani yakeyi meyasa jiddah takesan zubar masa da cikin sa wacce irin kiyayya ce takeso ta nuna masa ta haka,.. Tsaki ya danyi sannan ya tashi yafara hada kayansa.. Mommy na zuwa ta dafa ruwan tea ta zuba flask sannan ta haɗa mata jellof ɗin cous cous, sannan ta shiga dakinta dan dauko wayarta.. A kasa ta samu wayar ta tarwatse, dauko wayar tayi sai idanuwanta suka sauka kan takardar da Habib ya rubuta, hannu na rawa mommy ta dauka ta buɗe.. Zaro idanuwanta tayi cikin mamaki da tsoron abinda idanuwanta suka gani.. Saki ne Habib ya rubuta saki daya1, ran mommy yayi matukar ɓaci sosai haka ta fice rike da takardar a hannun ta ta koma palour.. Tsaf ya gama haɗa kayan sannan ya nufo part din mommy hango motar ne ya tabbatar da ta dawo.. A plaour ya sameta ta dauki abincin zata fice,, tana ganinsa annurin fuskar ta ya ɗauke.. Har ƙasa ya duka saidai kawar da kanta gefe tayi.. Duk da baisan halin da jiddah ke ciki ba yanzu ba kuma bai kula da irin abinda yayi mata ba, amma yasan yayi laifi tunda mommy ta sauya fuska,.. "Gobe zan koma Russia dan Allah..." Katse shi tayi kafin yafara mata magiya dan yanzu bazata taɓa sauraran shiba yakaita makura a bacin rai.. "Allah ya kiyaye hanyar" tace tana barin palourn kai tsaye motar ta ta shiga ta fice daga gidan.. Ya dade a duke sannan ya shima ya fice zuwa part ɗinsa... A asibitin mommy ta samu Afnan harta zo taji dadin hakan sosai, dan hibban ma yana ciki bai fita ba.. suna nan zaune jiddah tafara motsi da gudu hibban ya fice kiran Dr,, mintina biyu suka shigo tare.. Oxygen din ya fara cire mata dan har lokacin jinin da ake kara Mata bai kare ba, a hankali ta buɗe idanuwanta da sukayi ja harda taruwar jini hawaye ne ya zubo mata ta fara motsa baki tana kiran mommy,. Dr Ahmad ne kaɗai dake kusa da ita yaji abinda take cewa sannan ya sanar da mommy ta karaso da sauri tana rike hannun jiddan.. "Mommy mutuwa zanyi hannu na zafi yake min" "Jiddah bazaki mutu ba muna na tare da ke kiyi hakuri kinji" Batace komaiba sai hawaye dake ta zubo mata mommy na sharewa.. Har akayi magrib jiddah bata sake magana ba, lokacin ancire roban jinin tana buɗe ido a hankali ta kalli su mommy. Dr Ahmad yayi mata allura sannan yace su bata wani abu ta danci.. Da dabara mommy ta dagata ta jingina da pillow sannan ta lallaba ta tasha tea mai kauri.. Zuwa dare jiddah tayi kwari saidai ba sosaiba har magana takeyi da murmushi dan kawai taga mommy ta fita a damuwa saidai har lokacin fuskar ta bata dawo dai dai ba.... 7am su mommy suna zaune tagama ba jiddah tea danshi take sha tun jiya, turo kofar dakin ne yasa suka kalli Kofar, Habib ne cikin kyakkyawar shiga ya shigo sai zuba ƙamshi yake, alamar shirin tafiya yayi.. Yau su hibban duk basu fita ba shima bai damu da rashin fitar tasu ba,,. Bai kalli gadon da jiddah take ba kamar yadda itama bata bata ko jiyo gefensu ba saima rufe ido da tayi danko ganin Habib batasan yi.. Mommy ma dauke kai tayi tana ji Habib ya kamo hannun ta yafara bata hakuri saidai bata juyo ba harya kau karshen maganar sa.. Juyowa tayi tace "Ni bakayimin laifi ba Habib kuma ban kullace ka abu daya na sani kawai ka hutar dani nemawa jiddah sakinta a wajenka, naga sakon takardar daka rubuta ta saki daya kuma mun gode sosai ka hutar damu nida ita, zatayi idda ta auri wanda takeso yake santa wanda bazai mata irin wannan cin mutumci ba"! Ba hibban da Afnan kadai na har jiddah saida gabanta yayi mummunan faduwa jin abinda mommy tace, hawayene suka zubo mata sai yanzu ta gaskata irin tsanar da Habib ke mata tunda harta kai ga ya saketa tana kwance a gadon asibiti.. Takaici yasa hibban barin ɗakin Afnan tabi bayan sa itama hankali a dan tashe... Sosai Habib yake ba mommy hakuri sannan ya faɗa mata abinda ya faru.. "Mommy koba yanzu ba nasan saita zubar da cikin nan, maganin da likitan ya bata magani ne wanda zai iya taba mata mahaifa saboda karfin sa, nayi kokarin ganar da ita amma takasa fahimta harta kai ga zata koma a karo na biyu ta zubar da shi wanda bansan mezai faru a lokacin ba.." "Wannan shine dalilin dayasa ka ɗauki mataki kafin taje ta zubar ɗin ko" "Da banji wannan maganar ba mommy yanzu da ba'a san halin da take ciki ba".. Kwarai mommy bataji dadin abinda jiddah tayi ba kuma gaskiya Habib ya faɗa saidai bazata taɓa goyan bayanshi akan wannan ba tunda shima ya tafka babban laifi daya kasa faɗa mata ya dauki hukunci dakanshi.... "naji, hukuncin da kayi kam yayi, nina hakura aure ne dai yanzu ka raba shi Saika tashi ka tafi Allah ya kaika lpy bazan taba fushi dakai ba Habib".. Jiki a sanyaye yayi mata sallama ta amsa ya fice zuwa airport.. 8am jirginsu ya daga zuwa Russia✈✈ Jiddah ma tasan gaskiya Habib ya faɗa saidai bazata taɓa yafe masa wannan wulakancin dayayi mata ba harya saketa bayan tarin wahalar daya bata amma bai haƙura ba.. Juyo da kanta tayi tana kallan mommy tana zubar da hawayen nadama,. Dakyar ta bude baki zatayi magana mommy ta dakatar da ita kawai tace "Ki bari ki samu lpy" daga haka ta tashi ta fice... *Ɑɱɛɛɳɑ ɱuรɑ*✍🏻 4/12/2019 *ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ғɪʀsᴛʟᴀᴅʏ*✍🏻[1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 вч *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ✍🏻 *wαttpαd:-ameenafirstladyy* *🌈K͎a͎i͎n͎u͎w͎a͎ W͎r͎i͎t͎e͎r͎s͎ A͎s͎s͎o͎c͎i͎a͎t͎i͎o͎n͎*🤝🏻 {31} Sosai mommy taci gaba da bawa jiddah kulawa kuma tana samun sauki sosai,, hibban da Afnan kuwa kullum suna asibitin dan anan yake barin Afnan ya tafi office saiya dawo yake ɗaukanta su tafi gida shima sai mommy tayi ta faɗan suzo su tafi saboda dare.. Kwanan su biyar jiddah ta warware sosai komai nata ya dawo nrml saidai rashin kwarin jiki saboda bata iya cin abinci sosai mommy tayi fadan harta gaji... Kwana biyu jiddah ta kara taci gaba da zuwa makarantar ta hankali kwance saidai bata sake kula Amra ba Dan haushin ta takeji ganin take kamar ita taja mata koma menene.. Tare da mommy suka cigaba da rainon cikin nata wanda yanzu yafara girma duk da sai Afnan ta riga ta haihuwa, dan ita tuni hibban ya hanata fita ko ina.. tunda Habib ya koma sau biyu kawai sukayi waya da mommy saidai sama sama suke gaisawa ta kashe wayarta, duk da yasan dalilin amma yanaso yaji lafiyar dansa sannan ya sake yiwa jiddah jan kunne akan karta sake yunkurin zubar masa da cikin dan yasan ta da taurin kan tsiya kodan ta bata masa rai zata iya attempt din sake zubarwa.. tsaki yayi kasa ƙasa sannan ya ajiye book ɗin dake hannun sa ya dauki wayar shi yafara neman layin mommy.. mommy dake zaune itada jiddah sakamakon weekend ne, taji karar wayarta.. lokacin wayar na hannun jiddah tana ganin Habib ne ta sauya fuska sannan ta mikawa mommy wayarta tabar palourn Dan batasan ma abinda zai sake hadata da shi.. itama mommy ba yabo ba fallasa ta amsa gaisuwar,.. shiru yayi bai sake cewa komaiba, jin haka yasa mommy tace "akwai wani abu ne kuma"? kamar bayasan maganar yac "a'a babu"! "shikenan ka kulada kanka" kafin yayi magana mommy ta katse kiran sannan tabi bayan jiddah zuwa dakinta.. a kwance mommy ta samu jiddah tana karatu, saidai kallo daya tayi mata ta gane tunani ne fal zuciyarta,. kusa da ita ta zauna sannan ta kamo hannun ta tareda kiran sunan ta. itama jiddan kallan mommy tayi saidai tuni hawaye suka zubo Mata. "meya faru"! mommy ta Tambaye ta.. cikin kuka jiddah tace "Ina tsoro kar yaya Habib ya mayar da auran mu, dan Allah mommy karki saurare shi dan wlhy kashe ni ne kawai bazaiyi ba muddin naci gaba da zaman aure dashi, nasan nayi kuskure kema bakiji dadin Hakan ba. " hararan da mommy tayi mata ne yasa tayi saurin yin shiru. "bana ce karna kara jin wannan Maganar ba tunda ta wuce, kuma saidai idan ke kika so Habib ya mayar dake"..! kallan mommy tayi tareda taɓe fuska cikin shagwaba tace "Allah mommy bazan so ba, to tayaya ma zanso komawa wajan wanda baya sona.." murmushi mommy tayi dan ta fahimci har yanzu da yarinta akan jiddah sosai. "kinsan Habib bayasan raini bayasan wargi da taurin kai saboda haka ko mezai hadaki dashi saiki kiyaye ko kiranki yayi karki dagawa dan yanzu ya gano bakyasan zama dashi ne da zarar kinyi masa wani abu magana daya kawai zaiyi ya mayar dake kuma shikenan kinjawa kanki saboda saiki kiyaye"... mommy tace tana saukowa daga saman bed din sannan tace "kinji dai abinda ne idan kika jawa kanki babu ruwana".ta fice tabar jiddah a ɗakin.. maganganun mommy sun shigeta saidai har zuciyarta ta kudurta bazata taɓa daukan wulakanci daga Habib ba a yanzu saidai koma menene ya faru amma bazata dauki wulakanci ba ita kam.. Habib kuwa yakai makura wajan ɓacin rai sai faman tsaki yake shi kadai da tunanin jiddah a ranshi"muddin ta zubar masa da ciki to tabbas matakin da zai dauka bazaiwa kowa daɗi ba tunda ya fahimci har yanzu batayi hankali ba,.. jin ana masa nocking ne ya katse masa tunanin sa sannan yabda iznin shigowa duk yasan Sultan... a hankali Sultan ya shigo saidai kallo daya yayiwa Habib ya gano ransa a bace yake, murmushi yayi sannan ya zauna yana daga kiran da Angelina tayi masa.. sun dade suna waya kamar karsu rabu sannan suka ajiye wayar yana maida kallanshi kan Habib wanda fuskar kamar hadari babu alamun fara'a ko kadan a kanta.. murmushi Sultan ya sakeyi sannan yace "ya akayi ne abban unborn"! dan sassauta fuskan nashi yayi saidai baice komai ba. "look habib fadamin Matsalar rike damuwa bashida wani amfani"! saida ya dauki dan lokaci kamar bazaiyi magana ba sannan yace "Sultan kasan maganata bata wuce ta waccan yarinyar" "wacce yarinyar kenan!?" Sultan ya tambaya cikin rashin fahimta. tsaki Habib yayi sannan yayi banza dashi dan gani yake Sultan ya gane raina masa hankali yake.. "ohhh! jiddah kake nufi wai"? "yahh! ita" Habib yace sannan ya faɗa komai har sakin da yayi mata sannan ya baro ƙasar.. sauke numfashi Sultan ya kalli Habib yace "gaskiya kayi kuskure Habib". harara Habib yabi shi dashi sannan yace "danayi me"? "jiddah tanada hakuri meyasa zakaga laifin ta bayan kaine mai laifi duk fa macen da nunawa kiyayya to zata iya abinda yafi wannan tunda itama ba sanka takeba, tana ganin kamar dan cikin kake santa duk ranar da babu zataga wulakanci to dole tayi yunkurin zubar dashi, kuma kaga har yanzu jiddah she's youn so saina lallaɓata sannan zata fahimce ka"! wani kallo Habib yakewa Sultan harya gama, murmushi yayi dan maganar Sultan ɗin ta karshe dariya ma tabashi wai kamar jiddah zai lallaba.. "yanzu me kake nufi" "ina nufin ka mayar da ita tunda har saita haihu sannan ta gama iddarta" "na mayar da ita,"! Habib ya tambaya cikeda mamakin kalmar. "eh mana haka nake nufi" tsaki Habib yayi yace "never, tayaya kake tunanin Ni zan cigaba da zama da wannan yarinyar"! mamaki ne ya kama Sultan dan shi sai yau ya dada tabbatar da cewa Habib baisan menene so ba.. duk yadda yaso ya fahimtar da Habib yaki fuskantar shi dole ya kyale shi suka rabu a haka tun kafin ya sauya mishi Yanzu... Habib ya dade yana juya maganar Sultan a ranshi saidai shi sam baya jin zai iya sakewa harya mayar da auran nasu dan yanajin zafin abinda tayi har yanzu... yau kwana biyu Kenan da Habib ya kira mommy saidai bai sake tunanin sake kiran nata ba duk da yanaso ya samu yaji lafiyar dansa saidai babu yadda zaiyi sai hibban ya kira yace ya dinga kaita duk inda zataje.. "to yaya". "karka kara sakacin barinta zuwa wani wajan ita kadai"! "Amma yaya akwai lokacin da nake tsaka da aiki mezai hana a samo mata driv.." da kakkausar murya Habib ya kira sunan shi sannan yace "kafi kowa sanin banasan gaddama, ko"! "I'm sorry Yaya" tsaki kawai yayi ya kashe wayar, har zai ajiye sai kuma ya yafara neman layin jiddah,cikin fushi ya kara wayan a kunnen shi saidai tun kafin ta daga yaji kamar ya katse dan baisan me zaice mata ba... cikin tsananin mamaki jiddah take bin wayar da kallo, maganganun mommy ta tuna yasa tayi saurin dagawa saidai Muryar a cunkushe.. "waye"? ta Tambaya cikeda rainin hankali.. wani bugu yaji zuciyarshi tayi cikin mamaki da takaici ya yanke kiran kawai yana huci.. ya dade yana juya abin a ranshi da kyar ya dauki wayar tashi ya tura mata da sako.. "karki sake fita batareda izinina ba, sannan hibban zai dinga kaiki duk inda zaki.."! Yana ganawa yayi sendind sannan ya shiga bathroom.. tsaki jiddah tayi ganin sakon nashi dan abin ma haushi ya bata wai karta sake fita waya faɗa masa yanzu zataji maganar shi bayan sakin dake tsakanin su, cikin takaici itama tayi masa reply.. "ohh Yaya Habib I'm sorry, saidai idan fita ta kamani zan fita kawai tunda baka nan, sannan ka kyale yaya hibban shima abubuwa sunyi masa yawa so zan dinga hawa na haya kawai, kuma ka rage isa yanzu akwai saki tsakanin mu watanni ya rage nayi iddah..." fitowar shi kenan yaji karar shigowar sako, saida ya gama shiryawa sannan ya buɗe sakon saidai kafin ya gama karantawa kanshi yafara wani mugun sara masa babu shiri ya saurin zama kan bed ɗinsa Dan yadda yaji wata juwa na daukan shi ga wani zufa dake karyo masa tako ina kamar ba daga wanka ya fito ba... ✍️✍️✍️✍️ [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ռǟ *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ✍🏻 *wαttpαd:ameenafirstladyy* *🌈ĸaιnυwa wrιтerѕ aѕѕocιaтιon*🤝 {32} A hankali ya dafe kanshi dayaji yana sara masa, sam yaƙi yarda da jiddah ce kemasa magana haka.. To kodai ba ita bace"? Ya tambayi kanshi sannan ya tashi da sauri ya dauki Car key ɗinsa ya fice ranshi a matukar ɓace.. Murmushi jiddah tayi dan tasan yanzu bakaramin bata masa rai tayiba, koba komai yau ta rama wulakancin daya saba yi mata,,wani murmushi ta sakeyi sannan ta nufi palour wajan mommy.. Zama tayi tana murmushi wanda yaki yankewa fuskarta, mommy ta lura da hakan saidai batayi niyyar yiwa jiddan magana ba saida taga murmushin yaki karewa.. "Wai lafiyanki kuwa kike ta faman murmushi ke ɗaya"!? Saita fuskarta ta ɗanyi sannan tace "babu komai fa mommy, Afnan ce ta kirani Wai Yaya hibban ya hanata fita" "To kuma shine kike mata dariya kema ai na kusa hanaki fitar".. Shiru jiddah tayi batace komaiba dan tasan idan taci gaba da jan maganar yanzu itama sai mommy tace ta daina fitar gaba ɗaya.. Har dare Habib yarasa abinda yake damunsa duk hankalin shi na kan abinda jiddah tayi masa saidai ya rasa taya zai nuna mata ƙarshen iskancin ta.. Wani irin murmushi yayi wanda har saida sautin sa ya fita sannan yayi kwafa yana jawo wayarshi yafara tura mata sako.. Yana gamawa ya tura mata sannan ya gyara kwanciyar shi yana ci gaba da murmushin wanda shi kadai yasan ma'anar sa... Jiddah kuwa tanaji wayarta tayi kara alamun shigowar sako saidai bata duba ba saima hirar su suka cigaba dayi itada mommy hankali kwance sam batayi tunanin Habib bane.. Sallama tayiwa mommy Dan bacci ne sosai takeji sannan ta koma ɗakinta ta shirin kwanciya.. Buɗe sakon ɗazu saidai a zabure ta tashi tana dan zaro hankalin ta a tashe dan tuni hawaye suka fara sauka kan fuskarta.. Cilla wayar Tata tayi gefe sannan taci gaba da kukanta mai tsuma zuciya,,.. "Meyasa Habib yakemata hakane, meyasa bayaso takarasa rayuwar ta da wanda takeso, shi ba santa yakeba kuma yanzu bazai bari ta auri wanda takeso ba Kenan shiyasa yayi saurin mayar da auran nasu dan yaci gaba da cin mutuncin ta kenan"? Rasa amsar da zata bawa kanta tayi sai kuka da taci gaba dayi sannan ta kwanta dan zazzaɓi yafara rufeta sosai,,, da kyar ta samu bacci barawo ya sace ta bata sani ba.... Da sassafe mommy ta sauko palour saidai tayi mamakin rashin ganin jiddah dan ta saba kullum tana riga mommyn fitowa palourn, har ta nufi ɗakin jiddan sai kuma ta fasa ta koma kitchen dan haɗa coffee Kamar yadda ta saba,,, Shiryawa jiddah tayi ta fito palourn, kai tsaye kitchen ta nufa wajan mommy ta gaida ta,. "Jiddah lpy kuwa"!? Kasa tayi da kanta sannan tace "babu komai mommy"! Hankalin mommy ya tashi dan tasan jiddah kuka tayi amma taki faɗa mata abinda ya faru.. "Jiddah I'm your mother, tell me what happened"!? "Mommy kaina ne yayimin ciwo jiya shine nayi kuka amma babu abinda ya sameni" Sauke ajiyar zuciya mommy tayi sannan tace "kinsha magani ko"? "Eh Nasha". "tam jeki barina na hada miki wani abu kici" da sauri jiddah tace "a'a mommy fita zanyi ai"! "ina zaki da safiyar nan, yau ba school ko kin manta ne"! "pls mommy gidan yaya hibban zanje, inaso naji yaushe zamu koma hospital awo ne" ta karasa tana kasa da kanta dan taga irin kallon da mommy ke mata. "toke da bakida lpy kuma kibari saiki kira shi a waya" "pls mommy Dan Allah kibarni naje" "gaskiya jiddah kin fara koyan yawo sosai, Yakamata yanzu kisan kinyi nauyi 6month fa amma ke naga kamar bakyajin nauyin jikin ki,,kije saiya dawo dake karki dawo da kanki" da hanzari tace "tam mommy ngd, I Miss you" ta faɗa tana ƙaƙalo murmushin dole.. "shikenan ki fasa zuwan kawai tunda idan kinje ma kewata zakiyi" mommy tace tana ci gaba da aikinta.. "a'a mommy aiba dadewa zanyi sosai" tana faɗa ta fice daga kitchen din da sauri kamar mommyn zatace ta dawo.. dan murmushi mommy tayi danta gane saurin da jiddan keyi.. napep ta tare har gidan hibban ɗin duk da ba wani nisa ne dasu sosaiba, tana zuwa ta biya me Napep din ta shige.. a palour ta samu Hibban ɗin yana kallan laptop ɗinsa, jin sallamar tane yasa shi dagowa, sai kuma yayi saurin tashi yana murmushi.. "yau uwar biyu ce a gidan da safe haka"!.. murmushi kawai tayi ta zauna dai dai fitowar Afnan tana "ashe yau za'a yi ruwa harda ƙanƙara kenan'! gaida hibban ɗin tayi saidai bai amsa ba sai Binta da kallo da yayi yanasan nazartar fuskarta. "jiddah akwai matsala ne"!? hawaye ne ya zubo mata takasa bashi amsa Afnan kuwa na ganin haka ta basu waje dan tasan magana ce ta kawo jiddan tunda ga alaman ta fara kuka.. Afnan na barin palourn hibban ya dawo kujerar dake opposite ɗinta cikin nutsuwa yace "fadamin meya faru"? share hawayenta tayi Sannan tace "yaya hibban wai yaya Habib ne yace ya dawo dani ɗakinsa..".. kuka ya sake kwace mata.. shiru hibban yayi na wani lokaci sannan yace "ma'ana kenan yanzu ke matarsa ce tunda bikiyi idda ba"? daga kai tayi kawai batace komaiba.. sai can sannan tace "narasa me yaya Habib yake game dani, ko soyake saiya gama sa rayuwata a bakin ciki sannan zai rabu dani, sam bani yakeso ba tuntuni ya fadi haka har saida ya rabu hankalin shi ya kwanta amma saboda ya cimma wani kudirin yake muci gaba da zama, zaman na bazan san wanne irin zama zankira shiba" kuka ya sake kwace mata.. tabbas hibban yasan halin yayan nashi saidai zuwa yanzu yafara gano nasarar auran jiddah dashi dan ya sauya abubuwa da yawa daga cikin rayuwar dan uwan nashi, bazai taba so wani abu ya rabasu ba a yanzu, saidai bazai iya jure ganin jiddah a wani irin hali na bacin rai koda yaushe ba, saboda yanajinta kamar kanwarsa da suka fito ciki dayane kuma koba komai shine silar kasancewar ta anan a Yanzu dole ya damu da damuwar ta kuma dole ya sama mata yanci da kwanciyar hankali koya yayane.. da kyar ya iya saita yanayin shi ya fara yi mata a hankali.. "shine kike kuka jiddah" ɗago kai tayi tana kallanshi da manyan idanuwanta, "ya kakeso nayi yaya hibban ko so kakeyi bakin ciki ya karasa Ni..."