[29/02, 19:22] Zulaihatu Aliyu:                     DA KAMAR WUYA                             Part 1       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited.......   Bismillahir Rahmani Rahim Dukkan yabo da godiya sun tabbata GA Allah, mamallakin duk kan komai da kowa. Ina rokon Allah da ya bani ikon fara wannan littafi, ya bani ikon kammalashi, ya bani ikon isar da dunbin sakon nin dake cikin sa. Ya bani ikon kammala daya littafina mai suna kuskurenmu, ya bamu ikon daukar darussan dake ciki. Dedicated to all the one read my story......... "Hubby please kar ki ci masa abinci, kin san yau full day ne, ya kike so yayi, kinsan baya cin abincin kowa a school din nan. Harararta tayi " ai dama haka nake so, kinga jikinsa zai gaya masa kenan. Zai ji anani burdade yau. "amma dai kin san abinda kikeyi bakya kyautawa ko? Koba komai ai ke babbace, bai kamata ki dinga cin zalin yaron mutaneba don kinga kawai baya shiga saugarki. "Kinga yusra ya isheki haka!!! Ke bakya ganin irin rashin mutuncin da yake min ne. A matsayina na yayarsa ban isa ya gaisheni ba, sai wani ji da kansa yake kamar baya kashi. Ai ko don junaid ya dinga girmamani. "Wow!!! Hubby ki rage son girma, kin San halinsa ba kowa yake kulawa ba, me yasa zaki damu kanki? Banza hubby tayi da ita, ta ci gaba da cin jollop rice din da tasha hadi, ga kifi nan Manya Manya, yamafi rice din yawa. " dan banzan yaro, shiyasa kullun yake Kara kumatu. Dole yaki cin abincin jamaa, don shima kar aci nasa. Kin San kalar dadin abin cin nan? Ta fada tana gutsuran kifi, ko cokali bata bukata ba, don tunda taga abincin miyanta ya tsinke. " kice dai yau kwadayinki ya motsa " "Kema da kinsan kalan dadin abincin nan da baki ki ci ba. Dagaji girkin maman Aliyu ne, bana yan aiki bane. Dan Menan yaro yana wahalar min da innah. "kyadai ji dashi, Allah yasa ya zo ya sameki, kina cinye masa abinci. Dariya hubby tayi, da dai wani ne, ba wannan muskilin banzanba. Ya kamata ki hakura haka, kija girmanki, kinga shi kwata kwata bakya gabansa. Rufe curler din tayi, bayan ta cinye abincin tas, ko kwayar rice bata bari ba. Duk da ji da take cikinta kamar zai fashe, don koshi. Oya muje in wanke hannu Kafin a dawo class. Ta fada tana lashe hannu. " naga ranar da zaki canza? Har yau halin yan kauye bai bar kiba. Yusra tace tana binta a baya. " naga dai duk tsiyar mutun asalinsa kauye ne. Ke barima kiji, ni wallahi da zaa Mai Dani kauyen dana fi farin ciki. Inda zan sakata in wala, in tsula tsiyata yadda nakeso. Nayi missing kakus fiye da zatonki. Har yajin aikin cin abinci nayi,  amma mutanen nan, ko a jikinsu. Sai da naga haza, in na mutu basu da asara  tunda bani kadai suka Haifa ba. Yasa na dawo aikin cin abinci. Don lokacin har na fara ganin kamar kowa ma farin kaya yasa a jikinsa. Kin ga alamar mutuwa ta matso kenan.. Dariya yusra keyi harda rike ciki. " ke din ce zaki iya wani yajin cin abinci?  Azumi ma da yaya kike kaiwa, balle ba'a azumi?  Suna fita class din, su kuma suna shigowa.  Wani hadadden matashi na gani, Wanda bazai wuce shekara sha biyar, zuwa sha shida ba, yana sanye da kayan kwallo na kamfanin NIKE farare,  kafarsa na sanye da farin canvas shima na kamfanin NIKE da farar safa. Fari ne sosai, yanada tsayi,  bayi da jiki. Amma da gani za'ayi hadadden guy mai kyan jiki,  da kira. Kyakyawane na bugawa a jarida. Fiskarsa doguwa,  Mai dauke da dogon hanci,, ma-dai -dai tan ido,  masu matukar haske, sai Dan madai daicin baki , mai dauke da jerarrun hakora,  farare tas,  gasu sunada tsayi kwanin sha'awa. Yanada dimple both side din fiskarsa. Gashinsa bakine sidik, mai matukar laushi. Wanda yasha gyara. Yanada gashin gira baki Mai yalwa, ga baki, gashin idonsa kamar anyi piecing din su. Shine a gaba, sai sauran tawagar student din. Ko wanne da kayan kwallo a jikinsa, duk sun hada zufa. Alamar daga field suke. "Anty -Anty Allah ya bar mana Anty. Wasu daga cikinsu suka fara fada ganin hubby da ke fitowa a class din. Hararar na gaban tayi,  Kafin ta wuce abinta,  yusra na binta a baya. Ko kallon inda take baiyi ba ya wuce locker dinsa. Kayansa ya gani a bar baje, da sauri ya karasa wurin.  Da food placks dinsa ya fara cin Karo. Ganin ba komai a ciki,  yasashi mai da hankalinsa kan kayansa. A can gefe ya hango rigar uniform dinsa. Daukowa yayi. Dubawar da zai yi duk shatin mai da alamar da rigar aka goge hannu,  bayan an cinye masa abinci. Wani bakin ciki da takaicine ya lullubeshi. Don yasan duk fadin school dinnan. Habiba (hubby) ya rasa mai ya tsare mata a rayuwa, ta takura masa. Shi ba shiga harkarta yake yi ba, duk da tana yar uwarsa. Zai iya cewa jinin sa bai hadu da nata ba. Shiyasa ko kallo bata ishe shiba. Don shi haka yake,  in ransa baya son mutun no matter how close they are. Ba ruwansa dashi. In ka girmeshi dai zai gaishe ka,  amma banda gaisuwa ba zai taba yadda wani Abu ya hada ku ba. Ita din yayar sa ce, a kalla ta bashe good 6year's,  but amma yanayin childish behavior dinta yasa ko kallonta baya son yi. Don ba karamin haushi take bashi ba. Kafadar sa da aka dafa,  yasa shi waigowa.  Daya daga cikin student din ne, " I'm very sorry broth " ya fada da yanayin damuwa a fuskarsa. Murmushi ya kago " never mind, it's OK " ya fada, tare da tattara kayansa. Wanda ya dafa shin ne ya miko masa shirt " take this. I were the one she spoil" " no I will manage. Zama yayi kan sit dinsa. Food Plack's student din ya ajiye akan table din,  tare da Jan yo kujera ya zauna. " please haydar kar kace min bazakaci abincin nan ba. Murmushi Wanda aka Kira da haydar yayi.  Junaid you know me very well, I'm not eat that food. " so what do you eat? Jakarsa ya dauko ya fito da dairy milk, Wanda ya tabbatar bata gan shiba da bai tsira ba. Ya fara ci. I will manage with this. Girgiza Kai junaid yayi,  yana jinjina halin abokinshi kuma Dan uwansa, A ransa. Duk yadda junaid ke jin yinwa, ganin Dan uwansa bai ci komai ba, yasa shima kasa cin nashi abincin.  "Have some" haydar ya fada yana Mika mishi chocolate din. Tsaki junaid yayi,  tare da hararar chocolate din. " amma kasan you have a problem ko? Murmushi yayi,  ya ci gaba da shan chocolate din shi. Ransa ba dadi, har aka tashi daga school.              ******************* Alhaji yusuf zubair Oregon. shine asalin sunan kakansu.  Dan a salin kasar Lebanon (Lebanese ) middle East. Wanda take boda da Syria, Israel da kuma Cyprus. Aiki ya kawo yusuf garin kaduna. Wanda Allah ya kaddara zamansa a nan. Matarsa Hajiya Aisha Aliko. Haifaffiyar garin kaduna ( malali) sai yaransu uku: jamal,  jamil, omer. Mutun ne na mutane. Yanada arziki dai dai misali.  Bayan ajiye aikinsa ya koma harkar restaurant Wanda dama tun yana aiki ya Fara bude su. Kammala karatun Jamal na degree, yasa shima ya fan tsama sanaar mahaifin nasa. A yanzu Alhaji jamal nada matan aure uku, : Hajiya Hadiza mai yara biyar.  Ummu kulsum, ummu Aiman,  ummu sulaim, ummul khair,  sai auta Aliyu haydar.  Sai Hajiya Amina mai yara uku : samirah, Ahmad, Abdulkharim . Sai Hajiya saadatu Mai yara biyar : yusuf,  Abdul majid,  Abida,  Aisha,  Airah. Alhaji Jamal yanada arzkiki sosai, shine mamallakin gidajen abinci,  da ake ji dasu a jahohin Nigeria,  wato eat more restaurant. Mutun ne mai son addini,  Wanda yakewa addini hidima da dukiyarsa, da karfinsa. Ya na son jamaa. Mutun ne mai jin kan iyaye, da kula da hakkokinsu,  mutun ne jajirtacce adali mai kyautatawa iyalansa. Sai dai fa in ka tabosa akwai fada 😎 akwai doka da oder sosai a rayuwar gidansa. Alhaji jamil maaikacin currant affairs dake Abuja. Rikakken dan boko,  amma Wanda aka surka da ilmin addini 😊 yanada arziki dai dai misali. Yanada mata daya Hajiya maryam, da yara hudu : Aslam, Aaryan, Aashir,  Abdul Alim. Rayuwar gidansa rayuwace ta wayewa. Amma ba wadda ta kauce sharia ba. Alhaji jamil nada kirki kamar Dan uwansa. Sai Alhaji omer business tycoon.  Mazaunin Lego's duk ya fisu dukiya. Yana da mata biyu Hajiya Zuwaira da yara hudu: Aisha (nana) Asima, Asiya, Asnah. Sai hajiya Bilkisu mai yara uku : Arif (omer), Abdul fatta, Abdul Hafiz.  Mommy Hauwa kanwace a wurin Hajiya Hadiza. Su biyu iyayensu suka Haifa, suna kanana Allah ya yi musu rasuwa.  Sun taso a hannun kanin babansu, Malan tsalha. sun samu tarbiyya  dai dai kwarkwado, da ilmi na addini dana boko. Duk da kalubalen da suka samu da maidakin nasa umma larai. Bayan auren Hadiza da yan watannin ta dauke kanwarta,  ta ci gaba da kula da ita. Anan Allah ya hada Hauwa da Munir, abokin omer ne tare sukayi karatu a malesia. Shi dan ainihin katsina ne,  cikin kankiya local government. Yana zuwa Hutu kaduna wurin yayyen mahaifinsa da ke nan kaduna. Kasan cewarsa aboki na kut da kut ga omer,  yasa kowa ya sanshi a family din. Ummu Habiba ita ce yarinyarsu ta farko,  sai jabir, jafar sai junaid Wanda yake sa an Aliyu. Ummu habiba ta taso wurin kakarta,  wadda ta dauketa a nono. So ko bayan ta isa makaranta gwaggo kin dawo da ita tayi. Munir shi kadai suka Haifa,  daga kansa basu sake haihuwa ba. Wannan yasa ta ki mayar musu da habiba. Rayuwar habiba a kankiya,  rayuwa ce ta ba sawa ba hanawa,  abinda take so shi gwaggo ke mata,  don ma Alhaji kawu na taka musu birki, in yaga abun yayi yawa. Rashin kunya,  tsokanar fada,  Rashid son karatu,  kazanta, duk halin habiba ne. Batajin magana ko kadan,  ga dan banzan barna. Tanada shekara goma,  amma har lokacin ajinta uku,  a primary school duk da kyan makarantar,  amma rashin maida hankali a karatu yasa ake mata repeating. Ko kadan bata kaunar zuwa kaduna wurin iyayenta Hutu. A cewarta sun cika takura. Ganin haka gwaggo tace ba mai takura mata, tunda batason zuwa a gyaleta. Wannan halayya na habiba na cin ran iyayenta. Musamman ta bangaren karatu. Habiba Nada shekara sha hudu sai lokacin ta gama primary school duk abokanta suna ss 1,  wasu na js3. Ganin haka ya sa Alhaji kawu budewa gwaggo wuta, kan ta mayar da habiba, GA iyayenta, don ya Lura in ya ci gaba da zuba ido abun ba zaiyi kyau ba. Don habiba bata son Karatu ko kadan,  Sai tayi sati bataje school ba. Shi kuma ba mazaunin gida ba,  in ya fita Sai yamma can,  koma dare. Da kansa ya dauki waya ya Kira Munir,  yazo ya dauki yarsa. Da kuka da birgima haka suka nufo kaduna. Suka bar gwaggo cikin matsar hawaye. Don ba kadan ba take son habiba. Har ciwo tayi na rashinta. Lokacin jabir da jafar  sunyi exams din jsce.  Junaid na js1.  Dakyar suka samu aka dauketa a js1 saboda ko spelling mai kyau bata iya ba,  bata iya karatun Hausa ba ma balle English.  Sun amsheta da sharadin zaa nema mata lesson teacher.  Aji daya aka sata da su junaid da Aliyu. Son girma, mu samman da taga duk ajin ta fisu shekaru, duk da bata da girman jiki. Wannan yasa duk ta fitini kowa, musamman in zaka ganta kaki gaishta,  ko ta kamaka kana mata dariya,  in an tambayeta amsa bata sani ba,  To ka shiga uku. Kusan ko yaushe a cikin fada take,  ba maza ba mata. Dole yasa suke ce mata anty don gudun jarabarta. Duk wannan abun da takeyi ko kallo bata ishi Aliyu ba, so da yawa har desk dinsa zata zo, ta duddungure shi,  tana masifa,  ko daga kansa bazai yi ba balle yasan tanayi. Wannan shi yake Kara bakanta mata rai,  baya ko kallonta,  balle ya gaisheta kamar yanda yan ajin keyi,  ko anty din ma bata samu arzikin sa ba. Ko a gida suka hadu,  shi yazo ko ita taje, Ba ruwansa da ita. Tasha Kai kararsa wurin mommy da Haj amma ba abunda ya canza. Wannan shi yasa tadau damarar yi masa rashin mutunci,. Tun daga lokacin ta maida rayuwarsa living he'll.. Sai dai abinda ke Kara bata haushi har yanzun nan da suke Shirye shiryen zana final exams dinsu, bai taba tanka duk abinda zatayi masa ba. Wanda ita ba haka ta so ba. Aliyu najin zafin abinda take masa,  amma kullun maganar Haj in ya gaya mata, shine yayi hakuri,  ya rabu da ita, in ta gaji zata daina abinda take masa. Kuma yar uwarsa ce bai kamata ya biye mata suna fada ba. Duk da ta zubar da girmanta to shi ya dauki girman yayi hakuri.              ********************* School bus dinsu na shigowa, bai tsaya baba ya Gama ko parking ba, ya Saba jakarsa ya balle murfin motar ya fito. Da kallo baba da sauran kannen nasa suka bishi. "Shida mutuniyar ne ko?" baba ya tambayi su abida. " kai ma kasan Sai ita,  don yaya bashi da abokin fada. Aisha ta ce tana Saba Jakarta. "kai wannan yarinya,  Allah ya yi fitinanniya. Baba ya fada Da Yaya Ahmad sukaci Karo,  yana fitowa. "Sweet broth well come " " thanks " ya fada yana kokarin wucewa ciki,  ba tare da ya Kalli yayan nasa ba. " what happened to you?  Ahmad ya fada yana juyo dashi. Ganin yadda yake faman huci,  yasan ran kanin nasa a bace yake. " I'm sick and tired of that useless girl, I have to teach her a big lesson of her life. Murmushi Ahmad ya yi,  don yasan yau ma an kuma. " me kuma tayi yau? " she finish my food,  don wulakanci a jikin uniform dinsa ta goge filthy hands dinta. Dariya Ahmad yayi, " lallai wannan yayar taku,  bata kyauta ba. " Ba yayata ba. Allah ya kiyaye inyi yaya da wannan good for nothing din. " don't say that.  Ni na rasa gane meye yake hadaku, ko kana mata wani Abu ne da bata so? " me zan mata,  yarinyar da ko kamarta,  bazan iya tan tan cewa ba. Daga yanzu na daina kyaleta, zan gwada mata nawa rashin mutuncin. Dama hajiya ke cewa inyi hakuri, da tuni nayi maganinta. " Aa Aliyu, ko Ba komai taci albarkacin mommy da junaid.  Zan sameta zamuyi magana. Zuwan su Aisha yasa suka katse zancen,  ya shige part dinsu,  yabar Ahmad suna gaisawa da su Aisha. A falo ya samu hajiya da mmn samira.  Suna duba wasu lessis da aka kawo na siyarwa. Gaishesu yayi,  ya wuce dakinsa.  Mmn samira ta Kalli hajiya, yaya yau mutumin naki,  a sama yake.  Tabe baki hajiya tayi " nasan baya wuce shida habiba,  na rasa me yasa basa iya zama inuwa daya. ita son girma,  shi kuma kinsan halinsa sarai. Murmushi mmn samira tayi " lamarin Aliyu sai shi. Na dauka yana girma abun na raguwa,  amma kullun gaba yake karawa. " kedai bari,  nayi fadan,  nayi dukan duk a banza. Addua nake masa Allah ya yaye masa wannan halayya. Fitowa yayi, ya wuce main kitchen. A nan ya tarar da mmn yusuf na kokarin daura abincin dare. Gaisheta yayi cike da girmamawa.  Murmushi tayi " haydar an dawo?  "Eh " ya fada yana bude fridge. " ga abincinka nan,  yanzu nayi worming. Tana nuna masa microwave. " thanks,  you are the best.  Ya fada bayan ya dauko bottle water da maltina. Bude microwave din yayi ya fito da plate din.  Murmushi yayi saboda favorite dinsa da ya gani. " Wow!!!!  Na gode sosai, kamar kinsan yunwa sosai nakeji, ina bukatar favorite,  don inji dadin ci. Murmushi tayi. Shigowar hajiya ya sa ya dauki plate dinsa yayi gaba, da harara ta rakashi.  Kafin ta maida kallonta zuwa ga mmn yusuf da ta ci gaba da aikinta,  ba tare da tako Kalli hajiyar ba. Tsaki taja, ta wuce fridge ta dauki abunda zata dauka ta fita.......... [29/02, 19:22] Zulaihatu Aliyu: 💐DA KAMAR WUYA💐                             Part 2       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Falon da yake mallakin yaran gidan ya nufa. Su Anty khulsum ya samu a folon suna kallon series a Tashar zee would. Sallama yayi, ya wuce dinning ba tare da yace musu komai ba. Suma bayan amsa sallamar da kallo suka bishi, har ya zauna a kan kujerar dinning din,  ya fara cin abincinsa. "Muskili kafi mahaukaci ban haushi, wannan dashi aka fara haifa a gidan nan da mun bani" cewar Anty Aiman. "da gani yauma wani ya taboshi" sulaim ta fada idonta a kansa.  " brother ba gaisuwa? Kamar bazai amsa ba,  da dago ya kalleta " nayi sallama " yace a takaice yaci gaba da cin abincinsa. " munsan da kayi sallama, amma ka gaishe mu ko? Anty khulsum ta ce tana harararsa. Abincinsa ya ci gaba daci, ko dago Kai bai yi ba,  balle tasa ran zai amsata. Khair ce tace " haba haydar ba dakai ake magana ba,  kayi mata banza. Harararta yayi, don duk cikin yayyen nasa yafi rainata, saboda shi yake binta.  " sallama itace wajibi kuma nayi.  Ya fada Tsaki tayi Allah ya yaye maka mugun hali,  wata rana ayi abun arziki dakai wata rana iskancinka yafi na tsohuwar mota.  Khair ta fada tana harararsa, wanda bai ma San tanayi ba. " naga dai mmn yusuf aiki take a kitchen, ne makon kuje ku tayata, kunzo kuna kallon abinda bazai anfane kuba "  ya fada yana kallon su " Zanci gidanku kam yanzu,  mu Kake gayawa muje muyi aiki a kitchen?  Anty khulsum ta fada cikin fada da jin haushinsa. " zo ka kwashemu ka kaimu,  Dan ban zan yaro, Mara kishin uwarsa. Sulaim ta fada Bakin shi ya tabe, tare da daukan plet dinsa yayi waje. "Allah yaron nan sai hajiya ta tashi tsaye a kansa, in ba hakaba wata rana cewa zai Ba ita ta haifeshi ba.  Khairi ta ce Anty Aiman tayi murmushi "lamarin haydar sai a hankali, tunda kunsan halinsa, meye na tada jijiyar wuya, wani irin fada ne hajiya batayi ba,? amma me ya canza?  So ku Dena bata bakinku a banza. Sallamar su Abida, ya katse maganar da sukeyi.            ******************** Hajiya hadiza (hajiya) uwar gida a gidan Alhaji Jamal. Auren hadi aka musu da ita. Mahaifiyarsa ta zabo masa ita, kasan cewarsa mai biyayya ya amsa da hannu biyu. Matace mai kirki dason jamaa,  but akwai son iko, da nuna isa.  Bayan aurensu da she kara biyar,  ya auro Hajiya Amina itanma kusan zamu iya cewa hadine yar aminin babansa ce.  Mata mai hakuri,  da biyayya. Duk iya abunka baka taba ganin bacin ranta.  Haihuwarta daya ya auro Hajiya saadatu itan ma hadi ne, kanwar abokinsa ce dake Niger.  Akwai kirki, sai dai bata daukar raini. Hajiya hadiza da Hajiya Amina kansu a hade yake, koda Hajiya saa tazo, sai ta zama wararriya a cikinsu.  Ba shiri ko kadan tsakaninta da uwargidan. In kaji fada ya tashi, ko ana sulhu to tsakanin hadiza da saa ne. Don ita Amina bata da abokin fada a tsakanin su. Tun tasowar haydar Allah ya hada jininsa Dana Hajia saa, yana sonta. Haka favorite brother dinsa yusuf, yaronta na farko,  suna matukar shiri. Wannan Abu na matukar bata ma hajiya rai,  tayi fada har duka amma ba abunda ya canza.  Musamman ganin duk yadda take da Hajiya Amina amma haydar gaisuwa ne kawai ke hadashi da ita. Duk da kirkinta mu samman akan shi.                 ****************** Still hajiya da mmn samira ya samu, a falon hajiyar.  Dakin sa ya wuce ba tare da ya ce musu komai ba,  bayan sallamar da yayi. Suma gaba daya hankaalinsu nakan kayan da suka zaba, don bikinsu anty khulsum ya matso. " to yanzu zamu kirata ta duba ne ko ya zaayi?  Mmn samira ta tambaya.  Hararar mmn yusuf tayi " kin jiki da maganar banza, kedai ba kin zabi naki ba?  Sauran da suka rage,  zan aika mata, ya rage nata kuma. " bakya gudun tace bata so,  har maganar taje kunnen Alhaji?  Kin san abun bazai yi kyau ba. " ke dai wallahi anyi matsoraciya, mai jiya tayi balle yau?  Naga mune gaba da ita a gidan nan. " haka ne, amma kin san bata raina abin fada. Kuma ya kamata in ma zamu Fara zaba, mu zaba a gabanta. " Tsaki hajiya tayi, tare da harararta" an dai ji haushi,  kwashe sauran kayan in kin kai ta zaba sai ki dauki sauran."  Aliyu ta kwalawa Kira. Fitowa yayi bayan ya amsa, fuskarsa Ba faraa, don yana jin duk abinda suke cewa, ya rasa wannan kishi dake damun hajiya. Abu yaki karewa tun kuruciya,  gashi har an Fara manyanta. Amma kullun sabon rigima suke bullowa dashi. Ganin yanayin fuskarsa yasa ta harareshi,  " kwashe kayan nan ka kaimin daki ". Ta nuna masa kayan da ta zaba. Kallonta yayi yana son yayi magana,  amma baiga fuska ba. " zaka dauka ka wuce, ko sai naci gidanku,  a wurin nan " ta fada tana ci gaba da harararsa. Dauka yayi ya wuce dakinta dake kallon nasa. " kinga kwashe kayan nan, kiyi gaba" ta fada tana gyara zamanta Murmushi mmn samira tayi " me yayi zafi, shi ba wuta ba " " ai kece kina bani haushi wani lokaci" " Aliyu dauki kayan nan ka kaiwa mmn yusuf" mmn samira ta fada tana nuna masa kayan da suka rage a gefe. Ranshi bai so ba, ya dauka ya fita. Can Sai gashi da kayan,  " tace bata so, ku hada duka" ya fada yana ajiye kayan inda ya dauka. Mmn samira ce ta Kalli hajiya " kinga dama abinda nake fada ko? Murmushi hajiya tayi " wannan kuma ya rage nata, kaya dai dole ta amsa,  in bataso Sai ta bari, in wanda ya ajiyeta ya dawo, ta mayar masa, don ni kam na riga na zabi nawa" Kayan ta zuba a Leda, ta fita zuwa kitchen. Har lokacin mmn yusuf na ta kokarin hada abinci, don hajiya ta aiki Mai tayata aikin, duk don ta kun tata mata,. Su abida da ke taimakonta yau basu dawo school da wuri ba,  gashi kuma kowacce ta dawo da home work. So dole ita kadai take aikin, don tasan ko zata mutu su khulsum bazasu tayata ba, saboda suna taya uwarsu kishi,. Sannan don kuturun wulakanci Alhaji ya aiko da kaya amma bazasu kira ta ba, sai sun gama zaba sannan don sun rainata su aiko mata da abinda sukaga dama. " to sababbiya, gashi nan in Wanda ya aiko da kayan ya dawo ki mayar masa, don nikam bazan ajiyesu wurina ba. " hajiya ta fada tana jefa mata ledar can gefe. zuciyar mmn yusuf ne ya fara tafasa, ba don komai ba sai jifo kayan da hajiya tayi. Cikin bacin rai ta juyo tana kallonta. " Allah sarki duk inda akayi da jaki, sai yaci Kara, kin dai san gidan da na fito?  Ke kaya ya dama, da har kike wani takama akai,  ki hada da naki ki rike, banso, kin San zan iya siyan dubunsu in har naso, ke kike fatarar kaya. " tayi tsaki ta juya don ci gaba da aikinta. " kam bala'i, ni kike gayawa wannan maganar, dadin abun mun san komai, balle a mana fiffika, gidanku yafi gidan mune?  Da har kike wani ikirarin ansan gidan da kika fito?  Muko muka san gidan da kika fito. Dadin abun da gidan uba ake tinkaho,  Ba gidan yaya ba. Kaya kuwa in kinga dama ki zubar a bola, bai daman ba. Dole inyi tinkaho da kayan mijina, ba Wanda zan siya da kudin da nayiwa yayana yar murya ba.  Banza karya tseeeee!!!!!!! " ni kike kira karyar?!!!!!!  Mmn yusuf ta fada tana nuna kirjinta, cike da bacin rai Dariya hajiya tayi, "au!!!! Da kin dauka da WA nake?? " kun kyauta, nawa tukuicin kenan, ina can ina Nemo muku abinda zakuci kuna nan kuna tona min asiri" Alhaji Jamal da ya shigo tun fara hayaniyar tasu,  ya tsaya yana jin duk abinda suke yi ya fada cikin tsananin bacin rai. Juyowa sukayi a tare jin muryar mijin nasu............. "sannu da zuwa" hajiya ta fada cikin rawar murya, ganin yadda ransa ke bace. Harararta yayi,  yayi tsaki ya wuce part dinsa. Itama tsakin tayi ta koma falonta. Mmn yusuf ta ci gaba da aikinta, cikin bakin ciki, da bacin rai. Don bata so abin ya tsaya a haka ba 😎 duk da tasan magana bata mutu ba.                 ***************** Zaune suke a falon Mai gidan, bayan sun kammala cin abinci. Yau gaba daya cin abincin ba armashi, don ran Mai gidan a bace yake dasu. " dauko min fruit salad din da nace ki hada min" ya fada yana kallon mmn yusuf. Shiru tayi kamar baza tayi magana ba " bari in je in hada. Yau aiki yamin yawa shiyasa ban samu yi ba. " ban gane aiki ya miki yawa ba?  Duk yaran dake gidan nan? " ya fada yana kallon ta " hajiya ta aiki ladi, su abida yau basu dawo da wuri ba, already kowacce ta dawo da home work, so I have to do it by myself " Kai ya kada cike da bacin rai. Su kam hajiya da mmn samira ba wadda ta tofa nata suka ci gaba da kallon news. Har ta kusa fita dakin, yace ta dawo ta zauna.  TV ya kashe tare da gyara zamansa, ganin haka, yasa kowacce shiga cikin natsuwarta. Hajiya ya kalla " meye maanar abinda nazo na samu kunayi dazu? Kallonta takai kan mmn yusuf dake zaune can gefen Alhaji. Itama kallonta take yi, harara suka aikawa juna. "dake nake " ya fada cikin daga murya " kayan da ka aiko mana ne, na aika mata da nata,  ta dawo min dashi wai bata so. Shine na dauka na bita dashi kitchen." Tayi shiru " sannan sai akayi me? " ya tambaya. " magan ganu ta fara gaya min ni kuma naga bazan iya yin shiruba na Meyer mata. Juyawa yayi wurin mmn yusuf " me yasa kika maida kayan bayan an kawo miki " " da aka kawo kayan, in da sun shirya gaskiya ai nima sai su kirani mu zaba a tare, in ma su zasu fara zaba, bazan damu ba. Amma basu kirani ba saida Suka gama abinda zasuyi suka aiko min da saura, bayan sun zabe, shiyasa nace ya mayar musu banso, su hada duka. " " ke Amina ya akayi? Ya juya yana kallonta. Shiru tayi ta rasa abun cewa, don ta tsani tashin hankali a rayuwarta. Da hajiya taji shawararta da duk haka bata faru ba. " kun kyauta. Amma ku sani bazan dauki wannan halin banzan ba,  na gaji da matsalarku, kun girma amma kullun abinku karuwa yake.  Yaran ku ake kokarin aurar wa, wannan shine tarbiyyar da zaku basu su dinga yi a gidan mazajensu? Ku dubeni da kyau son kowa kin wadda ta rasa, kyau, kudi, Hali mai kyau. San kacecen mutun Irina 😂 na kwasoku don in rufa muku asiri, ni kuke kokarin tona min nawa ko?  To kuji da kyau duk randa irin haka ta Kara faruwa, gaba dayanku Sai kun bar min gidana. Don duk cikinku ba wadda naje na makale a soron gidansu don neman soyayyarta. Balle ta zame min matsala a gida. Hajiya ce cikin bacin rai tace "kai kullun Abu ya faru Sai ka mana gori?  Naga ba masoya muka rasa ba, muma ai mun rufa maka asiri" " ja can ki rufe min baki. Duk samarin naku sun Kama kafata ne?  Shi yasa kuna ganina duk kuka rude, kunga hadadden yaro. Da nasan in na taimake ku abin da zakumin a gida ke nan da ban kwaso ku ba.  Mu samman ke da wannan yana nuna saa kunfi kowa matsala. Kuje ku kwaso kayan ku kawo min. Ina duk akan rabo ne fadan?  To zan raba da kaina. Tunda ni zaawa kwalliyar ko wacce nasan Wanda zai dace da ita." Dole kowacce taje ta dauko ta kawo masa.  Rabawa yayi da kansa ya dauka ya mikawa kowacce. " ku Ba kyau ba, Sai Dan banzan fitina, 😂 dole ne yanzu nima in kwas kware in Nemo sweet sixteen zabin zuciyata, ko na more, sauran kuruciyata. Duk kansu hararar sa sukayi, in da sabo sun Saba da halin mijin nasu. Duk ranar da suka bata masa rai, sun shiga uku da gori. " Ai wallahi kai kanka kasan duk cikin mu ba mummuna, Kai din ma banda fari mai zaka nuna mana" mmn yusuf ta fada tana tura baki kamar wata karamar yarinya. Dariya yayi ganin yadda suka Shaka, ko wacce ta cika tayi fam, banda mmn samira dake murmushi kasa kasa. " ke kam in ana magana, be kamata kisa baki ba, ki bar Amina tayi magana, duk da ita din ma in muna wuri, bata isa zuwa ba. Ku Bari ku ga zankada ziyyar da zan kawo muku. Tattaro min kan yarana " Ya fada yana kallonsu. " Allah ya kawo ta lafiya,  ta makara tunda ka zama saura, sai dai ta samu sidi. " hajiya ta fada cikin jin haushi Murmushi yayi ya tashi yana Dan jujjuyawa a gabansu " waya gaya miki na miji na tsufa?  Don baki san yanda yan mata keta kawo min Hari bane, Yanda kuka San zasu lashe muku ni. 😝 ba komai, zan nuna muku har yanzu irin mu ake yayi. Sallamar yaran nasu sukayi, suka basu izinin shigowa. Sun gaishe da iyayen nasu, suka nemi wuri suka zauna. Kallon yaran yayi cike da jin dadi, da alfahari " Masha Allah LA kuwwata Illa billah" ya ambata Kamar yadda ya Saba in ya gansu haka a hade. Kallonsu yayi ya nuna khulsum " meye cikakken sunan ki?  Kallonsa tayi cikin rashin fahimta. " ina nufin da wane suna kike bearing " "ummu khulsum jamal yusuf " Kai ya kada, haka ya dinga tambayar sauran ma kowa na fada masa. Bayan sun Gama ya ce " waye Jamal yusuf zubair Oregon? " Aaira ce tayi saurin cewa " kai ne mana daddy " Murmushi yayi, ya daurata kan cinyarsa " yau wa autan kaji" Kallon sauran yaran da suke sauraron abinda zai ce, don duk sun shiga rudani. "kun yarda nine dai daya ubanku ko?  Amsawa sukayi da "eh !! " " fine!!!  Na lura da wasu abubuwa dake faruwa a gidan nan, da zuciyata bazata laminta ba. Ni ne dai daya mahaifinku duka, kuk kanku daga tsatsona kuka fito,  kunga kenan Baku da ban banci, Ba nason halin yan ubanci da kuke son tsiro dashi, so nake naga kun hada kanku, ku so junanku don Allah, ku zama tsinstiya madaurinki daya, ku zama sirrin juna. Masu taimakon juna, da jin kan juna,  wannan shi nake bukata a cikin gidan nan. Ya juya wurin su hajiya " a matsayinku na iyayensu mata, zan so ku hada kawu nan ku, ku so juna don Allah, ku zama masu taimakon juna, da son ci gaban juna, babu bakin ciki, ba kyashi.  hadi kan ku shi zai tai maka wurin hadin kan yara na. Amma ku sani, muddin na ci gaba da ganin baraka a kan yarana.  Wallahi duk sai kun tafi gidajenku. Magana ta gaskiya kenan, bazan lamunce, ku raba min kan yara ba, zan gwammace in rabu daku, in Nemo waanda zasu kulamin dasu. Ban yadda yarana su raina daya daga cikin ku ba, wai don ba ita ta haifeshi ba, dole su girmamaku kamar yadda zasu girmama mahaifiyarsu. In har kuna son zama lafiya a gidan nan. Yan mata na, dole ne ku Saba musu da shiga kitchen, in dai suna da free time. Ba ban banci da wadda take girki a lokacin. Sannan daga yanzu har sati biyu Kafin bikin su khulsum, su zasu dinga girki a gidan nan. Kafin lokacin ko wacce ta samo Mai tayata aiki, ranar girkinta. Case close " In akwai Mai magana yana iya yi? Ya tambaya yana binsu da kallo. Duk jikinsu a sanyaye,  kowa yayi shiru. " OK kuna iya tafiya, ku kuma mazan ina da word daku " Fita su khulsum sukayi, bayan sunma iyayen sai da safe. Kallon shi yakai kan yusuf  " yah!!!  Ka gama shawarar? " Kai yusuf ya sun kuyar cikin jin kunya. A hankali ya kada kai tare da cewa " eh!!! Daddy " " good kana nan akan bakan ka ko ka canza shawara? " aa " "ka tabbata kana sonta, itama tana sonka? Kun dai dai ta? " "eh!! Daddy " ya fada cikin jin kunya. Su hajiya da basu San kan zancen Ba, shiru sukayi suna sauraro. " Masha Allah.  Wannan Abu yayi min dadi, Allah ya sa albarka a ciki. " Amin sukace gaba daya. " wai zancen me Kake yi ne?  Kun samu a duhu? " hajiya ta tambaya Murmushi daddy yayi " maganar yusuf da yar wurin Hauwa, habiba." " wace habiban?  Mmn yusuf ta fada tana zaro ido. " habiba dai daya da kika sani, yara sun hada kansu, tunda Ahmad ma ya fito da tashi, gara a hada gaba daya da nasu khulsum. "Tabdijam !!!!! Wallahi bazata sabu ba......... 😮😬   [29/02, 19:22] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 3       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau Har yaushe suka hada kan nasu, bamu da labari? Wannan Abu ba mai yiwuwa bane, garama tun wuri kar a farashi Daddy ne ya zabga musu harara " ku kuma asu wa? Da sai da amincewar ku sannan zan zartar da hukunci? To Bari kuji da kyau gida nane, yaya nane ba wadda ta isa ta kawo min matsala a abinda yake ba sabo bane, sunnar manxo S. A. W za a hada, kuke kokarin tada jijiyar wuya? To ku sani nafi kowa murnar wannan aure, ko ba komai ya zama ishara gareku in kuna da hankali. Ku tashi ku bani wuri, ya rage naku ku fara shiri, ko karku fara, ba abunda zaa fasa. " Samarin ne suka fara yin waje,. Mmn yusuf ta ce " gaskiya da sake. Bayan kasan da maganar hanifa (yar wanta) amma zaka yadda da wannan hadin gwarman "? Tsaki ya ja " matsalana daku rashin tunanin. Ita hanifan da kike magana a kai shi yace miki yana sonta? Hadinki ne, kuma dama na gaya miki ba auren hadi, ko dole a yarana, Wanda suke so zan basu, matukar ba illah a ciki. Hajiya da ta cika tayi fam, don fushi, hararar mmn yusuf tayi tare da ficewa a dakin cikin fushi. Itama mmn samira sallama ta musu tabi bayan hajiya. " tsakani da Allah, ba a min adalci ba, yanzu mai Kake son in gayawa yayah? " Cikin rashin damuwa da zancen nata ya ce " komai ma, kina iya fada masa " Ganin yadda ya hade rai Ba wasa a tattare Dashi yasa ta tashi ta wuce dakin baccinsa.... ******************** "Yan zu yayah zero head din nan zaka kwaso mana ? Haidar ya fada bayan sun iso farfajiyar gidan Dariya yusuf Da Ahmad SuKa yi ," yayar taka Kake Kira zero head " Ahmad ya fada yana dukansa a kafada " zero head ce mana, ban san ya akayi PC ya yadda ta zana waec ba. " "karka sake kiran wify Na zero head, she is your sister and sister in-law, so respect her for that " yusuf ya fada yana murmushi "ok, but ka sani bani a yan zuwa gidanka, Kafin nan ma I will teach her a lesson from tomorrow so that kar rainin yayi yawa Bayan ta shigo" " haba brother, don't say that, your my best, how can you be not coming to my house? " Ahmad ya fada yana dafa kafadar haydar " sorry I can't help it " haydar ya fada Ahmad yayi dariya "wow Yau Na ganku a rana, but kanaji fa yana cewa zai koya mata hankali? But u not bothering to ask him. U know him very well " Yusuf ya Kalli Ahmad sannan yakai kallonsa kan haydar " what are u planning "? " hankali zan dan koya mata kadan, my be kafi jin dadin zama da ita" " aa haydar live my wife alone " " your wife? What about me? Kasan kalan rashin mutuncin da take tatamin? Wane mataki ka dauka da nake kawo maka karanta? Kalli idona yau kasan rashin mutuncin da ta mun? Da ma ai promise my self saina koya mata hankali, just forget naji tsakaninku yanzu, thos not change everything " Ganin yanda ya hasala yasa yusuf dan buga kafadarsa kadan " take it easy, don't forget u are man " " forget about that " haydar ya fada " please karka kakkaryata kaga biki ya kusa, don akan yayanka zai Kare, tunda shi zaka Bari da jinya" Ahmad ya fada yana murmushi Yusuf dai na tsaye shima murmushin yake, don yasan halin kayansa tunda ya furta, Ba abunda zai hanasa aiwatar wa. ****************** Waya ta dauka tana kokarin kiran kanwar tata, idonta ne ya sauka a kan agogon wayar to 11 na dare. Ajiye wayar tayi tana huci. Yau bacci barawo, da kyar ya suri hajiya. Bawai bata son yusuf bane aa ita uwar yusuf dince da basa shiri, bata so, su Kara hada zuriya😕 (niko nace hada zuriya na nawa kuma?) ***************** " Rike gaisuwarki, in kin samu lokaci kozo ina nemanki, " hajiya ta fada har lokacin Ba annuri a fuskarta "in sha Allah inanan zuwa anjima kadan, " Hauwa ta fada cikin damuwa don tasan tabbas wani babban alamari ne, tunda taji muryar yayar tata a sama. " hajiya ni banga abin damuwa ba anan, naga da habiba da yusuf duk daya ne, me zai sa ki tada hankalinki haka? " sulaim ta fada Harararta hajiya tayi. " abinda babba ya hango yaro ko rimi ya hau bazai hango ba, don haka kar wacce ta Kara sa bakinta cikin wannan maganar " Haydar dake hada takardunsa ya juyo yana kallon hajiya, murmushi yayi " ni naga taimakon ku ma yaya yusuf zaiyi ya auri wannan dakikiyar yarinyar da ba komai a kanta, sai fitsara da rashin kunya" " ungo nan " hajiya ta masa dakuwa " yayar taka Kake kira dakikiya? " " tun da ta fara school din mu cikin mu 25 daga 21, 22 take zuwa sai so daya da tayi na 19. Amma a wurin rashinji da neman masifa 1 ce, ga dan banzan surutu, ina tausayin yaya yusif wallahi Sam basu dace ba " " don ubale sai kasa ya fasa ai" hajiya ta fada cikin fushi da jin haushi maganar haydar. " kai dai kace bata da kokari, amma ai habiba ta hadu karshe, son kowa wallahi " khulsum ta fada "kin san halin kaninki, yanzu haka bai taba tsayawa ya Mata kallon tsaf ba, tunda jininsu bai hadu ba " sulaim ta fada Jakarsa ya Saba ya musu sallama ya fice, yana tunanin hukuncin da zai fara yanke mata. ***************** Suna zaune a class room bayan teacher ya fita. Book din physics ne a gabansa ya na solving wani question. Ji Kake fas a keyarsa. Da sauri ya dafe keyar, saboda azabar zafi da ya ziyarci kwanyarsa. Dariya ta bushe dashi, harda shewa. Abin da ta jefeshi dashi yabi da kallo. Lemune Wanda ya wargaje