*DAURIN GORO* SHAFI NA DAYA (1) ©️HAFSAT RANO ALKALAMI TV https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo WATTPAD: HafsatRano ********** *MAFARIN KOMAI*. A guje ta fito daga dakin jikin ta cikin shigar kayan ma'aikatan jinya, da sauri duk suka mik'e ganin ta nufo su "Ta sauka Dr!" Suka tambaya a rude kuma a tare "Ina maigidanta?" Ta maida musu ba tare da ta amsa tambayar tasu ba. Matsowa yayi da sauri yace "Gani." "Ok muna so ka saka hannu ne, ba zata iya haihuwa da kanta ba dole sai dai ayi mata aiki." "Innalillahi, aiki kuma Dr?" Ya tambaya a kideme "Shine kadai abinda zamuyi mu ceto rayuwarta data abin cikin ta. Kayi hakuri babu lokaci." "Shikenan, Allah sa ayi a sa'a." Bin bayan ta yayi, suka je ya saka hannu sannan ya dawo wajen sauran ya tsaya yana kaiwa da komawa. Bayan shafe tsawon mintuna arba'in da shigar su ta sake fitowa, wannan karon akwai alamun nasara a tattare da ita. Kafin ta k'arasa garesu sukayi saurin isa, fuskar su dauke da alamun tambaya, hannun ta ta mika alamun abata tukwuici kafin tace "Congratulations Your highness, an yi nasarar ciro muku dan saurayi." Da sauri ya kalle ta kamar be ji me tace ba, gid'a masa kai tayi alamun gamsarwa, maida kallon sa yayi wajen sauran da duk fuskokin su ke cike da farin ciki yace "Alhamdulillah ya ALLAH!" Ya furta da karfi A duniya bashi da wani buri da ya wuce yaga an haifa masa d'a namiji, yau sai gashi Allah ya cika masa burin sa, ba ma shi ba, duk wani makusancin sa yana masa sha'awar haka. Duba da irin tarin dukiyar da Allah ya bashi. Ya hakura ya barwa Allah zabin sa, sai gashi ya bashi a lokacin da beyi zato ko tsammani  ba. A take wajen ya kaure da murna, babu wanda ya tsaya tambayar lafiyar mahaifiyar, tuni kowa ya hau kokarin kiran waya domin sanar da yan'uwa da abokan arziki. THE ONE AND ONLY HEIR To *MARWAN DIKKO* FAMILY IS BORN. A daidai lokacin Inno na kwance a gadon asibitin, babu tazara tsakanin dakin da take da babban dakin da aka ajiye Matar Alhaji Marwan, saboda haka tana jiyo hayaniyar mutane me cike da tsantsar farin ciki, kallon jaririyar dake kwance kusa da ita tayi, zuciyar ta tayi rauni, anya? Anya bata zalunci yarinyar ba kuwa? Kallon gefen ta tayi taga jakar da aka hado mata tare da jaririyar, soyayyar ta da kudi abu ne me girma, babu abinda ba zata iya aikatawa akan su ba, sai dai tana tsoron abinda zai je ya dawo gaba, gashi babu ko digon soyayyar yarinyar a zuciyar ta. Abu daya ta sani shine rayuwar jaririnta, rayuwa me inganci da tsananin gata da zai taso da ita. Idan ta tuna wannan sai ta ji ta samu sauki, sai dai fa tana da kudurin komai daren dadewa sai ta karbo shi. Shigowar su Yalwati da sauran jama'a ne yasa ta ɗan saki ranta, suka shiga daukar jaririyar kowa yana yaba kyawun ta, ita dai Inno jin su kawai take ba tare da ta tanka ba, ganin zasu cigaba da chaja mata kai da hayaniyar su yasa ta rufe idon ta alamun bacci take yi, hakan ya bata damar cigaba da yin tunanin da take akan wannan babban al'amari ne cike da tarin matsaloli a gaba. Hmm **** *AMINATU* Kowacce rayuwa cike take da kalubale, sai dai ni tawa rayuwar da wani salon na sarkakiya tazo min. Rayuwa ta cike take da abubuwa masu yawa. Duk da haka  bazan ce nafi kowa shiga matsin rayuwa ba, sai dai ina da tabbacin ina cikin sahun farko na mutanen da za'a kirasu da wanda rayuwa tayi *Daurin Goro*. _Eh daurin da nake tunanin babu wani mahalukin da zai iya warwareshi, na riga na sare, na barwa Allah ikon sa, ina kuma kyautata zaton zai kawo min yankewar sa kafin barin numfashi na._ Ajiyar zuciya na sauke ina bitar Rayuwa ta daki-daki kamar a lokacin komai yake faruwa. Zaune nake a faffad'an tsakar gidan mu wanda ke dauke da dakuna hudu falle falle sai madafi daga gefe, randunan ruwa manya, daga dayan bangaren rijiya ce babba da makewayi a gefenta, gidan gidane babba daya hada da mutane da yawa sai dai kowa yana ɓangaren sa inda babban zauren gidan shi ya haɗa kowa da kowa. Dakin farko ya kasance dakin Baba, sai dakin Inno daga chan gefe, dakin yara matan gidan ne a kusa dana inno, daga dayan barin dakin Yalwati ne sai dakin samari dake daura da hanyar fita daga shashen namu. Tsintar shinkafa nakeyi tun kafin rana ta fito gashi har ina neman makara ban samu na gama ba, a gurguje nakeyi saboda lokacin makaranta kar na makara, cikin sa'a na kammala nayi saurin zubawa a ruwan waken dake ta tafasa bayan na tabbatar da dahuwar waken saboda gudun abinda zai je yazo. Gyara wutar nayi ganin ta fara zarewa na karasa gaban rijiya domin yin kwaskwarima. Cikin sauri sauri na zura uniform d'ina wanda duk ya tsofe wani wajen ma ya yage na sake fitowa, lokacin har yaran gidan sun fara fitowa ana layin alwala. Haka dabi'ar gidan mu take, tun tasowa ta kawo yanzu hakan bata chanja zani ba, kafin su gama alwalal sai sunyi fada kashi dari. Murmushi kawai nayi na fada dakin Inno dan gaishe ta, a tsaye na ganta tana kokarin daura dankwali tana ganina ta tsaya. "Ina kwana Inno.?" Na durkusa har kasa kamar ko yaushe. Bata amsa ba sai kallon kayan jiki na da tayi kadan kafin tace "Kin gama aikin naki ne da zaki wuce makaranta?" "Eh." Nace ina kallon ta. "Kin zuba ko kin gama?" Iya sani na Karime ke karasa wa idan na zuba, tun da ita ba makarantar take zuwa ba, a darare nace "Na zuba karasawa kawai zatayi a kwashe Inna." Dan bata fuska tayi tana yatsine baki kafin tace "Jeki jira ta karasa yau babu me karasa miki Karime bata jin dadi." "Toh." Kawai nace na mike jiki a sanyaye na koma bakin dakin mu na zauna ina kallon yadda rana ta d'aga sosai alamun na makara, ina nan zaune kowa ya fito aka hau hada-hadar shan koko, ban bi ta kai ba ni dai buri na na ganni a makaranta. Sai bayan wajen rabin awa sannan na kammala na sake dauraye kafata na fice daga gidan da sauri kafin Inno ta ankare ta kawo abinda zai hana ni zuwa duk kuwa da na kan yi mamakin dalilin da yasa inno take bari na zuwa makaranta, bayan haka bama kowa ne a yaran gidan ke samun zuwa makarantar ba. A babban zauren gidan naci karo da Nura, da alama lokacin zaiyi sallah, gaishe shi nayi na wuce ba tare da jiran amsar sa ba. Tafiya ce mai tsawo kafin ka isa makarantar guda daya jallin jal dake a kauyen,  Kamar kullum babu malamin daya shigo har nazo, haka dabi'ar makarantar take, a rana sai ka samu malami daya ne kawai zai shiga duk suna zaune a staff room suna hira, a haka dai muke dan samun abinda muke samu wanda bamu da tabbacin daidai suke koya mana sai dai saboda ba gane wa zamuyi a lokacin ba yasa muke binsu a haka. Musamman ma ni da na taso da son karatu da kuzun zama wani abu a kauyen namu tun bayan ganin da nayi wa jikokin mama Ladi makociyar mu dake zaune a birni, sun kawo mata ziyara, tun daga lokacin na sawa raina zama kamar su, sai dai hakan ba mai yiwuuwa bane duba da irin gidan dana taso. *** Haka rayuwa ta cigaba da garawa, babu abu daya daya sauya na daga al'adun gidan mu, tun da na taso nasan Inno ita ke ciyar da gidan mu ko nace shashen mu, shiyasa ko babanmu baya mata musu, Yalwati kuwa ta zama kamar ba kishiiyar ta ba, dan bayan na gama girkin shinkafa da waken da karime take fita dashi wajajen sha biyun rana, Yalwati ce zata dora alala, sannan tayi dambu da wake shima a sake fita dashi, duk kuma jarin na Inno ne. Inno mutum ce wadda tasan darajar nema, bata taba zama haka nan, yau ta buga nan gobe ta buga chan, bayan sana'ar saida abinci har kiwon akuyoyi take yi da kaji, ga sana'ar abin kad'i dangin su kuka da su kubewa, da sauran abubuwa, sai ya zama ma a kaf kauyen namu babu wanda zai kama kafa da ita Indai a samu ne, shiyasa kaf gidan mu suke shakkar ta, babu wanda ya isa ya daga mata yatsa balle Baba da Yalwati da suka zama kamar yaranta, sai abinda tace musu ake aiwatar wa. ******* Kiran da Karime ke kwala min yasa na ajiye kibiyar hannu na na fito, riko ni tayi da sauri tana haki "Lafiya dai?" Nace ina kallon yanayin ta "Ina fa, dalla kowa yana chan kallon bak'in gidan Bature sun zo ke kina nan kina tsifa." "Dan Allah!" Nace ina fad'ad'a fara'ar fuska ta "Wallahi ana chan duk ana ta kallon su abin sha'awa, na duba ban ganki ba shine nazo kirankii, kinga motar da suka zo acikin ta, har da wata yarinya kamar girman mu, kinga kayan jikin ta kuwa? Wayyo yan gayu sun ji dadi wallah" Ta fada tana rik'e haba, da sauri na koma ciki na dauko dankwali na na daura muka fice da gudu, dukkannin mu sirara ne babu kibar arziki, yadda muke gudun kadai zaka tabbatar da yarintar mu, dudu du a lokacin ba bazan bi shekaru goma sha biyu ba, tsiran mu da karime shekara daya ne saboda haka ba zaka gane wani banbanci me yawa a tsakanin mu ba. Tun kan mu karasa muka ga ana juyowa, hanne ce ta tsaida mu tana dariya "Ina zaku wai, kallo ya barku ai sun koma gida, sai wani jikon kuma." Haushi ne ya kamani, duk zuwan  da zasuyi ban taba samu na gansu ba har su tafi, a take na kudurce a raina wannan karon babu abin da zai hanani ganin su, ko nima na samu na dorar da labarin su. Kullum da safe idan na tashi ta kofar gidan nake bi, haka ma idan na dawo, ban taba samun nasarar ganin ko da cikin gidan bane. Gida ne me girman gaske, hade da babban gidan gona da tsayawa fasalta yanayin girman sa ba mai yiwu wa bane. Duk da karancin shekaru a lokacin da kuma yanayi na duhun kai da kauyanci na gane cewa ba karamin masu kudi bane mamallaka wannan wajen, duk a irin wannan lokacin suka zo gaba d'ayan su su jima sosai, idan suka tafi kuma shikenan sai wani lokacin me tsawo. Gidan Bature kamar yadda mukayi wa gidan da lakabi, sai dai a zahiri ba haka sunan me gidan yake ba, tsari da yanayin gidan da bamu taba ganin kamar sa ba yasa muke kiran gidan da gidan Bature. *** Tun gabanin magriba garin yake ta hadewa, alamun za'a iya samun ruwa a kowanne lokaci, muna daga kofar dakin mu dasu hanne muna hira da karad'i Inno ta kwala min kira, tashi nayi na karasa wajen ta ina kallon hannun ta "Yi maza kije shagon Umaru ki siyo min maganin sauro yanayin garin za'a iya ruwa kowanne lokacin." Karba nayi na juya da niyyar kiran me rakani, dakatar da ni tayi ta hanyar cewa "Ina kuma zaki koma?" "Su karime zan kira su rakani Inna." "Saboda ku tsaya min shiririta a hanya ko? Kin wuce da sauri ko sai na bugo ki?" Da sauri na juya nayi hanyar waje zuciya ta duk babu dadi, duk yawanmu na rasa dalilin da yasa ni kadai Inno take takurawa. Sanda na isa shagon ya riga ya rufe, juyawa nayi ina tunanin yadda zanyi, sama na sake kalla naga yadda hadarin ke sake hadewa nayi saurin daga kafata na kara sauri don zuwa shagon dake chan kasa kadan. Sauri sauri nake nabi ta wani lungu ina kokarin ganin na isa kafin ruwan ya sakko, cikin sa'a na samu shagon yana bude shima yana kokarin rufewa, da sauri na bashi kudin na karbi maganin sauran na juya na kamo hanyar gida a lokacin garin ya kara hadewa. *** *Gidan Bature* Dukkanin su suna zaune a babban falon gidan, kallo suke suna hira gwanin sha'awa, sun kusa a ƙalla su goma maza da mata, Ja'afar ne ya kalli Farouk da tun da aka fara hirar yana rike da waya be tanka musu ba, magana suke akan fitar da zasuyi gobe dan zaga gari. "Ya Farouk." Ya kira sunan shi yana kallon sa "Uhum?" Ya amsa yana yin kasa da wayar dake hannun sa "Maganar fita gobe, U haven't said anything bayan kuma kai kadai ne zakayi convincing Dada ta yadda." Be tanka ba ya sake maida kansa kan wayar kamar ba zai ce komai ba, ganin haka yasa Ja'afar zungurar Amal ya nuna mata bangaren Farouk din, duk ciki tasu tafi zuwa d'aya, babu wani abu da zata nema beyi mata ba sai dai idan bashi dashi din. Tashi tayi tsam ta isa gefen sa ta zauna ta marairaice murya "Dan Allah Yah." Hade hannayenta tayi waje d'aya tana sake kallon sa, hararar Ja'afar yayi kafin ya mike yana ware hannayen sa, duk sun maida hankalin su kansa suna jiran su ji me zai ce, takawa yayi a nutse har gaban window dake makale a falon ya zuge curtains din, sama ya kalla yaga yadda garin yayi, murmushi yayi ya tura hannun sa gaba daya waje yana kama sanyayyiyar iska dake kadawa a hankali. Wajen mintinan biyu yayi a haka kafin ya zaro hannayen nasa ya juyo ciki yana kallon su. "Zan yi magana da Dada, shikenan?" Ihu suka sa gaba daya cikin murna, yana jin su ya juya da sauri ya fada dakin su, ƙatuwar rigar ruwa ya dauka ya saka hade da takalmin sa na ruwa ya fito ya fice daga gidan gaba daya. ZAFAFA BIYAR KAUNAR MU: MAMUH GEE ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL DAURIN GORO:HAFSAT RANO. IGIYAR ZATO: MISS XOXO *_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_* 2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_ saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863* *_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇 *09032345899* _Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 DG Shafi na biyu (2) ****** Lokaci daya iska me karfin gaske ta taso, gaba daya bana ganin gaba na, wani irin tashin hankali ne ya ziyarce ni, na sani sarai idan har na bari ruwan nan ya taba lafiyar jiki na kashi na ya bushe, ganin da gaske bana ko ganin hanya yasa na makale gefen wani shago na kudundune kaina ina jin matukar tsoro. Ina nan makale yayyafi ya fara sauka a hankali, tsoro na ya dadu, zuciya ta tayi rauni sosai, kamar daga sama naji an dafa kafada ta, cikin tashin hankali na dago kaina,ban samu nasarar ganin fuskar kowaye ba, saboda tsananin hasken torch light din da aka sa aka haske ni. Cikin muryar tsoro na furta "Waye!" Be amsa ba, ba shi kuma da niyyar amsawar, illa sake dalle ni da yayi, take hasken yayi tasiri rage kaso tamanin cikin dari na gani na, baya da ƙurar da ta riga ta cika min idon nawa, da sauri na mike ina kokarin daidai ta zaman riga ta, na fara alamun barin wajen, hannu naji an saka an riko ni, cikin wata iriyar murya mara fasali ya furta "Gidan uban wa zaki? Ai wallahi kinyi kadan tsuntsu daga sama gashashshe." Tsoro ne ya bayyana ƙarara a fuskata jin muryar Garbati, mutumin da ko a mafarki bana fatan hada hanya dashi, waye be san shi ba kaf kauyen nan namu, tantirin dan iska ne, lamba daya, gashi babu wanda ya isa dashi kaf kauyen. Da sauri na ja da baya ina kokarin sake shiga cikin ruwan sosai, damko ni ya sake yi nayi kara da karfi jin zafin rikon da yayi min, ja na ya shiga yi yana kokarin turani cikin shagon da tun zuwa na wajen na lura da yar kofar dake bude, amma banyi tunanin akwai mutum ciki ba, da karfin gaske na hau kokarin kwatar kaina, sai dai ko kusa da hakan ban kai ba , duba da yanayin karfin ba daya ba. Tuni na hau kuka ina magiyar bashi hakuri, tunda ayi ƙarancin shekaru na nasan hakan da yake me yake shirin aikata min. Be saurara ba, ko ma nuna alamun yaji abinda nace, haka ya tura ni ta karfi ya maida kofar ya tura yana sakin wani shu'umin murmushi. Tuni na watsar da aiken Inno, na shiga ihu da dukkannin murya ta ko Allah zai sa a jiyo ni, dariya ya shiga yi ba kakkautawa. "Yarinya da kin hakura babu shegen da zaiji ki, uban me ya fito dake a wannan lokacin shegiya." "Aike na akayi wallahi." Nace ina sharbe hawaye da majina. "Daidai kenan, idan na ci ubanki zaki gane shayi ruwa ne." Ya fada yana kokarin matsowa kusa dani. Sosai na kara karfin murya ta, cikin tsananin tashin hankali, magiya nake masa ina rokon sa, sai dai hakan ba sa ya fasa aiwatar da abinda ya kudurta a ransa. Tun daga nan bansan me ya kuma faruwa ba😭😭 *** *** Tafiya yayi sosai yana mai jin dadin yanayin garin, kafin zuwa lokacin da iskar ta taso, sauri ya kara don ganin ya isa gida, be yi tunanin ruwan zai zo da iska haka ba. Saukar ruwan ne ya rage karfin iskar sosai, hakan ya bashi damar cigaba da tafiyar sa cikin kwanciyar hankalin ruwan na dan taba fuskar sa kad'an-kad'an. Kamar daga sama yaji ihu, ihun ma na mace me karancin shekaru, sai dai karar saukar ruwan yayi tasiri kwarai wajen kasa tantance daga ina ihun yake, hankali ya tashi ya hau neman ta in da muryar ke fitowa, kamar mahaukaci haka ya shiga kai kawo a cikin ruwan, hankalin sa ne ya kai wajen, da wani irin mugun guda ya nufi dan karamin shagon daya gama tabbatarwa daga nan ɗin ne yake jin kukan, beyi wata wata ba yana zuwa ya daki kofar da dukkan karfin sa. Abinda ya gani yayi mugun daga masa hankali, da gudu yayi kansa ya shiga dukan shi, duka me cike da tsantsar bacin rai. Yanayin rashin karfi da a tattare da Garbatin ya hana shi katabus, sai daya yi masa duka sosai sannan ne hankalin sa ya dawo kanta, tana kwance kamar mara rai, abinda ya dade yana jin labarin yana faruwa ga yara masu kananan shekaru ne ya faru da yarinyar nan, yarinyar da dududu ba zata wuce sa'ar Amal ɗin su ba, da sauri yayi kanta ya dago ta, tuni ta sume saboda tsabar firgicin data shiga, wani irin kuka ne ya taso masa, wannan wane irin rashin imani ne?. Da dukkan karfin sa ya daga ta ya sata jikin sa, be bi ta kan Garbati ba da yake kokarin tare shi, har ya kai kofa maganar shi ta dakatar dashi "Ni kayi wa wannan dukan? Akan wannan yar iskar yarinyar?" A halin da yake ciki ba zai iya magana ba, saboda haka ya juya da sauri dan ganin ya ceto rayuwar yarinyar. Yana juyo hargowar Garbatin me cike da gargadin abinda zai aikata masa. Gida ya wuce kai tsaye yana jin kamar zuciyar sa zata bar jikin sa. Har lokacin dukkan su suna falo ya shigo da sauri dauke da ita Baba maigadi na bin bayan sa, a tare duk suka mike suna kallon shi cike da mamaki. "Yah Farouk..! Amal ta fada tana zaro "Bude min daki na." Da gudu ta yi gaba suka take masa baya, dakin sa ya kaita, ya kwantar da ita saman gadon sa, sai a lokacin ya ga fuskar ta, kallon su yayi duk sunyi cirko cirko kamar sun ga abin tsoro. "Kira Dada Ja'afar." "Wacece ita Yah Farouk?" Ya tambaya ba tare da ya motsa ba. Kallon sa yayi rai a bace daa karfi yace "Will you go and call her or..." Da sauri ya juya ya bar dakin, dafe kansa yayi ya sake dagowa yana hararar kowa. "Duk ku fice min anan, Amal ki tsaya." Yar rige rigen fita suka hau yi, kowa zuciyar sa cike da tambayar abinda yake faruwa. Gefen sa amal ta zauna tana kura mata ido "Yah bata da lafiya?" Ta fada cikin tausaya wa. Daga mata kai yayi zaiyi magana Dada ta budo kofar cikin tashin hankali. "Babana,me ya faru?" Ta fada tana shigowa dakin, ganin da tayi mata yasa tayi saurin ƙaraso wa wajen "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me zan gani haka?" Hannun sa ya saka cikin na Dadan yana kokarin saita yanayin bugun zuciyar sa. "Bani ruwa da sauri ke Amina." Da sauri amal ta tashi ta dauko ruwan, karba ta shafa mata a fuska, sai data yi wajen sau uku sannan ta bude ido tare da sakin wani irin ihu wanda ya karade kusan kowanne lungu da sako na gidan. Bude ido na nayi wanda yayi min matukar nauyi ina kallon kowa na dakin, a lokaci daya zuciya ta ta shiga tariyo min abinda ya faru, kuka sosai na saka ina jin tsananin zafi kamar an watsa min barkono, riko ni dattijiwar tsohuwar dake kusa dani tayi tana kokarin sani a jikin ta. "Kwantar da hankalin ki, yi shiru, babu abinda zai faru kinji? Yi shiru karki karawa kanki ciwo." Abinda kawai naji tana ta maimaitawa kenan yana shiga kunne na cikin wani irin yanayi dana kasa tantancewa. "Dada asibiti zamu kaita, She's bleeding so Badly." Muryar sa ta daki kunne na, kallon sa Dada tayi kafin tayi magana cikin harshen turanci. "Who is she?" "It's a long story, babu time zan sanar dake komai, for now let's help her please." Ya karashe a marairaice. "Owk, Amma Ina son sanin amsar, kasan dai mahaifinku, kasan kuma labari zai kai