! dan murmushi hibban yayi sannan yace "karki damu, yanzu dai ki samu kici abinci sai muyi maganar".. "banaci na koshi" ta faɗa a hasale. dariya hibban ya farayi mata "ke matsala ta dake kafiya da taurin kai yanzu idan bakici abinci ba tayaya zaki fahimci abinda zance miki" share shi tayi kamar bada ita yake magana ba, har gabanta ya kawo abincin da kyar ya samu taci sannan yace ta huta tukun kafin yayi wanka ya fito.. a daki ya samu Afnan a kwance, zama yayi yana jawo ta jikinshi "babynah kalau kike kuwa"? dariya tayi tace "har kun gama maganar"? "a'a wanka zanyi tukun, muje kiyimin naga kinfini sauri idan ke kikayimin" "naki wayon salon duk ka jikani da ruwa bayan kasan yanzu nayi nawa" dariya shima yayi sannan ya shige bathroom din yana rufo Kofa... tsaf ya shirya ya fito palourn, lokacin Afnan na kitchen jiddah kuma na zaune inda ya barta.. zama yayi sannan yace "ina Afnan ɗin" "tana kitchen"jiddah ta bashi amsa.. "ohh! ya Allah na hanata aiki sosai saboda yanzu tayi nauyi da yawa amma takiji" hibban ya faɗa yana Binta kitchen din. jiddah na nan zaune suka fito rike da hannun juna sai shagwaba take masa ya barta tayi aikin shikuma yana mata dariya, bakaramin burge ta sukayi ba saitaji inama itace a wannan yanayin yanzu.. daki Afnan ta koma tace zata kwanta tunda yaki barinta tayi wanke wanken.. "yauwa my baby, dama bacci yakamace ki yanzu ai" hibban ya faɗa.. dariya tayi tabar musu palourn taje tayi kwanciyar ta abinta.. shawara hibban ya fara bata sannan yace tabi duk wata hanya da zata daina yawan hadata faɗa dashi.. "kenan naci gaba da zaman wulakancin"!? murmushi hibban yayi yace "jiddah ke kika jawa kanki wannan" da mamaki ta kalle shi tace "kamar yaya kenan"? "yaya Habibullah yana sanki jiddah halayenku ne yasa kuka kasa fahimtar juna,tun farko ke kika nuna kina tsoron shi sosai Sannan Nasha faɗa miki duk yadda kika dauki yaya Habib haka zaki same shi" "wlhy Habib baya kaunata ne yaya hibban, bazai taba sona ba kuma"..! "shikenan ki gwada ki gani nina faɗa miki yaya Habib yana matukar kaunar ki amma bazaki gane hakan bane saikin gwada shi"... a haka hibban ya dinga bata shawara karshe dai saida jiddah taji kwarin guiwa da kwanciyar hankali.. daga karshe jiddah ta kalli hibban tace ""Allah yasa karya bani matsala" "saidai kiba kanki matsala, amma yaya Habib bashida wata matsala zaki fahimce shi fiye dani".. saida Hibban ya tabbatar jiddah hankalin ta ya kwanta, sannan ya yace ta tashi ya mayar da ita gida tunda mommy harta fara kiran shi.. ✍️✍️✍️ [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ռǟ *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ✍🏻 *wαttpαd:Ameenafirstladyy* ________________________ *🌈ᴋᴀɪɴᴜᴡᴀ ᴡʀɪᴛᴇʀs ᴀssᴏᴄɪᴀᴛɪᴏɴ* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motives the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation _________________________ {33} Suna zuwa kuwa mommy tafara yi masa faɗa akan meyasa ya bari takai rana haka.. Saurin tarewa jiddah tayi da cewa "mommy kinsan idan na hadu da Afnan bamasan rabuwa" hararan ta mommy tayi tace aina sani dama daga yau dai bazaki sake fita ba saidai awo ko school" tana gama fadan haka ta wuce sama ta barsu.. Hibban bai wani zauna ba yayi mata sallama ya tafi dan yanada aiki a gida. Kwanaki sun ja kamar yadda cikin jiddah yanzu yakai 7month, yanzu kam tanajin nauyin kanta sosai, saidai hakan bai hanata zuwa makarantar taba sannan komai tanayinsa yadda Yakamata dan sosai ta mayar da hankalinta kan karatun nata.. Sam yanzu babu abinda ya sake hadata da Habib dan ko mommy yanzu ba sosai take samun shi a waya ba shiyasa take komai hankalin ta a kwance sannan take saurin manta wa dashi a matsayin matsalar ta, sai shirin exam kawai takeyi yanzu, bakaramin murna takeyi ba yadda abin yazo mata cikin sauki zata haihu batareda wani tunanin makaranta ba.. Yau da sassafe ta fito cikin shirin ta tana sauri sauri zata fice daga tsaye take breakfast din cikin sauri.. Mommy ce ta sauko palourn taga yadda jiddan ke sauri taki zama taci abincin cikin nutsuwa.. "Saurin duk tafiya school ɗinne"? "Eh mommy karna makara shiyasa" Kyaleta mommy tayi sannan ta wuce kitchen dan haɗa coffee. Hibban na shigowa ta ajiye cup din hannunta tana fadin "yauwa yayana dama kai nake jira" Dan kallanta yayi sannan yace "ai saki bari na gaisa da mommy ko" ya faɗa ya nufa kitchen din. Tare suka fito da mommy sannan sukayi sallama suka fice daga gidan.. Cikin ikon Allah jidda ta fara exam hankali kwance duk da cikinta yayi girma sosai amma haka take kokari takeyi batareda wata damuwa ba, kullum hibban ke kaita kuma ya dauko ta shima kuma ba karamin tausayin ta yake jiba.. Da asuba mommy ta tashi jiddah tace zata tafi asibiti Afnan ce zata haihu, cikeda murna jiddah tace zata bi mommyn amma tace babu inda zata bita tunda yau ma tana da exam.. Jiddah na cikin shiri taji karar wayarta, sunan mommy ne yasa tayi saurin picking,, wani dan karamin ihu tayi na murna jin afnan ta haihu. Mommy kuwa kashe wayarta tayi dan tasan halin jiddah yanzu saita fara yi mata shirme... Jiddah sai ita kadai ta tafi dan hibban bai samu kaita ba, har aka tashi suka fito, tayi mamakin ganin hibban yazo ɗaukar ta da murmushi ta karasa jikin motar tana tsokanar shi.. "Yaya hibban yau an ka zama baba" ta faɗa tana dan taɓe baki. Dariya yayi yace "saura ke zaki zama mama, wai wayaga jiddah da baby" shima ya faɗa yana mata gwalo.. Haɗe fuska tayi tace "wlhy kasan nikam zanyi kyau da baby ba Kamar kai ba".! "Ni dama nace zanyi kyau ne, saidai ke mu jira muga irin kyaun da zakiyi ai" Sarai tasan magana ya faɗa mata dan tsokana amma saita fuske ta shige motar yaja suka bar school ɗin.. Kai tsaye gidan shi tace ya kaita, acan ta samu mommy tana shiga ta fara murna tana daukan baby girl din tareda zuba mata ido kamar ta hadeyi ta.. Sai yamma itada mommy suka bar gidan,.. "Amma Afnan tasha wahala sosai ko mommy"? "A'a bata sha wata wahala sosaiba" "Amma naga ko magana batayi sosai" ta sake tambayar mommy.. Mommy dake driven kuwa dariya jiddan ta kusa bata amma sai make tace "nima dai bansan Dalili ba".. Sai tambayoyi jiddan ke mata tana bata amsa sannan tace "mommy mu wuce shopping pls" Batareda mommyn tace komaiba ta juya kan motar suka wuce shopping mall dan tasan idan ma bataje ba ta shiga Uku da shagwaban jiddah.. Sosai ta jidi kaya kamar hauka mommy kuwa duk siyayyar kayan babies tayi dan yanzu tana sane cikin jiddah ya shiga wata na tara, ba kananun kudi mommy ta kashe a lokacin ba ita kuwa jiddah batasan ma mommy nayi ba hankalinta yana kan kayan makulashe.. Yau su jiddah suka gama exam suka samu hutu bakaramin daɗi taji ba dan sunan Afnan zatayi shi hankali kwance gobe sai faman shiri sukeyi gidan.. Tun asuba ta tafi gidan hibban, acan ta shirya akaci suna aka zubar da dukiya dan hibban yayi bajinta ya zubar da kudi ba kananu ba,,.. Tunda Afnan ta tafi gida wanka badan hibban yaso ba ya barta dole ya dawo part ɗinsa Dan yace bazai iya zama gidan shi kadai babu matar sa ba duk sanda ta dawo ya saiya koma shima, jiddah tayi masa dariya da tsokana sosai saidai shi bai kulata ba saidai yayi dariya kawai... Dakin mommy jiddah ta koma da kwana dan dole mommy ta tilasta Tata ta koma dan kar haihuwar tazo ba kowa kusa da ita.. _pls kuyi manage da wannan_👈 coммenт and voтe 🤝🏻 *ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ*✍🏻 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ռǟ *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ✍🏻 *wαttpαd:-Ameenafirstladyy* *🌈ĸaιnυwa wrιтerѕ aѕѕocιaтιon*✍🏻 {35} ....Ranar suna yaro yaci suna Abdulmalik, mommy da hibban sunyi gwaninta dan an zubar da dukiya kamar hauka sun nunawa jiddah gata kamar yar cikin su, jiddah har kukan farin ciki tayi a boye dan batayi tunanin zata ga gata kamar haka ba, iya shagali kam anyi mutane sunyi sam Barka da tarin kyaututtukan da suka samu.. inna marka da sauran Yan uwan jiddan sunso tafiya da ita ƙauye amma fafur mommy taki yarda tace baza'a rabata da yarta ba idan tayi arba'in da kanta zata kawo ta, badan sun so ba bayan kwana biyu da sunan mommy ta haɗa musu sha tara ta arziki suka koma cikeda da farin ciki.. mommy da kanta take bawa jiddah kulawa sosai, Abdul kuwa sai kiba yake abinsa ga kamannin sa da mahaifin sa dake sake fitowa ziryan,.. iya so jiddah na nunawa Abdul dan yanzu kam ta gane ta kusa tafka kuskure na zubar da ciki da yanzu Abdul baizo duniya ba gashi yanzu wani irin so take masa wanda bazata iya fasaltashi ba.. kwana biyar ya rage ta koma school duk ta gama shirye shiryen ta, mommy Kam fafur tace ta dinga tafiya da Abdul dan bazata bar mata shiba.. "wlhy yacika fitina bazai barni nayi karatu yadda ya kamata ba" "ai sai kiyi kuma, naga mai zaici idan kika barshi a gidan"mommy ta faɗa bata kalli inda jiddan take ba. da sauri jiddah tace. "sai a siya masa Madarar jarirai"..! kallan bakida hankali mommy tayiwa jiddan sannan tace "jiddah ki fita ido na na rufe ke haka akayi miki, tsabar iskanci gaki da lafiyar ki za'a sai masa wata madara saboda wani Banzan karatu naki, to wlhy baki isa ba tun kafin ranki ya ɓaci banasan sake jin wannan maganar..."! a fusace mommy tabar palourn.. duk jikinta sai yayi sanyi sam batasan zata bata ran mommy haka ba, dole ta ɗauki Abdul tabi bayan mommy Dan bata hakuri.. .."mommy dan Allah kiyi hakuri zan dinga tafiya dashi wlhy"! juyowa mommy tayi yadda taga jiddan ta langabe kai har hawaye sun fara taruwa a idanun ta yasa mommy yin murmushi Dan batasan ganin hawayen jiddah ko kaɗan... "waya faɗa miki nayi fushi, banaso ne Abdul ki saba da bashi madara bayan kinsan irin tarin sinadaran na nonon uwa ke dashi ga ƴaƴanta saboda nace ki dinga tafiya dashi kinji yar albarka" ta faɗa tana shafa kan jiddah dauke da murmushi.. itama jiddan murmushi tayi tace "samun uwa kamar ki sai an tona sosai shiyasa koda yaushe nake ganin babu wanda yayi dacen uwa kamar ni, ina sanki mommy fiyeda yadda nake san kaina".ta karasa tana lumshe ido tareda kwanciya kan kafaɗar mommyn.. har zuciyar mommy saida taji wani dadi da farin ciki da wani sake jin saban soyayyar jiddah a zuciyar ta dan tun ba yau ba ta fahimci irin san da jiddan keyi mata sam bata kallan ta a matsayin marikiya saidai a koda yaushe tana mata kallan cikakkiyar MAHAIFIYAR ta, hakan yake daɗa sa shakuwa tsakaninsu.. "Allah yayi miki albarka jiddah, tashi maza kije ki kwanta ki huta zan tashe ki an jima zamu fita".. da murna jiddah ta tashi ta fice tabar Abdul a wajan mommy Dan hanata bacci zaiyi idan ta tafi dashi... jiddah ta koma school ɗinta kuma sunci gaba da karatu sosai, tareda danta take tafiya kuma bai hanata komaiba hankali kwance take rayuwarta yanzu duk tana sane da auran Habib dake kanta saidai har yanzu sunki fadawa mommy itada hibban Wanda ya hanata faɗan.. tuni Afnan ta dawo gidan ta shiyasa hibban ma ya koma dan dama rashin ta ne yasa shi komawa wajan su mommy,.. hankalin jiddah yanzu ya kwanta babu mai takura mata a bangaren komai hakan yasa take bawa danta kulawa sannan ta mayar da hankali kan karatun ta, wanda yanzu ya rage saura shekara guda ta gama gaba daya.. Abdul yayi wayo sosai kamar bashi ba yaro mai shiga rai, yanzu a gida jiddah take barinsa da Yaddar mommy tunda yanzu bai wani damu da nono ba gaf take ma da yaye sa gaba ɗaya tunda ya iya tafiya duk da tafiyar ba wani kwari tayi ba.. shekarar Habib daya da rabi kenan da komawar shi Russia wanda yanzu yayi dai dai da kammala karatun nashi na cikakken likitan mata wato (gynecologist).. yau ya kira mommy zai dawo jibi dan haka ta kira hibban akan gyaran gida.. hibban kuwa yayi farin ciki sosai jin ɗan uwansa kuma farin cikin sa zai dawo hakan yasa da ɗoki yace gobe zaizo da masu gyaran.. yau ta kasance Lahadi jiddah bataje school ba sannan batasan wainar da ake soyawa ba, dan tana dakinta itada Abdul yana sata nishadi dan ko kallan shi tayi saita tsanci kanta dayin murmushi mai tarin ma'anoni.. shigowar mommy ne yasa ta ɗago kai tana kallan mommyn dake rike da car key.. "tashi ki shirya Abdul ku same ni a mota"! da murna jiddah ta sauko tana fadin "ina zamu mommy" "gyaran jiki zamu kinga mun dade bamu je ba kuma naga kanki na bukatar gyara" jiddah kuwa harda tsallen murna dan sun kwana biyu basu je, sam bata kawo komai a ranta ba ta shirya Abdul suka fice.. a mota suka samu mommy, suna shiga ta ja motar suka bar Compound din...... *ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ* *⒞* ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ sʜᴜ'ᴀɪʙᴜ [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ռǟ *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ✍🏻 *_(FIRSTLADY'N KAINUWA)_* *wαttpαd:-Ameenafirstladyy* *🌈K͢a͢i͢n͢u͢w͢a͢ w͢ri͢t͢e͢rs͢ A͢s͢s͢o͢c͢i͢a͢t͢i͢o͢n͢*✍🏻 {36} ......wani haɗaɗɗen wajan gyaran jiki mommy ta kaisu, jiddah aka fara yiwa dan mommy saloon kawai akayi mata amma jiddah har gyaran jiki da kafa aka sake yi mata,.. fes jiddah ta fito da ainihin kyaun ta na Fulanin asali fatar ta har wani shining takeyi da haske kamar wata sabuwar amarya, ita kanta saida tayi mamakin kyan da tayi dan dama ta sauya sosai jikin ya sake fresh dashi ga wata yar kiba ta kwanciyar hankali da ta zauna mata tayi masifar kyau sosai.. sun dade a wajan sai yamma sannan suka koma gida bayan siyayyar da mommy ta wuce dasu har Abdul yayi bacci sai jiddah ce ta sabo shi a kafada suka shiga cikin gidan.. yau ta kasance Monday da sassafe jiddah ta shirya ta fito palour,.. mommy na zaune a palour tana shan coffee jiddah ta fito rike da Abdul, "mommy ni zan wuce" "shikenan sai kin dawo, amma ki jira hibban yazo ya kaiki mana" "na kira shi yace baya gida ma yanzu, zan je na hau taxi kawai" mommy Kamar zatayi Magana sai kuma ta fasa faɗa mata dawowar Habib ɗin tace "shikenan sai kin dawo". hibban kuwa baisha wahala samun masu aikin ba, suna zuwa suka fara aiki dama part ɗinsa kawai zasu gyara da kuma palourn mommy saboda haka da wuri suka gama suka tafi,,. hibban har zai tafi mommy tace yaje ya dauko jiddah dan itama batasan tana hawa taxi dinnan.... "mommy tasan Yaya Habib zai dawo kuwa'!? hibban ya tambayi mommy. "a'a bata sani ba amma yau zata sani ai"! hibban bai sake cewa komaiba yayi wa mommy sallama ya tafi ɗauko ta.. ..tunda yayi Parking take bin part din Habib da kallo dan tsaf ta gano saban fentin da akayi wa wajan, hand bag ɗinta ta dauka ta wuce ciki bata jira hibban ɗin ba, shima ya kula da yanayin ta saidai kawai yayi murmushi ya kuma ficewa daga Compound din.. da gudu Abdul ya cafe ta itama tayi sama dashi tana dariya duk da zuciyarta cikeda take da fargaba, kusa da mommy ta ƙarasa ta ajiye shi sannan tayiwa mommy sannu da gida ta wuce ɗakinta.. saida ta shirya tsaf sannan ta fito suka zauna cin abinci, kallan fuskar ta mommy tayi taga hankalin ta na kan abincin ta, ci kawai takeyi hankali kwance.. "jiddah kinsan gobe Habib zai dawo" duk da gaban jiddah ya fadi da maganar mommy Amma Sam bata nuna ba saima murmushi da tayi tace "na sani mommy, ai naga an gyara part ɗinsa yanzu, karfe nawa Flight dinsu zai sauka"!? "5:30pm yace min ɗazu, ai lokacin kin dawo ko saiki raka Ni keda Abdul ɗin"! shiru jiddah tayi kawai dan batasan zuwa saidai bazaki maganar mommy ba.. babu wanda ya sake magana sai Abdul dake ta gwarancin shi, shi kadai.. yau Tuesday, jirginsu Habibullah yau zai sauka tuni mommy ta gama shiryawa ta shirya Abdul bakaramin kyau yayi ba, jiddah kawai suke jira data dawo daga school yanzu, mommy ce ta kalli Watch ɗinta ta ɗanyi tsaki tana fadin "jiddah wai yaushe za'a daina jiranki a shiri ne, mu mun tafi nida Abdul lokaci yafara kurewa ke ki zauna a gidan sai mun dawo'! mommy ta faɗa tana daukan Car key ɗinta dake saman Centre table ta dauki Abdul suka fice.. tana jin tashin motar su ta sauke ajiyar zuciya dama basan zuwa takeyi ba, tabi lafiyar gado abinta tafara bacci.. 5:30 daidai Flight dinsu Habib ya sauka, mommy sai zuba ido takeyi ta hango,,, tafe ta hango shi yana tafiya kamar bayasan saukowa sanye yake cikin bakaken suit sunyi matukar amsar shi hasken fatar shi ya bayyana sosai, wani farin ciki ne ya mamaye zuciyar mommy Dan kallo daya tayiwa Habib ta tabbatar da kwanciyar hankali da hutu sun ratsa shi yadda ya haske mutanen dake kusa dashi kamar wani Balarabe a cikin bakar fata,, bakaramin sauyawa yayi ba kamar bashi ba yakara kyau da kwarjini uwa uba aji da gayu kamar wani matashi.. sannu a hankali ya sauko ya fara waige, idanuwan shi sanye cikin wani siririn farin medicated glass Wanda ya Kara masa kyau sai wani basar wa yake.. hango mommy da yayi ne yasa ya dan saki murmushi sannan ya karasa kusa da ita saidai cike da mamaki yake kallan Abdul dan ko ba'a faɗa ba ya gane shi... "Welcome back my son"! murmushi ya sakeyi sannan ya amshi Abdul, a hannun ta suka wuce mota tana rike da jakar shi.. sosai yake wasa da Abdul murmushi yaki yankewa a fuskarshi, mommy sai hira take masa amma sam hankalin sa baya wajan, lura da tayi hankalin sa na kan dansa yasa tayi shiru a zuciyarta tana jinjina irin tsantsan soyayyar Abdul ta gani a idanun Habib ɗin, tabbas yanzu ta yarda bakaramin so yakewa dan nasa ba dama kullum shine abin tambayar shi.. babu kowa a palourn iya waige waigen sa bai ganta ba, baiji daɗin hakaba amma sam fuskar shi bata nuna ba yana maƙale da dansa sai zuba masa shirme yakeyi,,. bai dade a palourn ba ya tashi saɓe da Abdul a kafadar shi, yayi magana kamar mai rada cikin dakakkiyar Murya "mommy zanje na ɗanyi wanka na fito" ya faɗa yana hanyar fita, "da Abdul ɗin zaka tafi" mommy ta Tambaye shi.. batareda ya juyo ba yace "eh zamu dawo yanzu" ya faɗa ya ficewa.. tsaff ya samu palourn nashi sai ƙamshi mai daɗi dayake fita ya samu komai nitse kamar yadda yakeso, hakama dakin nasa saida ya dade a tsaye sannan ajiye Abdul a kujerar dake cikin dakin ya bashi ƙaramar wayar shi ya shiga wanka.. ya dade a bathtub Sannan ya fito jin Abdul yafara aniyar zaiyi kuka.. jallabiya jalar sky blue ya zura ya dauki Abdul ɗin suka yo part din mommy, yana ajiye shi ya fice zuwa masallaci zuciyarshi cikeda da tunanin inda jiddah ta shiga... *ʄıγʂɬ ιąɖყ'ŋ ƙąıŋųщą* *🌹αмєєиα мυѕα ѕнυ'αιвυ*🌹 [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ռǟ *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ ✍🏻 *wαttpαd:-Ameenafirstladyy* {34} Yauma zaune suke suna breakfast jiddah sai juya abincin kawai takeyi amma ba wani ci takeyi ba, hibban ne ya lura da haka yace "jiddah meye hakane sai faman juya spoon kike kin kasa cin abincin".. Dan hararan shi tayi tace "kai kuma idanka na nan saika hadani da Mommy",,, "Jiddah ko bakida lpy ne.."