can gaban board. Cikin kunan rai ya zaro Coca Cola dake jikin aljihun bag dinsa ta waje, yana juyowa sai ji Kake bum!!! Fassss!! Ya sameta sosai a kirji, don lokacin tana tsaye. Sannan ya fashe ya bata mata uniform, mu samman farin hijab din. Wani Kara ta sake, Wanda hatta class din sai da ya amsa. Kwanciya tayi a kasa ta dinga ihun kuka. Hubby akwai tsokana, gashi bata son abinda zai taba lafiyarta ko kadan. Saukar wani jifan taji a bayanta, ihu ta Kara sakewa ta dafa bayan da hannu daya. Ya daga daya canvas din zai Kara aika mata, Abdul Alim ya rike masa hannun. "please it's okay dud " Gaba daya matan aji sunyi kanta, sai faman ihu take, kamar Wanda aka kwakulewa ido. Mrs Brown ce ta shigo, ganin yadda class din ya hautsine yasa ta fara tambayar abinda ya faru. Da kyar aka samu hubby tayi shiru. "she never expect him to do this to her " "Take her to the PC office " Mrs Brown ta fada ma su yusra da suka rikota. "Aliyu follow me to the PC office " Mrs Brown ta fada tare da ficewa a class din. Canvas dinsa ya dauko yasa, friends dinsa Sun fito zasu rakashi ya dakatar dasu. A hanya ya hadu dasu, saboda yadda ta langabe, sun tsaya tana hutawa, yana zuwa baiyi wata wata ba, ya kwashe kafa fuwanta sai gata a kasa, yayi wuce warsa. PC na tsaye a bakin office dinsa Mrs Brown na masa bayanin abinda taji a bakin yan aji. Duk kansu sunga lokacin da ya kwashe kafafunta. Yana isowa PC cikin bacin rai ya Kalli Aliyu "I never expect this from u, bill down " Kallonsa haydar yayi cikin bacin rai jijiyoyin kansa sun tashi, sai faman hura hanci yake " don't tell me to nill down, because I'm not doing it " ya fada in horse tone Kallomsa PC ya keyi cike da mamakin maganarsa. Yasan yaron bashi da matsala ko kadan, zai iya cewa tun primary zuwa secondary baa taba kawo masa karar saba. He is nice boy Wanda suke alfahari dashi. To amma sweet heart dinsa ya taba, after all har a kan idonsa yaga ya kwashe kafafunta... To fahhhhhh😯 Mu shiga daga office, PC ya fada yana shigewa cikin office din. Binsa Su haydar suka yi. " a matsayinka na namiji, bai kamata ka tsaya kana fada da mace ba, wannan bai dace ba sam. Kai yaron kirkine, baa taba kawomin kararkaba, shi yasa zan maka alfarma wannan ya zama na karshe da zaa kawo min kararka. Amma gaskiya yau, I'm disappointed about what you did, ban taba tsammanin you stood so low by fada da mace ba, after all she is your sister," haydar dake tsaye jikin table din PC, bai ce komai ba, sai cika yake. Juyawa yayi wurin hubby " shi din ba kanin ki bane? PC ya wurgo mata tambayar. Murmushi tayi cike dajin dadi, (hubby da son girma) " kani nane, na wurin biyu ma " ta fada tana kallon haydar da ya Kara cika tam, " kema be kamata ki dinga biye masa ba, nasan duk yadda akayi kin kai shi bango, ki Rike girmanki. Kar in kuma jin wani abu ya sake tasowa a tsakaninku. " PC ya fada yana binta da wani sihirtaccen murmushi ya Kara da cewa. " in an barki dashi kashi zaki sha tunda karfin namiji da mace ba daya bane. Karki kara neman fada dashi. " " amma dai zaka sa a Zane shi ko? Ji yadda ya mayar Dani gurguwar karfi da yaji, kafafuwana ciwo suke min, ban iya takasu. " ta fada kamar zatayi kuka. " duk abinda ya faru ai, lefin kine, da baki shiga shirgin saba, ai da bai miki haka ba, haydar duk school din nan bashi da abokin fada, I know yadda kika sa shi a gaba, bai taba ramawa ko ya kawo kararki ba, yan zun ma kin kureshi ne. " Mrs Brown ta fada " is OK. Haydar she is your sister make peace with her, ban son sake jin irin wannan a tsakaninku. Ke kuma karki Kara tsokanarsa, kai ka tafi class, ku kuma ku rakata clinic a duba kafar. " Kallon PC hubby take idonta cike da Hawaye, don taso PC yasa ama haydar dukan tsiya, amma ya kyale shi ya tafi, watan ya bugi banza kenan? Tafdijam Ashe bata cika habiba ba in har ta barsa yaci bulus. Koda tsiya koda tsiya tsiya sai ta dauki fansar cin zalinta da yayi. This is her promise. PC kam gaba daya jinsa yake, wani iri, gani yake bai mata adalciba, amma ya ya iya, shaidu sun nuna karara itace bata da gaskiya, after all behavior din Haydar na yau ya tsaya masa a rai. Tabbas Mai hakuri bai iya fushi ba. In yace zai hukun tashi komai zai iya faruwa, don already ya fusata sosai. Ko da ya dawo class bai cewa kowa komai ba, kujerarsa yaja ya zauna, ya ci gaba da duba books dinsa. Suma friends dinsa ganin yadda yake a fusace yasa suka Kama kansu. "please hubby na rokeki ki fita hanyar yaron nan, he did nothing to u. Kin takura masa, duk abinda ya miki ke kika siyama kanki " Kallon yusra hubby tayi cike da jin haushinta. " Sai kiyi kuma " hubby ta fada "Alim " Hayder ya kira, Wanda aka Kira da Alim ne ya taso ya nufoshi, kus kus sukayi, ko Junaid dake kusa da su baiji me suka fada ba, sai dariyar Alim yaji, yana komawa sit dinsa. *************** "Da saninki ake wannan kulle kullen, amma kika kasa sanar Dani, don baki daukeni a bakin komai ba? A ce magana har tayi girma haka Sai dai in ji a sama " hajiya ta fada cikin kunfar baki da bacin rai. Hajiya hauwa da itama take cikin damuwa, ga ganin yadda yar uwar ta ta dau zafi, wadda take matsayin uwa gareta, yasa ta sassauta murya, " ki yadda Dani yaya, ban san komai ba, sai jiya nima yake gayamin. Wallahi sam ban san ya a kayi hakan ta kasan ce ba. Don tun da mukayi magana dake na toshe duk wata hanyar da zasu hadu, waya ma har yau ban yadda an bata ba. In sun zo ma gaba daya muke zama a falon har su gama zamansu su tafi, ni kai na nayi mamakin maganar. Shi yasa jiyan na tutsiyeta. Ashe hutun da ta tafi kankiya shine ya bita anan suka dai dai ta magana, gwaggo kuwa ta goya musu baya, don dama burin ta da Alhaji kawu ummi na gama secondary tayi aure, don cewar su duk saoin ta sunyi aure wai harda yara. " Shiru hajiya tayi tana sauraron kanwar tata " to ita habiban ta nuna aure take so ko sune suke son tilas ta mata? " " yaya ke nan, kina Abu kamar baki san halin ummi ba, ni dama na dade da dagota, shi yasa bata son mai da hankali kan karatu, yanzu in ma na matsa a barta tukunna, ba karatun take so ba, kin ga kuwa gara auren tunda shi take so. Ni yanzu yadda zamu bullowa abun ne don su Alhaji kawu da abbanta duk sunyi naam da abun, ita kanta na Lura tana mugun son yusuf, don jiya kwana tayi tana kuka, don nace dole ta rabu dashi ta fitar da wani tun da auren take so kuma tana da mane man." " bana jin yusuf, hauwa, nafi jin uwarsa da danginta, kin san tsakaninmu ba sai na fada ba, sannan abin da nafi ji shine, maman shi ta na da wadda take so ya aura. Tun ba yau ba, bana son ayi abinda daga baya za azo ana da an sani. " " haka ne yaya, zan turo miki ummin wata kila ke, zataji abinda zaki gaya mata, don yanzu magana na wurinta, yau dama yace zai tambayeta yaji raayinta, don sunyi magana da uncle kan yana son susan raayinta Kafin su je kankiya on Saturday maganar neman aure " " shi ke nan, ki turota, ni nasan yadda zan bullo mata " hajiya ta fada hira sosai sukayi da kanwar tata, Kafin sukayi sallama ta tafi. ********************* "Allah mommy ina sonta sosai, bazan iya hakura da ita ba, kiyi hakuri ki barni in aureta, ke kanki bazaki ji dadi ba in auri matar da bani da filling a kanta ba " Harararsa maman yusuf tayi cike dajin haushinsa. " saboda baka kishina ko? Duk yan matan dake garin nan Ka rasa wadda zaka dauko min sai jinin hadiza, to tsaya kaji tun muna shaida juna, Kafin ranka ya baci, kaje kace ka fasa. Na yadda ka nemo ko yar waye amma banda jinin hadiza. " ta fada cike da jin haushinsa Duk yadda ya so fahimtar da mommy kin saura ronsa tayi, daga karshe ma cewa tayi ya tashi ya bata wuri, ya kuma tabbatar yau din nan ya shai dawa daddy dinsa ya fasa. **************** "Tabdijam yau za ayi tashin hankalin da baa taba yi ba a school din nan." hubby ta fada tana Kara bude culers din su na abinci. Da suke empty a wanke tsaf. " kin ga karma ki fara, duk bake kika jawo mana ba, ki barmu muji da guda daya please " yusra ta fada cikin muryar gargadi. Aisha dake gefe ta buga tagumi, tana tunanin yadda za suyi surviving ba tare da abinci ba, har su tashi. Don already yunwa take ji kamar taci babu. " meye solution yanzu, don gaskiya yunwa na keji " " I have some cash with me, muje musha drinks da meat pie, ma raka " Harararta hubby tayi " ke ma kin san waannan baza suyi maganin yar banzar yunwar da nake ji ba, yau ko karyawa ban yiba na fito. Yanzu haka cikina ya hade da hanji " " Aisha tashi muje kinji, don ni 500 kawai nake da, " Ganin da gaske tafiya zasuyi su barta, yasa ta tashi ta bisu, tana din gisa kafa. " Allah yaron nan shima ya dana. I will deal with him later " " kinga shawarar da zan baki, Ki fita hanyarsa, don kin shiga black list dinsa, Ba ke ba har mu, sai mun gayawa yan garinmu. Aisha ta fada " rabu da ita, jiki magayi ai, sai randa ya karasa kafafun gaba daya " in ji yusra Aisha ta yi murmushi " ba tasan halin haydar bane shi yasa. " sun isa canting bude jaka yusra tayi ta dauko Math set dinta don anan ta boye kudin. Nan fa kudi yace dauke ni inda kika ajiye ni, zazzage jakar tayi tsaf Ba komai a ciki. Kallon kallo aka fara tsakaninsu. " yanzu meye abun yi, wallahi da hannuna na saka 500 da safennan cikin Math set don gudun yan sibare, amma gashi ban tsira ba " yusra ta fada kamar zatayi kuka " kumu yafi class kawai, already lokacin break ya kusa karewa, maci hamma yau kam " inji Aisha Hubby kam kasa cewa komai tayi, don ba karamin yunwa takeji ba, ko breakfast batayi Ba ta fito, wai ita tayi fushi, to ga abinda fushin cin abinci ya ja mata. Don da tayi break fast bazata damu sosai ba. Gashi tasha ruwa da ta dau niyyar azumi, ko ba komai ta samu lada. A hanyarsu na komawa class, sukaci Karo da group din su haydar da abokansa. Sun shinfida dadduma kamar yadda suka Saba, kowa da food Plack's din abincinsa ga drinks suna ci suna dariya da iface ifacen su irin na teenage boys. Wani uban ihu suka sa, lokacin da su hubby sukazo zasu wuce, tare da kwashewa da dariya. Haydar kam ko dago Kai beyi ba, junaid shi kam tsorone fal cikinsa, don yau yasan in sun koma gida Allah kadai zai kwaceshi daga jarabar hubby. Don yayi mamakin yadda yau ta yi sanyi, ya Tabbatha da sai sunyi upside down da school din. Juyawa tayi zata isa wurinsu, da sauri Aisha tajata " please hubby live them " "let me go, and give them my peace of mind, ko zuciyata tayi sanyi. " hubby ta fada tana huci Da kyar suka hanata zuwa, suka nufi class. Ko wacce ciki na kiran ciroma. ******************* Part din mmn samira ta fara shiga ta gaisheta, kamar yadda ta Saba duk lokacin da tazo gidan sai ta shiga part din Abokan zaman hajiya ta gaishesu, tukun ta wuce part din hajiyan. Cikin farin ciki mmn samira ta karbeta kamar yadda ta saba, suka dan taba hira, Kafin ta nufi part din mmn yusuf, kirjinta na faman dukan tara tara. Sai da aka bata ikon shigowa, bayan tayi sallama. Ta shiga cikin tafiyarta ta natsuwa kanta a kasa. Mmn yusuf na zaune tana kallon film a tashar African magic Hausa. Zama tayi a kasa ta gaisheta, ba yabo ba fallasa ta amsa mata, tare da tambayar hajiya hauwa da sauran kannenta. Shiru falon ya dauka. Su hubby an natsu kamar wata mummuna 😷 shigowar abida yasa ta dago da idonta dake kan yan yatsunta da take wasa dasu. Kallon uku saura kwata tabi hubby dashi, tare da Jan dan karamin tsaki. " mama zan bi yaya Ahmad dauko su Aisha " ta fada tana dauke kanta daga kallon hubby. " sai kun dawo, ku biya gidan hajiya karima ki ce ta baki sakona" "Tom " ta fada tana kokarin shigewa dakinsu don ta dauko gyale. " anty abida ina wuni " hubby ta fada cikin mutuwar jiki. Jiyowa abida tayi tana wurga mata uwar harara, taja tsaki, ta shige ciki, ba tare data amsa gaisuwarba. Mmn yusuf na jinsu, bata ce komai ba, ta ci gaba da kallon ta. Hubby na zaune jiki yayi sanyi abida ta fito ta fice a dakin. Itama tashi tayi tama mmn yusuf sallama ta nufi part din hajiya. Zuciyarta a cun kushe. ****************** Da gudu ta fada jikin hajiya, kamar yadda ta saba, don ba karamin shakuwa bace a tsakaninsu. " ni dagani, karki karasani, yar neman yarinya " zama tayi kusa da ita tana dariya. "ni din guda nawa nake da zan karasa ki, dube nifa kamar ki hure ni in fadi " dariya hajiya tayi " me kike ci na baka na zuba, kiba lokacinta na zuwa, don haka ki kwantar da hankalinki " " wane better kika tanadar min? An ce kina nemana,. " Zama hajiya ta gyara " akwai better din ma, amma magana nake son muyi, na tsakanin ya da uwarta. " Murmushi hubby tayi don ta Riga ta dago zan cen. Watau mommy nan ta kawo kararta ke nan.? " " yusuf yaron kirki ne, bashi da matsala ko kadan, amma bakya tunanin matsalar da zaki fukanta ta wurin uwarsa da yan uwanta? Suruka da danginta na matukar taka rawa ta wurin zaman lafiyar gida ko akasin haka. Ina ji miji tsoron muta nen nan, don nasan su farin sani, basu da kir ki ko kadan. balle kuma ta gefe daya kin fito daga tsatsona ko wannan kawai zai sa bazasu kauna ceki ba. Zan so ki hakura da yusuf in har aure kike so, ki fitar da wani ko kuma ni da kaina zan zabo miki. Fiye da yusuf." da sauri hubby ta Kalli hajiya cike da tashin hankali. Wai me yasa sun kasa gane, soyayyarta da yusuf daga Allah ne, tana son yusuf, Shima yana sonta, wannan kawai ya ishesu, don tasu mamanshi da danginta ai bada su zata zauna ba, balle ta damu kanta. Ido hajiya ta kafeta dasu tana karantar yanayinta. Murmushi hubby ta kakalo " shi kenan hajiya," "Kina nufin kin hakura, zaki fitar da wani ko yaya abun yake? " hajiya ta tambayeta don bata yadda da amsar hubby ba. " na hakura " ta fada tana murmushi Rungumota hajiya tayi cike dajin dadi, mu samman ganin yadda bata sha wani wahala kamar yadda tai tunani Ba, wurin karkato da hankalin hubby. " yawwa yar albarka, Allah ya miki albarka, in sha Allah da kaina zan zabo miki miji na nunawa saa " Dariya hubby tayi a ranta, "in kun san wata ai baku san wata ba, mai rabani da hasken zuciyata Sai ya shirya. He is mine, I'm his. Try as much as u can 😎" Hayaniyar yan matan gidan ne ya cika kunnensu...............     Not Edited.......   [29/02, 19:22] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 4       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... "hubbyn hajiya, sai yau ake ganinki a gidan nan? " sulaim ta fada tana zama kusa da hubby tare da dada mata duka a cinya. " Kai Kai Kai,  kefa matsalata dake muguwa ce, ta bugawa a jarida, daga haduwa sai cin zali " hubby ta fada tana shafa inda sulaim ta bugeta "Haba matar yaya, ni na isa In ci Zalinki?  Kawai nayi missing dinki ne, kin Dade baki zo gidan nan ba. " "Ke meya hanaki zuwa namu gidan in har da gaske kinyi missing dina" " week end din nan mukayi niyyar zuwa biko, matar yaya " khair ta fada tana murmushi Harara hubby ta maka mata " ke kuma waya sa dake?  Manya na magana kina tsoma baki. " Dariya duka dakin suka sa " kin bani da son girma, yarinyar nan?  Shi yasa bakwa shiri da autan hajiya " khulsum ta fada " ki barni da autan hajiya, idona idonsa, sai na karya kafarsa ko hannu.  Jibi yadda ya mai dani gurguwar karfi da yaji " ta tashi tana nuna musu kafarta. " autan hajiyan zaa karyawa kafa?  Ba dai nace ki fita harkar Saba kin ki? In dai aliyu ne kadan kika gani "  aiman ta fada tana duba kafar hubby da har lokacin tana dingisa kafar. " aliyu bai kyauta ba, ki barni dashi zaizo ya sameni " hajiya ta fada bayan ta gama jin duk abinda ya faru daga bakin hubby " kema bakya jiran kanki, ki fita harkarsa.  Ni na rasa me yasa jininku bai hadu da shi ba. " sulaim ta fada Murmushi kulsum tayi " kema kin san halin shi, kamar wani mai Al matsutsai haka yake, in baya sonka to fa baya sonka, ba zai taba shiga harkar kaba, kallo ma baka ishe shiba. Tun da kika kureshi Allah kadai zai raba ki dashi. Shawara daya zan baki, ki bashi hakuri, ki kuma fita hanyarsa " ai Kafin ma kulsum ta karasa hubby ta dire " tabdijam in bashi hakuri fa kika ce?  Kanin nawa zan ba hakuri?  Yayi tsararo wallahi " "Sai kuje kuyi tayi ai, Wanda yaji wuya ya hakura" " ku dai barni dashi zan masa magana, ke kuma ki fita hanyarsa,  ki tashi kije gida magriba ya gabato " to hajiya, baki bani abun dadin ba? " uhummm  su akwa Dede, har yanzu dai hali na nan" Fari tayi da ido " me zaa fasa, abin da ya kawomu birni kenan, muci zaki muci maiko, tun da suka raboni da gwagwgwota ai sun hadu da ata gwangwama. " dariya sukayi gaba daya " zan basu shawara su mai dake, ko sa huta da halinki " sulaim ta fada " da nafi kowa farin ciki wallahi " " wani lokaci kamar baki da wayau wallahi, taya mutumin da yasha ruwan birni, ya dinga mar Marin kauye? " duka hubby ta kai ma khair " banza waya gaya miki kankiya kauye ne? Sai kinje yarinya kisha mamaki " "ke da zaki tafi dakin miji, ina maganar wani kankiya? "sulaim ta fada tana murmushi. Hajiya ce ta fito, da wata Leda mai dan girma dauke da tambarin delema Beckry.  Ta mikawa hubby. Amsa tayi tana murna don tasan her favorite chocolate ne da sweets kamar yadda hajiya ta Saba mata. " Allah hajiya kina shagwaba yarinyar nan!  Da yawa " khair ta fada cikin fuskar fishi -shagwaba.  " jealousy baby,  zaki kone in dai tsakanina da hajiya ne, eheee! " hubby ta fada tanama khairi dariya tare da shafa mata fuska da ledar. Godiya tama hajiya da su kulsum, sulaim da khair suka rakota, parking lot, In da driven gidansu ke zaman jiranta. Ba kowa a compound din.   wait!!!  Sulaim ta fada bayan da suka kusa isa wurin mota " yanzu hubby duk yadda Muke dake ki kasa gayamin tsakaninki da yaya yusuf Sai dai muji a sama?  Baki kyauta min ba, bankuma ji dadi ba, Aisha ma dazu da muke maganar cemin tayi baki gaya mataba, duk da ko yaushe kuna tare a school,  sai yau ta samu labari, she is not happy with u,  not telling her " Murmushi hubby tayi " very sorry.  Nayi tunanin matsala in har aka samu labarin nan a gida, shi yasa muka barshi a tsakaninmu har Sai magana tayi karfi tukunnan.  Amma gashi still abinda muke gudu shi ya faru. Many people are against it " ta fada cikin damuwa " is true, but ya kamata ku jajirce, nasan in har anyi dole kowa ya hakura, ya rungumi kaddara, hakika kun balain dacewa, ke da yaya yusuf, kinyi dacen miji, don haka ki toshe kunnuwanki da duk abin da za kiji ko zaki gani. "  rungume sulaim tayi cikin jin dadi " thank you sister, ke kadai kika gayamin magana mai dadi, bayan dad dasu gwaggona, " Khair ce ta dafata " we are all support u,  Allah ya sanya alkhairi " " thank you " hubby ta fada tana murmushi. From no where taji saukar Abu a kafadarta " mieun mueum! " gaba daya sun tsorata don khair kam har ta isa cikin gida, a 360. Mage ce kan kafadar hubby Sai makal kalewa take, tana kuka. In akwai abinda hubby ke tsoro to mage na daya daga ciki. Garin kokarin gudu, ta Kara turgude kafarta me ciwo, ga mage ta dafe mata a wuya, ihu take tana Menan dauki tare da kokarin cire magen a wuyanta, bata san lokacin da ta saki fitsari ba, don tsananin tsoro da tashin hankali,.  Da sauri driven gidansu dake zaman jiranta ya fito, ya nufo su.  Sulaim ce ta dauke magen a wuyanta da kyar, duk ta yakushe mata wuya. Da gudu ta fada motarsu, tana ihu, tare da numfar fashi, kamar ranta zai fita, ga kafarta data fama tana wani balain zugi. Kuka ta fashe dashi. Da sauri su kulsum, suka karaso motar, suna mata sannu, tare da lallashinta. Suyi sunyi tazo su koma ciki, ganin yadda duk ta fita hayyacinta taki. Tsugunnawa yayi ya dauki magensa, yana mata shillo, ya nufi cikin gida, ko kallon in da suke be yiba. Da kallo suka bishi, ita kanta hubby dake faman kuka, tsayawa tayi Tana kallon sa.  "anyi Dan banzan yaro " kulsum ta fada, tare da bin bayansa ranta a bace. Hakuri suka Kara ba hubby Kafin suka nufi cikin gida, su kuma suka tafi.                **************** Sosai hajiya kema haydar fada, kamar zata dukesa.  Shiru yayi kansa a kasa, ya cika yayi fam!!! Jin ta gama fadan yasa ya dago ya Kalli hajiya da idonsa da suka kada sukayi ja " kiyi hakuri " ya fada tare da tashi ya Mufi dakinsa. " Allah ya shiryamin kai, da wannan bakar zuciya " hajiya ta fada tana binsa da kallo                  ***************** Ko Kafin hubby ta isa gida, kafa ta kumbura sintim,  mommy hauwa na ganin kafar tasa aka Nemo mai gyaran targade. Ihu da kyar aka samu a ka gyara mata targaden data samu a kafa. Sai da yayyinta jabir da jafar suka danneta tukun na. Fadin ihun da hubby tayi baa magana. Don bata son duk wani Abu da zai taba lafiyar jikinta. Fada sosai mommy hauwa ta mata, don tasan duk abinda aliyu ya mata laifin tane. Sai da hubby ta kwana uku, bata iya zuwa school ba, tana jinyar kafarta, tare da shirya irin ramuwar da zatayi kan haydar, don ta kuduri niyyar sai ta fanshe no matter how.                ***************** Daddy hubby ne, zaune kusa da ita, kan gadonta da take jinyar kafarta. " ummina ya maganarmu?  A ina muka kwana, don gobe suke son zuwa kankiya, amma in munji ta bakinki.  Kin amince ko aa? " ya tambayeta yana kafeta da ido. Kallonsa tayi cike dajin kunyarsa, Kafin ta mai da kallonta kan mommy hauwa dake tsaye bakin kofa, ta kafeta da ido cike da gar gadi.  Duk da zuciyarta a kwance take, jin yadda hubby sukayi da hajiya. Kwanciya hubby tayi a kan cinyar daddy " na amince " ta fada tana Kara boye fuskarta a jikinsa.  Shafa kanta yayi cike da farin ciki " Allah ya miki albarka, yasa albarka a cikin wannan lamari " " gaskiya abban jafar akwai matsala, " da sauri ya dakatar da mommy hauwa " ba na son jin komai daga bakin ki, ke zaki zauna mata dashi?  Meye aibun yaron nan.?  Ban son kana nan maganarku na mata,  ke dai a matsayinki na uwa, albarka kawai ya kamata kisa, tare da binsu da addua, amma ba ku tsaya kuna wasu kananun magana marasa tushe ba.  Ni zan fita, in na dawo mayi magana, sai ki fara shiri tun da wuri, don tare suke son a hada Dana su kulsum.  Kinga ba isashshen time " " wai duka duka ummin nawa take, da zamu biye mata " " nace ya isa haka ko?  Ban son jin another word " ya fada cikin daurewar fuska, ya Shafa kan hubby Kafin ya tashi ya fita.  Harararta mommy hauwa tayi tayi kwafa, tabi bayan mijinta. Ajiyar zuciya hubby tayi, tare da dafa saitin zuciyarta dake faman bugawa.  Ta lumshe ido. Tana tunano Rabin ranta.                  *************** Yusuf Jamil Yusuf Zubair Oregon  Wanda abokansa ke kiransa da Oregon Babban da na miji ga Alhaji jamil. Yusuf saurayi ne, Dan shekara 25 a duniya yayi degree dinsa na daya Dana biyu, duke a ABU Zaria inda ya karanci business admin. Yanzu haka shi ke kula da restaurants din Alhaji jamil dake other states. Yusuf saurayine kyakyakyawan gaske, kamarsa sak da mahaifinsa, sai idon mmn yusuf daya dauko. Fari ne sosai, mai sirki da ja, sumarsa irin ta larabawa baka Mai matukar laushi.  Doguwar fuska gareshi Mai dauke da yalwataccen gashin gira Dana ido, gazar gazar,  idonsa Manya ne, don wani lokaci in yana kallon ka Sai ka dauka yana zaro maka sune, farare kar da kwayar baka Mai daukar ido.  Ya nada dogon hanci, Mai kyan tsari da karamin baki mai dauke da kyawawan labba pink, hakoransa a Jere suke tsaf gwanin shaawa.  Maabocin barin sage mai hada da dan gajeren gemu, daya Kara kawata fuskarsa Yusuf mutun ne mai ilmin addini, mai hakuri, don duk yaran Alhaji jamil ba Wanda ya kai sa hakuri  da son jamaa. Alhaji jamil na matukar alfahari dashi, saboda biyayyarsa,  duk wani hali na alhajin, yusuf ya hada su, in ka dauke zafin zuciya, don yusuf mutun NE mai matukar hakuri da dawuya kaga bacin ransa.                ****************** Daga fannin hajiya har mmn yusuf ba Wanda ya samu yadda ya ke so.  Don alhaji jamil ya tsaya sosai ganin basu kawo wani cikas akan maganar auren yusuf da hubby ba. An tsai da magana zaa hada da nasu kulsum. Wanda yayi dai dai da sati daya da kammala jarabawar kammala secondary school din hubby.                  ****************** Makarantar gaba daya ta dai nama hubby dadi,  yanzu bata da kawa ko daya a school din.  Tun da ta dawo daga jinyar kafarta na kwana uku,  ba me kulata a school din.  So da yawa tana Lura da yusra da Aisha kamar zasu mata magana amma sai taga suna waige waige cike da tsoro.  Daga karshe ma canza wurin zama sukayi. Tsare junaid tayi a gida, kan Sai ya gaya mata abinda ke faruwa.  " dariya yayi doka ce ba mai kulaki, duk Wanda ya karya doka, zai hadu da hukunci mai tsauri, don haka live with it,  ki rabu dasu yusra kar ki sasu a Matsala, don ranar da aka kamasu suna kokarin miki magana, hukunci ya hau kansu, shi yasa suka canza sit " " kanata maganar doka - hukunci,  uban waye yasa wannan dokar? " ta fada tana zazzaro masa ido " kin fi kowa sanin waya sa dokar, kin San dai duk yadda ake tsoronki a school din bai Kai yadda ake tsoron saba ko? Har yau baki San waye haydar ba, shi yasa nayi ta Jan kunnenki ki fita harkarsa, kika ki " Duka ta dada masa " banza sa karai, da wannan yaron ne ya saku kuke min izgilanci?  Duk Sai naci ubanku daga ku harshi, Allah ya kaimu Monday " " aa hubby,  kibi a hankali " ya dada cikin tone din gargadi " fice min anan, solobiyo kawai " ta turashi waje                ******************* Monday tana zuwa school,   ta nufi office din PC tayi reporting din haydar A assembly PC ya musu gargadi, tare da neman haydar ya samesa a office. Koda ta shigo aji, already kowa yana mazauninsa.  Hararar su yusra tayi, dake sit din bayanta ta zauna.  Abinda ya daure mata Kai har aka tashi break Ba Wanda ya kulata, tana kallon kowa ya fice a class din. Su yusra ma a kan idonta suka fita. Jakarta ta dauka da food Plack's tayi waje, cafeteria ta isa ta nemi wuri ta zauna ta fara cin abincinta, kamar yadda ta saba, kwana biyu da basu Aisha. Su haydar ne, suka shigo da tawagar abokansa.  suta faman dariya da iface iface kamar yadda suka Saba. Kowa ya nemi sit dinsa.  Zama yayi a saman table din teacher, gaban board.  Hannunsa rike da doguwar sanda, yana kada kafarsa a hankali. " hi!!!!!  Class " ya fada a yangace Kamar baya son yin magana.  Gaba daya class din ya dauka " hiiii" ban da hubby dake faman shan chocolate dinta, tana kallon ikon Allah. " yama Su nan alder din class dinnnan? " ya tambaya, gaba daya suka amsa da " Anty hubby " " right!!!! kamar yadda PC yace, u can talk to her. Amma tunda yake ita ce alder a class din nan bakwa tunanin we have to do some changes? " "yes!! yes!! yes " suka dauka gaba daya " anty hubby, bai dace da ita ba, we have to come with nice name da zaiyi fitting nata, any ideas " Nan fa Kowa ya fara fadan sunan da yake ganin ya dace. Hubby kam ko a jikinta, ta Kalli wanna sannan ta Kalli wan can. Tana shan chocolate dinta, hankali kwance. " gogwgwo habi " alim ya fada yana dariya Shiru haydar yayi yana juya sunan. Class gaba daya ya dauka gwaggo habi!!!!= gwaggo habi!!!! " it's ok tun da sunan ya muku. From now on duk wani Abu na gwaggon mu ya zama namu, her food, drinks, water, chocolate, biscuits. Everything da gwaggo tazo dashi na ci, duk Wanda ya gani yana so. Just tell me. Or my friends. Ido hubby ta zaro " kam balai,  naga Dan iskan da zai matso kusa dani balle ya dauki abuna. " ta fada da karfi in warning tone. Daya daga cikin friends din haydar yace " ina son chocolate din hannunta, Kai har ma dana cikin jakar. " " gwaggo friend na son chocolate, so pass it here " haydar ya fada idonsa kan Jakarta data kwakume a cinyarta............. Fito yayi,ko kafin hubby ta farga Hafiz yayi sama da Jakarta, kasa motsi tayi tana binsa da kallon mamaki, yaron dake girma mata anty sama anty kasa, yau shi ne da fisgar Jakarta. "Don't worry gwoggo, we have gift for you." ya ba Hafiz damar bude jakar. "gwaggo na wuta fah!!!!  Na dauka manya basa shan zaki, amma wannan gwaggon  namu sha zumamu ce, zamu dan mai da komada," Alim kam kwashe sweet da chocolate masu tsada,  ya dura a aljihu " godiya dubu gwaggo habi. " wannan shine gift din mu me taken welcome to the hell 😈😈😈" Ya daga wani ledder Mai kyau, yana nunawa class, Kafin ya jefa cikin jakar hubby. Ya duro daga desk ya koma sit dinsa.  Hafiz ne ya mayar mata da Jakarta.  Tashi tayi ta tsaya daga sit, dinta.  Bude murya tayi yanda zasu jiyota,  fuskarta cike da murmushi.  " thank you class,  na gode da sabon suna, I like it,  because Su nan the most  precious person in my life, my love, my life my everything my grandma,  ana kiranta gwaggo, some people call her gwaggo habi.  My parent name me after her. So no problem u can call me gwaggo habi as much as you can,  I don't care " har ta zauna ta Mike " thanks for the gift" Speech dinta bai ma friend din haydar dadi ba, don sun so tayi masifa ne kamar yadda ta saba.  Free time dinsu is off.  So teacher ya shigo kamar yadda ya saba. Jakarta ta bude ta dauko note book dinta, sai lokacin taci Karo da ledar gift din, har ta manta da wani gift.  Tabe baki tayi, ta Fara duba book din da take da bukata.  Motsi taga kamar ledar nayi,  natsuwa ta Kara yi don ta tabbatar da abinda idonta ke gane mata, tabbas motsi ledar keyi, kadan kadan,  hannunta takai kan ledar cikin karfin hali, laushi taji da Dan karfi karfi,  bude bakin ledar tayi, don ta ga abinda ke ciki, wani tsalle tayi, tare da cillar da Jakarta gefe, tana ihu na daga hankali,  fita tayi daga class din a 360 yayin da yan aji suma suka tsorata ganin yadda ta daka tsalle da ihu tare da wulli da Jakarta, yasa dalibai da yawa rufa mata baya, suna ihu duk da basuga abinda ya firgita ta ba. Baki teacher ya sake yana kallon yadda ajin ya hargitse, kadan ne masu karfin Hali suka rage, Sai tambaya yake "what happened" Nesa da class din, taja birki tana maida numfashi, ta tsugunna tare da dafe kirjinta da hannu, da takeji kamar zai Faso ya yo waje. Yan class din da suka rufo mata bayama burki sukaja, suna mai da numfashi,  tare da tambayarta me NE ne? " sneak ,maciji 🐉 I'm telling you is sneak " ta fada cikin rawar murya tare da hada haruffan dakyar. Aisha ce tace " a ina kika ganshi? " " inside my bag, the gift " Teacher din su ne ya kwala musu Kira, yana daga brander na class din.  Duk kansu jiki a sanyaye cike da tsoro suka nufi class din. " what kind of nonsense ne, yasa zaki tar watsa min class,  what happened " ya tambayi hubby cike da bacin rai,  don iya dube duben su, basuga abin da zai sa ta yi haka ba. " sir sneak inside my bag " ta fada tana nuna masa Jakarta dake yashe gefe daya Kallonta ya tsaya yi, for a second, jikinta sai rawa yakeyi, kana ganinta kasan a firgice take.  A hankali ya taka zuwa wurin jakar ya zazzage ta, tare da duddubawa bai ga komai ba. " inside that leader sir " tana nuna masa leadar dasu haydar suka bata. Leader ya dauko ya bude yana kallon abinda ke ciki. Cike da bacin rai ya dago yana kallonta " what kind of jork is that? " ya fada yana zazzage leader din.  Cike da tsoro, take bin abin da yake zazzagewa da kallo lollipops ne 🍭🍬 da sweet.  Cike da mamaki take bin lollipop din da kallo. Ita tasan ko kurani aka bata zata dafa cewar maciji ta gani, but how ya koma lollipop? Yan aji ne, suka fara dariya, waanda sukasha gudu, kuwa ransu ya baci, ganin yadda sukasha gudu a banza. Sai mita da korafi suke yi, hubby kam da mamaki ya gama kasheta, kallon ta takai kan haydar dake zaune  kafa daya akan daya, yana faman sauke murmushi. Kallon ta ta kai kan junaid, yayi saurin dauke kansa, alim ne ya daga mata gira tare da murmushin gefen baki.  " Allah ya isa na, gudun da kuka sani" ta fada under her breath tana harararsu Hakuri ta Fara ba teacher din, Wanda da kyar ya hakura, bayan ya mata bulala uku, sauran mukarra banta biyu biyu, Kafin ya barsu suka zauna.                    *************** Maganar auren hubby da yusuf ta tabbata, an tsaida lokaci dai dai danasu khulsum.  So ko wanne bangare Sai Shirye Shirye ake.  Fannin masoya kuwa abun baa cewa komai.  Don yanzu ne su hubby ke barge soyayyarsu,  wani irin so sukewa juna na ban mamaki,  tun mommy Hauwa najin haushin yadda hubby ke rawar jiki akan son yusuf, har ta dawo ta zuba mata ido, tana mai binsu da addua.  Tare da gyara yar tata, yadda ya kamata. Ta fannin Mmn yusuf ma, hakurin da kaddara ta runguma, ganin hatta yayanta bai bata goyon baya ba, akan lamarin.  Hankalinta gaba daya a tashe ne, ba wai tana kin hubby bane,  tasan yarinyace mai nagarta, wadda ta fito gidan mutunci.  But matsalarta ta fito daga tsatson Hajiya,  wadda duk duniya ba wadda take kishi sama da ita, uwargida kuma mafi soyuwa a zuciyar mijinsu,  duk da adalcinsa, da kokarin boye filling dinsa akan matansa. Wannan yasa take kishin hajiyan sosai,  musamman ganin hajiyan bata fita da komai ba, a cewarta. sema ita da zata nuna mata kyan fiska, da ilmin Boko da wayewa. Mmn yusuf mace ce Mai kyau kallo daya zaka mata kasan ta hada jini da buzaye ko Fulani, farace fari mai daukan ido, ga gashi har baya baki mai laushi, akwai manyan ido farare, tanada hanci dai dai mai kyan tsari da madai dai cin baki, kallo daya zaka mata ka shaida kyanta, jikinta Dan daidai doguwacce mai murjajjen jiki, ita Ba lukuta ba ita ba siririya ba, ba laifi tanada kyan Kira dai dai ita. Mmn samira Hajiya Amina mace ce mai matukar kyau cikakkiyar bafulatanar manbila. Farace sosai  tanada gashi dogo ga baki, akwai hanci har baka, idonta madai daita masu daukar ido, karamin baki, gashin idonta dana girarta gazar gazar Wanda suka Kara kawata doguwar fuskarta.  Gajera ce mai kyan diri.  Yayanta sunfi kowa kyau a gidan, in ka dauke yusuf da haydar da suke Kama da mahaifinsu. Hajiya ba wata kyakyakyawa bace,  chocolate color ce, mai matukar kyan fata, da laushi, gashinta irin na hausa rober heir baki Mai dan tsowo, dai dai parking. rown face take da shi, mai dauke da ido madai daita sai hanci dan dai dai shiba nakushasheba shiba godo ba, bakinta karami mai dauke da red and black lips. Kallon farko baka gane kyanta, Sai ka kalleta sosai. The more kake kallonta the more kake kara ganin kyanta.  Ita ba doguwaba Ba kuma gajera ba,  akwai body na daukar hankali, don duk da girma ya fara kamata kallo daya zaka mata kasan Allah ya yi Kira a wurin. U can emerging kuruciyarta.  That's Alhaji Jamal's wifes.                 ****************** "Nace aba Hajiya karime aikin decorations kin ce aa, meye hujjarki na sa baki a abinda bai shafekiba,.?"  Hajiya ta fada tana huci Mmn yusuf dake zaune a kan kujerar roba, a bakin kitchen. Ta dago tana kallon hajiyar a dage " saboda na isa, yasa nace ba zaa bata ba, ina ita akaba contract din gidan professor wali, daga karshe me ya faru?  In banda kunya da akasha, don tana kawarki kawai Sai mu kashe kudi a banza ba biyan bukata?  To bazai yiyu ba " Dariya Hajiya tayi Mai hade da shewa tana tafa hannu " iko sai Allah, karki manta wannan ba abinda ya shafeki bane, iya karki ido,  bana son shishshigi tunda kudin baa aljihunki zai fito ba, don an samu matsala a wan can, bashi ke Nuna wannan ma zaa samu matsala ba. Nafa Dade da Lura da adawarki kan kawance na da Hajiya karima, to nan gani nan bari " " "miji nane, dole inyi iko dasu kamar yadda ya bukata, don bazan yadda ki mallaki naki ba, sannan ki dawo ki mallake nawa ba,  kamar yadda kike gulle gullen yi, to ki sani na Dade da gane plan dinki. Kuma it's not work. " " eh ehimmm!!!  Nan kuma kika nufa?  