masa zuwa gobe, i just hope ba kaine ba." Ta zura masa ido tana son ganin gaskiyar sa. Be yi magana ba, sai ma mikewa da yayi ya fice daga dakin, jim kadan ya dawo yana kallon Amal data makale a gefe tana mun kallon tausayi. "Zaki rakamu ko?" Da sauri ta daga kanta. "Dada ga driver ya dauko motar, muje ko?" " Shikenan." A hankali ta daga ni zata mikar dani, wata irin kara na saki me cike da azaba, da sauri ya waiwayo ya fasa kokarin fita daga dakin, da baya da baya ya dawo ya daga ni chak ya fita dani suna take masa baya. *** Tun Inno na zuba idon dawowa ta har hankalin ta ya fara tashi, ganin tasowar hadarin yasa ta sake shiga tashin hankali sosai, turawa tayi aka kira mata Nura a zaure ya bi bayana, lokacin iskar nan ta taso sosai. Safa da marwa Inno kawai take yi, duk wajen kowa yayi tsit ana jiran dawowar Nura, tsawon mintuna talatin ya dawo hankalin sa a tashe, babu ni babu dalili na, hakan kuma yayi daidai ta tsugewar ruwan, iya kar tashin hankali Inno ta shiga, bata fatan abinda zuciyar ta ke raya mata ya zama ya faru,bata da wata hujjar kare kanta a duk lokacin data shirya karbar muradin zuciyar ta, ko ma ba haka ba, baya cikin yarjejeniyar da sukayi tsakanin su, ko ba komai zata ci darajar nata dan. Tuni su karime da sauran yaran suka fara kuka, babu me rarrashin wani, ana haka ruwan ya fara tsayawa, gaba daya suka fito dan zuwa nema na, lungu da sako babu alamun za'a same ni, tashin hankalin da ba'a sa maka rana kenan, gida suka dawo kowa yayi jigum jigum ana tunanin ta in da zan ɓullo, duk da zuwa lokacin kowa ya gama saddak'arwa wani mugun abin ya same ni. Duk suna zaune sunyi cirko cirko, makotan da suka shigo duk sun tafi, yara sunyi bacci sai yan kadan, aka yi sallama a kofar gidan, da sauri su Nura suka fito tare da su Baba. "Garbati?" Nura ya fada yana kallon su. "Mune nan." Ilu ya amsa yana jingina a jikin garu "Lafiya dai ko?" Baba yayi tambayar ganin basu ce komai ba. Ilu ne ya kalli Garbati kafin ya shiga magana "Dama akan Aminatu ne." Da sauri a zabure suka hada baki. "Kun ganta ne?" Ilu ne ya dora "Bamu ganta ba, sai dai mun san inda take, dan munyi iya kar kokarin mu wajen ganin mun taymaka mata, garin haka ne ma Garbati yasha wannan dukan da zaku ga jikin sa haka." Ya fada yana haske Garbatin "Tana ina?" "Ina bakin gidan Bature? Daya daga cikin su ne muka kama shi, dan a lokacin da muka je ko numfashin kirki batayi, garin kokarin mu ne ma yasa masu gadin su sukayi wa Garbati mugun dukan nan, sannan ya dauke ta ya tafi da ita." "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." ZAFAFA BIYAR KAUNAR MU: MAMUH GEE ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL DAURIN GORO:HAFSAT RANO. IGIYAR ZATO: MISS XOXO *_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_* 2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_ saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863* *_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇 *09032345899* _Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_ Mucigaba da shakatawa da wannan kafin a fara kafta WASAN😁👉🏻📻©Rano ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899                          (3) Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Suka hada baki suka fada a tare. "Yanzu ina ya kaita?" Baba ya tambaya cikin jimami. "Wallahi muma bamu sani ba, mun dai zo mu sanar ne dan a sani, amma abunda yafi shine mu dunguma muje gidan su, idan yaso sai a sa ya fito da ita. " "Abinda za'a yi kenan, kai Nura shiga kira min Yahya da Lawan duk mu dunguma, ba dan dare yayi ba ma wajen maigari zamu fara zuwa." A tare suka fito, Inno na tambayar su yadda ake ciki babu wanda ya tanka mata, suna fita ta sulale kanta na juya mata, tsananin tsoro ya hana ta motsi, idan ta tuna abinda zai faru. Babu kowa a hanya har suka isa gidan, haske fitilu ne tarwai kamar rana, buga kofar Ilu ya hau yi da dukkan karfin sa Garxali na taya shi, Baba maigadi ya taso a zabure yana tunanin ko sune suka dawo. Yana budewa yayi turus ganin mutanen da be wani waye dasu ba a wannan daren, kallon kallo sukayi wa juna kafin yayi karfin halin tambayar su "Lafiya dai?" Lawan da duk yafi zafi cikin su ya bata rai yana leken gidan "Yarinyar mu da kuka sace muka zo ku fito da ita." Da sauri Baba maigadi ya kalle su yana tuno abinda ya faru kafin isowar su, kar dai ace? Da sauri ya kauda tunanin yana mai tabbatarwa kansa hakan ba mai yiwu wa bane, yasan waye Farouk, yasan me zai aikata, duk da ance ba'a yabon yaran yanzu, sai dai yana kyautata masa zato ko ba komai yaro ne nutsattse. "Kayi magana mana, wallahi ko a fito da ita ko mu nuna muku mune muke da garin nan dan uwar mutum." Garbati ya katse masa tunanin da ya tafi na wucin gadi, kallon su yayi daya bayan daya yana yanke  hukuncin abinda ya kamata ya sanar musu. "Bansan me kuke magana akai ga gaskiya, babu kuma wata yarinya da tazo gidan nan, amma ku bari na shiga ciki na yi magana da masu gidan." "Karya ne wallahi, karku yarda Malam Ayubah, yaran gidan ne a gaban idon mu ya sungume ta ya tafi da ita, bayan ya gama da ita, Allah ma yasa ba yan yankan kai bane wallahi." "Subhanallah!" Sai a sannan Baba yayi magana yana jan murya "Kayi wa Allah idan diyata na hannun ku ku fito min da ita, hankalin mu gaba daya a tashe yake, dan Allah na roke ka." "Wallahi Baba bansan komai akan maganar da kuka zo da ita ba, amma me zai hana mu bar maganar zuwa garin Allah ya waye, a lokacin masu gidan ma sun tashi, kunga sai ayi magana sosai." "Kana nufin mu bar maganar yar mu har sai gobe, bamu san halin da take ciki ba, idan ma cinye ta za'a yi ko kashe ta zuwa goben kaga shikenan ko?saboda ba yarka bace ta bata ba. Toh wallahi ba'a isa ba." "Ni dai kuyi hakuri dan Allah." Zasu sake magana Baba ya dakatar dasu "Mu bar wa goben idan Allah ya kaimu, ita kuma Allah ya bayyana mana ita, ku muje dare na sake yi." Haushi ne ya taso wa Garbati, ba haka yaso a tashi wasan ba, so yayi su kutsa kai gidan ya samu damar cin uwar yaron nan, kwafa yayi a ransa yana ayyana kalar rashin mutuncin da zai masa idan Allah ya haɗa su. Zai gane ya tana Gaza Boy. ***Karamin asibitin dake garin suka kaita, babu alamun ma ana aiki a asibitin, maigadi ne kawai yayi saura da yar karamar torchlight din sa babu isasshen haske, Farouk kamar zaiyi kuka haka yaji sanda maigadin ke musu bayanin babu kowa a ciki sai majinyata.  Juyawa sukayi suka dau hanyar fita daga kauyen baki daya. A lokacin jiki na ya kara tsami sosai, ko ina ciwo yake min zufa nake kamar wadda ta hadiyi kunama, babu abinda nake sai kuka Amal na tayani, Dada kam duk hankalin ta ya kara tashi, musamman ganin yanayin da na sake shiga daga fitowar mu zuwa yanzu. Juyowa yayi a hankali yana kallon bayan motar be ce komai ba sai kura musu ido da yayi yana jin kamar ya bude motar ya fita, yasan Amal  da raguwar zuciya da saurin kuka, kasancewar ta marainiya wadda bata san mahaifiyar ta ba yasa yake tausaya mata, baya son ko kadan yaji kukan ta, sai dai kukan yarinyar da yake ji yana neman danne kukan Amal din, har ya zama baya jin na Amal din sai nata kawai dake masa yawo a cikin kunnen sa, zuciya da ruhin sa. Suna zuwa asibitin aka karbe su, suka zauna a reception aka shiga da ita ciki, Farouk kasa zama yayi ya shiga kai kawo a wajen yana ayyana rashin imanin wasu mazan, basu da maraba da dabbobi. Fitowar Dr Iman yasa duk suka mike, kallon su tayi sosai taga babu alamun kauyanci a tattare dasu, dan bata fuska tayi kafin tace "Kuzo office Ina son magana daku ku biyu." Ta fada tana nuna Farouk da Dada, rufa mata baya sukayi suna shiga ta tura kofar tana jingina a jikin kujerar ta "Menene alakar ku da patient din nan?" Kallon Farouk Dada tayi zatayi magana yayi saurin katse ta "We are Family Dr." "Good." Tace tana zama "Kenan my guess was right, kunyi wa yarinya karama at her age aure, sannan saboda rashin imani ka kasa hakuri da kankantar ta, kayi forcing kanka akanta ko?" "A ah likita..." Dada tayi saurin katse ta, kafin ta k'arasa yayi maza ya sauke kansa kasa a hankali ya furta. "Haka ne Dr, I'm very sorry, kuskure ne." Biron hannun ta ta saka a bakinta tana kallon sa, shi a karan kansa ba wani babba bane, bata jin zai dora shekaru 20 idan ya dara to ba zai fi da biyu zuwa da hudu ba, yanayin jikin sa na girma da cika yasa zaka kasa tantance shekarun sa, sai dai duk da hakan ba za'a hada shi da yarinya yar shekara goma da doriya ba. Cire glasses din idon ta tayi ta fara magana a hankali cike da nasiha, dan a yadda tayi niyyar shigar dashi kara duba da yadda ta ga halin da ya saka yarinyar a ciki, sai dai yadda ya amsa laifin sa kai tsaye yasa ya sauko ta shiga nasiha da dukkan kokarin ta. Hannayen Dada a makale da ita ta zuba su akan Farouk din, mamaki ne karara kwance a fuskar ta, bata gane nufin sa ba, bata gane inda ya dosa ba, tasan shi da tsananin tausayi amma bata taɓa tunanin zai iya aikata daukar laifi a ajiye akansa ba, tuni zuciyarta ta sake tsinkewa, idan har hakan ne kuwa ya tabbata Farouk din ne ya bata musu yarinya, in kuwa hakan ta kasance bata san ya zatayi ba. Bayan sun fito daga dakin Dr yaki yadda su hada ido sam Dada, yasani sarai tana bukatar gamsasshen bayani, amma baya so ya sanar mata da komai sai ya samu nutsuwar zuciya. Dakin da aka kwantar da ita suka tura suka shiga, Amal na zaune kan kujera tana bacci, drip ne a daure hannun ta, bacci take sai dai yanayin fitar numfashin ta ya nuna tsantsar wahalar da take ciki, karasa wa yayi gaban gadon yana sake kallon ta. "Umar!" Dada ta kira sunan sa, yanayin Muryar ta kadai yasa ya gane abinda zata ce, kasa juyowa yayi har sa data maimaita kiran nasa. "Na'am Swthrt." "Ba wasa nake maka ba, kasan kuma ni ɗin ba sa'ar tsohon ka bace balle kace zaka maida ni mara hankali ko wata chan daban, wacece yarinyar nan? Menene alakar ka da ita?" Juyowa yayi yana fuskantar ta, ganin ta bata rai sosai babu alamun wasa yasa shi takowa har gaban ta. Sai da ya daidaita tsayuwar sa a gaban ta sannan ya fara magana cikin son gamsar da ita. "Kiyi hakuri idan na bata miki rai, hakan da nayi ba wai nayi ne dan na bata miki ba, wallahil azim bani da wata alaƙa da ita,hasalima bansan wacece ita ba, bansan komai game da ita ba." "Aina ka samo ta toh idan baka santa ba?" "A daidai lokacin da Allah ya saukar mana da daya daga cikin ni'imomin sa, a daidai lokacin wani mara imani ya aikata mata wannan aika aikar, babu digon tausayi ko imani a tattare dashi, bansan shi ba, bansan waye ba, ihun ta kadai naji, na taimaka mata." Kallon sa take har ya kai karshe, ganin bata ce komai ba yasa shi kama hannun ta "Ki yarda dani, ba zan taba iya aikata wa wata mace makamancin wannan ba." "Naji! Amma menene dalilin ka na amsa wa likitar nan a matsayin kaine mijin ta? Baka tsoron maganar ta fita, bayan kasan waye mahaifin kuma." "Hakan shine daidai, karki manta wannan abun babban tabo ne a tattare da duk wata ya mace, da zai iya zama wani babban gibi a rayuwar ta. Banyi hakan da wata manufa ba face don kare mutuncin ta." Turo kofar akayi, hakan yasa yayi shiru yana duban su, Dr Iman ce sai wata nurse a bayan ta. Dan dube duben su sukayi suka juya, har ta kai kofa ta juyo. "Af na manta, akwai alluran da za'a yi mata da safe gobe, , so ka zama around please." "In Sha Allah." "Good." "Kai zaka kwana kenan?" Dada ta fada tana kura masa ido, har zai ce eh sai kuma yayi wani tunanin daban "A ah, kece zaki taimaka." "Amal fa? Kalli a yadda tayi bacci." "Eh zanje na tambaye su idan akwai spare gado sai su bamu mu biya sai ku kwanta akai, dama dare yayi yanzu komawa hanyar nan akwai risk, in yaso ni sai mu kwana a mota." Dan jim tayi kadan kamar zatayi magana sai kuma ta girgiza kanta kawai ba tare da tace komai ba ta koma gefen gadon ta zauna tana kura mata ido kamar me karanto wani abu a tattare da ita. *** Da safe na bude ido na ina karewa dakin kallo, daidai lokacin aka turo kofar aka shigo hade da sallama, zuba masa ido nayi ina kallon sa har ya iso gaban gadon, shi din ma kallon nawa yake fuskar sa dauke da murmushi. Juyawa yayi yana kallon Amal dake bacci hankalin ta a kwance, karar ruwan da yaji a toilet yasa ya gane Dada na ciki.  Sake matsowa yayi gaban gadon ya furta a hankali "Ya jikin?" "Da sauki." Na amsa da sauri ina kallo sa "Sannu kinji." "Toh." Nace ina sake bin fuskar sa da kallo kamar me son tuno abu. Murmushi ya sake yi yana kallon drip din dake shiga cikin jikina a hankali, file din dake ajiye saman drawer saka magunguna ya dauka yana dubawa har Dada ta fito. ***Yanayin horn din kadai ya tashi kowa na gidan, a firgice su ja'afar suka fito falo kowa ya tsaya, ba sai an fada musu ba sun san kowa ye, tsoron su daya abinda ya kawo shi a irin wannan lokacin, iya sanin su ma baya kasar baki d'aya. Motoci uku ne suka shigo a jere, kai kawo Baba maigadi ya shiga yi har suka daidai ta a harabar gidan. Cikin shigar sa ta Babban sojin kasa ya fito daga motar fuskar sa dauke da yanayi marar misaltuwa. "Barka da zuwa." Kawai kake ji kowa na kawo gaisuwa. Jiki a sanyaye su Ja'afar suka dunguma zuwa harabar gidan kowa tsoro fal zuciyar sa. A daidai lokacin aka fara bugo da mugun karfi kamar za'a balla gate din gidan, hayaniyar mutane ke tashi da alama ba mutane ne kadan ba. Da sauri ya kalli Baba maigadi Yana neman karin bayani. ZAFAFA BIYAR KAUNAR MU: MAMUH GEE ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL DAURIN GORO:HAFSAT RANO. IGIYAR ZATO: MISS XOXO *_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_* 2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_ saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863* *_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇 *09032345899* _Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_ Mucigaba da shakatawa da wannan kafin a fara kafta WASAN😁👉🏻📻*DG* ©️Rano ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 ALKALAMI TV https://youtu.be/LxY42ErBf_8                          (4) ***** Babu wanda yayi kwakwaran motsi a cikin su, kowa da abinda yake ayyanawa a ransa. Jin bugun na sake karfi ne yasa shi juyawa da kansa ba tare da yayi magana ba ya nufi hanyar gate din. Budewa yayi yana kallon mutane dake tsaye, wasu dauke da makami, ganin haka yasa sojojin sa suka yo wajen da sauri. Hannu yasa ya dakatar dasu yana bin mutanen daya bayan daya cikin tsananin tashin hankali, sai dai duk da hakan ba zaka tantance yanayin da yake ciki ba, fuskar sa tana nan kamar ko da yaushe. "A fito mana da yar mu!" Muryar daya daga ciki ta bakunci jin sa, daya bayan daya ya hau kokarin fassara kalmomin acikin yan sakanni. Take wajen ya kaure da ihun kalmar da yake da bukatar amsar ta cikin gaggawa. Sake daidaita kansa yayi, ya kuma saka dukkan jikin sa ya fito waje sosai yana sake duban su, mutane ne yawancin matasa sai wasu dattijai guda uku daga gefe, kai tsaye ya nufi wajen su, yana me sake daidai ta kansa. Yana isa ya mika musu hannu daya bayan daya, kwarjinin sa ya cika wajen baki daya. Lawan dake niyyar rashin kirki ya ji ba zai iya ba, girma da cikar haibar sa kadai ta isa ka girmama shi. Balle kuma da shigar sa ta nuna ainihin shi din waye ne. A nutse ya kai duban shi wajen sauran yaran kana ya maida kansa garesu "Me yake faruwa?" Ya tambaya yana nuna su Garbati, "Yar mu wadda take cikin gidan nan muka zo tafiya da ita." "Yar ku? Kuyi hakuri ban gane kan maganar ba, zuwa na kenan." "Alhaji jiya daya daga cikin yaran gidan nan ya dauke mana yar mu, bayan mun gaji da neman ta muke samun labari ta wajen daya da ga cikin matasan garin da abin ya faru akan idon sa, toh jiya munzo a daren bamu samu ganin kowa na gidan ba sai Maigadi, shiyasa muka shiryo muka zo yanzu, dan har mun sanar wa maigari ma." Hannu yasa yana shafa kansa, be tsinci komai a bayanin ba, sai dai ya fuskanci suna zargin batan yar su ne a gidan sa, a gidan nasa ma kuma cikin yaran sa, dan jim yayi kadan yana nazari kafin yace "Ku bani mintina biyu dan Allah ina zuwa." Juyawa yayi ya nufi cikin gidan, ya zo shiga Garbati ya daga murya yadda zaiji sosai yace "Wallahi sai an fito da ita, ga Fyade ga sata, haba ai abin yayi yawa." Chak ya tsaya da tafiyar da yake, wani irin bugu zuciyar sa tayi, babu abu daya daya ki jinin ji kamar kalmar fyade. Maganganun da suka cigaba ne suka shiga maimaita kansu a cikin kwanyar sa, da sauri ya fada gidan, suna nan tsaye duk a in da ya barsu, daya bayan daya ya shiga binsu da kallo kamar me lissafa su, duk sun tsure iya kar tsurewa sun gama sanin me hakan ke nufi. "Ina Farouk?" Shiru babu wanda yayi magana, a fusace ya sake tambaya cikin daga murya sosai. Da sauri har suna hada baki suka ce "Sun...sun fita da Dada da Amal." " Ina suka tafi da sassafe haka bayan kuma ku da alama ko dukkanku tashin ku kenan." "Asibiti suka tafi kai wata yarinyar." Dafe kansa yayi ganin zancen na fitowa. "Da yaushe suka tafi?" "Jiya da daddare." *** Zama Dada tayi tana jiran Amal ta idar da sallah, Farouk na zaune a kan kujerar dakin yayi nisa a tunani, shi kadai yasan me yake tunawa, alluran da ya kamata ayi mata duk anyi mata. Tana idar wa ta tashi ta je gaban gadon tana kallon ta "Ya Farouk ta samu sauki ko?" Ta tambaya tana nuna masa ita. Daga mata kai yayi yana murmushi "Amma mene sunan ta?" Girgiza mata kai yayi alamar shima be sani ba, murmushi tayi tana sake kallon ta. "Ina son ta da kawa, me kyau kamar ta cikin cartoon din nan." "Tashi zakiyi mu tafi ba surutu zaki tsaya yi ba." Sai kuma ta maida kallon ta wajen Farouk "Kai ma tashi zakayi muje, idan yaso sai a nemi iyayen ta a sanar musu suzo dan yanzu nasan hankalin su a tashe yake." "Da wai sai na zauna da ita har suzo ɗin, kinga be kamata a bar ta ita Kadai ba." "Farouk!" Ta bude idon ta sosai "Baka da hankali ko? Kasan abinda hakan zai haifar? Lallai kai yaro ne." "Dadah ki barmu anan nida Ya Farouk dan Allah, kinga idan ta tashi bata ga kowa ba zatayi kuka." "Toh uwar iya, wallahi tashi zakuyi mu tafi, ba zan iya da matsalar da zata taso ba, na riga nayi magana da wata nurse zasu shigo suna dubata har suzo iyayen nata." Kamar ya fashe da kuka haka yaji, shi be ga dalilin da zai sa Dada tace sai sun tafi ba, gashi idan ta kafe babu abinda zai sa ta hakura, tashi yayi tsam yana kallon gadon kafin ya juya ya fice da sauri. Kwafa tayi ta ja hannun Amal suka fito, a tsaye ta hango shi tare da Dr Iman suna magana, karasawa tayi wajen "Dr Barka da safiya." "Yawwa Mama, ya me jiki?" "Alhamdulillah, mungode Allah." "Allah ya kara sauki, zan shiga sai na duba jikin nata." "Ok Dr, nima zan dan je gida ne na dawo." "Ok yayi,ka same ni a office idan na gama round zan yi magana da kai, amma yanzu ka koma dakin karta farka taga babu kowa." Ta fada tana yin gaba,kallon Dada yayi yana marairaice fuska, ganin yadda tayi kicin kicin da fuska. "Sai ka zauna ai dama abinda kake so kenan, amma wallahi Babana ina ji maka tsoron abinda zai je ya dawo, ba fata nake ma ba, amma baka san halin mutanen mu ba." "Babu abinda zai faru sai Alkhairi Dada." Ya fada cikin gamsuwa. "Shikenan, Allah yasa." "Amin." Yace yana murmushi. "Zan tsaya wajen ka Yah." Kama bakin sa yayi da sauri yana kallon Dadan, tsaki tayi ta juya tana mitar sun raina ta. Ciki suka koma da sauri, har lokacin bata tashi ba tana sauke numfashi a hankali. **** Zagaye da hannayen sa yake kaiwa da komowa, wani irin tashin hankali me matukar girma yake hasasowa idan har abinda yaji ya zama