? Mommy ta Tambaye ta cikin kulawa. Da sauri tace "a'a mommy kawai na koshi ne kinsan yau tare muka sha coffee ɗazu". "Ban yarda ba sauri ki cinye abincin nan ki tashi banasan gaddama"! Mommy ta mayar da hankali kan abincinta.. Sai hararan hibban takeyi a boye shi kuma yana mata dariya ƙasa ƙasa dan yasan ranta bakaramin ɓaci yayi ba, suna gamawa ta tashi zata wuce daki taji Muryar hibban yana ce mata "kizo mu fita shopping". "Banaso kaje kai ɗaya" ta faɗa ko jiyowa batayi ba, tanaji yana mata dariya mommy na masa faɗa ya daina.. Dariya ya kumayi yana faɗin"duk cikin yasa ta sauya kamar ba itaba ta ɗanyi muni".. Hararan shi mommy tayi tace "dayake ai matarka kyau tayi sosai da tanada cikin ko"? Shiru yayi baice komai ba dan ya gano mommy magana ta faɗa masa,,,har zai kuma yin magana mommy ta dakatar dashi tace "tashi ka ficemin daga palour dan bazaka dinga ciwa ƴata fuska a gabana ba".. Tashi yayi ya fice yana cigaba da dariyar sa yadda yaga mommy ta dage bataso ya fadi gaskiya... Jiddah kuwa tana zuwa daki ta kwanta, kiran Afnan tayi suka dade suna waya sannan ta kuma kiran khairat suka gaisa.. Tana gama wayar bata dade ba bacci yayi awon gaba da ita.. Satin Afnan uku da haihuwa amma kusan kullum sai hibban yaje, mommy tayi masa magana ya rage zuwan amma yaki karshe ma ce mata yayi saidai idan sun gaji su dawo masa da matarsa, hakan yasa Mom bata sake yi masa magana ba ta kyale shi.. Yau jiddah tun dare takejin ciwan mara saidai tayi ta juye juye a hankali dan kar mommy ta fahimta, saida safe sannan ciwo ya karu jiddah ta fara juye juye tana kiran sunan mommy cikin wahalalliyar Murya, a rude mommy ta Kira Hibban ya fito da mota, shima hibban a matukar kidima ya fito da motar lokacin tuni mommy ta fito da jiddan suka dauki hanyar asibiti.. Tun safe sai bayan azhar sannan jiddah ta haifo kyakkyawan baby boy ƙato dashi.. Murna wajan mommy da hibban kuwa ba'a magana bakinsu har kunne, yaron na hannun mommy sai kallan shi takeyi takasa tantance kamar yaron dan yafi jiddan kyau nesa ba kusa ba saboda hasken fatarsa sai tafi dangantashi da mahaifinsa... Sai yamma sannan aka sallame su saboda jiddan kalau take yanzu, cikin kankanin lokaci ƴan uwanta na ƙauye da sauran mutane suka san haihuwar jiddah, kowa murna yake musamman da sukaji lafiya take.. Zuciyar jiddah cike take fal da tunanin yadda zasu kaya da Habib, sau daya kawai sukayi waya tunda ya tafi shima ba wani magana sukayi ba, mommy ce kadai zata iya kiran shi ta faɗa masa duk da batasan yadda zai dauki maganar ba... jin an shigo dakin nata ne yasa ta ɗago kai tana kallan Hibban dauke da cup a hannun shi. Tea ne mai kauri mommy tabashi ya kawo mata ganin tana tunani ne yasa hibban tambayarta lafiya kuwa.. "Lafiya lau yaya hibban kawai banaji na nrml ne"! Murmushi yayi mata yace "keda jin nrml kuma aiba yanzu ba jiddah, gashi nan mommy tace ki shanye tas tana can tana hada miki abinci da kanta" ya faɗa yana hanyar ficewa daga ɗakin.. Kwana biyar kenan da haihuwar jiddah yan uwa da abokan arziki duk sunzo, su inna marka kuwa tun safe suka zo sai bayan suna zasu tafi, hankalin jiddah duk ya tashi dan batayi tunanin Habib bazai dawo ba,. Tana dakinta ita Afnan da tazo tun safe sai faman kuka takeyi afnan harta gaji da lallashinta dan batasan kukan me takeyi ba,sai hibban ta kira tace yazo yaji kukan me takeyi.. Mintina kadan hibban ya shigo cikin kyakkyawan shiga harda hula, ficewa Afnan tayi ta basu waje dan duk lokacin da zasuyi magana bata zama a ganinta yan uwane dole akwai sirri tsakanin su. Zama yayi gefenta bai tambayi inda jaririn yake ba tunda ya ganshi hannun mommy a palour. Kwantar da murya yayi yace "jiddah meya faru, Meyasa kikeso ki dinga sa kanki damu a damuwa"!? "Yaya hibban dole nayi kuka a wannan lokacin, shikenan yan uwana zasu fahimci irin auran danayi, wancan lokacin da kyar mommy tasa yazo suka ganshi amma wannan lokacin gashi bashida alamar dawowa har sai sun fahimci ba auran soyayya mukayi ba, tunda gashi ko murnar samun dan baiyi ba dama nasan hakan saita faru..."kuka ya sake kwace mata. Shiru hibban yayi baice komaiba, saida ya jima a zaune sannan ya fice zuwa dakin mommy.. Bata palourn sai baki dake ta hira abinsu, hakan yasa kai tsaye ya haura upstairs ɗakin ta ya shiga ya same ta zaune tana danna wayarta, ganin hibban a ɗakin ta ya tabbatar mata akwai maganar da ta kawo shi,.. wayar Tata ta ajiye sannan ta fuskance shi tace "hibban akwai wani abu ne"!? zama yayi yace "eh mommy"! ya faɗa yana zama kusa da ita. "mommy jiddah tana can tana kuka, kuma banga laifin taba dan yaya Habib ya wulakantata wancan lokacin gashi wannan karan ma zai maimaita, kaf yan uwanta bazasu ji daɗi ace yarinyar su ta auri wanda baya santa bata sanshi ba kuma suna gaf da gano hakan, dan Allah mommy ki takura masa ya dawo ko jiddah zataji daɗi"..! harya kai aya mommy bace komai ba saida ya tsaya da maganar tashi sannan tace "nina hana shi dawowa hibban, tun ranar data haihu yake damuna da zai dawo yanzu shigowar kama dashi na gama waya na ja masa kunne akan karya dawo, kafi kowa sanin halin Habib indai har ya dawo to sai yayi abinda ran kowa saiya ɓaci musamman akan jiddah".. "amma mommy yanzu ita jiddan me zata cewa yan uwan nata"! "karka damu Hibban na riga na faɗa musu mijin nata baya nan, tunda dama basu san cewa yanzu ba matarsa bace" da sauri hibban ya kalle ta zaiyi magana sai kuma ya fasa tunawa da yayi har yanzu mommy batasan auran Habib akan jiddah ba. "akwai wata Matsalar ne"!? mommy ta sake tambayar shi. "a'a mommy, saidai kije ki lallashe ta da kanki zatafi yin shiru"! "shikenan yanzu zanje".. jiddah na zaune a ɗakinta ta gama kukan nata mommy ta shigo, murmushi ta ƙaƙalo tayiwa mommy sannan hawaye ya fara zubo mata.. "jiddah ki daina damuwa haka mana, ni da kaina na hana Habib dawowa tunda dawowar tashi ba wani abu zata karemu da shiba, kuma kinga watanni ya rage masa ya gama karatun nashi, saikiyi fatan Allah ya fito miki da wani mijin na gari ki aura nasan dama ba komawa Habib zakiyi ba kuma nima na yarda da hakan, saboda haka ki daina damuwa kinji" daga kai kawai jiddah tayi jikinta yayi sanyi dan tasan bata fadawa mommy komai tsakanin ta da Habib ba tun bayan dayayi mata saki ɗaya.. haka mommy tayi ta yimata nasiha sannan ta fice daga ɗakin nata.. ✍️✍️✍️✍️✍️✍️ [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ռǟ *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* ǟʍɛɛռǟ ʍʊֆǟ✍🏻 *_(Firstlady'n kainuwa)_* *wαttpαd:-Ameenafirstladyy* *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION* {37} Jiddah na tashi daga bacci tayi Sallar magrib sannan ta fito palour dan neman abin da zataci. Mommy ce kadai da Abdul a palourn sai wasan shi yake yi, kusa da mommy ta zauna tana kwantar da kanta saman cinyar mommyn.. "Mommy yunwa nake ji sosai wlhy"!. "Gashi ba'a gama dinner ba saidai ki shiga kitchen ki dan dafa ko indomie ce" mommy ta Bata amsa tana shafa kanta. Tashi tayi ta wuce kitchen din ta fara girkin ta hankali kwance harta gama sannan ta fito, dai dai shigowar Habib daga masallaci.. Sam shi bai kula da itaba yana shigowa ya zauna yana jawo Abdul jikin shi.. Sororo ta tsaya kallan Habib cike da tsananin mamaki ganin yadda ya sauya kamar bashi ya kara kyau da kwarjini, kamar mara Laka a jiki itama ta karasa shigowa ta zauna kamar munafuka.. "Jiddah yadai ko bakida lpy ne"!? Mommy ta Tambaye ta Ganin ta zubawa abinci ido.. A hankali ya ɗago kanshi jin an ambaci sunanta, kallo daya yayi mata ya dauke kai tare da saurin rintse idanuwanshi yana jin wani abu na fizgar zuciyarshi.. "Babu komai mommy" ta fada sannan ta fara cin abincin tana satar kallan shi ta gefen ido.. Babu wanda ya sake magana a palourn dai Abdul dake wasannin shi, shi kuwa Habib kanshi na kan waya saidai kuma tunanin shi na kan jiddah,.. Mommy ce ta katse shirun da cewa su tashi suyi dinner an kammala.. "Na koshi Ni" jiddah ta faɗa.. "Ai dama nasan ke baci zakiyi ba tunda kinci abinci Yanzu" Habib ma tashi yayi ya nufi hanyar fita, mommy ta dakatar dashi "ina kuma zakaje"? "Part ɗina, Amma a kawo min coffee yanzu" ya faɗa yana ficewa.. Sarai jiddah ta gane da ita yake amma tayi fuska ta wuce ɗakin ta mommy kuwa batace komaiba itama taci abincin ta ta wuce ɗakin ta.. Tun yana jiran coffeen harya gaji bacci ya sace shi cikeda takaici.. Kashe gari yaba mommy tsaraba yace tabawa kowa, jiddah har mamakin kayan tayi musamman na Abdul wanda tasan ba ƙanan kudi ya kashe ba,... Kwanan shi biyu da dawowa kullum saiya dauki Abdul sun fita yawo ko zancan fara fita aiki bayayi, sai dare suke dawowa, yauma dawowar su kenan ya ajiye Abdul ɗin wajan mommy ya fice ya nufi part ɗinsa, yana zuwa ya kwanta bacci ya sace shi dama a gajiye yake.. Cikin dare ya farka tare da wani irin ciwan mara mai zafi wanda yake damun shi kwana biyun nan, da kyar ya iya jingina da jikin pillow dinsa yana rintse idanuwanshi tareda cije lips ɗinsa, saida ya kusa mintina goma sannan ya zufa ta fara karyo masa ya fara maida numfashi a hankali jin ya dan samun relief, drawer dake jikin mirror dinsa ya janyo, wasu magunguna tablet ya dauka tare da fita palourn shi.. Ruwa ya dauka cikin fridge sannan ya koma dakin sa, ya zauna gefen bed, tas ya shanye maganin yana wani yamitsa fuska, ya dade a zaune a wajan sannan ya kwanta cikeda takaici da ɓacin rai yana da matar sa amma duk yabi ya saka kanshi cikin wani tension din na ban, dole ma gobe ya cire kunya ya nuna yana bukatar matarsa dan yasan mommy ce ta hanata dawowa part din nasa duk da baisan Dalilinta ba, amma tabbas shi yanzu yakai makura da bukatar matarsa a kusa dashi duk da babu soyayya tsakanin su amma yanzu yana jin wani abu game da ita a koda yaushe, da wannan tunanin wani wahalallan bacci ya sake dauke shi.. Yau ya shirya fita aiki, da sassafe ya shirya ya nufi ɓangaran mommy, babu kowa palourn sai Laraba dake gogo goge, haurawa sama yayi dakin mommy ya sameta tana sawa Abdul kaya da alamar a wajan ta ya kwana... Yana gaida Mommyn ya dauki Abdul din sannan ya mayar da kallan shi ga Mommy "mommy anan ya Kwana ne"? "Eh dama anan yake kwana mana tunda ta yaye shi" "Yaye" ya maimaita kalmar kamar bai santa ba.. "Eh haka nace"! "Amma mommy Abdul ai bai isa yaye ba" ya faɗa a dakile.. "To ai saika nemo masa wata uwar tacigaba da shayar dashi tunda bai isa yaye ba kamar Abdul" mommy ta mayar masa da amsa a dan zafafe.. Shiru yayi baice komaiba ya ajiye Abdul yana mata sallama zai wuce aiki.. "A dawo lafiya" A zuciyarshi kawai ya amsa ya fice daga ɗakin.. Ya dade a palour yana kallan dakin jiddah kamar mai san ganin wani abu sannan ya danyi tsaki ya fice.. Ya samu sauƙin aiki sosai, dan yanzu Ameenu ke kula da sauran bangarorin hakan yasa yake da saukin aikin sosai.. Ko breakfast jiddah batayi ba hibban yazo kaita school, mommy ce keta faman faɗa akan lallai ta nemi wani abu taci acan karta zauna da yunwa danta fahimci yan kwana biyu nan gaba daya jiddah batada sukuni sosai akan abinci... Hibban da jiddah sai dariya suke yi ganin yadda mommy ta dage kamar zata ari baki.. "Au dariya ma kuke min ko"? Kwantar da kanta tayi a kafadar mommy tana murmushi "haba mommy mu mun isa, ki kwantar da hankali zanci abinci sosai acan banaso na makara ne shiyasa"! "Naji to ki kula da kanki" "Tom sweet momma" Hibban dake tsaye yana kallan su cikeda kauna da kuma sha'awar kaunar da suke nunawa junansu wani lokaci har mamaki yake.. "Mommy ni bakice na kula da kaina ba" hibban yace yana dan bata fuska.. Hararan shi mommy tayi tace "ban sanka ba ƴata kawai na sani saura kayi gudu da ita a mota"! Fita sukayi suna cigaba da yin dariya abinsu dan bakaramin dariya mommy ta basu ba.. hibban na ajiye ta ya wuce wajan aikinsa,.. saida suka fito lecture farko sannan ta wuce neman abinda zataci.. kaɗan taci abincin duk ya fice mata a rai saboda tunanin Habib daya tsaya mata a rai, tarasa dalilin da yasa tun ranar daya dawo ta ganshi zuciyarta takasa samun sukuni da tunanin shi a koda yaushe, haka kawai zata tsinci kanta da tunanin shi wani lokacin har murmushi kan suɓuce mata, saidai tayi aniyar rabuwa dashi ta har abada ta nemi wanda yake santa kuma bazai wulakantata ba kamar Habib ɗin duk da har yanzu a matsayin matar shi take dole ta nemi hanyar dazai karasa saki biyun dake tsakanin su, Gara tunanin shi ya kashe ta data koma gare shi.... *ʄıγʂɬ ιąɖყŋ ƙąıŋųщą* *ąɱɛɛŋą ɱųʂą*✍️ [1/1, 2:25 PM] Aunty Usee: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹 ŋą *🌹ʄıγʂɬ ιąɖყ🌹* ąɱɛɛŋą ɱųʂą✍ *{ʄırʂɬ ιąɖყ'ŋ ƙąıŋųщą}* *wαttpαd:-Ameenafirstladyy* _________________________ *_🌈Kainuwa Writers Association_* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https//www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation _________________________ {38} Sai yamma hibban yaje ya dauko ta jiddah har tausayin shi takeji ta yadda bai taɓa gajiyawa ba kullum yana kan hanyar kaita da dauko ta... "Yaya hibban kana kokari, yakamata a samomin driver ko kuma a koyamin tukin na dinga zuwa da kaina"! Ta faɗa tana kallan gefen shi.. Dan murmushi yayi yace "haba dai, saura watanni fa ki gama wanne gajiya zanyi saidai ki koya kodan kai Abdul school idan an saka shi".. Shiru kawai tayi tana dan murmushi bata sake magana ba har sukaje gida.. Mommy ce kawai a palourn itada Abdul dake jikinta a kwance, tana ganin shigowar jiddah ta fara murmushi, "kin dawo"? "Eh mommy, ya gida"! "Kalau, yanzu dan rigimar taki ya gama kukan kiran ummin shi" ta faɗa tana kallan Abdul ɗin .. Dariya jiddah tayi tace "gajiya yayi kenan yayi bacci, da baiyi bacci ba da yaya hibban ya tafi dashi can ai". Da sauri hibban yace "tab nayi yaya dasu su biyu duk yan rigima ne ai"! Dariya mommy tayi sannan hibban yayi musu sallama ya tafi gida.. Har dare jiddah bataji motsin Habib a gidan ba gaba daya, tanasan tambayar mommy saidai batasan tayaya zata fuskance ta da Maganar ba hakan yasa tayi shiru da bakinta kawai saidai zuciyarta cike take da tunanin inda ya tafi har bayan isha haka. Shi kuwa Habib yana office ayyuka sun tsayar dashi, duk haushi ya kama shi ga dare yayi dole ya ajiye komai ya nufo gida yana faman tsaki,.. Ko mai Gadi bai kula ba dayake faman yi masa sannu da zuwa fuska a haɗe ya shiga palourn mommy yaga babu Kowa, tsaki ya kumayi ya wuce part ɗinsa rai a dan ɓace kamar ya hadiyi zuciya haka yake ji.. Kamar yadda ya saba al'adar sace sai yayi wanka yake kwanciya, yau ma yana fitowa ya sanya sleeping dress ya Kwanta, saidai kuma baccin sam yaƙi zuwa saima ji yayi duk baccin da gajiyar sun gudu,, tashi yayi yana duba agogon dake jikin drawer gefen bed ɗinsa, ganin dare baiyi wani sosai ba 8:30 ya tashi ya nufi part din mommy.. Kai tsaye dakin ta ya wuce dan yayi mata maganar ya kamata jiddah ta dawo part ɗinsa kafin ya kamalla ginin sa dayake san Zama dan yasan tabbas mommy zata fahimci abinda yake nufi.. A hankali ya tura ɗakin nata, a zaune ya sameta tana yiwa Abdul addu'a wanda ke bacci kusa da ita, jin sallamar shi ne yasa ta ɗago kai cikeda mamaki tana kallan shi saidai kallo daya tayi masa ta dauke kai tana fadin "lafiya Habib a cikin wannan daran"!? "Abdul yayi bacci ne"? Ya mayar mata da tambayar.. Wata harara ta maka masa "au Ina tambayar ka shine Nima ka maido min da tambayar Ko"? Shiru ya ɗanyi yanaso yayi Magana amma yarasa ta ina zai fara. Ganin yanayin sane yasa ta gane da magana yazo.. "Habib menene fadamin ina sauraran ka"? Shiru ya sakeyi na wasu mintina sannan yace "mommy dama.. maganar....""" Katse mommy tayi ganin yana kame kame "idan bazaka iya faɗa ba ka tashi ka ficemin a ɗaki zan kwanta"! "Maganar waccen yarinyar ce dama nace Yakamata ta dawo part ɗina kafin na gama.." "Dakata Habib, wai jiddah kake nufi.."? Gaba daya jikinsa yayi sanyi tunda yaga ta dakatar dashi yasan abu ne mai wahala ta Amince... Kai kawai ya iya daga mata batareda yace kala ba.. Kallan mamaki mommy tafara yi masa da tsananin bacin rai "Habib kana kuwa da hankali, tayaya matar da kayiwa saki ɗaya tayi iddah zakace ta koma part dinka da kwana koka manta yanzu ba matarka bace har saita yarda sannan za'a mayar da auran ku.." Shiru yayi bai bata amsa ba dan Maganar tata ta gama daure masa kai.. "Da alamar zama cikin waɗan da ba musulmai ba yafara sauya ka, tsabar rashin kunya kazo gabana kanamin zancan jiddah..."ta karasa maganar tana kallan face ɗin sa da yayi kasa da ita.. Jin tayi shiru ne yasa Habib ya ɗago kai, jijiyoyin kanshi duk sun tashi, kallo daya tayi masa taji jikinta yayi sanyi saboda tabbas tasan yanzu Habib dole ya bukaci mace kusa dashi saidai bazata biyewa san zuciya ta sake hadashi da jiddah a karo na biyu ba dole tabawa jiddah dama ta samo miji irin wanda takeso yake santa.. Kwantar da murya tayi ta sigar lallashi tace "Habib kayi kuskure na sakin jiddah da kayi samun mace kamar ta zaiyi wahala a yanzu, amma nabaka dama ka gwada Sa'a ka lallaɓata ko zata amince ta sake zama dakai.."! Nan ma daga kai kawai yayi dan ya zama speechless gaba daya a yanzu abubuwan sun gama daure masa kai ɓacin rai da takaici ya hanashi yin magana tabbas yasan mommy batasan har yanzu da auran shi da jiddah ba, to Amma Meyasa bata fadawa mommy ba gashi yanzu yasan mommy bazata taɓa yarda da maganar shiba"... "Yanzu ka tashi kaje ka huta.."