To zamu gani, tun wuri ki Kira decorator dinki ki bashi hakuri.  Maganar mallake yara kuwa ke har kina da bakin magana?  Amma ba komai time will tell " Mmn samira ce ta fito jin haya niyar tayi yawa " haba jamaa, wai ku bakwa gajiya?  Jiya jiya aka gama wani case din amma har kun fara kunno wani?  "Da Kata, " Mmn yusuf ta fada tana kallon Mmn samira " kina ganin zan dauki, abunda ke zaki dauka ne?  Ba Wanda ya isa ya takani in kasa ramawa wallahi.  Kuma tunda mijina ya bani go ahead kan ragamar ocesions din da zaa ayi, banga wadda ta isa ta dakatar Dani ba. " Kallon Hajiya Mmn samira tayi,  ganin yadda take cika take batsewa.  Harararta hajiyar tayi " taya zan zuba ido ina gani, amin iko da baba kere.  Haka kurum, in gaskiyane me yasa baa dauraki a Kai ba sai ita?  Nasan kilbibin da munafurcin data Saba ne, yasa ya bata wannan damar " " duk da haka, tunda ya bata ai shi ke nan, sai ki barta tayi abinda ya dace, bai kamata ku tsaya kuna sa insa haka ba, ba girmanku bane, ko don albarkacin wannan Sabon zumuncin da zai kullu a tsakaninku ya kamata ku manta da komai. Kudai kuyi fatan ayi taro lafiya a watse lafiya, a fita kunyar jamaar da zaa tara. " " gaya mata dai,  munafurcin ma ai iyawane, in mutun ya isa yaje yasa a kwace , banda kaddara ma ni har yaushe!!!? " Hajiya har ta bude baki zatayi magana, Mmn samira ta jata sukayi part dinta. Da harara Mmn yusuf ta bisu tare da tsaki.  " Ba girmanki bane, kiyi kokari ki taushi zuciyarki, ki daina biye mata, kin san kadan take nema. " " ta Yaya zai min haka?  Ya rasa wadda zai daura a kai Sai ita?  Ni nasan ba wani Abu bane Illa so take ta tozar tani cikin jamaa." " ki kwantar da hankalinki, zanyi Supervising in tabbatar bamuji kunya ba, ita ma nasan bazata fara ba, tunda fada take nema wurin shi. " Hirar sauran Shirye shiryen daya rage suka fara, duk da har lokacin zuciyar Hajiya na zafi, game da hukuncin da mai gidan ya yanke, ba tare da shawartar suba.                ****************** Fara exams din su hubby yasa ta samu sassauci, daga living he'll din da haydar ya mayar da rayuwarta a wata dayan  da ya rage musu a school. Yanzu shakkarsa take, don yasa what he is capable of.  Gashi duk abinda yake mata, ta kasa Kai kararsa gida, Don gani take taci baya. Aisha da junaid ma ido suka sa musu, don abun yafi karfinsu. Bata manta ranar da abun ya isheta ta sameshi yana karatu a library.  Sai da ta gama masifeshi tas, ko dago Kai be yiba balle ya tankata. Haushi taji ta fige book din,  tana huce.  " ka gama rainani after all I'm your senior sister  and I'm going to married your brother, so respect me for that" gyara zama yayi idonsa na kallon gefenta yana murmushin gefen baki " wow!!! wow !!!wow!!! Ya kamata ace kina can kina duba books dinki, ba neman magana ba,  koda yake na manta, Zero head ce, no matter how u read u never understand. Ne man fada, tsokana, surutu shi kika kware a kai,, So please stop disturbing me, and give my book back, or else. " " are you treating me? " ta fada in high tone " yes!!!!  And stop shouting at me, I'm not your kid " " ina son ka sani, duk abinda Kake min baka ci bulus ba, no matter how sai na rama, I promise you that. Agric chicken kawai " ta wurga masa book din tayi waje cikin bacin rai. " zero head ........" ya fada yana dariya kasa kasa. ya ci gaba da karatunsa............    [01/03, 19:40] +234 706 771 8610: DA KAMAR WUYA                             Part 5       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau Shagali sosai akasha, inda naira tayi kuka, baki ta ko ina, tun daga kan gogaggun yan Boko, yan kasuwa da manyan yan siyasa na kasa. Mutanen Lebanon ma, baa barsu a baya ba, sun samu hallarta, maza da mata. A babban masallacin sultan Bello aka daura auren duka, har na su hubby da Ahmad. Wanda aka samu fahimtar juna tsakanin waliyyan ango dana amaren. Don samun saukin zirga zirga. An daura auren Ummu khulsum da zai'dul abidin,  ummu Aiman da Abdulmufassir, samira da Abu turab,  Yusuf da Habiba sai Ahmad da muna'ya. Direct reception suka wuce bayan daurin aure, wanda aka shirya a sabon branch na eat more restaurant dake Unguwar sarki.  Wurine yalwa tacce, da aka kawata shi sosai, gwanin sha'awa.              ******************* Hubby chocolate color ce, fatarta mai matukar daukar ido ce, ga taushi kamar na kulba.  Doguwar fuska gareta, mai dauke da dogon hanci, mai kyan tsari,  idonta basu da girma, su kuma ba chines eyes ba, bakinta dan dai dai, mai dauke da siraran labba, masu walkiya, hakoranta a Jere farare masu dauke da siririyar wushirya sama da kasa, tana da yalwar gashin gira Dana ido da suka Kara kawata fuskarta.  Tanada yalwataccen gashin Kai, Wanda ke sauka har kafadarta. Baki Mai cika. Tanada madai dai cin tsayi, ita ba doguwa ba Ba kuma gajera ba.  Hubby akwai Kira ta daukar hankali, don ta biyo kirar su Hajiya,. Yatsun kafarta Dana hannunta dogaye masu dauke da fararen farce dogaye, kamar tayi piecing dinshi.  Hubby akwai kyau na daukan hankali, shi yasa mommy Hauwa ta saba mata da saka hijab, da dogayen riguna.                 *************** "Wow!!!!!  Kin ganki kuwa?  Dole yaya na ya rude, irin wannan hadaddiyar beb haka "  sulaim ta fada tana gyarawa hubby head dinta.  Murmushi hubby ta yi " kin cika sharri duk kyauna na Kai kine? Tsoro ma nakeji kar mu fita a rasa amaryar a cikin mu. " Dariya sukayi gaba daya,  yusra dake faman daukan su selfie ta ce " ina ita ina kamo kyan Amarya,  ni kaina da ban sanki ba, na ganki ban iya ganeki, kinga kyan da kikayi?  Koda yake nasan harda rashin son kwalliyarki yasa muke Kara ganin kyanki, kin San Wanda baya kwalliya in yayi ba karamin kyau yake yi ba " " wato kina nufin kice, hubby bata da kyau, makeup ne ya fito da ita? " ido yusra ta zaro " ke asima ki rufamin asiri, ni na isa nace hubby bata da kyau?  Ko makaho ya shafa ai yasan gidan kyau ya tarar. Nufina makeup din ya Kara fito da ita sosai." Dariya suka sa, suka ci gaba da hirarrakinsu, suna shiryawa, don ranar wuni ne. Hubby sanye take cikin wani dakakken less, mai asalin kyau,  cotton yasha adon flowers da stones, kalar red and milk. Taklalmi, jaka, milk, sai head me hade dana yafawa milk and red. Maganar kyau da daukar ido baa magana. Sai glowing kawai take.  Haka yan matan Amarya kowacce taci ado, da ashobi,  na atamfar new edition. gwanin shaawa. Part din saukar baki, na gidan aka bar mata ita da kawayenta.  Kayan ciye ciye fannin food, snacks, drinks, dessert gasu nan Kala Kala, sai Wanda ya maka. DJ mace, suka Kira musamman tai ta sake musu sauti suna cashewa. A mai camera da video sunata aikinsu, hatta iyaye da Abokan mommy suma baa barsu a baya ba, wurin cashewa. Phone Aisha B ta kawo mata,Bganin mai kiran yasa tayi daki da sauri inda ba jamaa. " princess ina kika shiga, waya nata ringing? " " sorry hayaniya yayi yawa ban jin ringing, phone din yana wurin Aisha B " " OK.  Ya akaji da jamaa? " " Alhamdulillah " ta fada " Masha Allah la kuwwata Illa billa.  Burinmu ya cika, now u are all mine, I'm yours. " Murmushi tayi, ga kunyar da ta lullubeta. Jin muryarsa mai cike da jindadi. Daga ji yana cikin farin ciki, Mara misaltuwa.  Jin tayi shiru "  answer me, mana.  I want to know how happy you are " Murmushi tayi har yana jin sautin ta a kunnensa. " shi ke nan, tun da rowar jin muryar ake min,  muna kofar gidanku, zamu gaisa dasu mommy, I want to see you, please ki dan leko in ganki. " Dariya tayi " this is not possible,  akwai jamaa sosai, bazan iya fitowa ba, ina jin kunya " Murmushi yayi " ba cewa nayi ki fito ba, lekowa nace kiyi " " ba kyau leke fah!! " ta fada tana murmushi " who tell u that?  Don kin leki mijinki ai ba laifi bane ko,?  please I want to see you right now " " sorry Yaya, I can't " " it's OK, I know dama ni kadai na damu dake " ya fada cikin dakewar murya " is not true, sai ka shigo zakaga yanayin gidan, ba chance " " it's ok " Jin yadda ya amsa ta tasan beji dadin hakan ba, yasa ta sauke muryarta cikin daddadar murya " sorry Yaya kar kayi fushi dani. I'm sorry " Murmushi yayi, yayin da yaji wani sanyi da natsuwa sun dirar ma zuciyarsa.  " it's ok, yanzu dai send me a pic of you, I miss you so much " " right away, I miss you too " ta fada cike da kunya. "love you, sai mun hadu a gidana  yanzu ko? " Murmushi tayi tare da saurin kashe wayar, don bata son ya tsokano wannan hirar, he is not a gentleman at all a wannan fannin, yanzu zai bata kunya. Pictures ta tura masa, Kafin ta koma cikin friends nata, suka ci gaba da hidimominsu.                ********************* An kai amare gidajensu, kamar yadda aka Saba, ummu kulsum ce kawai take gida, Sai washe gari zasu wuce Lebanon in da mijinta yake zama.  Ummu aiman gidanta na rigacukum, sai samira da aka kaita NNPC quarters, hubby da munaya millennium quarters dake malali. Gidan hubby simple, cute and beautiful.  3 bedroom plat with 2 fallow. Kitchen da store a hade.  Ko wanne daki da toilet dinsa.  Sai main fallow ma da nashi toilet din. Ko ina yaji kaya na alfarma, masu tsada da nagarta. Don ba karamin kokari mahaifinta yayi ba, Hajiya Hauwa ma baa barta a baya ba, kana ganin gidan kaga gidan yar gata, don komai in higher class aka yishi. Compound din yana da girma, mai dauke da dakin maigadi da toilet,  boys quarter's 2 rooms with toilet.  Sai parking space, ga shuke shaken flowers masu kyau da kamshi.  Gida ya hadu iya haduwa, sai fatan zama lafiya. 8:30 suka fara Shirye shiryen tafiya dinner.  Da zaa Yi still a eat more restaurant. Wurin ya kawatu, iyaka kawatuwa.  Hubby da yusuf ne karshen isowa a amaren.  Sanye take da code less light purple, sai head da Vail, dark purple, taklalmi da pose dark purple,  dinkin doguwar Riga, har tana Jan kasa, irin bridal style din nan, mai tsari da kyau. Tayi kyau har baa magana, ga dinkin ya Kara fito da ita, sosai.  Yusuf ma yasha ado da light purple shadda, mai matukar daukar ido, Tasha ado da zare dark purple, Sai cover shoe dark purple da hula, Masha Allah, kana ganinsa kaga cikakken balarabe. Agogon I phone watch din dake daure a tsintsiyar hannunsa, ya kalla, a kalla sun kai 5min da isowa harabar wurin.  Amma damuwarsa yadda zai iya yadda su fita a haka. Don gaskiya yana ganin is a bad idea. Kallon hubby ya kara yi,  gaba daya jikinsa yayi sanyi, he knows hubby is beautiful, cute.  Bai taba ganinta a irin wannan dressing din, mai fitar da sura ba,  zai iya cewa shi dai yasan yana matukar sonta, hubby kusan ko yaushe yalwatattun kaya ne a jikinta, sau da yawa yana jin kannansa na mata tsiya,  ita goyon kaka ce, bata ko irin gayun nan na wayayyu,. Sai yau yagane hikimar yin hakan.  Tayaya zai iya yadda su fita a haka, mazan wurin su gama Kalle masa ita?  Tsananin kishinta ne ya karu a zuciyarsa.  Gaba daya surar hubby ta tafi da imaninsa, wani mutuwar jiki yake ji, ga wani filling da bai San yana da shiba, Sai yanzu, dake Kara taso masa.   Kallon ta yake cike da so da kauna, hannunta ya kamo cikin nasa, Wanda ya haddasa musu gaba daya jin wani shock, laushin hannun ya Kara rikita yusuf.  Cikin kasa lalliyar murya yace " princess Anya baza mu hakura da dinner din nan ba?  Gaskiya I'm jealous mutane su gama kallemin ke, I want teak it." Shiru tayi don gaskiya she is not comfortable, this is the first time da suka zauna so close da juna ita dashi, ga mayun idonsa dake kashe mata jiki ya zuba mata, Sai faman lumshesu yake. Zuciyarta da gangar jikinta rawa kawai suke yi, ko Kari take ta zame hannunta, don ji take Kamar wani Abu na bi ta hannun zuwa sassan jikinta. Kwan kwasa window din motar ne, ya dawo da yusuf daga duniyar daya Lula, a hankali yakai kallonsa ga mai nocking din.  Engr Sahabi his best friend, a hankali ya sauke glass din motor.  " what takes you so long, sauran angwaye da amare duk sun iso, ku kawai ake jira, kazo late kuma ka makale a mota, " kallon sa yakai kan motocin dake Parke,  tsaki ya dan ja a hankali.  " I think I have to go back home " " what???? " engr ya fada yana zaro ido " I can't take ku gama  Kalle min Mata gaskiya " yusuf ya fada in serious Dariya engr yayi harda rike ciki " kai dai fadi gaskiya, kace ka kosa ka kebe da madam kawai,  stop acting Child dish please " ganin da gaske tsakani da Allah yusuf yake yi, gashi sai faman hon ake musu, alamar sun gaji da jira daga amaren har kawayen Ba Wanda ya sakko a motarsa.  Yasa engr gyanan murya " I understand u, ka zo mu shiga, in yaso sai ka tsare madam basai ta tashi ba, no dancing no greeting , it that OK for you? " shiru yayi na Dan lokaci Kafin ya amsa. " OK get ready, let me inform them . Nan fah kawaye da abodan ango suka firfito, kowannen sun sha ashobi,  ko wanne,  kowanne kawayenta da kalan nasu ashobin.  Kawayen hubby na sanye da code less ash sai head silver, silver shoe and pouch. Abokan yusuf sadda ash color black cover shoe.  Kwanin shaawa, suka nufo motar dasu hubby ke zaune.  Yana rike da hannunta suka fito, abokansa da Nata suka rufa musu baya, kamar sauran amare da angwayen. Tsaye suke jikin motar da suka zo da ita, a kalla sun kai ten, ko wanne yasha ado har baa magana (yara manyan gobe☺) ke nan haydar and his friends, sanye yake da boil light blue, janfa da Wando yasha aiki, sai black sandals anko sukayi shida junaid, sunyi kyau sosai.  Mu samman haydar. " kai yayan kan nan ya iya yawa, fisa bilillah tun dazu munata faman jira, ya iso kuma fitowa ya gagara " Hafiz ya fada yana duba agogon hannunsa. Tsaki alim yayi, tare da danewa saman motar da sukaxo da ita.  " kun San ni ban jure ma tsayuwa. Harka da gwaggo dama ai sai hakuri. "Kai fa wulakancinka yawa ne dashi, ko ba komai kwa dinga min Kara, balle yanzu da take yayarmu ta bangare har biyu.  So stop calling her gwaggo. She is our anty know. " " gaskiyarka junaid, dole mu koma Anty sama Anty kasa, kar muje gidan Yaya lomar tuwo tafi karfinmu, don nasan kadan daga aikin Anty. Tananan tana targeting din mu, she takes revenge on ours. "  amir ya fada Hafiz da Hafiz omer kam gaba daya hankalinsu na kan groups din amare.  " wow what a nice couple " Hafiz omer ya fada yana kara gyara zaman hularsa. " kaifa Dan iska ne, watau har yanzu Hali nanan? "  duka Hafiz omer ya Kai ma amir " I will beat you, black and blue in ka kara kirana dan is. Naga I'm not different than u, ji yadda Kake faman lumshe ido kaga bebs" dariya sukayi baki daya, banda haydar da hankalinsa ke kan phone.  " gaskiya ne, wannan da shine Lego's boy da sai prayer " alim ya fada yana dariya. Haydar ne ya dago yana kallon yadda suke tama juna shegantaka suna dariya. Murmushi yayi " let go duds " ya fada yana yin gaba.  Already holl din ya cika, da kyar suka samu table din zama da zai ishesu, don there in cepratable, A cewarsu. Aisha ce tazo dai dai kunnen hubby ta rada mata " kinyi wuta fa Matar yaya, every eyes is on u" murmushi hubby tayi ta kai mata duka kadan. " u are joking with me?  Look " ta nuna mata samira da ke gefen hagunta.  " to tell you the truth, your the best " ta fada tana kashe Mata ido daya,  let me, take selfie.  Yusuf ne ya harareta " gulmar me like yi a nan? " dariya tayi  " sorry brother " ta koma wurin sauran friends din su. " a u ok?  Ya fada yana Kara dantse hannunta dake cikin nasa.  Murmushi tayi tare da kada kanta. Dinner na tafiya yadda ya dace, duk yadda family and friends suka so su hubby suyi rawa ki yusuf yayi, gaba daya ya kasa ya tsare ya hanata tashi daga sit dinta, masu son pictures da ita, Sai dai su karaso nan. " wai kai da WA Kake dariyar nan, I start to wonder, Anya kanka daya?  Or you are going nuts? " Amir ya fada yana kallon alim. "I'm pity my self, my dreams shattered in front of my eyes, I couldn't do anything " alim ya fada yana jijjiga kai. Gaba dayansu kallonsa suke, cike da mamaki, ganin yadda lokaci daya ya Koma wani abun tausayi. " what happened dude? Don't tell me u serious about it? " Hafiz ya tambaya yana tsareshi da ido. Murmushi yayi, mai ciwo. "I'm serious. I'm in love with her, I wish we are destiny to live together for ever " " stop beating row the bosh, what is going on? " " amir loves Anty hubby " " what? 😱😱😱 " kamar sun hada baki, suka fada suna zaro Ida nuwa. Haydar kam murmushi yayi, yaja ashir, " dud muje ka rakani in dauko Abu a mota" tashi yayi suka fita. Murmushi Amir yayi, " u never understand, tun da na fara ganinta, naji ta kwanta min a rai, behavior dinta na burgeni. Recently I'm totally sure I'm in love with her. Ina planning ina kaiwa 2Level zan yi proposing dinta, duk da nasan she is alder then me, yaya yamin over taking. " ya fada gwanin tausayi 😥 " lallai kana dakon wahala, kai a tunaninka Anty ko kallonka zatayi? Kama manta wacece hubby? Da jarabar son girma? In ka manta bari in tuna maka " ya makale murya yana kwaikwayon yadda hubby ke masifesu, wani lokaci can Baya " yaran nan, bakuda mutunci, ina son kusan bakin rijiya ba wurin wasan yaro bane, don na Lura rainin hankalinku ya fara yawa. A haihuwar tumaki nayi jika daku, balle haihuwar kaji da nayi jika, tattaba kunne, harda ihi!! Hi!!!, don haka rai zai matukar baci wallahi kuka ci gaba da kawo min rainin hankali. In kunne yaji 🙉" ya fada yana rike kunne kamar yadda tayi, musu a lokacin. Gaba daya dariya sukayi harda shi kanshi Hafiz mai gwada war. Alim ne ya dafa kafadar amir, " sorry brother, Allah ya zaba maka wadda ta fita. Never mind " Murmushi amir yayi " thanks. Ba matsala tunda yayanmu ne, da bare ne danafi jin haushi. But know I'm happy for them, sun masifar dacewa. Luke at them " ya fada yana kallon su Dukansu kallon su hubby sukayi, " gaskiya ba karya Antynmu ta hadu karshe, nima da zan samu irinta ai da anga jilali, dole a barni in shiga Daga ciki. Akwai sauran beb a gidanku? " Hafiz Omer ya fada yana kallon junaid. Harararsa yayi " ba saura!! In kuna shirmenku don't put me there. " " Kyale yan banza, ne makon tunanin how we planned to achieve in life, sun tsaya suna shirme, soyayya ba naku bane yanzu, build your self, then you can go ahead " haydar ya fada yana zama "it's true, but let's us enjoy a little. Kalli waan can bebs din, tunda muka zauna suke faman kallonmu, let's upper them a dance, nasan they want disappoint us, alim ya fada yana Dariya kasa kasa Da gaske sun tafi da hankalin matasan yan matan, Wanda yawan cinsu family ne they know them well. Yanayin shigarsu da girman jikinsu Kai ka rantse wasu manyan samari ne, sai ka Kalli idonsu da yanayin hirar zaka gane there young adults. Duk yadda yaso kaucewa shiga filin rawa, bai samu haka ba, don sister's din Mmn yusuf suka tasa shi gaba dole suka Dan cashe, tare da daukar pictures da amaren da sauran jamaa. Yana makale da ita kamar wani zai kwace masa ita. Gyalenta na zamewa da kansa yake faman gyara mata shi, duk da yasan ba wai yayi duhun da zai Hana hango komai bane, but ya taimaka ko ba komai. Gaba daya hubby a takure take jin kanta. Musamman kusancin da jikin ta Dana yusuf ya samu, gaba daya ya saukar mata da kasala, wanda a wurin yusuf shi kadai yasan yadda yake yaki da gangar jikinsa da zuciyarsa kan yadda yake ji. "Masha Allah, yusuf kam ya dace mata wallahi, dole yaro ya rude, irin wannan tsaleleyar yarinya haka. " harararta daya Matar dake kusa da ita tayi. " ke kam Hajiya ai baki da zuciya, yaron da Kiri Kiri yaki yarki, amma har ke ce da fadar irin wannan magana,? Ai wallahi abun yamin ciwo sosai, har me wannan zata nunawa nafisa? " Dariya wadda aka Kira da Hajiya ai tayi " dadina dake sakina rashin lissafi, shi aure ai nufin Allah ne, matar mutun kabarinsa, Allah ya yi ba mijinta bane, sai ku tayata da addua itama Allah ya fito mata da nata mijin, ni kwata kwata wannan Abu bai dame ni ba, tunda dama bawai shine da kansa yace yana sontaba" Tabe baki Sakina tayi " Allah ya kyauta, da zakiji shawarata da kun tilas ta masa ya aureta ita ma, don gaskiya naso wannan hadin, zai Kara dankon zumuncinmu sosai". Matar dake can gefe duk hirar da suke suna sauraran su. Ta gyara zama " banda abinki Sakina ai, abinda Hajiya ai tayi ce shine kan hanya, ina amfanin badi ba rai? Itama Allah ya bata Wanda ya fishi,." "Amen " sauran matan suka fada baki daya. Dattijiwar cikin su ta ce " kar ki mata bakin shiga gidan kishiya, kishiyar ma jinin Hajiya. Sanin kanku ne daba dan kaddarar Allah ba, da ba abinda zai sa Alhaji Jamal Kara aure. Ki Kalli yariyar nan da kyau, irin su ake Kira mowar mata, Matar da bata bora a gidan miji, hada miji da irinsu sai ka shirya. Saboda sun hada duk abinda namiji ke bukata ga mace, Wanda samun irinsu sai an tona a cikin mata. Tabbas yusuf yayi gamo da katar ya dace da mata daya tamkar da dubu. Allah ya sa halin yafi surar kyau don ya more rayuwar aure, mai dorewa. " Da sauri ta kusa da ita ta hayayayyako cikin bacin rai " innani ai dama na dade da sanin kina adawa da hadin yusuf da nafisa, na fada aka ce Ba haka ba, gashi yanzu anyi walkiya kowa ya ganki, in Hajiya ai na Kara ma dan yaruwar miji, ke kuma fah? Karki manta ciki daya kuka fito da mahaifin yarinyar nan? Har me waccan zata nunawa nafisa? Da kika zage kina yabonta haka? Kowa yasan Hajiya da asiri ta mallake Alhaji Jamal, ba wani Abu ba, amma ita kanta da me tafi sauran matan nasa? Hajiya saa dai ta Riga tayi sake, yanzu kuma Sai dai taji da sauran yaran, don na tabbata yanda basu bar uban ba Ba zasu bar dan ba. Tun yanzu ma Kalli yadda yake rawar jiki, kamar wani sallamamme,." Nan fa table ya dauka baki daya, kowa na tofa albarkacin bakinsa. Hajiya ai kam da innani shiru sukayi suna kallon ikon Allah. Kuka sosai take, yusuf na gefe yana faman lallashi, tun da sukayi sallama da family and friends dinsu, take faman kuka. Don daga wurin dinner kowa zai Kama gabansa angwaye zasu dauki amarensu. Friends din yusuf suka ne zasu mai da kawayen hubby gidajensu, tun da taga kowa ya Kama gabansa ta fara aikin kuka. Har suka iso gidansu, tana faman kuka, shi kansa yusuf ya rasa yadda zaiyi da ita, da kyar ya samu ta fito daga motar, yana rike da hannunta suka nufi cikin gida. Direct dakinsa ya wuce da ita, ya zaunar da ita a bakin gadonsa, tsugunnawa yayi a gabanta hannunsa duka biyu cikin nata, ya zuba mata kyawawan idonsa. " princess please stop crying, na dauka yau ranace ta farin ciki a gare mu, why do you want to spoil it for us? " hannunta yakai kan kirjinsa " zuciyata bazata jure jin kukan kiba, kiji yadda take faman bugu, in kuma nima kukan kike son nayi to? " kanta ta kada a hankali, hawaye nabin kuncinta. " to ki daina kukan haka, in ba haka ba depenetly nima kukan zanyi," zama yayi ya jawota jikinsa, ya fara share mata hawayen. "see how u spoiled your face, look at your eyes? " zafin da yaji a goshinta ga jijiyoyin kanta sun fiffito yasa ya tabbatar kanta na ciwo, "kinga abinda kika Jawa kanki, jikinki yayi zafi, I'm sure kanki na ciwo. Lamo tayi a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, don wani ciwon Kai da zazzabi zazzabi take ji. Tun baaje ko ina ba ta fara kewar gida. Ji take kamar tace ya maida ita gida ta fasa auren. Kwantar da ita yayi, ya shiga toilet ya hada mata ruwan wanka, ya cika bap din ya zuba turaren wanka, da bobble liquid soap. Nan da nan toilet din yadau kamshi. Ya fito ya samu har bacci ya fara daukarta. Tashinta yayi taje tayi wanka. A hankali ta Mike ta nufi toilet din. Kayan baccinta ya ajiye mata saman bed, ya kwashi abinda zai bukata ya nufi daya bed room din don ya shima ya kimtsa. Masha Allah toilet din ya mata kyau sosai, white and gold. Gashi wadatacce, ban da bap ga Jacuzzi, duk Wanda Kake bukata,. Ta dade a cikin ruwan, Kafin ta samu tayi wanka, don ruwan ya Mata dadi, ga kanshi mai sanyaya rai. Ganin baya dakin, Yasa ta samu damar sakewa ta shirya. Rigar daya ajiye mata ta daga tana kallo, " not bad " ta fada tana murmushi. Cotton ce, tsawonta zuwa gwuiwa, Mai hannun brazer, sai cup da akama ado da wani silk and less mai daukar ido. Rigar farace kal. Bayan ta sa ta feshe jikinta da body splash, deodorant, perfume masu matukar kamshi ...Yana rungume da ita, sai faman sauke ajiyar zuciya yake, ga wani annuri daya cika fuskarsa.  A hankali yake tapping din bayanta, tare da yi mata kiss saman goshinta. Gaba daya jinta take kamar a sama, jikinta ko ina yayi tsami, ajiyar zuciya take, zuwa lokacin hawayen sun riga sun kafe daga kwayar idonta. Iyakar wahala yau kam tasha ta, duk da dauriya da juriya da tayi, dole ta gaza.  Don gaba daya yusuf yayi losing control dinsa. Baccine ya dinga fizgarta a hankali, in no time ta shilla 😴 ajiyar zuciya yayi, ganin bacci yayi gaba da ita.  Kiss ya mata tare da kyara matakwanciya a jikinsa, ya Kara rungumeta Kamar zaa kwace masa ita.  Murmushine ya subuce a fuskarsa, kansa ya dan shafa, tare da kara godiya ga Allah, daya kaddara masa samun hubby a matsayin matarsa, tabbas ba karamin baiwa Allah yayi masa ba, da samunta cikin rayuwarsa.  Duk yadda yaso bacci ya daukesa amma ina Abu ya gagara, still wani sabon filling yake ji yana taso masa. She can take it,  yasan tayi hakuri dashi,, he don't want to hurt her. He has to control him self.  Shi kansa bai San yana da bukata haka ba, sai yau.  He have 3 row supper, but still filling for it. Sai gab da asuba, bacci mai dadi yayi awon gaba dashi, hakan yasa suka makara. Sai 6 ya bude idonsa a hankali, bakinsa dauke da adduar farkawa daga bacci. hasken da gari ya fara ya hango ta labulen window. " subhanallah " ya fada under his breath, rabonsa da missing sallah a jam'i har ya manta when last yayi sallar asuba a makare. Kallon ta yayi, murmushi yayi, har lokacin tana manne a kirjinsa, she sleep like child. A hankali ya gyara mata kwanciyarta, ya nufi toilet. Tana jin lokacin da yake gyara mata kwanciya, don tun da ya farka itama ta farka, amma bata son ya gane idonta biyu, don bata San da wane ido zata kalleshi ba.  Tana jin karar Kofa  alamar ya shiga toilet. Ta bude idonta tana bin dakin da kallo. Kokari tayi ta Mike, da kyar don duk da ruwan zafin data shiga at night, still. Jikinta gaba daya ciwo yake, musamman kasanta. Din gisawa tayi zuwa dakinta, tana Mai zubar da hawayen azaba. Don duk taku ji take har kwanyarta. Ruwan dumin ta Kara hadawa, kamar yadda ya hada mata da daddare, ta shiga tana mai Kara fashewa da kuka.  Hubby akwai raki, bata son duk wani Abu daxai taba lafiyar jikinta☺. Koda ya fito, yaga bata dakin, kasa tada sallar yayi, ya nufo dakinta, don tabbatar da lafiyarta.  Jin motsin ruwa a toilet ya nufi kofar, amma to his surprise tasa key.  Murmushi yayi, ya Kama kan carpet din sallah dake dakin ya kabbara sallah. A hankali ta fito, tana din gisa kafa. Wood rope ta nufa ta, dauko doguwar Riga arebian da hijab. Sai da ta gama kimtsawa still tana share hawaye da cije lips duk lokacin da tayi taku.  Juyowar da zatayi sukayi idon hudu, da sauri ta dauke idonta, ziciyarta na bugawa da sauri da sauri.  Wani kunyarsa da tsoronsa ne suka cika zuciyarta. Kasa motsawa tayi daga inda take. A hankali ya tako inda take, rungumota yayi zuwa jikinsa, tare da sauke ajiyar zuciya.  Sumbatarta yayi saman goshi, sannan ya dauketa bridle style zuwa kan abun sallar. Ganin ta kabbara sallah, ya nufi kitchen kettle ya jona, tare da hada kayan tia a wani hadadden trey, yayi worming gas meat, ya zuba a wani hadadden bowl.  Koda ya shigo already ta idar da sallar, ta koma ta kwanta. Kujerar mirrow ya janyo gaban bed din ya daura trey din akai. Shigowarsa yasa hubby Kara dukun kunewa wuri daya. Rungumota yayi jikinsa " princess!!  Tashi ki sha tia, ko zaki Kara jin dadin jikinki. Kuka Mai karfi ta barke dashi, tana Kara shigewa jikinsa.  Lallashinta ya hauyi, cike da so da kauna, dakyar ya samu tasha tia din, ya bata pain killer. Kwance suke yana rungume da ita, kalmomi masu dadi, yake gaya mata, tare da shafa kitson dake kanta. Har a zuciyarta tana jin dadin wannan yanayin da suke ciki, tare da jin dadin kalmominsa, na nuna soyayya, da yabo gareta. Cikin muryarta Mai sanyi tace " dama haka aka nuna ma mutun soyayya, a kusa kashe shi? " Murmushi yusuf yayi " hakan ma ai duk cikin soyayyarne princess, da kin san yadda matsayinki, da kimarki suka Kara karuwa tsakanin jiya da yau da ke da kanki zaki ce a maimaita " ya fada yana dariya kasa kasa Share hawayenta tayi " Allah ya kiyaye, wallahi ni auren ma gaba daya na fasa, don bazan yadda ina ji ina gani ka kashewa gwaggo niba" Kara matseta yayi ganin tana kokarin kwace kanta. " waya ce miki aure na kashe mutun?  Ko kin taba ganin wanda aure ya kasheshi? " Tura baki tayi, cikin shagwaba " gani!!!  Numfashi ne kawai ajikina, meye ban banci?  Ni ka kiramin gwaggona, in ganta Kafin in karasa. " Dariya yayi cike dajin dadi " don Allah karki tafi ki barni, kinga ban gama shanye zumana ba, dan taimaka ki Kara min koda rown daya ne ." Kuka ta Kara fashewa dashi, tana yarfe hannu, bayan ta kwace jikinta dakyar " wallahi ban yadda ba, dama tun jiya nasan ka daina sona, shi yasa ka gana min irin wannan izayar, duk bai isa ba Sai ka kara sa sauran dan numfashin da yayi saura a jikina? Allah na fasa auren ka kiramin gwaggona nace " " me zaki ce mata in na kirata din? " ya fada yana dariyar ganin yadda ta tsure. " zuwa zatayi mu tafi, nasan baza ta yadda ka kashe mata jika, a banza ba " " ke yanzu kina tunanin akwai abunda zai rabaki da yusuf?  Ni dake mutu ka raba,  takalmin kaza. Gwaggo kam taji abinda yasa kika sa a kirata fada zaki ci, ni kuma in sha yabo, don I'm good taken care of u. " Ya fada yana mata dariya Haushi ne ya cika hubby ganin yana mata dariya.  Ga kafarta ta rike, jikinta ya Kara tsamin.  " please and please ka kiramin ita, na yadda tamin fadan, mutuwa zanyi "  yayi dai dai da durkushewar da tayi a tsakiyar room din,. Tana zubar da hawaye Da sauri ya nufo wurinta, dagota yayi zuwa bed din " I'm joking, ba abunda zan sake miki, me yake damunki yanzu?" Kamar bazata tanka shi ba cikin jan hanci tace " wurin na ciwo, kafata da jikina ko ina ciwo,  ta Kara fashewa da kuka. " Lallashi sosai yayi, da kyar ya samu tayi shiru. " Bari in sake hada miki ruwan dumi, ki shiga, zuwa an jima in ba wani improvement dole muje hospital a dubaki sosai. Very sorry I'm at fault " Ganin ya nufi toilet din, ta janyo wayarsa dake kan bedside drawer numbar gwaggo tayi dialing, bugu biyu muryar gwaggo ta cika kunnenta..                 ****************** Wasu kam basu more aure ba, wallahi.  Allah ya kyauta, a ce gari ya waye tun dazu, yanzu kusan karfe 7 na safe amma mata bata fito don kimtsa gidanta ba, balle nemawa mijinta abunda zai ciba. An bar komai hannun yan aiki.  Wallahi da ba daon gudun bacin ran malan ba, ba abunda zai Hanani yima wannan yaro aure, har yaushe zaka zauna da mata, komai Sai yan aiki zasu maka, ita tana can tana faman gantalin aiki, in ma tana gida ba abunda zata tsinana na ayyukan mata a cikin gida. " wai gwaggo ke da wa kike faman mita da safen nan?" cewar daya Matar dake kwance kan katifar kusa da gadon da gwaggo ke kwance. Tsaki gwaggo tayi " lamarin rayuwar gidan nan ke damuna, duba kiga gida cike da baki, amma matar nan ta lunkume a daki, Sai yan aiki keta hidima, ko ba komai ai ta fito ta kula da kowa ya samu kulawar daya dace" Tashi Matar tayi ta zauna tana gyara zaninta daya yaye " ki gode Allah, ko ba komai Alhaji bai taba kawo miki karar iyalinsa ba, ko ba a fada ba suna zaman lafiya. Bazan boye miki ba wani lokaci ina kishinki, ganin yadda Alhaji da iyalansa suke kyautata miki, ga jikokinki Masha Allah. Ni kuwa yanzu yaushe rabon nawa dan yazo inda nake, in ban manta ba yayi wata uku, Sai aike, bani da ikon zuwa gidansa, daga ni har yan uwansa, saboda wulakanci da izzar matarsa.  Rabon matarsa da kankiya tun bikin auta na, yau shekara ta hudu ake nema, haka yaransa. Ke fah!?  Duk Hutu suna tafe, baa cikakken wata uku bai kwashi iyalansa sun zo muku weekend ba.  Ina rokonki daki dauke idonki kan rayuwarsu, karki manta yan Boko ne, kuma yan zamani, rayuwar ta ban banta da ta da.  Ba komai ki dubi tarbiyyan yaran,  Masha Allah basu da aibu." numfashi gwaggo taja " duk  Abinda kika fada gaskiyane, ni aikin nan da take fita ne kawai ke cimin tuwo a kwarya.  Yaron nan nada arzikinsa dai dai gwargwado me zai Hana ta zauna ta kulamun dashi da jikokina.? Murmushi Matar tayi " let dai ki zuba musu ido, ki bisu da addua " " Sai nayi magana Kafin in tafi, don nakai makura " Kada Kai matar tayi tana murmushi sanin halin gwaggo na kafiya "ai shi kenan " ta fada "yar albarka na can ko ya take?  Gaba daya yau ban iya bacci ba, hankalina na wurinta. " Dariya Matar tayi " ke kam da takwararki sai a hankali, ana can ana cin amarci ". Wayar gwaggo ce ta hau Kara, kasan cewar Bata iya karatuba, alamamomi ne ake sa mata akan numbobin, Wanda yake taimaka mata wurin gane mai kiran. Hoton yara ukun da ta gani yasa tayi murmushi cikin jin dadi ta daga da sauri.  " yan halas Sunki ambato. " Salamu Alaikum " gwaggo ta fada Jin muryar gwaggo, hubby ta fashe da kuka, tuni hankalin gwaggo ya tashi, cikin kidima ta hau tambayarta lafiya. Cikin muryar kuka tace " don Allah gwaggona kizo, zan mutu "  " subhanallahi mutuwa kuma? To to!!!!  Gani nan " ko Kafin ta karasa hubby ta kashe wayar. Mikewa tayi, ta Zari gyale, already tayi wankanta, don ta Saba tana sallar asuba take wanka, Kafin ta fara aikace aikacenta. " ba dai gidanta zaki tafi ba, da farar safiyar nan? " matar ta fada tana kafeta da ido " hafsi kenan, ina naga ta zama? " " Sai naga bai dace ba, ki je gidan yanzu. " Harara gwaggo ta zuba mata " se ki rike kafata ai.  Yarinyar ta kirani Tana kuka, in kasa zuwa Inga dalili? " " sabon aurene fah?  Wane dalili kike nema banda hakan? " " Sai kiyi kuma hausi, ni na tafi, in sauran sun tashi ban ce ki fada musu inda naje ba " Da kallo hausi ta bita har ta fita a dakin. Kitchen ta nufa, maaikata na ta faman hada break fast.  Gaisheta sukayi, cike da girmamawa, don sun San matsayinta a gidan. Daya taga tana hada abinci a kan wani hadden trey. " wannan fah?  Ta tambaya " abincin Alhaji ne " ta Bata amsa cikin girma mawa. Tabe baki tayi.  " kuna da wandon Dakar abinci ko? " shiru yarinyar tayi don bata gane abinda gwaggo ke nufi ba. Dayar ce tace akwai, taje ta dauko.  " shirya min waannan kwanukan a ciki " tana nuna abincin da aka shirya na Alhaji. Cike da jimami yarinyar ta Fara jerawa a basket din. " kwa dafa mishi wani, dauki muje ki rakani wurin mota, Allah ya sa drevan naku yazo." A bakin kofar kitchen sukaci Karo da mommy Hauwa.  Cike da girmamawa ta gaishe da surukar tata. Ganin zata fita, ga yarinya da basket na binta.  Mommy Hauwa ta ce " fita zakiyi ne? Yatsina fuska tayi " eh!!!  Saina dawo, kya nemawa mijin naki abinda zaici, don nayi gaba da nashi " murmushi mommy Hauwa tayi tare da cewa " adawo lafiya " ta shige kitchen din. Jafar, jabir da wasu daga cikin baki mazan da basu koma ba.  Suna zaune kan kujerun compound din, da baa kwashe ba,  Har lokacin. Bayan sun gaisheta, tare da Wasa irin na jika da kaka.  Ta Kalli jafar " solobiyon mijina muje, ka kaini unguwa " gaba daya kallon jafar sukayi suka fashe da dariya. Harararta yayi " nemi direbanki, ni kam bacci zan tafi nayi." "baccin lafiya, da ranar nan?  