gaske, ya zaiyi? Da wacce fuskar zai kalli mutanen kauyen. Tabbas idan hakan ta kasan zai dauki mummunan mataki akan Farouk, baya fatan zargin sa ya zama gaskiya dan zai iya yafe shi ba ma a cikin yayansa ba, a cikin dukkan ahalinsa. Duk kuwa da dimbin soyayyar da yake masa duk cikin ya'yansa. Jin tsayuwar mota yasa ya juyo da sauri yana kallon gate din da tun zuwan sa yake tsaye wajen ya rasa me zaiyi. Idanun sa akan gate din har aka gama budeshi. Ganin motar gidan yasa ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya, duk da baya hango cikin motar amma yasan sune suka dawo, a yau da ace ba tare da mahaifiyar sa suka tafi ba be san abinda zai iya aikata mishi ba, sai dai dole ya saita kansa yaji komai a baƙin ta. Hannun sa ya harde a kirji yana jiran daidaituwar motar da yake ganin kamar da gangan driver yake lankan jin ajiye ta a mazaunin ta. Dada ce ta fito tana me kallon harabar gidan cikin tarardadin abinda yake faruwa, farko mutanen da ke waje tsaye kamar masu jiran a fito musu da gawa su kaita kushewa, sunyi kungiya kungiya suna tattaunawa, yanzu kuma tsayuwar Janar a harabar gidan ya kara tabbatar mata da abinda take tsoro take gudu ne ya faru. Jiki a sabule irin na wanda yayi fama a filin daga ya isa gareta kafin ta ƙaraso. "Dadah.! Ya furta muryar sa a bude sosai me nuna yanayin da yake ciki. "Muje ciki." Ta fada tana kallon sojojin da sukayi dafifi a wajen suna tsaye cikin jiran cika umarnin uban gidan na su. Be musa ba, sai jan kafar sa da yayi da tayi matukar sanyi yabi bayanta. Ajiye mayafin ta tayi ta zauna tana daidata nutsuwar ta, dan tabbas ta hango tsananin tashin hankali da firgici a idon yaron nata, kasancewar sa babban soja hakan be sashi zamaar mata tamkar yaron goye a duk sanda yake tare da ita ba. Tabbas haka Farouk yake, a duk yayansa shine ya biyo shi, babu abu daya daya bari nasan tun daga dabi'a da yanayin yadda yake daukar a'alamri, abu daya tasani shine Farouk yana da sanyin zuciya da saurin yarda da komai, banbancin sa da mahaifinsa kenan wanda ya kasance mutum me tsauri sosai da rashin yarda a duk sanda abu ya gifta tsakanin ku, duk yadda kake dashi zai bar ka, barwa ta har abadah kamar yadda suka rabu da mata mafi soyuwa a gareshi bisa babban kuskuren data aikata masa. Ruwan da aka ajiye a gaban ta ta kalla tana kallon Ja'afar daya kawo ruwan. Dauka tayi ta zuba ta mika masa. "Sha ruwa Muhammadu, ko zaka ji saukin zuciyar ka." Karba yayi ba tare da yayi magana ba ya kafa kai ya shanye tas yana ajiye kofin. "Me yake faruwa?" Ta wurgo masa tambayar tana nakaltar nazarin sa. Sai da ya sauke ajiyar zuciya kafin yayi magana cikin dakiya "Ni kaina na rasa me yake faruwa, zuwa na kenan, na tarar da wannan tashin hankalin, shin da gaske ne abinda mutanen garin nan ke tuhumar Farouk?." "Me suke tuhumar shi akai? Maganar yarinya ne ko?" Ta fada kai tsaye dan tasan kwanan maganar kenan. "Eh ita Dada, suna zargin Farouk da yi wa yarinyar su fyade sannan kuma ya sace ta, wannan wanne irin tashin hankali ne Dada." Shiru tayi tana maimaita innalillah wa inna ilaihi raji'un a ranta, abinda take gudar wa Farouk kenan, ya kasa ganewa. "Dadah dan Allah, ina ya kai yarinyar, kuma shin da gaske abinda suke zargin sa akai ya aikata?" "Yarinya dai tana asibiti dan yanzu ma daga chan nake, kuma tabbas yazo da yarinya a cikin mayuwacin hali, kuma nayi magana dashi na tambaye shi idan shine ya aikata mata, yayi mun rantsuwar dan musulmi bashi bane." "Shikenan, Farouk ya gama dani." "A ah kar kayi saurin yanke hukunci, ka tsaya kaji ta bakin nasa." "Haba Dadah, yaran yanzu fa sun wuce tunanin mutum, kuma ba'a shaidar su sam, dan wanda kake ganin ba zai aikata abu ba yafi aikatawa." "Yanzu menene abinyi?" "Tashi zanyi naje asibitin, gani gashi ga iyayen yarinyar, harda maigari ma." "Shikenan, amma kabi komai a sannu." **** Shigar su dakin yayi daidai da sake farkawar ta, a dan tsorace take kallon su, kafin ta maida idon ta da sauri ta kulle su gam. Amal ce tayi saurin karasawa wajen gadon ta rik'e hannun ta, jin an rik'e ta yasa ta bude ido ta sauke su akan ta. "Ya sunan ki?" Amal ta tambaya dan ta matsu tasan sunan ta. "AMINATU!" Da sauri ya juyo, sosai yaji sunan nata har cikin ransa, sauti da amon muryarta ya shiga masa amsa kuwwa, yana jin Amal na fada masa sunan su daya tana murna ya kasa amsa mata, sai ma binsu da ido kawai da yake yi kamar be san me yake faruwa ba. Hira sosai Amal ta shiga yi mata, kallon ta kawai take yi ba tare da ta gane komai ba, ido kawai tasa mata. "Zan sha ruwa." Ta furta a hankali, da sauri Amal ta tashi ta dauko mata ruwan, kokarin tashi tayi taji zafi, kuka ta saka yayi saurin tasowa, "Sannu." Daga masa kai tayi tana gogen hawayen da bayan idon ta. Ruwan ya bata Amal na tsaye kamar zatayi kuka. "Gida zan tafi." Tace tana kallon sa. Zaiyi magana aka turo kofar, wani irin faduwa gaban sa yayi yasa hannu ya rike wajen zuciyar sa da sauri. "Daddy!" Amal ta fad'a tayi wajen sa da sauri, rike ta yayi ya matsar da ita gefe bayan ya shafa kanta, Maigari ne ya fara shigowa,sai Baba, Inno na bin bayan sa, sai Lawan Da Yahya. Garbati da Ilu suna take musu baya. Da sauri Inno tayi wajen gadon tana sakin kuka. Gyaran murya maigari yayi, Inno tayi shiru duk aka nutsu ana kallon sa. "Garbah!" Ya kira sunan Garbati yana masa alamun ya matso. "Maimaita abinda kace." Gyara tsaiwar sa yayi cikin dakiya ya nuna Farouk da hannun sa "Gashi nan, jiya ana ruwan nan ta gefen daki na naji kamar ana kuka, da har na share sai na kuma jin kukan na tsananta, kamar wasa na dauko toci ta na leko, in haska sai ga tashin hankali, ido na cikin nasa yana aikatawa karamar yarinya, nayi kukan kura na rike shi, muka haure da kokawa, shine fa ya samu yayi min mugun duka, kuma ya dauke ta ya gudu, duk da haka sai dana bisu a baya, naga gidan daya shigar da ita, shine fa nayi gaggawar zuwa sanar da iyayen yarinyar." Tun da ya fara magana Farouk ke  kallon sa, gaba daya jijiyar kansa ta fito, numfashin sa ya shiga fita da sauri da sauri, duk suka zuba masa ido suna kallon sa, Daddy kuwa kasa yayi da kansa yana jin kamar kasa ta zage ya shige, sai dai bashi da ta cewa, duk abinda gaskiya ta bayyana zai goyi bayan ta, ba zai taba goyon bayan zalunci ba ko da daga dan cikin sa ne. "Kaji abinda ake tuhumar ka dashi, shin kana da abinda zaka kare kanka, duk da dai ga zahirin ganin ku tare da mukayi anan, amma ko zaka fada mana dalilin da ya jawo hakan." Maigari ya fada yana duban shi, kokarin magana yake ya kasa, motsa bakin sa yake ya kasa, kallon Garbati kawai yake cikin tsananin bacin rai, bai taba tunanin akwai mutane masu aiki irin na dabbobi kamar shi din ba, kallon Amal yayi yaga ta zuba masa ido kamar me son ganin wani abu, ya sake maida kansa wajen Aminatu, itama shi take kallo, tana share kwallar dake zubo mata. Runtse idon sa yayi ya bude ya maida kallon sa wajen Daddy, yanayin daya ga fuskar sa kawai ta gamsar dashi abin da zai je yazo idan har ya kasa fitar da kanshi daga wannan daurin. Kokarin daidai ta kansa yayi ya shiga kokarin magana a nutse duk kuwa da tarin tashin hankalin da yake ciki "Allah ne..." "Kai ne kayi mata Fyade ko ba kai bane!" Daddy ya fada cikin k'araji dan ya gaji so yake kawai ya amsa da a ah ko Eh. "Daddy Wallahi tallahi Allah ne shaida ta..." "Will you shut your mouth, amsar ka kawai nake so kai ne ka aikata mata Fyade ko kuwa?" "Fyade!" Dr Iman da shigowar ta kenan ta karbi kalmar, duk suka juyo suka kalle ta. "I'm sorry to interrupt, kuna nufin dama yaron nan ba mijin ta bane, fyade yayi mata suka rufa min yace shi mijin ta ne?" Da sauri Farouk ya kalle ta zuciyar sa na sake tsinkewa. DAURIN GORO😢😢😥😥😓 ZAFAFA BIYAR KAUNAR MU: MAMUH GEE ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL DAURIN GORO:HAFSAT RANO. IGIYAR ZATO: MISS XOXO LITTAFI DAYA 200 BIYU 300 UKU 400 HUDU 450 BIYAR 500 *_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_* 2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_ saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863* *_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇 *09032345899* _Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_*DG* 5 *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo ©*Rano*                               (5) **** Duk suka maida kallon sa gare ta, takowa tayi ciki tana kallon fuskar Farouk din. "Me kike cewa Dr?" Daddy ya tambaya yana kallon fuskar Farouk din "Nice likitar data karbi case din yarinyar, a yadda mukayi magana na zata matar sa ce, dan shi dinma ya nuna min hakan, duk da cewa akwai karancin shekarun ta da nashin ma kansa, sai dai ya amsa laifin sa kuma ya bada hakuri, amma kuma naji wata maganar daban duk da ba dani ake ba, amma ina da right na sani saboda matsayi na na likitar ta." "Babu wata matar shi, makaryaci fyade yayi mata kila ma sai daya sha ya bugu sosai sannan." Garbati ya fada yana huci. Kasa hakuri Farouk yayi ya kalle shi cikin konar rai "Sharrin da zakayi min kenan, kasan nasan komai shine kake kokarin jona min laifin da ka aikata?" "Ni? Ni zaka wa sharri, na ganka ido da ido, shine zaka maida abin kai na, na shiga uku, wallahi Maigari karya yake min so yake ya maida abin kaina." Sake duban sa Farouk yayi yace "Kaji tsoron Allah, ka sani akwai mutuwa akwai hisabi, kar kaga idon mutane anan, ka fadi gaskiya ko dan rayuwar yarinya karama." "Wallahi tallahi sharri yake min, shine ya aikata karya yake min wallahi." Garbati ya fada yana karashe wa da fashewa da kuka kamar gaske. Dafa kai Daddy yayi ya kalli farouk, ya gaji da wasan yaran nan da suke musu, magana daya yake son ji, idan shi ya aikata ya amsa eh ko a'ah. Rike masa riga yayi cikin bacin rai "I'm asking u for the last time, Kai ne ko ba kai ne ba?" Kukan Amal da Aminatu ne ya kara karfi a wajen, juyawa Farouk yayi ya dube su daya bayan daya, sosai kukan nasu yake taba masa rai, kallon Daddy yayi ya shiga girgiza kai. "Alhaji ina ganin tun da ga yarinyar nan a zaune, duk da karama ce amma ba zata kasa tantance wani abu ba, ina ganin a tambaye ta, idan yaso kowa ne ya aikata mata wannan abin, a cikin su, to fa dole ne a aura masa ita bayan hukuncin da shari'a ta gindaya ga wanda ya aikata irin wannan laifin, dan kaf kauyen nan namu babu wanda zai yarda ya karbi aurenta, musamman yanzu da zance ya zagaya ko ina, ina tsoron sai dai ta karasa rayuwar ta a haka." Maigari ya katse su, sakin sa Daddy yayi ya hankada shi har sai daya kusa bigewa da karfen gadon, dago idon sa yayi ya sauka cikin nata, wani irin abu yaji ya taba shi, wanda be taba jin irin sa ba, raunin da ya gani a cikin idon ta, yarintar ta da tsantsar tausayin ta suka hadu. Idan har yaji daidai abinda mai gari ya fada, yana nufin aura wa Garbati ita kenan, auren da yake nufin lalacewar rayuwarta har abadah, auren da yake nufin yanker war duk wani jin dadi na rayuwar ta, auren da yake nufin rayuwa da mutum wanda bashi da maraba da dabba, dabbar ma mafi kaskanci acikin dabbobi. Kasa dagowa yayi ya rasa me yake masa dad'i, yana jin sanda Maigari ya kira sunanta, yana jin lokacin da ya tambaye ta, kukan ta ya kara karfi, be san yaushe ba, be san yaya ba, kawai ya samu kansa da amsawa a maimakon ta tun kafin ta samu damar yin magana. Da wani irin karfi Daddy ya riko shi, ya shak'e shi, kakari ya fara kamar wanda yake shirin mutuwa cikin sauri Baba ya shiga tsakani. Yayi kokarin bangare shi daga rikon da yayi masa, "Alhaji kar kayi mishi illah." Ya fada cikin tashin hankali ganin yadda idon yaron ya kakkafe "Barni na kashe shi, ya cancanci haka, ko ma fiye da hakan, barni dan Allah, harbe shi zanyi kowa ya huta." Ya sake riƙe shi sosai, bugu ya fara kai masa ta ko ina, tun Farouk na kokarin kwatar kansa har jikin sa ya saki ya shiga fitar da jini ta ko ina. Lawan da sauran ne suka shiga tsakani, ganin haka yasa Garbati da Ilu sulale wa su bar dakin suna fita suka ci karo da sojoji, a darare suka gifta su suka bar asibitin da sauri. Ba karamin duka yayi masa ba, da kyar suka kwace su, duk da haka sai daya hankad'a shi da karfi kansa ya fashe, Amal ce tayi saurin isa wajen sa tana kuka taa dago shi. Haki kawai Daddy yake, kamar wanda ya shiga filin daga, cikin tsananin bacin rai ya nuna shi da hannu yana kallan su Maigari. "Maigari, Malam da sauran wanda suke wajen nan, ku zama shaida, ga shi nan, duk hukuncin da kuka yanke akansa bani da ja, kuyi masa duk abinda kuka ga dama babu ruwana, karku duba girma na, arziki na ko khakhi na, kuyi masa hukuncin daya dace daidai dashi." Ya dora... "Sai dai ina neman alfarmar kowanne hukunci za'a yanke ya zama cikin kwana biyu, dan zan koma in da na fito." Juyawa yayi ya nufi kofar fita da sauri yana jin ba'a taba bata mishi rai irin na yau ba. Daya bayan daya suke dinga zamewa suna barin dakin ya rage sai su Inno kawai. Tashi tayi ta dago shi tana kallon fuskar sa "Baka aikata abinda ake zargin ka dashi ba, amma me yasa ka dauki laifi me girma ka dora akan ka?" Ta tambaya tana karantar sa. Mik'ewa yayi yana goge bakin sa yana kallonta "Bansani ba, bansan dalili ba. Ina ganin hakan da nayi shine kawai mafita." Juyawa yayi ya bar dakin Yana rangaji, Amal ta bishi da sauri tana kiran sa. Kuka na fashe dashi, Inno ta harare ni tana zama a gefe na "Kukan uban me kike?" "Inno kinga fa kuka yake, duk kuma jini a jikin sa, yana da kirki sosai." "Toh sai akayi uban me? Ke yanzu karamar ki dake kinsan wani yana kuka, baki ji maganar da mai gari yayi ba, idan na yarda akayi miki aure idan ranar da nake jira tazo nayi yaya kenan?" "Na'am?" Na tambaya cikin rashin gane abinda take nufi "Manta kawai, abu daya nake so dake, idan aka tambaye ki kice ba zaki auri kowa ba, babu inda zaki matsa daga nan sai ranar da Allah ya yanke miki wahalar nan." Gid'a mata kai nayi ina share hawayen dake faman kaikawo a fuskata kamar an kunna fanfo. Tashi nayi ta taimaka min na wanke fuska ta, ina zama ya shigo fuskar sa anyi dressing ya dire kayan tea ba tare da yayi magana ba ya juya ya sake fita. *** A hargitse ya shiga gidan, Dada na zaune a falo tana jira shigowar sa, ganin yanayin sa yasa tasan komai ya ɓaci, be zauna ba, ya shiga kwala wa su Ja'afar kira, sai daya tara su duka sannan ya hau fada, sosai yayi musu fada sannan yace duk su shirya kaya zasu bar garin a ranar. Duk suka amsa da toh sannan ya sallame su. Zama yayi cikin kujerar falon yana zare butiran din hannun sa. "Dadah yaron nan ya amsa laifin sa, dan yau dama ka haife shi ne baka haifi halin sa ba." "Yanzu menene abin yi? Kana nufin shi baban nawa ya amsa laifin?" "Ya amsa har ma sun yanke hukuncin bashi auren ta." Da sauri ta tashi "Aure kuma? Dududu Baban nawa nawa yake? Karka manta alƙawarin da kayi wa Marigayi." "Toh ya za'a yi Dadah, tun da yasan ya bata wa yar karamar yarinya rayuwa ai gwara a aura masa ita kawai kowa ya huta, idan yaso sai ya hakura da karatun nasa su zauna anan ɗin tunda irin rayuwar da ya zaba ma kansa kenan." "Amma ka tabbata shi ya aikata?" "Nima da ina ta tunanin hakan, amma daga baya daya amince da laifin nasa kinga ai babu maganar tantama, ya aikata din" "Kai wannan abu beyi dadi ba, amma ita yarinyar fa? Bata fadi kowa ba?" "Kin ganta dai Dadah, karama ce sosai dan ko Amal ta fita girma da cika ido, ga kuma kauyanci da rashin wayewa, bayan haka ba'a kai ga tambayar yarinyar ba ya amsa laifin sa, kinga ai babu bukatar kuma wani dogon bincike da dai be amsa bane." "Toh Allah ya sauwake, amma sam banji dadin abin nan ba, amma dai ƙaddara ce dan sam ba haka halin babana yake ba kai ma ka sani, bansan dai me ya faru ba, Allah ya kara kiyaye wa." "Amin ya ALLAH." "Bari na shiga ciki, in sha Allah da an gama komai jibi zamu wuce baki daya, su yaran suyi gaba yau, nima ina da ayyukan yi da yawa, dalilin admission din farouk din ne ya shigo dani garin wallahi." **** Tafiya yake a kasa bayan ya bawa driver umarnin ya maida Amal gida, be san ina yake saka ƙafarsa ba, ya dai san kawai yana tafiya ne akan kasa, sai dai kafatanin tunanin sa ya tafi ne akan abinda ya faru a yan awannin da basu wuce ashirin ba, gaba daya rayuwar sa ta chanja, ya rasa duk wani girma da kima a idon mahaifin sa, haka Allah yake ƙaddara wa bawa ƙaddarar sa, ba tare da ya shirya ma hakan ko yayi tunanin hakan zai taba kasancewa dashi ba. Tsaiwar babur a gaban sa ce yasa ya dakata yana kallon na kai, Garbati ke da Ilu, cikin kazamar shiga irin ta yan Iskan kauye, sigari Garbati ya busa masa a fuska yana dariya. "Ango ango." "Lafiya?" " Ita ce ta kawo hakan, ka dai ga kadan daga aikin Garbati ko?" "Bani da lokacin tsayawa magana daku, kamar yadda ban dauke ku a cikin jerin mutane masu hankali ba." Da haka ya rabe ta gefen su ya wuce, yana jin Garbati na kutuntuma masa ashar, be bi ta kai ba, burin sa kawai ya isa wajen da babu kowa.    Kansa ya haɗa da gwuiwar sa, ba zan iya fadar yanayin da yake ciki ba, zuciyar sa ta yi nauyi, ta cunkushe kamar zata budo kirjin sa ta fito, so yake yayi kuka ko zai samu sauki, sai dai babu ko digon hawaye sai na zuci da ya ka faman yi. Da fari ya so ya tabbatar da gaskiyar sa, ko dan irinsu Garbati masu halin dabbobi, sai dai furucin auren da yaji ne ya rusa komai, ba zai iya barin yarinya karama Kamar Amal ta rayu da Garbati ba, rayuwa irin ta aure me cike da tarin matsaloli, dalilin hakan yasa yayi ma kansa mugun dauri, daurin da yake tunanin har karshen rayuwar sa zai cigaba da bibiyar sa.     Ya jima sosai a wajen, ba zai iya lissafa adadin awowin daya bata ba, ya dai mike ne kawai da niyyar zuwa gidan ko me zai faru ya faru. Sai a lokacin ya lura da irin nisan tafiyar da yayi. Har ya karasa gidan be bar fargabar haduwa da Daddy ba, ya san shi sarai yasan abin da zai iya aikatawa akan shi, abun mafi tsoro a tattare dashi shine bakin sa, baya son wata kalma ta muzantawa ta fito daga bakin sa, ba zai iya daukar hakan ba sam.    