! Tashi yayi sannan yace saida safe ta amsa masa, harya kai bakin kofa ta kira sunanshi "kaji dai abinda na faɗa maka ka lallaɓata ta amince sannan zan iya wani abu"! Daga kai ya sakeyi sannan ya fice.. A palour ya tsaya yana dafe kanshi cikeda bacin rai, ɗakin jiddah yake kallo kamar wanda zai gano ta, a zafafe ya yakarasa kofar dakin nata sannan ya murda handle din Cikin Sa'a yaji a bude dakin yake, kai tsaye ya shiga cikin.... Cikin baccin ta taji an buɗe dakinta a ɗan hanzarce ta buɗe idanuwanta, ganin Habib ne ya shigo yasa ta tashi a zabure tana saukowa daga saman bed ɗinta haɗe da zaro idanuwa.. "Me kakeyi a ɗakina Yanzu"!? Ta tambaye shi tana dakewa bata nuna alamar tsoro ba... Hura hanci yayi yana fitar da iska ta bakin shi sannan yace "mene, kina nufin nayi laifi ne bayan dakin matata ne"! Ya faɗa batareda ya saki fuska ba.. "Kaine kasan wannan"! Ta mayar masa da amsa.. Wani takaici ne ya kara kamasa ganin yadda take mayar masa da amsa kai tsaye.. Gyara tsayuwar shi yayi yana kokarin boye fushin sa, "meyasa baki fadawa mommy na dawo dake ba".. "Zata sani amma sai lokacin da ka datse ragowar igiyar auran mu dakai.." Shiru yayi yana juya maganganun nata a ranshi tabbas yasan harda yarinta ke damun jiddah saidai yau duk fushin sa yakasa yi mata komai.. Wani murmushi mugunta yayi sannan yafara matsowa kusa da ita, ganin haka yasa jiddah cikin tsoro tafara ja da baya..... *ąɱɛɛŋą ɱųʂą* *ʄıγʂɬ ιąɖყ* 31/12/2019 [1/1, 8:06 PM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: 🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* ŋą ąɱɛɛŋą ɱųʂą✍ *🌹ʄıγʂɬ ιąɖყ🌹* *wαttpαd:-Ameenafirstladyy* *{fírѕt lαdч'n kαínuwα}* {39} Jinta tayi a jikin bango hakan yasa ta buɗe idanuwanta da sauri, saidai a tsaye ta ganshi ya kafe ta da matattun idanuwan shi masu rikita ta... Saurin yin kasa da kanta tayi jin wani abu na taso mata game dashi.. "Ɗago idanuwanki ki kalle ni sannan ki sake maimaita kalmar bakya san sake zama dani"! Ya katse mata tunanin ta.. Da sauri ta ɗago kanta saidai takasa kallan kwayar idanuwan shi hakan yasa ta kalli gefe.. Kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya juya ya fice cikin sassarfa.. Ajiyar zuciya tayi sannan ta zauna a gefen gadon ta hawaye na zubo mata wanda batasan kona menene ba, tabbas tasan karya takeyi tace batasan Habib dan shi ne mutum na farko da zuciyarta ta tsumu da tunanin shi tun kafin idanuwanta su ganshi tana san Habib irin soyayyar da bazata iya fasalta shiba saidai bazata juri irin wulakancin dayake yi mata dole ta nemawa kanta yanci koda hakan zai sa ta sallama farin cikin ta to amma tayaya zata jure rabuwa dashi ɗin anya kuwa zuciyarta zata iya karbar wannan hukuncin".. rashin samun amsar tane yasa ta rufe idanuwanta tana hasko Habib a zuciyarta.. Habibullah kuwa daran yau gaba daya sam bacci baiyi nasarar sace shiba, gaba daya tunanin jiddah yau yayi "tayaya zai iya rabuwa da ita, meyasa yakejin zuciyarshi bazata iya rabuwa da itaba, meyasa yake jinta a jinin jikin sa"..! Da wannan tunanin sai sallar asuba yaji ana kira, baiyi mamaki ba danshi dama ƙaguwa yayi safiyar tayi.. Alwala yayi sannan yayi nafila ya dade a zaune kan mat sannan ya fice masallaci jin ana kiran sallar shiga.... Wanka yayi ya shirya cikin kyakkyawar shiga ya nufi wajan mommy, a palour ya same su itada Abdul yana shiga Abdul yayo kanshi da gudu.. "My boy harka tashi"! Ya faɗa yana kama hannun shi suka koma wajan mommyn.. "Good morning momma"! "Morning too, har zaka fita'. "Eh" ya bata amsa a takaice.. "Ka wuce da jiddah dan Yakamata hibban ya huta haka"! Shiru yayi sannan ya nemi waje ya zauna kawai, fitowar jiddan ne yasa ya dan daga kai ya kalle ta sannan ya yaci gaba da danna wayarsa.. Tana ganin shi tayi saurin nutsuwa sannan gaida mommy ta juya ta gaida shi.. Lafiya" kawai yace sannan ya fice yana faɗin "ki sameni a mota"! A mamaki ta kalli mommy "mommy shine zai kaini"? "Eh nice nace ya kaiki" Handbag ɗinta ta dauka sannan ta fice dan tasan bayasan jira.. A zaune ta same shi cikin motar ita kawai yake jira, tana shiga ya tayar da motar suka fice.. A wani shopping na saida drinks ya tsaya, bai wani dade ba ya fito rike da wata ƙatuwar leda, kallo daya tayi masa ta waigar da kanta gefe, shima baiyi wata magana ba yaci gaba da driving ɗinsa batareda ya kalli inda take ba.. Har sukaje makarantar babu wanda yayi magana sai picking call kawai da yayi.. Yana gama Parking ta buɗe motar tayi ta fice taku daya tayi taji yace "Wait"..! Tsaya tayi sannan ta juyo tana kallanshi, zagayo wa yayi rike leda a hannun shi da alamar wacce ya tsaya yayi shopping ce.. Miko mata yayi batare da yayi magana sai kafe ta da ido yayi yana kallanta alamar ta karba.. Amsa tayi cikeda da mamaki a ranta dan bata taɓa tunanin ita ya tsaya siyawa ba.. "Nawa ne"? Ta tambaya tana san gasgatawa.. "Eh, yayi sanyi da yawa ki bari yadan huce sannan kisha" ya faɗa yana juyawa zai tafi.. "Amma..naga kaima bakaci komaiba". Cak ya tsaya jin Maganar tata saidai bai jiyoba, baiyi tunanin ta damu dashi haka ba, wani murmushi yayi wanda har saida ya fitar da sauti sannan ya juyo yana kallan ta. "Eh banci ba, kin damu da hakan ne"!? "A'a ban wani damu ba saidai Yakamata ka nemi wani abu kaci kaima" Dan tsuke fuska yayi dan yaji haushin amsar Tata sannan yace "I'm full" ya faɗa yana juyawa.. Harya kama handle din motar ya rike saidai jin Maganar ta yasa ya sake tsayawa cikeda tsananin mamaki... "Mene"! Ya tambaye ta yana sake kafe ta da wani irin kallo wanda ke sake rikita ta. "Eh nace nima bazan ciba idan bazakaci ba"! Ga mamakin ta saita ga yana murmushi tare da kallan gefe yana wani motsa baki zaiyi Magana.. Takowa yayi har kusa da ita sannan ya zura hannuwanshi cikin aljihu ya kalle fuskarta.. "Shikenan saiki zubar tunda bazaki ci ba".. yana faɗa ya juya ya shiga Mota ya barta a wajan tsaye.. Cikeda jin haushin kanta tace "to maye nawa a ciki dana nuna na damu dashi karma yaci mana, gashi nan ya wulakanta Ni a Banza".! Tayi tsaki tabar wajan saidai har zuciyarta taji dadin hakan.. Tuki yake yi fuskar nan ba yabo ba fallasa, saidai kallo daya zakayi masa ka gane yana cikin farin ciki.. "Ashe ta damu dani" ya tambayi kanshi yana lumshe idanuwan shi.. Sam ya kasa yarda da abubuwan dayake tunanin dan wannan abun daya shiga tsakaninsu daga daran jiya zuwa yau yakasa yadda dashi ji yakeyi kamar bashi ba zafin kanshi duk ya ragu.. Gaba ɗaya yau jinshi kanshi yakeyi kamar bashi ba, har mutanan wajan aikinsa sun fahimci hakan har tsokanar shi Ameenu yayi amma bai kula shiba sai haɗe fuska yayi yace "shut up and get out" Sum sum Ameenu ya fice ganin ya dawo Dr Habibullah dinshi lokaci guda.. Lokaci zuwa lokaci yake kallan Watch ɗinsa, Sam bayaso ya makara wajan dauko ta.. Message ya tura akan ta jira shi zaizo ɗaukan ta idan sun tashi.. Lokacin tana zaune a capteria duk da ba abinci take ci ba tunani ne fal zuciyarta akan Habib.. Tana cikin tunanin ne taji karar shigowar message, ganin sakon yasa ta saki wani kayataccen murmushi tabbas yanzu ta yarda da soyayyar Habib ta gama rike mata zuciya kamar yadda ta lura shima ya fara canzawa.. *hαppч nєw чєαr*❣ 1/1/2020 {wєdnєѕdαч } [1/6, 8:21 AM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 ŋą *🌹ʄıγʂɬ ιąɖყ🌹* ąɱɛɛŋą ɱųʂą✍ *{ʄıγʂɬ ιąɖყ'ŋ ƙąıŋųщą}* _____________________________ *_🌈 Kainuwa writers association_* ```{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/Kainuwawritersassociation _____________________________ {40} 5pm dai dai ta fito daga lecture a matukar gajiye, ita harta manta ma sunyi dashi zai dawo daukan ta sai ganin shi tayi tsaye jikin motarshi yana kallan Watch ɗinshi.. Da kyar ta iya ƙarasawa kusa dashi tace "sannu da zuwa"! Can kasa ƙasa ya amsa da yauwa sannan ya buɗe mata gaban motar ta shiga shi kuma ya zagaya ya shiga ya tayar da motar.. Sun ɗanyi tafiya mai nisa babu wanda yayi Magana kamar lokacin tahowar su.. kallan gefenta yayi yaga ta kwantar da kanta jikin seat tana dan cije lips ɗinta.. "are you okay"!? ɓude idanuwanta tayi tace "I'm okay" sannan ta mayar ta rufe.. bai sake cewa komaiba yaci gaba da abinda yake har suka je gida.. yana gama Parking jiddah ta fice zuwa part ɗinsu, shima part ɗinsa ya wuce ya duba wani file sannan ya nufo ɓangaran su. tana shiga palourn taga babu kowa kai tsaye ɗakin ta ta shiga tayi wanka, bata wani dade ba ta fito ta shirya cikin doguwar riga yar kanti sannan ta fito palour.. tana fitowa dai dai shigowar Habib, kallan kallo suka shiga yi, itace tafara janye idanuwan ta, ta karaso ta zauna kan kujera sannan shima ya zauna yana amsa waya saidai idanuwan shi na kanta yana nazarin ta ganin yadda ta ɗan sauya.. mommy ce ta sauko palourn "har kun dawo"? a hankali jiddah ta buɗe idanuwanta tace "eh mommy"! "saiku wuce kuci abinci" "to" kawai jiddah tace amma bata tashi ba. tana jiran ya gama wayar. yana gamawa ya tashi yace "mommy saina dawo".. da mamaki suka kalle shi, "ina kuma zakaje"? mommy ta Tambaye shi. "zan koma office ne inada baki daga Abuja zasu ganni" yana daukan jacket dinshi ya fice.. takaici ya hana jiddah magana musamman da tuna tun safe baici komaiba, duk da batajin dadin jikinta haka ta tura abincin ta dawo palourn tana tambayar Abdul. "Sai Yanzu kika tuna dashi, to hibban yazo ya tafi dashi tun safe. " dariyar dole tayi tace "aikuwa yaya hibban ya kyauta dan mun huta da rashin jin shi.."! tunda ya koma office yake aiki, kusan mutane goma ya gani waɗan da suka yanki card, yana cikin hada files ɗin dake kan table dinsa wata nurse ta shigo.. "yallabai Habib akwai sauran mata uku kuma sun yanki card tun azhar".. da wani kallo ya bita wanda yasa tayi saurin bashi hakuri "sorry yallabai" tsaki yayi sannan yace"kya iya sallamar su zuwa gobe" yana faɗa ta fice da sauri tana fadin to.. Sai bayan da yayi isha a masallacin dake cikin hospital din sannan ya nufo gida a gajiye sosai ga yunwa da take damun shi.. kai tsaye ɓangaran shi ya wuce yayi wanka sannan ya ɗauki ledar magungunan da allurai daya taho dasu danyi wa jiddah dan tuni ya gane abinda ke damunta.. yana shiga palourn ya samu mommy tana hada mata tea, ganin shine yasa tace "yauwa Habib jiddah ba lafiya ka shiga ka duba ta"! kafin Mommy tagama magana ya nufi ɗakin nata.. a kwance ya sameta saidai idanuwanta a rufe suke jin ƙamshim turaren shine yasa ta buɗe idanuwanta sannan ta tashi zaune. tana ƙasa da kanta. a gefenta ya ajiye ledar ya fito da allurar sannan yace ta miko hannun. cikin kidima tace "yaya Habib na warware fa"! tsaki ya danyi sannan yajawo hannun nata. tanaji allurar ta shiga ta toshe bakinta tana kuka, saida ya gama ya ɗago kanshi yana kallan fuskar ta. "idan ance ki daina shan zaki bakya dainawa amma wajan allura kin iya kuka" ya faɗa yana miko mata magungunan. amsa tayi tana share hawayen ta, duk haushin shi takeji harda mugunta ya haɗa mata tana sane. "hararan ta mene haka"!? ya sake faɗa yana daga mata gira. harta bude baki zatayi Magana mommy ta shigo dakin rike da cup din tea a hannun ta,. Habib kuwa shigowar mommy ya fice daga ɗakin, ya wuce dining room yaci abincin sa sannan ya haɗa coffee yasha ya fice.. kwana biyu kenan jiddah bataje school ba duk da ta samu sauki amma bata koma ba, Habib kadai ke tafiya wajan aikin sa shima bai wani damu da rashin zuwan nata ba.. yau weekend Habib baije wajan aiki ba yana zaune a gida, gama lunch ɗinsu Kenan mommy tace ya dauki su jiddah su fita shopping. "mommy shopping kuma"? "eh mana, duk weekend haka nake daukan su muje tunda ka dawo bamu jeba dan haka saika kaisu yau"! kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru kawai... suna gama shirin jiddah ta riko hannun Abdul tace "yaya Habib mun shirya" tashi yayi kawai yace su tafi. babban shopping mall ya kaisu, suna fita yace idan tagama ta kirashi shi bazai shiga ba dan bayajin dadin jikin shi kawai dai bayasan yiwa mommy gaddama ne shiyasa ya kwaso su ya kawo su. sosai ta jidi kaya, saida ta gama ta kira wayarshi tace sun gama ya shigo ya biya. a hankali yake driving din murmushin dole kawai yakewa Abdul jiddah na kula da hakan. suna zuwa gida yayi Parking ta fice itada Abdul ɗin suka barshi a Mota. sosai yake jin ciwan cikin haɗe da wani zazzafan zazzaɓi dauriya ce kawai yake yi shiyasa ko ɓangaran su jiddan bai shigaba ya wuce part ɗinsa. "Ina Habib din"? mommy ta Tambaya tana duba kayan da suka siyo. kallan kofar shigowa jiddah tayi tace "may be yana mota"! tace tana wuce wa dakinta. har dare bai shigo ba, saida suka zauna yin dinner sannan mommy tace taje ta kirawo shi. shikam harya kwanta ya rufe jikinsa da blanket sai rawar sanyi yake yi. da sauri ta karaso kusa dashi tana yaye bargon tare dafa kanshi. "yaya Habib meyake damunka"! buɗe idanuwan shi yayi da sukayi masa nauyi da zafi sannan ya kalli fuskarta baice komaiba ya mayar da idanunshi ya rufe. a rude ta tafara danna wayarta,jin Muryar shi tayi a matukar wahale "yace me zakiyi"!? "mommy zan kira mana na sanar Mata" wani takaici ne ya kamashi duk dayasan ba laifinta bane amma Yakamata taji tausayin shi ta duba halin dayake ciki ta yarda ta su koma gidan daya gama kammalawa amma yarasa dalilin ta nakin amincewa. ganin ya kura mata ido ne yasa ta tashi zata fice, kamo hannun ta taji yayi ta rintse idanuwanta jin hannun nashi zafi rau.. "yaushe zaki fara tausayina ne jiddah, kefa ba yarinya bace, kinsan hakkin mace akan mijinta amma meyasa kike wasa da haka" Habib ya faɗa cikin irin wata kasalalliyar Murya wacce baisan ma yayi taba. kam ta tsaya a tsaye takasa motsa koda dan yatsan tane ƙwaƙwalwar ta ta daina aiki dan bata taɓa tunanin jin irin wadannan kalaman daga Habib koda a mafarki... janye hannun ta tayi ta fice a hanzar ce kamar wacce zai biyo, tana shiga palour ta wuce ɗakin ta, ta kwanta saidai ta rasa wanne irin tunani zatayi "shin dagaske Habib ne wanda ta sani kokuma kunnuwan tane suka ji maganganun nashi ba dai dai ba" kiran mommy ne ya katse mata tunanin nata. "jiddah muna jiranku fa, ina Habib ɗin" "gani nan mommy Ina ɗaki yanzu zan fito" ta yanke kiran dan harta manta ma abinci zasuci ta tafi kiran shi. da kallo Mommy tabi ta harta zauna ta fara cin abincin saidai sam ya fitar mata a rai sai juya spoon din kawai takeyi. "jiddah meya faru ko yayi miki wani abu ne, naga daga kiran shi kika dawo a haka"! da sauri ta girgiza kai tace "a'a mommy cewa kawai yayi bazai ci ba"! "shi ne kika wani canza haka"! murmushi tayi wanda iya kacinsa lips ɗinta sannan tace "nima ai a koshe nake shiyasa"! ta faɗa tana tashi, tanaji Abdul yana kukan zai bita dakinta amma ko kallan shi batayi ba dan tasan damunta zaiyi ga kanta nayi mata ciwo. ✍️✍️✍️✍️✍️[1/7, 10:06 AM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч ⓒᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ *🌹fírѕt lαdч🌹*✍ *wαttpαd* @Ameenafirstladyy *🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION* {41} Da kyar mommy ta lallashi Abdul yayi shiru suka je suka kwanta.. Sai juyi jiddah takeyi saidai takasa baccin tunanin Habib ne yasa duk baccin yakasa zuwa mata, tunanin ta yana kan yanayin data baro shi, dama ta sani ta zauna dashi dan tasan yana bukatar kulawar ta saidai bazata iya ba idan ta biyewa san zuciyarta ta nuna soyayyar gareshi a fili kamar zubar da aji ne a wajanta... Tsaki ta dinga yi kamar wani na jinta har asuba batayi wani baccin kirki ba haka ta tashi idanuwanta duk sun kumbura alamar bata samu bacci sosai. . mommy duk abin yafara daure mata kai, tun jiya bata gane kan Habib da jiddah kardai daga ya shawo kanta yaja wata Matsalar kuma"'! "Ohh! Ya Allah, Habib bayajin magana idan taki basaiya hakura ba ya nemo wata ba ko ana dole ne! Tayi maganar a cikin ranta.. Fitowar jiddah kenan ta samu mommy a palour, saurin sakin murmushi tayi dan kar mommy ta gane wani abu. "Ina kwana mommy"!? Kusa da ita mommy ta karaso batareda ta amsa gaisuwar ba, "Jiddah meya samu idanuwan ki, baki samu bacci bane, meya hanaki bacci" ta jerowa jiddah tambayoyin a jere saboda a ruɗe take a yadda taga jiddan. Murmushi jiddah ta kuma ƙaƙalowa ta riko hannun mommyn tace "wlhy mommy kalau nake Ido nane yakeso yayimin ciwo shiyasa kika kika ga haka"! "huh! Harna ji daɗi, yanzu muje kiyi breakfast kar lokaci ya kure miki" Badan taso cin abu ba tabi mommy har kan dining table, saida suka fara ci sannan mommy tace "meya hadaki da Habib" "Babu komai, ya fita aiki ne"? Ta kawar da zancen. "A'a bansan meyasa har yanzu bai shigo ba, bari naje na duba karya sa ki makara"! Jiddah kamar ta hana mommy zuwa haka taji amma ba yadda zatayi tana kallo mommy ta fice zuwa part ɗinsa. Da kyar ya iya Sallah kwana biyu shi kanshi yasan ya sauya amma jiddah ce ta sauya shi, baiga macen data dace dashi kamar jiddah ba idan yace zai rabu da ita wa zai aura.. Jin anayin nocking ne yasa yayi saurin tashi dan yasan mommy ce. Bata izinin shigowa yayi sannan ta shigo tana kare kallo. Har wata rama yayi sosai daga jiya zuwa yau, mommy ta Dan tsorata Amma Bata nuna ba. "Habib lafiya kake kuwa" Rigar jikinsa ya zame yana murmushi ya saura daga shi sai vest da wando trouser. "Eh mommy lau nake!" Ya Bata amsa a wata irin Murya ta marasa lafiya. "Amma tun jiya nake ganin ka kamar akwai wani abu dayake damunka" "A'a babu komai, zanyi wanka na wuce wajan aiki" bai jira amsar taba yayi hanyar bathroom ɗinsa rike da bathrobe a hannun shi. "Habib"!!!!... Cak ya tsaya jin yadda ta kira sunan nashi cikin taushi da nuna kulawa. Bai amsa ba saidai ya juyo yana kallanta. Har kusa dashi ta matso sannan ta jashi kan kujerar dake cikin ɗakin ta zaunar dashi itama ta zauna.. Saida suka dauki kusan mintina biyu sannan tace "ni mahaifiyar kace, zan gane kowacce irin damuwa idan ka shige ta, kuma nasan duk akan jiddah ce ko"!? Ta tambaye shi saidai bai amsa mata ba sai kasa yayi da kanshi duk jijiyoyin kanshi sun tashi. "Na fahimci irin san da kake mata tun ba yanzu ba hakan ne yasa na haɗa auran ka da ita amma ka watsa min ƙasa a ido, yanzu gashi ta kasa fahimtar ka, kaci gabada hakuri da lallaɓata zata dawo gareka amma karka nuna mata isa da wulakanci yanzu yashi kayi wankan tana jiranka karku makara" Yanaso ya fadawa mommy jiddah har yanzu matarsa ce amma yakasa faɗa mata tunda har jiddah bata sanar da ita ba koya faɗa ba lallai ta yarda ba, zaici gaba da hakuri har sai ta faɗa da kanta kuma ta amince batareda yayi mata dole ba. Kamar wani mutum mutumi haka ya tashi ya shige bathroom tana binsa da kallo sannan ta koma part ɗinta.. A kofar shiga taga jidda zata fito, da mamaki tace "ina zakije" Marairaice murya jiddah tayi tace "pls mommy khairat sai kirana takeyi nayi sauri inada test kuma yaya Habib kafin ya shirya aiki ne zan tafi na hau taxi"! "Shikenan kije amma ki kula fa" Tam mommy ta fada tana rungume ta sannan ta fice da dan gudu.. Bai wani dade ba ya shirya ya fito dan yasan jiddah na jiranshi, yana shiga palourn ya fara baza idon inda zai ganta. "Jiddah ta tafi tagaji da jira, saika zo kayi breakfast ka wuce wajan aikin"! "Whattt ta tafi, waya kaita"? "Taxi tace zata hau" Hanyar fita yayi mommy tace "abincin fa"? Dan tsayawa yayi bai jiyowa ba yace "na koshi mommy zan sameta a bakin titi ai" bai jira amsar mommy ba ya fice da sauri.. Tana tsaye bakin titi sai tsaki takeyi khairat ɗin taki fitowa ga taxi da napep sai wucewa sukeyi babu kowa ciki amma saboda jiran khairat yasa taki tafiya.. Wata red din mota ta tsaya gabanta, sannu a hankali ya sauke glass din motar. Sosai tayi mamakin ganin shi dan Afnan tace mata yaje karo karatu England.. Muryar shi taji a kusa da ita "ina zakije ne haka jiddah" Murmushi ta ɗanyi tace "school zanje khairat nake jira, ina kwana" ta gaida shi tana cigaba da murmushi. "Lpy kalau, muje na sauke ki mana nima hanyar can nayi. Kamar zatayi masa musu lura da hakan ne yasa Kabir yin murmushi yace "jiddah ki manta baya ki kalli yanzu, ni yayanki ne a yanzu kodan afnan dake auran yayanki saboda bazan cutar dake ko nayi miki wata magana wacce bata dace ba saboda nasan ke matar wani ce umm" ya faɗa yana kallan fuskar ta. Murmushi tayi dan tasan gaskiya ya fada, hakan yasa ta wuce ta shiga motar shima ya zagaya ya shiga suka tafi.. Akan idan Habib akayi komai, tsananin bakin ciki da bacin rai ne suka taru a zuciyarshi ko office bai wuce ba ya nufin gida Allah ne kaɗai ya kaishi dan wani mahaukacin gudu yakeyi kamar zai tashi sama. Mommy taji dawowar shi har zata je ta tambayi abinda yasa ya dawo saita fasa kawai dan tayi tunanin wani abin ya manta.. Fadawa saman bed ɗinsa yayi ta baya tareda lumshe lum sassun idanuwan shi yana fitar da wani zazzafan huci. "Waye shi, meyasa ta shiga motar shi meyasa yake mata murmushi tana mayar masa"! Ya jerowa kanshi tambayoyin da suka kara masa zafin zuciya.. Tsananin mamakin jiddah tayi ganin sun doshi gidan su khairat kasa shiru tayi tace "ina zamu je" "Wajan khairat mana"! Bata sake magana ba tana kallo ya kira khairat ɗin yace ta fito gashi shida jiddah suna jiran ta. "Ya akayi kuka haɗu" khairat data fito yanzu ta tambaya tana murmushi. Wani murmushi taga Kabir yayi haɗe da wani kallo daya tabbatar mata da su ɗin masoya ne. "A hanya muka haɗu tana jiran zuwan ki" "Ohh! Ku muje to"! Babu bata lokaci suka shiga ita dai tana baya tana jin hirar su har ya sauke su.. "Amma khairat naji daɗi wlhy, shikenan mu duka uku yanzu mun sake zama daya"! Dariya khairat tayi tace ai tun bikin su muka haɗu dashi wajan party na Afnan. Jiddah bakaramin daɗi taji ba, haka suka lecture suna ta Hira akan maganar.. 