Har yaushe ka tashi da zaka koma? " "oho dai ban zuwa ko ina " ya fada ya nufi cikin gida Da kyar ta samu jabir ya yadda zai kaita. Sai da suka fito, ya kalleta " ina zan Kai kine, ranki ya dade? " Murmushi tayi " gidan takwara " wani uban burki yaja, da badon Safiya bane da ba abunda zai hana Karo.  Ganin yana kokarin juyawa ta bata rai tare da rufeshi da masifa, harda cewa ya kuskura ya maida ita gida, to ubansa ne zai kaita da kansa. Sanin halin jarabarta yasa ya nufi gidan hubby rai bace. Da lamarin gwaggo da hubby. " ai sai ka dauko kwandon ka biyoni " ta fada tana maka masa harara, ganin yadda yake cika. A kofar shiga ya ajiye mata kwandon ya juya abinsa, tana masa maganar ya Jirata kar ya tafi. Shiko Allah Allah ya bar kofar gidan Kafin yusuf ya fito.  Key yayiwa Motarsa ya yi gaba. Tsaki gwaggo tayi " kai ka sani kuma dai " Door bell ta dan na kusan sau 5, ta dan dade tsaye kamar baza a bude ba,  can taji karar bude key, tsayuwarta ta gyara................      Not Edited.......   [01/03, 19:40] +234 706 771 8610: DA KAMAR WUYA                             Part 6       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau Duk yadda taso ya barta tayi wankan da kanta ki yayi, tana noke noke ga hawaye shabe shabe, tana ji tana gani ya zaunar da ita cikin bap din wankan. " naga alama yau dinnan hawayenki zai Kare, kuka tun jiya yaki karewa " ya fada yana murmushi Harararsa tayi, zuciyarta cike da jin haushinsa. " kika sake hararata, zamu hadu yanzun nan " ya fada yana kafeta da mayun idonsa, masu rikitata.  Sunkuyar da kanta tayi, tana Jan hanci. Da kansa ya mata wanka, ya nadota a towel kamar wata baby. Futowarsu a toilet din yaji kamar door bell na ringing.  Ajiyeta yayi, saman kujerar dressing  mirror. " I'm coming princess " ya fada yana barin dakin. Ganin gwaggo tsaye bakin Kofa, ya cika da mamaki, cikin girmamawa ya bata hanya ta shigo, tare da karbar basket din hannunta. Cike da kunya da jin nauyinta yake gaisheta.  Itam ma cikin sakin fuska ta amsa tare da tambayarsa hubby. Yana gaba tana baya, har dakin hubby da tun fitar yusuf ta kifa kanta kan dresser din, tana sauke ajiyar zuciya. Sallamar gwaggo yasa ta dago da sauri.  Mikewa tayi ta fada jikin gwaggo tare da sake sabon kuka. Sum sum sum yusuf yayi waje, yana murmushi, tare da jin jina shakuwar hubby da gwaggo.  Yau kam ya yadda da son jiki irin na hubby. Hirar su Hajiya ce ta fado masa a rai. Inda suke hirar halayyan yaran family dinsu.  Hajiya ke cewa " ai ni kinga habiba da Aisha ba mai sani rakasu labour room, sai dai ke, tana nufin Mmn samira, kuje tare.  Yara sai son jiki, basa son komai ya taba lafiyar jikinsu?  Dazu da naje gidan gaba daya Habiba ta hargitsasu da koke koke, wai ta yanke a hannu.  Na dauka zanga wani katon yanka, sai naga yan kan ma ba wai ya shiga bane, jinin da ta gani ne, duk ta rudasu da kuka, kamar yadda Aisha ke wannan iskancin a gidan nan. " murmushi ya Kara yi, tare da shigewa wanka. " ai ni kin ban tsoro takwara!!  Mutuwa fa kika ambata min, kin sani fitowa ba shiri " Baki ta tura cikin shagwaba, ga hawaye ta ce " numfashine fa kawai ajikina,  gara kizo in ganki Kafin na mutu. " Dariya gwaggo tayi " baza ki mutu ba  Sai kin santalo min kyawawan tattaba kunne. Allah ya miki albarka da kika tsare mana mutuncinmu, kika kawo budurcinki dakin aure, ni kam kin gama min komai. " " kafata kafarki, bazan yadda a kashe miki niba.  Dama ke kika zugani in ce aure nake so, na dauka auren dadi ne ai?  Ashe anani burdade ake ci. Kuma a haka kice kina sona? " ta fada cike da shagwaba " gatan kenan takwara, da kin warke shi kenan, na dan lokaci ne. Yan zu dai Bari kiga " ta nufi toilet Harararta hubby tayi " kiji mata wai na Dan lokaci,  bayan duk ke kika jamin ina zaman zamana. In da nasan dawan garin ai da sai dai mu karaci soyayyarmu a gida, in da ko hannu na bazai iya rikewa ba, balle. " tashi muje ki gani " " wayyo Allah na yanzu fah na fito daga wanka " " ke dalla rufamin baki, muje " ta hade rai. Dole hubby tabi bayanta tana dana sanin kiranta. Ruwa ta hada mata, da wasu itatuwa. Sai da ta tabbatar ta zauna Kafin ta fito. Ta barta a toilet din. Dube duben inda zata ga kasko take, bata gani ba, ta koma ta tambayi hubby. Gawayin kanti ta hada a kaskon,  ta dauko kujerar dorot ta daura a kai, hubby na fitowa ta zuba wani gari a ciki mai azabar kamshi, Tasa hubby zama a kai. " da nasan kema izayar da zakimin ke nan da ban kira ki ba " hubby ta fada tana kunbure kumbure. Murmushi gwaggo tayi " yanzu ya kikaji jikin naki? " Shiru ta mata, amma har ga Allah taji dadin jikinta, zata iya cewa ma ta daina jin ciwon da take ji a kasanta.  Sai abunda baa rasa ba. " tashi ki shirya, kwalliya nake son kiyi sosai. Bari in dauko abincin da nazo miki dashi. Baki hubby ta washe jin harda abinci gwaggo ta kawo mata, duk da bata jin yunwa. Super exclusive mai launin brawn and black, Sai shade din light yellow. Dinkin Riga da skeet 8 pierces dinkin ya zauna cas a jikinta, kamar wata yar tsana don kyau.  Jelar kitsonta da suka sakko har kafadunta ta tattara ta daure da ribbon.  Simple daurin Dan kwali tayi. Da simple makeup,  tayi kyau sosai, ga kamshin turaruka da humra dake tashi a jikinta. Washe baki tayi " Masha Allah,  in ce ko kina gode Allah bisa wannan sura da ya miki " kallon gwaggo tayi tana murmushi Gwaggo ta Kara da cewa " abinda nake so dake shine,  hakuri da juriya, duk mace da kika ganta a gidan mijinta ta kwashe shekara da shekaru to ba komai ya Kawo hakan ba Illa hakuri, juriya da jajircewa. Yanzu ne zaki natsu ki gane me dame mijinki yafi bukata a tare dake, don ki Kara in ganta zamanku.  Tsafta kula da jiki, kula da muhalli, tsaftar kitchen dinki da duk abinda zaa sarrafa a cikinsa. Tsaftar ban daki, da uwa uba turakar miji. A kalla kina samun wanka Kamar sau uku, zuwa biyar a Rana, na safe Kafin ya fita daban, na rana daban, sannan na dare watau na tarbar megida. Don Allah takwara ban da son jiki, nasan baki da kazanta, ki Kara dagewa, San nan kar ki yadda ki nunawa miji gazawarki ta wurin daukar nauyin bukatarsa. Ki zama me juriya.  Ki dage ki koyi girki nasan wannan uwar taki bata koya miki komai ba. Kin dai san gidan da mijinki ya fito. Kowa yasan akwai cima Mai kyau a gidan Jamal,. Karki biyo uwarki da komai Sai masu aiki zasuyi.  Don in baki dace da suruka Irina ba, tuni zata auro masa wadda zata kula mata da danta da kyau. Ko ta tasa min ke a gaba da rashin mutunci. " Murmushi hubby tayi " nifa ban son kishiya, naga kema baa miki ba, kike min fatan amin" ta fada tana tura baki "ba fata na miki ba, amma kika sake kikayi halin hauwa, kin hadu da kishiya kin gama yarinya. Ki zauna gidan mijinki ki kula da mijinki da yayan da Allah zai azurtaku dasu. Mijinki Nada halin da zai kula da duk bukatunki, in ma kina bukatar wani abun ne, GA Sana oi nan da zaki iya yi a gida, sun isa basai kin wahalar da kanki ba. " Shigowar yusuf ya katse musu hirar.  Sanye yake da lallausan voil fari kar da hula wadda ta dace da kayan sosai.  Kana ganinsa kaga balarabe sak, haskensa ya Kara fita sosai, ga wani kamshi Mai dadi da San Yaya rai na tashi. "Yau wa, zo kaci abinci " gwaggo ta fada tana janyo masa basket din. Murmushi yayi, tare da zama a bakin gadon,  hada ido sukayi da hubby dake kwasar farfesun Kayan ciki.  Murmushi suka aikawa juna, yayi mata blowing kiss.  Sunkuyar dakai tayi ta ci gaba da cin farfesunta.  Ya mata matukar kyau da kwarjini,  wani Karin son shi taji ya na bin jinin jikinta. Shi din ma haka, ya kasa dauke idonsa a kanta.  Duk da kokarin saita kansa da yake, tayi kyau sosai, komai Masha Allah. Beyond what he expected. Nasiha gwaggo ta musu mai shiga rai, Kari kan Wanda aka musu. Mika masa wayar tayi " Kira min wannan mai ranta memen kan" mirmushi yayi don yasan Wanda take nufi.  Saida ya Kira sau biyu tukunna aka daga, ya Mika mata. " to dan nema, zaka zo ka dauko nine ko  na Kira tsohonka shi yazo? " Hararar wayar yayi kamar gwaggon na gabansa. " kirashi man, sai me? " "au!!!  Haka kace?  To shi ke nan " ta kashe wayar. " Dani kake magana, ta fara lalubar number daddy su hubby.  Kira ne ya shigo wayar, yasa kiran daddy katsewa. Dagawa tayi, muryar jabir ne " gani nan zuwa " ya fada Kamar zai fashe da kuka " Dan nema, da karka zo man " " da baki kirashi ba, muje in mai dake " " aa,  barshi yazo, Dani yake magana ai. Ina ni ina fitar da ango daga gidansa. " ta fada tana kokarin tattara wormers din.  Da sauri hubby ta karbeta ta jera mata su. "ina kika samo wormers masu kyau haka? "  hubby ta tambaya tana juya karamin. " abincin ubankine nayo gaba dashi " daga hubby har yusuf tsayawa sukai suna kallon gwaggo.  Cike da mamaki " to shi kuma yaci me?  Hubby ta tambaya " wan nan ruwansu kuma " tayi ficewarta daga dakin Da kuka suka rabu da hubby, Sai da ta mata alkhawarin sake zuwa dubata Kafin ta koma tukunna,.                 ****************** Gaba daya ranar a  cikin baki suka yishi, masu zuwa Ganin dakin Amarya.  Tun daga ranar hubby ta San akwai babbar matsala tsakaninta da dangin  Mmn yusuf, don da yawansu sun kasa danne kishinsu gareta. Sai yamma can, su yusuf suka tafi bangajiyar surukai, yabar su yusra suna taya hubby gyaran gida. Nocking sukaji, suna tsaka da gyaran falo.  Asiya ce taje ta bude. Hayder, junaid, alim, amir, Hafiz da Hafiz omer. Kayayyakin cefane sukai ta shigo dashi da su bottle water, drinks, juices. A kitchen suka jibge musu.  " a taimaka a shigar dasu store mana " Aisha ta fada tana kallonsu, sunyi dai dai a falon. "aikin me kuke dabaza ku shiryasu da kan kuba?  Mu kam munyi namu, ya rage naku kuma, in kun so ku barsu a wurin " Hafiz ya fada yana kallon ta Harararsa tayi " dadin abun ba kutare muke ba " " na dauka ai kutarene " " ina wuni yayarmu, suka fada a tare, banda haydar dake danne danne a wayarsa. Suka fara gaishe da hubby data fito daga daki. Amsawa tayi tana murmushi, tare da tambayarsu gajiya. " Asiya kawo musu ruwa " ta fada tana kokarin zama a daya daga cikin kujerar dinning din. " barshi kawai yayarmu, Sai mun sake zagayowa, sauri muke, dama Yaya ne yace mu kawo sako " Hafiz omer ya ce yana mikewa. " na gode, sosai " ta fada tana hararar haydar da suka hada ido.  Kauda kansa yayi, yay gaba abinsa. Dublan alkaki, nakiya cin cin da sauransu tasa aka kulla musu Leda guda Asiya ta Kai musu har mota. " yayarmu za tayi kirki, yaushe zamu koma? " Hafiz omer ya fada yana cika baki da cin cin. " dole mu dinga zagowa, don nasan Anty Da kwadayi, zamufi maida komada da wuri. " amir ya fada Haka sukaita hirar, a tsakaninsu har suka isa inda zasu.                    **************** Amarci sosai hubby da oga yusuf suka sha, na tsawon sati biyu ba tare da ya fita ko ina ba, daga masallaci, Sai mein house da yake zuwa every 2days ya gaishe da iyayensa. Wani kyau ta Kara, da murjewar jiki, na ban mamaki. Ita kanta bata gajiya da kallon kanta, balle yusuf daya Kara susucewa a kanta.                 **************** Turaren ta karba tana fesa masa, kallon yake yana faman murmushi, ganin yadda ta turbune fuska, kamar zatayi kuka.  Hannunsa duka biyu ya daura a kafadarta.  " kiyi hakuri, it's just 2 days zanyi in dawo, in sha Allah.  Ke kanki kin San yanzu bazan iya yin nesa da keba na tsawon lokaci.  So please ki kwantar da hankalinki,  ki kulamin da kanki,  yanzu zan sa hayder ya kawo miki su Aisha su tayaki zama, Kafin in dawo. Rungumeshi tayi, tare da sake masa kuka, Mai cike da shagwaba, tana dan bubbuga kafa. Tuni ya Kara rudewa, tausayinta ya kamasa. Rungumeta yayi sosai,  yana bubbuga bayanta a hankali. Cikin murya Mai zaki, cike da shagwaba " how can princess survive without her king? 2 days it's like 2weeks to me " Dago kanta yayi, yana murmushi, tare da kada mata kai, alamar tabar kukan.  Bakinta takai kan nashi ta fara aika mai da hot kissing,  sun kai 10min suna abu daya. Dakyar ya samu yayi controlling din kansa, don ya san plan tayi don ta hanashi tafiya. Da gyar ya zameta daga jikinsa, tana Kara narkemasa.  Har mota ta rakoshi, Sai da taga fitar su daga get din, ta juya, cike da kewar mijin nata.  Hubby na zaune a falo, ita da yarinyar da take mata aikace aikace.  Ladi.  Suna kallon Hausa Film.  Su Aisha sukayi sallama.  Amsawa tayi cike da murnar ganin aminiyar tata.  Da sauri ta Mike suka rungume juna, suna ihe ihen murnar ganin juna. " ke kam baki da kirki, ban ma san me yasa na wani tare ki ba?  A ce tun washe garin ranar da aka kawoni, da kika zo, ban sake ganin kafarki a gidan nan ba, yan zuma nasan da badan yayanki ba, da yau ma banga ko keyarki ba " Dariya Aisha tayi " tuba nake matar yaya.  Dama nayi niyyar xuwa miki weekend,  ki tambayi yusra ma kiji, in baki yadda ba. " Harararta hubby tayi " daga ke har itan ina nan daku,  Sai na shuka muku rashin mutunci.  Tunda baku da kirki" " kiyi hakuri dama tare mukayi niyyar zuwa miki wuni " Sai lokacin hubby ta Lura da abida, dake zaune kan kujera ta daura kafa daya kan daya, tana kadawa a hankali,  idonta na kansu, tana harararsu, cike da jin haushinsu. " kiyi hakuri Anty abida.  Ban Lura tare kuke ba,  kwana biyu banga mutuniyar ba "  ta fada tana Kara sawa kusa da abidan fuskarta cike da faraa. Kallon uku kwabo abida ta bita dashi, ta kwabe baki.  " naga alama ai " ta fada a ya tsine.  Hubby bata damu da yadda abida ke yatsine yatsine ba. Don zuwa lokacin tasan matsayinta a wurinta. Tun last zuwan abidan 5 days ago taga take takenta.  Murmushi hubby tayi tana gaisheta tare da tambayarta mutan gidan.  Kamar an mata dole take amsata, tare da jin haushin hubby ganin yadda tayi kyau cikin lokaci kadan. " ina haydar din?  Kar ace a waje kuka barshi? " hubby ta tambaya tana kallon Aisha da suke magana da ladi. " kema kin fi kowa sanin halin mutuminki, yana ajiyemu ya juya abinsa.  Dama da kyar ya yadda ya kawo mu" Murmushi hubby tayi " Allah ya shiryi haydar da bakin hali,  na rasa inda ya samo bakar zuciya" " jininku ne, kawai bai hadu ba, amma kowa yasan he's good boy" Aisha ta fada tana dariya " arrogant boy dai " ta fada tana kin kimar jakar kayansu zuwa dakinta.                ***************** "Yau wa, make some things delicious, kin san ina koyon girki ne, yanzu "  hubby ta fada tana kallon Aisha.  Dariya Aisha tayi " yafi miki ai, ina can ina tunanin yadda zaki Kare, don nasan banda indomie, farar shinkafa, sai supergettie, kika iya. Ina tausayin yayana, ya Saba da kwasar delicious food. " Dukanta hubby tayi, "kin san yanzu na fara iyawa, yayanki na koyamin, next week zan fara zuwa catering school" " so dama duk wannan kadifirin da fiffika da ake, baa iya girki ba!!   Amma dai anji kunya wallahi "  duk kansu suka juya suna kallon abida dake tsaye a bakin kofar kitchen din. " haba ke kuwa, wane irin magana ce wannan.  " hararar Aisha tayi " ke Waya kasa dake? " Hubby tayi murmushi, tare da ma Aisha alamar tayi shiru. " Anty abida ke ya kamata ma kina zuwa kina koyamin wasu abubuwan please" Tabe baki tayi da Jan dan guntun tsaki  " ki nemi mai koya miki, tun dare bai miki ba,  da can me ya hanaki ki tsaya ki koya?  Muddin dai mukaga Yaya na rama, mataki zamu dauka, Wanda ba zai ma yarinya dadi ba wallahi.  Meye anfanin macen da bata iya girkiba? "tayi tsaki tare da barin kitchen din. Tana kada jiki. Suka bita da ido, cike da mamakinta😶😶😶.......... "Don't mind her" Aisha ta fada tana kallon hubby. Murmushi hubby tayi , tare da kada kai. "Me zamu girka Ne?" "Ehmmm!!! Fray rice, chicken deise, natural mango juice." "Good idea" hubby ta fada tana murmushi. " ni fa zanyi kawai ki dinga nuna min yadda zanyi" "Lallai Matar Yaya a serious, hakan ya Nuna min yadda ake ji da yayana, I'm so happy about that." " I will do any thing for My king " Dariya Aisha tayi " su King many a, Allah ya bamu masoya na Kwarai muma muji yadda ake ji, ko ma huta da iyayin hubby " Murmushi hubby tayi, " amin dai in da gaske kike. Kuda kuka CE sai kunga karshen Biro, tukunna" " in sha Allah  kam, sai na zama doctor Aisha Jamal Yusuf Oregon." " Allah yasa" " ya labarin karatu? Ko har yanzu kina nan akan bakanki?" Tabe baki hubby tayi " Ku dai da kuka kwallafa ranku, kuyi tayi. Hubby kam aure bautar ubangiji ta zaba,." " ilmi Nada dadi , ki daure ki ko ma school ko Kettering kiyi, zai anfaneki sosai a rayuwa. Ki daina bin zugar gwaggo don nasan duk hudubarta CE kike bi." " in muna magana ki daina sako gwoggona a ciki, raayina ne ba ruwan gwaggo. Zan dai ko ma islamiyya, don inji dadin Neman Aljan'nata" Haka Aisha taita nuna mata yadda zatayi, suna hirarsu gwanin shaawa. Har suka gama girki. " uhmm!!!! Gaskiya randa hannunki ya fada a girki, yayana zai kwashi gara. kinji yadda girkin yayi dadi?" Dariya hubby tayi " bar zugani yar uwa, a dai ci da hakuri kawai." " da gaske nake, ba wasa ba " " thanks, irin shi zan Ma king ranar da zai dawo " " good idea "                   **************** Suna zaune a falo bayan sun gama kwasar girki. Abida na dakin hubby, don tun da suka mata tayin abinci, ba Wanda ya kara bi ta kanta. Kallon kallo aka fara tsakanin hubby da Aisha. Abida CE ta fito daga dakin Yusuf daure da towel, ta Shiga dakin hubby minti kadan ta sake fitowa ta koma dakin Yusuf. Mamakine ya cika hubby, tabbas dakin a kulle yake ,ta Yaya abida ta samu keys din har ta bude? Ke nan bincike ta mata a daki? Dole ne ta taka mata burki don taga alamar in ta ci gaba da yi mata kawaici, ba karamin takata za tayi ba." Mikewa tayi ta nufi dakin Yusuf din, ranta na zafi,. Zaune ta sameta kan stool din gaban madubi tana kwalliya, kallonta tayi cike da raini ta ci gaba da abinda take yi. " duk dakunan dake gidan nan ki rasa India zaki baje hajarki sai nan? Bayan na tabbatar kin San hakan bai dace ba" Kallon sama da kasa tawa hubby " au!! haba? Ashe bai dace kanwa ta shiga dakin yayanta ba? A wace mashabar kenan? Don bani da masaniya" " ki Sani yanzu ba da bace, dakinsa sirrinmu ne, baya halatta gareki shigansa ba tare da iznin daya daga cikinmu ba. Wannan ya zama na farko kuma na karshe da zaki shigomin dakin miji kai tsaye, zan day komai amma ba zan yadda da tozarci ba" " ke har kin isa ki hanani shiga dakin Dan uwana? Da har kike gindaya min sharudda. Kin yi kadan wallahi" " kar ki yadda Dan sauran mutuncinki da nake gani ya zube, tun nuna shaida juna ki fita a dakin nan in ba haka ba, abun bazai mana kyau ba." Duk da abida ta tsorata da yanayin hubby, amma taurin rai ya hanata koda motsi daga in da take. Basu ji shigowar Aisha ba, sai maganarta da suka ji duk suka juya suna kallonta. Cikin harshen larabci ta farama abida magana " me yasa zakiyi haka? Kin San cewar hakan bai dace ba, Yaya ko lokacin yana gida baya yadda mu shiga masa daki balle yanzu. Kin manta fadan mom kenan? Duk gargadinmu da tayi amma na lura tun da suka zo kike nemanta da magana, bakya ko tsoron bacin ran Yaya, don muddin kika batama matarsa kamar kin bata nasa ran ne. Ina rokonki da kiyiwa Allah ki rufa mana asiri mubar gidan nan lafiya. " Jikin abida yayi sanyi, musamman data tuno irin farin cikin da ta gani a fuskar Yusuf lokacin da race itama zata biyo Aisha suzo tare, har alkhawarin sabiwar waya ya masu. Tabbas ko lokacin da take gida tun da suka fara tasowa ya hanasu shiga dakunan samarin gidan. Amma ya zatayi da dunbin haushin hubby da take ji? Hakika batason yarinyar ko dama can balle da ta zama sanadin rashin auren kawarta, yar uwarta da Yusuf. Kayanta dake kan madubin ta tattara, cikin jin haushi,. Ban gaje hubby tayi tare da Jan tsaki ta fice a dakin. Jingina hubby tayi da bangon dakin ta runtse idonta tana ambaton sunan Allah. " kin ci daraja daya, yau da kin gane ko wacece hubby, gobe ko an ce kiyi min iskanci bazakiyiba" ta fada a ranta tana Jan numfashi. Aisha CE ta dafa kafadarta " I'm very sorry, Anty abida bata kyauta ba, amma don Allah kiyi hakuri" Murmushi tayi " it's OK " Bayan fitar Aisha tabi dakin da kallon. Tsaki taja, iskancin abida har gadonsu sai da ta hau, ga alamar zama nan, gyara dakin ta karayi, ta nufi toilet anan ranta ya kara baci ganin kunfa ko Ina ga ruwa duk an zubar a kasan tails din, kamar ba bap a toilet din. Sai da ta tabbatar ta gyara ko Ina, ta saka turaren wuta, ta kulle dakin. A falo ta samesu, Aisha da Ladi na ci gaba da kallo, abida na kan dinning sai lokacin take cin Nata abincin. Direct wurinsu Aisha ta nufa, suka ci gaba da shaaninsu, like notting happen.                *************** " wai me kuke nufi ne? Bafa zata sabuba, in ci abinci da rana in sake ci da daddare." Da kallo suka bita, tana kwance a kan 3 sitter rike da wayarta. Aisha ce ta bata amsa da cewa " a kawai sauran abincin da zai ishesu, ba sai sun yi west din abinciba," Harararta tayi " bashi nake son ci ba, don kinsan ko a gida, bancin abinci sau biyu, naci da rana, ya isa Ku tashi Ku nema min abinda zanci." " ki dai ce in tashi, ita kam ai yanzu Matar Yaya ce, sai dai mu mu girka mata, ba Musa ta girka mana ba." Cikin larabci abinda ta fara masife Aisha " kefa naga wani raini kike son kawo min tunda muka zo, ki shiga hankalinki dani, ita har ta isa in shiga kitchen in mata girki? " " Allah baki hakuri, me zan dafa mini?" " tsaki taja, barshi banso aikin banza kawai , baa iya komaiba sai kadifirin tsiya" ta fito da wayarta tayi searching number tare da barin falon tana harararsu. Hubby da tunda suka fara ta dauke kanta kamar bata  falon. Don gaba daya tun da taga take taken abida, ta fita hanyarta, duk da Dama itama ba wani shiga harkarsu take yiba. " me kikaga ya kamata a dafa mata? " Kallon hubby Aisha tayi " rabu da ita kawai, in yunwar ta kwakule cikin ta nemi abinda zataci, Neman maganane kawai, ko a gida ba wani abinci take ci da daddare suya Suna nan zaune abida tazo ta wuce su. " Anty abida ina zuwa?" Aisha ta tambaya tana gaf da fita kofar da zai sadata da waje. " in da kika aikeni " ta fice a Bin ta. " Allah ya kyauta, nasan wannan Dan iskan saurayin Nata ne yazo, shi yasa ta nace ta biyoni, tasan in a gida ne bai isa ya taka kafarsaba." Hubby kam shiru tayi abinta, don bata son shiga hurumin da ba nata ba. Kusan 30 min sai gata ta dawo dauke da ledoji farare masu dauke da tambarin special suya. Ladi ta kalla cike da raini " ke maza ki hadomin tie, sauran kimin kazanta." Duk Kansu ba Wanda yabi ta kanta. Wayar hubby ce ta fara ringing, ganin mai kiran yasa ta daga, tare da nufar dakinta, don ta samu dama da sakewa tayi hira da King dinta. Wanda take cike da kewarsa. " hello princess, how's your day? " Tura baki tayi kamar yana kallonta cikin muryar shagwaba da Jan hankali " boring!!! I miss my King so much, how are you " " how can I be fine, without u by my side" Murmushi tayi cike dakin dadin kalamansa. " ya sokoto? Bayan kasha fura, kaci bula, da kilishi, ina zaka ita tunawa dani? Tun dazu nake expecting call dinka shiru, na kira ka yaki shiga." Dariya yayi, cike da jin dadin ya ce " very sorry tunda na shigo garin nan, sai yanzu na samu natsuwa, ga network ba kyau. Hira sukayi sosai, mai cike da nuna so da kauna, ko wanne yana kokarin nuna yan da yayi missing din dan uwansa.                 ***************** Yanzu nan da ku ka baje ina zan kwanta? Aisha ta kalleta tare da kara matsawa kusa da hubby. " wannan wurin ai ya isheki " tsaki tayi Allah yasa akwai mai banzan bacci a cikinku in koya mata hankali wallahi." Shiru suka mata, don sun San duk neman magana takeyi. Hubby ce ta musu sai da safe....                ****************** Yau 1 year ke nan da auren hubby da Yusuf, abubuwa da yawa na dadi, da akasinsu sun faru. Zama lafiya da kwanciyar hankali tare da tsantsar so da kaunar juna, kamar sa hadiya juna.ke tsakanin hubby da Yusuf, har lokacin hubby ko batan wata bata yi ba. Wanda ya kara hura wutar kiyayyarta a zuciyar dangin Mmn Yusuf. Hatta Mmn Yusuf din da take sassaucinta wasu lokutan, itama yanzu ta fara nuna damuwarta. Ganin duk Wanda sukayi aure a tare duk ko wanne nada dansa. Su haidar sun tsufa a Cyprus, in da suke karatu a Cyprus International University ( CIU ) shida friends dinsa. Inda yake karantar Computer science. Shida junaid, sai Alim da Hafiz health science, Hafiz omer da Ashir Jamil medicine. Aisha na Kaduna state university ( KSU) tana karantar health science, yusra na karantar geography. Hubby dai an samu da kyar anyi training na Kettering na 3 months. Yusuf yaso tayi joining dinsu Aisha tunda result dinta yayi kyau, amma ta nuna bata shaawa. Ganin hakan yasa ya rabu da ita. Islamiyya dake unguwarsu ta shiga daga 10 to 12. Mummy ta tayi fada sosai kan kin ci gaba da karatunta amma ko a jikinta. Don harga Allah karatun boko baya gabanta, tunda ta samu na karatu da rubutu and she can speak very well ai shi kenan.                  ****************** Gaba daya hankalinta a tashe yake, hada Maya kawai take tana tunanin yadda zata kwashe tsakaninta da yan uwan Mmn Yusuf, a Nigeria ma ya ta kare dasu balle kuma ta bisu har Niger. Niger din Ma bikin wadda itace tushen tsanar tata da sukayi. Babban damuwarta kasan cewar ba tare zasu wuce da Yusuf ba, Mmn Yusuf ta kasa ta tsare lallai sai ta bisu su wuce tare. Shikuma sai ana gobe daurin aure zasu iso da daddynsu. Aisha ma bazata samu damar zuwa ba, don suna tsakiyar semester. Abu ya hade mata goma da shirin. At lest da da Aisha zatafi jin dadi da sakewa. Don duk sauran matan dakin su Yusuf ba shiri suke yi dasu ba. Gin gine yake a jikin kofar dakin yana rungume da hannu idonsa na kan duk kan movement dinta. Ita kanta bata San da shigowarsa ba. Kallonta yake cike da tausayawa, ya lura tun da magana tafiyar nan ta taso, bata da walwala. Duk da tana kokarin boyewa karya gane halin da take ciki, wani sonta yaji ya kara mamaye zuciyarsa. Duk halin da take ciki da yan uwansa ba Wanda bai Sani ba, hatta da danben da suka kusa kwasa ita da abida, a gidan Ahmad yana da labari, amma dai dai da rana daya bata taba kawo mai kara ko korafin duk abunda zaa mata ba. Shi kansa zai so su tafi tare, amma ya ya ita dole yabi umurnin mummynsa, sai gargadi da Jan kunne da yama kannen nasa. Daga baya ya hada da lallashin su kula masa da ita sosai. Murmushi ta sake mai, lokacin da idonta yakai kansa, da gudu tazo ta dafeshi, bai yi wata wata ba ya cabeta sama ya fara juyi da ita kamar yadda ya saba, suna dariya...........     Not Edited.......  [01/03, 10:38] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 7       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... " wai yarinyar nan kwana biyu kin kara nauyi " Ya fada yana direta a tsakiyar dakin. Gimtse dariyar tayi tana masa harara mai hade da kallon love, " yar ni dinnan har zakace nayi nauyi? Randa na zama katuwa kuma fa? Kasan dai baka isa kace bazaka iya daganiba!! Don ba yadda zan ba, tunda ka saba min" " so dai kike ki buda min kirji, naga alama amma yar lukuta na nawa kuma, bayan yadda kike a yanzu?" Kafa ta fara bubbugaga cike da shagwaba,Wanda yasa duk kan jikinta juyawa, dama sanye take da kayan bacci. Rigace aimless da gajeran wandonta ko ciya bai rufe ba, Wanda ya fita da kyan sigarta. Tsayawa yayi yana kallon yadda komai ke juyawa gwanin shaawa, da burgewa. wani Abu yaji yana kara taso masa tun daga babban yatsansa har ysakarka. Jinshi shiru yasa ta tsaya da juye juyen da take. Kallo daya ta masa ta karanto tsantsar fitinan dake dankare a kwayar idonsa. Ido daya ta kashe masa, tare da daga kanta kadan alamar tambaya. Ajiyar zuciya yayi tare da murmushi, smacking ya mata tare da sanya hannu ya jawota. Kwasa tayi da gudu, still fuskarsa na dauke da murmushi ya bita, suka fara zagaye bed din dakin. Cafkarta yayi bai direta ba sai tsakiyar bed din dake cike da kayanta data barbaza tana zabar na tafiya. Dariya take tana maida numfashi, magana take son yi amma ko kalma daya ta kasa furtawa. Sun Dade suna kallon juna, cike da so da kauna, kafin yakai bakinsa kan nata ya fara kissing dinta. Ganin yana son wuce gona da iri, da kyar ta kwaci bakinta a nashi cikin maida numfashi tace " abincinka fa na jira a falo " kara jawota yayi jikinsa, ganin abun ba sauki yasa ta tallafi mijinta ta fara aika mai da nata salon cike da kwarewa da sanin ta kan mijin nata. Kukan shagwaba ta fara " Allah bazan yadda ba, ji yadda kamin da kayana" dakin yabi da kallo. A kwatin can gefe ya kusa bakin kofa, sai kayan da suke da a goge kowanne ya kama gabansa baa maganar guga. Shi kansa gadon da suke kwance kan wasu daga kayan ne, wanda fadin yamutsewarsu bata baki ne. " it's your folt princess, you look hot, " Kara shigewa jikinsa tayi Allah ya miki albarka, you make me a happeyers man on earth. Na gode Allah daya sakoki cikin rayuwata, Allah ya bamu zuria tsarka kakkiya. I'm very sorry da abinda ke faruwa tsakaninki da yan uwana, I known everything, I try my best to make things right. I known your worries, mu ci gaba da addua, wataran sai labari, ki dauka taki jarabawar kenan, don ko wanne Dan Adam da kika Ganshi yanada irin tashi jarabawar. Ki kula min da kanki sosai, na jama su abida da aira kunne sosai, in sha Allah ba wani matsala. Zanyi iyaka kokarina in ga na yi scuising time in zo da wuri, don nima hankalina ba zai taba kwanciya ba." Kwantar da kanta tayi a kirjinsa tana shafawa a hankali, ajiyar zuciya tayi " baka ci abinci ba fah?" Hancinta ya danja, yana murmushi, " me kike dafamin ne?" " you're favorite " Goshinta ya sumbata " thank u, I'm going to miss u" Hawayen da taji na Neman fitowa yasa tayi saurin mai dasu. " me too. " Bayan sun tsarkake jikinsu, suka nufi falo. Da kanta ta dinga ciyar dashi har ya koshi. Ga labarai na ban dariya da ta tanada, musamman don ta sashi nishadi. Cikin nishadi take ciyar dashi tare da bashi labarin dan fillo da babarbare, dariya sosai suke kwasa. Duk rashin son surutu irin na yusuf, in yana tare da hubby zaka sha mamakin yadda shima yake iya kokarinsa, wurin biye mata, hira  sosai yake zagewa ya mata,don ya lura shiru baya cikin kundinta. Duk yanda ta motsa idonsa na kanta. He never except irin wannan kulawar daga gareta, duk da auren soyayya sukayi,. Tsawon shekara dayan nan ba zai ce ga wani aibunta da ya ganiba. Kullun tana cikin tarairayarsa, da bashi kulawa, hatta abinci ya rasa when last da yaci abinci da kansa. Ta riga ta shagwabashi karshe, duk inda yaje Allah Allah yake yadawo gida. Idonsa ta hure cikin salon daukan hankali, ganin yadda ya zuba mata mayatattun idonsa baya ko kiftawa. Murmushi yayi tare da sauke ajiyar zuciya. Sai daya hadiye ruwan tie din daya kurba. Ya kalleta da dara daran idonsa, yana shigar dasu a hankali " I love u" murmushi tayi don inda sabo ta saba, akalla a rana takanji Kalmar a bakinsa ba adadi. Kiss tama bakinsa, da ta Dora goshinta kan nasa hancinsu na gogar juna " I love u more "  Sun Dade a na nuna ma juna kauna, kafin suka koma dakin ya tayata hada kayan da zata tafi dasu. Ranar kwana sukayi basuyi bacci ba.                   **************** Karfe 2:43 dai dai jirginsu ya sauka a Miami na kasar Niger. Mota biyu suka zo daukarsu,. Alhaji mamuda Hammani, ya ya ga Mmn Yusuf, kuma marikinta. Hamshakin Dan kasuwane, Wanda yayi fice a kasar Niger, wurin shigowa da Samar da kayan masarufi. Sannan dan siyasa, mai rike da mukamin dan majalisar tarayya. Alhamdulillah sun samu karba sosai, cikin mutunci da karramawa. Gidan cike yake da baki na nesa, yan kusan ma sun samu halatta saboda shirye shirye. Abida kam tuni ta shige cikin kawayen Amarya. Dayawansu dama duk yan uwan junane. Hubby na zaune ita da Aira, sai kannen Hajiya Ai dake ta aikin ware kayan Amarya. A hankali Aira ke janta da hira, tana gaya mata matsayin kowa a wurinsu. Ajiyar zuciya hubby tayi don bata taba zaton family din suna da yawa haka ba. Kwanciyar hankalinta, da tun da tazo bata samu matsala da kowa ba. Hatta abida silent treat ta mata. Kamar yadda Aira ke mata a da. Ita dai bata nuna bata son taba, amma ba ruwanta da duk wani harkarta. Daga gaisuwa shi kenan bata kara bi ta kanta. Amma ikon Allah yau ita Aira kewa hira? Muryar Aira ce ta dawo da ita daga dogon tunaninta. " nifa gidan Innani zan gudu, don gaskiya gidan nan ba dadi zai yiba, duba tun yanzu har gida ya cika." Murmushi tayi don tana yawan jin labarin innani a bakin Yusuf. So she known who she is. " kiyi hakuri mu zauna a nan, ban son zama ni kadai" Tabe baki Aira tayi " ba nisa fa, 3 houses ne kawai a tsakaninsu, in zaki je muje, amma ni bazan iya zama a nan ba gaskiya, ko dama can nafi sauka a gidanta, in munzo" " OK zan tambayi mommy in ta yadda sai muje" Saurayine da ba zai wuce 25 years ba,dogo wankan tarwada, yana da kyau sosai, ga alamar Hutu, da kwalisa bayyane a tare dashi, kallo daya zaka masa kasan irin mazan nan ne masu aji. Kyau, kudi, ilmi. Shigowarsa na uku kenan falon in ba batan lissafi nayi ba. Daya daga cikin matan dake jera decorations a cikin kwali ta dago ta kalleshi tana murmushi " lafiyarka kake ta mana sintiri a kai?" Keya ya dan shafa, yana murmushi idonsa na kan su Aira dake can gefe, suna hira sama sama da hubby. " kaji cikin ummana? Naga duk dakin nan iyayenane? Meye a ciki don na shigo?" Dariya sukayi gaba dayansu. Dayar ta ce " kaji da gulmarka, nasan sintirin da kakeyi ai, Mara kunyar banza, ina tun safe muke nan muna aiki? Ko keyar ka bamu gani ba sai yanzu, zaka ishi mutane da sintiri, bako kunya " " wayyo!!! Ai sai yanzu na harbo jirgin" wadda ta fara magana ta fada Ganin duk sun hayayyako masa yasa cikin borin kunya ya ce " nifa ba wannan ya kawo niba, kuke Neman fassarani, snacks nake so, Hajiya tace in zo wurin cikin umanta in karba" " kadai ji dashi, yaro" suka fada suna masa dariya. Kallon Aira yayi " please sister ki karba ki kawo min ina waje, kafin wa annan matan su tsitstsigeni" " OK" ta fada tana mikewa daga inda take zaune. Wani mayataccen kallo ya bi hubby dashi, kafin ya fice a falon. Hubby kam bata ma San wainar da suke soyawa ba, don idonta na kan waya, suna charting da junaid, sai Aira da ke mata hira jefi jefi. A waje ta sameshi da friends dinsa, sun shinfida katuwar dadduma, ga kayan shayi nan birjik ko wanne da kofinsa a hannu. "Mai hali bai fasa halinsa, iya saninta da Yaya Khalil duk yamma yake hada wannan majalisar ta abokansa, asha shayi, ayi musu, ayi hira da dariya. Da alama shi zai gaji Alhajin su ta fannin siyasa, don yanzu haka ya kammala degree dinsa na biyu akan political science. Duka duka satinsa daya da dawowa gida Niger. Sabanin sauran yayyensa dake harkar kasuwanci. Sallama tayi cikin muryarta mai sanyi. " Yaya Khalil gashi! " ta mika masa trey din. Murmushi yayi, Wanda ya bayyana kyawawan hakoransa farare masu dauke da wushirya. " thanks siste", Gaishe da friends dinsa tayi, sannan ta juya zata koma ciki. Biyota yayi da sauri " 2 min sister" tsayawa tayi, tana kallonsa tare da jiran mai zai ce. Murmushi yayi, yana shafa dan kyakykyawan gajeren gemun da ya bari. " na ganki da wata?  