Tura gate din yayi yaji shi a bude, a nutse ya tura kansa cikin gidan bakin sa dauke da addua, jami'an tsaron dake zube birjik a gidan ya fara cin karo dasu, duk suka zuba masa ido suna kallon sa, dauke kansa yayi ya haura kofar da zata sadaka da falon gidan. A dan tsorace ya tura kofar yana tarrradin abinda zai tarar, cikin tsawa aka dakatar dashi. "Tsaya anan!" Da sauri ya tsaya yana maida hannayen sa baya kamar me shirin arcewa. "John!" Daddy ya bud'e murya ya kwala kira, a guje ya shigo ya tsaya gaban sa. "Lock him up." Ya fada yana nuna masa Farouk dake tsaye kamar an dasa shi, yasan dama hakan zata faru. "Yes sir!" Ya amsa da sauri ya chakumi wuyan Farouk kamar kayan wanki. Tirjiya ya fara yi yana magiya "Daddy please ka saurare ni, dan Allah Daddy." Ko gezau beyi ba, sai ma hade rai da ya sake yi yana wa John mugun kallo "Me kake jira ne?" Da sauri ya karasa janshi, ya fita dashi. Tsaki Daddy ya ja ya tashi ya bar falon baki daya. DAURIN GORO😢😢😥😥😓 ZAFAFA BIYAR KAUNAR MU: MAMUH GEE ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL DAURIN GORO:HAFSAT RANO. IGIYAR ZATO: MISS XOXO LITTAFI DAYA 200 BIYU 300 UKU 400 HUDU 450 BIYAR 500 *_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_* 2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_ saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863* *_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇 *09032345899* _Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_*DG* *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo     ©Rano                     (6) *** Ina kwance ina ta kallon inno tana hada kan abubuwa da suke dakin, Nura ne ya shigo ya karba sannan ya fita dasu, kamani tayi ta lulluba min wani babban Mayafi muka fito, a hankali nake tafiya cikin wani yanayi mara dadi da ba zan iya tantancewa ba, har muka isa gaban motar da ban taba ganin irin ta ba, soja ne ya bude mana gidan baya muka shiga, ya rufe sannan muka dauke hanyar kauyen mu, kasancewar motar rufe take ruf da bakin gilashi hakan ya hana mutanen gari kallon mu, sai dai na lura duk in da muka bi sai an bimu da kallo. A kofar gida ya ajiye mu, Inno ta sake jan mayafin ta kare min fuska ta sosai ta fito dani, mata ne a tsaitsaye kowacce ta fito jin mota, da sauri Inno ta ja hannu na muka shige gida tana hararar su. Muna shiga matan gidan mu suka taso, kowa yana min sannu wadda ta kasance da biyu, daki Inno ta tura ni ta dawo wajen su tana amsa gaisuwar da suke min ta munafurci da gulma. Sun dan jima ina jiyo sautin karadin su, har suka watse, daga nan bacci ya dauke ni, ban sake sanin me yake faruwa ba. A bangaren gidan Maigari kuwa ya aikata aka kirawo su Baba da Daddy. Inno najin hakan ta rufo ni a daki ta yafa mayafinta ta bisu, Baba be isa ya hanata ba sai dai babu yadda ya iya. Suna zuwa Daddy ma yana zuwa cikin shigar fararen kaya manya, cikin girmamawa suka gaisa gaba daya, Inno na makale a gefe tana jiran taji dalilin kiran. "Abin da yasa na tara ku anan..." Maigari ya soma "Maganar da mukayi akan yaran nan, da kuma alfarmar da shi Alhaji ya nema ta a yi koma a kwana biyu, ina ganin abu daya da zamuyi wa yarmu shine aure, dan babu wani mutum a kaf kauyen nan da zai karbi auren ta, dan hakan ta taɓa faruwa a baya, a karshe saboda yadda yaran gari suka sako ita yarinyar a gaba yasa ta aikata abinda duk beyi mana dadi ba, shiyasa muka yanke hukuncin idan hakan ta sake faruwa, toh duk wanda aka tabbatar da ya aikata hakan xa'a aura masa yarinyar." "Gaskiya ne." Duk suka amsa cikin gamsuwa. "Toh yanzu Alhaji idan ka shirya, sai a gabatar da komai a nan." "A shirye nake ranka ya dade, duk abinda ake bukata sai a sanar dani." "Gaskiya ina da ja wallahi." Maganar Inno ta katse su, "Ina dah ja maigari, ya kamata ace a matsayi na na uwar yar nan anyi shawara dani, amma ace kawai a yanke hukuncin yi mata aure babu izini na, yarinyar da dududu nawa take, gaskiya ni ban yarda ba." Da tsananin mamaki suke kallon ta, babu uwa daya a kauyen nan kaf da irin hakan zata faru har ta tsaya jayayya, kamar bata san kalar wulakancin da yarinyar zata fuskanta ba? "Menene dalilin ki, na kin abinda muka zo dashi?" Maigari ya wurgo mata tambayar "Allah ya taimake ka, ni dai kawai bana so ne, ban yarda ayi mata aure yanzu ba, batun maganar mutane kuwa suyi tayi, zan san yadda zan ɓullo musu." "Kaji abinda maidakin ka tace Malam Ayubah, yar nan dai yarku ce, ku kuka haife ta, duk soyayyar da zamu nuna mata ba kamar wadda kuke yi mata ba, menene ra'ayin ka akai?" "Ranka ya dade ni dai na amince da maganar auren, ina ganin hakan shine kawai sauki." Ya fada ba tare da ya kalli bangaren Inno ba, dan yasan idan ya yarda suka hada ido ba zata taba barin sa ya aikata zabin zuciyar sa ba. "Sauran yan uwan yarinyar, shin kun amince ko kuwa?" "Mun amince." "Masha Allah, toh ke sai kiyi hakuri, dama aure a hannun Iyayen maza yake." "Alhaji Bismillah." Matsowa Daddy ya sake yi ya zura hannu a aljihun sa ya ciro kudi, alama yayi wa da driver sa ya fito da sauran kayan dake booth ɗin, ganin haka yasa Inno fashewa da kuka ta yi saurin fadawa gidan mai gari. Bisa ga shaidu da wakilan kowanne bangare aka shiga gabatar da daurin auren da ya zamo tsanin farko na duk wata rayuwa da Aminatu zata taka a gaba. *** Cikin dare ta kasa bacci, babu abinda take sai juyi, bata san yadda zatayi ba, idan har auren nan na nufin katanga da cikar burin ta, zata iya komai akai, duk da babu wanda yasan abinda ya faru sai mutane uku kachal a duniyar nan, amma ba zata bari damar ta ta karshe ta kwace mata ba, wanda auren nan yana nufin rugujewar komai. Har akayi asubah tana bitar abu daya, bata jira gari ya gama haske ba, ta tashi Aminatu ta bata kunu, ta ballo mata magungunan ta ta bata sannan ta dauki yar karamar purse din ta da mayafin ta, ta fice daga gidan. Tafiya me nisan gaske tsakanin kauyen nasu da wanda ke makwabtaka dasu, sanda ta isa gari yayi haske sosai, mutum daya jallin jal data san sirrin ta, sirrin da yake shirin zama tarihi idan har ta aminta da wannan auren, wajen ta tazo, dan samun mafita. Da sallama ta shiga gidan duk matan gidan suka kalle ta cike da mamakin wannan zuwan nata da sassafe haka, gaishe su tayi a tsaitsaye bata damu da irin kallon da suke mata ba ta fada dakin wadda tazo wajen ta. "Akwai matsala kenan." Ta fada tana kallon ta har ta ƙaraso ciki. "Ita ce ta taso ni, ina cikin matsala wallahi harira, bansan ya zanyi ba." "Lallai ai naga alama, me ya faru hala? Ko dai wani abun ya samu yar mutane ne?" "Kusan haka." Ta cire mayafin ta ta zauna gefen gadon, sannan ta shiga bata labarin komai. Ajiyar zuciya Harira ta sauke bayan ta gama sauraron ta "Kema dai Inno kinyi sakaci, bayan kinsan dalilinmu da kudurinmu a nan gaba, amma kikayi sakaci da yarinyar mutane har wannan abin ya faru da ita, kina ganin zasu yarda ne su kyale mu duk ranar da gaskiya ya fito? Bayan irin rikon da sukayi wa namu d'an." "Duk nayi dana sani wallahi, zuciya ce ta d'ebe ni, amma yanzu na gano kuskure na, ki taymaka nidai da shawarar yadda za'a yi da auren nan, idan yaran nan ya dauke ta suka bar kauyen nan kina ganin zai sake dawowa da ita ne?" "Gaskiya dai, gashi kince an riga an daura auren." "An daura wallahi." "Toh mafita daya ce gaskiya idan zaki iya..." "Zanyi koma menene idan akan d'ana ne." Murmushi harira tayi ta matso kusa da ita. *** Kamar kayan wanki haka suka fito dashi, a kwana biyun da yayi duk yai baki ya rame sosai kamar ba shi ba, kauda kai Daddy yayi daga kallon sa, sun riga sun fito a shirye zasu tafi, Dada kawai za'a bari itama dan tace babu inda zata ne, gashi ba zai iya musu da ita ba. Su Ja'afar kuwa tuni suka tsufa a can sai dai Daddy ya ja musu kunne akan maganar, baya son kowa yaji har sai ya dawo da kansa zai sanar musu. Atm card ya ciro ya wurga masa, sai mukullayen gidan. "Gashi nan, tun da kalar rayuwar daka zaba ma kanka kenan." Da sauri ya kalli daddyn, sanin hakan me yake nufi ne yasa ya hau rokon sa "Daddy dan Allah ka tsaya ka saurare ni, wallahi ban aikata abinda ake zargi na dashi ba." Da wani mugun kallo ya dube shi "Ni sa'an ka ne Farouk? Ko ka fara shaye-shayen ne dai da gaske?" "Wallahi ban taba shan komai ba, ka saurare ni kadai nayi maka bayani, wallahi bani da laifin komai." "You must be a fool, nace baka da hankali sam, idan har kana ganin zan tsaya sauraran ka bayan da kanka ba wani ya matsa bakin ka ba ka amsa laifin ka a gaban kowa, sannan yanzu kazo min da wani banzan zancen ka, toh kayi karya wallahi." Riko ƙafafuwan sa yayi da sauri yana sake sakin kuka "Wallahi ban aikata ba, bansan me ya hau kaina ba na amsa, dan Aallah Daddy kar kuyi min haka." Buge hannun sa yayi ya janye ƙafarsa yana matsawa. "Idan ka gama haukan naka zamu wuce." "Daddy ka taimaka min, maganar karatuna fa dan Allah, wallahi ban aikata abinda kake tunani ba, taimakon ta kawai nayi, wanda na dauke ta tamkar Amal." Tsaki Daddy yaja, ya gaji da jin wannan shirmen nasa, bashi da lokacin da zai kara batawa ya saurare shi, duk wata hujja tasa bata da amfani tun da be kawo ta a lokacin da ya kamata ba, ko a gaban alkali ne to Tabbas ya tabbata mai laifi tun da har yayi saurin amsawa. Duban shi yayi, baya so ya karya masa zuciya, saboda haka ya nuna shi da hannun sa "Kai yanzu ai na gama da kai, ba zan iya tsayawa sauraren shirmen ka ba. Maganar karatu kuwa in kana so zaka iya neman admission ka soma karatun anan, kar dai ka manta akwai responsibilities na matar ka kanka, so you have to be very careful." Hannu ya watsa baya ya juya cikin takun kasaita ya fada mota, Amal ce suka fito da Dada tana kuka sosai akan dole ba zata tafi ba, da sauri ya rarrafa gaban Dadan yana sakin kuka me tsuma rai. "Dada kiyi min rai dan Allah, Daddy ya dau zafi sosai yaki saurarata." Dago shi tayi ta bude kofar falon ta tura shi ciki ta rufe, motar ta nufa rike da hannun Amal, daddy na ganin haka ya fito. "Ka barta ta zauna tare dani har zuwa lokacin da za'ayi resuming makarantar su, sai azo a tafi da ita dan Allah." "Duk yadda kika ce haka za'a yi, mu zamu wuce." "Allah ya kiyaye hanya, ka kara nazari akan hukuncin da ka yanke wa Babana, duk abinda ka shirya sai ka sanar min a waya." "Shikenan in Sha Allah." Matsawa baya sukayi motocin suka fice daya bayan daya, ajiyar zuciya ta sauke ta kama hannun Amal suka juya ciki. Kaiwa kawai yake da komowa a tsakiyar falon, yana jin an bude yayi wajen ta da sauri ya fada jikinta yana sakin kuka. Bata hana shi ba, tasan zuciyar sa a cunkushe take kukan kadai zai rage masa radadin da yake ji. Ya dau lokaci sosai yana kokawa da zuciyar sa, yana jin kamar ya hadiye ta ya huta da radadi da zafin da take masa, a hankali ta fara sanyi sakamakon addu'ar da yaji Dadan na tofa masa, da sauri shima ya kama yana karanto innalillah wa inna ilaihi raji'un. Sosai hakan yayi masa tasiri kwarai, zamewa yayi ya zauna akan tiles yana sauke kansa kasa. "Babana..." "Tashi ka shiga kayi wanka ka gyara jikin ka, dukkan tsanani yana tare da sauki, kuma komai zai warware cikin ruwan sanyi. Ka cigaba da addu'a." Be musa ba, illa mik'ewa da yayi yana nufar dakin sa cikin tafiyar da tafi kama da wanda ya kwanta jinya me tsawo. ***Ina kwance yau ma kamar ko yaushe tun barowar mu asibiti bana iya aiwatar da komai sai abinda Inno tace, komai yimin ake abinci ma sai ta bani a baki, shigowa tayi tana tura kyauren dakin namu, gefen da muke ajiye kayan mu ni dasu Karime ta nufa, ta jawo ledar kayana ta fito dasu, set uku ne an wanke su sai hijabi daya da mayafi yellow, wata ledar sabuwa da alamun ita ta shigo da ita ta bude ta zuba kayan, takalmi na guda daya samfurin sukwal ta jawo shima ta saka min, sai dan kunne da sarka duk suma na sallah ta ne, ina kallon ta har tapp gama tana jan tsaki. "Tashi kije ki watsa ruwa maza." Mik'ewa nayi na amsa da toh na nufi bayin dake tsakar gidan mu, su Hanne na gani da su Karime sun cin kwalliya sun sa sababbin kayan su na sallah, kamar na tsaya yi musu magana sai kuma na fasa na shiga wankan. Mintuna kadan na fito na sake wucesu na shige ciki, da hannu Inno ta nuna min kayan dake ajiye a gefen tabarmar dakin. Dauka nayi na saka na koma na zauna ina tunanin inda zamu ake ta wannan shirin. Fita tayi ta barni a nan, ina ta jiyo hayaniyar yaran gidan sama sama, da gudu naji karime ta shigo gidan tana kiran Inno "Ga motar chan tazo Inno." "Naji me bakin aku." Ta katse ta tana hararar ta, mamaki ne ya kamani, yau Inno ce ke cewa karime me bakin aku, lallai ba karamin bacin rai take ciki ba. Shigowar ta dakin ne yasa nayi saurin kallon ta "Tashi maza ku kama hanya, saura inji ko in gani, ba dadewa zakiyi ba zaki dawo." Da sauri nace "Ina zani Inna?" "Ban sani ba, tashi nace ki wuce suna jiran ki." Tashi nayi jiki a sanyaye na fito tsakar gidan, Yalwati da Babar su Hanne na gani a tsaye duk sun sha lullubi, kamoni sukayi muka nufi kofar fita daga gidan. Motar dake ajiye a waje aka bude mana muka shiga, sai a lokacin naga Hanne da Karime a gaba, ajiyar zuciya nayi na ɗan ji sauki tun da bani kadai bace. Ina ji aka tashi motar muka dau hanya. Wannan tafiyar tana daya daga cikin shafukan rayuwa ta da bazan taba mantawa ba. Rano 😍  ©®HafsatRano *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo                       (7) ***Tafiya kadan mukayi muka isa gidan, da mamaki nake kallon gidan, gidan da nake da muradin zuwa a koyaushe, murna na hau yi Yalwati tayi saurin hararata, da sauri na nutsu, aka bude mana bayan motar ta gama daidaita a harabar gidan da nake wa kallon aljannar duniya. Tsallen murna su Karime suka hau yi Yalwati ta daka musu tsawa, sum sum sum suka dawo bayan ta suka makale, kofar dake kallon mu wanda ya kawo mu ya nuna mana. "Bismillah hajiyan na ciki ai." Sake riƙe ni gam sukayi muka nufi kofar, kafin mu karasa aka budo kofar aka fito, matar nan ce ta asibiti, da fara'a ta tarbemu,tayi mana iso cikin falon, wani irin azababben sanyi me hade da sanyayyen kamshi ya kaiwa kofofin hancin mu ziyara, ina kallon Babar su Hanne na sake bude kofofin hancin ta sosai tana shaƙar iskar da tayi mana maraba, duk muka rabe a kasa nida su Karime, aka shiga gaisawa cikin mutuntawa. Nidai ina ta son kallon ko ina a falon amma babu dama saboda yadda Yalwati ke kara rufa min fuskata, bansan dalilin da yasa take min hakan ba, bayan na ga su Karime da Hanne an bar su suna ta shan kallon su. Ina ta hasashen ina ma nice na more kallon nan. Chan na kurawa katotuwar talabijin din dake girke a bango ido ta cikin mayafin duk da ba wani sosai nake gani ba, wasu mutum biyu babba da yar matashiya suka shigo dauke da manya manyan farantai, ina kallo suka dire gaban mu aka sake gaisawa sannan suka juya suka fice. "Bismillah ga abinci." Matar ta fada tana nuna wa su Yalwati kwanukan da aka jere a gaban mu, wanda tuni kamshin ya fara sawa na manta yanayin dana baro, ina ji na kamar babu sauran damuwa ko takura a cikin rayuwa ta. Kamar su Yalwati ba zasu ci abincin nan ba, ina ta addu'a har sai dana ji matar ta sake musu magana, sannan suka sauko kowa ta hau diba dan dama nasan kawai kara sukayi wanda ni sam ban san su da ita ba. "Amal!" Ta bud'e muryar ta tana kwala mata kira, da sauri ta shigo, turus tayi ganin baki taki karasowa "Ƙaraso mana kika tsaya." Shigowa tayi tana sake kallon mu. "Ga kawar ki nan rike ta ku shiga ciki." Hannu na ta kama, muka bar falon, mayafin na cire muna yin gaba, kallo na tayi tace "Laaaaa Aminatu." "Na'am." Nace mata ina murmushi "Yaushe kika zo?" "Yanzu muka zo, nan ne gidan ku ashe." Daga min kai tayi "Zo muje kiga daki na." Da sauri na bita, muka shiga dakin nata, dan karamin gado sai single wardrobe da toilet, kan gadon muka fada muka saki dariya a tare. "Dakin ki mai kyau." Nace ina kallon ko ina, a raina ina raya dama nawa ne. "Thanks." Ta amsa tana murmushi "Bari na kawo miki chocolate din da Ya Farouk ya siya min." Ta fita da sauri, tashi nayi na bude kofar toilet din, tsayawa nayi ina kallon mamaki, bansan ina ne nan ba, na dai ga alamun akwai ruwa a ciki. Rufewa nayi na koma gadon na hau, na mike kafata ina murmushi. A raina na shiga raya dama daki na ne dana more. Dakin Farouk ta nufa tana kwala masa kira, yana zaune da waya a hannun sa suna magana da Ja'afar ta shiga, kallon ta yayi ya mata alamar tayi masa shiru, tura bakin ta tayi ta nufi in da ta bar kayan chocolate din nata ta dauka, har zata fita sai kuma ta dawo ta tsaya a gaban sa tana dariya "Kawata Aminatu ce tazo, tana dakina." A dan rikice ya kalle ta "Ina zuwa zan kira ka." "Me kika ce? Su waye suka zo?" Ya fada yana mik'ewa "Kawata Aminatu." Da sauri ya dafa kansa, da gaske kenan anyi aure, wani irin yar yaji tun daga kansa har tafin kafarsa, tunanin kalmar auren kadai na sa shi a wani yanayi. Ashe da gaske Daddy yak masa, kwata-kwata yarinyar nawa take, da har za'a yi mata aure. Gaban mirror ɗin dakin ya isa yana kallon kansa. He's to young for that, idan be manta ba next month zai cika 22years chif. "Ya Salam." Ya furta yana fadawa gadon "Me nayi wa rayuwa ta ne? Na daure kaina da kaina, yanzu idan Mummy ta samu labari ya zanyi?" Da sauri ya tashi, farar singlet ce kawai a jikin sa, sai dogon wando, ciwukan jikin sa na nan musamman na fuskar sa, dakin Amal din ya nufa da dan saurin sa, ya bude kofar da karfi. Suna zaune sun baje a saman gadon suna kwasar chocolate. Tsaye yayi yana kare musu kallo, da sauri yaga ta rufe idon ta ta sauke kafarta kasan gadon, kallon kansa yayi ya sake kallon dakin "Menene?" Amal ta tambaya tana kallon na. "Tashi ki rakani wajen su Hanne, kar naje ana jirana zamu tafi." "Kai dan Allah, ki kwana mana." Make kafada nayi, takowa ya shiga yi har ya ƙaraso gaban gadon, ya sa hannu ya rike ni, zaro ido nayi ina kallon sa, sai kuma nayi saurin rufe ido na "Tsoro na kike ji?" Ya fada yana kallon saman fuskata Da sauri na daga kaina, dariya Amal ta kwashe da ita har da tafa hannu "Tsoron Ya Farouk kike ji, ai baya suka fa." Bata fuskar sa naga yayi ya saki hannu na, be ce komai ba ya juya ya bar dakin. Ajiyar zuciya na sauke ina kallon Amal din "Ni dai muje ki rakani." Tashi taga nayi yasa ta mike itama ba tare da taso ba muka fito wajen Dada. Babu kowa sai ita kadai, kallon ko ina na hau yi da sauri alamun neman abu. "Kuzo nan yarana, Aminatu me kike nema naga kina ta kalle kalle.?" Ta fada cikin son ta yi min wayo "Ina su Hanne?" Nayi narairai da fuska kamar zanyi kuka. "Kinga ke anan zaki zauna ke da kawarki, kuyi wasa tare, kuyi komai tare har karatu zan sa ana koya muku, idan kika kwana da yawa sai ki koma gida." "Har karatu ma zamu dinga yi, kuma ba zanyi girkin shinkafa da wake ba ko??" Na tambaye ta ina kallon ta. "Girki! A ah banda girki, ai kunyi kankanta sai an kwana biyu, sai share dakin ku kawai da wanke toilet, sai kuma sallah." Washe baki na nayi, cike da murna na ce "Ni ba sai an maida ni gidan mu ba ma, ki barni ana kawai." Dariya suka sa gaba dayan su, nima na bisu mukayi ba tare da na gane dalilin dariyar ba. Abincin dazu aka zuba mana, muka hau ci muna kallo, tuni na manta da komai, muna gamawa Dada ta dauko magani ta bani na sha, sannan tace muje muyi sallah, bazan tuna rabon da Inno ta sakamu sallah ba, babu ruwan ta da munyi ko bamuyi ba, muna idar da sallar muka dora kallon mu, ranar gaba daya ji nayi kamar nafi kowa farin ciki a duniya. Sai gaf da magriba sannan muka koma dakin Amal da a yanzu ake masa lakabi da dakin mu. **** Gidaje biyu ne manya manyan gaske wanda suka cinye kafatanin layin tun daga gaba har baya, iri daya ne sai dai daya yafi daya girma da komai. Da dukkan alamu mamallaka gidan akwai alaka me karfin gaske a tsakanin su, ko ta yan uwan taka ko ta abota. Gidan farko da yake dauke da tafkeken gate me matukar tsawo da fadi aka yi saurin wangalewa sakamakon karar horn, da sauri mutane biyun dake zaune akan dan bencin zaman maigadin gidan suka tashi suka nufi wajen motar. Babban mutum ne dogon gaske, cikin shigar alfarma ya fito daga ciki, hannun sa dauke da wayar sa yana amsawa, yadda yake magana kadai zaka gane yadda arziki ya samu babban matsuguni a wajen, rike yake da murfin motar har ya gama wayar kafin ya maida duban sa bakin yana murmushi "Sannun da zuwa Alhaji." Suka ambata a tare cike da girmamawa. Amsawa yayi yana duban chan hanyar gate din. "Wai tun da mukayi waya kuke zaune kenan, sannun ku da zuwa, Bismillah." Gaba yayi suka bi bayan sa har kofar da zata sadaka da babban  falon gidan, daya daga ciki ne yayi saurin bude masa, godiya yayi sannan ya shiga da sallama, babu kowa a falon nasa, sai sautin  suratul bagra dake tashi daga cikin jerin speakers din da suka karawa falon kawa. "Bismillah, Ina zuwa." Wuce su yayi ya haura corridor din da zai maidaka part din matar gidan. Yana shiga yaron dake kwance akan sofa yana kallo ya taso da sauri "Daddy!" Ya rungume shi, "Kamal, kana nan kana sana'ar taka ta kallo ko, yau babu islamiyya ne." "Malam ne yace yau ba zai zo ba zai je garin