4:30 Kabir ya koma dauko su dai dai lokacin fitowar su lecture din karshe, hankali kwance jiddah tabi su, har shopping ya wuce dasu sannan ya fara sauke khairat dake kan hanya ya taho da jiddah gida, jefi jefi suke hira wanda shi yake tambayar ta tana bashi amsa. "Ya sunan yaron ki" "Abdulmalik, amma ya akayi kasan shi" "Na haɗu dashi a gidan afnan ai" Habib na kwance dafe da kanshi kamar ya tsage haka yake ji, kira ne ya shigo wayar shi yasa hannu ya zaro ta daga kasan pillow dinshi ya daga yana karawa a kunnen shi. "Hello yallabai akwai masu san ganinka yanzu"! Tsaki yayi dan sai yanzu ya tuna sannan yace "ok gani nan"! Yana tashi kiran mommy ya shigo "Kaje ka dauko jiddah lokacin dawowar ta yanzu yayi" "To" Muryar shi kawai taji tasan bashi da lafiya, a Compound ya samu mommy tana jiran fitowar shi. A hankali yake tafiya tabbacin bashida cikakkiyar lafiya da sauri ta karaso tace "Habib kabari zanje dauko ta kawai" "Mommy kaina ne kawai yake ciwo, ki bari zanje daga nan zan wuce office ana San ganina"! Zata kuma magana taga yayi murmushi ya kamo hannunta ya manna mata miss yace "karki damu zan iya zuwa" Itama murmushi tayi tace "shikenan Allah ya kaika lpy" sannan ta koma bangaren ta.. Yana kokarin buɗe motar sa yaji shigowar, tsayawa yayi yana kallan motar har sukayi Parking jiddah ta fito shima Kabir ya fito yana miƙa mata ledar hannun shi. Baiji abinda suke cewa ba saidai ya lura kamar bata yake tana kin amsa.. Dakyar jiddah ta amsa jin yace ba ita yayoba Abdul yayi wa ko zata raba ɗa da uba sannan ta amsa tayi masa godiya.. Saida ya tafi ta jiyo tana kallan Habib, murmushi tayi kasa kasa yadda bazai gane ba dan tagano tsananin kishi a cikin damuwan shi dama haka taso daga yau zata gane irin san dayake mata, makewa tayi zata wuce ta gaban shi.. "Waye shi" Taji ya faɗa cikin wata irin Murya kasa ƙasa. Bata kalli inda yake ba tace "bayan ka sake Ni shine wanda zan aura kuma nasan ka gane shi ai" Daga hannu yayi cikin wani irin fushi zai mare ta, Kara tayi tana rufe ido tana jiran taji saukan mari, jin shiru yasa ta ɗago kai tana kallan shi. Sosai ya rintse ido ya rasa wanne irin abu yake ji zuciyarshi na masa wani irin zafi ga ciwan kai ɗaya kara karuwa, cikin zafin rai ya buɗe motar shi ya fice da wuni irin gudu wanda ya tsorata jiddah ta shiga part ɗinsu, ta wuce ɗakinta da sauri tana sauke ajiyar zuciya Allah yaso mommy Bata palourn.. Gudu yakeyi sosai, duk inda ya gifta mutane magana sukeyi saboda gudun gangancin dayake yi, shi kam baima san abinda yake faruwa ba dan baima san gudu yake ba dan baya cikin Peace of mind dinshi hannun shi na dafe da saitin zuciyarshi da ɗaya hannun kawai yake driving yana dan rufe idanuwan shi.. Tuna yadda suke magana yayi tana mayar masa da amsa, wani duhu duhu ya gani ya gifta ta idan sa hakan yasa ya saki steering din motar ta kwace masa...... *_first lady_*✍✍ 7/1/2020 [1/14, 11:10 PM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 By ⓒᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ *🌹ғιrѕт lady🌹* *wαttpαd* Ameenafirstladyy {42} cikin firgici jama'ar wajan suka fara kokarin taimakon shi, da kyar suka iya ciro shi daga motar aka wuce dashi asibiti cikin gaggawa.. jiddah kuwa tana shiga ɗakinta wanka tayi sannan ta shirya ta fito palour, da mamaki mommy ta kalle ta tace "yaushe kika shigo bayan yanzu na aika Habib ya ɗauko ki"! murmushi ta ɗanyi sannan ta zauna kusa da mommy tace "ban dade da shigowa ba, gajiya nayi da jira saboda yunwar danake ji shiyasa kawai na taho"! "kin kyauta ai, saiki je kici abinci! "ina Abdul fa"? "yana daki na yana bacci" bata sake magana ba ta wuce dining room duk da bawata yunwa takeji ba ta faɗa ne kawai dan kar mommy tace Meyasa bata jira shi ba.. emergency room aka shigar da Habib, da kyar kwararrun ma'aikata suka samu damar saita numfashin sannan aka kaishi ɗakin hutu.. "an samu wayar shi a tareda shi kuwa" dan sandan dake wajan ya faɗa yana kallan wani dattijo wanda dashi aka kawo Habib ɗin asibiti.. "eh yallabai gata nan, cikin ikon Allah kuma babu abinda ya samu wayar" ya faɗa yana mikawa dan sandan wayar.. mommy na zaune tana yankewa jiddah Kumba sai faman shagwaba takeyi Abdul na gefe yana wasa wayar mommy tafara kara, ganin Habib ne yasa mommy ta ɗaga.. "Habib..."! Muryar dataji ne yasa tayin shiru tana sauraran abinda dan sandan ke faɗa. a razane ta mike tana fadin "wanne sabitin ne"? "shikenan gani nan"! tana faɗa ta ajiye wayar tana hanyar hawa upstairs. "mommy meya faru, waye a asibiti"! batareda mommy ta tsaya ba tace "Habib ne yayi accident suna special hospital" Bata jira amsar jiddan ba tabar palourn ta haye sama dan dauko Car key ɗinta.. tarasa wanne irin yanayi take ciki gabanta ke tsananin faduwa dan tasan tabbas abinda ya faru ɗazu ne yasa shi yin accident.. tana kokarin tashi ne mommy ta fito tace "ki zauna a gidan zan kira hibban ya same ni acan"! har mommy zata fice jiddah tace "dan Allah mommy ki tafi dani bazan iya zama batareda nasan halin dayake ciki ba"! "ki same ni a mota da sauri" mommy ta faɗa tana ficewa cikin sauri dan hankalin a matukar dagule yake.. hijjabin ta kawai ta dauka sannan ta dauki Abdul suka fice... kafin su karasa asibitin mommy ta Kira Hibban tace ya same a special hospital, shima cikin kaduwa ya taho duk hankalin sa a tashe.. saboda gudun da mommy keyi mintina kaɗan ne suka kaisu asibitin, sosai tayiwa mutanan da suka kawo shi Godiya sannan ta bukaci ganin doctor ɗin.. "kiyi hakuri Hajiya amma gaskiya abubuwan da suke damun shi suna da matuƙar haɗari, Yakamata ace kinsan damuwar danki kuma kin guji abinda zai shafi lafiyar shi" cikin zakuwa mommy tace "Dr, ban fahimci bayanin kaba, kayi yadda zan gane"! cire Glass din idanuwan shi yayi sannan ya kalli mommy yace "doctor Habibullah yana tare da hawan jini, sannan akwai wata cuta da aka haife shi da ita wadda nasan kin san hakan, wato duk lokacin da yaji kara ko ihu ko makamancin wannan abubuwan to zaiyi ciwan kai mai zafi a takaice dai komai zai iya faruwa".. kasa mommy tayi da kanta tana maimaita innalillahi, jiddah kuwa har idanuwanta sun fara kawo ruwa.. "yanzu doctor zan iya ganin shi"!? shiru docton yayi yana dan kallan watch hannunshi sannan yace "eh zaku iya ganinshi saboda nasan zuwa yanzu allurar da mukayi masa tana gaf da sakin shi, amma kafin nan ga waɗannan magungunan a nemo su da sauri"! "To doctor mun gode" mommy ta faɗa suna ficewa ita da jiddah.. suna fita motar Hibban ta shigo asibitin, a ruɗe ya karaso kusada mommy yana tambayar ya jikin Habib ɗin.. "da sauki, tunda kazo ga waɗan nan magungunan kaje a siyo su Yanzu, anaso daya farka yasha, sannan ka tafi da Abdul ka mayar da shi gida"! amsa hibban yayi ya fice daga asibiti, sannan mommy da jiddah suka nufi ɗakin da aka kwantar dashi.. tun daga bakin kofa jiddah take kallan shi cikeda karaya ganin yadda yaji raunuka har biyu, gaba daya an zagaye fuskar shi da bandage, sai damtsen hannun shi, mommy ma dauriya kawai tayi bata nuna karayar taba, tasan Habib da zurfin ciki amma batayi tunanin zai iya boye damuwar shi harya ki sanar mata ba.. har lokacin bai farka ba, likitan ne ya shigo yace "har yanzu bai farka ba"? "eh doctor akwai matsala ne"? mommy ta Tambaya.. "a'a babu wata matsala, karki damu zai iya farkawa at any time"! ya faɗa yana ficewa daga ɗakin.. duk sunyi jugum jugum gashi hibban har lokacin bai dawo ba, tashi mommy tayi tunawa da tayi hibban baisan inda suke ba tace "jiddah ki kula dashi zanje na taro hibban da bai san inda muka yo ba"! da kyar ta iya buɗe baki tace "to" amma duk da haka idanuwan ta na kan Habib.. mommy na fita yafara buɗe idanuwan shi a hankali harya bude su tar akan jiddah dake facing ɗinshi, da sauri ta matso kusa dashi tana jera masa Sannu.. kallanta yake kamar mai tuna wani abu sai kuma ya kawar da kanshi gefe yana dan lumshe idanuwanshi.. "ina mommy"!? ya Tambaya can kasan makoshin shi.. zata bashi amsa ne su mommy suka shigo, su duka sukayo kanshi da sannu.. murmushi kawai yake ɗanyi dan kwantar musu da hankali.. "ina Abdul fa"!? ya sake faɗa yana kallan mommy. "hibban yakai shi gida"! bai sake magana ba har doctor ya shigo ya dan duba shi yace "yanzu ya danci wani abu saiya sha magungunan da aka siyo" yana faɗa ya maida kallanshi kan Habib. "yace doctor Habib, ka taki Sa'a bakaji wani rauni sosai ba, amma dan Allah a kiyaye gaba kana consultant doctor yakamata kafi kowa kiyaye lafiyar ka ba" har doctor ya gama jawabin shi Habib baice komaiba sannan ya fice daga room.. saida yaci abincin da Afnan ta aiko dashi sannan yasha magani.. lokaci zuwa lokaci yana satar kallan jiddah wadda tayi kasa da kanta,.. "Habib meyake damunka ne wanda bakaso na sani harya kai da zakayi sanadin ranka, na lura yan kwanakin nan kana cikin damuwa da cuta amma sam kaki fadamin, meyasa bakaso na sani" mommy ta faɗa tana riko tafin hannun shi.. murmushi yayi mata yace "babu komai mommy, Nima kaina narasa abinda yake damuna saidai inaji kamar akwai wani abu danake so yake niyyar suɓuce min wanda rasa shi kamar rasa rayuwa tane da farin ciki na,"! da mamaki su duka suke kallan shi har jiddah wacce take jin maganar tashi kamar almara ko mafarki.. cikin kwantar da murya mommy tace "Habib duk duniya ku biyu kaɗai kuka rage min, kune farin ciki na kune rayuwata dukiya da arzikin danake dashi basuda wani amfani idan bana tare daku, ka faɗa ko menene idan har karfi da dukiya ta zasu iya nemo shi..."! "mommy karki damu addu'a kawai zakiyi min, Allah yasa ya kasance a tare dani" ya faɗa yana sake yin wani murmushin wadda yakara masa kyau.. haka suka zauna har dare sannan aka sallame su, duk Wani motsi na jiddah akan idan Habib takeyin shi, yanaji wani irin soyayyar ta wadda yanzu ya gama yadda ita kadai zuciyarshi ta kamu da kaunar ta tun baisan menene soyayyar ba, sai yanzu ya gaskata maganar Sultan tacewar jiddah ce kadai soyayyar shi ta gaskiya.. jiddah kuwa duk tunanin ya tsaya a kalaman Habib, kenan da gaske hibban yake dayace Habib yana santa kodai duk mafarki takeyi kalaman Habib a kanta... kai tsaye ɓangaran shi hibban yakai shi har zai fita yace "kasa a kawo min coffee right now"! fuskar nan a haɗe.. "To yaya" ya faɗa yana ficewa cikeda mamakin yayan nashi, mai hali dai baya fasa halinshi saidai ya rage wani abu ya faɗa yana yin murmushi.. yana shiga palour yaga mommy tana haɗa masa coffeen, dariya yayi yace "tabb yaya Habib fa ba lpy, yanzu hankalin mommy a tashe yake har sai first born ya warke" "eh naji dama haka ce ta dawo dakai part ɗina Kenan"? "a'a ba wannan bane patient dinki ne yace a kawo masa coffee, sai gashi ma naga har kin gama haɗa masa"! ya karasa yana kumshe dariyar sa.. "tunda ka isar da sakon saika barmin gida ai".. saida yagama tsokanar mommy sannan ya fice yace Abdul zai kwana a can duk da yasan idan ya hadu da khaleesat yarshi har gajiya suke da rashin ji.. ✍️✍️✍️✍️ [1/17, 3:53 PM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч aмeena мυѕa *🌹ғιrѕт lady🌹* *waттpad* Ameenafirstladyy {44} .....bata wani dade ba ta gama cin abincin, Sannan ta shigo palourn. a zaune ta same shi yana ganin shigowar ta ya mike tsaye yace "muje ko"! da mamaki tace "ina zakaje kuma kaida bakada lafiya" "saina ce miki bazan iya driving a haka ba kuma" shigowar mommy palourn ne yasa suka yi shiru kamar munafukai. "yadai na ganku a tsaye, ko kin fasa zuwa school ɗin ne"!? ta faɗa tana kallan fuskarta. "mommy Wai a haka zai kaini school"! kallan shi mommy tayi tace "haba Habib kabari ta hau taxi, kaga fa fuskar ka da hannun ka duk bandage"! cikin takaici ya kalli jiddah sannan ya mayar da kanshi ga mommy baice komaiba. "gaskiya bazan bari ka fita haka ba, kabari idan ka samu sauki saika koya mata motar a hankali kokuma ka dinga kai tan"! tana gama fadan haka ta wuce ɗakin ta. mommy na barin palourn ya zauna cikin tsananin baƙin ciki dan bazai iya yiwa mommy musu ba. ko kallan inda take bai sake yi ba hakan ya tabbatar mata da fushi yayi. ficewa kawai tayi dan tasan ko ta tsaya bashi hakuri bazai saurare taba. dakyar ta samu ya hakura, dan yanzu babu laifi suna nunawa junansu kulawa duk da haryanzu mommy batasan komai a kansu ba, saidai tanajin daɗin yadda yanzu suke shiri sosai, ko fita zaiyi suna fita tare bai kara nuna mata wani abu ba ko tazo part ɗinsa kawo masa coffee amsa kawai yakeyi ta fita batareda ya tsayar da ita ba shiyasa yanzu ta saki jiki dashi, shi kuwa ya kyaleta ne kawai yaga iya gudun ruwan hakuri kawai yakeyi yana saita kanshi.. cikin sati ɗaya Habib ya warke yaci gaba da zuwa aikin shi, jiddah kuwa yanzu shirye shiryen passing out sukeyi, Habib ya kashe mata kudi har saida tace ya isa haka amma ko sauraran ta baiyi ba, ranar taron kuwa ya nuna bajinta, sai yamma sosai dan gaf da magrib ne lokacin sannan suka dawo gida. anan su hibban da Afnan suka wuni da yarinyar su khaleesat yarinya mai kyau da wayo. suna zaune duk suna cin abinci Habib ne kawai baya wajan, mommy ce "hibban Yakamata a nemawa su Abdul da khaleesat school yanzu" "to mommy za'a nema" daga haka suka cigaba da cin abincin su. duk sun tafi mommy ce kadai da jiddah a palourn, sai Habib dake zaune can gefe yana danna wayarsa,. "Yakamata ki samu wanda zuciyarki ta aminta dashi ki kawo shi ayi magana, zamanki a haka bashida wani amfani jiddah" gabanta yayi mummunan faɗuwa ta juya ɓangaran da Habib ke zaune taga hankalin shi baya wajansu da alama ko maganar tasu baya saurara idanuwan shi na kan wayar shi. ƙasa tayi da murya tace "mommy..." katse ta mommy tayi tace "cikar mutumcin ki yanzu shine aure, kada tsoran Habib yasa ki kasa fitar da wanda kike so, saboda haka na baki kwana biyu kizo da magana mai Ma'ana dan nagaji da wannan shashancin naki" kasa koda daga baki jiddah tayi dan batasan taya zata zata faɗawa mommy ba Dan wata irin kunyar ta takeji gashi Yanzu itama tana buƙatar komawa ga mijin ta. "ina zakaje a daran nan" mommy ta Tambayi Habib dake kokarin fita. fuskar shi ba yabo ba fallasa yace "zan kwanta ne" "ok good night"! bai amsa ba yasa kai zai fita sai kuma ya juyo ya kalli jiddah dake zaune kamar an dasa ta. "ki kawo min coffee ko lemon tea"! yana faɗa ya fice ranshi a matukar ɓace. yana shiga part ɗinsa ya shiga bathroom yayi wanka sannan ya fito duk da haka kallo ɗaya zakayi masa kasan ranshi a bace yake sosai, sai faman huci yake yana ɗan hura hanci. jin anayin nocking ne yasan itace yayi banza da ita, gajiya tayi da nocking ta tura ɗakin ta shiga. yana zaune da wasu files a gabansa, harta matso kusa dashi ta ajiye masa cup ɗin bai ɗago ya kalle taba. "yaya Habib ga lemon tea ɗin" sai sannan ya ɗago kai ya kalleta, kallo daya tayi masa ta gano ɓacin ransa. ta ɗan tsorace tace "yaya Habib waye ya bata maka rai" tsaki yayi sannan taga ya mike zai bar ɗakin da sauri ta riko hannuwanshi tana ɗan girgiza kai. "pls ka fadamin meya faru"!? kara kuluwa da takaici yayi ya fizge hannun shi, yabar dakin. palour ta bishi ta zauna kusa dashi tafara hawaye. jin saukar hawayen tane yasa shi saurin kallanta yayi zuciyarshi ta karye ya kamo hannunta cikin nashi yafara yi mata magana kamar raɗa. "jiddah bazaki gane irin yanayin da halin danake ciki ba, shekaru na sun kai na yadda dole zan damu, nayi hakuri nayi kawaicin amma duk baki fahimta ba toya kikeso nayi, ina bukatar ki a kusa dani tayaya raina bazai ɓaci ba kin kasa faɗawa mommy gaskiya bayan kinsan Ni bazata yadda da tawa Maganar ba" ya karasa yana dan fitar da huci ta bakinsa. sai yanzu itama ta ɗago kanta tace "amma kasan dole naji kunyar mommy akan wannan maganar, tayaya zan iya tarar ta da wannan maganar".! "shikenan yanzu kwana biyun meza faɗa mata"!? ya tambaye ta yana kafe ta da kyawawan idanuwan shi. "zan sanar da ita komai zuwa kwana biyun"! murmushi ya ɗanyi sannan yace "idan bahaka ba fa"? ya faɗa yana kashe mata ido. kasa tayi da kanta cikin kunya batace komaiba. "wato dai wannan kunyar taki na fahimci itace babban Matsalar ta dake, zan san abin yi a kanta very soon"! dariya kawai tayi ta tashi zata tafi ya riƙo hannun ta yace "nayi zaton anan zaki kwana ai" zaro idanuwanta tayi tace "wa.. ni".. tabb,. da safe nace wa mommy me"! maƙe kafaɗa yayi yace "sai kawai kice wajan mijinki kika kwana inaga daga nan zata fahimci sauran zancan"! sosai yaba jiddah dariya, kamar karsu rabu haka taji dan sai yanzu ta kara tuna maganar hibban dayace duk zafin zuciyarshi yanada sauƙin kai da daɗin zama gashi cikin lokaci guda sunyi sabo har tana fahimtar shi akan komai....... Cikin kwana biyun da mommy taba jiddah, saura kwana ɗaya duk hankalin jiddah a tashe yake dan batasan amsar da zata bawa mommy ba.. da safe Habib ya shirya zuwa wajan aiki dan sai faman kiran shi akeyi, yana rike da jacket ɗinsa ya tashi daga kan dining table ɗin sannan ya ɗauki wayar shi dake ta faman kara ana kiran sa a office. sallama yayiwa mommy sannan yace jiddah tabiyo shi da brief case ɗinsa. kallan mommy tayi wacce ke cin abincin ta bata kalli ko inda suke ba. a cikin mota ta sameshi yana Ganin karasowar ta ya fito rike da key ɗin shi. "kar kunya ta hanaki faɗar Gaskiya"! yana faɗin haka ya amshi jakar shi ya shige mota ya bar gidan... tafiyar Habib yasa ta koma ciki duk jikin ta a sabule, mommy na lure da ita saidai ko ta kanta bata bi ba harkokin ta kawai takeyi.. yana zaune a kan kujerar shi a office idanuwan shi a lumshe yana dan cije lips, da kyar ya iya kiran Ameenu mintina biyu ya shigo. ko zama baiyi ba Habib ya faɗa masa wani magani yace ya nemo masa shi yanzu sannan kar a bari wani ya shigo min nan. ɗan tsayawa Ameenu yayi kamar zaiyi magana sai kuma ya fice yana girgiza kanshi cike da tausayin mai gidan nashi. a hankali yake fitar da numfashi dan ya fara galabaita, shigowar Ameenu ne yasa shi ɗago jajayan idanuwan shi. saida yasha sannan ya ɗan kwantar da kanshi yana maida numfashi a hankali. "Dr I'm sorry to say, wannan maganin yanada matsala yawan shan shi, kuma yan kwanakin nan kullum saika sha inaga kamar hakan zai iya haifar maka da matsala aure shine....."