I don't know her, please wa ce ce ita?" Gaban Aira ne ya mugun faduwa, mu samman ganin yadda yake ta sake mata murmushi. " she is our Anty, Matar Yaya Yusuf ce" Nan take annurin fuskarsa ya kau, hannu yasa yana shafa lallausar sumar kansa. Ji yake kamar ya kwala ihu, saboda abinda ya tsaya masa a kirji. Tunawa yayi Aira fa kallon sa take, zata iya harbo jirginsa, Wanda hakan bazai musu dadi ba. Murmushi ya yi, cikin basarwa " amma baki da kirki, shine baki min bayani ba in kwashi gaisuwa" Murmushi tayi " sorry na shaafa ne" " shike nan, bari in je na bar friends dina, zan shigo anjima in kwashi gaisuwa " " OK no prb" Jiki a salube ya koma wurin friends dinsa, nan suka dinga tsokalarsa wai yayi new catch. Ajiyar zuciya tayi " iko sai Allah, bisa duk kan alamu ya kamu da son hubby, shin bai San da alkawarin hadin aure tsakaninta dashi bane? Bisa dukkan alamu bashi da masaniya a kai. Bayan hadin auren Yusuf da Hafsat ya wargaje, shine suka maida abin kan abida da Khalil, nan take abida ta nuna ita bata yadda ba don akwai Wanda ta ke so, juyin duniya taki, ganin haka yasa aka yanke shawarar a hada Aira da Khalil. Baa samu matsala a wurin Aira ba, don lokacin ko secondary school bata gama ba, bata fara kula samariba. Wannan kenan. Jikinta a San yaye, ta koma ciki, don gaskiya tana matukar son Khalil, tun ba yau ba, yana burgeta sosai,.                ****************** Sosai innani ta karbesu, mu samman hubby. Abin ya matukar burge hubby, yanda innani ta dinga nan nan da ita. Innani kanwa ce gasu Mmn Yusuf, su uku Allah yaba iyayensu. Itace karama. Yaranta uku. Khadija ( kadi) wadda saa ce gasu abida, sai Fatima ( ya fati) Saar su aira, sai auta umar, Wanda duka duka shekarunsa biyar kenan, don har ta cire ran sake haihuwa, sai ga ciki, on expected. Mijinta Dan kwangilane, yana da rufin asiri sosai. Dakin kadi aka sauke hubby, kasan cewar kadi na cikin kawayen Amarya, yasa ya xama hubby ce kawai a Dakin. Sai Aira da ta sauka a dakin Best friend dinta yah fati.                  *************** Lallausan cotton less ne a jikinta kalan lilac da milk, dinkin straight skirt, dinkin rigar ambreller ne, zuwa gwuiwa. Dinkin yasha aiki ga stone sai daukar ido suke, set din White gold tasa mai hade da siraran bresslet guda biyu. Dan kwalin less din tayi hadadden dauri dashi Wanda ya kara fito da kyan fuskarta sosai, simple makeup tayi, ta feshe gikinta da turaruka masu matukar kamshi da tsada. Don hubby akwai son kamshi, ta hadu da oga Yusuf da baya jin tsadar siyan turare komai tsadarsa.  Gyale milk color ta yafa, sai takalmi da Jakarta milk and lilac. Juyawa tayi tana kallon kyan da tayi ta jikin dogon mirrow da  ke manne a side din dakin, Wanda zai baki damar ganin Head to toe dinki. Gadiya tayi ma Allah daya kagi halittarta. Take Yusuf ya fado mata. Murmushi tayi. Shigowar yah fati ne ya dawo da hankalinta. " woww!!! Masha Allah, Matar Yaya kin hadu ba karya wallahi" yah fati ta fada tana bin hubby da kallo, fuskarta fal murmushi. " yayanmu ya iya zabe, irin wannan full option haka" Murmushi hubby tayi tare da hararar yah fati, don dan zaman da tayi da ita daga jiya zuwa yau ta lura yarinyar akwai barkwanci, ga saukin kai,.jininsu ya hadu, kamar yadda ya hadu dana innani. Kadi ce dai har lokacin basu haduba. Ganin hararar da hubby ke aika mata, yasa tayi dariya, "Matar Yaya kefa muke jira, don in mun rakaki can gidan, mu kam gari zamu shiga" Nan danan fuskar hubby ta canza. su tafi su barta da wa? Bayan dasu kadai take iya sakewa, su ke debe mata kewa, tunda ba sanin kowa tayiba. " ban gane zaku shiga gari ba?" " zamu je gidan wata friend din mu ne, daga nan Yaya Abba zai kaimu yawo, kin San kanwar taki, kamar shan shani take,." Marai raice fiska tayi " please karku tafi Ku barni ni kadai, kunga Ku kadai na saba da, kuyi hakuri mu zauna" " wai zaman me kuke a daki? Daga bari in je in kirata kin zauna kamar an aiki bawa garinsu!"  Da kallo tabi hubby " kinyi kyau " ta fada tana murmushi " thanks, don bakuga kanku bane, na tabbatar kunfini yin kyau" hubby ta fada tana mayar mata da murmushin Kallon Kansu sukayi, tabbas ba karya sunyi kyau sosai, sanye suke da atamfa super exclusive Riga da skirt Wanda kowacce yabi jikinta das gwanin shaawa. Komai nasu iri daya. Don dama haka sukeyi in sun hadu, komai iri daya suke sawa like twin's. A fisge kuma akai saa suna kama da juna ta wurin hasken fata, da yanayin bakinsu. Don itama yah fati badai kyau ba, babanta buzune, mahaifiyarsa kuma babarbariya. " kin dai zagemu kawai, "  yah fati ta fada tana dariya. " zagi ko gaskiya. Look at you" hubby ta fada tana nuna su jikin mirror din. " kina wuri ai bamu isa yin magana ba. I had a lot about you. Ashe ma kinfi yadda ake kwatan tawa " ya fati ta fada tana murmushi " haka dai kika ce, but ban yadda ba " Haka sukayi ta musu, cikin anna shuwa. Kafin daga karshe zuna nufi gidan bikin. Mmn Yusuf ce ta bukaci su aira dasu zagaya da hubby ta gaishe da sauran muta nen gidan. Sai a lokacin hubby ta tabbatar da girman gidan, don hatta yaran gidan manya su uku a nan cikin gidan suke zaune da matansu, kowa part dinshi daban. A part din babban Yaya badamasi suka samu sauran matan. Matar badamasi hilwa, ta karbesu cike da faraa. Tana Jan yah fati da wasa, da a lama mutuniyarta ce. Ya fati ce ta gabatar musu da hubby. Sannan ta fara introducing dinsu ga hubby, hilwa Matar yaya badamasi, sai yasin Matar yayaKabir, sai humaira Amarya a wurin Yaya Abba. Ya fati ta karashe tana dariya. Dariya humaira tayi " fadi ki kara, uwargida, kuma amarya. In zaki zage ki nemo naki, ki zage don na tare gaba na tare baya. Don haka a kara gaba a daina shin shina min miji." Duka dariya suka sa, ganin yadda humaira keyi. Banda yasin data hade fuska sai wani harare harare take. " oh !!! Ji yadda kike wani tada jijiyar wuya. Kisa ranki a inuwa da ina da bukatarsa da baki samu shigowa ba, don kiji. Ni nan da kika gani sai na zaba na darje. Mijinki ya zama second hand yanzu. Ki rike kayanki." " kin dai ji tsoro kawai" humaira ta fada tana dariya " Allah ya kiyaye in ji tsoronki. In ina da bukata, kwace shi ba zai min wuya ba, ke kinsan haka." " oho dai abi wani sarkin '' Hilwa ce ta katsesu da cewa " kun bani kullun kuka hadu sai an zubar da hali. Wannan ma ya hadaku ai karasashi zakuyi" " barta kawai, yanzu haka ma dashi zamu fita, please Anty hilwa ga amanar Anty hubby a hannunki yanzu zamuje mu dawo." " lallai ne, ke yanzu kina kallo yarinya karama tana kokarin juya miki miji.? Kar kiji tana wani dadin bakin ba son shi take ba. ki sake jiki a miki sakiyar da ba ruwa.yan matan yanzu da suke neman miji ido a rufe, balle an samu ready made. Kina nan sai dai kiji labari yasha ban ban." Yasin ta fada cikin yatsina tana kallonsu a Dage. " iko sai Allah, cin dankon har da su kaza.? Ina ruwan agwagwa mai bakin baki. Allah mun gode maka da kasa sauran garin ba baki bane kamar dayan, da kunun ba zai shawuba." Ya fati ta fada tana kafeta da ido cike da rashin kunya. " karki fara!!! Ko yanzu in tattaka yarinya a wurin nan" " tafdijan!!!! Da kin tarowa kanki mach wallahi. Kuma kashedi ban saka mutun ba ban son ya tsoma kansa. Ehe!!!!!!! Shish shigi ba aji" Tashi yasin tayi zata fallawa yah fati mari, da sauri humaira ta tare, tare da janye yah fati da sauri. " haba ke kuwa? Wannan ai ba girmanki bane." Humaira ta fada tana janye yah fati. " abinda kike bakya kyautawa, na ga dai ba da ke take ba? Bana son irin haka. Ke ce babba ya kamata ki kama kanki. Da baki tanka taba ai bazata gaya miki magana ba." Harara yasin ta makawa hilwa " dama ai ke kike daure mata gindin yiwa mutane rashin kunya." Kallon su yah fati hilwa tayi " ki wuce ku tafi kayanku." Harara ya fati ta jefawa yasin tare da Jan tsaki, ta ja hannun Aira da tun dazu ta daskare a wurin tana kallon ikon Allah. Sukayi waje. Hubby ji tayi kamar ta bisu. Don gaba daya  jinta take kamar akan kaya. Ga wani kallon banza da yasin ke aiko mata, kamar ita takar zomon. " gaskiya ce bakwaso, ni kuma sai na fada, kina wani yashe mata baki, ke a dole wasa, baki San a wasa ake cutar ka wani lokacin ba! Ga example nan a gabanki ai." Ta  nuna bubby da yatsa Cikin bacin rai hilwa ta ce " kinga ban son dibar albarka, zo ki wuce gidanki tunda ke har abada baa iya zama lafiya dake." " ko baki ce in fita ba, tafiya zanyi. Don bana zama inuwa daya da snatchers. Gashi nan Allah ya kama su ai, dan farin cikin nan da kowa ke samu, da karuwa sun rasa, har yanzu shiru. Waya Sani ma ko juya ce, an gama gantali a titi, an ga sankacecen yaro an manne masa. " Duk inda bacin rai yakai hilwa da humaira ransu ya baci. Hubby kam baa magana zuciyarta ce taji tana mata wani zafi, ina ma ace ba bakunta taxo ba, da yau yasin sai ta raina kanta, sai tasan ta taba hubby. Duba da duka duka bazata wuce Saar taba. Kallon yasin take, mai cike da maanoni da dama. Har zata fita ta juyo, tayi saa kuwa duk suna binta da ido. Murmushi tayi " da kika tsareni da ido, in fitsarin kaza kunfa ne, wata tayi mana. Nan da wata Tara muzo suna. In har ba juya aka kwaso mana ba. Snatcher kawai" tayi tsaki ta fice......... " kiyi hakuri don Allah, wallahi halinta ne, duk nan hakuri muke da ita." Humaira ta fada cike da damuwa Hilwa ta kara da cewa " karki sa abinda ta fada a ranki don Allah. Nasan da zafi, kwata kwata bata iya magana ba, bata iya ban bance kalaman da ya kamata ta gayawa mutun, komai yazo bakinta fada take." Murmushi hubby tayi mai ciwo. " ba komai ya wuce" Hira sosai sukayi ta Jan hubby dashi, cikin kan kanin lokaci ta sake jikinta, don hubby akwai saurin sabo.                 ******************* Yau kwanan su hubby biyar a garin Miami. Zuwa lokacin ta saba dasu hilwa da humaira sosai, in ka gansu kamar dama can sun San juna. Hubby mai farin jini ce, da shiga rai muddin zaka zauna da ita na dan lokaci, tuni zata shige ziciyarka. Kamar yadda ta samu masoya haka ta samu makiya da yan hassada (Allah ka mana tsari da hasiduna) Yasin da mukarrabanta dama kadan suke jira, su dinga yada mata da habaici da mafanganu,dasu gori. Bata daga kanta ma balle ta nuna musu ta damu da abinda suke yi, sau da yawa su humaira ne masu shiga mata suyi uwa suyi makar biya. Hakika sun nuna mata kauna wadda bazata misaltu ba. Sai ana gobe daurin aure su Yusuf suka sauka a Miami. Shida Alhaji jamal, Ahmad, Sai Mmn samira da  ummu sulaim. Wai zo kaga murna wurin hubby, ganin ummu sulaim. Don tun bikinsu da suka raka ummu khulsum gidanta a Lebanon suka riketa a can.               ****************** Alhamsulillah yau su hubby suka dira gida Nigeria. Da kyar ta lallaba ummu sulaim ta bita su kwana biyu. Don ba karamin kewar juna sukayi ba. Koda ummu khulsum tazo haihuwa gida, lokacin ummu sulaim na shirye shiryen exams a can aka barta.                  ****"""*""********** A kwana a tashi asarar mai rai, inji masu iya magana ( but nah true oo) yau auren hubby da Yusuf 4years kenan. Abu buwa masu dadi, da akasasinsu sun faru. Har lokacin ko batan wata bubby bata taba yiba. Su Kansu abin ya damesu, Sai dai duk asibitin da sukaje a ka gama gwaje gwaje zaa ce musu komai normal. Ba wata matsala a tare dasu. Yanzu haka satinsu daya da dawowa daga Egypt, ganin doctor, suka wuce saudi don yin umra. A hankali ya tako in da take tsaye a gaban mirror tana shirin tafiya suna gidan Ahmad. Matarsa munaya ta haifi second yaronta namiji. Rungumota yayi jikinsa yana shakan kanshinta, yana faman limshe ido. Murmushin karfin hali tayi, duk a kokarinta na boye damuwarta. Don tun da akayi haihuwarnan take fuskantar wulakanci da gori iri iri. Hatta Wanda bata taba tsammanin haka daga garesu ba. Balle yau da gidan zai cika. Shafa lallausar sumarsa tayi tana kallonsa ta mirror din. " nayi latti fah!!!" Ta fada cikin shagwaba "I know " ya fada yana juyo da ita, suna fuskantar juna. Kallonta yake cike da tausayinta, yayi mata kiss a goshi, hannunta duka biyu cikin nashi " take good Care of your self. Karki bari maganar wawayen cikinmu ta dameki, Allah shike ba da haihuwa ga Wanda yaso, ya hana, Wanda yaso, A lokacin da yaso.Keep that in mind." Murmushi tayi " in sha Allah " Yana rike da Jakarta suka fito, tana bashi labarin yah fati da yasin suna dariya. Don lokacin yah fati na matsayin Matar Yaya Kabir, kishiya ga yasin. Zo kaga drama. Sai da ya tabbatar ta zauna dakyau ya mika mata jakar, ya rufe mata kofar, ya koma driver sit, yaja suka nufi gidan Ahmad, dake kusa dasu. Sai da ya tabbatar ta shiga tukunna yaja ya tafi. Da Anty samira suka fara cin karo,. " manyan mata, sai yanzu ake ganin Ku?" Ta fada tana karewa hubby kallo. Murmushi hubby tayi " kai bisa wuya,   ina kwana" " lafiya kalau, gimbiya a gidan Yaya Yusuf. Zan zo dai abani sirrin nan" " Anty samira kenan, sirri kam ai yana wurinku " Ido samira ta dan fito dashi " suwa ? Ke dai kice bazaki bani ba kawai." Ganin Jan maganar zaiyi yawa yasa hubby saurin katseta, " su Aisha fah?" Tabe baki tayi " suna ciki " Da sauri tabi hanyar da zai sadata da falon gidan. Da kallo samira ta bita tana tabe baki.                     ************** " kai amma less dinkin nan yayi matukar kyau, baki ga yadda ya fito da keba wallahi" hubby ta fada tana kallon munaya Murmushi munaya tayi don irin matan nan ne masu son ace sunyi kyau, ko kuma abunsu ya burge. Don yar karyace ta karshe. A kwai daukar wanka kam. " thanks Matar Yaya. Kin ganshi musamman nayi oder dinsa daga England. Da  aka kawo sai naji bai yi min ba. Amma sweetheart ya ce ya masa kyau, shi yasa na dinka, da kyauta zanyi dashi." " yayi kyau sosai, ba karya kin fito " Murmushi munaya tayi cike dajin dadi " thanks " Anties dinsu Ahmad ne suka shigo. Dayar ta kalli munaya tana murmushi " mejego ta fito ras, wannan kwalliya haka kamar zaki gasar sarauniyar kyau." Dayar ta amshe da " masha Allah kyau ya tarda kyau " Hubby ce ta fara gaishesu, ba yabo ba fallasa suka amsa. Dayar ce ta dawo kusa da hubby " yauwa dama ina son magana dake, " Gyara zama hubby tayi tana kallon ta cike da ladabi, don ta girmeta nesa ba kusa ba. " yanzu don Allah Habiba me yafi wannan dadi?" Tana nuna munaya mace duk kyanta duk kudinta, duk nasabarta in bata haihuwa meye anfaninta? Ina baki shawara tun wuri in har kin San da gaskene kwayoyin hana daukar ciki kike sha, ki shafama kanki lafiya ki bari. In kuma matsala ce Ku nemi magani tun kan lokaci ya kure miki. Don mace lokacinta takai tacce ne, ba kamar namiji ba. Kar kiga kin mallake miji, sai yadda kikayi dashi, akwai ranar kin dillanci. ban da haka ma ai haihuwa rahama ce. Shawara ce, don ni bazan fada a bayan idonki ba, kuma ba zan iya shiru ba." Tunda ta fara maganar kan hubby na kasa, duk kokarinta na danne kukanta ya gagara. Hawaye ne suka fara bin kuncinta. Jin Matar tayi shiru dayar ta amsa " gaskiya kam, surutu yayi yawa a kanki. Naji ma kamar aure uwarsa take nema masa " Da sauri hubby ta dago tana kallon matar. Itan ma kallonta take yi " da gaske gara kinsan abinda kike ciki. " haba Ku kuwa, Ku kyaleta taji da abunda ke damunta. Ni nasan hubby bazata taba yin abin da ake fada a kanta ba, suma sun San haka, son zuciya ne, kawai da kin gaskiya. Haihuwa kuma ta Allah ce, ni nasan da ana siyarwa da kun samu sun kai goma a wurinta, yanda take son yara." Munaya ta fada tana zama kusa da hubby Maganganu masu sanyaya rai ta dinga gaya mata, har ta samu natsuwa, suma hakuri suka bata . tace ba komai ta gode. A ranar hubby tasha bakaken magan ganu da habaici iri iri. Su Aisha ne su ka dinga shiga mata, su dinma daga baya hanasu tayi. A daddafe takai 5, ta zame jikinta tayi gida. Kuka ta sha kamar ba gobe, sai da tayi mai isarta sannan ta nufi toilet ta wanka  ta dauro alwala. Ko da yaje daukarta su Aisha suka shaida masa ta Riga ta tafi. Kamar yadda ta saba masa komai yauma haka, ko afuska bazaka taba ganin damuwa ba. Shima bai tada maganarba duk da Aisha ta gaya masa komai. A kullun addua da godiya yake ma Allah daya azurtashi da mata ta gari.  Duk abunda yan uwansa zasu mata bata taba kawo masa kararsu, saanninta in sun mata ta rama, in ka girmeta ta kauda kanta. Ko a fuska bata taba nuna masa an bata mata, ko an mata ba dai dai ba.                 ******************* Zaune suke a babban falon yaran gidan, bakajin komai sai karar cokula da tashin muryoyi maban banta, da dariya. Ummu sulaim, Ummul khair, Aisha, sai yaran uncle omer asima da asiya. Ko wacce na cikin farin ciki sai zolayar juna suke. Gwanin shaawa. Da sallama ta shigo falon. Wani ihu Aisha tasa ta rungumota tana murnar ganinta. Ita din ma dariya tayi tana kara rungumeta. " ke karfa ki karya mana Matar Yaya" asima ta fada tana dariya. " congratulation my betsy " hubby ta fada tana mikama Aisha hannu bayan sun saki juna. " thanks, na dauka ai bazaki zo ba " " ni a wa? " Hubby ta fada tana dariya.  Sadi driver yayi sallama sai da suka bashi izni bayan sun amsa ya shigo da wasu manyan kwalaye guda biyu ya gaishesu, ya ajiye ya fita. Gaisuwa suka fara cike  da kaunar juna. Suna tsokanan hubby. " congratulation to you too " hubby ta fada tana rungume ummu sulaim. " thanks sister " Zama hubby tayi kusa da Aisha. " to su alhuda huda, an kammala degree an dire, what is next? " Duka Aisha ta kai mata. " tun da kin ji tsoro kinki direwa. Mun dire kuma sai A B U, kin ga mun zama daya kenan." Dariya hubby tayi " wane ke yarinya, kya hada Wanda ya ke da 4 years experience da Wanda ya shiga new? Na gaba yayi gaba,." Dariya sukayi " gaskiya ne kam, za muzo daukar lectures, don gaskiya kina bala'in burgeni, yan da ake kula da yayanmu, ina son nima in sace zuciyar sweety na, da irin waannan salona. Ya zama ba kowa a gabansa sai ni." Asiya ce ta tashi tsam daga inda take zaune ta koma kusada hubby dake zaune kusa da Aisha, ta zauna. " gaskiyarki sister Aisha, nima please zan zo a bani horo na musamman." Dariya sukayi gaba daya. Ummul khair ta rike haba tana dariya " amma dai rashin kunyarki yayi yawa, ki bar manya suyi maganarsu, ba ke ba dako secondary yanzu kika kammala. Amma kike maganar koyon zaman aure, anyah???" Harararta Asiya tayi " wa yasa dake? " " gaskiya ta gaya miki, muna maganar manya Ku daina sa mana baki." Ummu sulaim ta fada " kefa surukata ce be kamata kina min haka ba. Kamata yayi ki roki antinmu ta bani hints na yadda zan sace zuciyar !! Eh !!!! Kin gane ba sai na fada ba" Dariya ummu sulaim tayi tana nuna Asiya da yatsa " ina warning Dinki bakyaji, I don't want u to get hot at end" Bata rai Asiya tayi cikin tura baki " just pray for me " Asima ta tabe baki cike da jin haushin kanwar tata " ki kyaleta Wanda yayi nisa baya jin kira, jiki magayi ai, in ji masu iya magana " Hubby dake zaune tana jinsu. Aisha ta kalli Asiya " rabu dasu sister, ba dai kina son shi ba? I will teach u, how to woo him, he felt for u, like crazy." Dariya ummu sulaim tayi har da rike ciki. Da ido suka bita, sai da tayi mai isarta sannan. " lafiyarki kuwa? Mu gudu ko mu tsaya ?"  Hubby ta ce yana tsareta da ido. Don sun San muddin kaga ummu sulaim tana irin wannan dariyar to ko dai ta mugunta ce, ko kuma ta gama raina maka hankali. " waannan har yau baku gama sanin waye haidar ba!!! Ya wuce da sanin da kikai masa can baya. Ina gudun miki wulakancinsa, in kinga yadda yake gara yaran jamaa a IUC zakisha mamaki. Bashi da mutunci ko kadan. Kin San Afrin ai? Yarinyar uncle Harris. Kwanciyarta a hospital 2, akan haydar dan banzan daga karshe dukan kawo wuka ya mata, wai ta addabi rayuwarsa. Dole uncle Harris ya dauketa ya mai da family house a Oregon, Saboda abun yaki ci yaki cinyewa. Kadan ke nan wasu ma ban iya fada, shiyasa na baki shawara matsayina na yayarki, but tunda kinji kin gani, shi kenan. Allah ya baku saa keda teacher din taki" " zai aika abin da yafi haka ma, in dai wannan mai idon a tsaitsaye ne " hubby ta fada Jikin Asiya yayi sanyi, don tasan afrin farin Sani, duk wani Abu da take takama dashi, bata kama kafarta ba. Don uncle Harris babban mai kudine da duniya gaba daya an San da zamansa. Yana cikin top 20. Haka ta fannin kyau, da wayewa. Mamakin haydar ya cika zuciyarta lallai halinsa sai shi, yanzu haka a gidan uncle Harris din suke zaune, shida yayanta Hafiz omer da friends dinsu. Amma ya iya karfin halin dukan yarinyar da ko kaffara baza ta yiba in ta ce baa taba dukanta ba, tunda tazo duniya. Don yar gata ce ta bugawa a jarida, ya daya mace tilo a wurin iyayenta. Amma ina so ya gama rufe mata ido. Take wata zuciya ta fara ayyana mata ita zata iya samun matsayin da sauran suka kasa samu. Don abun daga jini ne. Mu samman in tayi laakari da yadda suke shiri dashi. " Wanda yai nisa baijin kira." Asima ta fada in I don't care tone Ummul khair ta ce " Ku kyaleta ta gwada saarta. I'm so happy in har hakan ta kasance. Nasan kanina is in good hand. Dama ni bana wani son afrin din nan. Jin kanta yayi yawa, ga izgilabci. Gara ma daya mata haka, ko tayi hankali." " me kika kawo mana gift ne,?" Aisha ta tambaya tana kokarin janyo kwalayen da driver ya shigo dashi. Murmushi hubby tayi. " open it and see!" Wanda sunan ummu sulaim ke jiki, ta mikawa Asiya " mika mata nata"  ta fara kokarin bude nata kwalin don ganin abinda ke ciki. Su Ummul khair suka matso su tayata ganin abin da ke kunshe a kwalin da yasha rapping sheet mai kyau da daukar ido.....   [01/03, 10:41] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 8       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... " wowwoo!!!!" Suka fada a tare, Ummul khair ce ta zaro hadaddun gowns guda biyu. Red, Navy blue and black. Masu masifaffen kyau. Kowacce da takalminta da jaka to mach, Sai congratulation cards. Gaba daya saboda farin ciki Aisha daskarewa tayi a wurin. Don kayan kyansu da darajarsu sannan her favorite color yasata kasa ko da kwakkwaran motsi, sai bin kayan take da kallo duk wanda ya daga. Rungume hubby tayi cike da matukar farin ciki. " thank u very much, besty. Your the best " Dariya hubby tayi ganin yadda ta makalkaleta. " is Notting kunfi haka a wurina, I hope shi zaku sa a party?" "Sure"  Ummu sulaim ta fada lokacin da ta iso. Itama rungume hubby tayi tana mata godiya. Every thing the same, except color. Na ummu sulaim purple, blue and pusher pink. Suma da takalmi da jaka kowanne. Nan suka kwasa zuwa nunawa iyayensu. Cike da farin ciki.                   **************                         CYPRUS " dud, abinda kake baka kyautawa, tun dazu muka shirya muna faman jiranka, don iskanci, Ashe kai ko shiryawa ma bakayi ba" Tsaki yayi still idonsa na kan system din gabansa. Wata hadaddiyar murya naji, mai matukar dadi, da kwantar da hankalin mai saurare, " sorry dud, ina tunanin Ku tafi kawai, ina kokarin solving issue din kayan nan ne, bana son su wuce gobe. So I need more time. " " u can do it letter, " " no dud, kai kanka kasan in kayan nan basu isa cikin satin nan ba zaa samu matsala. It won't be good for us" Janye system din da akayi ne yasa shi dago idonsa. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Masha Allah. Na fada ganin kyan fuskar wannan saurayi, da kwarjini. Farine tas, hotonsa na yarinta na hango tabbas ba kowa bane a gabana sai Aliyu haydar zubair Yusuf Oregon. Tabbas yaci agric chicken din da hubby ke kiransa ganin girman da yayi, dogone, mai murjajjen jiki,. Kyan sufa, da kyan siga baa magana, kamar shi yayi kansa. Daga shi sai singlet da shot nicca.  HAYDER Wanda ya janye system din nabi da kallo, tabbas da gani ba tambaya don suna yanayi kadan da hayder, sai dai hayder ya fishi kyau da tsayi. Hafiz omer kenan. Sai wanda ya fara shigowa, da sai lokacin nakai idona Kansa. Da gani ba tambaya junaid, kyakyawan saurayi wankan tarwada, tsayinsu zai zo daya da haydar, sai dai hayder ya fishi sufar karfafa. Shi din siriri ne. Masha Allah gaskiya Guy's din nan sun hadu. " mayen kudi, kai kam ban San in da zaka da jarabar neman kudi ba. Duk tsiyarka ka hakura muje mu dawo. Don zumunci ya wuce wasa. " Hafiz omer ya fada yana ajiye system din kan wani kyakyakyawan center table. Harararsa hayder yayi. " alhamdulillah I'm looking for my halal my own sweating. " " please tashi ka shirya muje, auren mutuniyarka fa ne, mu nan duk yan rakiya ne, amma don wulakanci mune masu zaman jiranka, abin da ya dace ace ka riga kowa shiryawa." " bazaka gane bane, new customer ne uncle ya hadamu dashi, this is the first time, kaga bai kamata a samu matsala tun daga farawa ba. That why."  Ya fada yana mikewa daga tsaye. " duk da haka, muje u can finish it after we're back, Anty bata can canci haka daga gareka ba. " " I known, just 10min" ya fada yana shigewa wata Kofa dake daya side din. " don Allah banda irin wankan kan nan na 2 hours. " junaid ya fada yana zama a 3sittr din dake falon. " muna waje in kun gama, amma please ka azalzala masa don ya shirya da wuri u known him" Murmushi kawai junaid yayi ya kunna TV yana kallon kwallo cikin kwanciyar hankali. Don ya San haydar bai dade ba yayi 1 hour.                ***************** Hayder da junaid sun gama degree dinsu, one year back. Suna courses ne a kan software development.  Sai Hafiz da alim su kuma suna rubuta final exams don shekarun course din su daban, su 4 years ne, su kuma su hayder 3years. Sai Hafiz omer da Ashir Jamil. Already suna horsemanship, but suma watanni ya rage musu su kammala. Business sosai hayder da friends dinsa suke yi. Tun first year dinsu a school. Amir ne ya fara kawo shawarar,. Lokacin da suka aika masa da wasu belts. Daya ke shi ABU Zaria ya tafi. Ganin kyan belts din da abokan karatunsa da suke ta yaba belts din yasa ya ce musu mai zai hana su siyo su turo masa ya siyar musu, don shi iyayensa basu kai karfin nasu hayder ba. Kamar wasa ya matsa musu. Kudinsu da aka basu suka har hada suka sayi 10 dozens suka tura masa. Cikin yardar Allah wata na karewa sai ga alert a wayar hayder na kudinsu, da riba, ta kusan Rabin kudin. Nan da nan suka kira amir, anan yake shaida musu still ana neman belts din. Shima ya gaya musu abinda ya samu daga ribar da a kaci. Don dama sun ce mishi ya dauki 20% . Kusan 1 year suna tura masa belts, lokacin sun tara riba mai yawa, sai hayder ya bada shawarar su hada da takalma, don ya lura suna da takalma masu kyau da in ganci. Suma sun samu karbuwa sosai. Don tun amir yana siyarwa cikin school har ya zama yan wajen school ma suna oder ta anfani da whasapp, Facebook, Instagram da sauran su. Har ya kasance yan kasuwa kanana na Sara a wurinsa. A cikin 3 years da sukayi yanzu suna wannan business din. Ba abunda basa sayarwa daya dan ganci bukatar gayu. Har da su perfumes. Ta ko ina customers suke samu, jarinsu yayi karfi sosai. Yanzu haka amir dake kula da komai a nan gida Nigeria ya mallaki muhallin kansa, ga motar hawa,. Duk abinan da sukeyi ba wanda ya sani, sai daga baya. Hakan ya matukar burge uncle omer. Don haka ya kara musu jari, sannan ya hadasu da kampanonin da zasu dinga sarar kaya a wurinsu, ko su sasu suyi musu irin wanda suke so. Daga kasashe daban daban. a farashi mai sauki. Sannan ya hadasu da costumes da zasu dinga sarar kayan da xarar sunyi ready. To wannan shine first customer daya fara yin ordering kaya a wurilimited iyasa hayder rashin sukuni, na ganin basuyi dis appointing din saba. Every month suke lissafin ribar da a kaci, su ware wanda zaa kara a kan jari, su raba a junansu sauran. 7frinds for ever company limited shine sunan company din nasu. Yara da kudi, abokan tafiyarmanya. Duka dukan su basu wuce 20years ba, don harder da junaid are 19years old. Amma sun San zafin neman na Kansu. Above of that. Hayder and junaid a software developers, duk da basu gama course din ba, amma har sun fara cin moriyar abun ta hanyar creating din applications, kamar su games, learning applications da sauran su. Wanda kullun kwanan duniya alart ne ke shigowa ta account dinsu. 1 hour ke nan suna faman jira, banda tsaki ba abinda Hafiz omer ke yi. Su Hafiz kam kowa ya kama loja a Sit din katuwar jeep kirar Mitsubishi,  din da zasu tafi da ita. Sun sake music. Ashir da amir suna gefe suna dan hirarsu. A cikin takunsa na kasaita mai cike da natsuwa ya fito da ga main door din. Sanye da back trouser sai White and red shart da jacket dinta black and red, black facing cap, white canvas. Ya yi kyau matuka. Harararsa Hafiz yayi. Murmushi ya sakar masa tare da daga masa gira daya. Key din motar ya jefa masa, ya cafe su ko tsaf duk da Nisan tazarar dake tsakaninsu. " this is you're punishment, for letting us waiting " Wurga key din yayi sama ya cafe, driver sit ya bude ya shiga. Bai yi wata wata ba ya bata wuta suka hau main hanya. Wani hadadden hotel suka nufa, Khuzaifa sultan motel. Naga an rubuta da manyan baki. A daya side din hotel din ne naga an kawata wutin sosai, ga sweemig pool a tsakiya. Haka sukayi ta gaisawa da friends dinsu, har suka isa wurin Amarya da angonta, wanda sun sha kyau. Da faraarta suka fara gaisawa idonta na kan harder dake Sosa sajensa da key din hannunsa, alamar rashin gaskiya. Ganin kallon da take masa yasa yayi murmushi tare da rike kunnensa, "im very sorry uhteee" kada kai tayi tana murmushi " na Sani ai, tun da naga 5 ya wuce, ban ganku ba nasan Kaine.na rasa lokacin da zaka dinga daukar Abu so serious ". Hafiz ne ya amshe " kamar kin san tin 3 o'clock muka shirya" " I known " ta fada tana Harararsa. Sai lokacin ya samu gaisawa da angon nata. Ta hanyar rungume juna, sannan ya sumbaci hannunsa, yana masa congratulation tare da bashi hakurin zuwansu late. Wata kyakykyawar budurwa ce ta karaso in da suke. " yau wa khairat, kai su wan can table din" tana nuna mata table din dake kusa dasu. Wanda aka tanada mu samman saboda special quest. Kallon hayder tayi " kai kuma zamu hadu an jima." Murmushi yayi, yabi bayan su ammar da already sun ma isa wurun table din. Da kallo yake bin wurin, duk ya wanci yan school dinsu ne. Kowa ka kalla ya kure adaka. Cikin farin ciki. Uhtee kamar yadda ya kira amaryar. Ai nihin sunanta Sadiya Shehu sambawa. Haifaffiyar garin Kaduna. Mahaifinta Shehu sambawa, shine. Mataimakin Governor of Kaduna state. Karatu ya kawota Cyprus. Same school dasu haider. Jininta ya hadu da haydar duk da ba department dinsu daya ba. Sun hadu a restaurant din cikin school. Sadiya zata ba hayder good 2 years. Zakayi mamakin yadda hayder ke girmamata. Don Sadiya akwai kamun kai, bata da rawar kai irin na yaran masu kudi. She is simple person. Da farko su junaid sun dauka soyayya suke, don abune da basu taba ganin hayder na hira da Mace ba, har kaga 32 teeth dinshi. sai akan Sadiya. Sai daga baya suka fahimci kawai shakuwace da haduwar jini. A nan Cyprus Sadiya ta samu miji, maaikacin costume, Osama bin hashim. A Nigeria aka sha biki, bayan ta kammala course dinta. So yanzu sun shirya yar kwarya kwaryar liyafa ne, saboda friends dinsu da basu samu damar zuwa Nigeria ba, Irin su hayder. Ashir ne yama hazif signal. A tare suka mike " one min" Hafiz ya fada yana Jan hannun ashir. murmushin gefen baki hayder yayi. " Allahu yaha dikum." Dariya sauran sukayi baki daya. A hankali take takowa, kamar tana tausayawa interlocking din dake shimfide a gasan. Sanye take cikin ashobin yan matan Amarya. Grown marron da black, kanta daure da wani net mai adon flowers multicolor, kafarta yasha high hill black. Kallo daya zaka mata kasan ta hadu ta ko ina. Gaba daya hankalin da yawan mazan wurin yana kanta. Nasrin ke nan, balarabiya haifaffiyar Egypt, karatu ya kawota Cyprus. Shekara biyu da ta wuce. Kyakykyawace ta bigawa a jarida yar kimanin shekara 17 to 18, tun da Allah yasa ta daura idonta a kan haider taji duk duniya ba wanda take so da kauna sama dashi. Sai dai babbar matsalar duk yadda taso ta fahimtar dashi irin dunbin kaunar da take masa, bata samu wannan damar ba. Don tun da ya lura da take takenta, ya sanya duk wata Katanga da zata zama sha maki tsakaninsu. Yau kam taci alwashin Isar da manufarta gareshi. Zuwanshi wurin babban dama ce a gareta. Daga nesa junaid ya hangota. Kallon hayder yayi yana murmushin mugunta. " gafa mutuniyarka nan tafe"  haider da idonsa ke kan wayarsa yana sipping coke a hankali, ya dago yana kallon junaid, kafin ya mai da kallon sa in da suke kallo. Tsaki yayi ya ci Gaba da abinda yake yi. " masha Allah, gaskiya yarinyar nan ta hadu karshe, " Hafiz omer ya fada yana kare mata kallo, kamar ranar ya fara ganinta. Alim da shima baa barsa a baya ba ya shafa sajensa, " gaskiya kam ta wanku" Sallamarta ne ya sa su dan risinawa daga kallon kurillan da suka kafeta dashi. Lumshe ido Hafiz omer yayi, jin zazzakar muryarta. Alim da junaid ne suka samu damar amsa mata salkamar, tare da fara gaishe gaishe. Gogan ko ko daga kansa bai yiba balle ya samu damar amsa gaisuwar da tayi. Junaid ta kalla, cikin fuskar ban tausayi. " ina son ganin abokinku minti biyu don Allah " Murmushi junaid yayi, tare da kallon haydar dake faman danne danne a waya. Cikin harshen Hausa ya ce " don Allah hayder ka saurari yarinyar nan kaji abinda zata ce, " kallon kasan ido yabi junaid dashi, ganin haka ya sa junaid kara marai rai cewa " please mana, tun da kaga ta tako har nan kai ma kasan maganar mai muhimmanci ce " Kallon sa yakai kanta, ido hudu sukayi, ta sake masa wani kayataccen murmushi. Kansa ya kawar gefe, tare da furzar da wata iska mai dumi daga bakinsa. A hankali ya mike, ya nufi can gefe dake da karancin jamaa. Nasrin  ta take mai baya. Akwai irin dogayen kujerun nan a wurin, don haka yana isa yayima kansa mazauni, wurin tamkar lambu haka yake, sai kamshi, saboda flawers kala kala dake shuke a wurin. Same kujerar ta zauna, sai dai dan nesa kadan dashi. Sun kai 5 min ba wanda ya cewa dan uwansa komai, kallonsa kawai take, tana faman sauke ajiyar zuciya jefi jefi, tana tunanin ta inda zata fara. Don gaskiya yana mata matukar kwarjini, balle yanzu da take gabansa. Shi kuwa zaman ne ya fara isarsa, ga haushinta da ya cika zuciyarsa. Ya ci a ce ta gane baya muradinta tun ba yauba. Amma ta kasa ganewa, shi ya rasa me yasa wasu matan basu da tunani, ya kamata in mutun ya nuna baya muradinki ki hakura, amma wasu a lokacin ne suke kara zage damtse, sun manta baa soyyaya dole, kamar yadda baawa zuciya dole. Tunawa yayi da karon battarsu da naufal, tsaki yaja a hankali. "Sorry na San na takura maka da yawa, amma kasan ba laifina bane, laifin zuciyata ce, data kasa amincewa da rashinka a kusa da ita. Na dade ina neman irin wannan damar da zan bayyana maka sirrin xuciyata, ban samu ba, ko kuma ince baka bani dama ba. Ko ban fito na fada da baki ba, nasan ka dade da fahimtar dunbin soyayyata a gareka. Don idanuwana da gabbaina sun dade da nuna hakan. Ba zan boye maka ba, gaskiya zuciyata ta kamu da matsananciyar soyayyarka, wanda har nake jin bazan iya rayuwa ba, matukar babu kai a cikinta." Shiru tayi tana son ganin reaction dinsa. Amma ko kadan bata iya gane komai ba. Sun dau some minutes ganin bashi da alamar tanka mata, ta kuma kasa karantar yanayinsa. Yasa ta marai rai ce fuska " please hayder don say u not love me, Allah zuciyata bugawa zatayi" kyawawan idonsa ya zuba mata wanda ya sata dan rawar jiki, da nemo Karin natsuwa ta sawa kanta. " wane irin soyayya ne kike magana? A iya sanina soyayyar da zaa yi for some time ayi aure, right? " kai ta daga don muryar ma ta kasa fitowa, saboda tsoron amsar da zai fito daga bakinsa. Kai ya kada tare da gyara zamansa " look at me " ya fada yana tsareta da ido. Kasa kallon kwayar idonsa tayi, ta sunkuyar da kai, tana wasa da phone dinta. " I'm just 19 years all. At lest nan gaba ina bukatar 5 to 7 years kafin in yi settling in fara maganar aure. Ta Yaya kike son in fara soyayya dake bayan nasan bani da feature dake? Nan da 2 to 3 years nasan ko baki fitar da miji ba iyayenki zasu fito miki dashi, su aurad dake. So ta Yaya kike son mu yaudari kanmu? Bayan kin Sani na sani  wannan is not a good idea, and it's not work." Shiru sukayi, kowa na nazari . cikin miryarta mai zaki " I'm wait for u, ni dai fatana ka soni ko da rabin son da nake maka ne, nasan iyayena baza su takura min ba, musamman in sun tabbatar da kayi alkawarin aurena in har lokacin yayi. Ni kadai iyayena suka Haifa, suna son duk abinda na keso, already sun dade da jin labarinka, ganinka ido da idone kawai basu yi ba." Kallon ta yake, tabbas iya gaskiyarta take fada. " I need some time, to think about it" ya fada yana mikewa. Jiki a sanyaye ta mika masa wayarta " you're number please " wayar ya juya yana kallon yadda aka kawatata da flawers sai katon heart a bayan wayar dake daukar ido MY HEART BELONGS TO YOU A.  