su." "Ah lallai, yau ranar hutawa ce." Kallon ko ina yayi kafin ya sake shi yana cewa "Ina Mamyn taka ne? Naji gidan tsit." "Tana daki, wai kanta ne yake ciwo na dame ta da surutu shine ta koroni." "Toh zauna na dubo ta, kai ɗin ne watarana akwai zuba kamar..." Buga kafa ya fara yi irin ta shawagabbun yara, dariya kawai yayi ya nufi dakin gimbiyar tasa. Tana kwance ta juya bayan ta ya shiga, yadda yaga yanayin kwanciyar ta ta yasa ya gane da gaske kan nata ke ciwo, dan dama gwanar ciwon kance, fasa tada ta yayi ya juya ya koma wajen bakin sa. Sun jima suna tattaunawa kafin su tafi, daga nan ya bada umarnin kar a bar kowa kuma ranar yana so ya huta sosai. Watsa ruwa ya fara yi, yaci abincin da ke jere a saman dining din part din nasa, sannan ya nufi bangaren Hajiyar sa. *** Gaba daya ran Inno a jagule yake, ta rasa yadda zata bullo wa al'amarin, gaba daya ji take dama bata amince da bukatar su ba, da tuni zuciyar ta na nutse bata da wani tashin hankali. Babban matsalar ta ma zuwa da tayi wajen Harira da ta tambaye ta labarin yaron ta, yadda ya amsa mata ya nuna cewa bata san komai akan halin da yake ciki ba. Tun bayan abinda ya faru da Aminatu, kullum bata samun isasshen bacci, bare yanzu da ta koma wani gidan sai take ganin kamar babu ita babu cikar burin ta. Duk da sunyi alkawari da Harira akan haka sai dai bata jin zata samu nutsuwa kenan har idan ba dawowa din tayi ba. Ita da zai yiwu ma da sun hakura da komai ta maida ta wajen iyayen ta, hankalin ta ya kara tashi ne saboda samun ainihin labarin waye iyayen ta, kuma dadin dadawa babu hannun mahaifiyarta ko mahaifinta a bin da ya faru, Harira ta rufe ta, ba ta sanar da ita duk wannan ba, yanzu idan suka ki yarda suka hada su dukka suka kulle su fa, bata tunanin duk duniya akwai wanda zai iya fito dasu. Haka zasu kare rayuwar su a ba wan ba kanin. Ita kam abubuwan sun mata yawa. *** *Sati Daya* Wasanmu kawai muke nida Amal, bamu da wata damuwa ko kadan, ina matukar jin dadin zaman gidan. Wajen yanayin jikina kuwa sosai magungunan da nake sha suka taimaka min wajen samun lafiya ta. Har na murmure abu na, kaya kuwa na Amal nake sawa kafin nima a karo min nawa kamar yadda Dada tace. Muna zaune a falon Amal na karanta mana wani story book duk da ba gane wa nake ba, idan ta karanta sai ta fassara min da hausa. Sosai hakan ke min dadi. Shigowa yayi fuskar sa babu walwala kamar ko yaushe ya wuce, duk ya rame yayi baki, ina ji dai ranar Dada na masa fadan ya saukaka wa kansa, damuwa babu inda zata kai shi, duk da hakan be chanja ba. Kullum yana aikin waya, a rana sai ya kira Daddy sau nawa ba tare da ya kosa ba duk da hakan baya dagawa, daga karshe ma sai ya sashi a blacklist. Har ya gifta mu sai kuma ya dawo da baya ya tsaya a gaban mu. Duk muka kalle shi a lokaci guda dan ba kasafai yake shiga harkar mu ba. "Me kuke yi?" Ya tambaya yana zaman a hannun kujerar ta gefen da nake. Mika masa littafin Amal tayi tana matsowa "Story book muke karantawa." "Kuna son mu fara lesson?" Da sauri muka amsa, murmushi yayi ya mika mana littafin "Shikenan anjima zamu fara idan nayi bacci na tashi." Murna muka hau yi ya wuce ya bar mu yana girgiza kai. Bayan wani lokaci sai gashi ya fito cikin shigar kananan kaya, yanzun ma wayar ce a kunnen sa suna magana da wani, zama yayi yana wayar yana kallon in da muke, har ya gama be dauke idon sa daga kanmu ba, tashi yayi ya wuce dakin Dadah, yau duk wunin ranar a daki tayi saboda ciwon kafarta da ya matsa mata,daga mu sai masu aiki sai yanzu da Ya Farouk ya dawo. Jim kadan sai gashi ya fito dauke da mukullin mota yana jujjuya shi. "Kuzo muje ku rakani." Yace yana yin hanyar fita, da gudu muka yi daki, muka sako takalmi muka fito, yana tsaye jikin motar suna magana da driver, muna fitowa ya bude mana baya muka shiga shi kuma ya zauna a gefen me zaman banza driver ya data motar muka fita daga gidan. Tunda nazo yau ce rana ta farko dana fita, murna sosai nake ina jin kamar muyi ta dawwama a irin yanayin da muke ciki a yanzu, kadan kadan nake tunawa da yan gidan mu shima ba ko yaushe ba, yawanci nafi tunawa dasu idan Amal tayi bacci ta barni. Bani da sauran matsala komai muke so mukeyi, sai nake jin kamar nafi kowa sa'a a duniya.   Fita daga kauyen namu mukayi baki daya muka shiga cikin gari, a bakin wani babban shago muka tsaya,ya Farouk ne kaɗai ya fita ya bar mu a motar, chan ya dawo da kaya ya zuba a booth sannan muka nufi wani shagon, haka mukayi ta yawo daga nan zuwa nan wani wajen ya shiga damu wani ya bar mu a mota. Bamu muka dawo ba sai yamma likis cike da gajiya dan Amal tun a hanya tayi bacci ta barni. ****Tun daga ranar muka fara karatu da Ya Farouk, kullum da abinda zamuyi, chan baya muke tafiya mu saka babar darduma mu baje sai mun gaji sosai yake kyale mu musamman ma ni, dan mafi ya yawan lokuta ni yake wa karatun dan ita Amal ta wuce wajen.   Muna cikin wannan yanayin Daddy ya turo aka tafi da Amal, ranar nayi kuka sosai nace lallai sai an maida ni gidan mu, da kyar shi da Dada suka shawo kaina na hakura na zauna, amma bani da wani kuzari tun bayan tafiyar ta ta wadda Dada tace min sun koma makaranta ne kuma ba nan kusa bane. Haka dai na hakura na cigaba da daukar karatu da yanzu yafi min komai a rayuwata. Wata na hudu cif a gidan, sau biyu su Karime suka zo ita da yan gidan mu suka wuni, suka tafi, anan ne suke fada min ai aure akayi min shiyasa nake zaune anan, kuma Inno ce take hanasu zuwa shiyasa. Ban dauki zancen nasu da muhimmanci ba, haka na tattara na cigaba da sabgata saboda ba karamin sabo nayi da Ya Farouk ba, gashi kusan kullum sai ya kira min Amal da daddare munyi waya.    Ranar da bazan taba mantawa da ita ba, nayi bacci na tashi kenan, dakin ya Farouk na nufa da sauri na ina tunanin ko ya zo tashi na ya ga ina bacci ya gudu bayan yayi min alkawarin yau zai kaini gidan mu har na wuni, kwana yace zanyi na fafure nace sai dai yini, yayi ta min dariya yana tsokana ta, ban damu ba,dan zama na anan ɗin yafi min dadi musamman ma saboda karatun da nake yi.   Tura dakin nayi na shiga bayan na kwakwasa ya bani izini, Yana lullube a bargo ya rufa har kansa, kiran sunan sa na fara yi ina k'arasa ciki. Cikin muryar bacci ya amsa min, dariya nayi na haye kan gadon ina jan bargon dan nasan ba bacci yake ba, mafiya yawan lokuta ya saba yi min hakan. Rike bargon yayi yana ja ina ja har na samu na bude masa fuskar sa. "Laaa bacci karya fa kake ya Farouk." Nace ina dariya, bude idon sa yayi cikin yanayin bacci ya zuba su a kaina "Bacci nake fahhh..." Ya fada cikin wata irin murya kamar ba tasan ba, jan bargon yayi ya sake rufawa nayi saurin janye wa ina sake yin dariya "Ni dai ka tashi, ba kaine kace zaka kaini gida yau ba." "AMINATU pleaseeeeee..., bacci anjima zan kaiki." 'Dage kafada nayi na sake janye bargon ina bubbuga masa damtsen hannun sa. Da wani irin karfi nayi ya riko ni, gaba daya na shige cikin jikin sa, ya jawo bargon ya rufa akanmu. A tsorace nake kallon sa, idon sa a kulle ya sake maidashi ya rufe, zura wa fuskar sa ido nayi kamar wadda ta fara ganin sa, na kasa kwakkwaran motsi, balle na yi yunkurin tashi. Takun tafiya naji yana tunkaro dakin, hade da karar abu kamar ana jan wani abu, janye bargon nayi daga saman fuskar mu na zuba wa kofar shigowa dakin ido tun da dama dana shigo ban rufe ta ba ina sauri. Cikin wata irin shiga ta alfarma, me cike da haiba tayi wa kofar dakin tsinke, tsaye take janye da yar karamar jakar matafiya, sai handbag din ta dake sakale a sangalalin hannun ta. Cikin mintuna da basu gaza biyar ba nayi mata kallon tsaf, yadda naga ta buda idon ta sosai akanmu ya ɗan tsorata ni, cikin tsananin mamaki naji ta kira sunan sa da d'an karfi. "Son!" A firgice ya dago idon sa ya sauka a kanta, yayi wani irin tashi da dukkan karfin sa har yana ture ni daga jikin sa, cikin sakin bakin ya furta "Mom!" DAURIN GORO😢😢😥😥😓 ZAFAFA BIYAR KAUNAR MU: MAMUH GEE ALKAWARIN ALLAH; HUGUMA GUDU DA WAIWAYE: BILLYN ABDUL DAURIN GORO:HAFSAT RANO. IGIYAR ZATO: MISS XOXO LITTAFI DAYA 200 BIYU 300 UKU 400 HUDU 450 BIYAR 500 *_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_* 2260792279 _MARYAM SANI_ _ZENITHBANK_ saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇 *07067124863* *_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇 *09032345899* _Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_©️®️HafsatRano *ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo                       (8) *** Kallon mu take babu ko dauke ido cikin wani yanayi, ranta a matukar bace, da sauri ya isa gaban ta yana mika hannu zuwa wajen jakar kayan ta "Welcome Ma. Ashe kina hanya." Kallon banza tayi masa, ta wuce shi ta shigo dakin, har in da nake, bina ta cigaba da yi da kallo tana tabe baki kafin tace "Yanzu akan wannan ka zabi ka katse rayuwar ka, ka hakura da komai ka anan, yaushe ka zama haka Farouk?" Ta fada tana buɗe idon ta sosai akan sa "Mummy Please, ki huta sai muyi magana." "Naki na huta ɗin, kana son ka kashe rayuwar ka abanza kana cemin ma huta, saboda kai kafi kowa tausayi a duniya ko? Abin da kuma nazo na tarar fa, ko shima tausayin ne? Kuna kwance tare amma a waya kana nuna min kai kawai kana son taimaka mata ne." "Ya Salam... Mummy bafa abinda kike tunani bane." "Toh mene?" Ya fada a harzuke Kallo na yayi ganin yadda nake ta binsu da ido kamar na samu tv yace "Jeki dakin ki Aminatu, anjima sai na kaiki gidan ko?" Zumburo baki nayi cikin jin haushi na tashi na bar dakin, sakin baki tayi tana dubanshi. "Farouk!" "Mummy dan Allah, here me out, idan kika ji komai sai ki yanke min hukuncin da kika ga ya dace dani." "Farouk wanne abu kuma zanje bayan wanda ka fada min, Ja'afar ya fada min, akwai wani sauran point ne da ban ji ba?" "Ja'afar...?" Ya ambata cike da mamaki "Ban isa ya fada min ba ne ko me? Ina chan ni sam hankali na ya kasa kwanciya kai kana nan kana baccin ka da yar yarinya karama, toh wallahi an gama, munafukar kakar taku sai tazo ta warware wannan kullin da tayi, ko da bana gidan naku amma ido na na kan duk wani motsin ku, kuma wannan karon bazan yarda ba wallahi." Dafe kansa yayi ya juya mata baya da sauri, matsalar mahaifiyar su kenan, ya rasa dalilin da yasa a komai take blaming Dadah, bayan babu wani abu da tayi mata, shi yasa yayi ta iya kokarin sa na ganin ya kwantar mata da hankali amma sai da Ja'afar ya kai mata gulmar,  yana jin ta tana sababi kafin ta nemi waje daya ta ajiye kayan ta tana zaman gefen gadon. Dakin ya bari ya nufi wajen Dadah dan sanar mata kar sai ta fito su hadu, tana zaune akan babbar darduma da alama ta gama sallar walaha kenan, tana dan bitar karatun Alkur'ani, gefen ta ya zauna har ta kai aya ta rufe ta juyo tana murmushi "Babana an tashi kenan." "Uhum." Yace yana tankwashe kafarsa "Dama Mummy ce tazo." Ya fadi maganar kamar wanda baya so, shiru Dadan tayi cikin nazari, tabbas tasan zuwan nata ba zai zame musu Alkhairi su dukka ba, sai dai abu daya ta take tsoro shine yadda zata dauki maganar Aminatu, tasan ta sarai mace ce wadda take da son kanta, ba lallai ta fuskanci maganar ba, shiyasa take ta kokarin ganin Daddy yasauko ya bar su sun tafi baki daya, idan yaso Farouk sai ya koma makarantar sa ita kuma a sata a ko tasu Amal ce, sai dai hujjar daya bata na cewa wa'adin daya deba wa Farouk din be cika ba yasa ta hakura, sai dai zuwan mahaifiyar shi a yanzu yasa ta ɗan ji tsoron abinda zai je ya dawo. Duk da haka ba zata shiga hurumin da bana ta ba, d'anta ne   tafi kowa sanin ciwon sa. "Ah sannun ta da zuwa, yaushe ta zo?" "Yanzu." Ya amsa yana kallon yanayin ta "Madallah, sannun ta da zuwa." "Uhum." Kawai yace ya tashi "Dan Allah Dadah... Kinsan halin Mummy, karki bari tayi abinda ba dai-dai ba dan Allah." Kallon sa tayi ba tare da tace komai ba har ya juya ya bar dakin, tashi tayi ta koma saman gadon ta tana tunanin yadda abubuwan zasu zama. *** Kwanciya na koma nayi ina jin haushin katse min zuwa gida da matar tayi, ido na a lumshe kamar ina bacci aka turo kofar dakin, da sauri na bude ina kallon kofar, yana tsaye ya rike hannun kofar yana kallon ciki, tashi nayi zaune ina saukowa da kafata kasa "Ya Farouk wacece datazo?" "Mamana ce." Ya amsa min yana sakin kofar, ciki ya shigo ya zauna gefen gadon yana matso dani kusa dashi ssosai. "Kina son ta ko?" Ya tambaye ni yana kallon fuska ta, da sauri na girgiza masa kai alamun a'ah, ware idon sa yayi gaba daya akaina. "Are you serious! Mamana ce fa." "Eh ni bana son ta." Na faɗa cike da yarinta Da sauri ya rufe baki yana harara ta "Kar na sake ji kin fada, kice kina son ta." "Ni toh ba masifa take maka ba, ni bana son ta, ni kai kadai nake so sai Amal,sai yan gidan mu." Murmushi naga yayi, ya rike hannu na cikin nasa ya murza a hankali "Ni kina so na ko?" Ya tambaye ni "Eh mana, kana da kirki ai." "Toh idan kina son na, kiso mummy ma kinji." A cunkushe na amsa da toh "That's my girl." Yace yana mik'ewa. A nutse ya juya ya bar dakin ina kallon sa har ya gama ficewa. ***Waya ce a rike a hannun ta sanda ya shiga, yanayin da take magana ya gane akan sa take wayar, kai tsaye wajen kayan sa ya nufa ya tattara abubuwan da zai bukata ya kai chan dakin su Ja'afar ya zuba sannan ya shiga Kitchen yasa masu aikin gidan suka bashi breakfast ya kai mata dan yasan bata karya ba. Ko da ya koma ta gama wayar tana dan dube dube a cikin iPad. "Mummy gashi nasan baki yi breakfast ba, in Kika gama sai kije ku gaisa da Dadah pls tasan kinzo." Tabe baki tayi ta ja tray din gaban ta ta bude, juyawa zaiyi ta dakatar dashi "Ka daina gudu dole muyi magana kaji da abinda nazo, ba zama nazo yi ba ina da abubuwan yi da yawa." "Watsa ruwa zanyi sai nazo muyi maganar, kiyi hakuri." "Yayi, ina jiran ka." "Ok." Yace ya nufi dakin Aminatu, budewa yayi ya ganta tana kokarin zuge zib ɗin doguwar rigar dake jikin ta, karasawa yayi ya taymaka mata ta cire sannan yace tayi wanka ya kaita, da gudu tayi toilet shi kuma ya nufi dakin su Ja'afar da ya zama nasa a yanzu. A gurguje ya shirya ya fito dan baya so taje neman sa dakin sa, baya so sam su hadu ita da Mummy su biyu ba tare da shi din a tsakani ba. Aikuwa a hanya sukayi kicibis ta tafi dakin nasa, riko hannun ta suka juya zuwa hanyar fita murnar ta take tsayawa. Babu driver da alama Dada ta aike shi, sai driver mummy shi kuma baya so ya nuna masa gidan dan be san abinda mummyn zata iya aikatawa ba. Kawai sai ya yanke shawarar su tafi a kafa tun da babu nisa. Fita sukayi a kafa hannun sa sakale cikin nata, tana tayi masa hira duk yawanci akan wayar su da Amal ne, sama sama yake sauren ta, hankalin sa ya tafi akan yadda zai ɓullo wa Mummy. Sun kusa isa gidan suka yi kicibis da Garbati da Ilu, da mamaki suke duban su, sam Garbati be yi tunanin abin a iya nan zai tsaya ba, wani haushi ne ya taso masa, yayi saurin shan gabansu, da sauri ta koma bayan Farouk din tana buya. "Me hakan?" Farouk ya fada bayan ya haɗa girar sama data kasa. "Babu komai, kawai dai ajiya ta ta wajen ka nake dubawa, naga alama kuma dai babu wata matsala." Haushi ne ya kama Farouk, sai dai ba zai biye masa ba, dan yaga alama sam Garbatin baya cikin jerin mutane masu ƙwaƙwalwa, hannun ta ya damke sosai suka raba ta gefen su suka wuce kawai ba tare da yace komai ba. Haushi sosai ya kama Garbati, yaji kamar ya jawo shi ya ta bugun sa ko zai huce, haka yayi ta zage zage Ilu na bashi baki suka wuce in da zasu. A kofar gida ya tsaya ta shiga ciki ya tabbatar ta shiga sannan ya juya ya bar wajen. *** A tsaye na tarar da Inno wajen in da take kiwon ta, tana gani na ta saka min ido cike da mamaki, da sauri nayi wajen ta ina murnar ganin ta, murmushi ta k'ak'alo wanda ya zauna iya saman fuskar ta, ta ajiye abinda take "Ke kuma daga ina?" Ta tambaya tana yin gaba, bin bayan ya nayi lokacin su Karime suka ganni, ihu muka hau yi muka dane juna. Nan da nan aka fara shigowa daga cikin gidan namu zuwa gani na, hakan ya bata ran Inno ta kwala mana kira ni da Karime muka shiga dakin ta, waje ta nuna mana da hannun ta sannan ta fice ta bar mu a dakin bayan ta ja mana kunne akan karmu sake fitowa sai ta kiramu. Hakan da tayi ya rage masu shigowar dan sun sane abinda take nufi, hirar mu muka baje irin ta yarinta nida Karime ina ta bata labarin gidan Bature, murna take tana jin dama ita ce. Chan da azahar Inno ta kira Karime ta kawo mana dambu da wake, rabon dana ci irin abincin gidanmu an jima, ai kowa na saki ciki naci sosai harda k'ari, nasha ruwa nabi lafiyar katifar Inno na baje abina cikin jin dadi. **** Tun da ya koma gidan yaki yarda sam su hadu da Mummy, rufe kansa yayi a daki ya cigaba da aikin da yake na neman admission din sa tun wajen sati biyu da ya wuce, be samu gama wa shi yasa yau ya dage ya gama. Baya so ya kara bata wani zangon karatun a banza kamar yadda yayi wannan karon, shiyasa ya yanke shawarar chanja akalar karatun nasa zuwa abinda yake da tabbacin zai taimaka masa matuka wajen hukunta mutane irin Garbati. Knocking din dayaji a kofa yasa gaban sa ya fadi, kin magana yayi aka cigaba da knocking din, ya zata zata hakura ta tafi, ganin da gaske take yasa ya kashe komai ya mayar waje daya, ya nufi kofar cikin tafiya irin ta masu bacci. Budewa yayi tana tsaye ta harde hannun ta. Kallon da tayi masa ne yasa cikin sa murdawa, takardar hannun ta ta ware ta wurga masa. "Tun da kaki yarda muyi magana, sai ka duba wannan, kuma dole cikin biyu kayi daya, idan kuma ba haka ba, abinda da biyo baya ba zai maka dadi ba, dan na lura sam baka da hankali baka san ciwon kanka ba." "Mummy..." Juyawa tayi ta bar wajen bata ko sake kallon sa ba. Kasa ya tsugunna ya dau takardar hannun sa na rawa, layi cikin layi ya fara bin rubutun, gaban sa yayi wani mummunan faduwa, a take ya juya da mugun gudu ya nufi dakin da take, yana zuwa tana rufe kofar, bugawa ya hau yi yana kiran sunan ta da sauri "Mummy dan Allah karki fara, dan Allah Mummy, nasan me nake da hankali na wallahi, zanyi ko menene kika ce amma dan Allah karki min haka." Babu alamun zata saurare shi, zamewa yayi a wajen ya zauna kansa na juya masa. Manage 🙏😥©®HafsatRano *ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo                       (9) ***Fitowar ta kenan zata dan taka kafarta ta hange shi a durkushe a kofar dakin sa, da dan saurin ta ta k'arasa "Babana?" Dagowa yayi idon sa sun kada sunyi ja ya kalle ta "Tashi muje daki na." Ta fada tana mika masa hannu, mik'ewa yayi cikin sanyi jiki yabi bayan ta, Mummy na jinsu ta tabe baki, babu wanda ya isa ya sata ta sauya ra'ayin ta akan abinda ta haifa, ba zata bari tana kallo a lalata masa rayuwa ba dan shi yafi kowa sauƙin kai. Suna isa dakin ya zame ya zauna kasan carpet din dakin yana jin zuciyar sa na tafasa. "Menene matsalar?" Ta saka masa ido, tana kallon yadda kirjin sa ke kaiwa da komowa. Shiru yayi ba tare da yayi magana ba ya mika mata takardar Mummy. Murmushi kawai tayi bayan ta gama karantawa ta mika masa, tasan zata aikata fiye da abinda tace ɗin, dan bata shakka ko kokonton hakan, sai dai babu yadda ta iya, musamman da babu wata alaƙa yanzu dake tsakaninsu da ita sai ta ya'ya, amma tana jan girman ta, bata so kuma wani abu ya shiga tsakanin shi da mahaifiyar sa. "Kayi mata abin da take so kawai Babana, shine zaman lafiyar kowa." "Dadah....?" "Shine maslaha, abu ne me sauki, kuma tabbas kayi kokari ma ladan ka yana wajen wanda kayi domin sa." Matsawa yayi jikin kafarta ya dora kansa a saman, zuciyar