! wani kallo ya watsawa Ameenu da jajayan idanuwan shi sannan yace "get out of my office" da sauri Ameenu ya bashi hakuri ya fice cikeda mamakin wannan hali irin na mai gidan nashi da shegiyar kafiya. *🌹 firstlady 🌹*✍️✍️✍️ [1/19, 11:31 AM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч ᴀᴍᴇᴇɴᴀ ᴍᴜsᴀ *🌹ʄɨʀֆt ʟǟɖʏ🌹* *wαttpαd* Ameenafirstladyy {43} ...... mommy har zata kai masa da kanta sai kuma ta nufi ɗakin jiddah.. a kwance ta sameta idanuwanta a rufe, jin an buɗe dakin tane yasa ta buɗe idanuwanta ta ɗago kanta. "jiddah lafiya kike kuwa"!? "eh mommy na gaji ne kawai" "to tashi ki kawai Habib coffee saiki bashi magungunan shi daga nan, Ni zanje na gyara dakina"! dan sauya fuska tayi tace"wlhy mommy bazan iya da masifar wannan mutumin ba" dariya mommy tayi tace "babu abinda zai miki wanda bashida lafiya ina yaga ta faɗa"! kamar zata sakeyin magana sai kuma ta amsa ta fice daga ɗakin.. a hankali ta shiga palourn tana bin ko ina da kallo, ganin baya palourn ne yasa ta wuce ɗakinshi saidai kasa shiga tayi tana dan tsorace dan har yanzu da sauran tsoran shi da take ji Musamman data san itace silar accident din nashi. kasa ƙasa tayi sallama dan ta tabbatar bazaiji sallamar Tata ba, a kwance ta hange shi ya dafe kai da lafiyayyan hannun shi, ɗan ɗaga murya tayi ta sakeyin sallamar.. ƙasa ƙasa shima ya amsa sannan ya tashi yana kallanta duk da tayi kasa da kanta, har tazo kan Centre table ɗin kusa da bed ɗinsa ta ajiye sannan ta ɗago kai suka haɗa yayi saurin kawar da kanshi gefe yana ɗan tsuke fuska. "gashi mommy tace kasha sannan na baka magungunan ka"! banza yayi mata kamar baisan akwai mutum a kusa dashi ba. ganin haka yasa jiddah ta kwantar da murya tace "dan Allah yaya Habib kayi hakuri, nasan nayi laifi amma wlhy ba abinda na faɗa maka bane a zuciyata kawai a hanya muka haɗu ya rage min hanya amma babu wata soyayya tsakani na dashi" saida ta gama sannan taji ya sauke ajiyar zuciya tareda lumshe idanuwanshi baice komaiba ya fara sipping coffee ɗinshi harya gama sannan ta dauko magungunan tana bashi yana sha harya gama tas. sannan ta tashi zata tafi, ji tayi ya riko hannunta ta baya, jiyowa tayi tana kallanshi tareda daga masa gira tana kallan hannun nasu. kamar mai koyon magana yace ta zauna. batayi masa musu ba tazauna tana cigaba da kallan shi. "wannan kallan fa, na mene"! "nasan sanin dalilin hanani tafiya mana" taɓe baki taga yayi sannan yace "a bayanai da kikayi na fahimci kema kina sona wani dalilin ki mara amfani shine ya hanaki faɗa wa mommy matsayi na a wajan ki ko"? ya tambaye ta yana kallan kwayar idanta. "ni banida wani dalili, kuma ai bakaji nace ina sanka da bakina ba ko"! ta karasa tana haɗe fuska tare da kawar da kanta. murmushi yayi har saida taji sautin fitar shi, kamar bazaiyi magana ba taji yace "amma nasan kema kina bukatar wani a tare dake, shiyasa har kika kasa hakuri kike so na sake ki ki auri wani, koba haka bane "? ya sake jefa mata tambayar yana wani shu'umin murmushi.. da sauri tace "banajin wani abu ni, dan zan iya karasa rayuwa ta ba tareda na nemi wani da namiji ba..." maƙale kafaɗa yayi yace "shikenan tunda haka kikace bari na tabbatar da gaskiya kika faɗa.."! tashi tayi zata gudu taji ya fizgo da ƙarfi, mutsu mutsu ta shiga yi dan kwatar kanta amma ko gezau hannunsa baiyi ba, kamar jira yake yake ta buɗe baki zatayi Magana saiji tayi ya haɗe bakin su waje ɗaya.. wani zazzafan kiss yake yi mata kamar zai cinye bakin gaba daya, duk yadda taso ya sake ki yayi, tun tana kokarin kwantar kanta har saida ta gaji ta hakura. Habib kuwa tuni ya fara nisa, dayake Gwarzo ne wajan iya abin tuni ta fara mayar masa da martani suka cigaba da aikawa da juna sakwanni.. sunyi nisa sosai harya fara zarce wa da romancing yaji karar wayar shi. zare jikin shi yayi daga nata yana maida numfashi idanuwan shi duk sunyi ja, jiddah kuwa ƙasa tayi da kanta cikin tsananin kunyar biye mai da tayi. cikin husky voice taji yace "yanzu na gano gaskiyar"!.. jin an sake kiranshi ne yasa ya matsa yana daga wayar ganin mommy ce. dakyar ya iya saita kanshi ya daga wayar. "Habib ina jiddah ne tun ɗazu bata dawo ba.."! "gata nan tana dan dafa min ruwan zafi ne, zan gasa jikina saboda ko motsi nakasa yi" "ok tayi hanzari ta dawo to"! "ok Mom" yayi saurin ajiye wayar jin tana ta kokarin fizge hannun ta. "an faɗa miki nidin rago ne da zaki iya kwace wa a hannun na" "dan Allah yaya Habibullah ka sakemin hannu na tafi" murmushi yayi yace "yau ai anan zaki kwana, better for you kawai ki nutsu ma yarinya" ganin da gaske yake bazai barta tafi ba tace "shikenan naji amma kasan me zaka fadawa mommy da safe"! kallan fuskarta yayi ya danyi murmushi yace "naji," "to sakemin hannu nayo wanka" sam bai kawo guduwa zatayi ba yana sakinta tayi hanyar fita da gudu, sannan ya leko yanayi masa gwalo yana daga Kafa ta sa gudu tabar ɗakin yana jiyo rufe palourn shi datayi. dariya ta bashi ganin yadda take cin uban gudu kamar zata tashi sama, saida ya gama murmushin shi sannan ya tashi ya shiga wanka cikeda farin ciki.. a firgice ta shiga palour, mommy na ganinta tace "keda waye kike gudu haka, "mommy kin sanni da tsoro" "shine kike wannan gudun, ta faɗa tana dan nazarin jiddan" "eh wlhy, ji nake kamar an biyo NI"! tana faɗa ta wuce ɗakin ta dan ta lura da irin kallan da mommy keyi mata.. sai wajan 8:00am jiddah ta tashi, dan sosai yau bacci yaki sakin ta, da sauri sauri take shirya wa tana gamawa ta dauko jakarta ta fito palour. kai tsaye dining room ta shiga, yana zaune cikin wani ligt blue na yadi mai shegen taushi gaba daya dakin ya gauraye da ƙamshin turaren sa, cak ta tsaya takasa ƙarasawa kusa dashi, bai kula da ita ba saida ya ɗago ya ganta takasa karasowa. harya buɗe baki zaiyi magana mommy ta shigo, "ya kika tsaya anan, lokaci fa ya kure zakiyi asarar lecture ta farko"! "umm kyaleta mommy, may be wani abu take tunawa take tsoron kar a maimaita" yayi maganar shi hankali kwance. "wanne abu Kenan" mommy ta tambaye shi. "ina nufin may be tana tunani kar tayi asarar text ɗin da zatayi irin na wancan satin"! "ok to kinji saikiyi saurin kammalawa ki wuce". Habib yagama ba jiddah mamaki, saiya yanko magana ta wayance dayin karya, sam yanzu yagama sauyawa halayen sa sun canja sosai ba kamar da ba mommy kuwa saurin yadda takeyi dan tasan Habib bai iya tsara zance ba. kuma abinda yafi bata mamaki ko alamun sakin fuska babu a tare dashi fuskan nashi a haɗe ta yadda dole mommy ta yadda da maganar shi. zama tayi kawai tafara cin abincin, kasa ƙasa yayi da kanshi saitin kunnen ta yace "kin gama gudun yanzu kuma gamu tare" yana faɗa ya tashi ya fice palour. *Kuyimin afwa readers rashin yin typing dina inada babban dalilin shiyasa amma yanzu komai yayi dai dai, na dawo da hot ɗina😀😛😛* Maman hajiya shamsiyya mamman Maman hmy fathema abdull dnj firdausi daughter Kuna Raina a kowanne lokaci 🌹🌹 [1/19, 11:33 AM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч αmєєnα muѕα *{🌹fírѕt lαdч🌹}* *wαttpαd* Ameenafirstladyy {45} ...Fitar Ameenu daga office ɗin ya ɗan kwantar da kanshi kan table ɗin dake gabansa, sam bai damu ba saboda yasan yau zai kasance da matar sa danya tabbatar zuwa yanzu mommy tasan komai.. mommy kuwa ko tayar da maganar batayi ba ta kyale jiddan, ita kuwa ganin mommy batayi mata magana ba yasa tayi shiru batace komaiba ba sai murna da takeyi a ranta, duk da batasan yadda zata kaya tsakanin ta da Habib ba. sai yamma sosai ya nufo gida, da kyar ya iya kai kansa gida saida Ameenu ya dage ya bari ya kaishi amma yaƙi yace yayi driving ɗinsa da kanshi. ko jakar shi bai ɗauka ba ya nufin part ɗinsu mommy,.. tana zaune a palour taga shigowar shi, da sauri ta tashi tana masa sannu da zuwa. murmushi yayi kadan kawai ya zauna yana lumshe idanuwanshi. "Habib yanzu ka dawo ne"! mommy dake saukowa ta tambaye shi. "eh yanzu na shigo" "kalau kake kuwa na ganka kamar baka da lafiya"! "kalau mommy na, kawai gajiya ce" "alhamdulillah to saika tashi kayi Sallah kazo muyi dinner" a hankali ya tashi dan bayaso ta fahimci wani abu, wani kallo yayi wa jiddah dauke da murmushi sannan ya fice ya bar palourn. wanka ya faɗa ya gasa jikinshi sosai da ruwan zafi sannan ya fito ya shirya yayi Sallah, ji yayi bazai iya komawa wajan su mommy ba gashi har yanzu baya jin shi dai dai juriya kawai yakeyi. wani farin ciki yake ji a ranshi saidai baiji mommy tayi masa wata magana data danganci maganar su shida jiddah ba. "to kodai so takeyi saimun gama dinner Sannan tayi min maganar"!? ya tambayi kanshi, baiso komawa part ɗin nasu ba amma haka ya tashi ya nufi ɓangaran nasu cikeda kwarin guiwa.. duk sun zauna shi kawai suke jira ya shigo sai zuba ƙamshi yake yi. "kabari sai jiran ka mukeyi" "I'm sorry mommy wanka na ɗanyi" "shikenan" kawai tace tafara cin abincin ta har suka gama cin abincin ya zauna yana kallan dole danshi ba ma'abocin kallo bane, ganin babu alamar yi masa maganar ne yasa ya tashi yace saida safe mommy, sannan ya kalli jiddah da Abdul ke kwance kan cinyar ta yace "ki kawo min wani abu mai dan zafi nasha"! "kace ta kawo maka coffee ko ruwan lipton kawai meye ne wani abu mai zafi" murmushi kawai yayi jin Maganar mommy baiyi magana ba ya fice daga palourn.. mommy ta mikawa Abdul sannan ta shiga kitchen ta haɗa masa hot coffee, har zata fita mommy tace "Ni zanje na kwanta ki dawo da wuri ki kwanta" "tam mommy, yanzu zan dawo" palourn nashi a rufe saida tayi nocking sannan ya fito ya buɗe, saurin kawar da kanta tayi ganin shi babu riga sai wando trouser. shikuwa yana buɗe mata yaga tayi saurin kawar da kanta ya taɓe baki, a zuciyarshi yace "kiyi ki gama yau kam bazan kyale ki ba" yana gama zancan zucin sa ya wuce daki ya barta da cup a hannu. ajiyar zuciya ta saki dan ganin Habib haka saida ta dauke numfashi, zama tayi akan kujera tana raba idanuwa dan bazata iya shiga yana irin yanayin ba, kusan mintina goma ta dauka a zaune bata shiga ba, cikin kwarin guiwa ta nufi ɗakin nashi dan tasan zuwa yanzu ya gama shiryawa kuma tasan ko kwana zatayi a zaune anan bazai fito ba. ganin baya dakin ya tabbatar mata da yana bathroom, ajiye cup din tayi zata fice dai dai fitowar shi daga bathroom din yana rike da towel yana goge kai. kallan kallo suka shiga yi ita kuwa sam hankalin ta bata tareda shi duk da idanuwanta na kanshi amma sam ƙwaƙwalwar ta bata wajan. murmushi yayi ganin ta zaro dara daran idanuwan ta kuma da alama bashi take kallo ba. a hankali ya tako zuwa kusa da ita, batayi tsammani ba saijin numfashin ta tayi yana haduwa da nashi, a razane ta ɗago kai tana kallan shi, kallan dayake mata ne yasa tayi kasa da kanta kan faffadan kirjin shi wanda ya yalwatu ta gashi kwance, jikin shi murde na cikakken namiji.. "yadai, wannan kallo haka"! ya faɗa yana kara matso da kanshi saitin fuskarta. baki ta turo gaba "mezan kalla wanda ban sani ba"..! "gashi kuwa duk kin kasa komai ganina a haka"! a tsorace ta ɗago kanta dan batayi tunanin a fili tayi maganar tata ba sai amsar shi kawai taji. kasa motsi tayi tana ji yayi murmushi mai sauti sannan yabar kusa da ita,,. jin alamun yana rufe kofar dakin ne yasa jiddah dagowa a zabure tana cigaba da zaro idanuwanta. gira ya daga mata yana wani ni'imtaccen murmushi wanda tafara gano ma'anar shi. "yaya Habib dan Allah ka buɗe min na fita"! make kafaɗa yayi yana wuce wa ta gabanta zuwa wajan mirror ɗinshi yafara ƙalƙale jikin shi bai jiyo ya kalleta ba.. kamar zatayi kuka ta sake cewa "dan Allah ka buɗe min" kallo ta yayi ta mirror yace "ki ɓude mana ki fita ga hanya nan" ya faɗa yana cigaba da abinda yakeyi. yana kallanta ta isa bakin kofar tana kokarin budewa dariya ta bashi ganin yadda ta dage tana bugun kofar.. har saida hannun ta yafara zafi sannan ta dawo bakin gadon ta zauna ranta a ɓace tsaf ya gama shirin shi sannan ya dauko maganin shi yasha ya dawo kusa da ita.. yana zama ta tashi tsaye ya riko hannunta sannan ya juyo da ita yana kallan fuskarta.. "meyasa baki sanar da mommy ba"!? ya jeho mata Tambayar.. "batayi min zancan ba, ni...kuma..ina.kunyar faɗa mata". ta bashi amsa cikin in Ina. cikeda jin haushi yace "kunya kike ji shiyasa kika kasa faɗa mata kenan" "eh" ta bashi amsa. "shikenan tunda bazamu iya faɗa mata ba, zata gane da kanta" ɗago kanta tayi ta kalle shi, sai taga ya kashe mata ido yana murmushi. "gaskiya bazan iya ba" "Ni kuma zan iya" zata fara marairaice murya taji ya haɗe bakinsu waje ɗaya.. cikin kankanin lokaci suka fice hayyacin su nayi saurin barin ɗakin 🏃🏃🏃.. (Anki a dauko rahoton😂😂) tuni bacci ya dauke ta sai sauke ajiyar zuciya take tana fitar da numfashin wahala kana gani kasan ba baccin daɗi take ba, shi kuwa yana kwance gefenta ya zuba mata ido murmushi ya kasa kwacewa fuskar shi, ya rasa ta yadda zai misalta yanayin dayake ciki a yanzu, wani lallausan murmushi ya sakeyi daya tuna magiyar ta a daran jiya, sannan ya gyara mata bargon daya rufe ta ya tashi ya shiga bathroom dan bazai iya komawa baccin a wannan lokacin ba. sallah yayi raka'a biyu sannan ya zauna yana addu'oi har aka kira sallar asuba,. motsi ta farayi jin sanyin asuba, a hankali ta buɗe idanuwan ta da sukayi ja tana buɗe wa suka hada ido tayi saurin rufe wa. jin maganar shi tayi a kusa da ita "my half ki tashi asuba tayi"! ko motsi batayi ba balle yasa ran zata amsa masa. murmushi ya sakeyi mai sauti yace "kunyar ce har lau, ashe akwai sauran aiki kenan, bari nayi kokarin ƙarasawa" ya faɗa yana yaye blanket din data rufa, wata yar siririyar karar shagwaba ta saki tana rike bargon. shi kuwa saurin rufe kunnen shi yayi yana dariya, sannan yace "to tashi na kaiki bathroom din"! girgiza kai tayi tace "zanje" da kyar ya lallaɓata kamar wata yarinya ta nufi bathroom din a hankali take tafiya.. saida ta shiga sannan yayi murmushi ya gyara gadon da dakin.. haka ta dinga zuba masa shagwaba iri iri, dan itama yau wasai take jinta.. da kanshi ya haɗa mata ruwan tea Tasha danya warware mata ciki sannan ya bata magunguna tasha dan yaga tafiyar bata sauya ba, tana sha wani baccin ya ɗauke ta.. tsananin mamaki ne ya kama mommy ganin jiddah shiru bata fito ba, ɗakinta ta shiga taga wayam har bathroom da toilet da duba bata ga jiddah ba, ga wayarta a kan bed ɗinta bataje ko ina da wayar tata ba. Kiran Habib tayi shima wayarshi a kashe tuni gabanta ya fara faduwa tana Tambayar kanta inda jiddah ta tafi, dan sam bata taɓa kawowa kanta tana wajan Habib ba.. a firgice ta tashi tana kallan agogon dake gefen gadon shi kan drawer, ganin 9:25 yasa tayi saurin saukowa daga saman bed din tana waige waige, ganin baya dakin yasa ta nufi palour. yana zaune da laptop a gabansa da alamu aiki yakeyi sosai, yana ganin fitowar ta ya tashi yana mata murmushi. "my cute, kin tashi"? hawaye ne ya zubo mata da sauri ya matso kusa da ita yana rike kafadun ta yana kallan face ɗinta yace "lafiya meya faru, ko haryanzu kina jin ciwo ne"? ya jero mata Tambayar a jere. kai ta girgiza, yace "to menene"? da kyar bakinta ya furta "mommy"! ajiyar zuciya ya saki sannan yace "karki damu muje nizan faɗa mata komai, kuma idan zatayi faɗa Ni zatayi wa ba ke ba kinji"! ya faɗa yana rungume ta tsam a jikin shi, sannan ya ɗago ta ya share mata hawayen ya rike hannun yace "muje to"! dakile wa tayi taki tafiya ya juyo yana kallanta "muje mana"! "kabari zanje nayi mata bayani nasan zatafi fahimtata"! "idan tayi miki faɗa fa"? "bazata yi ba mommy tana sona bazatayi min faɗa ba saidai nasiha" ta faɗa tana yin murmushi danta kwantar masa da hankali. "shikenan muje na raka ki" "a'a ka barshi, banaso tasan tare muke"! murmushi yayi mata ya manna mata kiss a goshinta da lips ɗinta sannan ya rike hannunta suka fita. suna fita tace ya koma da kyar ta samu yabarta ta tafi yana hango ta harta kusa shiga sannan ya koma ciki ya fara shirin tafiya wajan aiki. ta daɗe a tsaye kofar shiga palourn ta kasa shiga, saboda tsabar fargaba, batasan me zata cewa mommy ba Dan tasan idan shine yazo da kanshi saiya fi shan faɗa amma idan itace bazatayi mata sosai ba shiyasa kawai ta taho ita kadai dan bataso ranshi ya ɓaci tunda itace silar komai.. mommy na zaune ta zuba uban tagumi taga shigowar jiddah, kamar munafuka, da hanzari mommy ta tashi tana fadin "jiddah ina kikej...." cak ta tsaya ganin irin tafiyar da jiddan keyi kuma tana hawaye.... *🌹 First lady🌹*✍️ [1/26, 9:07 AM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч αmєєnα muѕα *🌹fírѕt lαdч🌹* *wαttpαd* Ameenafirstladyy {46} cikin wata razananniya da firgitacciyar murya ta kamo hannun jiddah "na shiga Uku jiddah daga ina kike meya same ki" ta jera mata tambayoyi har biyu. kasa amsawa tayi taci gaba da hawayen ta dan batasan ta yadda zata fara ba kuma dayake tasan babban laifi ne sukayi ita da Habib ɗin saidai dole yau mommy ta sani ko wanne irin hukunci zatayi musu... kamata mommy tayi har ɗakinta ganin bazata faɗa mata komai