sa tayi rauni sosai, ba ya jin zai iya aikata abinda Mummyn tace, ya kuma rasa dalilin sa na son kin amincewa bukatar ta. Shafa kansa ta shiga yi tana ayyana yadda komai yake tafiya. "Babana..." Ta sake kiran sunan sa "Kana son Aminatu ko.?" Da sauri ya dago kansa jin tambayar a bazata, abinda yake ta kokawa da zuciyar sa kenan, ya rasa dalilin da yasa yake jin yarinyar har cikin ransa, komai nata yana jin kamar an haɗe shi da rayuwar sa ne, yanzu da Mummy ta kawo zancen rabuwa sai yaji kamar zare wani abu me muhimmanci ne a cikin rayuwar sa. Be san me haka yake nufi ba, sai dai yana daukar ta a matsayin wata babbar ƙaddarar sa. "Kana son ta ko?" Ta sake maimaitawa "Nima ban sani ba Dadah, kawai ina jin tausayin ta ne, She's too young for that, sannan na mata plan na good future,." "Shikenan, Ina da shawara, amma dole sai da taimakon mahaifiyar ta, kaga ni yanzu mahaifin ku ya matsa lallai sai na tafi saboda ciwon kafar nan tawa daya matsa min, da babu irin taimakon da ba zan baka ba, toh mahaifiyar ta ita kadai ce zata taimaka mana, wajen ganin mun samu abinda muke so." "Ta yaya kenan Dadah?" "Ka kai ta boarding school, ka damka amanar ta wajen mahaifiyar ta, ka sanar mata da kudurin ka nason ganin ta zama wani abu,nasan babu mahaifiyar da zata ki cigaban yar ta, kai kuma kaga sai ka dawo kayi wa mahaifiyar ka biyayya, kayi karatun ka, ka kara mallakar hankalin kanka, lokacin babu wanda zai fada maka yadda zaka yi da rayuwar ka, a lokacin sai ka dawo, ka cika burin ka." Da sauri ya tashi ya rungume Dadah, "Shisa nake sonki Granny, wallahi you are the best." "Ja'iri." Tace tana kai masa duka "Allah kuwa, gashi kin kawo solution cikin sauki, idan Daddy yaji labari sai nace masa makaranta na maida ita nima zan koma tawa, kinga ba zai ce komai ba." Daga masa kai tayi tana murmushi. Tashi yayi da karfi da kuzarin sa ba kamar dazun da ya shigo ba. "Bari naje na sanar wa Mummy na amince da komai data ce, sai na fara shiri." Ya fada cike da farin ciki. Fita yayi da sauri, a kofar dakin sukayi kicibis, basarwa tayi kamar bata gama jin komai ba tayi gaba ya bi bayan ta. Zama tai kawai ya shiga tsara mata zance. "Mom na amince da bukatar ki, amma dan Allah karki yi mata komai, bata da laifin komai bata san komai ba, idan ma hukuncin ne ni zakiyi wa, amma yanzu zan rabu da ita, zan biki mu tafin idan hakan zai saki farin ciki." Murmushi ta k'ak'alo wanda ya tsaya a iya saman fuskar ta tace "Madallah da kai, ka kyautawa kanka, ka kyauta mata, sai ka fara shirin tafiya dan bazan tsaya bata lokaci ba." "Kiyi gaba dan Allah, zan biyo bayan ki wallahi nayi Alk'awari, ki bari na dan karasa wani abu dana fara, ba zan dau lokaci ba." Dan jim tayi tana tunanin amince wa, kamar tace a'ah sai kuma tayi wani tunani. "Shikenan ni zan koma gobe, saura kaki abinda nace, kasan dai sauran ba sai na fada ba." "In Sha Allah hakan ma ba zata faru ba." "Jeka toh zan dan kwanta." Fita yayi ya ja mata dakin, ya wuce dakin Aminatu, budewa yayi ya haye saman gadon nata yana lumshe ido, tunanin yadda komai ya fara ya shiga yi, daga san da ya fita daga gidan zuwa yanzu da yake shirin daukar wani babban tsani a rayuwar su. Yadda komai ya zama kamar a film haka ya dinga bin komai daki-daki. Murmushi yayi ya mirgina gefe yana sake duban komai daya zama mamallakin ta a dakin sai yan abubuwan Amal. "My Destiny." Ya furta a hankali kamar me rada. Eh dole ya kira ta da Destiny dan shine kadai sunan da yake ganin ya dace da ita, ƙaddarar sa ce, wadda a yanzu yake jin babu wani abu da zai iya raba shi da wannan ƙaddarar. Haka ya jima a dakin har gabanin magriba kafin ya mike a kasalance ya fada toilet din dake manne a dakin. Alwala yayi ya fito ya tsaya gaban mirror yana kallon fuskar sa. "A yau shafin rayuwar mu zai fara Aminatu, daga yau ba zan sake barin wani abun ki, ko cutarwa yazo kusa dake ba, nayi alkawarin zame miki babban tsanin cikar farin cikin ki ko da kuwa hakan na nufin... Ko da kuwa hakan yankewar nawa." A fili yayi maganar, sannan ya juya cike da karshashi ya bar dakin, sallah ya fara gabatarwa kafin ya nemi driver su tafi dauko ta. ***Ina zaune Inno na gefe tana ta aikin lissafin Kudi,yadda ta tsare ni a dakin gaba daya ya sa naji duk na gaji, tun Karime na tayani hira har itama ta gudu ta barni, gashi Inno ta kafa ta tsare ko ina, ina jin su suna wasa a tsakar gida kamar inyi ihu. Sai data gama ta tattare kan kudaden ta bude inda take ajiye wa tayi musu kyakkyawan boyo, har ta rufe sai kuma ta sake budewa da jawo wata jaka, bude cikin ta tayi ya dudduba sannan ta mayar ya rufe, ina kallon ta, ganin zata juyo yasa nayi saurin janye ido na, kallo na kuwa tayi tana juyawar. "Bacci kike?" Ta tambaya tana matsowa "Wasa nake son zuwa nayi nida su Karime dan Allah." "Ba zaki ba." Kawai tace tasa kai ta bar dakin, kuka na saka cike da jin haushi, duk sai naji dama ban zo ba, kallon tagar dakin nayi naga duhu ya fara zuwa alamun dare kenan, Ya Farouk be zo ya tafi dani ba, duk sai naji ina son tafiya. Addu'a na fara yi Allah yasa yazo. Jin shiru shiru yasa na kwanta lamo ina jin haushin kowa, da haka bacci ya fara fisgata. Sama sama naji Inno na taba ni. "Keeee...ke." Ta bubbuga min jiki na A gigice na tashi "Ya Farouk!" Na ambata ina mik'ewa, kallo na tayi kawai cike da mamaki. "Na'am." "Tashi maza ku wuce, kin hangame baki kina bacci ko tuwon baki ci ba." Da sauri na mike, na yayimi mayafi na na fito, a kan tabarmar gidan daidai kofar Baba na hange shi, kallo na yayi nayi saurin jan kafata zan karasa wajen, ji nayi an riko ni, Inno ce ta banka min harara, da sauri nayi kasa da kaina. "Ku wuce dare nayi." Tayi magana tana kallon bangaren su Baban. Tsam ya mike, yayi sallama da Baban sannan y fita, sai a sannan ta sakar min rankwashi a kai sannan tace su Karime su rakani. "Uwar rawar kai." Ta ambata tana jan tsaki. Daki ta fada cike da tunanin abin da zatayi. Ga maganar da yazo da ita wai makaranta zai sata ta kwana, kenan babu ranar da zai sake ta, bayan Harira ta karbi kudin ta tace ko wata biyu auren ba zai ba, sai gashi ana maganar wata biyar, idan tayi sake kuwa sai dai taji ana maganar suna. Dolen ta gobe ta koma taji in da aka kwana, ba zai yiwu ta zuba ido haka nan ba. ***Tun da muka fita bamu wuce gida ba, zakayi kawai muke tayi har bayan sallar isha'i, a mota suka barni suka yi sallah sannan ya je ya siyo mana tsire, sanda suka dawo har na fara bacci, tashi na yayi ya bani naman, ina ci na sake komawa na kwanta. Bansan yaushe muka koma gidan ba, ashe baya so mu hadu da Mummy ne shiyasa yayi ta jan komawar. Ban san me ya faru ba, nidai na farka naganni a dakin Dadah, tashi nayi na koma daki na na sake maida kai na cigaba da bacci na cikin kwanciyar hankali. Wajen bakwai da rabi na sake farkawa, sallah nayi na kwanta akan carpet din na cigaba da bacci. A hankali aka turo kofar, kallon gadon ya fara yi sannan ya hange ni a kasa. Banji takun tafiyar sa ba, kawai sai ji kayi an daga ni sama, dan karamin hijabin danayi sallah ya shiga kokarin cire min, na sake runtse ido na kamar me baccin gaske, ina ji a cire ya ajiye a gefe ya kwantar dani a gadon, ido na ne ya fara rawa alamun baccin karya ne. Murmushi yayi me sauti ya mintsine ni a hannu na "Wayyo." Na bude ido na ina kokarin yin kuka "Baccin karya ko?" "Na gaske ne fa, kaine ka tashe ni." "Umm amma idon ki yake ta rawa." Dariya nayi na tura baki gaba, kallo na naga ya tsaya yanayi sosai, babu ko giftawa, hannu nasa naja gashin idon sa cika da tsokana. "Ouch, kai kika min haka?" Ya tambaya yana taba idon nasa "Abu zan cire maka fah." "Karya ne." "Da gaske." Na saka dariya ina matsawa. Riko ni yayi ya dawo dani kusa dashi. "Kina son kiyi karatu ko?" Da sauri na daga masa kai na "Good... Zan saki a makaranta. Kina so?" "Ina so wallahi." Na faɗa cike da murna "Ok Tam, zan saki amma sai kinyi min alƙawarin zaki yi karatu sosai, sosai." "Zanyi Allah." "Good." "Toh yaushe zaka sani, kuma aina makarantar take." Shafa kansa yayi alamar tunani kafin yace "Yau zan fara zuwa neman makarantar, in Sha Allah zanyi kokarin ganin an samu, duk da ma anci term daya amma hakan zaki shiga ciki, sai kiyi kokari sosai ki kamo su." Murna na hau yi sosai kamar zanyi rawa, hannun sa ya rataye a saman kirjin sa yana kallo na, sauka nayi na jawo littafan da muke karatu dasu na fara jera su daya bayan daya. Be yi magana ba, sai murmushi kawai yake. Chan ya mike da sauri yana dafa kai, shaf yaso mantawa da tafiyar Mummy, abinda ma ya tashe shi da wurwuri kenan. Fita yayi yaja min kofar na cigaba da hada littafan cike da farin ciki. ***Har airport ya rakata, ba zatayi tafiyar mota ba wannan karon wai Lagos zata wuce akan wani kasuwancin ta, dole sai dai driver nata yabi bayan ta a mota ya koma gida, sanda suka isa ta kara jaddada masa alkawarin su, amsa mata yayi da toh da haka sukayi sallama. Be koma gidan ba, sai kawai ya bazama neman makarantar da zatayi daidai da Aminatun sa, makaranta yake so me kyau me tsada wadda zata taimaka mata kwarai wajen cikar burin ta, be damu da ko nawa za'a kashe ba, kudin da ya karba wajen Mummy da wanda yake dashi dana Daddy zasu ishe shi komai. Shi dai kawai ya samu ya tabbatar yayi wa dukkan su abinda suke so ba tare da ya fifita daya ba. Sai yamma sannan ya samu ya gama wasu abubuwan, duk da ba dukka ya gama ba amma yaci karfin komai, ya samu makarantar da tayi masa, har ma sun bashi damar ya kawo ta interview. A gajiye ya shiga gida, sallah kawai yayi yaci abinci ya sake shiryawa ya fita, gidan su ya wuce kai tsaye dan yana so su sake magana da mahaifiyar ta, a kafa ya taka a hankali kunnen sa sakale da earpiece suna magana da Ja'afar, har ya kusa karasawa gidan suna magana yana fada mishi yadda komai yake tafiya a gida. Daga nesa kadan yaga ta fito, cikin zulumi, kallo daya zakayi mata kasan ba a nutse take ba, da sauri ya kashe wayar yana kokarin tsaida ta yaga ta kara sauri, har zai juya sai kuma yayi tunanin ko babu lafiya, da sauri yabi bayan ta don tabbatar da babu wata matsala dan yanayin ta kawai ya nuna ba kalou ba. Tafiya take tayi  hakan kuma shima be fasa bin nata ba, kamar daga sama ta hango Harira tana nufo ta, ja tayi ta tsaya jikin wata bishiya har ta ƙaraso, ganin haka yasa yayi kokarin juyawa, sai dai kalmar da yaji yasa shi dakatawa yana kokarin ganin yaji komai "Wai Menene wannan kiran haka, kinga fa shiyasa kawai na yanke shawarar fitowa mu hadu a hanya dan yan gidan ma har sun fara zargin wani abu. " Hariran ta fada tana karasowa. "Maganar Aminatu ce kin sani ai, fisabilillah bayan kin min alƙawarin ko wata biyu ba za'a yi ba zai sauta ta dawo gida, shiru kake ji gashi ana maganar watanni biyar, kinsan me hakan zai haifar nan gaba." "Toh nidai bansan ina matsalar take ba, a gabanki na dauki kudin na bawa malam Tsalha da zauren gidan mu, ya tabbatar mana da ba za'a dau lokaci ba, toh ni bansan ina matsalar kuma take ba." "Ni duk ba wannan ba, yanzu gaba daya bani da kwanciyar hankali wallahi, ni idan zai yiwu kawai ki nemo Hajiyar nan, ayi magana, ta in da ake hawa ta nan ake sauka, na fasa wallahi gwara su karbi yar su." "Kamar ya? Abinda aka yi yarjejeniya, da zarar yaron nan ya kai matsayin da ake so ya kai din, sai ayi komai cikin sauki, amma yanzu daga farawa kice kin gaji, me ma akayi?" "Ba zaki gane ba, dalilin baki san yadda yaya suke a zuciyar iyayensu ba, ni kam gaskiya ba zan iya ba, nayi nadamar abinda kika sani na aikata, yanzu zuwa zakiyi ki bani addireshin su, na je na same su a warware komai, na maida musu da yar su, tun kafin ranar da nadama ta ba zatayi min amfani ba." Wani banzan kallo Harira tayi mata "Amma dai kamar ba a hayyacin ki kike ba ko? Kar ki manta su waye mutanen da kike cewa zaki je, kina tunanin zasu tsaya sauraren ki? Bayan haka ma wacce hujja kike da ita da zaki nuna musu?" "Jini ba karya bane Harira, wallahi suna ganin Aminatu ko ba'a fada ba zasu gane tasu ce, bayan haka kinsan dai ina da hoton mijin dana matar da muka dauka a saman file din asibitin su." Dariya Harira ta saka sosai hadda tafa hannu "Lallai Innaro, bansan ma kwata kwata tunanin ki baya ja ba sai yau, kinsan kuwa me kike shirin yi? Ina tabbatar miki da kina zuwa zasu kamaki su rufe ki, daga ke har zuri'ar ki kuwa babu wanda zai tsira." "Ki fuskance ni, akwai matsala ne idan aka cigaba a haka, wadda zamu shiga sai tafi ya yanzu wallahi, idan muka samu yaron nan ya tsinke igiyar auren, sai mu tattara mu mayar musu da yar su, in yaso ita matar data tsara komai sai su kare chan, nidai Buri na d'ana ya dawo, rashin sa ya fara tabani. Nayi nadamar komai wallahi." "Da kika gama kafa kanki da kudin da kika karba ba, ke fa wallahi san kanki yayi yawa, wato kinci moriyar ganga ko, toh bari kiji in fada miki gaskiyar magana, bansan in da suke ba, bansan aina za'a same su ba, rabona da su tun sanda muka rabu a asibiti, na yagi rabona, bayan wannan bansan komai akan su ba, ke wallahi ko sunan su ban sani ba, na sai tuna sanda Hajiyar take fada mana sunan da take so a sawa jaririyar, Aminatu MD. Daga wannan bansan komai akan su ba." Wani irin kukan kura Inno tayi ta  damki wuyan Harira, tuni kokawa ta rikice tsakanin su. Farouk dake tsaye a gefe yayi mutuwar tsaye tun sanda ya fara jin komai har zuwa sanda abubuwan suka dau zafi. Sosai maganar ta taɓa shi, wani irin mugun tausayin ta ya kara dirar masa fiye da wanda yake ji a baya, an cuci rayuwar ta, an raba ta da gatan ta, sai dai ya kasa gane dalilin daya sa suka aikata hakan, kenan babu sanin mahaifanta, toh wacece wannan data zabi rayuwar yarinyar ta lalace akan wani banzan burin ta mara tushe. Ya kasa gano hakan sai dai ya dau alwashin sai ya tabbatar da duk ya warware wannan daurin, ko da kuwa hakan na nufin.... Jin yadda suke abu kamar yara ne yasa shi magana cikin tsawa dan ba karamin bata masa rai sukayi ba. "Ku dakata!" A firgice suka juyo, wani irin bugawa kirjin Inno yayi, ta ɗora hannu a kanta kamar zata fasa ihu "Yanzu kune kuke kiran kanku matsayin iyaye? Masu tarbiyyar yayan su? Tir daku wallahi." "Faruku... Tsaya kaji, duk ba abinda kake tunani bane wallahi, yaudara ta akayi..." Katse ta yayi cikin tsananin bacin rai "Babu sauran girmamawa ko mutuntawa a tsakanin mu. A dah ina miki kallon uwa ne, wadda tasan ciwon kanta dana ya'yan ta, ina ganin girman ki,a matsayin wadda ta kawo Aminatu duniya. Sai dai a yanzu babu ɗaya daga cikin wannan da zai sa na cigaba da ganin girman naki, ki sani a yau ni Farouk, ni zan zame wa Aminatu uwa, uba da dukkan gatan ta, har zuwa lokacin da zan hada ta da iyayen ta, babu kuma daya daga cikin ku da ya isa ya raba auren mu, ƙaddara ce ta haɗa mu, kuma babu wani mutum da ya isa ya raba." Yana kaiwa nan ya juya a zafafe ya bar wajen, kwala masa kira take cike da tashin hankali, amma babu alamun zai tsaya balle ya saurare ta,kallo Harira tayi cike da tsana tace "Sai kin yi dana sanin abinda kika aikata min." Dariya ta saka harda tafa hannu tace "Ko ke kiyi dana sani ba, uwar yan son zuciya ai nice maganin irin ku." RanoHafsat Rano                          (10) *** Rai a bace ya shigo gidan, muka bishi da kallo nida Dada, be tanka ba, dan ko sallama a ciki ciki yayi ta yayi saurin wucewa dakin sa, yana zuwa ya maida mukullin kofar ya rufe, shiru mukayi baki daya babu wanda yayi motsi, ni a raina mamakin abinda ya sashi wannan tsananin fushin haka nake, ita kuwa Dadah ina kyautata zaton tasan tabbas koma menene akayi mishi ba karami bane. Har dare be fito ba, naje na buga dakin nasa yafi sau nawa baya budewa, duk na rasa ina zaka saka raina. Komawa nayi na shige cikin kujera nayi lamo na kasa ko cin abinci. Ina kwance na fara kuka kasa kasa, bansan dalilin kukan nawa ba, kila hakan na da na saba da yunwar da ke nukurkusata ne, jin karar bude dakin sa yasa nayi saurin tashi, shi dinne ya fito cikin shigar kananan kaya, fuskar sa tayi fayau kamar wanda yayi ciwo, tashi nayi na zauna sosai ban bar hawayen dake zuba a fuskata ba ya karasa sauka. Da sauri ya ƙaraso gareni ya zauna yana leka fuska ta "Kuka?" Ya tambaya yana mamaki. Daga masa kai nayi ina sake matsar kwallar. "Menene?" Ya furta yana matsar da hannu na daga fuskar tawa, goge min hawayen ya shiga yi yana girgiza min kai. "Karki kara kuka kinji? Babu abinda zai sake faruwa." Daga masa kai nayi ba tare da na gane abinda yake nufi ba, matsawa nayi baya kadan na sake kwanciya ina kokarin kama cikina da naji ya murda. "Kince abibci?" "Umm umm." "Ok Ina zuwa." Ya tashi tsam ya nufi Kitchen din, chan sai gashi da abinci a tray da ruwa, zama yayi a kasa ya tankwashe kafarsa ya nuna min kusa dashi "Oya..." Da sauri na sauko dama abinda nake jira kenan, tare muka shiga ci yana bani labarin makarantar da yaje, nan danan na ware na shiga yi masa hira nima, ni na kwashe kayan na mayar na dawo na zauna ina duban wayar sa dake saman kujera.. "Dan kira min Amal dan Allah na bata labari." Girgiza min kai yayi yana cewa "Karki fada mata, ki bari kawai sai dai tazo ta ganki da uniform." "Tohm shikenan." Nace ina murmushi. Mik'ewa yayi ya nufi kofar fita yana cewa "Kije ki kwanta kinji, gobe da safe zamu fita." "Toh." Nace ina mik'ewa dá sauri nayi daki. ***Da safe shine ya tashe ni, ya taimaka min na shirya muka fito, dakin Dadah muka wuce yana rike da hannu na, tana ganin mu ta riko ni tana sani a jikin ta, kallon shi naga tanayi cike da tsantsar tausayi. Girgiza kai kawai yayi yace "Zamu wuce Dadah, ayi mana addu'a." Hannu ta ɗora a kaina ta yi min addu'a, sannan ta rike hannun shi shima ta haɗa waje daya da nawa.. "Dan Allah Farouk karka yi wasa da abin da mukayi magana akai jiya, zan iya cewa kwana nayi ban runtsa ba ina tunanin komai." "In Sha Allah." Ya amsa mata Sakin hannun tayi tace muje Allah yayi mana albarka. Haka muka fito yana rike da hannun nawa har mota, wannan karon bayan shima ya shiga tare dani maimakon gaba, driver yaja muka dau hanya. Har muka isa makarantar be daina amsa waya ba, bansan da wa suke maganar ba amma tabbas maganar me matukar muhimmanci ce, lokaci zuwa lokaci yakan kalle ni ya sakar min murmushi. Sai daya ga mun doshi cikin makarantar sannan ya ajiye wayar, waje muka samu muka zauna har aka fara zuwa, ina ta kallon komai kamar almara, dandazon daliban dake kaiwa da komowa a cikin makarantar su suka fi jan hankali na, uniform dinsu ma kawai abin kallo ne, cikin tsafta da tsantsar nutsuwa. Sai wajajen goma da rabi sannan wani mutum yayi mana umarni da muka shigo, shiga mukayi muka zauna ya ɗan fita ya barmu. Kallo na ya Farouk yayi yace "Idan suka tambaye ki sunanki, kice Aminatu Farouk MD kinji?" Kafin nayi magana mutumin ya sake shigowa, zama yayi ya umarci ya Farouk ya ɗan jira a waje, fita yayi ya rufo mana kofar, kujerar kusa dashi yace na dawo, ya shiga yi min tambayoyi, da yawa ban san amsar ba, musamman bangaren turanci da lissafi, duk da na kan fuskanci wani abun saboda dan zaman da nayi da Ya Farouk da karatun da yake min dukka da turancin yake min su, sai dai ba komai ne nake ganewa ba duba da yanayi da makarantar da nake yi a dah. Tashi yayi ya leka ya sake kirawo shi. "Mr Farouk, mun mata interview sai dai fa she's left far behind, ya zata iya catching kuwa? I doubt so." Folding hannun sa yayi yana duban ya Farouk, murmushi yayi ya ce "Sir munyi duk maganar nan da principal, zamu biya kudin extra lesson da za'a dinga mata har Allah yasa tayi picking, and bani da doubt zata kamosu, tana son karatu sosai so ina da hope akan ta." "Ok Good, if that's the case, sai muyi komai yanzu, next week Monday ta zama full student, ina ga hakan zaifi." "Hakan ma yayi, thank you very much." "It's our pleasure." Tashi yayi yace ya mu biyo bayan sa, muka bishi wasu offices, duk wasu formalities bamu bar school din ba sai da muka gama su, a ranar aka bani komai har da uniform, murna da farin cikin da nakeyi ba'a magana, haka muka dawo gida ina rungume da komai kamar wani ne zai raba ni dasu. *** Dukkanin satin a cikin shiri muka karasa shi, sosai akayi min provision na dukkan abinda zan bukata, wannan karon Dada da kanta take tsaye akan komai, da ita aka gama shirya min komai. Sai dai ina lura kamar su ɗin ma hada kayan su suke tayi waje daya,sai dai ban kawo komai ba, na dauka ko wani abun dai zasuyi kawai, ana gobe tafiya makaranta dana matsu ina ji kamar na jawo ranar Dada tasa mai aiki ta rakani gidanmu. Gaba daya Inno tayi laushi kamar ba ita ba, ta rame sosai babu alamun walwala a tattare da ita. Kasa shiru nayi har sai dana tambaye ta ko bata da lafiya ne, ta bini da ido kawai ba tare da tace komai ba. Da muka zo tafiya ta dauko wata leda ta bani wai na makaranta ne, na karba nayi godiya na bawa mai aikin ta rike min, zamu tafi ta sake kirana daki ta hau min nasihar da bazan ce ga musabbinta ba, duk yawanci akan kula da karatu na ne, nidai kawai amsawa nake cike da mamaki, ban taba tunanin Inno zata min kwatankwacin hakan, duk sai naji babu dadi bana so na barta, da muka zo tafiya kuwa har da sharar kwalla ta cike da tausayin Inno da abinda yake damunta da bansan ko menene ba. Washegari da wurwuri na shirya tsaf cikin uniform d'ina sababbi kal, na zauna zaman jiran Ya Farouk, ina zaune shima ya fito, dan tsayawa yayi da baya yana kunshe dariyar sa, hatta jakar da komai na ajiye a gefe, zaman jiran sa kawai nake, karasawa yayi ya zauna yana dauke kansa. Ban gaishe shi ba, kawai na fara maganar tafiya, kin amsa min yayi ya wuce Kitchen ya hado tea ya fito. "Jeki nemi abu kici." Yace yana zama cikin kujerun falon, ganin fuskar sa babu wasa yasa na tashi tsam nayi Kitchen din, tea din nima na hado na dauko bread na fito, kamar magani haka nake ci cike da daukin tafiya, yana ta kallo na ta gefen ido har zuwa sanda ya gama ya maida komai Kitchen yazo ya fice, sauri sauri nayi na karasa na sake gyara komai na zauna ina kallon kofa. Chan sai gashi ya dawo dauke da wasu ledoji, a saman kujerar ya watsa su ya wuce dakin Dadah, jim kadan suka fito a tare itama ta shirya alamar tare zamu tafi. Da fara'a ta na gaishe ta, daga nan muka rankaya waje muka shiga mota ina ta murna kamar bakina zai yage. Uffan be ce min ba, yana dai noticing duk motsina. Haka nan yaji ba dadi, ko ba komai akwai matukar shakuwa tsakanin mu, amma hakan shine mafita ga dukan mu. Sanda muka isa makarantar sai naji duk babu dadi, Ina labe a bayan Dadah har aka gama komai, tuni fuska ta ta chanja dana ji an kirawo wata an ce ta tafi dani, da sauri na kankame Dada ina sakin kuka, dariya suka saka baki dayan su, hakan ya kara tunzura ni, hannu na ta kama cikin harshen turanci tace "muje ko?" Kwace hannu na nayi na sake saka kuka ina kallon Ya Farouk, shi dinma ni yake kallo, hannu yasa ya kirawo ni, da sauri na tafi gareshi, maimakon yayi min magana sai yaja hannu na muka fita daga office din, chan baya wajen wasu shuke-shuke ya kaimu, yana zuwa ya cika hannu na yana ja da baya. "AMINATU..." Ya kira sunana yana saka idon shi a cikin nawa, raw raw na sake yi da idon zan cigaba da kukan, da sauri ya furta "Ohh Ya Salam! Baki son makarantar ne?" Girgiza masa kai nayi na cigaba da kuka na. "Toh menene, kin fasa karatun ne?" Nan ma girgiza kai nayi "Bude baki ki faɗa min kinji." Ya fada yana sake matso wa sosai kusa dani, cikin muryar kuka nace "Ni ba tafiya zakuyi ku barni anan ba." Dan murmushi yayi kadan, yasan kwanan zance, lallashi na ya hau yi cikin son gamsar dani muhimmancin hakan, tare da alƙawarin zuwa duba ni kowanne lokaci, da kyar na sa kaina na amince, sai dai ban bar kukan ba, haka ya sani a jikin sa yana shafa bayana a hankali, lamo nayi na kasa kwakkwaran motsi, ina jin shi yana kokarin raba jikina da nashi jin takun tafiya, Dadah ce ta iso wajen tana nazarin mu. "Babana sallamar ta isa haka nan, karka manta fa muna komawa..." Kallon danayi mata ne yasa ta gimtse maganar tana yin gaba "Kuyi sauri dai ina mota ni, Aminatu Allah ya bada abinda aka zo nema, banda kawayen banza." Daga haka ta bar wajen dukkanninmu muka bi bayan ta da kallo babu ko kiftawa, a hankali ya kamo hannu na, ya ciro dan karamin akwati ja me masifar kyau daga aljihun sa, bude ta yayi dan karamin zoben azurfa ya bayyana, ya kama ring finger na ya zura min, yana kallon fuska ta. Babban harafin D cikin wata irin kwalliya shi ya karawa zoben kyau da kawa, kura ma hannun nawa ido nayi cikin tunani me tsawo da bansan me nake son tunawar ba. A hankali cikin wata iriyar magana ya furta... "Alk'awari kaya ne Aminatu, ki rike Alk'awari, nima zan rike, kiyi karatu, kiyi karatu har sai kin ji kamar kwakwalwar ki xata fashe, a sannan zan tabbatar da buri na ya cika, ina so ki zama cikakkiyar lawyer saboda wani kudiri nawa." Daga kai kawai nayi ina cigaba da kuka ganin da gasken tafiya zasuyi, gaba yayi kawai nabi bayan shi da sauri, haka muka jera har gaban motar, da wani irin sauri ya fada ba tare da ya sake kallon bangaren da nake ba, ina ji ina gani suka fice daga cikin makarantar. Jan kafafuwa nayi na wuce ina jin kamar wani babban bangare na rayuwa ta ya bar ni. ****Suna isa gida suka sauke Dadah, kai tsaye gidan su Aminatu ya wuce, Inno na zaune tana kulla kayan miya aka sanar mata da isowar sa, sai da gaban ta ya fadi, amma ta dake tace a shigo dashi dakin ta, shiga yayi ya zauna yana karewa ko ina kallo, a matukar sanyaye ta shigo dakin, bayan tasa Karime ta kawo masa ruwa, zama tayi daga chan gefe tana tunanin ta in da abubuwan zasu fara. ***Rayuwa na shiga yi sosai a makarantar, bani da wani lokacin kaina sai ka karatu, kawata daya ce Asma'u, tare muke karatu muyi komai, bani da wata matsala sai ta rashin Ya Farouk da nake matukar jin sa a jinin jikana. Lokacin visiting nayi sai gashi yazo, shi kadai yazo nayi ta murna, dariya kawai yake ina bashi labarin makaranta da wahalar karatun da nake, tun da ni kullum akwai wani extra lesson da ake min bayan normal lesson da muke yi baki dayan mu, hakan yasa nake shan wahala sosai, wani lokaciin ma sai naji kamar na sare, sai na tuna kalaman sa na ƙarshe, su ne suke sake zaburar dani dan ganin na cika masa burin sa kamar yadda yace. Lokacin da akayi hutun makaranta, sabuwar principal din da aka sake wadda na lura da zuwan Ya Farouk na karshe sun jima suna magana da bansan ta mecece ba tasa aka kirani, ta tabbatar min da ni bazan je gida ba, anan makaranta zan zauna wajen ta na cigaba da extra lesson d'ina, ranar wuni nayi ina kuka, haka ina ji ina gani kowa ya watse ya bar ni. Rayuwa ta haka ta cigaba da tafiya, ina iya kar kokari na wajen ganin nayi karatu, maganar zuwa gida hutu kuwa na rasa dalilin da yasa bana zuwa ɗin, tun ina damuwa har na hakura bayan munyi wata doguwar waya da Ya Farouk da wayar headmistress din, tun daga nan na watsar da komai na cigaba da karatu na ka- in- da-na- in. Lokacin da mukaje aji uku ne, akayi hutu sai ga mutanen da ban taba tsammanin ganin su ba, Ya Farouk ne tare da Amal, Dadah sai Inno da Karime, karamin hauka ne kawai banyi ba, amma tabbas zan iya cewa na jima banyi farin ciki irin wannan ranar ba, abu daya na kasa gane kansa, shine yadda Inno tayi laushi sosai, ta zama wata shiru shiru, duk in da nayi tana bina da kallo kawai, wani lokacin ma sai na ga kamar tana sharar kwalla, ban kawo komai ba, na cigaba da nan nan dasu, har suka zo tafiya, sosai naji son bin su, amma kuma nasan hakan ba me yiwu wa bane. Haka suka tattara suka tafi suka barni da tarin kewar su. Tun daga nan karatu na ya kara daukar zafi, babu wanda ya kuma leko ni, sai dai lokaci zuwa lokaci ya Farouk kan kira a wayar principal ta bani, kullum maganar sa daya nayi karatu, haka na cigaba da dagewa sosai. Zuwa lokacin zuciya ta ta gama sanin menene so, menene kauna, abinda nake ji game da Ya Farouk wani yanayi ne da zuciya da ruhi ne kadai zasu iya tabbatar dasu, baki na yayi kadan ya fasalta yanayin da nake ji game dashi din. Har muka shiga Ss2 be sake waiwayo ni ba, kiran da yake min sam ya daina, sai na dauki hakan a matsayin yana son yaga na yi karatu ne, aikuwa na sake jajircewa. Exams muka fara ta karshen Ss2, wadda zamu shiga ajin karshe, hakan ya sa na kara zama serious, bani da lokacin komai sai na karatu, sosai kuwa nake jin dadin exams din, ranar da mukayi final exams ne na fito ina tafiya a hankali, iska ake kadan kadan, yammaci ne me cike da ni'ima akwai alamun za'a iya ruwa kowanne lokaci, tafiya nake ina tunanin shi, iya sanin da nayi masa nasan shi mutum ne me matukar son yanayi irin na damuna, jin kamar ana min magana ne yasa na dan dakata ina juyowa, wata yarinya ce yar junior session, hannun ta rike da tarin littattafai. "Kiran ki ake a bayan garden din chan." Tace tana nuna min da bakin ta "Ni kuma, wake kira na?" Nayi tambayar cike da mamaki "Kije zaki gani." Ta amsa min tana wucewa abin ta, cike da mamaki na zuba wa hanyar garden din ido, mamakin me kira na nake, har zan wuce hostel sai kuma na fasa na juya zuwa hanyar da zata sadaka da dan karamin garden din makarantar, ina isa na shiga wurga ido na ko zan ga wanda yake kirana, ban ga kowa ba, tsaki naja kadan na juya da nufin barin wajen. Kamshin turaren sa ne ya daki kofofin hanci na, da sauri na juyo, ido na suka sauka akan sa, sanye yake cikin shigar Kufta baka, wadda tasha aiki sosai da bakin zare ɗinkin three quarter , kansa babu hula sai dai yana rike da ita a hannun sa. Cikin wani irin yanayi yake takowa gareni, na kasa ko da kwakwaran motsi balle nayi tunanin abin yi. Ya chanja kwarai, ya zama babban mutum, me cike da kwarjini da tsari, tsananin nutsuwa da tsagwaron hutu sun nuna kansu a tattare dashi, bayan wadannan abubuwan babu abu daya daya chanja a tattare dashi d'in, shine dai Farouk d'ina, wanda nake ganin sa a matsayin rayuwa ta, komai na. Hannun sa yasa ya murda a saman fuska ta ya bada sauti, da sauri na shiga kokarin boye fuska ta, tsananin kunyar sa ce naji ta rufe ni lokaci daya, wadda ban taba jin hakan ba sai yau din, wanda nake kyautata zaton hakan na da nasaba da yadda zuciya ta ke kara jaddada min matsayin da yake dashi a cikin ta. "My Destiny..." Ya kirani da sunan da dukkannin bangarorin jiki na sai da suka karbe shi, kasa daga kai nayi balle ya sa ran zan kalle shi, ina jin shi yana sakin dariya kasa kasa, kallon tsaf yake mun tun daga sama har kasa, a yau ya sake tabbatar da cewa Aminatun sa ta kai, ta isa dukkanin yadda yake da muradi. "Yau ni yar Aminene take jin kunya?" Ya furta yana dariya Da kyar na harhada kalmomin gaisuwa waje daya na furta "Ina... Wu..ni?" "Ah laillai, na yarda yau Aminatu na ta girma, kunya Aminatu? Ya farouk dinki ne fa, this is unbelievable!" "But I like it." Ya fad'a yana kawo bakin sa daidai kunne na. Da sauri na ja baya, hakan yayi daidai da zamewa ta, cikin zafin nama ya tare ni da dukkan karfin sa, ido na shiga zarewa kamar zan fita da gudu, hannun sa ya saka cikin nawa ya jani zuwa jerin kujerun dake zagaye a harabar wajen, banyi musu ba, na shiga bin sa, ina fatan abinda nake ji a yanzu ya zame min wani tsani da zan sake takawa na rayuwa, sai dai kash!. RanoONAR TASFAH                11 ©️®️HafsatRano *ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo                       *** Hannun sa ya sabule daga jikin nawa ya zauna yana nuna min kusa dashi, a kunya ce na zauna, kafe ni yayi da ido na kasa koda kwakkwaran motsi, duk da hakan be dauke kansa daga kaina ba, yana so lallai sai yaga tasirin da idanun sa suke min, hannu nasa na kamo karshen hijabin nawa na shiga wasa dashi, bin hannun yayi da kallo yayi murmushi. "AMINATU... Wai Menene hakan ne? Kunya ta kike ji? Akan me?" Duk a lokaci daya yayi min wannan tambayar, ni kaina mamakin kaina nake ji yadda tsananin kunyar sa ta mamaye ni, na kasa kwakkwaran motsi, kwarjinin sa ne duk ya cika wajen, duk yadda naso na sake dashi na kasa, ina jin sa yana magana nayi kus kamar bana wajen, tashi naga yayi, ya zura dukkan hannayen sa cikin aljihun rigar sa, cikin jin haushi yace "Tun da haka ne, bari na tafi kawai tun da ba'a son gani na." Da sauri na rike hannun sa, "Dan Allah karka tafi." Hannun nasa ya kalla sannan ya kalle ni, ya kwashe da dariya, da sauri nayi kokarin zare hannu na amma sai ya rike "Baki isa ba ai, ana so ana kaiwa kasuwa." Dariya muka sa a tare baki daya, duk kunya ta sake kamani. Komawa mukayi muka zauna muka hau hira, mafi akasarin hirar shine yake min, duk da na dan sake kadan kar yace zai tafi. Acikin hirar ne na daure na tambaye shi karatun sa, wayar sa ya bude ya shiga gallery ya mika min, baki bude nake bin jerin hotunan nasa da suka gama bayyana irin karatun da yayi, no wonder na ganshi ya sake zama babba, ko ina na jikin sa ya murje, irin na ingarman namiji. "Soja Ya Farouk!"  Na faɗa ina kallon sa. Daga min kai yayi yana dariya "Burin both Daddy da Mom ne, sannan kuma burin Farouk dinki ne, saboda wani babban dalilin sa." Jinjina kai nayi ina sake kallon sa. "Ni da nake tsoron soja kuma..." "Sai ka mijin ki soja ba, sai ayi yaya? Karki manta fa ance... A wife of a soldier..." "Can never be a soldier." Nayi sauri amsa masa ina dariya. Dariyar shima ya saka ya kai hannu ya dungure min kai "Sarkin wayo, toh ba haka karshen yake ba." Muka kara saka dariya a tare. Hira muka cigaba ba dayi har zuwa sanda aka kira magriba, tashi yayi yana nannade hannun rigar sa. "Ya za'ayi?" Ya daga min kira sama, "Uhum." Nace ina tashi nima. "Kinga ba'a rufe makaranta ba sai gobe, wannan ma dan dai principal din ta hannun damar Mummy ce, kar mu shiga dokar makaranta, zan wuce, amma zan dawo gobe, kinsan da maganar zana waec dinki a Ss2 ko?" Daga masa kai nayi "Ok zamu je gida sai kiyi sati daya... Dagowa nayi da sauri, murmushi yayi min yace "Daga nan sai a dawo makaranta, kinga ba za'a dade ba zakiyi exams, kina gama wa..." Be karasa ba, yayi shiru yana sake fad'ad'a fara'ar fuskar sa "I can't wait ranar nan tazo, duk plans d'ina na ranar ne, Allah dai ya kaimu, zaki yi mamaki sosai." Bude baki nayi zanyi magana yayi saurin katse ni "Karma ki tambayi me zai faru ranar, kedai kawai ki shirya mata, it's going to be the biggest day of our lives." "Shikenan." Nace ina matsawa gaba. "Ba sallama?" Ya marairaice murya yana bude min hannayenku sa, sarai na gane me yake nufi, dariya nayi, na kara yin gaba, sosa kansa ya shiga yi yana kallo na, sai dana tabbatar nayi nisa daga in da yake sannan na daga mishi hannu ina masa gwalo, da hannu yayi min alamar zai kamani ne. *** Washegari tun da wuri na tashi, ina nan da d'abi'ata ta dauki idan zanyi abu na tashi da duku-duku na hau shiri, ina ji aka kad'a kararrawar assembly da ake yi a duk ranar da za'a rufe makaranta, a gurguje aka gabatar da komai da ranar da za'a dawo makaranta, kasancewar akwai sauran wajen sati uku kafin a fara Waec yasa aka bawa yan Ss3 hutun sati daya, sai kuma a dawo a fara karatun jarabawar kafin lokacin ta ya zo. Da haka kowa ya hau watse wa cike da farin ciki zuwa gida. Ina tsaye a saman barander classes dinmu na kafa wa gate ido naga shigowar shi, ji nayi kamar zan zame, haka dai na daure na nufi wajen motar, ina zuwa yana fitowa, idanun mu suka sarke waje daya, da sauri na janye nawa na hau gaishe shi, murmushi kawai yayi ya wuce wajen da aka signing, a gaggauce yayi signing din ya taimaka min na dau yan kaya na muka dau hanyar kauyen mu. Sanyin Ac da kamshin turaren da ya bulbula ne suka cika motar, lamo nayi jikin kujera ina jin wani yanayi ne wuyar fassara, magana yake min kasa kasa wanda zaka rantse ba dani ɗin yake ba, idon sa na kan titi sai dai hannun sa daya na rike da nawa yana murzawa a hankali. Har muka isa gida na kasa sakat, shi kuwa babu abinda ya dame shi, sha'anin gaban sa kawai yake cike da tsantsar farin ciki da ya kasa boyuwa a saman fuskar sa.   A kasalance na fito daga motar bayan ya tsaya, gaba nayi kawai dan Allah Allah nake na isa ciki na samu sauƙin abinda nake ji, ina shiga daki yana turo kofar, tsaye yayi kamar yadda ya saba a wanchan lokacin, hannayen sa jingina da makarin kofar, idanun sa na zagaya wa lungu da sak'o na dakin. "Garin sauri kin manta kayanki Madam." "Na manta wallahi." "Dole ki manta ai, kina gudu na, duk kin chanja Aminatu, what's wrong with you?" Ya fada yana takowa cikin dakin, saurin kasa nayi da kaina ina jin sanda yazo daf dani "Look at me." Ya furta a chan kasan makoshinsa, a dan darare na dago na kalle shin, sai naga ya cika gaba daya wajen. Tallafo fuska ta yayi ya dago ni "Kinsan matsayi na wajen ki ko? Kinsan dai ba zan cutar dake ba, then why are you behaving like this? Kamar kin ga bako." "Ni kawai kunyar ka nake ji Allah." Na faɗa kai tsaye. Dariya yayi ya saki fuskar tawa ya fada saman gadon dakin, tsaye nayi ina tunanin abin yi, ji nayi ya finciko ni na fado gadon kusa dashi, har saman keyata na buguwa da sangalalin hannun sa, matsowa yayi sosai yana kura min ido "Shekarar ki 17 if i'm not mistaken, ni kuma i'm 29, nasan abinda ya dace da wanda be dace ba, karki damu, babu wani abu da zan miki da nasan zaiyi hurting dinki, ki daina tsoro na ko kunya ta, ki dauke ni kamar dah, Ya Farouk dinki, ni a waje na,har yanzu yar karamar Aminene nake kallon ki." Dariya na saka, na kai masa dukan wasa, da sauri ya tare yana hade hannaye na waje daya ya murde su, yar kara nayi kamar zanyi kuka na shiga magiyar yayi hakuri, da kyar na samu ya hakuran, amma sam yaki barin dakin, ni kuma na matsu ya fita dan na samu na watsa ruwa na cire kayan jiki na, kiran wayar da akayi masa ce ta taimake ni, da sauri naga ya daga wayar yana kokarin fita daga dakin baki daya, da haka na samu damar saka key a dakin na aiwatar da abubuwan da nake so. ***Har dare be sake waiwayo ni ba, ina zaune a dakin ban fita falo ba, gidan tsit babu motsin kowa, kaina ke dan saramin saboda yunwar da ta fara addabata, ban dauko komai cikin provision dina ba, gashi naje Kitchen ɗin babu komai balle na samu abinda zan dan taba. Zamewa nayi na kwanta a saman tiles din dakin hannu na rike da wani story book ina karantawa saboda rage kadaita, turo kofar akayi, hannun sa dauke da ledoji manya guda biyu, tashi nayi da sauri na zauna. Ajiye ledojin yayi a gabana ya zauna. "Ya Farouk yunwa." Nace ina bata fuska. Tura min ledojin yayi "Kiyi hakuri abu ne urgent ya fitar dani." Matsawa nayi na bude na dudduba, kafin na tashi dan zuwa dauko abinda zan juye a ciki.   