ba, saida ta tabbatar tayi shiru sannan tafara lallashin ta cikin taushin murya. "jiddah ni mahaifiyar kice, zan iya gane duk wani yanayi da kike ciki kuma zanji daci da bakin ciki musamman idan na tuna ke kamar amana ce a wajena, nasan kinyi kokari wajan kare mutumci da kimar ki na wasu shekaru amma yau daya kin zubar da wannan kimar da mutumci...." hawaye ne suka zubowa mommy na kunar zuciya. a firgice jiddah ta kalli mommy tsoro biyu ya haɗe a zuciyarta, kenan mommy zarginta takeyi da tabi wani namiji, sannan harta kai da ta zubar da hawayen ta.. tashi mommy tayi zata fice bayan ta share hawayenta, ji tayi jiddah ta kamo hannun ta, dan juyowa mommy tayi tana kallan jiddan fuskarta babu alamar walwala. cikin kuka jiddah tace "mommy Dan Allah kiyi hakuri ba yadda kikayi tsammani bane, Habib.. Habib..ne...! shiru tayi takasa ƙarasawa. jagwab mommy ta zauna kusa da jiddan, dan ta fahimci zancen jiddan tunda ta ambaci sunan Habib. kamo hannunta mommy tayi cikin nata sannan tace. "Habib ne"? daga kai jiddah tayi batace komaiba. a zafafe mommy ta tashi zata fice da sauri jiddah ta tare gaban tana rungume mommy. "mommy karki ga laifin shi nice mai laifi dana kasa faɗa miki gaskiya tun lokacin daya mayar da auran mu, nayi hakane saboda wani banzan dalili na amma nagane kuskure na dan Allah mommy kiyi haƙuri"! mamaki da farin ciki ne ya gama kama mommy, takasa boye farin cikinta ta ɗago da Jiddah... "shikenan bari na haɗa miki ruwan zafi kiyi wanka muke kiyi breakfast" tana gama faɗin haka tabar ɗakin ta shige bathroom ɗinta ta haɗata mata ruwa mai zafi sannan tace ta tashi ta shiga, saida taga shigewar jiddan sannan ta fice dauke da murmushi.. gajiya yayi da zaman jiran ya kira wayarta yaji yadda tayi da mommy Amma yaji a kashe, tsaki ya danyi cikeda fargaba ya shiga wanka dan tafiya office.. yana fitowa kiran mommy ya shigo, a darare ya daga wayar haɗe dayin sallama. "bazaka je office bane yau"? "zanje yanzu zan shigo ai" "shikenan ina jiran ka" tana gama faɗa ta ajiye wayar ta, sannan ta ɗauki abincin jiddah takai mata dakinta. cikin kunya jiddah takasa ɗago kai ta haɗa ido da mommy, murmushi mommy tayi ta ɗago kan mata tace "yau kuma mommyn taki kike jin kunya" ƙasa ta kumayi da idanuwanta, sannan taji Muryar mommyn ta sake katse ta. "jiddah kinasan ci gaba da zama da Habib"? jin Tambayar mommyn ne yasa ta ɗago kai tana kallan mommyn har hawaye sun fara taruwa a idanuwan ta. "wlhy ina sanshi mommy dan Allah karki ce zaki raba mu"!... katse mommy tayi dauke da murmushi tace "nima ba niyya ta kenan ba, zanfi kowa jin dadin kasancewar ku tare amma banaso nayi miki dole a wannan karan, tunda kin amince shikenan zanyi magana dashi Habib ɗin naja masa kunne akan ki sannan banaso ki ƙara yadda dashi har sai kin tare kamar yadda aka tsara tun farko" nodding Kai kawai jiddah tayi sannan mommy ta fice daga ɗakin.. yana gama shiryawa ya nufo ɓangaran mommy cikeda kwarin guiwa, babu kowa palourn ya nufi dining room, mommy na zaune tana gyara table ɗin taji ƙamshin turaren shi. juyawa tayi ta kalle shi ta ɗauke kai. "bazaka shigo bane ka tsayamin anan" basarwa yayi ya shigo ya ajiye jakar zuwa aikin shi sannan ya gaida ta ta amsa amma bata saki fuska ba. "idan ka gama ka same ni a sama" bata jira amsar shi ba ta fice.. yana shiga ya same ta a Zaune tana jiran zuwan shi, kasan kafarta ya zauna yayi kasa da kanshi kamar mara gaskiya. "Habib.!" "na'am"! "meyasa ka ɓoyemin maganar auranka da jiddah tsawon lokaci kana zalin tar kanka"? shiru yayi yakasa bata amsa. "ta fadamin komai kuma na gamsu dan nasan bazata yi min karya ba, Sa'a daya kaci jiddah nada hakuri da harta amince da cigaba da zama dakai, tunda kun sasanta kanku saika fara shirin tarewar ku a saban gidan daka gama dan baza'a fasa ba, sannan ka samu lokaci kuje can ƙauye ku sanar dasu.." murmushi ne kwance kan face ɗinsa, har mommy tagama jawabin ta yace "Nagode mommy nizan wuce asibiti" "saika dawo" harya tashi zai fita tace "sannan banaso wani abu ya sake shiga tsakanin ku har saikun tare ina fatan kaji abinda nace" dariya yayi kasa ƙasa yace "angama mommy baza a sake ba" dariya tayi tana yi masa daƙuwa, shima yana dariyar ya fice. a palour ya tsaya kamar ya shiga ɗakin nata sai kuma ya fice kawai cikin farin ciki.. tana daki taji fitar shi, wayar ta ta dauko ta kira Afnan da khairat ta sanar musu. "sai wani ɗoki kikeyi kamar ba kece me cewa batasan Habib ba wancan lokacin" cewar khairat wacce itama ake shirye shiryen bikinta da Kabir.. "da kenan yarinya ai yanzu inasan abin na".. haka dai suka dinga hirar su tsakanin su.. yau Habib kowa yayi mamakin sa a wajan aiki dan babu faɗa ba wani dacin rai sosai amma babu wanda ya tambayi dalili musamman da suka san halin shi yanzu saiya juye musu. sai yamma ya dawo, a palourn ya samu su hibban da Afnan sai khaleesat da Abdul da suke ta faman rashin ji, gwanin sha'awa sai hira sukeyi. yana shiga jiddah tayi kasa da kanta dan yanzu kam nauyin shi takeji sosai, yana ankare da ita murmushi kawai yayi ya ida shigowa palourn, mommy na ganin shi ta dan taɓe baki tace "hmm yau kuma"! babu wanda ya gane abinda take nufi sai hibban ne ya lura da fuskarshi wasai ba damuwa yace "yaya yau lafiya kuwa kake ta fara'a haka.."! hararan shi Habib yayi kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru yana tsuke fuska. "kayi murmushi mana tunda matarka ta dawo, nidai abinda nasani ko bacin rai ka sata saina raba auran dan ina san ƴata fiye dakai Gara ma kaji karka dinga bata mata rai atoh".. su duka sukayi dariya har Habib ɗin saida yayi murmushi sannan ya tashi ya fice ya barsu suna cigaba da dariyar su.. "gaskiya naji daɗin haka jiddah, dama na faɗa miki yaya Habib yana sanki lokaci ne bai bada damar kisan haka ba amma gashi yau yabaki dama" hibban ya faɗa yana mata dariya. Afnan na zaune itama tace "ammafa duk da haka saikin dinga haɗawa da hakuri, dan wannan halin nashi na miskilanci da sakin fuska duk bazai daina suba saidai ya rage.." hararan wasa jiddah tayi mata tace "bakisan yanzu su nafi so a game da halayensa ba ni sai yanzu ma na yarda yaya Habib na musamman ne a cikin maza.." "eee lallai yau kanwata ta rufe idanuwanta" hibban ya faɗa yana riƙe haɓa.. dariya suka dinga yi masa daga karshe ya bar musu dakin shima yana dariya.. cikin yan kwanaki mommy ta tsara komai har sabbin akwatuna da furnitures tayo odar su wanda ta kashe kudi harda na ban mamaki, Habib yaso hanata yace zai siya tace ita bata yarda ba so takeyi tayiwa yarinyar ta kamar yadda kowacce uwa kewa yarta haka ya kyale ta tayi da kanta. sati biyu kawai aka tsayar da ranar, tuni mommy ta ɗauko mai gyaran amarya tafara gyara jiddah gyara na musamman. yau suka shirya zuwa ƙauye su fado tarewar, daga mommy sai jiddah sai Habib ɗin dake yin drivern. an tarbe su hannun bibbiyu.. sun so tahowa da jiddah amma inna marka tace abar mata ita tayi kwana biyu zata haɗa mata nasu magungunan irin na ƙauye badan mommy taso ba tabar jiddan tace zata dawo da tafi da ita jibin, har bakin mota ta rako mommy suka tafi, Habib kuwa ko kallan inda take baiyi ba tsabar takaici dan gani yake kamar itace tace zata zauna. "amma mommy bai kamata ta zauna har kwana biyu a irin wannan ƙauyen ba, dan ko abincin su ba lallai ta iya ci ba"! haɗe fuska mommy tayi tace "banasan zancan banza, kai zasuyi wa gata ai saina hana su kake so kome"..! "gata sukemin ko cuta ta dai"! ya faɗa a ranshi.. sai dare suka isa gida, ta kira wayar mommy suka sha waya sannan mommy tayi mata faɗa akan duk abinda suka bata ta tabbatar tasha gata suke mata, cikeda kunya tace "to momma" sannan sukayi sallama, ta kira Habib. kamar bazai daga ba saida ta kusa yankewa sannan ya daga a daƙile ya amsa sallamar Tata. murmushi ta ɗanyi dan tasan bakaramin zuciya yayi ba tunda taji shi haka. "idan bakida magana zan yanke wayata" "dama cewa zanyi kunje gida lpy" "eh munje"! ya bata amsa a takaice. "kayi hakuri bazan iya yin jayayya da maganar su.."! "ok shiyasa kika manta da neman izinin a wajena kenan" "I'm sorry izinin mommy nabi but I'm so sorry"! tanaji ya saki ajiyar zuciya sannan yace shikenan ya hakura suka ci gaba da wayarsu cikin nishadi da kaunar juna.. kwana biyu mommy tazo ta ɗauke ta suka koma gida akaci gaba da gyaran jiki..... *Alhamdulillahi Ala Kulli Halin*✍️ [1/26, 9:07 AM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч αmєєnα muѕα *🌹fírѕt lαdч🌹* *wαttpαd* Ameenafirstladyy {47} .... Tunda ta dawo mommy ta hanata fita daga daki sai ɗaki dan ko palour bata fita koda yaushe suna daki ana mata gyaran jiki ko shan magunguna kala kala harta fara gajiya. Habib tun yana nacin da faɗa harya gaji ya kyaleta kawai yaci gaba da shirye-shiryen taron da zasuyi.. saidai koda yaushe suna maƙale ta waya ba dare ba rana.. kwana huɗu ya rage yau mommy ta shirya kamu na Musamman, anyi kamu angama lafiya gida duk ya tara jama'a.. washe gari da yamma aka dunguma zuwa walima cikin wani babban hall da aka kayata shi abin sha'awa. yaso mommy tace yazo ya kaisu danya ga jiddah amma tace bata yarda ba saidai yayi nashi zuwan daban shida abokansa tunda walimar harda shi aka tsara. tare yaje dasu Sultan da Dr Ahmad daman sune manyan abokan nashi da yake dasu, saida kowa ya hallara sannan su mommy suka zo wajan tana rike da hannun jiddah wanda yasha bakin lalle da ja. kanta na kasa rufe har mommy ta kaita kusa dashi ta zaunar da ita sannan ta dan matsa kusa dashi daya kafe su da idanuwa Kamar ya lashe.. "saura kayiwa mutane rashin kunya a wajan walima" murmushi shima yayi ya matso da kanshi kusa da mommy yace "amma ai ta buɗe fuskar tata ko mommy"! dukan wasa takai masa ya farayin dariya, basu wani daɗe da zuwa ba malaman da aka gayyato suka fara nasiha da wa'azi duk hall ɗin yayi tsit da alamu maganganun suna shigar su.. har aka gama ba wani hayaniya shiyasa Habib bai damu ba shida bayasan hayaniya ko kadan, lokaci zuwa lokaci yake kai kallanshi kanta amma sam har aka tashi bata ɗago ba kanta na ƙasa cikin wani mayafi mai shegen kyau.. a matuƙar gajiye suka koma gida, shi dai Habib duk takaici ya gama kama shi na hanashi ganin amarya shi da akayi, yanzu ma dayake driving zaikai Dr Ahmad gida da Sultan tare da matan su sai surutu sukeyi shidai yayi shiru kawai.. "wai Habib yadai duk ka wani shiru kamar ba shagalin ka akeyi ba" tsaki ya ɗanyi sannan yace "Sultan kyale ni kawai ina bukatar matata amma ko ganinta ya faskara"! su duka sukayi masa dariya har Angelina da take ɗan jin Hausa yanzu. "kaida zaka tafi da ita gaba daya kubar gidan ma meye na wani jin haushi" shiru yayi kawai bai ba Dr amsa ba dan yasan bazasu fahimci irin abinda yake ji gameda matar tashi ba.. dare nayi ya shigo palourn su, mutane sai tsokanar shi sukeyi amma bai saurare suba, yanaji suna masa tsiya wai dama wannan ɗan kurman ba kula ku zaiyi ba wannan jiddah ta shiga Uku kafin ma ta koya masa magana aiki ne balle akai ga su saba.. sosai maganar tasu tabashi dariya har ya shiga dakin mommy yana murmushi. "kalau kuwa ka shigo kana faman murmushi kai kaɗai"? "babu" "to me ya kawo ka dakina na"!? "ohh! momma coffee nakeso kisa jiddah ta haɗa min"... kallan shi tayi kamar tanasan cewa wani abu sai kuma yaji tace "shikenan zata kawo maka"! bai ja maganar tasu ba ya fice yana godiya kawai tun kafin ta sauya shawara.. dakin jiddan ta shiga tana zaune da wasu ƴaƴan makwabtan su na ƙauye da aka zo dasu suna ta hira mommy ta shigo tace ta shirya taje ta haɗa masa coffee yace takai masa part ɗinsa. amsawa tayi sannan ta shiga kitchen ta haɗa masa hot coffee ta ɗauko mayafinta ta wuce kai masa.. tunda ta shigo dakin ya kafe ta da idanuwanshi ko ƙiftawa bayayi harta karaso ta ajiye masa kan table tace "ga coffeen Nan na kawo"! murmushi yayi sannan ya taso ya riƙo hannun ta yace "aiba yanzu zan sha ba" ɗago dara daran idanuwan ta tayi zatayi Magana taji yace "mata ta naso gani dama, ko nayi laifi"!? "a'a bakayi laifi ba amma haɗa zance babu kyau ai" wani lallausan murmushi yayi har kyawawan fararan haƙoransa suka bayyana reras dasu. "haɗa zance ma kamawa takeyi ai, anayin tane dan asamu hanyar bullewa.." dariya itama tayi tana ƙasa da kanta.. "zan koma kar mommy ta dawo taji ban dawo ba" "to menene aita san kina nan wajan mijinki" "amma.."! "shhht! ki saki jikin ki babu abinda zata ce nima kuma babu abinda zanyi miki kawai zaki ɗan tayani hira ne before you leave"! saida ya gama shan coffeen sannan yace ta taimaka ta dafa masa noddle Dan yunwa yake ji.. bata tafi ba saida ta dafa masa sannan ya zaunar da ita yace tare zasu ci danya fahimci bataci komai ba itama.. dakyar ta samu ya rako ta ta dawo sannan ya koma cikeda kewar matarsa.. ranar dinner party kuwa sai yamma sannan aka fara shirya jiddah, tana dakin su inna marka can aka kai makeover tafara tsantsara Mata kwalliyar ban mamaki.. "wannan kwalliya kamar baza a goge taba kai jama'a ƴan birni kuna abinda kuka ga dama a bi a narka kuɗi akan wannan aikin banzan" inna marka take ta faman tsiya kamar wacce da kuɗin ta zata biya. "inna idan kinaso kema ki zauna ayi miki idan bahaka ba ko hall ɗin baza a barki ki shiga ba". "yo Kar a bari mana dama nace muku zanje ne irin wannan wajan saika ga wata kamar aljana haka kawai nakai kaina na dawo a razane" dariya sukayi tayi mata har aka gama mommy ta kawo mata kayan ta. wata haɗaɗɗiyar dinner gown ce sky blue har Ƙasa take ja cikin kankanin lokaci aka cakara mata head tie ɗinta ta fito kamar ba ita ba.. tuni motocin kawayen ta suka tafi, dama Habib ya dame su da kira tayi sauri ta fito lokaci yana kurewa.. Sultan ne yaja su har hall din suna zuwa suka wuce wajan da aka tanadar musu sannan aka fara gudanar da taro sun zama taurari a wajan kashewa kowa ido sukeyi da kyaun su.. duk wani motsin su tare da yaron su sukeyi wanda shima aka ƙure masa wanka kamar ba yaro ba yana tsakiyar su abin gwanin sha'awa... (wannan shine ake kira da ƙara'i😂😂😂😂) a matuƙar gajiye suka dawo daga wajan dinner saidai duk takasa cin abinci duk da tana jin yunwar, mommy harta gaji da lallashinta ta fice tace ai cikin tane.. Habib na shigowa palourn mommy ta fito daga ɗakin jiddan tana mita. "yauwa tunda kai tanajin tsoron ka har Yanzu saikaje kasa ta taci abinci tunda ni bazataji tawa ba, ayi yarinya da shegiyar kafiya" ta faɗa tana barin palourn.. kai tsaye dakin ya shiga, kawayen nata na ganin shi fuskar nan a haɗe suka fice, da sauri ta tashi tsaye tana rarrabe idanuwa kamar munafuka. jin saukar hannuwanshi tayi a ƙugunta tago kai tana kallan shi.. "meyasa ƙika ƙi cin abinci"!? "na koshi ne..."! ji tayi ya haɗe bakinsu waje ɗaya ya fara yi mata wani salo na musamman saida ya tabbatar ta nutsu sannan ya sake kallanta da idanunshi da suka yi wani iri yace. "kinaso ki jamin matsala ne, kinsan fa ba'a so mace ta zauna da yunwa kota dinga ci fiye da ƙima duk suna haifar illa.."! zata sakeyin magana ya kuma haɗe bakin nasu, wannan karan kam saida tafara kokarin kwantar kanta sannan ya sake ta yana murmushi. "muje kici abinci, ko kuma.." yayi shiru yana ɗan cizan lips ɗinshi haɗe da cigaba da kallan ta da rikitattun eyes ɗinsa... ✍✍[1/27, 9:49 PM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч αmєєnα muѕα *🌹fírѕt lαdч🌹* *wαttpαd* Ameenafirstladyy {48} ...... kamar yarinya haka ya kama hannunta har dining room, saida ta zauna sannan yasa mai girkin ta kawo masa abinci. fafur taki yadda ya bata tace da kanta zata ci basaiya bata ba, kyaleta yayi kawai ya fice yana dariya.... tana gama cin abincin ta, ta koma ɗakinta tanaji kawayen nata na tsokanar ta amma bata kula su ba tunanin mijinta ne fal zuciyarta har bacci ya ɗauke ta. tsabar gajiyar jiya saida ta makara tashi da safe tunda tayi sallar asuba ta koma bacci, saida mommy ta turo abdul tace yazo ya tashe ta sannan ta tashi. "good morning ummy" Abdul ya faɗa yana dariya. hararan shi tayi tace haka ake tashin mutum daga bacci ayi masa ƙara a kunne"! marairaice murya dan yaga ta bata rai yace "I'm sorry ummy bazan sake ba".. "hmm, da kyau yarona kaje kacewa mommy gani nan fitowa"! "to" ya faɗa yana ficewa sannan ta shiga bathroom danyin wanka.. saida ta gama wanka ta fito sannan taji ƙarar wayarta tana dubawa taga Habib ne, fuskarta ɗauke da murmushi ta daga da sallama. amsawa yayi sannan yace ta zo tayi masa abinci yunwa yake ji.. "mommy bazata barni ba saidai nayi na aiko maka dashi" "No kibari kawai" yana faɗa ya kashe wayarshi tasan haushi yaji amma babu yadda zatayi dan mommy ba barinta zatayi ba. da kanshi ya tashi ya daga noddle, kaɗan yaci ya tashi ranshi a bace ya bar gidan gaba daya.. ganin bai sake kira bane har azhar ya tabbatar mata da fushi yayi sosai, sau biyu tana kiran shi yaki dagawa hakan yasa itama ta share shi kawai taci gaba da sabgar ta. mommy da kanta taje gidan daya gama aka shirya wa jiddah kayanta duk da sun samu nashi wanda aka riga aka jera su amma mommy Bata fasa zuba nata a palourn sama ba, gidan yayi masifar kyau dan sam ba tsarin kasar bane sama da kasa ne duk wanda yaga gidan saiya yaba da kyan shi.. tunda akayi sallar magrib aka fara shirya jiddah dan kaita gidanta, saidai kukan da takeyi ne yabawa kowa tausayi musamman Wanda yasan dalilin kukan nata. dan dole aka fasa yi mata kwalliyar sai light makeup kawai Afnan tayi mata, mommy ma tana ɗaki zuciyarta a karye sam batasan rabuwa da jiddah saidai babu yadda zatayi dole su rabu ta tafi gidan mijinta.. duk yadda suka so jiddah tayi shiru ki tayi dan ko sauraran su batayi, saida akayi isha sannan mommy ta shigo dakin nata mutanen duk suka fita.. rungume mommy tayi tana kuka kamar wata karamar yarinya "dan Allah mommy kicewa Yaya Habib mu zauna anan wlhy banasan tafiya na barki"! murmushi dole mommy ta ƙaƙalo Dan kwantar mata da hankali sannan ta farayi mata nasiha mai ratsa jiki, da kyar ta samu ta hakura sai dai bata daina kukan ba... da kyar aka raba ta da mommy suka tafi tana kuka sosai.. kowa ya yaba da kyan gidan musamman mutanan ƙauye,.. Afnan da khairat ne keta faman lallashin jiddah amma takiyin shiru haka suka kyaleta suka ci gaba da hirar su kafin su tafi. inna marka kuwa sai raba ido takeyi tace "oh Ni Marka!! jiddo ya zaki iya zaman gidan nan ke ɗaya kuwa"! dariya su Afnan sukayi sannan khairat tace "inna ko zaki taya ta zama ne" daƙuwa inna marka tayi mata "gidanku khairat kinga nayi kama da zama a irin wannan gidan, kaɗaici ma kawai ya isheka". dariya suka kumayi su duka, jiddah dai tana jinsu batace komaiba ba dan har yanzu hawaye takeyi.. tanaji suka tashi tafiya, babu yadda zatayi haka