Bayan mun gama ci na tattare komai na maida na dawo dakin, ban tarar dashi a ciki ba, na shirin bacci na kashe wutar, ina cikin addu'a akayi knocking, tashi nayi na bude, yana tsaye cikin shigar bacci shima, rabawa yayi ta gefe na ya wuce ciki, tsaye nayi a jikin kofar ina kallon sa, har ya haye gadon nawa yana jan dubet zuwa saman kafadarshi. "Idan kin gama tsaiwar, ki rufe kofar kizo ki kwanta." Muryar sa ta daki kunne na, jim nayi kamar ba zan motsa ba, sai kuma na shigaa jan kafata da kyar kamar wadda kwai ya fashe wa na isa dayan bangaren, a darare na hau gadon na kwanta gefe daya, ina jin sa ya mirgino zuwa bangaren da nake, ya dora kansa saman pillow na yana saka ni cikin jikin sa. Jiki na ne ya hau rawa kamar mazari, a hankali ya dora bakin sa saman kunne na ya furta "Let sleep princess, Goodnight." Manage pls nayi typing ya goge 😥😥😢😓🙏 Comments yana taimakawa sosai wajen motivating writer🙏 Thanks All Jazakumullah bhi khair*ONAR TASFAH*                *OROG NIRUAD* *RIYAB AFAFAZ*                  *EGAP (12)* *** Kamar tsohuwar munafuka haka nayi ya raba idanu, gaba daya na rasa yadda zanyi, duk na takura,kasa koda kwakkwaran motsi nayi ina jin shi yana karanta mana addu'ar bacci. Bani da kuzarin da zan iya bude baki na, nayi addu'ar nima, haka nayi shiru ina tunanin abinda ke faruwa. "Princess." Ya kira ni da sabon sunan da ban san yaushe na same shi ba. "Uhum ." Nace kamar me ciwon hakori,. "Please ki saki jikin sa, bacci nake ji nasan kema haka, beside ni mijinki ne, mata da miji basa raba daki sai da kwakkwaran dalili, so kawai ki saki jikin ki dan ba fita zan ba, ina nan anan zan kwana atau." Ban tanka ba, ina jin sa yana ta kokarin ganin sai na saki jikina, wanda ni kuwa har ga Allah ba iya wa zanyi ba, a yadda nake ji ma yanzun Allah sa nayi runtsawa, yadda yabi ya kanainayeyi, bana jin zai barni na shaki iska me dadi yau kuwa. Har ya gama surutan sa ya fara jan numfashi sannan na sauke ajiyar zuciya, gaba daya bani da sukuni balle nutsuwa da zan iya runtsawa. Sake sake na shiga yi ina tuna wani Novel dana taba karantawa. Da haka bacci barawo yayi awun gaba dani ba tare da na shirya masa ba. *** Kira wayar sa ce ta farkar dani, baya dakin, na kai duba na wajen wayar, sunan da na gani yana yawo a saman wayar na kura wa ido, har ta gama ta katse wani kiran ya sake shigowa, ita ɗin ce dai, tsam na mike nayi hanyar toilet ba tare da na sake bi takan wayar ba. Tsawon mintuna talatin na dauka a toilet din, gaba daya na hado har da wanka na fito, a gurguje na hau shiryawa ina kallon kofa kar ya shigo, har na gama ɗin kuwa be shigo ba, sai a lokacin na lura ya dau wayar tasa kenan ya shigo ina toilet, ban shafa komai ba sai yar powder da wetlips, na dora hijabi na a saman sabuwar atamfar da na saka ta sau daya a makaranta, blue ce da adon baki anyi mata zanen ganye. Half covered shoe d'ina black na jawo a cikin kayan dana zo dasu na zura na yo waje. Yana zaune a saman kujerar falon, hannun sa rike da mug yana fitar da tururi alamun abu me zafi ne a ciki, shi dinma yayi wanka ya shirya cikin ƙananan kaya black top da wandon su na sojoji, kallo ya hau bina dashi har na karasa ina zama a kasan carpet daidai wajen da kafafun sa suke. Zamowa yayi ya zauna kusa dani kafadarsa na gogar tawa yayi saurin cewa "Good morning princess." Murmushi nayi na gaishe shi da ina kwana? Amsawa yayi yana mika min mug din hannun nasa "Tayani sha wallahi cikana a cunkushe yanke." Mika hannu nayi zan karba ya girgiza min kai, hanyar bakina yayo dashi a kunya ce na bude ya kafe min cup din, a hankali na shiga kurbar kunun gyadar daya sha madara da sugar, ina sha ina tunanin in da ya samo shi, tas na shanye, ya jawo tissue ya mika min yana tashi "Anji dadi an shanye min." Dariya nayi ina karba shi "Ni kawai dan ka takura ne nasha, amma ba dadi." "Really!" Yace yana rike kugun sa. "Umm." "Ai shikenan, gobe ma rana ce, za'a kawo min ne ba zan baki ba." "Waya kawo maka?" Nayi saurin tambayar shi dan dama ina son sani. Make kafadar shi yayi ya juya hannun shi "Ba sai kinji ba." Murmushi kawai nayi ina ayyana a raina wanda ya kawo mishin, ganin zan bata wa kaina lokaci da tunani yasa na wuce Kitchen ɗin, na wanke mug din na gyara wajen na fito. A tsaye na tarar dashi yana kokarin saka p-cap a kansa "Muje na ajiye ki a gidan sai yamma na dawo, nima ina da abin yi yau din da yawa." Da sauri na juya, na dauko yar karamar jakata na saka tarkacen chocolate da sweet na fito, tuni ya shiga mota achan na iske shi muka dau hanya.   Muna fitowa yayi daidai da lokacin da Garbati yazo wucewa a saman machine din sa, gaba daya ya chanja kamar ba shi ba, riga da wandon jikin sa kadai sun isa su fada ma halin da yake ciki, duk yayi baki ya rame bakin sa yayi duhu alamar yasha sigari ya koshi. Kansa yayi da motar, ya ɗan taba shi, take ya fadi a wajen, balle murfin motar yayi idon sa yayi jawur ya fito, Garbati na kokarin mik'ewa cike da masifa ya dira a gaban shi. Kafa yasa ya take machine din, yana kallon fuskar shi. "Uban waye kai da zaka ture ni, kuma..." Maganar sa ta makale sakamakon wandon daya fara cin karo dashi bayan ya dago. Cikin in da in dah yace "Me nayi maka?" Farouk be tanka ba, sai kafa daya sa ya tardes shi, tuni ya baje a wajen bakin sa ya fashe, hannu yasa ya hau zare belt din jikin sa, da sauri na balle murfin motar na fito, na isa wajen, rike shi nake kokarin yi, ya juyo a fusace ya nuna min mota "Wuce ki koma ciki." Yadda yayi maganar da yanayin fuskar sa, yasa naji yan hanjin cikana sun juya, da gudu na koma na zauna ina rawar jiki. Be wani tsaya bata lokaci ba ya shiga laftawa Garbati belt din nan, ihu yake yana magiya amma sam yaki sauraran sa, Dukan sa yake da dukkan karfin sa, tuni abin ya fara bani tsoro, ganin yadda ya koma kamar ba Ya Farouk ba, ya juye gaba daya ya zama kamar wani horror, kuka na soma a hankali ina daga zaune a motar, sai daya tabbatar yayi masa laga-laga sannan ya ture shi ya nufo motar, da bayan hannu na, na shiga share hawayen fuskar ta. Be ko kalle ni ba, ya tada motar muka dau hanya, ta gefen ido nake satar kallon sa, yadda kirjinshi ke kaiwa da komowa. Sosai nayi mamakin tsananin zuciyar shi. Muna zuwa kofar gida nayi saurin kama kofar motar zan fita, naji ya riko hannu na. "I'm sorry." Ya furta yana kallon ido na, daga mishi kai nayi ina sake kokarin bude kofar dan har ga Allah na tsorata da yanayin sa.  Lock din kofar ya danna, ya matso daf dani, da sauri na kulle ido na zuciya ta na harbawa, tsoro na daya kar nima ya jibgen,  a hankali naji saukar light kiss a saman goshi na, sake runtse ido nayi na kankame jikina. "Ohh shit." Ya daki steering motar, "Kinga, pls karki ji tsorana, i can never harm you, shi wanchan kuwa zan masa fiye da wannan, wannan somin tabi ne, saboda haka kar na sake jin kinyi kuka idan ina abu makamancin wannan." "Toh." Nayi saurin cewa. "Zan tafi." Na nuna masa kofar motar. Dan karamin tsaki yaaja ya bude min da sauri na fita ina yin hanyar zauren gidan. Sai dana shiga sannan yaja motar ya tafi.   Sallama nake tayi a tsakar gidan namu, baki daya komai ya sauya, sosai gidan ya sake tsufa, duk kofofin sun lalace, dakin Inno na kalla naga an dan turo kyauren alamun bata nan, Yalwati ce ta fito daga dakin Baba, da mamaki take kallo na, sai kuma ta fadada fara'ar fuskar ta. "Wa nake gani kamar Aminene?" Dariya na saka na karasa ciki. "Ah laillai, maraba da yan makaranta." Kasa na tsuguna na gaishe ta, ta amsa sosai, kafin tace "Shiga wajen Baban naku, Inno dai ta je hayi karbo magani, kinsan duk ba dadi suke ji ba ita da shi." "Allah ya sauwake." Nace ina tura kofar dakin, yana kwance daga gani yana jin jiki, kallo na yake har na isa gaban sa na zauna. "Sannu Babah." Na gaishe shi cike da tausaya wa, hannun sa daya naga ya daga min, alamun na matso, matsawa nayi sosai na rike hannun sa ina jera masa sannu. Yalwati ce ta shigo rike da kofin silba cike da ruwan randa. "Tsautsayi ya gamu dashi ai, faduwa yayi a banɗaki shikenan barin jikin sa daya ya shanye, kin gashi nan baya ko magana." Kwalla ce ta zubo min cike da tausayin baba, mutum me sauƙin kai da hakuri, bashi da ta cewa kowanne lokaci sai abinda Inno ta gindaya masa, yau shine rayuwa ta juya wa baya haka, da ido yake min alamar nayi shiru, kasa kasa na cigaba da kukan nawa ina masa addu'ar samun sauki. Ban fito daga dakin ba, sai da Inno ta dawo. Tana gaban dakin ta ta baza ledar magungunan gargajiyar data karbo na fito, da ido ta kafe ni cike da mamakin gani na. "Yaushe kika zo.?" Tun kafin na gaishe ta ta watso min tambayar, murmushi nayi kawai dan hausawa sunce me hali baya fasa halin sa. "Sannu da zuwa, ina wuni?" Na bagarar da tambayar da tayi min na maye gurbin ta da gaisuwa, amsawa tayi tana cigaba da duba kayan data zo dasu kamar bata damu da zuwan nawa ba. Dakin nata na shiga, duk yayi kacha-kacha, ajiye hijabi na nayi na shiga kokarin ganin na gyara. Ina cikin gyaran ne nazo kan jakar da nake yawan ganin tana ciro ta, ta duba. Hannu nasa da nufin bude jakar ta shigo. "Kee!" Ta daka min tsawa, da sauri na saki jakar ta sabule daga hannu na "Me kike yi haka?" "Um.. um.. dama gani nayi dakin..um yayi datti shine nake sharewa." Zuwa tayi gabana ta dauke jakar ta bude sip dinta ta saka. "Yi sauri ki karasa sharar ki fito zaku gaisa da mutane." Daga haka ta fice ta barni, sauri sauri na karasa na fito, na shiga sauran gidajen dake cikin gidan namu. Bayan na dawo ina ta tunanin ina yan matan gidan suke, chan dai na tambayi Inna, sai a sannan nake sanin ashe duk an musu aure. Hanne ta haihu ma Karime kuma ta kusa. Sosai nayi mamaki, naso a ranar na samu me rakani, ana la'asar sai ga kiran Ya Farouk a waje, ban so ba, haka na shiga dakin Baba nayi masa sallama sannan na fadawa Inno yazo zan tafi. Shiru tayi kamar me nazari, sai kuma tace "Kice masa dan Allah yazo ina son magana dashi." Da toh na amsa mata na fito nayi wa sauran sallama. Waya yake yanzun ma, ina bude kofar yayi sallama yana dage min kira sama. "Ina wuni?" "Lafiya lou, kin gama ai ko?" "Eh na gama." "Ok." Ya hau kokarin data motar, "Dama inna tace na fada maka tana son magana da kai wai." Da sauri ya kalle ni "Kunyi wata magana ne?" Ya tambaye ni "A ah bamuyi ba." Na amsa. Ajiyar zuciya naji ya sauke kafin yace "Shikenan zan zo gidan gobe, yanzu ana jirana ne." Bance komai ba yaja motar muka bar kofar gidan. *** Tsawon satin haka mukayi shi, babu abu d'aya, daya chanja, kullum zamu kwanta kamar yadda muka fara a ranar farko, tun ina nokewa har na saki jikina ganin babu abinda ya faru, sai dan abinda ba za'a rasa ba.😜 Naje gidan Karime da Hanne, sannan na koma gidan mu sau biyu na sake duba Baba, bansan ko yaje sunyi maganar da Inno ba, ba ta kara dai yimin maganar yazo ɗin ba, sai kawai na share ban tambaya ba. Daren ranar da zan koma makaranta dukkan mu bamu da walwala sam,sai nace har gwara ma ni ina dan daurewa, amma shi ƙarara ya nuna damuwar sa, hira nake masa da son ganin ya ɗan saki ransa, amma fafur yagi, shinkafa da miya nayi mana a daren ranar, na samu yaci ba laifi dan tun rana be sa komai cikin sa ba. Da wuri yace muje mu kwanta, ranar babu petir a inji be fita ko nan da chan ba. Haka muka yi shirin kwanciya bayan na tabbatar da na gama hada komai nawa a waje daya. Wanka na fara yi saboda yadda garin ya hade rai alamun za'a yi ruwan sama, babu iska ko kadan sai kugin hadarin kawai kake ji. Ina fitowa daga wankan naji garin ya ɗan fara saki, doguwar rigar bacci kawai na zura na haye gado na kwanta, ina kwanciya ya shigo yana haska wa da torchlight ɗin wayar sa, rufe ido na nayi da sauri alamun bacci, wucewa yayi gaban mirror ya shafa roll on dina ya hawo gadon ya jawo ni jikin sa. Muna nan kwance babu wanda yayi wa wani magana, aka soma yayyafi, saki na yayi ya tashi ya bude windows din sosai iska ta shiga zagaye lungu da sako na dakin, yana tsaye ya zura hannayen sa yana kama yayyafin dake sauka kadan kadan. Cikin dan kankanin lokaci dakin yayi sanyi, ruwan da aka farayi da karfi yasa ya sake rurrufe glasses din windon ya saki curtains din. Da sassarfa ya hawo gadon ya kwanta yana ware hannuwansa. "Alhamdulillah, ni'imar Allah ta sauka." Ya furta yana mirginowa waje na. Shiru mukayi dukkannin muna sauraron saukar ruwan da karfi a nutse babu hayaniya, irin ruwan da za'a iya kiran shi da peaceful rainfall, babu tsawa babu tsananin iskar nan, hakan ya haifar da wani yanayi a tsakanin mu. Shirun da mukayi kowa da abinda yake ayyanawa, a daidai lokacin Ya Farouk na fama da zuciyar shi akan abinda take kokarin bijiro mishi dashi, duk kuwa da alkawari ne ya dauka wa kansa, amma a yadda yake ji yanzu, tabbas baya jin zai iya cika shi, yadda zuciya da ruhin sa ke azalzalar sa, da ingiza shi zuwa abinda ba haramun bane, sai dai shi din daya haramtawa kansa, bisa wani dalili nasa da yake ganin hakan shine daidai. Sake mirginawa yayi yana kokawa da zuciyar tashi, kaso saba'in cikin dari na tsarin zuciya da ruhin shi sun aminta da abinda yake ji ɗin, yana ganin ba zai iya kuma bata wasu dakiku ba tare da aiwatar da abinda suka riga suka yanke masa ɗin ba. "Princesssssss?" Ya kira ni yana sake matsowa. "Kina jina?" Ya sake maimaitawa yana lalubar hannu na. Runtse ido na nayi ina jin yadda numfashin sa ke sauka bisa saman fuskata. "Uhum." Nace ina kauda fuskata gefe yadda yage faman zagaye hannun sa a saman fuskar tawa. "Alhamdulillah." Ya ambata a chan kasan makoshinsa wanda ba karamin me kunne ne zai jiyo shi din ba. "I can't hold it anymore." Yace yana kokarin chanja karatun dana sani wanda na riga na gama dauka a wajen sa zuwa wani sabon shafi na daban. Tuni kwakwalwata ta tsaya tsak, ta daina aiki, komai ya shiga chanjawa, a hankali komai yake tafiya har zuwa sanda abubuwan suka sauyawa baki daya. Shafin rayuwa ta na baya ya sake maimaitawa kansa a karo na biyu a siga ta daban. ****Yar karamar ƙwaƙwalwa ta ta gaza aike min da komai zuwa ilahirin sassan jiki na, baki daya bani da kuzarin aiwatar da komai, na gaza tantance abinda nake ji a halin yanzu, karar kafuwar hakora na kawai ke tashi waje daya, tuni zazzafan zazzaɓi me cike da ma'anoni da yawa yayi min rufdugu, ina jin shi yana magana, da dukkan kalmar da zata zo bakin sa, kokari yake yaga ya fahimtar dani komai, bana fahimta, ba kuma zan fahimta ɗin ba. Kalma daya kawai nake iya tantancewa "hakuri" kalmar da yake ta nanatawa kamar a bakin sa aka halicce ta. Da kyar na bude baki nace "Zan sha ruwa." Da sauri ya tashi ya kawo min, ya taimaka min nasha, sannan ya gyara min kwanciya ta yana kara nanata kalmar hakuri. Bansan sanda bacci ya dauke ni ba, bacci me dauke da ma'anoni da yawa. A yau na sake taka wani mataki na rayuwa, matakin da ba zan iya sanar daku da yanayin da yazo min ba, abu daya na sani, yana cikin manyan matakan rayuwata dana gaza mantawa. ***Komawa ta makaranta ta ruguje, babu wanda ya tuna da hakan tsakaninmu, zuwa da safe naji dama dama, da taimakon sa na samu na sake komawa bacci a karo na biyu, wanda ban samu farkawa ba sai da rana ta daga sosai. Da fuskar sa na fara tozali, yana zaune a gefe na cikin shigar sabuwar shadda fara kal tana sheki , kansa babu hula kamar ko yaushe, yayi kyau ainun, da sauri na maida ido na na kulle. "Good morning My Dee." Ya ambata yana min peck a saman kuncina, dariya na saka ina rufe fuska ta da tafin hannu na. Tashi yayi ya fita, hakan ya bani damar saurin fadawa toilet, na sake gyara jikina da ruwa me dumi, kayan jikina na mayar na dora hijabi akai na fito, yana zaune gaban sa da babban tray, wuce wa nayi na dau doguwar rigar atamfa me karamin hannu na sake komawa toilet din na saka na dauro dan karamin mayafi a saman kaina na fito. Breakfast din ya tura min gabana yana ciro wasu jerin magunguna daga cikin leda. Sosai naci abincin ya bani maganin nasha na koma saman gado na kwanta. Shi ya tattare kayan ya fita dasu sannan ya sake dawowa dakin.   Kwana biyu muka yi a haka, komai shi yake mana, sosai nake jin kunyar sa, shi kuwa babu ruwan sa, budirin gaban sa kawai yake, a kwana na ukun ne aka matsa masa da kira, dole ya fara shirin tafiya nima na hau nawa shirin dan ma tuni yayi waya da principal dinmu.   A tare muka fito gaba daya, muka dau hanyar makarantar mu, har muka isa hannun sa na cikin nawa, da kyar ya kyale ni na tafi bayan doguwar sallamar da muka tsaya yi.   Sanda na dawo har sun fara wasu subjects din, haka na yi joining aka cigaba dani, kullum dare da tunanin sa nake kwana, dashi nake tashi, duk da hakan ban bari ya shafi karatu na ba, dan ina so yayi alfahari dani. Munyi waya sau biyu a wayar principal, daga ranar ban sake magana dashi ba. Bayan sati biyu muka fara Waec, tuni kaina ya dau zafi na ajiye komai, sai dai kullum da matsanancin ciwon kai nake kwana, nake tashi, a haka nake daurewa nake karatun. Wata guda muka dauka da yan kwanaki muna jarrabawar, a ranar da mukayi ta karshe ne jikina ya kara rikicewa, ban iya fitowa daga examz hall ba, sai da wasu seniors suka taimaka min zuwa clinic din makaranta. Tashin farko ta sani zuwa nayi fitsari na kawo a yar wata container, haka nayi fitsarin na kawo, ta rubuta min wasu magunguna tace su rakani hostel, gobe kafin mu tafi gida sai nazo na karbi result. Haka na koma hostel na kwanta, ban iya aiwatar da komai ba, sosai nake jin jiki, a daddafe nayi bacci har gari ya waye, wata roommate dina ce ta taimaka wajen karasa hade min kayana waje daya.   A nutse nake tafiya har na isa clinic din, Ina zuwa na samu waje na zauna dan bata ƙaraso ba. Can ina zaune tazo, tana gani na ta sakar min fuska "Shigo ciki ko." Ciki na shiga ta ban kujera na zauna, envelope ta ciro ta mika min "Test ɗin da akayi miki baya wani daukar lokaci, ina so dama nayi magana da principal ne shiyasa nace ki dawo yau, toh munyi magana ma kuma dai babu wata matsala tunda dama ashe kina da aure ko?" Daga mata kai nayi ina juya takardar hannu na. "Ok Masha Allah, Kinga sai kiyi rainon cikin ki a gida cikin kwanciyar hankali.' Kaina ne naji yayi wani gingirin, na bita da kallo kamar wadda bata jin Yaren da take min. "Yes! You are pregnant." Ta fada tana murmushi, wani yar naji tun daga kaina har tsakiyar kafata. Ni kuma? Ciki? Ikon Allah. Tashi nayi na mata godiya na dau magungunan data bani na fito. Sai na rasa ina zanyi, nayi ta zagaye saman barander daga farko zuwa karshen ta, ina kallo ana yayewa daya bayan daya, har ya zama na kowannne dalibi ya tafi, saura ni kadai. Tun ban fara damuwa ba, har abin ya fara damuna, ina tunanin abinda ya tsaida Ya Farouk, bayan yasan yau ne ranar, ranar dani dashi muke jira, ranar da yayi min alkawari da dama akan ta. Waje na samu daf da kayana na zauna ina kallon kofar. A hankali aka zuge gate din, wata bakar mota ta shigo, baka ganin komai na cikin ta saboda glass din ta me duhu ne. Tsayawa naga anyi daf da security man din dake tsaye daura da gate din. A hankali glass din motar ya shiga sauka, hannu ne ya fito, rike da wata farar takarda, hannun na mace ne, dauke da jerin awarwaraye masu matukar kyau da sheki. Takardar da mika wa security man din tare da sanar dashi wani abu. Ina kallo ta maida glass din motar ta rufe, ta juya ta fita daga cikin makarantar da mugun gudu. Ganin security man din ya nufo ni yasa na tashi ina sake riƙe takardar result d'ina, yana zuwa ya mika min takardar cikin harshen turanci yace "Sakon ki ne inji Farouk." Karba nayi hannu na na rawa, na bude ido na ya sauka akan abinda ke rubuce baro baro cikin manyan harafi. A take naji kaina na juya min, na fara ganin komai biyu- biyu, dafe kaina nayi da dukkan hannu na na kwalla kara da ta cika makarantar baki daya. Daga nan bansan me kuma ya sake faruwa dani ba. Rano ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER* 07067124863 *Ko kuma* 09032345899 *ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽 https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo                       ***