suka barta ita kadai tana hawayen ta dan kukan ya daina fita mommy kawai take tunanin, saida ta gaji dan kanta sannan tayi shiru ta share hawayenta.. basu wani daɗe da tafiya ba taji shigowar motar Habib, gabanta ne ya fadi dan sai yanzu ta tuna tun safe da yayi fushi basu sakeyin waya ba... tana nan zaune taji shigowar shi, tago kai tayi tana kallanshi suna haɗa ido tayi saurin yin ƙasa da kanta ganin irin kallon dayake mata. murmushi ya ɗanyi sannan ya ajiye ledar dake hannun shi ya karaso kusa da ita ya zauna. ɗago kanta yayi yana kallan fuskarta saidai ita kasa ɗago kanta tayi sai hawaye daya zubo Mata. hannu yasa ya share mata hawayen sannan taji maganar shi ƙasa ƙasa. "kukan farin ciki ne na gani a tare dake har abada ko kuma na rabuwa da mommy da Abdul ne"!? ya tambaye yana kafe ta da idanuwanshi. tasan tsokanar yakeyi shiyasa tayi shiru bata tanka masa ba. tanaji yayi murmushi mai sauti sannan ya tashi yana cire Watch ɗinshi,. "shikenan ki tashi muyi salla naji matsalar daga baya"! ya faɗa yana sake kai kallanshi kanta. shiru tayi masa tana kallo ya shige bathroom din bai wani jima ba ya fito sannan ya kalle ta yace "oya tashi kiyo alwala"! kallan tayi kamar bazata tashi ba. "ko saina raka ki ne".. saurin girgiza kanta tayi sannan ta shige bathroom din tana jin dariyar shi kasa ƙasa.. sun daɗe suna addu'a bayan idar da sallar sannan suka tashi. ɗakin sa ya koma yayi wanka ya shirya cikin jallabiyar shi sky blue sannan ya dawo dakin nata.. tana cikin saka kaya taji shigowar shi, da sauri ta juya tana kokarin karasa sawa, ji tayi ya rike hannunta ta baya kasa juyowa tayi kuma takasa ƙarasa saka rigan sai jikin ta daya fara rawa. ganin haka ya sake ta ya koma Palour saida ya tabbatar ta gama shiryawa sannan ya shigo ya sameta a zaune gefen gado.. taɓe baki yayi sannan ya wuce ya kwanta abinsa saiji tayi ya janyo ta jikin shi ya rufe su da blanket.. cikin kunnen ta taji maganar kamar raɗa "ki saki jikin my wife".. tanaji ya fara sarrafa ta, ta gurzu iya gurzuwa har saida taji Kamar First night ɗinta.. Tasha kuka da kiran mommy, lallashi da lallaɓata kam yayi tana sane take dada shagwabewa duk tabi ta ruɗa shi takasa komawa bacci, saida yayi mata allura sannan ya samu bacci ya dauke ta.. da asuba ya tashi ya wuce masallaci dan yasan ba yanzu zata tashi ba saboda allurar dayayi mata sai zuwa 7 na safe hakan yasa yana idar da Sallah ya dawo gida.. sai bayan 7 sannan ta tashi, a hankali ta buɗe idanuwanta da sauri ta tashi ta sauko gadon dai dai shigowar shi dan lokaci zuwa lokaci yake lekowa kota tashi.. kokarin shigewa bathroom tayi saiji tayi ya dauke ta gaba ɗaya har bathroom ɗin. kuka tafara yi masa akan ya ajiye ta sannan ya fice yana murmushi danya gano harda shagwaban ta... sauti sauri take shiryawa karya shigo, tana gamawa ta fito palour, cikeda mamaki take kallan yadda ya gyara palourn sai ƙamshi ke tashi. "lallai yaya Habib akwai tsafta".. da kanshi ya haɗa musu breakfast, Tasha mamakin yadda yayi wannan aikin duk shi kadai. "kina mamaki ne"? "eh tayaya..." "kinga let's eat first sannan seki Tambaye ni" tare suka ci abinci tun tana dari ɗari dashi harta sake danta fahimci basan kunyar yakeyi ba.. ✍️✍️✍️ [1/28, 6:30 PM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч αmєєnα muѕα *🌹fírѕt lαdч🌹* *wαttpαd* Ameenafirstladyy {49} ....Duk wani motsin da jiddah zatayi yana manne da ita, har mamaki takeyi yadda gaba daya ya sauya kamar ba Habib ɗin data sani ba.. "yaushe zamuje dauko Abdul ne" ya katse mata tunanin ta. kallan shi ta ɗanyi sannan tace "mommy fa bazata bamu Abdul ba, Gara ma mubar mata shi kawai dan yafi sabawa da ita.."! bata tsammani ba saiji tayi ya dauke ta cak ya nufi ɗakin shi da ita, sai faman wutsil wutsil takeyi yaki sauke ta sai dariya yake mata. yana ajiye ta saman bed ɗinsa ta tashi zata sauko ya riƙo ta. "babu inda zaki saimun samawa Abdul kanwa ko Kani"! "what..."! ta faɗa tana zaro idanuwanta. ido ɗaya ya kashe mata sannan ya janyo ta jikin shi.. wunin ranar abu guda Habib ya dinga yi, tun tana janye wa harta saki jikinta bata koyi masa musu.. tsantsan soyayya zalla Habib ya nunawa jiddah a wannan ranar duk saita gane ashe duk yadda ta dauke shi bahaka yake ba.. cikin sati ɗaya har fatar jiddah saida ta sauya kallo ɗaya zakayi mata ka gano tsantsan jin dadi da farin ciki a tareda Ita, ɓangaran Habib kuwa har wani shining fatar jikin shi keyi tabbacin samun kwanciyar hankali a tare da shi.. yauma kamar kullum yadda yake taya ta haɗa breakfast Dan baya barinta da aiki ko kadan ne saiya ce zai taya ta, saida suka gama breakfast ɗin sannan ya shirya zai fita, ji yayi ta riko shi ta baya tsam. "ohhh! my wife kinaso na makara ne! "a'a banaso ka makara"! tayi Maganar cikin shagwaba. riƙo hannun ta yayi ya zagayo da ita gabansa sannan ya kafe ta da eyes ɗinshi yana faɗin. "to shikenan ki barni na tafi"! "pls ka kaini wajan mommy"! shiru ya ɗanyi kamar bazaiyi magana, saida yaga ta langabe kai tana maimaita plss cikin wata irin Murya mai jan hankali sannan yayi murmushi yace "ok ki sameni a mota, idan kika wuce 5mnt saidai kiga babu Ni nayi tafiya ta na barki"! wani tsallen murna ta saki ta nufi ɗakin ta, shi kuwa ficewa yayi kawai yana murmushi ƙasa ƙasa. mommy taji dadin ganinsu musamman yadda taga ƴar tata ta zama wata babbar mace. yana ajiye ta ya wuce office yace zai dawo ya tafi da ita.. sai azhar ta kira shi tace zata wuce gidan Afnan saboda shirye shiryen bikin khairat da suka fara. "Mrs Habibullah banasan yawo fa, ki hakura kawai"! "khairat bazata ji daɗi ba baka yadda tasha wahala a namu bikin ba"! ɗan taɓe baki yayi sannan yace "shikenan sai akace saikin rama mata wahalar datayi miki"! kamar yana ganinta haka ta girgiza kai. jin tayi shiru ne yasa Habib ɗorawa da "bazaki ba ina ganin ki hakura da zuwan zaifi" "shikenan na haƙura.."! tana faɗa ta kashe wayar kawai ta kwanta duk ranta a ɓace. mommy ce da Abdul suka shigo palourn Abdul na sanye da kayan gym. kiss ya manna wa jiddah a cheek ɗinta, ɗago Kai tayi tana dariya. "my son Ina zuwa haka"! "gym room zani! "ohh, that's good my dear" mommy ce tace "wuce ka tafi zaka dame ta da shegen surutun ka ko"! saida Abdul ya fita ya fita sannan mommy ta maida kallanta kan jiddah tace "lafiya naga duk kin sauya"! cikin shagwaba tace "mommy ya hanani zuwa gidan Afnan, kuma bikin khairat ya matso shine muke ta shirye shirye"! murmushin manya mommy tayi sannan tace "tsakanin kune wannan saiki bari ya dawo ki sake Tambayar shi". jiddah bata sake magana ba ta kwanta abinta cikeda takaici.. tana nan kwance taji ihun Abdul yana kiran sunan Daddy, hakan ya tabbatar mata da Habib ne ya dawo. haushin datake ji ne yasa bata tashi daga inda take ba harya shigo palourn Abdul na hannun shi. mommy ce tayi masa sannu da zuwa sannan tace "jiddah jeki haɗa masa abinci ki kawo masa nan" kallan inda jiddan take yayi harta tashi zata shiga kitchen din taji yace "a'a mommy fita zamuyi kuma a koshe nake."! "ina zaku je kuma"!? mommy ta Tambaye shi.. "anguwa zamu ɗan fita badai zamu dade ba zamu dawo" yana gama faɗin haka ya tashi yana kallanta yace ta same shi a Mota.. da murnarta tabi bayan shi, tana shiga ya tayar da motar saida sukayi nisa sannan ta kalle shi fuskarta a marairaice. "kayi hakuri yaya Habib" "da kikayi laifin me" "dana kashe maka waya ɗazu" baice komaiba yaci gaba da driving ɗinsa har sukaje gidan hibban yayi Parking Yana jiran ta fita dan wajan aiki zai koma. ganin taki fita yasa shi ɗan kallan gefenta. "sauri nakeyi ki fita zan koma jirana akeyi" girgiza kai tayi tace "a'a mu koma kawai na hakura da zuwan"! tsaki ya danyi yana dan fitar da iska ta bakin shi. sannan ya kuma kallanta yace "karki batamin lokaci, saboda naki kawo ki har fushi kikayi dani saida mukazo sannan kice kuma kin fasa"... hakuri tafara bashi kamar zatayi kuka dan tasan ranshi ya ɓaci yayi hakane kawai dan karta ji haushi itama nata ran ya ɓaci shiyasa ya kawo ta. "look dear bafa Wai fushi nayi ba, kawai banji dadi bane amma yanzu I'm ok na haƙura ki shiga idan kun gama saiki kirani nazo na maida ki" nodding kanta tayi sannan ta juya zata fita ya kamo hannunta ta juyo. "bazakimin murmushi ba, ko so kike nakasa yin wani abin kirki a office din" dariya tayi tana kai masa bugun wasa sannan ta fice tana dariya shima ya juya motar shi yabar gidan cikeda farin ciki... kullum yanzu tare suke fita da jiddah Saboda bikin khairat, taci Sa'a ya barta anyi komai da ita taron mutane ne kawai ya hanata ta haƙura,.. soyayya yake nuna mata bata wasa ba, duk wanda yaga Rayuwar su saita birge shi bashida wata matsala yanzu saidai kuma ta wacce baza'a rasa ba.. 8month later kwance take saman faffadan kirjinshi tayi luf yana shafa bayanta a hankali kamar wata baby girl, a hankali ya kira sunan ta cikin rada ta amsa. "yadai ciwan kan ya sauka" ya tambaye ta yana leka face ɗinta. cikin muryar shagwaba ta amsa masa da eh. cikin dabara ya kwantar da ita shi kuma ya tashi yana mata messages a jikin ta, cikin kankanin lokaci bacci mai daɗi ya kwashe ta sai numfashi take saukewa a hankali. saida ya tabbatar baccin ta yayi nisa sannan shima ya kwanta.. cikin baccin ta taji yana wasa da gashin kanta, a hankali ta buɗe idanuwanta tana kallan shi dauke da wani tsadaddan murmushi. "my life, ki tashi ki shirya muje kiyi breakfast" da sauri ta tashi zaune tana kallan shi saidai wannan lokacin kallan mamaki take masa. ganin irin kallon da take masa ne yasa shi yin murmushi tareda daukan ta cak har bathroom. tare sukayi wankan sannan suka fito, saida ta fara shiryawa sannan ta matso tana taya shi sa neck tie ɗinsa.. sai faman bata masa lokaci takeyi duk tare yake so su fita ya sauke ta wajan mommy.. ganin tana bata masa lokacin ne yasa yace "oh my God, kullum saina makara wajan wannan shirin daga yau nizan dinga yin abina dan na fahimci kina sane kike batamin time" dariya tayi masa harda gwalo sannan ta fice da dan gudun ta daga ɗakin.. yana tsaye yaga ta dawo. "badai kaine ka hada mana breakfast ba" murmushi yayi yana janyo ta jikin shi tareda haɗe fuskarsu waje ɗaya,. "nine nayi, saboda jiya kin kwana da ciwan kai kuma banaso ki wahala that's why nayi da kaina". fushi tayi zata fice ya sake kamo hannunta, "haba my dear badai fushi kikayi ba" "ohh Tambaya ta ma kakeyi, meyasa baka tashe ni munyi tare ba tunda haka muka saba shine zakayi duk wancan aikin kai kaɗai"? "naga bakyajin dadi ne ai, yanzu dai kinga lokaci na wucewa muje muyi breakfast I'm hungry"! har dining table ɗin suka karaso hannun su na sarke cikin juna. zama yayi yana nuna mata kan cinyar shi alamun ta zauna. gefe ta juyar da kanta tana basarwa tace "bana ci kaci kai kaɗai kowa ya dafa nashi"! "ok shikenan Ashe bazaki wajan mommy ba Kenan" ya faɗa yana kokarin tashi.. da sauri ta zauna tana dariya shima murmushi yayi sannan suka fara cin abincin cikeda farin ciki sosai... mommy tayi farin cikin ganinsu sosai duk yanzu duk bayan sati yana kawo ta su wuni anan wajan mommyn.. sai yamma sannan ya dawo suka tafi bayan sunyi dinner a can.. yauma kamar kullum da sassafe ya shirya ya fice office, sai yamma ya dawo gida yana shigowa palour yaga bata nan kamar yadda ya saba yana shigowa take dafe masa tana masa Oyo yoo.. kai tsaye ɗakin ta ya shiga ya hange ta kwance cikin blanket. da sauri ya ajiye breif case ɗinsa ya karasa kusa da ita yana jera mata tambayoyin lafiya take kuwa. jin jikinta yayi zafi sosai, duk yabi ya ruɗe. murmushi tayi masa tana tashi Zaune "fever ne tunda ka tafi nake kwance amma yanzu I'm feeling better tunda ka dawo lpy" "meyasa baki kirani kin fadamin ba, kinji yadda jikin ki yake kuwa" zata sakeyin magana ya cire bargon yan dauke ta har ɗakinsa sannan ya dauko first aid box din dake ɗakinsa. dakyar ya lallaɓata tasha magani sannan ta kwanta wani wahalallan baccin ya sace ta... *first lady* 27/1/2020 NOT EDITED 〰️〰️ [1/29, 7:59 PM] 🌹Aɱɛɛŋą fírѕtlαdч 🌹: *بسم الله الرحمن الرحيم* *____________________________________* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *____________________________________* 🌹🌹🌹🌹 *_DR. HABIBULLAH_* 🌹🌹🌹🌹 вч αmєєnα muѕα *🌹fírѕt lαdч 🌹* *wαttpαd* Ameenafirstladyy 🔚 {50} ... kafin yamma jiddah ta wahala sosai har ƙarin ruwa yayi mata da allurai, sai faman lallaɓata yake taki cin abincin sai shagwaba take masa. "pls dear kici koyaya yake saiki sha magani"! tana kwance jikin shi tayi luf tace "nifa banci danko ƙamshin abinci ma banaso"! "little baby meyasa kake wahalar da ummin ka" ya faɗa yana sumbatar cikin nata. "yanzu me kikeso kici" "dan wake" ta bashi amsa idanuwanta a rufe. "dan wake.."! ya maimaita kalmar danshi bai taɓa ciba ko a gida idan mommy tayi ko ganin shi bayasan yi dan yafi kaunar abincin turawa tunda dashi ya saba amma yanzu gashi kaddara ta hau shi na dole ya nemo shi.. "haba my baby wannan abincin zakici kuma, yanzu a ina zan samo shi". ya faɗa yana daɗa rungume ta tsam a jikin shi. "nidai gaskiya idan bashi ba saidai ka kyale ni haka dan bazan iya cin komai ba" "a'a baza'a yi haka ba bari na kira mommy naji ko za'a samu" bai jira amsar taba ya janyo wayarshi dake kan stool ya Kira layin mommy bugu biyu ta daga. saida ya gaida ta sannan yace "mommy za'a samu Wannan a gidan nan kuwa"! jiddah najin yace wannan tafara dariya kasa ƙasa. "meye kuma wannan bashida suna ne Habib"! "dear yana sunan shi" "dan wake" ta bashi amsa sannan ya sake Tambayar mommyn. dayake mommy tasan zancan da hanzari tace za'a samu yazo ya karba mata, sannan tace yaba jiddah wayan. bata yayi sannan ya shige bathroom danyin wanka.. tun kafin yaje mommy ta gama haɗa mata, yana zuwa ya amsa ya koma gida, a zaune ya sameta tana game a wayarta. ajiye abinci yayi ya tashi zai bar wajan yaji ta riko hannun shi. "mene kuma"? kallan abinci tayi sannan ta kuma kallanshi batace komaiba sai murmushi da takeyi. "badai kina nufin nima naci ba"! "eh haka nake nufi naga kaima ai bakaci komaiba" "haba never kedai daya zame miki cuta saiki ci ai, Ni zanyi nawa abinci da kaina" ya faɗa yana tashi. ture cooler Abinci tayi tace nima banaci to. badan yaso ba ya koma ya zauna suka fara ci tare, tana ci tana masa dariya dan ci daya yayi ya tashi yana bata fuska.. tunda ta samu cikin ba sosai yake zuwa aiki ba kullum suna manne da juna, duk wani motsin ta yana lure da shi ko aikin ya fita suna maƙale a waya.. watan cikin bakwai mommy tace su dawo gidanta saisu koma part ɗinsa da zama, haka kuwa akayi yasa aka gyara masa part ɗinsa suka dawo mommy taci gaba da bata kulawa.. yauma tunda ya fita tana wajen mommy, azhar nayi sukaji sallamar shi yana riƙe da brief case ɗinsa ya shigo palourn. ita kadai ya samu a palourn dan Abdul yana school. kiss ya manna mata sannan ya ajiye breif case ɗin ya zauna ya jawo ta jikinshi. zaro idanuwanta tayi tace "kai hubbi mommy fa tana daki tana bacci" "ai kinji bacci takeyi, Ni kuma kewar ki nakeyi shiyasa ma na dawo"... watan haihuwar jiddah ya kama, Habib gaba daya ya bar zuwa aikin cewar shi kar haihuwar tazo bayanan a rasa mai kaita hospital. "ai dayake ni ka raina driving dina ko" mommy ta faɗa tana hararan shi. sosa kai yayi yana murmushi yace "a'a ba haka nake nufi ba Mom"... 7yrs later "pls dear kabari mana na dinga zuwa kai Nihal school dakai na" yana tsaye yana daura neck tie ya Dan kalleta yace "kibari hibban zai dinga kaita kinga bai kamata kifara fita da Aiman yana jariri haka" kallan Aiman tayi yaron da yake rarrafe ake cewa jariri. dariya abin ma ya bata tace "Aiman ɗinne jariri, kawai dai baban Aiman ɗinne bayasan bari fitar" jitayi ya janyo ta jikin shi, ta faɗa tana Yar dariya. "ashe kin gane banaso ki wahala ne" da kyar ya yarda da ta dinga kaisu school ɗin saita jira a tashe a gidan mommy ta wuce ta taho dasu. tare suka fito palour da gudu Nihal tazo ya rike Habib. "Nihal yau ba homework ne kika zauna kina kallan kwallo" "nayi ai" "that's good my love" jiddah ce ta janye ta daga jikin Habib ɗin tana faɗin "Nihal kibari Abbi ya tafi aiki ko" kafaɗa ta maƙe tace "a'a zan bishi ya kaini wajan yaya Abdul ne" ta faɗa tana sa rigima. Habib ne yacewa jiddah ta dauko Aiman kawai na ajiye ku a wajan mommyn.. suna mota Nihal na rike da Aiman a back seat suna wasa, su kuma suna front seat. "dear dafa nice nace ka kaimu bazaka kaimu ba ko"!? dan kallan gefenta yayi sannan yaci gaba da driving ɗinsa, sannan yace "ai kinsan wata kusan tafi wata kusan" da sauri ta kalle shi tace "wato sun fini kenan kake nufi" shiru ya ɗanyi Kamar bazaice komaiba, sai kuma ya ɗan taɓe baki yace "mamaki kikeyi wai"? ya karasa yana dan kallan face ɗinta. ganin ta haɗe rai ne yasa shi yin murmushi yace "see you, I'm joking keɗin rayuwa ta ce dan bazan iya rayuwa babu ke ba" murmushi tayi tana yi masa dukan wasa sannan ta kwantar da kanta jikin kafaɗar shi.. a gidan mommy suka samu su hibban da Afnan tare dasu khaleesat sai Abdallah karamin yaron su, duk sun cika palourn da hayaniya. Habib yana shiga sukayi shiru suna mazurai, yana gaisawa da mommy ya fice dan kanshi harya fara ciwo ɗan hayaniyar dayaji hakan yasa da sauri ya fice... mommy dake zaune Abdul na gefenta tunda ya gaida baban nashi ko ɗago kai bai sakeyi ba fuskar nan babu fara'a a tare da ita. "Lallai Habib wannan cutar taka tana bukatar magani, ayi mutum baisan hayaniya bayan gashi nan kafara tara iyalai, duk ka koya musu halinka yara kamar basu a waje idan kana tare dasu" mommy ta dinga mita suna dariya.. "ai gashi nan ya koyawa wannan tunku ɗin koda yaushe fuska a haɗe harta na fara tunanin korashi wajan iyayen su sukarata dashi can tunda sun saba" mommy ta sake faɗa tana kallan Abdul, wanda ya tashi fuu yayi Dakin shi.. "yaya hibban yau bazaka je aiki bane" jiddah ta Tambaye shi. hararan wasa yayi mata yace "ban sani ba, ai kinga dai tare nake da matata ba zaman banza nake ba" daƙuwa mommy tayi masa tana barin palourn danta fahimci yanzu zata fara raba faɗa dan hibban da jiddah indai suka haɗu sai sun tsokani juna.. cikin ikon Allah rayuwar jiddah da Habib kamar rayuwar hanta da jini ne dan koda yaushe suna tare koda yana wajan aiki basa jimawa basuyi waya ba.. babu laifi tana kaiwa ƙauye ziyara time by time, dan yanzu kawu Audu yana sana'ar shi a gida wanda jiddah ce ta buɗe masa katon shago a kofar gidansa... ******* *Alhamdulillah ina godiya ga Allah daya bani ikon gama wannan Novel lpy, Kuma Allah ya yafemin kura kuran danayi a cikinsa,,, saimun haɗu a sabon Novel dina* *RANA TSAKA*✍️✍️✍️ ina godiya gareku mutanan Wattpad, godiya mai tulin yawa👏 *🌹first lady🌹* 29/1/2020