Da manyan baki cikin harshen larabci. Tabe baki yayi, ya typing number ya mika mata wayar. "Thanks" A hankali suka tako zuwa table din su hayder, Tun da suka doso idonsu junaid na Kansu. Ganin kallon yayi yawa yasa haider aika musu da harara. Sallama ta musu ta nufi wirin zamanta. Ko yanzu ta samu peace of mind duk da tana taraddadin amsar da zata fito daga gareshi. " kai dud, amma fa kun balain matching,. Gashi kuma da alama wannan ta samu babban matsayi tunda har aka saurareta, har da jerowa tare.'"  Alim ya fada cike da murmushi a fuskarsa. Harara haider ya aika masa, tare da Jan kujera ya zauna. Plate ya jawo ya fara serving kansa, da abubuwan cin, da sha, da aka cika table din dasu. Yana jinsu suna ta masa tsiya yaki kulasu, don yasan so suke suji kanun labari, shi kuma bai shirya ma topic din ba. Sai lokacin su Hafiz suka dawo, daga shan shisha, da aka ware guri duda ga masu bukata. " Allah ya shiryeku kullun mutun yayi ta durama cikinsa hayaki, kamar wani gafiya, Ku ko Dan tsoron cututtukan nan bakwayi? Please anaiwa kai fada mana?" Dariya su ashir sukayi " lallai kam, ba gara mu ba da muka tsaya a hayakin! Kai har kanada bakin yiwa wani fada, ka fara da kanka tukunna" Hafiz ya kara da " namu ai mai sauki Ne, baifi ace your die Young ba, kaifa hatsarin dake cikin naka yafi namu sau dubu" Hafiz omer yayi dariya " shi ke nan ai, tunda bakwa son gaskiya. U will die young " " better to die young than to die in shame"  ashir ya fada yana Jan plate. Junaid dake faman musu dariya ya kalli ashir " surukin naka kake gayawa haka? " Baki ashir ya rufe yana kallon Hafiz omer dake faman aika masa da harara. Kunnensa ya rike da duk kan hannayensa " I'm very sorry dud, subutar baki Ne." Duk Kansu sai da sukayi dariya yadda ashir din yayi da fuska yana bada hakuri. " kaga ai ni ban ce wani Abu mai zafi ba, duk wannan dan iskan ne, yake son hadamu" ya kaiwa Hafiz duka. " daga yau ko kallon in da ake shan shisha ban sake yi, balle in sha, sai in tsautsayi Wanda baya wuce ranarsa. Kamar yadda kai ma tsautsayi ke giftawa tsakaninka dasu Linda. " Murmushi Hafiz omer yayi, tare da kauda kansa gefe. Har ga Allah yaji wani iri a ransa. Ya zai yi he can control his desires, shi yasa yana komawa gida aurensa zaiyi, don baya son irin wannan rayuwar ta zamo masa jiki. Don ko yanzuma sai abun yafi karfinsa yake Dan ganawa da Linda. " yayi kyau ka gama gyara fadarka, zamu hadu ne" Hafiz ya fada yana murmushi Haka sukai ta hirarsu da raha, ga kayan ciye ciye. Har to 11, sukayi sallama da Amarya tare da bata gift din da suka kawo mata suka tafi. Hafiz ne ke Jan motar wannan karon Duk Kansu San darewa sukayi a tsaye, ganin wadda ke tsaye a bakin kofar da zata sadasu da apartment din su, jin gine jikin kofar ta rungume hannayenta. Gaba daya idonta na Kansu............... Wani wawan kallo harder ya yiwa Hafiz omer. Murmushi yayi tare da tabe baki, yana daga kafada alamar he has no idea. Da sauri ta matsa a jikin kofar ganin yadda ya taho cikin fushi, ga uwar harara da yake narka mata. Hatta hantar cikinta rawa take, don tana matukar tsoron haider, bata manta warning dinta da yayi. Tsaki yaja ya wuce ciki. Da sauri Hafiz omer ya ja hannunta sukayi gefe. " what bring u here?  After all the warning? Na gaya miki koma menene mu hadu a inda muka saba haduwa, ban son na kara ganin kafarki a nan." Marairace fuska tayi, tare da shigewa jinsa. " I'm very sorry, na nemi wayarka na kasa samu, kuma I need some money" Tsaki yaja " what is your problem? Nafa fara gajiya da yawan tambaye tambayenki. Ke kullun baki da aiki, sai a baki, a baki. Banki ne ni aka gaya miki, ko bishiyar kosai ne, kika shuka?" Kirjinshi ta fara shafawa da hannunta da yasha adon fake nails. " haba nawan! in ban tambayeka ba wa zan tambaya? Kasan kai kadai nake kulawa,. So u have to take care of my needs. In kuma kaga ka gaji shi kenan their so many ways to the market " cikin fushi ya dago fuskarta yana faman aika mata da kallo mai kama da harara " me kike nufi?" Murmushi tayi tare da zuba masa kananan idonta masu kama da na Chinese " na San ka fahimci abun da nake nufi." Furzar da iskar bakinsa yayi, tare da lashe lips dinsa. " I don't have money, so it's good idea to go our separate ways. I had enough of u." Da ido waje cike da mamakin kalamansa take kallonsa, don bata taba zaton zai ce su rabu ba. Ko da ta ce masa zata bi wasu, ta dai fada ne kawai. Ita da take fatan ta zamo matarsa ta ina zata yadda ta rabu dashi? Duk wani Abu da take bukata ga namiji ya na dasu, to ita kuwa ina zata nema, bayan gashi a gabanta." I'm very sorry, karka sa zuciyata ta buga, u know how much I love u? Ya zan iya rayiwa ba tare da kai ba? You're my everything. In na bata maka rai kayi hakuri. Dama foodstp dina ne suka kare, shi yasa kaga na biyoka nan." Kallonta ya keyi cike da tausayawa. Linda Matthew haifaffiyar kasar Ghana ce, karatu ya kawota Cyprus. Yawancin responsibility din karatunta ita take fafutuka ma kanta, don iyayenta basu da karfi. Ko da tazo Cyprus aiki ta fara a wani restaurant, ta nayi a lokutan da ba a karatu, da kudin take tallafawa kanta. Haduwarta da Hafiz omer yasa ta samu sauki sosai ta fannin bukatunta. Hatta da aikin restaurant din ta ajiyeshi a gefe.  Kallonta ya keyi cike da karantar yanayinta. Tabe baki yayi " ki je zan tura miki ta account, but ya kamata ki San yadda zaki dinga managing abubuwa, don na kula yanzu abin naki ya fara wuce tunanina." Rungumeshi tayi, tare da kai bakinta kan nashi,  ta fara kissing dinshi, da kyar ya banbareta daga jikinsa, don shima ta fara sashi a wani yanayi. Da sauri ya shige ciki yana jaddada mata zai tura mata. Da kallo ta bishi tana murmushi. " I love u so much " ta fada a hankali kafin ta juya ta nufi super market don tasan tunda yace zai tura mata, zai tura within no time kuwa. Zaune yake gaban sa computer yana faman danne danne. Gefe daya cup din black tea ne ya na sipping a hankali, sai su junaid dake faman kallon boll a katon TV dake manne a falon. Da alama dawowarsu har sunyi wanka. Don dukkansu sanye Duke da kayan bacci. 11:23 dai dai Hafiz omer ya fito, shima sanye da kayan bacci a jikinsa. " kaga angon Linda " ashir ya fada yana murmushi. Harararsa Hafiz omer yayi. Sai da ya hada tea mai kauri ya koma kusa da junaid ya zauna. Hayder ne ya dago yana kallonsa, with seriousness ya ce " mai zai hana in son yarinyar nan kake ka aureta kawai a huta, amma gaskiya bana jin dadin abunda kuke yi." Sai daya kurbi shayin tukunna cikin dariya " baka da hankali, in rasa wadda zan aura sai wannan? In mafarki kake ka farka, kai yanzu in nace zan aureta sai ka yadda!?" " mai zai hana, da zaman haramci ai gara halalin. Meye marabarta da Matar taka a yanzu? Hidimar da kake yi mata ai tafi ta wani mai iyalin. Please stop all this, in aure kake so just married her" Kallon hayder yake yi cike da mamakinsa, sauran kam sai dariya suke musu kasa kasa. " in mafarki kake ka farka. Haduwar bariki, rabuwar bariki, me zanci kuma da ita? In aureta in ce na auri wa? Ko ka manta fadar manzo S.A.W da ya ce Ku zabawa yayanku uwa ta gari? Wace irin tarbiyya ka keson yayana su taso dashi? Salihatun, mu'uminatin, kanitatun, sa'i'hatun, wa' ab' khara. Ita zan nemo ba wannan da ta gama ganyali a titi ba" Gaba dayansu dariya suka fashe dashi, su Hafiz har da rike ciki. " amma guy din nan Dan rainin hankali ne. Ta yaya zaka ce bazaka iya aurenta ba? Bayan duk kan alamu sun nuna da kai kadai take yarayya. Ai kawai ka aureta musha biki kaji." Alim ya fada still yana kwasar dariya. Junaid ya ce " kai kafi dacewa ka aureta" " inah!!!! Sabuwa dal zan baro, ba second hand ba. Don haka wallahi ya isheku haka. In kuma da mai so to bisimilllah. " Allah ya kiyaye" kusan a tare alim da ashir suka fada. " kai ma da ka mori gangan mai yasa baka killace ta ba, sai mu da ko kamshinta da amonta bamujiba." " Allah ya shiryi yan matan da suke sakema yan iska irinku jiki, Wanda da zaran kun gama morar ganga sai Ku yada korenta. Don duk Dan iska in ya tashi aure baya neman yar iska yar iwarsa, neman salaha yake ya aura. Ita kuma an mai data taxi no gari, daga wannan ya Mora yayi dumping sai wannan ya amsa, a haka rayuwar zata kare ba albarka." Hararar junaid Hafiz omer yayi. " ni nema dan iskan ke nan?" Baki junaid ya rike yana murmushi " ni na isa, in ce maka dan iska. Musali kawai na kawo." Kada kai Hafiz omer yayi, ya ci gaba da shan tea dinsa. " ka gaya mata kar na sake ganin kafafuwanta anan, in ba haka ba daga kai har Ita Will pay the price " Kallon hayder yayi cike da jin haushin maganarsa. " bazan fadan ba, naga kai ma kana da baki, me yasa da ka ganta baka gaya mata da bakinka ba." Murmushin gefen baki hayder yayi " ok, in sake ganinta kaga" Tsaki Hafiz omer yayi " kar ka manta I'm older than u, so respect me for that " Kada kai hayder yayi, ya ci gaba da aikinsa. Hafiz omer ya taso ya dawo kusa dashi ya zauna. " I'm sorry, na tabbata bazata kara zuwaba, already na mata warning" Gaba daya dariya suka sama Hafiz omer. Harararsu yayi. " better for u, dan wallahi muddin ta kara takowa nan, ka tabbata ka aureta ka gama. I have a lot of probe da zanyi sending yanzunnan kaga aiki da cikawa." Marai rai cewa yayi "i say sorry mana"  don yasan halin kayansa tsaf zai aikata abunda yafi haka ma in dai hayder ne. " it's OK" " ammafa gaskiya kasan ka takura mana ko? Kamar ba matasa ba, ka mai damu ustazan karfi da yaji!! Dan club din nan bada mu ba, dan night party din nan shima. Nayi regrating biyoku Cyprus, da yanzu ina England ina shanawa abuna." Da kallo suka bi Hafiz omer ganin yanda ya haki kance, alamar anfa takura masa. Ashir ne ya bude baki zaiyi magana hazif omer ya daka masa harara, ya na zaro ido. Murmushi Ashir yayi " mai da wukar, bani na kar zomon ba. Sai dai ina laifin wanda ya ce ka gyara kayanka? Te makonmu yayi, aboki na gari shine Wanda zai ga kana ba dai dai ba ya nuna maka kurenka, ya kuma nuna maka hanya mai kyau, wanda zaku tsira duniya da lahira. Ina amfanin kuruciyar da mutun zai yita cikin sabon Allah? Kyakykyawar kiruciya Ita ce wadda zaa yita cikin tsoron Allah, biyayya gareshi da kiyaye dokokinsa. Sai mutun yaci ribar kuruciya, yaci ta tsufa, San nan ya samu kyakykyawan karshe. Don haka ka dai na ganin hakan a matsayin takurawa, nasan wataran zakayi alfahari da hakan." " I know, but kasan zuciya, na son walwala, komai kan kantarsa." " baka yadda da maganar ashir ba kenan? Naga duk da sa idon nasa, still a hakan bai hanaka  shanawa ba? Junaid ya fada yana murmushi " kai ma ai danuwan dayan ne, na rasa daga kauyen da kuka fito?" Yayi tsaki " Lego's boy " suka fada a tare suna dariya, don dama in ya kwafso musu wani abun haka suke masa kirari. Don so da yawa yakan ce musu yan kauye, su basu waye ba, balle Susan takan rayuwa. Banda Haider dake kan system dinsa, ko dago kai bai yi ba balle suyi tunanin zai amsawa Hafiz omer maganarsa. Daga karshe ma daukan computer dinsa yayi, ya musu "good night" ya shige warsa. Haka suka ci gaba da hira suna kallon boll har to 1am kafin kowa yayi makwancinsa.                  ****************** " princess " cike da mamaki ta juyo. Gani tayi ya bude kofar ya fito. Rungumeta yayi, ba tare da ya damu da salis abokinsa dake drive sit yana kallonsu. Ajiyar zuciya suka dinga saukewa a tare, ya dauki lokaci yana rungume da Ita, kafin ya lalibi lips dinta ya fara aika mata da hot kisses. " I'm going to Miss u, ji nake kamar in fasa tafiyar nan" ya fada yana maida numfashi. Murmushi tayi tare da rike hannayensa duka biyu. " Allah ya dawo min da kai lafiya, ni kai na ba na son tafiyar nan, tun da kake tafiyar ban taba jin haka ba." Murmushi yayi " ko dai, ko dai " Dariya tayi ganin yadda yake mata da ido. " yes!! I'm jealous, ko laifine in yi kishin mijina?" Ta fada tana masa fari da idanunta masu matukar burgeshi. Murmushi yayi yana dage mata gira daya " I'm only yours, daga ke ba kari, sai hurul "ain in munje can, In sha Allah. Can kuma kinga baa kishi. So sa ranki a inuwa." Rungumeshi tayi, sannan ta sumbaceshi a chick " I love u so much my king " " love u too princess " Hon salis ya fara sake masa, kiss ya mata ya juya da sauri, yana dannawa salis harara. Murmushi salis yayi yana shafa kai. " yanzu don kuturun wulakanci ka shanyani anan kaje kana kwasar love!!! Time yana ta tafiya" Kwantar da kansa yayi jikin kujerar motar idonsa a rufe, sai murmushi yake sake wa. " u won't understand " ya fada a hankali ba tare daya kalli salis din ba. Tsaki salis yayi " Allah ya bamu ikon shigowa daga ciki, ko ma huta ganin wulakanci. A yi ta daga ma mutun hankali a banza." Dariya Yusuf yayi " da dai yafi, sa ido sana' ar banza, ni ban San abinda yakai idonka, in da baa so ya kai ba." " Abu a gabana!! Sai a hanani bama idona abinci, ai da baa so na gani, da an shiga ciki. Ammafa gaskiya mutumin you're very lucky. Allah ya samu a danshinka." Murmushi Yusuf yayi " mu fara zuwa main house." Agogo salis ya kalla " amma kasan time ya tafi ko?" Kamar bazai bashi amsa ba. " please muje I need to see my parent before I go." " why not in mun dawo mu biya? Kasan  su auwal ba hakurine dasu ba, dama tun dazu suka isheni da waya." " don't mine them, just 10min." Badon salis yaso ba, ya nufi main house. Don sun so shiga garin abuja da wuri, kafin lokacin daurin auren. Yusuf maitama yelwa, shine sunan abokinsu da zaiyi aure, a garin abuja yake da zama,. Sun yi karatu tare da su Yusuf. Akwai zumunci sosai tsakaninsu.                     **************** Sai da taga fitar motarsu kafin ta nufi cikin gida. Gaba daya ganin gidan tayi ya mata wani fayau. Zuciyarta ba dadi, ga faduwar gaba da ta addabi rayuwarta, tsawon sati kenan in har bata manta ba, gaba daya satin bata da wani kuzari, jinta take tamkar wadda ta tashi daga cuta. Ga yawan faduwar gaba. Shi kansa mai gidan nata ta lura ya rage walwala, ga yawan tunani data lura some time yana yi, ta dauki hakan kan tsananin takura da take ciki na dangin miji. Don ta kai har Hajiyasu Yusuf da takan samu sauki a wirings ta fito kiri kiri ta shaida mata dole Yusuf ya kara aure, don ba yadda zaa yi ta rungumi hannu tana ganin dan da tafi ji dashi duk cikin yayanta, ya kare da juya. So koda taga rashin walwalar mijin nata, sai ta dangana shi da waccan maganar. Daga ita har shi suka maida komai zuwa ga Allah. Don gaba daya a satin mijin nata ya canza, duk da dama mutun ne mai matukar rikon addini, amma abin sai ya nunku a kan da. Ga yawan waazi, mai kama da wasiyya da yake yawan yi mata da zaran sun zauna zaman hira. Don bata manta ranar da take ce masa. " ni kam ban gane maka kwana biyun nan, ka kara zama shiru shiru, ga waazi kamar sabon liman, wani lokaci kalamanka suna ban tsoro, har inji hanjin cikina na kadawa. Please me yake faruwa ne.? Murmushi yayi kanta a kan cinyarsa ya Sumba ceta. " kin San rayuwa bata da tabbas, dole sai anayi ana tuno da gidan gaskiya, wanda a nan duniya dan adam ke tana dawa kansa shi. Fatana mu samu kyakykyawan karshe. Kwanan nan wasu irin mafarkai ke damuna, wanda suke sa in ji imani, da girmama karfin mulkin ubangiji, sun mamaye zuciyata. Jina nake kamar wani bako matafiyi, wanda ke kan hanyarsa ta komawa gida." Kallon sa take cike da tsoron kalaminsa, tana kokarin hasaso inda maganganunsa masu kama da juna suka nufa. Hure mata idon yayi yana murmushi. " don't worry ba mutuwa nake nufi ba, in sha Allah sai naga kwanmu nida ke, naga kuma abin cikin kan." Kwal kwal tayi da ido " in sha Allah my king. please ka daina min irin wannan maganar, hankalina tashi yake." Murmushi yayi yana Kada kai " i'ihim i'himm" Bakinsu ta hada wuri daya, ta fara aika masa da hot kisses. Ganin zaman gidan bazai mata ba, ta kirashi a waya, lokacin sun fita daga garin Kaduna. Kan zata main house, bai hanata ba. So a gurguje ta shirya ta Zari key din motarta tayi waje. 15min ya kaita main house. A harabar gidan ta faka motarta kirar CRV2018 jeep  black. Ahmad ne da Abdul majid kanin Yusuf tsaye jikin daya motar dake kusa da inda hubby tayi parking. Da faraa suka fara gaisheta. Don gaskiya bata da matsala ko kadan dasu suna matukar girma mata. Anty sama Anty kasa. Itama cike da faraa take amsawa tare da yambayar Ahmad munaya, da yara. " kai kam kayi wuyar gani, naga alamar nan gabama sai mun cike form tukun nan zamu samu ganinka" ta fada tana kallon Abdul majid Dariya suka yi gaba daya " sai hakuri Anty kin San yanayin aikin namu, da kyar na samu far mission na one week, dazu nake maganar da mijinki zan zo kwasar gaisuwa sai gaki." Murmushi tayi. Ahmad ya ce " wannan aikin naka kam bai yi ba Sam wallahi, ina tausayin Matar da zata yadda ta aureka, kullun mutun yana cikin teku kamar wani kifi. Baka da lokacin kanka ina ga iyali?" Dariya Abdul majid yayi " kaji brother mai zai hanani samun mata? Haka zatayi hakuri dani, har ta saba." "Lallai kam" Ahmad ya fada. Sallama sukama hubby zasu dan fita, Abdu majid "ya ce bari muje in gaishe da kakus I hope zan sameki?" " a gaishe min da su da kyau, sai yamma zan koma" ta musu sallama ta nufi cikin gidan. Part din Maman Yusuf ta nufa. Don tunda ta auri Yusuf Mmn Yusuf ta sa dokar bata yadda ta fara zuwa ko ina ba, sai ta fara zuwa wurinta tukunna. Duk shakuwarsu da Hajiya yanzu kiri kiri bata isa tayi good 20min a part din Hajiya ba, sai Mmn Yusuf ta hauta da balain wai ta zauna a can suna kulle kullen makircin da suka saba. Ganin hakan yasa dole take kiyayewa don a zauna lafiya, don bata son ya zama duk zuwanta ana samun matsala tsakanin Mmn Yusuf da Hajiyan. Sai dai a waya, zata kira hajiyan su sha hirarsu, tare da bata shawarwari masu nagarta, wanda take ganin fa idarsu da anfaninsu.   [02/03, 12:31] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 9       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau No comment, no vote, no update on time, eheee...    A hankali ta ke bude idonta, da takejin sun mata nauyi, p.o.p, da fankar da ke faman juyawa idonta suka fara sauka a kai, kafin ganinta ya kai kan dogon karfen da ke sagale da ledar karin ruwa. Gefen damanta ta kalla mata ce zaune a kan kujerar roba ta kifa kanta kan gadon da hubby ke kwance,. Dakin tabi da kallon, tabbas a asibiti take. Sai lokacin abubuwan da suka faru suka fara dawo mata tiryan tiryan, kamar ansa majigi. Hawaye suka fara ambaliya, daya hannunta mai lafiyar ta daura a kan kirjinta dake zafi tare da karanto. "INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNI FI MUSIBATI WA AKHLIFNI KHAIRAN MINHA. "Allah ya jiqanka ya mukhtar ya gafarta maka,ya Allah ka tsareshi daga azabar qabari da fitinarsa,ya Allah gashinan yana mai buqatuwa izuwa rahamarka,kai mawadaci ne daga barin azabtar da shi,idan ya kasance mai kyautatawa ya Allah ka qara masa kan kyawawan ayyukansa,idan ya kasance mai sabo ya Allah kayi masa afuwa,ya ubangiji ga mukhtar nan,bawanka ne Allah ka gafarta masa kayi masa rahama,ka yalwata masa makwancinsa,ka wankeshi daga laifuffukansa da ruwa da qanqara kamar yadda ake tsaftace farin tufafi daga dauda,ka sauya masa gida wanda yafi gidansa,da iyali wadanda suka fi nasa,da mata wadda tafi tasa......." Jin muryarta yasa gwaggo dagowa, daga gyangyadin daya tafi da ita. Ganin kukan da hubby keyi, cike da ban tausayi, gwaggo ta rungumota jikinta, tana lallashinta, da kokarin kwantar mata da hankali, tare da nuna mata, yanzu fa Yusuf ba abunda yake bukata daga gareta, sama da adduarta. Haka suka kwana, daga ita har gwaggon ba wanda ya samu damar runtsawa. Cikin kwana daya tal amma ji take duniyar ta mata daurin huhun goro,babu abinda qwaqwalwarta keyi sai bitar rayuwarta da yusuf, idanunta sunqi dakatawa da zubda hawaye dai dai da second d'aya,cikin kwana gudan tal ta rame ta fige ta fita hayyacinta,ba ta cewa uffan sai ido kawai, da yawa yan uwa suka zo dubata a asibitin, amma ko gaisuwa aka yi mata saidai ta amsa da ka,daga jiyan zuwa yau babu abinda ta kai bakinta illa ruwa da  take kurba, shi din ma gwaggo ke matsa mata shansa, sai tea lokaci zuwa lokaci idan an matsa mata,sam abincin bai iya wucewa ta maqogaronta balle ya kai ga uwar hanjinta,a washegarin ranar aka sallamota. Direct part din Mmn Yusuf aka wuce da ita, wanda tun rasuwar basu haduba., don ita tana jin maganar rasuwar ta sume. Baa samu kanta ba, sai dare can. Ita kam bata samu damar ganin gawar dan nata ba. Tana ganin Mmn Yusuf sai sabon kuka ya balle tsakaninsu,ba qaramin tausayawa hubby tayi ba,yarinya qarama amma taga jarabtar rayuwa iri iri,da qyar aka sha kansu. Bayan sallar la'asar tana saman abun sallah tana lazumi cikin dakin  gadon Mmn Yusuf,Aisha, ummu khulsum da ta iso tun daren jiya, ummu ruman, ummu sulai, samira ummul khair, sai kawayenta na family. Kowa ka kalla cike da tashin hankali da damuwa, ga carbi wasu na ja, wasu na karatun Qur'an. Gwaggo ce ta shigo, hannunta dauke da karamin trey. Ummul khair ce ta matsa, don ta samu damar zama kusa da hubby. Cike da tausayawa ta kalli hubby " takwara tashi, ga dan kunu na samo miki ki dan sha ko kyaji karfin jikinki, baya yuwuwa dan adam ya zauna bai ciba, a ce tun jiya banda ruwa ba abin da kika sa a bakinki." Hawayen idonta ta share " banjin yunwa, bakina daci yake, ko ruwanma dakyar yake wucewa."  Ta fada cikin dasashshiyar muryarta. " haka zaki daure ki ci abinci ko mai kan kantarsa, kar wata cuta ta shigeki, kiyi hakuri, ki dau dangana. Wanda ya mutu baya bukatar komai sama da addua, ita kuma adduar sai da natsuwa, wanda bai ciba kuwa ina yaga natsuwa, da karfin jikin da zai samu damar yin adduar? Ki daure takwara kici ko kadan ne." Da kyar suka samu tasha kunu kadan da farfesun kifin. Tasha magungunanta da tunda aka sallamota ko kallonsu batayi ba. Sai da gwaggo ta tabbatar tasha sannan ta fita. Muryar da taji a falo ne ya sata saurin dagowa daga kwancen da take, jikinta na faman rawa, zuciyarta na bugawa. In ba kunnenta da jiya zuwa yau yake yaudararta da kamar jin muryar Yusuf, tabbas ma yanzu kamar muryar tasa taji yana magana da yan falon. Ko kafin takai ga mikewa tsaye da nufin fita falon. Junaid yayi sallama bayan su sulaim sun amsa ya shigo, hayder, na biye dashi a baya. Saboda tsayawar da yayi, yana kara ma yan uwan Mmn Yusuf gaisuwa. A hankali ta gyara zamanta, tana sauke ajiyar zuciya. Hawaye na bin kuncinta. A gabanta junaid ya tsugunna ya kamo hannayenta duka biyu yana kallonta, shima idonsa na zubar hawaye. Yayin da hayder ke gaisawa da yayyennasa, tare da musu gaisuwa. Kallo daya zaka masa kaga tsantsar rama da tashin hankali a tare dashi, idon nan sun Kada jajur, sun kara shigewa ciki. Kamar yadda fuskarsa tayi ja, a lamar kuka. Abinka da farin mutun. Aisha ke tambayarsu saukar yaushe. " 30min ego " cikin murya mai cike da alamar rauni. " Allah ya ji kansa, yasa aljanna ta zama makomarsa, Allah ya bamu hakurin rashinsa. What a great lost Anty!!!" Cikin muryarta da bata fita, saboda dashewar da tayi, ta amsa masa da "amin" tana kallonsa hawaye nabin kuncinta. " take heart Anty,." Ya fada a hankali yana share mata hawayen, wanda shima hawayen ke bin kuncinsa. Kallon yadda hubby ta koma lokaci daya ya karawa karyawa hayder jiki, tausayinta, da tausayin Mmn Yusuf yafi komai daga masa hankali,. Don yasan ba wanda zai kaisu jin mituwar, sai daddy da shi kansa. Bai San lokacin da nashi hawayen da yake kokarin boyewa suka fara saukowa ba. A hankali ya karasa kusa da hubby " ya hakurinmu " a hankali ta dago ta kalleshi " alhamdulillah " lebbanta kawai zaka iya kalla ka gane me take fadi. " Allah yaji kansa, ya gafarta masa." " Amin " Juyawa yayi ya koma wurinsu Ahmad. Junaid ya dade da ita yana kwantar mata da hankali kafin ya bi bayan hayder.               ******************* Haka aka ci gaba da karbar gaisuwa. Jamaa nata tururuwa, ta fannin ko wanne member of there family. Su mommy Hauwa sun so Kwarai hubby ta koma gida, bayan 40days. Amma Alhaji Jamal da Alhaji babba (Yusuf zubair Oregon) suka ki. Part din Hajiya ta koma, inda Hajiyan ke ci gaba da kula da ita. Tunda gwaggo ta koma, after 40 days. Rayuwa tama hubby zafi, a wannan lokacin, gaba daya ta canza kamar ba hubby ba.  Har lokacin kullun dare haka take raba dare da ibada, tana nema ma Yusuf gafara da rahamar Allah. Kuka kam har lokacin a cikinsa take, mu samman in ta kadaita. Takanyi Allah ya isa ga wanda suka zama sanadin rabata da masoyinta. Sanadi Bayan sun kama hanyar abuja, kamar yadda suka fita salis ke driving sai Yusuf a gefensa. Sai motar su Engr Sahabi da Imran da ke gabansu, don sun rigasu yin gaba, saboda Yusuf ya sasu biyawa main house.  Sun kusa isa zuba. Yan fashi ko in ce kidnappers suka tare motar su, da wasu motoci biyu. Gaba daya suka sasu fita daga motocinsu sukayi daji dasu. Basu dade suna tafiya ba Yusuf ya yiwa  salis signal a Lamar su kokarta ko zasu iya escape. Kafar dayan ya tadiyo, ya zube a kasa, wanda ya jawo hankalin sauran. Signal yama salis yana nuna masa na kusa dashi, cike da tsoro shima ya masa kafa, nan fa mutanen suka farga da abin da ke shirin faruwa. Fada ne ya kaure a tsakaninsu duk da hannayensu Yusuf a daure suke bai sa sun kasa kokarin kare Kansu ba.  Suma sauran mazan da aka kamo tare dasu Yusuf basuyi kasa a gwuiwaba. " try as much as u can. Daku mutu a hannun karnuka gara ku mutu kuna masu kokarin kare rayukanku," Yusuf ne ya fada masu salis da karfi don ya kara musu karfin gwuiwa. Kasan cewar basu da bindigogi, sai su takubba, da gariyo, ga kuma su Yusuf na neman yin galaba a kansu. Yasa dayan janyo addar dake kusa dashi ya dabawa salis a kafa, ya kara daba masa a baya. Jin ihun da salis ya saka, tare da zubewa a kasa jini na zuba, yasa Yusuf dakatawa daga dukan dayan da yake yi, cikin tashin hankali da kidima ya nufi salis. Tun kafin yakai biyu suka rike shi. Da sauri babban ya janyo hankici da wata kwalba a aljihunsa ya zazzaga abin cikin kwalbar akan hankicin ya nufo Yusuf yana huci " kai mai taurin kai ko? Gaka jarumi! In mun je can ka gwada jaruntar taka a can." Ya fada yana kokarin shakawa Yusuf a hanci, kauda fuskarsa yayi tayi, daya dake bayansu ya daga gariyo ya bugawa Yusuf a keya " wan nan balaraben dan banzan taurin kai ne dashi, gashi da alama zamuja kaya so ba wasa." Ya fada bayan ya sauke masa gariyon. " lailaha illallah, muham.....ko kafin Yusuf yakai ga karasawa dayan ya shaka masa hankicin. Salis ne cikin karfin hali yake kaiwa mai shakawa Yusuf hankicin duka a kafa. Kallon salis yayi yana murmushin mugunta. Still duk da jikin Yusuf ya sake alamar he is uncountious bai sa ya dage hankicin ba. Ya ci gaba da kallon salis da murmushi a kan fuskarsa. Harbi suka fara jiyowa ta ko ina da sawun tafiya, na tunka rosu. Tuni suka tsorata. Ganin tabbas suka tsaya bata lokaci, zaa cin masu. Sake Yusuf sukayi suka tasa sauran jamaar dake tare da su a gaba. Basu bi takan salis ba da shima ya ke yashe cikin jini, yana sauke numfashi da kyar. Sun San daukar Yusuf da salis a halin da suke ciki barazana ce a garesu. Operation shaf shaf. Tun lokacin da aka tare motocin su Yusuf, wani bawan Allah dake aikin neman magunguna a cikin jejin ya gansu. Kuma dama yana da number na operation shaf shaf, saboda irin haka, tun da shi maa bocin hurda da dazuzzuka ne, suna ganin abun za suyi reporting. So ba bata lokaci ya kirasu ya shaida musu. Wannan shine So ko da suka isa dasu Yusuf abuja general hospital, dan danan aka fara attending dinsu. Still Yusuf na unconscious. Isowar ta wagar ango, da da Alhaji Jamil kusan a tare hankalinsu duk a tashe. Lokacin an gama dressing din ciwon salis Allah ya taimakeshi yankan bai shiga ciki sosai ba, musamman na bayan. Karfe uku dai dai doctor din dake kan Yusuf ya fito fuska ba annuri, da sauri Alhaji Jamil da Engr Sahabi suka nufeshi. Kallonsu yayi yana mai furzar da iskar bakinsa " I'm sorry Allah ya masa cikawa, saka makon over dose na...... Da bugun da aka masa a keya ya hana jijiyoyin dake sadar da jini ga kwakwalwa sun samu matsala. Tun kafin doctor ya karasa bayani, tuni Alhaji Jamil yayi cikin dakin su Yusuf ango da gaba daya baka gane hakan saboda tashin hankalin da suka samu Kansu ciki. Suka rufawa Alhaji Jamil baya zuwa gadon da Yusuf ke kwance. Tabbas mutuwa ba karya bace, nan danan suka fara hawaye Alhaji Jamil kam zubewa yayi a wurin a sume. Imran ne yayi karfin halin kiran waya ya shaidawa Ahmad halin da ake ciki.                  *************** A kwana a tashi asarar mai rai. inji bahaushe. Yau hubby ke fita daga takaba. Daukacin kannen Yusuf mata da kawayenta, da yan'uwa sun zo tayata murnar kammala takaba lafiya . Ta bangaren hubby har lokacin tana cikin damuwa, gaba daya ta rame kamar ba hubby ba. Dan yawan faraar nan ma yanzu duk babu, duk surutun hubby yanzu tana zaune za asha hira, amma ko uffan dinta baza kaji ba. Wannan Abu na matukar damun su Hajiya, tayi fadan, tayi nasihar duk a banza. Ga yawan kukan da ta lura hubby ta mai dashi ibada. kullun ta farka da daddare sai ta sameta ko tana ibada ko tana aikin kuka. Don haka suka yanke shawarar da zarar ta kammala  takabarta, ta tafi wurin gwaggo a kankiya. Don sun San ita kadai ce zata iya da hubby a wannan gabar. Haka ko akayi, hubby na kammala takaba, jafar ya dauketa zuwa kankiya.............     Yau gidan gwaggo cike yake. Alhaji Munir da iyalansa. Alhaji Kawu ma yau bai samu fita ba. Alhaji Munir na tare da mahaifinsa Alhaji kawu, sun lume a falonsa suna tattaunawa kamar yadda suka saba duk lokacin da suka kadaita da juna. A falon gwaggo kuwa mommy Hauwa da gwaggo sai jafar da hubby,Jabir. " gaskiya tsohuwar nan ta iya girki, dole in nayi aure in daukeki ki zauna a can kina dafa min beta. Shi kuma Alhaji Kawu mu nemo masa wata yar duma duma haka" hararar jafar gwaggo tayi " Allah ya sittiri bukwui, ni kam nayi ma nisa yaro, garama jafaru zan iya da rantamemen kan nasa. Amma kai kam ga dan Karen yanga, ga lalaci ina!!!! Bada ni ba." Dariya suka yi " da tsohuwar Zuma dai ake magani, kafin ki samu jabir jafar kika samu. Don ma zan rufa miki asiri, da wannan rigimar taki wa zai iya dake? In ba ni  din ba?" " ka ji cika baki? Kalleni da kyau na wuce alfarmarka. Karka manta har kujerar umra aka bani cin hanci." Dariya suka yi gaba daya. Mommy Hauwa ta ce " Kwarai kuwa, autana ya kwace mata kuna nan zaune." " wane shi mommy, aurena da gwaggo baya mutuwa. Takalmin kaza ne, mutu ka raba. Munci kujerar umra a awuf." Jabir ya fada yana kara danna lomar sakwara. " kayya dai!!! Ni na fara jiyo kamshin gidan junaid, ina ga zanyi na ywnmatan zamani nima. " gwaggo ta fada tana murmushi tare da turo dankwali gaban goshi. " kai kai kai!!! Wallahi baki isa ba, kin gama more min, sannan ki canza? Duk wahalar zuwa ungwuwar da nake kaiki? Dan goro na da kika cinye, dan turarena duka?" Harararsa gwaggo tayi cikin wasa, ta kara  tura dan kwalinta gaban goshi. " sai kayi lissafi junaid zai biyaka, har da kari. nifa ba mai min dole heh!!!!!!" " mai idon cin naira kenan?" Sai lokacin hubby ta sa musu baki. Mommy Hauwa kam tun dazu bin hubby da kallo take, cike da tausayawa. Yanzu kam tayi kyan gani, sai rashin walwala. Ta koma wata shiru shiru. " ganemin hanya sis " " kasan koda mukaje umra duk adduarta a kan junaid ne? Har da Allah yaja da ran mai halin tsoho, ko sau daya banji ta ambaci jabir ba, balle jafar." Hubby ta fada tana kallon jabir dake faman zaro ido cikin wasa. " lallema tsohuwar nan, watan kinci moriyar ganga ko?" " takwara akwai  sharri, kina ina nai ma kowanne dawafi na musamman. Kaji megidan kyaleta so take ta hadamu." Mommy Hauwa ta yi murmushi " aiko dai alkawari bai ce haka ba. Ke kikawa auta alkawarin duk randa ya kaiki hajj ko umra, to baki da miji sai shi, kin ga ko kyan alkawari cikawa. Ya kuma cika nasa. Mun shaida aure ya dauru ke da auta." Dariya gwaggo tayi tunowa da yarje jeniyarta da junaid wani Hutu daya zo mata, kusan shekaru Tara da suka wuce. " ai shi kenan. Yanzu dai shiga ki debo mana namu tsarabar umran. "  jabir ya fada " oh!!oh!! Ni banyi tsaraba ba, na dai muku addua. Kudina kuwa munci kaji, kayan marmari, da laban." Dariya sukayi ganin yadda take yi da baki da hannu don kwatan tawa. " lallai tsohuwar nan. Kije har kasa mai tsarki ki dawo, babu tsaraba?" " kullun ne ake kwana a gado? Wannan karon ban yi ba, dadin kudina naji, sai Ku jira zuwa na gaba, in Allah ya mana yawan rai." " sister kema bakiyi tsara barba?" Jafar ya tambayi  hubby Kai ta kada mishi, tana murmushi. " Allah ya kyauta, zanje next time don't expecte anything kuma." " ga zam zam can, dauka kasha. Ina laifi." Gwaggo ta fada tana nuna masa jarkar zam zam 5liter dake can gefe. Jabir ne ya kalli hubby cike da tausayawa. " sister menene plan Dinki? Kin ga zaman gida bazai miki ba, at least you have to fine some thing da zai kipping naki busy." Duk Kansu ido suka zuba mata suji amsar da zata basu, don jabir kamar ya sosama mommy Hauwa in da ke mata kai kayi ne, amma ta rasa ta inda zata faro. Shiru tayi tana wasa da yatsunta. " yo!! Mace kam ai da zaman gida aka Santa, fatana Allah ya fito mata da miji tayi aurenta,." Da sauri hubby ta kalli gwaggo. Cike da fushi ta ce " na ce kibar min irin wannan maganar, nida aure har abada, Nayi na gama." Rike baki gwaggo tayi " aa lallai, da kuruciyarki da komai ki ce kin gama aure? Wasa kike yarinya. Gara ki farka tun kan dare ya miki, don bazamu ajiyeki muna kallo ba kamar photo." Ganin hawayen dake bin fuskar hubby yasa jikin su jabir yin sanyi. " kiyi hakuri, naga an fara registration na JAM ne, in kina da shaawa sai kiyi, at least karatun zai debe miki kewa." Kada kai tayi tana share hawayenta tare da Jan hanci. " haka zaki zauna ba karatu? Ko dai ta bakin gwaggon ne, aure kike so?" Harararsa tayi " ina zuwa islamiyya Saturday and Sundays. Sannan akwai kankiya woman association committee da zan shiga, don tai makawa gajiyayyu, da marasa galihu, da Samar musu da sanaoi." Shiru sukayi suna kallonta. Jabir ya kada kai ya CE " har yanzu kina  nufin baki da interest a kan karatu? Haba sister u have to wake up. Lokaci ya wuce da mutun zai zauna ba tare da ya nemi ilmi ba. Ilmin addini yafi komai muhimmanci ga rayuwa, duniya da lahira, ammafa ki Sani shima ilmin zamanin yanada nashi anfanin. Don shi giahirine na rayuwa. My advice to u shine ki daure ki yi jam in yaso sai ki karanta Islamic studies, ko Arabic ,tunda kinfi son fannin addini, ga Islamic low ma duk u can do it." Jafar ne ya tare tare da ci gaba da cewa. " in da son samu ne, zan so ko midwifery ki yi, is good. " " wai ina dalili ne? Yarinya ta ce bata so, basai a gyaleta ba, Ku waya matsa muku kukayi karatun? Ina raayinku ne? To ita ma ku barta tayi abunda ta ke so. Haba tun kan yarinyar nan tai auren farko ta nuna bata raayi, don haka kar wanda ya takura mata, ku barta. Ku dai ku tayata da adduar Allah ya bata miji na gari tayi aurenta. Ba gararanbar gantalin karatu ba." " wai sau nawa kike son in gayamiki ki daina min maganar wani abu can aure? Nayi na farko nayi na karshe, in kika matsamin tattare kayana zanyi in yi gaba." Hubby ta fada cikin fushi tana share hawaye. Daga karshe ma tashi tayi ta shige bedroom din gwaggo tana faman mita. Da harara gwaggo ta bita " bansan ranki ya baci ba, sai naji duka. Aure kam ya zama wajibi, in da baa aure a haigoki? In sha Allah sai naga yayanki takwara. Don haka yanzu na fara miki maganar aure, kin dade baki tattara kin tafi ba. Don can din ma ba bakona bane ehee!!!" Mommy Hauwa dai nata ido, duk da zuciyarta tana cikin damuwa, da takaicin decision din hubby, amma tasan bata da ikon tofa nata, a gaban gwaggo,. Haka dai sukayi ta hira har yamma kafin sukayi sallama dasu, suka nufi Kaduna.                 ***************** Hubby ce da gwaggo suna fitowa daga wani special hospital kankiya. Dubo wani makwafcinsu da aka kwantar. Wurin parking suka nufa, don hubby ce ta tukosu. Sallamar da sukaji yasa su juyowa. Gwaggo ta amsa. Ganin mai sallamar yasa ta washe baki " aa doctor bokan turai, yaushe a gari?" Murmushi yayi tare da rusinawa ya fara gaisheta. " dazun nan na iso Umma take gayamin rashin lafiyan Alhaji, shine nace bari in zo in dubashi." " aiko ka kyauta. Jiki kam alhamdulillah ya fara samun sauki. Ya kishiyata da kannenta?" Cike da faraa ya amsa " sunanan lafiya, sun ce a gaisheku" " muna amsawa,." Sai lokacin hubby ta samu damar gaisheshi. Cike da kulawa ya amsa, yana tambayarta kannenta. Gwaggo ce tai karaf ta ce " suna can Kaduna, kasan ita tun da ta gama takabarta muna tare" " ayya haka ne, Allah ya ji kansa da gafara." Ya fada duk da yaje har Kaduna ya musu gaisuwa. Ran hubby ya baci. Fadi baa tambaye kiba, ta fada under her breadth. Juyawa tayi ta shige mota tana mai amsawa da " amin" da kallo ya bita yana murmushi, sai da ya daina ganinta kafin ya maida kallonsa kan gwaggo dake gaisawa da wasu yan mata da suke gaisheta. Sosa kansa yayi da key din motarsa yama gwaggo sallama da alkawarin zaizo kafin ya koma. Shiya budewa gwaggo kofar motar sai da ya tabbatar ta zauna kafin ya mata sallama. Kallon hubby yayi yana murmushi " kanwata sai anjima ko " hannu kawai ta daga mishi ta figi motarta tayi gaba. Yana tsaye a wurin fuskarsa dauke da murmushi har ta bacewa ganinsa, kafin ya kada kai tare da shigewa cikin hospital din. Kallon hubby gwaggo tayi, ganin yadda taketa kunbure kunbure, tana cika. Gwaggo ta ce " ke ko lafiyarki kike hawa kaman farashi?" Shiru ta mata, sai can ta kalli gwaggo " daga tambaya, meye naki na wani tsayawa kina masa dogon sharhi?" Haba gwaggo ta rike " too!!!!! Hashimu ne fa! Ko baki gane shibane? Dan gidan hausi" Haushine ya kara cika hubby. " ya zanyi in manta da mugu irinsa?" " aa takwara, hashimun ne mugu?" " eh!! Mana. ban manta muguntar da yayi ta min ba lokacin ina primary,." Dariya gwaggo tayi " mugunta ko gyara? Lokacin maganar wa kike ji? Daga Alhaji Kawu sai shi. Ai ni ko don yadda ya samin ido a kanki yasa nake son yaron." Tunowa hubby tayi da yadda yake tasata a gaba zuwa makaranta. Tana kuka tana komai, wani lokacin har da bulalarsa yana tsula mata in yaga tana son yawo da hankalinsa. In tayi tsokana ko rashin ji, shi yake hukuntata. Tun gwaggo na jin haushi har ta hakura. Wani lokacin ma da kanta take kai karar hubby wurinsa. Tsaki hubby tayi. Tunowa da alwashin da sukaci ita da kawarta dija, na  Duk randa Allah ya sa ya haihu, sai sun rama a jikin dansa.  Tabe baki gwaggo tayi, ta ci gaba da kalle kallenta, har suka iso gida.                  ***************** Kamar yadda Hashim yama gwaggo alkawari, ko sai gashi da yamma. Hubby na tsakar gida tana shara, gwaggo na daga falonta, ta daga labule suna magana da hubby kan community da aka kafa wanda zai yattauna da chairman din kankiya local government da kansiloli, don tattauna hannoyin magance matsalolin rashin aikin yi ga matasa da Samar musu da abubuwan yi. Mu samman mata. Sallamar shine ta katse musu hirar. Da sauri ta yayibi hijab dake jikin igya ta zunbula.  A hankali yake takowa idonsa a kanta har ya zo daf da ita. Idonta akan tsintsiyar duk da jikinta ya bata ita yake kallo, bata dago ba. Jin takunsa da kamshin tururensa yasa tasan yazo gaf da ita. " ina wuni " ta fada a takaice ba tare data kalleshi ba. Cike da faraa ya amsata. Tare da shigewa falon gwaggo dake faman masa sannu da zuwa. Tsaki hubby taja ta ci gaba da shararta. Hira sosai sike shida gwaggo, dan game da aikinsa, da iyali. " baka kyautawa hashimu, yanzu shekara nawa rabon yaranka da garin nan? Ko ba komai ka kawosu suga yan uwa, don su sansu, su saba dasu, ba in an haduba a zama bakin juna. Ku yan boko Sam rayuwarku ba tsari. Zumunci ya wuce komai. In baka sabawa yaranka shiga cikin yan uwanka ba sai yaushe? Kai kanka yaushe rabonka da garin nan? Kullun zancen mahaifiyarka ke nan. Kai baka damu kazo ba, ballan tana iyalanka. Su kuma in sun je maka ba dadi. Wace irin rayuwace wannan? Ina rokonka don Allah kayi kokari ka gyara. Ko duk wata ne kazo ka duba iyayenka, in anyi hutu ko kwana uku ne ka kawo yaranka suga gida. Ta haka ne sai kaga zumunci da shakuwa ya wanzu a tsakaninsu. Dama wannan ne yasa nake son ganinka." Kanshi a kasa, tabbas duk abinda gwaggo ta fada gaskiya ne. Shi kansa abun na damunsa, amma ba yadda ya iya. " in sha Allahu zan gyara. Na gode sosai." Murmushi gwaggo tayi, tare da kwalawa hubby kira " ki kawo ma hashimu ruwa mana" " Habiba ta koma makaranta ne? Ko har yanzu hali nanan na kin makaranta?" Ya tambaya Nisawa gwaggo tayi " wane makaranta kuma banda Wanda tayi. Islamiyya dai take zuwa." Girgixa kai yayi yana murmushi " ilmi yana da amfani da ta daure ta koma ko diploma tayi yafi zaman haka." Dai dai lokacin hubby ta kawo masa ruwa, da 5 alive. Tabe baki gwaggo tayi " Ku barmin ita tayi abin da take so. Suma kannenta da iyayenta maganar kenan. Tun da bata da raayi, ina dalilin tursa sawar bayan mun samu ta dawo hayyacinta da kyar. Shiyasa na ce kar Wanda ya kara takura mata kan maganar makaranta. Fatana Allah ya bata miji na gari tayi aurenta. Duk da shi din ma na lura zaayi yaki da ita, don ba aure a rayuwarta. Yarinya karama kuwa kamarta ba yadda zamu ajiyeta gida muna kallo." murmushi yayi don yasan tsakanin gwaggo da hubby " Allah ya zaba abinda yafi alkhairi." Ya fada " amin ya Allah" Alhaji Kawu ne yayi sallama. Shima Cike da faraa ya ce " aa Hashim ne yau a gidan?" Dariya gwaggo tayi " aiko dai gashi nan." Murmushi Hashim yayi yana shafa keya. Tare da gaisheda Alhaji Kawu. Hira sosai suka sha, sai gaf da magriba ya musu sallama ya fito. Har lokacin hubby na zaune a tsakar gida kan kujera yar tsugunno tana gyara busasshen zogale. Muryarsa da kamshin turarensa taji a kanta. " sister can I have your phone number. " Dago fararen idonta tayi ta sauke a kansa. Wanda ya kara sakarma da Hashim wani irin yanayi a tattare dashi. " bani da phone. " ta fada tana ci gaba da gyaran zogalenta. " really? I can believe baki da phone. Sai dai kice bazaki bani ba kawai." Ba tare data dago ba ta ce " da gaske nake, don bani da bukatarsa." Murmushi yayi tare da Sosa kansa. " can I buy u are one ?" Cikin sauri da kosawa tace " no, I don't need it." " OK " ya fada cikin sanyin murya Har ya juya zai tafi, ya dawo " zan iya kiranki a phone din gwaggo? Don akwai magana mai muhimmanci da nake son mu tattauna." Dago kanta tayi, alamar ranta ya fara baci, don ya hango zallar bacin rai a idonta. " please Yaya Hashim don Call me." Ta fada tare da tashi ta shige falon gwaggo. Da kallo ya bita kafin ya girgiza kai, yana murmushi ya bar gidan.              ********************** Hashimu Adam kankiya, shine asalin sunansa. Da ga Alhaji Adam da Hajiya hafsatu, wadda su gwaggo ke kira da hausi. Makota ne, tsakaninsu gida biyu. Su biyar ne a wurin iyayensu, shine babba. Yayi karatunsa primary da secondary anan kankiya, kafin ya tafi ABU, in da ya karanci medicine. Yanzu haka cikakken doctor ne mai zaman kansa. Wanda ya mallaki hospital na kashin kansa a garin abuja. Hashim baki ne, amma ba wuluk ba, mai matsakaicin tsawo, mai kyan sura da cikar kamala, shi baza a kirasa kyakyawa ba, bakuma ya cikin sawun munana. Dan kimanin shekaru 47 amma saboda jin dadi, da gogewa yasa baza ka dauka yakai hakan ba. Yanada mata daya da yara hudu. Biyu maza biyu mata. Mutun ne mai nagarta da halin dattako, sai dai baiyi Saar abokiyar rayuwa ba. Fatima irin matan nan ne masu son kansu. Sun fi son mijinsu ya zamana daga su sai yayansu da yan uwansu. Hakan ne yasa bata zauna ba. Wurin Neman asirce asirce don ya zama nata. Tako yi nasara don sai ya shafe fiye da 3month bai waiwayi iyayensa ba. Dama ita ba zuwa take ba. Sai da babban dalili, haka yaran bata yadda su rabi dangin uban ko kadan, sai danginta. Suma dangin nasa basa zuwa, saboda kalolin wulakanci da cin zarafi da suke fuskanta a wurin Matar gidan da yaranta. Hatta yan aikin gidan basa girmamasu, shi yasa suka dauke kafarsu Suma. Abin na matukar damun Hashim amma ba yadda ya iya,." Tun hubby na karama take burgeshi, Abu daya ke hadasu bata son karatu ko kadan, shi kuwa bashi da buri irin yaga kannensa sun yi ilmi sosai, lokacin tana primary 2 shi kuma yana 3ooL. So haka yake fama da ita kan rashin son zuwa makaranta, tare da kanwarsa Khadija wadda take kawa ga hubby, sai dai ita Khadija tana kokari sosai a school, ta riga hubby gama primary da 2years, repeating din da aka musu na farko a tare, da yazo ya musu dukan mutuwa, tun daga nan Khadija ta shiga hankalinta. Duk da da yawa tare suke rashin jin su. Zumunci ne sosai tsakanin gidan Alhaji Kawu da gidan Alhaji Adam. Duk da Alhaji Kawu ya girmema Alhaji Adam sosai anma bai hana amin takarsu karfi ba. Haka hausi da gwaggo, don ta dauki gwaggo kamar Yaya, kuma yar uwa, mai bata shawara.               ******************** Parking dinta kenan a dai dai hole din da suke metting, ko training. Sanye take da doguwar riga ta atamfa, light blue sai dogon hijab mai hannu purple kalan design din atamfar. Ba wani makeup a fuskarta, daga powder, kwalli, sai wet lips. Tayi matukar kyau fuskar nan sai daukan ido take don glowing. Tana kokarin fitowa, wata mota kirar landcruser 2018 baka mai bakin tilted tayi parking kusa da ita. Sai da ta mika hannunta gefe ta dauko handbag dinta, ta bude bayan ta dauki wani jaka madai daici, sannan ta rufe motar da remote. Juyowa tayi don nufan cikin hole din, ganin mutun tayi tsaye jingine jikin karshen motarta ya mikar da kafarsa, yanda bazata samu damar wucewa ba matukar bata kan kafafun zata bi ta wuce ba. A hankali ta dago don ganin wannan mai karfin halin, da rainin hankali......   [02/03, 12:33] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 10       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau Wani haushine ya kume hubby. Ta Dade bata ga mutun mara zuciya irin wannan bawan Allah dake gabanta ba. Kallonta yake cike da so da Kauna, sai wani killer smile yake sake mata. Har bata San lokacin da ta dalla masa harara ba, Tare da Jan tsaki. Murmushi ya kara sake mata " mai nema baya fushi, mai son dan tsuntsu shi ke binshi da jifa. Na gani ina so, don haka no matter how u try bazan taba barin abinda rai ke so ba. Nasan zaki ce wannan mutun ya cika naci? But I don't care, haka nake da naci kan abinda nake so." Ya fada yana tsareta da kyawawan idanuwansa. Ganin tana kokarin komawa cikin motar yasa ya iso da sauri ya rufe kofar da already ta bude, ya jingina jikin kofar dare da mikar da kafafunsa. Yanda bata da choice dole ta tsaya. Saitin zuciyarsa ya kai hannunsa ya dafe yana kallonta still da murmushi akan fuskarsa. " please ki taimaki zuciyata ki tsaya ki saurareni koda sau daya ne." Agogon hannunta ta kalla, tare da scanning din wurin, taga ba wata hanya da zata iya escaping. Kallonsa tayi tare da hada hannayenta alamar roko " na rokeka don Allah ka fita a rayuwata, ka daina bibiyata haka, ka takuramin, bana bukatar jin komai daga gareka, Please live me along." Murmushi yayi Wanda ya bayyanar da kyawawan jerarrun fararen hakoransa. " Habiba ke nan!! Ke kina ganin akwai abinda zai sani daina bibiyarki? Zuciyata bazata dauka ba, don bataji bata gani, in dai a kanki ne. Tunda idona sukayi arba dake a saudiyya har yau zuciyata bata samu sukuni ba. Kin San daga inda nake bugo mota duk 4 to 5 days in zo kankiya don in ganki? U don't have idea? Nazo gidanku yafi a kirga kin ki fitowa, na biki wurare da dama, kin ki saurarena. Kina tsammanin duk hakan zai sa zuciyata tayi fushi ta rabu dake?" Murmushi yayi mai sauti. Never bibiyarki kuma yanzu na fara matukar baki saurareni kin ji bayanan bakina ba." Wani Abu ne ya tsayawa hubby a zuciyata, ga haushinsa ta taji ya kara mamayeta, ji take kamar ta man mangara mai mari ko taji saukin haushinsa da takeji. " malan don Allah kaban hanya in tafi, kaga nayi latti. " Tsayuwarsa ya gyara. " in kinga mun bar nan, kin saurareni ne, ko kin bani appointment din inda zamu hadu, da alkawarin zaki tsaya ki saurareni. In ba haka ba, zamu shekare a nan ni dake." Harara ta watsa masa. Murmushi yayi tare da daga mata gira daya,. Ganin da gaske yake, ya tasata gaba sai kallonta yake, yana murmushi. Alamar yanayin na nasa dadi, don har wani lumshe ido yake. Wanda yasa hubby kara fusata. " ka matsa na wuce, ko nayi maka ihun barawo." Dariya yayi, yana kallon area din. " da kin kyauta, don nasan bazan rasa masu tayani rokonki da ki tsaya ki saurareni ba. Dama ihun kwarto kikayi da, da dan sauki,. " ya fada yana kashe mata ido. Tsaki tayi ta kauda kai. " i like everything about u, komai naki me kyau. Hararaki, tsakinki, fushinki duk suna miki matukar kyau. Keep it up." Ganin in har ta biyeshi tabbas zata bushe a wurin yasa ta kalleshi cikin fushi da gundura. "Bari in baka phone number dina." Murmushi yayi tare da ciro phone din a aljihunsa na Jeans ya mika mata. Number tasa ta mika mai. " ban hanya na wuce." Murmushi yayi " not so fast, let me try the number first. " Gabantane ya fadi, tana ta shiga uku da wannan mayen, tare da rokon Allah ya rabata dashi. Don ya addabi rayuwarta. " number baya shiga" ya fada yana kafeta da ido. Kauda kanta tayi " phone din na gida na barshi ba charge, sai na koma zan sa a chargi sai ka kirani." Dariya yayi " bana bukatar number, appointment nake bukata." Kallonsa tayi, tana harararsa,don haushi bata san lokacin data furta " wai kai wane irin maye ne." " in a kanki ne, ki kirani da fin haka ma in kinso, don bakiga komai ba, sai mun shekare a nan  tukun." Tayi minti 2 tana tunanin yadda zata rabu da wannan mayen ta huta. " OK ka dawo nan da 1month." Dariya yayi sosai " lallai ma, so kike zuciyata ta buga kenan." " don Allah ka tafi, ai dai nace ka dawo ko?" " zan zo gabe da yamma gida, in kin min alkawarin zaki saurareni fine." hararasa tayi tana tura baki. " kinyi alkawarin zaki fito in nazo?" Ya fada yana murmushi Kauda kanta tayi " yes " ta fada tana daukar Jakarta data ajiye a kasa. Murmushi yayi " thanks " ya fada yana murmushin jin dadi. Jakar ya karbe a hannunta " muje in kai miki, bana son kina wahala." Gaba yayi ba tare daya ko saurareta ba. Jiki a sanyaye tabi bayansa, tana tunanin yadda zata bullowa lamarinsa. Har kofar hole din yakai mata jakar, ya ba security ya karasa mata dashi cikin hole din, Sannan ya juya. Already ta samu har an dade da fara program din. Hakuri ta basu kafin ta nemi wurin zaman da aka tanadawa members.                  ****************** Suraj M. Sa'ad Kangiwa, da na miji tilo ga Alhaji Muhammad Sa'ad  kangiwa. Haifaffen garin kangiwa dake jahar kebbi. Mamallakin kangiwa groups of company. Wanda suke harkar sufuri, na motoci gari zuwa gari, na shiga, dana daukar kaya, har da na jirage masu taken kangiwa air lines. Suraj yarone matashi dan shekara 30, yayi karatunsa a aviation dake Zaria, in da ya wuce   Cairo don Karin gwanan cewa a harkar tukin jirgin sama. Yanzu haka yana  daya daga cikin matukan jiragen  company din mahaifin nasa, na kangiwa airlines limited. Kyakyawa ne,  dogo mai dan jiki, sai dai shi baki ne, irin mai daukar idon nan, ga kuma Hutu. Yana da kanne mata uku. Biyu sunyi aure, sai autarsu. Suraj a kwai kirki, ga kyauta, ga son jama'a,. A kwai naci a kan duk abinda yake so. Ya fara ganin hubby a garin madina a farfajiyar masallaci. Suna zaune ita da gwaggo da Alhaji Kawu. Sai abokin Alhaji Kawu, malan saminu. Su kuma suna zaune daga gefen su shida abokinsa, BK. Tun da ya daura ido a kanta, ya nemi natsuwa ya rasa. Lokaci daya yaji soyayyyarta ya ratsa zuciyarsa. Fargabansa daya Allah yasa bata da aure, don yadda ya ganta cikin shiga na doguwar riga, brawn da hijab dogo mai hannu brawn da milk. Dissent dress hatta kafarta tana sanye da sock's, daga fuskarta sai tafukan hannunta kawai kake iya gani. Wanda yasan matan aure ne suka fi yin hakan. She look classy Lady, in good dissent way. Ba abunda ya kara tafiya da shi, irin yanda take magana cikin sanyi, sanyi- shagwaba - shagwaba. Murmushinta. Su suka shagalar dashi da kallonta. Har KB ya farga da abokin nasa. Bai boye masa ba ya gaya mishi halin da yake ciki." " baka gudun ko Matar aure ce? Daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zaki? Ko dai halin ne ya motsa?" KB ya jero masa tambayoyi yana tsareshi da ido Harararsa yayi " haba duk iskancina ai banayi a kasa mai tsarki ba. In har bata da aure to nikam nayi mata, zai yi wuya in tana da aure, da gani yarinya ce karama." " taya zaka yi ka banbance? Kar ka manta a nigeria ba wani abu bane aure da wuri, so ba abun mamaki bane in tanada shi. Kaga yanayin shigarta ma?ko ina a rufe, bayan nasan full option kake nema." Murmushi yayi " koma ya cikin yake ina so haka, don tamin, da gani cikin ma zai yi kyau." Dariya KB yayi " na manta dan hannu ne ashe. " " tuba yazo tunda naga matar aure." " Allah yasa." " yanzu ya zaayi in samu information a kanta?"  Ya tambaya still idonsa na kan hubby " karka damu, na san dayan hotel dinmu daya dashi, tare sukazo da his Excellency, ban san ya akayi na ganshi kuma a nan ba." " maybe sun san juna,." " its quite obvious, zuwa gobe in sha Allah zan samo maka duk wani information a kanta." " na ko gode" Har washe garin ranar suraj na cikin zullumin abunda zaiji a kan hubby. Don zuciyarsa ta gama matowa a kan sonta. Har mamakin yadda yake jinta a zuciyarsa yake. After 2 days sannan KB ya zo masa da albishir cewar bata da aure, tana zama da kakan ninta a kankiya, amma iyayenta na Kaduna. Iya abinda ya samo kenan. Hankalin suraj ya kwanta, sai tunanin yadda zai tunkareta. Don duk ganin da zai mata suna tare da gwaggo. A Makka ne yayi nasarar yi mata magana da suka hadu a Hilton, ya taki saa lokacin ita kadai ce. Ta fito siyan chocolate. Duk yadda yaso ta saurareshi ki tayi, don ko kallon arziki bai samu ba. Tun daga nan ya shiga bibiyarta, har ta gane, don baya samun damar yi mata magana sai tana ita kadai. Don haka ta dena fitowa ita daya. Har suka dawo bai samu damar Isar mata da sakon zuciyarsa ba. So koda ya dawo yana yawan zuwa kankiya musamman don ita, amma bai taba samun damar ta saurareshi ba, in yaje gidan bata fitowa, har ya gaji da tsayuwarsa ya tafi. Kusan duk inda take zuwa ba inda bai Sani ba, saboda bibiyarta, ko zai samu ta saurareshi amma ina. Sai yau Allah ya bashi Saar ritsata. After good 5month of supering. Har mamakin kansa yake yadda yan mata masu kyau da aji ke bibiyarsa yana musu yanga, yau sai gashi ta juyo kansa, shi mace da da bai dauketa komai ba, face abar holewa da jin dadi, ke ta garashi, kamar gare."                ******************* Yau gidan gwaggo yayi albarka. Zuwan su Ahmad da kakarsu Hajiya Aisha. Bayan sun tafi sai gasu yusra da humaira kawayen hubby na secondary. Zo kaga murna wurin hubby. Tama rasa ina zata sa su don dadi. Wannan shine karo na farko da yusra ta kawo mata ziyara kankiya. Ita kanta gwaggo taji dadin wannan ziyara. " gaskiya naji dadin ganinki, haka ake son musulmi ya zama mai tawakkali, da rungumar kaddara in tazo masa, mai kyau da mara kyau. Shi yasa kwanakin baya baki ganni ba, don yadda naji su Aisha na bani labari, sai naga bazan iya jurar ganinki a hakan ba." Murmushi hubby tayi " ya zanyi? In ma na ci gaba da daga hankalina, ba abunda zai canza. Sai dai har yanzu nakan ji wani lokacin abun ya zamemin sabo, duk yadda naso ban iya jurewa." Dafata yusra tayi " hakane dama, baki isa ki cire shi kwata kwata a ranki ba, addua ita ce garkuwa ga mumini, in har kin ci gaba, sai Allah ya kawo miki sauki, sannan ya musanya miki da abinda yafi Wanda kika rasa alkhairi." " Alhamdulillah addua kam inayi. Zuciyata ta danyi sanyi, bana jin kuna kamar da." Humaira tace " Allah ya baki Wanda ya fishi, shi kuma Allah yaji kansa yasa ya huta." " Amin" sukace gaba daya. " ni kam na gama aure ai. Fatana in zama uwargida a wurin king dina, anan duniya da kuma can Aljannatul firdaus in sha Allah. " Murmushi sukayi, humaira ta ce " kina wasa ne, ta Yaya kike tsammanin zasu zuba miki ido kiyi ta zama ba aure? Wannan ai tatsuniyace, mutuncin ya mace dakinta, da kuruciyarki, ko haihuwar farko bakiyi ba. Amma ki ce kin gama aure? Haba hubby ki canza tunani, nayi imanin ko shi Yusuf din bazai so haka ba." " gaya mata dai! Wata kila Ku taji naku." Gwaggo ta fada tana shigowa falon. Harararta hubby tayi. Daga ita har humaira " ban san mutun na hararata ba sai naga idonsa a kasa. Ke yanzu baki gode Allah ba? Yanmata da zawarawa nawa suketa gararamba suna neman ko mai shinshinawa ne, basu samu ba. Amma ke kin samu kina wulakantawa. Jibi gidan Alhaji jibo, yan mata sun kai biyar, haka gidan Alhaji mamman ga gidan Alhaji Ibrahim duk ko wanne cike da yan mata,kuma duk a layin nan, amma ba mazan aure, ke kuwa fa? Nawa zuwa yanzu suka fito? Banda Wanda kike kora ban Sani ba." Baki su yusra suka rike " gaskiya baki kyautawa, ni kaina da na samu mijin ai da tuni nayi aurena na huta. Amma ina kullun wannan yazo ya zuba min karyarsa, da anyi maganar ya fito baki kara ganinsa. Don Allah hubby kiwa kanki fada." Harara hubby ta zubawa humaira " Allah ya baki na gari, keda kike nema, ni kam akai kasuwa." Kwafa gwaggo tayi " yi iya yinki yarinya. Don muddin kika kaimu makura sai dai kiji an daura. Gara ma ki natsu ki fitar da Wanda kika ga ya dace da tsarinki." " tabdijam!!! Asheko zaku kwance shi ba shiri. Na kusa tattara inawa I nawa in bar miki gidanki, don na lura so kike ki takurawa rayuwata." Hubby ta fada tana tura baki cike da fushi "Allah raka taki gona, can din ma ba bakona bane ai, na dade da jin wannan zan cen." Bayan fitar gwaggo yusra ta kalli hubby " gaskiya gwaggo ke gaya miki, yanzu shekara daya kenan da rasuwar Yusuf, ba laifi bane don kin sake aure. Aure shine gata da rufin asirin duk wata ya mace, duk abunda zaki samu, ko zaki zama a duniya, matukar baki da aure kinyi aikin banza. Kar kiyi wasa da damarki, Allah ya dube ki ya baki masoya ki natsu ki fitar da miji, kiyi aurenki." Cikin fushi da daga murya hubby tace " Ku wai me yasa kun kasa ganewa ne? Kowa aure aure. Kina ganin zan iya wata rayuwa da wani namijin in ba Yusuf ba? Bazan iya ba, Yusuf kadai zuciyata taso shi kadai zata ci gaba da so har karshen rayuwata." Hawayen da suka ga yana bin kuncinta yasa duk jikinsu yayi sanyi, cike da tausayawa suka fara lallashinta. " yusra ba sai na gayamiki komai ba! Ke kanki ganauce ba jiyau ba, ke zaki ba wani labarima, kinsan yadda rayuwata, da zamana da Yaya Yusuf yake. Wane namiji kike ganin zai soni, ya kula dani, koda kwatan kwacin na Yaya Yusuf ne.??? Babu, wane ne zan zamu mai nagartar Yaya Yusuf? so please live me along, Ku barni inyi rayuwata the way I want" " I known hubby, Allah ya zaba miki mafi alkhairi, amma karki debe tsammani ga rahamar Allah. Sai kiga ya baki Wanda ma yafishi komai da komai, ke dai ki ci gaba da adduar neman zabin Allah, aduk kan rayuwarki." Yusra ta fada in carm voice. Tsaye yake a tsakar gidan, duk abunda suke fada yana jiyosu daga inda yake. Duk da hirar da gwaggo ke masa bai hanashi maida hankalinsa don jiyo abinda ke kara karyar masa da gwuiwa ba. Saboda ita yake yawan ziyartar kankiya a watanni biyu da haduwarsu, yazo kankiya a kalla sau biyar kenan, abunda bai taba yi ba a tarihin rayuwarsa, tun da aikinsa ya koma abuja. Sai haduwarsa da hubby da ta sace dukkan natsuwarsa. Soyayyarta ta gama ratsa duk kan zuciyarsa burinsa ta aminta dashi. Sai dai kash wadda yakeyi don ita bata ma san yanayi ba. Don duk wata hanya da zai cimmata ta toshe masa shi. Shi kuma kunya da nauyi ya hanashi ya magantu ga iyayensu. Duk da ya lura sun gama da goshi, sun dai zuba masa ido ne suga gudun ruwansa. Wannan zuwan yayi alwashin bai komawa abuja sai da gamsashshiyar magana tsakaninsa da hubby. But wannan kalaman nata da yaji yasa gwuiwarsa ta fara sanyi. Amma duk da haka yaci alwashin ganawa da ita. " takwara kizo Ku gaisa da hashimu.? Gwaggo ta fada cikin daga murya, yadda hubby zata jiyota. Yi tayi kamar bataji ba, sai da gwaggo ta kara maimaitawa, sannan ta amsa. Tsaki taja don ta dade da harbo jirginsa. " ke ko lafiya kike yiwa mutane tsaki?" Tsskin ta kuma tana kallon yusra " I hate him, naga alamar yana son takurawa rayuwata, ita kuwa gwaggo ta kasa ganewa, sai wani yashe masa hakora take kamar kantin cukula." Humaira ce tayi dariya " lallai kin rika, gwaggo kike fadawa haka?" Harararta hubby tayi. Yusra ce ta tambayi hubby dake kokarin zunbula hijabinta, kafin gwaggo ta fara sababi. " waye ne shi?" " no body. Just a nevour." Murmushi dukayi a tare, don sun dago zancen. Humaira ce ta mike, " nima bari in zo mu gaisa" mikewa yusra tayi ta gyara gyalenta. " muje nima in kwashi gaisuwa." Da kallo hubby ta bisu ta gyabe baki tare da kada kai, a tare suka fito. Cike da girmamawa suka gaisheshi. " aa sister baki kika yi ne?" " eh!!" Ta fada a takaice tana kara tamke fuska. " sannunku da zuwa" ya fada yana kallon su yusra Gwaggo ce ta amshe da " kawayenta ne suka kawo mana ziyara tun daga Kaduna." Murmushi yayi " masha Allah, kun kyauta, kuma kunyi zumunci. Ya karatu ko kuma yan uwan dayan ne?" Murmushi sukayi, hubby kam tuni ta koma inda ta fito. " karatu alhamdulillah, ni na gama, service nakeyi, wannan kuma tana final level. " yusra ta fada tana nuna humaira. " waw wonderful." Nan yayi ta jansu da hira. Aikuwa tuni suka saki jikinsu dashi suka fara hira, Wanda yawancin labarin secondary school life dinsu ne. Hashim kam na cikin walwala musamman jin wasu labarai na ban dariya na mutuniyarsa, Wanda suka sashi nishadi Kwarai da gaske. Hubby na daga falo ta cika   tayi tam, don haushin yadda su yusra suka saki baki sunata bashi labari suna kwasar dariya. Hashim mutun ne mai faraa da saurin sabo, akwa hira. Shi yasa suke shiri da gwaggo. Ya dade dasu kafin ya musu sallama ya tafi, Tare da musu kyautar 10k. Ganin suna ta mata magana tai banza da su. Yasa yusra darawa. " Haba gimbiya a gidan doctor Hashim, Allah ya baki hakuri, don nasan haushin munsha hira da doctor ne yasa ake mana shan kamshi." Tsaki hubby tayi " aikin banza, daga ganin mutun Ku zauna Ku saki baki, fadi baa tambaye kuba." Dariya su kayi " because he is a nice man. He Love's u so much. Kin ga kallon da ya dinga miki kuwa?" Yusra ta fada tana dafe zuciyarta tana wani kashe ido " wow, kin tafi dashi." Duka hubby ta Dada mata a cinya. Don't u Dare say it again." " wai wai wai" yusra ta fada tana Sosa inda hubby ta duketa. " meye aibunsa? To me, kun dace sosai kin san ance in kanason more rayuwar aure to ka auri Wanda ya baka shekaru da yawa. Ya fika ilmi da sanin rayuwa, so zai iya jure duk yarintar da kaje masa da ita." Banza hubby tayi da su, sunata tattaunawarsu a tsakanin yusra da humaira, sai gwaggo data shigo daga baya. Itama ta shiga anayi da ita. " hashimu yaron kirki ne, mata ce kawai baiyi saa ba. Bata da mutunci ko kadan, a cewarsu ashahadu a wuyansu, don ban ganiba, kar a tsaidani ranar shaida. Ance har shige shige takeyi,."  Dariya sosai su yusra keyi ganin yadda gwaggo keyi ta baki da hannu. " Allah ya zaba mata mafi alkhairi. " humaira ta fada still tana dariyar gwaggo " amin dai, amma ni kaina ban son auren hashimu nan da takwara. Saboda wannan shuumar Matar tasa, zai yi wuya ta bari a zauna lafiya. Shi yasa nake fatan kar ma ya samu damar furta abinda ke ransa." Murmushi yusra tayi " nima dai ban mata fatan auren mai mata wallahi." Sallamar da akayi ya katse masu hirarsu. Driver dinsu yusra ne ya dawo, don dama shima ya shiga gari duba wani baffansa, bayan sun bashi time din da zai dawo daukarsu. Sallama sukawa su gwaggo. Sha tara ta arziki hubby da gwaggo suka musu, hubby ta rakosu har mota, sai da taga bacewarsu kafin ta juya ta nufi cikin gida. Ta dafa get din gidan kenan da nufin turawa ta shiga, taji sallama daga bayanta. Tare da wani daddadan kamshi daya doki kofofin hancinta. A hankali ta juyo don ganin mai mata sallamar tare da amsawa, don sanin muhimmancin amsa sallama a musukunci. Ido hudu su kayi da......... ,   ...Wani bakin ciki da takaicine ya cikata a lokaci daya. Nan take ta kara tamke fuska, tare da shigewa farfajiyar gidan. Bayanta ya bi fuskarsa cike da murmushi Wanda hubby ta dauke shi a rainin hankali. Sanye yake da black Jens, da shirt mai gajeran hannu, maron colour  mai cubes din adon baki. Kafarsa sanye da covershoe baki, sai agogo silver mai matukar daukar ido, kamar yadda gashin kansa yasha gyara tare da siririn sajen daya hade da gemun da aka sai sayeshi sosai, Wanda ya karama fuskar kyau da kwarjini. Kana ganinshi kaga big guy mai ji da ilmi da hutu, musamman yadda fatarsa ke glowing duk da yake baki. Ganin tana kokarin shigewa ciki ta barshi yasa shi shan gabanta cikin sauri. Yana mata wani hadadden smiling mai fallasa sakon zuciya ga maabociyar zuciyar. " me yasa kike hakane? Kin ce nazo yau. nazo tun 4:30pm ina kofar gidan nan, ina faman tunanin ta yadda zan samu mai kiramin ke, tun da kin hanani phone number, Ban samu ba. Allah yaji kaina ya turo min ke. Ta ina kike ganin zan bari ki subuce min?" Kallon gefenta tayi, " zan fito ai, daga rakiya bai kamata aga na dade ba." Murmushi yayi yana cikin jin dadi " OK. Ai da sai kiyi bayani." Ya fada yana bata hanya. Da sauri ta shige cikin gidan. Da kallo ya bita yana murmushi, wani farin ciki ne ya lullube zuciyarsa. Runtse idonsa yayi yana furzar da iskar bakinsa. "Ya Allah" ya fada a hankali tuno kyawawan hannayenta masu dauke da dogayen yatsu, kumbunan dogaye sun sha adon bakin lalle, lukui lukui dasu, haka kafarta gwanin shaawa, kamar ka taba jini ya fito, duk da ba fara bace, amma tanada haske mai daukar ido, don bazaa kirata chocolate ba. Yadda ya lura da juyawar jikinta, ya sa shi shiga wani yanayi,  duk da tana sanye da dogon hijab har kasa, ash mai hannu. don ko kayanta na ciki baka iya hangoshi ta kasa. Sai plat shoe yellow mai adon White stones manya. Wanda ya kara fito da kyan kafafunta. " ya Allah, suraj aure kazo nema fah!" Ya tunawa kansa tare da shafar sajen kansa. Yana sauke ajiyar zuciya. "I wander abun da yarunyar nan ke boyewa cikin wannan zunbulelen hijaban, ko zafi bata ji." Wata zuciyarsa ta fada Kujerun roba ya hango kusa da wani daki, da gani dakin megadi ne, amma bai ga alamar akwai megadin ba. Biyu ya jawo tare da zaro handkerchief a aljihunsa ya goge sannan ya gyara zamansa, kafa daya akan daya yana bin gidan da kallo. "Not too bad"  wata zuciyar ta fada Gidane dan dai dai, ginin zamani, mai wadataccen fili, da shuke shuke. Gwaggo ta samu a tsakar gida " har sun tafi." Ta tambayeta " eh!!!" " To Allah ya saukesu lafiya." " amen" hubby ta fada tana kallon gwaggo ta rasa yadda zata gaya mata. Ganin yanayinta yasa gwaggo ta kalleta da kyau " lafiya dai ko?" Tsaki hubby ta ja dan shiru tayi kafin ta iya lalubo abin cewa. " wannan da nake gaya miki ya takuramin tun a saudiyya, shine mukaci karo dashi, yanzu haka yana get." Baki gwaggo ta washe " masha Allah. Maza jeki  kin barshi a tsaye, ai haka ba kyau." Harararta hubby ta yi ganin yadda gwaggo take faraa kamar wadda akawa albishir da gidan aljanna. ". Ke maza wuce mana, kika tsayamin akai." Har hubby ta juya zata fita gwaggo ta kirata. " a haka zaki fita? Ba dan ko gyara fuska, balle aje da bashi ruwan sha? Ke kuma kalan naki kenan?" Juyawa hubby tayi ta fice tana mai jin haushin gwaggo dashi kansa suraj din Bai kai matsayin da zata tsaya tana wani kwalliya saboda shi ba. Mutun daya ne, kuma yanzu babu shi. Ita yanzu neman hanyar da zata rabu da wannan karfen kafar takeyi. Murmushi ya sakar mata, tare da nuna mata kujerar dake kusa dashi. " bismillah gimbiyata" Harararsa tayi tare da janye kujerar can gefe ta zauna tana kallon gefenshi. Shi abun ma dariya ya bashi, ganin tazarar data bayar a tsakaninsu. Matsowa yayi kadan, still akwai space a tsakinsau. Shirune ya biyo baya, na wasu minute. Kallonta yake yana godiya ga Allah, tare da fatan ta zamo rabonsa. Don shi kansa baisan iya adadin son da yake mata ba. " kiyi hakuri, nasan na matukar takura miki, I'm sorry." Shiru tayi masa, ganin bata da niyyar tanka masa yasa ya gyara zamansa. Cikin muryarsa mai dadin sauraro ya fara da " labarin zuciya, masu iya magana suka ce a tambayi fuska. Nasan kin dade da gane manufata a kanki, but yana da kyau kiji daga bakina. Da farko sunana......" Nan ya bata takaitaccen tarihinsa da matakin da yake a yanzu na aiki, ya kara da tun ranar da idona ya sauka a kanki, zuciyata ta kamu da so da kaunarki, Wanda ni kaina ban san adadin son da nake miki ba. Tun daga lokacin na rasa walwala, da natsuwa, har sai idona yayi tozali da naki, koda bazan ji ko kalma daya daga bakin kiba. Ina fatan ki bani dama na shigo cikin rayuwarki, na tabbata ba zakiyi dana saniba, aure nake fatan ya kasance a tsakaninmu nan da dan lokaci kadan, in sha Allah. " Shiru yayi yana kallonta da kokarin gano yqnayin da take ciki. Wasa take da yatsunta, a hankali ta dago ta kalli gefensa, tare da sauke ajiyar zuciya. Wani murmushi ne ya subuce mata, saboda idea daya fado mata a rai. Ta dan kalleshi kadan yanda ya kafeta da tsayayyun idonsa yasa tai saurin dauke nata idon. Dadine ya cika suraj ganin Murmushinta Wanda ya bayyanar da jerarrun kyawawan hakoranta, masu dauke da wushirya. Yana ganin Wanda murmushi ke musu kyau, amma bai taba ganin wadda mirmushi ya mata kyau irin hubby ba. Cikin muryarta mai dadin sauraro, kamar ana busa sarewa ta ce. " na gode da kaunarka gareni. But ina baka hakuri, don abinda kake so bazaka samu ba." Kallonta yake cike da so da kauna. Ko kadan kalmarta nata girgizashi ba, don ya dade da sanin hakan, ko yadda ta ki saurarensa yasan zai sha fama da ita. " ko zaki iya gayamin dalili?" Sai da taja numfashi sannan ta amsa shi " ba wannan a tsarin rayuwata. Sannan kai kanka kasan abinda kazo dashi ba mai yiwuwa bane, so kayi hakuri." Shafa kansa yayi yana Kallonta. Murmushi yayi " ko zan san dalili.? Kallon gefen ido ta masa, cike da jin haushi don duk ta kosa ta shiga gida, jinta take kamar akan kaya. Amma ta lura wannan mutumin ya wuce inda ta ke zato a naci. So bari ta masa gwari gwari. " na taba aure, Allah yama mijina rasuwa." Wani kishi ne ya mamaye zuciyarsa, amma yanzu ba lokacin nuna kishi bane, duk da ya dade da sanin hakan. " I known. "Ya fada a hankali tare da karawa da " Allah yaji kansa yasa aljanna ta zama makomarsa." " amen ya Allah. Na gode." Ta fada, tare da jin zuciyarta na karyewa. " shine mutun na farko da zuciyata ta aminta dashi, ina fatan ya zama na karshe, so na yanke maganar sake aure a rayuwata, har zuwa nawa lokacin. Ina fatan yadda muka rayu a nan duniya, mu rayu a aljannatul firdaus in sha Allah. " Kallonta yake yi, ya tabbatar iya gaskiyarta ta fada, don idanunta har sun kada sun canza launi. Ajiyar zuciya ya yi. " ita rayuwa da kika ganta ba mu muke tsarawa kanmu yadda muke son ta tafi ba, huwacewa ce ta ubangiji. Ni nayi imani Allah ya kawoni rayuwarki ne don in maye miki gurbin abinda kika rasa. Don in nayi laakari da tawa rayuwar, wata uku baya duk Wanda zai gayamin zan tsinci kaina a matsananciyar soyaytar wata, tabbas zan ce karyane. Amma ta shi daya Allah ya sanya sonki da kaunarki a raina. Wanda har nake ganin in baki  rayuwata bazata yiyuba. Ina rokonki da ki bani dama, ko ban zama 100% at least  kya samu 80%. " Shirune ya biyo baya, kowa da abinda yake sakawa. " 1 baka taba aure ba, ni nayi for 4 good year's. 2 your billionaire only son, I'm no bodys daughter. You're educated, I'm just ordinary secondary school woman. I'm barrier women also." Ta fada tana kallonsa " so please live me along. Kaje ka nemi dai dai kai." Murmushi yayi " duk abubuwan da kika lissafo ba Wanda ban Sani ba. I known everything daya kamata na Sani a kanki, so please give me a chance, that all I asks for. " " sorry. Kamar yadda na gaya maka ne, ba aure a rayuwata. So please ka gyaleni kawai." Shiru yayi for sometime yana nazarinta da kalamanta.  " OK zan baki lokaci kiyi shawara, sannan kiyi tunani." Kallon sa tayi kafin ta galla masa harara. " ni kam me yasa baka da ganewa ne? Bana bukatar wani lokaci, ko tunani. This is my decision." Murmushi yayi " Allah ya huci zuciyarki, I understand  know. Ki bani phone number dinki to, ko gaisawa mu dinga yi." Karamin tsaki taja ciki ciki. " bani da phone. " Dariya ce ta kufce masa, yadda take wani shan magani. Phones din dake hannunsa I phone 10, ya zare sim din ya mika mata. Kallonsa tayi, ta kalli phone din, ba tare da ta nuna ko alamar karba ba. Ta dan tabe baki " bana bukatar ta ne, Shiyasa ban rike ba, bawai don bazan iya mallakanta bane." Murmushi yayi " na sani, nima ai bance bazaki iya mallanta bane. Amma bazan iya barin nan ba, ba tare da na Samar da wata hanyar da zan dinga jin ko muryarki ba ne. So please ki karba, yanzu zan dauko miki sim card a mota." " kabar kayanka, don bani da ingress akan rike waya." " kin yadda in dawo next week?" Kallon data masa ne ya sa shi sakin dariya. " I'm sorry na cika naci ko?" Ta shi tayi ta nufi cikin gida " don't come hare again. " ta shige ciki Murya yadan daga yadda zata jiyosa " sai nazo next week. Thanks for the time u give me. " ya juya yana murmushi ya fice. " yarinya naki wasane yanzu muka fara." Ya fada yana tada motar.                ******************** Tun isowar suraj a idon Hashim, har tafiyarsa. Yana daga benen gidansu yana hango wurin da suraj yayi parking, yaga lokacin da yabi hubby ciki. Zuciyarsa ta fara zafi, ya rasa sukuni, don haka ya fito ya nufo gidan. Amma abinda ya kara rikitashi ganin shi zaune da hubby a farfajiyar gidan. Da sauri ya juya.Wani nauyi ya ji kirjinsa ya masa. Sam idonsa ya rufe har baya iya ganin gabansa. Karo sukaci da abokinsa muh'd shima mazaunin unguwarne. "Aa doctor daga ina haka? I hope lafiya, na ganka a hargitse. Ajiyar zuciya yayi, yana Jan numfashi. "I'm in trouble friend" Kallonsa muh'd ya yi na dan lokaci, yana nazarinsa fuskarsa dauke da murmushi. " ko dai zargin da nake ya tabbata. " " na me fah" Hashim ya tambaya " you're in love with habiba, right?. " Kallon muh'd Hashim yayi, kafin yayi murmushin " yes friend. How do u known? " " tun da naga kana sintiri a garin nan, nasan akwai bayani ai." Ya fada yana dariya. Fitowar siraj, yasa duk hankalinsu ya koma kansa. Kasan cewar suna kusa da inda yayi parking ya sa shi yi musu sallama tare da mika musu hannu. Cikin mutunci muh'd ya mika masa, kafin ya juya ga hashim da ke dan basarwa, haka dai ya daure ya mika masa hannu. Zuciyarsa na zafi, kamar ya mangareshi. " suraj  kangiwa right.?" Muh'd ya fada still da murmushi akan fuskarsa. shima murmushin ya masa " right " kara mika masa hannu Muhd yayi. " nice to meet u, I'm Muhammad mustafa, that my friend doctor Hashim Adam. "  " nice to meet u too." Ya fada yana murmushi tare da musu sallama, don ya kagu ya bar wurin, ganin irin kallon da Wanda aka kira da doctor Hashim yake binsa dashi. Bayan bacewarsa ne, muh'd ya kalli Hashim " lallai kam kana cikin matsala abokina. Suraj kangiwa da kansa?." Cike da jin haushi, Hashim ya ce " saboda iskanci kuma ka zauna kana washe masa baki. Naso in mangare ka, daga kai har shi din." Dariya muh'd yayi. " I'm sorry, so nake na tabbatar da cewa shidin ne." "To yanzu da ka tabbatar sai me?" " let go and find the place to discuss the issue."               ******************* Gwaggo sai faman washe baki take " har ya tafi?" Haushine ya cika hubby, so ko kulata bata yi ba ta fara cire hijab dinta. " ke kam anyi sokuwa, kayi bako ko ruwa baki bashiba har ya tafi? Wannan ai ba hali mai kyau bane, rowa." " ke meya hana ki dauki ruwan ki kai masa tunda kin damu da yasha?." Ta fada cikin jin haushi " ai sai in kai masa, ina laifin mai son naka?" Gwaggo ta fada cikin son tura haushi " sai ki sa himma ai." " a cikinta nake kin sani, bako bai taba sa kafarsa a gidan nan ba, sai ya sha yaci na tabbatar bashi da damuwa in dai ta cikin sane." Shiru hubby ta mata, don tasan in har ta tanka to sun dinga kenan, ita kuwa bata da lokacin wannab. She have so many things in her plates. " ki kira mommynki, ta kira tana maganar zuwa co gurandin din su junaid ko me? Ban gane zancen ba." " graduation, aka ce." Hubby ta fada tana murmushi. " koma dai menene. Nayi kokari ai, tunda ba yaren qurani bane." " kin yi kam Hajiya gwaggo. " Murmushi su kayi gaba daya. " bikin gama karatunsu junaid ne, za ayi next week. Tun jiya jafar ya fara min maganar. Mommy ta ce zanbi daddy da jabir muje,." Washe baki gwaggo tayi " masha Allah, yanzu har su junaid an kammala karatu? Rayuwa kenan." " abin ba wuya ai." Hubby ta fada " haka ne kam, kamar yau sukazo min sallama shida balarabena. Kinga har an gama?" Kiran sallar magriba ne, ya katse musu zancen. Kowacce ta yi alwala suka nufi daki don gabatar da sallah.               ******************** Zaune suke gaba daya a farfajiyar gidan, dadduma ce mai kyau da laushi shimfide. Sai kayan abinci, gaba dayansu a trey daya suke cin abincin gwanin shaawa. Wannan yana daya daga cikin abinda ke sa hubby son kasan cewa da kakan nin nata. Don in kaga yadda suke gudanar da rayuwarsu abin shaawa, baka taba cewa sun kwashe irin Wannan shekaru a tare, kullun a cikin tarai rayar juna da nuna kulawa suke ga junansu. Bayan sun kammala, hubby ta tattara wurin, kafin ta dawo kusa da Alhaji Kawu ta zauna. Cike da shagwabar data saba masa " jibi zan tafi Kaduna, zamuje graduation din junaid." Murmushi Alhaji Kawu yayi. " babanki ya min bayani dazu. Allah ya kaimu, ya dawo daku lafiya. " amen" suka fada a tare. Alhaji Kawu ne ya gyara zamansa. " dama ina son muyi magana, dazu su Hashim sun sameni da magana a kanki. Sai dai na shaida musu Wannan tsakanin ke da shine, don haka an jima zai zo. In kin aminta dashi mu namu addua ne kawai. Don yanzu ke kike da yancin zabawa kanki miji ba muba." Baki hubby ta tura " gaskiya ni ban sonshi, da kawai ka bashi hakuri, ban son damuwa, yazo ya ishi mutun da surutan banza." " aa Habiba ai baa haka. In ma bakya son sa ki bishi a hankali, a rabu lafiya, kin dai san tsakaninmu?" Haba gwaggo ta rike" oh ni haihuwar Fulani. Hashimun ne mai surutan banza? Ko dai da na dazu zaa yi ne?" Da sauri hubby ta kalleta " Allah ya kiyaye. Ya takurawa rayuwata ne, shi yasa kawai na saurareshi don ya fita hanyata." Nan ta kwashe labari Kaf ta basu. " kangiwa, kangiwan da na sani?" Alhaji Kawu ya tambaya cikin mamaki " shi " ta bashi amsa a takaice Kada kai yayi. Gwaggo ta amshe da " mai jirgin saman da muka tafi hajji shekarar data wuce?" Kai Alhaji Kawu ya kada mata " shifa " Haba gwaggo ta rike, tana kallon hubby " iko sai Allah. Banda abinshi ai kwarya tabi kwarya KO, ina mai sunana ina dan kangiwa? Murmushi Alhaji Kawu yayi " shi aure ai nufin Allah ne, in Allah yayi matarsa ce ba abun da yake gagararre a wurin Allah. Fatana Allah ya zaba mata miji na gari. " "Amin dai" gwaggo ta fada Sallamar da akayi ne, ya sa su maida hankali ga mai shigowar. Saif ne, kanin Hashim. Bayan ya gaishesu ya shaida musu Hashim ne ke son ganin Habiba. " kamar wani bako, kace ya shigo." Gwaggo ta fada fita saif yayi don ya Isar da sakon da aka aike shi. " tashi ki sa muku kujera daga can." Gwaggo ta fada tana nuna mata gaban part din Alhaji Kawu, Wanda daga inda suke suna iya hango su, sai dai bazakaji mai ake fada ba, in ba daga murya nutun yayi ba, saboda yar tazarar dake tsakani. Ruwa da juice gwaggo ta daura a wani karamin trey da cups. " oya dauka ki kai masa." Bata rai hubby tayi, dama a cike take tam. Tabe baki gwaggo tayi " in mun ajiyeki gidan me zaki mana? Jikaki ki ke son muyi, musha? Ki shiga hankalinki dani wallahi." Gwaggo ta fada tana aikawa da hubby harara Zun bura baki tayi, tare da figar trey din tayi gaba. " kyaji dashi kuma" Alhaji Kawu murmushi kawai yake yana kallonsu. Sai da ya karasa ya gaishe dasu gwaggo, sannan ya dawo ya zauna, kujerarshi nesa kadan data hubby. Murmushi ya sake mata. Dauke kanta tayi tana kallon gefe. Gyara zama yayi, tare da gyaran murya. " ba sai na gabatar da kai na ba, already kin san ko ni wanene, daga ina na fito. Abu daya ne baki sani ba, ko in ce kin runtse idonki, shine irin sonki, da kaunarki da nake yi. Hakika zuciyata ta kamu da kaunarki. Fatana ki bani dama, don wallahi ba wasa ya dawo ni ba, in kin amince wata daya yayi yawa, don ni a shirye nake." Shiru sukayi na wani lokaci, ganin bata da alamar tanka masa yasa ya kara karkace murya. " shirunki na min nuni da amin cewarki." Ai bai karasa ba hubby ta tareshi " aa. Maganar gaskiya, kayi hakuri, ba aure a rayuwata." Murmushi yayi " ta ya zaki fadi haka? Bayan dukan mu nan aure ya samar damu?" Numfashi taja tare da dan Kallonsa, yanda ya kafeta da ido, yasa ta daukar da nata kasa. " na san da haka. Ni dai rokonka nake da kayi hakuri, in Karin auren kakeso ga yanmata nan birgik a gari. Na tabbata ko nan cikin unguwar bazaka rasa wadda zaku dai daita ba." Dariya yayi mai sauti " Habiba kenan,!! Na san dasu din, amma na tsallake zuwa gareki. Don ke kadai zuciyata ta zaba cikin dunbin matan nan, da ke kuma take son kulla alaka ta har abadan. In kuma nine ban miki ba ki fito kai tsaye ki gaya min. Maganar aure ta wuce wasa, duk kanmu nan ba yara bane, mun mallaki hankalin kanmu." Duk yadda take jin haushinsa, bazata iya bude baki ta ce bata son shi ba. Duk da ko kadan har yau din nan bata kallon ko wanne da namiji da wani kallo na daban. Ta riga ta sawa zuciyarta bata ba wata alaka ta soyayya ko makamancinta tsakaninta da ko wanne da namiji, no matter how Hansom's there are. Ganin tayi shiru, ya tabbata bazai samu wani gamsashshen amsa daga gareta ba. Duk da yana matukar son jin raayinta a kansa. " shi kenan, tunda kin ki cewa komai, zan baki time kiyi shawara,. " Ledar dake gefenshi ya mika mata. Kallonsa tayi, ta kalli ledar. Ganin bata da alamar karba " kyauta ce, tsakanin Yaya da kanwansa. So please don't say no." Ya fada cikin muryar lallashi. Karba tayi, tare da masa godiya. Mikewa yayi ya mata sallama. Ya tafi cike da Karin sonta da kaunarta. Ta hada kujerun ta maida su mazauninsu, ta juya da nufin komawa wurin su Alhaji Kawu da har lokacin suna wurin suna hira. Sunanta da taji an kirane yasa ta juyo. Ganin mai kiran yasa ta fadada faraarta. " babana daga ina haka?" Murmushi ya sake mata, tare da jin Gina da katangar dake kusa dashi, yana kada car keys din dake hannunsa. " tunda baa nemana ai dole ki ce daga ina." Dariya tayi " ni na isa, jiya muke maganarka da dija, Ashe kana tafe." Dadine ya kamashi, ya kara fadada murmushinsa. " really?" " of course. Ta ina zamu manta da hero." Dariya yayi " kun kyauta ai." Lú" yaushe a gari?" " jiya na iso, after ishaa. Mun sameku lafiya?. " lafiya kalau, ya aiki? " "Alhamdulillah." Ya fada yana gyara tsayuwarsa. " mu karasa man, ka tsaya daga nan." " ba matsala zan karasa ai mu gaisa dasu gwaggo. But kafin nan akwai maganar data kawoni." Kallonshi tayi tana murmushi ba tare data kawo komai a ranta ba. " I'm all Eyer's " " me ya kawo doctor wurinki?" " wane irin tambaya ke nan?" " just want to known. " " ba abunda ya shafeka bane." Ta fada tana tsareshi da ido " ni ko ya shafa." " as in how?" " because he want to take what is actually my." Kallonsa tayi cikin son Karin bayani. Murmushi yayi " nasan bai wuce zuwa yayi ya shaida miki yana sonki ba. Sai dai baku da ce ba. Daya ma bai iya controlling dinta ba balle ya kara. Koda yake is not my place to say so. But shine your eyes. Ni nafi da cewa dake, ni nasan zafinki, nasan kuma na fishi sonki da bukatarki. So please give me a chance, to show u how much I love u." "Dakata babana, me kake nufi ne. I don't understand u?" " please Habiba married me, I'm so much in love with u." Kallonsa ta tsaya yi, kafin ta kwashe da dariya. " u are joking right? " Serious face yayi. " I'm serious, Habiba, ba wasa cikin abinda nake fada. Tun ba yau ba nake son gaya miki. Ban samu chance ba.but amma believe me." Rike baki tayi, tana kallonsa. " lallai ma, to kai koda auren zanyi ai baka ciki. In aureka in ce na auri wah?" Karka manta tare mukayi wasan kuruciya, Duka duka 3 months ka bani a haife. Ta ya ma zuciyarka zata baka irin Wannan lamari?" Marai raice fuska yayi, yana hada hannunsa guri guda. " Wannan duk ba hujja ba CE, koda kin girmeni ai ba aibu bane don na aureki, kin ga nayi koyi da manzo S.A.W, balle ma na baki har wata uku. Don't say no please. " " dallal manta da wannan maganar, in aure kake so ni da kaina zan zabo maka, in kai ka kasa. Ni yanzu ba aure bane a gabana. So muje Ku gaisa dasu gwaggo. Tayi gaba tana masa dariya Binta yayi cikin sanyin jiki, dama abinda yake gudu kenan. Don ya dade da sanin hubby da son girma. Da wuya ta amsheshi cikin sauki, but zai ci gaba da trying don gaskiya yana sonta sosai, ba zai iya hakura ba, sai inda karfinsa ya kare. Sun dan taba hira dasu Alhaji Kawu, kafin ya masu sallama, har get hubby ta rakosa. Sannan ta juya cikin gida.               ******************** Munir mustafa da ga Alhaji mustafa, kani ne ga muh'd, Makota ga Alhaji Kawu.   Munir yaro ne dan shekara 25, ya kammala karatunsa na degree a alkalam, yanzu haka a can yake koyarwa, sannan yana karatun degree dinsa na biyu. Yarone mai kokari sosai, ajinsu daya da hubby a primary shi ke zuwa musu na daya a class. Da farko basa shiri da hubby, kullun suka hadu sai tasan abin da tayi ta sashi kuka. Saboda Alhaji Kawu na yawan mata fada, da misali da Munir Ta wurin kokari da maida hankali a karatu. Shirunsu ya faro ne, lokacin still tana aji biyu, shi kuma aji biyar, saboda repeating da ake mata. Su kayi wani danbe ta kusa cire masa yatsa da cizo. Alhaji Kawu ya musu sulhu ya nuna mata ko don sunan mahaifinta da munir keda shi, ya kamata ta raga masa.  Fada sosai ya mata. Wannan shine musabbabin da take kiransa babana. Daga nan kuma suka fara shiri sosai, koda ya tafi secondary school dake bording ne, in yayi hutu bini bini yana gidansu. Har barinta kankiya. Ta fannin halitta kam Sam bashi da makusa, yana da dan kyansa dai dai kwargwado, da cikar halitta, bashi da tsawo sosai, average person.                 **************** Alwala tayi kamar yadda ta saba kafin ta kwanta. Tayi azkar din kwanciya bacci kafin ta janyo ledar da Hashim ya bata. Waya ce, kirar Samsung galaxy x 10 silver da mtn sim card. Tsaki tayi ta maida wayar cikin gwalinta ta ajiye a gefe. " ko an ce masa ina fatarar waya ne oho? Na rasa me yasa mutane basu da ganewa." Ta kara Jan tsaki. Tunani ne ya rufeta mu samma yadda zata rabu da wa'annan sarakan nacin. Don ta lura baza su barta ta dadin rai ba.  Tunanin King dinta ne ya dawo mata, da moment dinsu a tare, hawaye ne ya fara zarya a kumatunta. Tunawa tayi da alkawarin data dauka. Suratul ikhlas ta karanta 7× ta roka masa gafara da rahamar Allah. A haka barci yayi gaba da ita.                  *************** Thursday jirginsu ya daga, Daga Abuja zuwa Cyprus............ Tofa!!!!Suraj, Hashim ko babanmu Munir? [03/03, 12:03] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 11       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Junaid da ashir ne suka je tarbarsu a airport. Direct masaukin baki suka wuce, na Don Harris, Wanda ke kusa da apartment din su hayder. Hubby, umma sulaim, Asiya, dakinsu daya. Sai Hajiya da Hajiya zuwaira, mahaifiyar Hafiz omer. Suma daki daya. Alhaji Munir nashi special suite. Abdul fattah da jabir kam apartment dinsu hayder suka sauka. Wanka kowacce ta fara gabatarwa, kafin suka fito tafkeken falon da ke tsakiyar dakunan don ba ciki hakkinsa. Nan suka samu duk kan samarin sun hadu. Nan fa aka fara gaisawa, da tambayar su hubby gajiyar hanya. Congratulation suka musu na kammala karatu. Ummu sulaim ta nufi dinning table din da aka Jere shi da dishes na abinci masu matukar kyau, da daukar ido. Bubbudewa ta fara, tana kallon abinda ke ciki. " wowhh!!!! Gaakiya kun burge, irin wannan delicious haka?" Ta fada tana Jan pleat signal tama hubby dake zaune a kusa da junaid suna hirar zuminci. Tashi tayi ta nufi in da sulaim ta ke. " na dauka zamu jira su Hajiya su fito, tukunna. Kin San cin abinci a tare nada dadi." Hubby ta fada tana kallon pleat din Harararta ummu sulaim tayi " tab har yaushe ina ganin abinci a gabana, zan wani tsaya jira? Kin ko San kalan yunwar da nakeji?" " maida wukar na manta, bakya juriyar yunwa." Ummu sulaim ta kalli Asiya dake zaune. " Uhtee ." Ajiyar zuciya Asiya taja tare da mikewa. Cikin sanyin jiki ta nufi wurin su hubby. Murmushi hubby ta mata, tare da dafa kafadarta " take it easy sis," ita ma murmushin tayi cikin jin kunya. Ummu sulaim ta tabe baki " aiki ya ganki," Fitowar su Hajiya ya sa falon kara armashi, kowa ya dibi abinda zaici, suna ci, suna hira sama sama. Cike da farin ciki. Kowa ka kalla fuskar nan a sake. Hayder na zaune kusa da Hajiya, kamar zai koma ciki, sai shagwaba yake kamar wani karamin yaro. Abincin ma pleat daya suke ci. Bayan sun ci, sun sha, ko wanne ya koma dakinsu don su  kwanta  huta gajiya. Suka bar samarin a falon, suna shan hirar yaushe gamo. " take this one." Ummu sulaim ta fada, tana mikawa hubby wani hadadden Dinki, atamfa mai combination din boil. Atamfar baki da touch din lemon green, voil din lemon green dinkin free half bubu da stret skirt. " wow amma kayan nan sunyi kyau sosai. Thanks " murmushi ummu sulaim tayi. " meye na wani godiya, yiwa kai Ne. Kin manta har yau bikici alayina na nysc ba." " gashi naci ai yanzu." Shiryawa sukayi don tafiya wurin convocations. Ummu sulaim ma da asiya same kaya sukasa sai dai colours din is different. Lemon green Vail mai touch din white da stone masu haske hubby ta sa. Sai black shoe and bag. Na kamfanin cucchi new design. " kuda ya kamata kuyi shigar larabawa, kuka je kuka zunbulo kaya haka kamar masu zuwa didan biki." Hajiya zuwaira ta fada tana murmushi tare da gyara zaman after dress dinta mai matukar kyau da tsada. " mommy kowa yabar gida, gida ya barshi, na tabbata yawanci arebian dress zasu sa. Kinga mu munyi namu different don bama son mu saje dasu. We want something different than others, shiyasa." Rike baki Hajiya tayi da itama take sanye da nata alkabbar mai matukar kyau. " lallai fa!! Kishin kasa Abu ne mai kyau, ana ganinka aga alamar in da ka fito. Nigerian lady's kunyi kyau kam ba karya. Kowa ya ganku yaga cikakkun yan arewacin Nigeria. Masha Allah." " a takaice dai Hajiya yaran nan na nufin mu bamu da kishin kasa fa kenan?" Dariya sukayi gaba daya, ganin yadda take bin dressing dinta da kallo. " Allah ba abunda muke nufi ba kenan. " Asiya ta fada tana rungume mahaifiyar tata tana dariya. Ta kara da cewa " don baki ga yadda kukayi kyau bane, wannan su daddy's suka ganku, kasa ganeku, zasuyi." Ummu sulaim tayi dariya " kina ga su Hajiya harda alkyabba kamar mai kai ziyara emir's place. " Duka hubby ta kaiwa ummu sulaim. " Ku barsu su wala, don shigarsu tafi tamu daukar ido, anya baza mu canza ba?" " yauwa yata, gaya musu dai. Ba maganar canzawa Nigerian lady's kumu tafi kawai kar kusa mu makara." Hajiya ta fada tana daukar hand bag dinta.                        ****************************************** A farfajiyan school din sukayi parking din land cruiser da suka zo da ita. Already wurin ya fara cika, a wurin da aka kayata shi da decoration. Suka nufa,. Gefen perent. sun samu har Alhaji Munir da Alhaji Jamil sun iso, sai mahaifin Hafiz Alhaji ayuba da yayansa Ahmad da suma suka samu isowa. Sai yayan alim da suke tare da jabir. Amir ma yasamu zuwa taya abokan nasa murnan gamawa. Zamansu ba dadewa, bayan sun gama gaishe gaishe. Aka fara gudanar da programs din. Bayan jawabin director na school din, da masu fada aji na kasar da suka samu halatta, aka Dan gudanar da entertainment, sannan aka fara rabon aword da gifts.  Cikin su shidan nan ba Wanda bai karbi aword ba. Don hayder aword uku ya samu, da gifts 2. Sai Hafiz omer daya samu aword 2, sauran 1. Abun yama iyayensu dadi, musamman kyakyawan yabon da yaran suka samu, daga bakin malaman har da students. Bayan an gama raba aword da gifts, sai entertainment, sannan aka nufi hall din da aka kawatashi don cin abinci. Tablets Ne da kowanne aka zagayeshi da kujeru sunsha decoration na cotton White da satin Amy green sai flowers da vases masu matukar kyau da daukar ido. Su Kansu plets da spoons din abin kallo Ne. Nan take aka  fara serving din jamaa, bayan kowa ya samu wuri ya zauna, ga kida mai taushi da sanyaya rai na tashi, cikin low voice.  already drinks kam waiters nata zagayawa dashi, ga maiso ya karba duk irin Wanda kake so. Ban dawanda ke kan tables din. Ga fresh fruit kala kala. Anyi hotuna videos kowa, da iyayensa da friends dinsa. Sai teacher's da baa barsu a baya ba suma. Asiya ta kalli ummu sulaim dake gefenta ta rada mata a kunne " waccan da take faman shishshigewa Yaya hayder wacece?" Kallonsu ummu sulaim tayi don itama tun dazu take son tambaya, bata samu damar da zata tambaya ba. Rada mata tayi " I don't known, ina ga school mate din su ce." " ki kalli fa irin kallon da take masa? Allah ba wani class mate. There is something " " jealousy beby. I don't thing so. Amma koma menene we go figure it out, ammafa ta hadu." Harara Asiya ta zuba mata. "Ina haduwa a nan? Abu a bushe." Dariya ummu sulaim tayi. Dan da nan Asiya ta toshe mata baki, tana kallon table din. Ganin duk hankalinsu baya Kansu, ta saki ajiyar zuciya. Hubby kam gaba daya hankalinta baya Kansu. Tunanin yusuf da kewarsa ne taji nan take ya rufeta. Musamman  yadda yaci burin akan graduation din nan. Amma Allah ya kaddara badashi zaa yi ba. A hankali take diban chocolate cake din zuwa bakinta. Dariyar da taji ummu sulaim tayi yasa ta dago ta kallesu tare da kada kanta ta ci gaba da cin cake dinta. Don tasan maganar bata wuce ta hayder har tausayin asiya ta ke, ganin yadda ta kwallafa rai ga yaron da bai ma San tanayiba. " da alama sis kinyi babban catch, " ummu sulaim ta fada tana kallon hubby tana dariya. Tsaki hubby tayi, ta ci gaba da cin cake dinta. Asiya ta kalli hubby tana murmushi " gaskiya kam, tunda muka zauna a wurin nan idon bawan Allah nan a kanki." Hubby dai tana jinsu tayi musu banza. Don gaba daya haushi ma suka bata. Tun da suka shigo school din ta ankare da yadda ya sa mata ido,. Daya daga cikin yanmatan da suke zaune table daya dasu hubby ce, ta kalli yar uwarta. " I can believed what my aye's so." Kallonta yar uwar tayi. Tare da bin inda yar uwar ke kallo tana nuna mata. " suraj kangiwa." Dayar ta fada under her breath Gaban hubby ne ya buga dam. Su ummu sulaim kam jin sunan suma suka bi wurin da kallo. Yana zaune a daya daga cikin kujerun table dinsu Alhaji Munir, suna magana. Ummu sulaim ce ta tambaya " dama shine, kangiwan da naji ana magana?" Dayar cikin farin ciki, da tun zamansu  wurin, ba Wanda zai dauka tana faraa haka. " Ally son of M. Saad kangiwa, CEO of kangiwa group of companies. " ta fada tana kada ido. " what bring him here." Dayar ta tambaya still idonta a kansa. " me be yazo wurin daddy ne." " I don't thing so, Sis." Hamida da Sadiya (sady) yayan abokin Alhaji Jamil ne, Alhaji salis,. Shima yazo graduation din yaron sa , Imran tare dasu sady Wanda suke yayye ga Imran, da mahaifiyarsu Hajiya fatee. Hamida da sady yan Hutu ne na karshe, don a England ma sukayi nasu degree din. Akwai jin kai da yanga ga son nuna su yayan wani ne. Shi yasa Sam tasu bata zo daya da hubby ba, don ta dade da saninsu, age mates ne, kuma duk shaanin da ake na family din Oregon suna zuwa, in dai suna kasar. " is he your boyfriend? " Asiya ta tambayi sady Rike baki sady tayi tana yamutsa baki. " no." " fadi gaskiya sady? Don naga tun tuni kin kasa dauke idonki a kansa." Kallon ummu sulaim sady tayi. Tare da yin murmushi. " he is my crush, amma yafi karfina." " haba babbar yarinya irinki har akwai wani da namiji da zaifi karfinki? Kin ganki kuwa?" Dadine ya kama sady don tana son a yabata ko a kodata. Ta kalli ummu sulaim " thanks for compliment. Amma da gaske yafi karfina. In kinga manyan bebs dake dying a kan guy din nan zakiyi mamaki." " ya hadu kam ba karya." Asiya ta fada tana kara kallonsa. Hamida ta ce " ko kema kin kyasa ne?" Ido Asiya ta zaro " ni ? Aa ko daya, nima ina da nawa crush din." Duka dariya suka sa. Banda hubby dake zaune kamar bata wurin. Hafiz omer da amir ne suka iso wurin. " hello sisters? How fah?" Hafiz ya fada yana murmushi, tare da Jan empty sit din daya rage ya zauna. " Anty hubby ba matsala ko?" Murmushi ta masa tare da kada kai. Amir ya ce " muje mu dan kashe pictures da zaman da kuke a nan." Asiya ce tai saurin mikewa " gaskiya kam, na gaji da zama wuri daya. Ina son in ga yanayin school din, don gaskiya ta burgeni ba kadan ba. Dana Sani nima nan nayi applying." Tashi sukayi, hubby ce ta gayawa su Hajiya zasu Dan zaga cikin school din. Sannan suka fito. A garden dake cike da dalibai da yanuwa anata kashe hoto, da videos. Masu hira nayi. A nan suka samu su hayder. Kallon ummu sulaim Asiya tayi, tana nuna mata hayder da wannan yarinyar zaune suna magana kasa kasa. Sai annuri ke fita daga fuskar yarinyar da gani tana jin dadin yanayin. " wa cece waccan yarinyar? Tun  dazu nake ganinsu a tare." Ummu sulaim ta tambayi Hafiz omer Murmushi yayi " Nasrin  Nada Khan ke nan, da alama da ita zaayi." Kirjin Asiya ne yayi wani irin dokawa, cikin tashin hankali take kallon su amir " kamar Yaya?" Da kallo suka bita. Murmushi ta kakalo  tana kokarin saita natsuwarta. Hannunta ummu sulaim ta kamo cikin nata. " ita ce fist yarinyar da hayder ya saurara, har ya bata lokacinsa a kanta. Kinga ko ai ta ciri tuta. Na tabbata tana da matsayi ko Yaya ne a ransa. Yarinyar bata da laifi, tana kuma balain son shi." Amir ya fada yana murmushi " he is lucky guy." Hafiz omer ya fada Da ido ummu sulaim ta ma Asiya alamar tayi cooling down. Hubby kam ta dade da isa wurinsu junaid. Cikin girma mawa suka kara gaisheta. Nan alim ya fara daukarsu pictures. A hankali hayder da nasrin suka karaso in da su hubby suke. Sallama ya musu. Cikin murmushinsa na miskilanci ya kalli ummu sulaim., sannan ya kalli nasrin dake binsu hubby da kallo. Jikinta yayi sanyi, ganin irin kallon fire da Asiya ke aiko mata, tun da suka nufo wurin. " meet my sisters. Ummu sulaim, hamida, Sadiya sady and Asiya. " hannu ta mika musu suka gaisa tare da rungume juna. Duk da zuciyar Asiya na zafi haka ta daure. Kallonsa ya kai kan hubby yana murmushin gefen baki " meet our Anty hubby. " hannu ta mika mata tare da rungume ta. Gaisuwa ta mata cike da nuna tausayawa. " thanks. " hubby ta fada don ji tayi kamar mutuwar ta dawo mata sabo a lokacin. " she is nasrin Nada khan. My friend " hayder ya fada yana kallonsu. Still da murmushi a fuskarsa. Murmushi sukayi. " friend manya, kuji wani sabon salo." Hafiz ya fada yana murmushi Harararsa hayder yayi. Nan suka ci gaba da daukar pictures dinsu. " can I joined u." Gaba daya suka juyo ganin mai maganar Sanye yake da blue Jean's, sai T-shirt White da lines din blue mai dogon hannu. Kafar sa sanye da White canvas mai kyau, sai agogon silver mai matukar daukar ido. Kanshi yasha gyara, ga farin glass a idonsa, Wanda ya karawa fuskarsa kyau da kwarjini. Ga wani kamshi mai dadi dake tashi a jikinsa. Suraj m saad kangiwa. Murmushi su Hafiz omer suka mayar masa " why not." Alim ya fada yana mika masa hannu. Kirjin hubby banda bugawa ba abun da yake yi. Ita kam taga ta kanta. Kin yadda su hada ido tayi, tana ji sunata gaishe shi. Shima cike da sakin fuska yake amsa musu, tare da musu congratulations. " very sorry, I came un invited. It's you're sister fault she didn't Tell me. But I can Miss our brothers gradations." Suraj ya fada yana murmushi idonsa kafe a kan hubby da ta sunkuyar da kanta, ta gagara dagowa. Don haushi da nauyin kannen nata. Gaba daya kallonsu ya koma kan hubby cike da mamaki............. Jin yadda gaba daya ido a kanta, ba tare da ta kalli kowa ba ta juya ta nufi hall din dasu Hajiya suke. Murmushi suraj yayi " 2min" ya fada tare da bin bayanta. Hafiz ne ya kalli alim, da jikinsa ya gama sanyi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da zama a kujerar dake kusa dashi. Ummu sulaim da su hamida sai kallon kallo ake tsakaninsu. "Habiba" jin ya kira sunanta, ta tabbatar biyota yayi kenan. Cikin fushi ta juyo tana jifanshi da wani riki taccen kallo. " don Allah wai maina tsare maka ne a rayuwa, kake son takuramin? Na Riga na gayama iya gaskiyata why can't u understand?" Murmushi ya sake mata, tare da kashe mata ido daya. " I never understand you're language Habiba. The ally think I known is that I'm  crazy about u. So duk yadda kike tunanin I will live u. Is not gonna happen. Ta Yaya zaki tafi da zuciyata sannan kiyi tsammanin zan iya barmiki ita?" Kallon sa tayi for the fist time ta tsaya ta kalleshi da kyau, for some second. Ta kauda kanta gefe tana jin jina naci irin na wannan bawan Allah. Maganar shi ce ta dawo da ita daga tunanin data tafi. " nasan kin San so? kin kuma San yadda bawa yakeji a duk lokacin da ya tsinci kansa a cikinsa. Ina rokonki don Allah ki bani dama mu fahimci juna. Wallahi ba yaudara tsakanina dake, face alkhairi. Har ga Allah ina sonki tsakani da Allah. Son da nake jin tamkar in baki ba zan iya ci gaba da rayuwa mai dadi ba, ke ce farin cikina. " For the fist time taji ya Dan bata tausayi. Tabbas da baya sonta bazai ajiye dunbin ayyukansa ya tako tun daga Nigeria zuwa Cyprus kawai don ya ganta ba. Duk da bata da tabbas din ita ya biyo ko tashi ce ta kawoshi. Ajiyar zuciya ta yi kafin ta dago ta kalleshi, still idonsa na kanta yana sake mata murmushi mai kayatarwa. Ganin Dan sassauci a kan fuskarta yasa shi jin wani kwarin gwuiwa da farin ciki, ya lullube zuciyarsa. " baki tambayeni ya akayi nazo nan ba." Tabe baki tayi, tana kallon gefe. Murmushi yayi, don hakan ba karamin burgeshi yayi ba." naje kankiya on Thursday, kamar yadda na miki alkawarin dawowa a satin. a ka cemin  ranar kika tafi Kaduna, sorry nayi magana da Alhaji kawu ba tare da izininki ba. I'm happy yadda suka karbeni shida takwararki." Da sauri ta dago tana kallon sa. Murmushi yayi tare da daga mata gira daya. Ajiyar zuciya ta yi, don ta yadda da gaske yake nashi abun. " tun jiya naso in taho, ayyuka sun sha karfina, amma fa still kina raina. Yau gari na wayewa ko mai ban jiraba. Burina in ga rabin raina, duk da nasan bazaayi farin ciki da ganin nawa ba." Ganin bata da niyyar tankashi, shikuma zuwa lokacin muryarta kawai yake son ji, mai dadin sauraro da tsumashi. Kallonta yayi yaga yadda take wasa da yatsunta da sukasha bakin lalle. Tabbas akwai sassauci a tare da ita, alamar ta fara sakkowa, hakan yafi komai yi masa dadi. Hubby kam yaki take da zuciyarta data kasu kashi uku. Daya na bata shawarar ta bashi dama ta gani, daya na mata shawarar ta tatamai rashin mutunci kawai yadda gobe ko mai sunanta ya gani bazai tsaya a kusa ba. Dayar na gargadinta data watsar da komai ta koma makaranta. Kamar zabin da Mommy hauwa ta bata, zuwantan nan. Muryarsa taji ta daki dodon kunnenta " yawan tunani bashi da kyau ga lafiya, ya kamata ki rage." Ajiyar zuciya ta yi ta kalleshi " naji zan baka chance, amma banyi maka alkawarin komai ba." Kallonta yayi for some time yana nazarinta. Murmushi yayi. " ban gane baki min alkawarin komai ba?" " just friends. " ta fada tana kallonsa. Dariya yayi wadda ta kara masa kyau " na yadda friends, but ki Sani  zata iya riki dewa." Kallon sa tayi " kamar Yaya riki dewa? Shafa kansa yayi yana murmushin gefen baki " forget it. Yanzu dai ni dake are friends right? " Kai ta daga masa. " good." ya fada yana murmushi "Muje nima a kashe pictures din dani ko?" Harararsa ta yi. Marai raice fiska yayi " don't forget  I'm you're friend, Kinga ba laifi ki dauki photo da friend dinki." " karka manta akwai ban banci da friend mace, da friend namiji. So stay in your limit. " " ban Sani ba, amma ya kamata mu zauna ki jeromin differences din don in kiyaye." Ganin tayi gaba, yasa shi binta. A tare suka jero zuwa wurinsu ummu sulaim da lokacin sun babbaje a kan grass carpet dake malale a garden din suna kwasar hira. Gefen ummu sulaim ta nema ta zauna. Shikuma jabir ne ya tashi ya mishi alamar ya zauna. Sannan suka gaisa, don dazu basa wurin shida Abdul Karim, Ahmad. Gaba daya hubby a tsarge take ganin irin kallon da kowa ke binta tashi. Ummu sulaim ce ta rada mata " kin kyauta" dagowa tayi ta kalleta da ido ta mata alamar " sorry I have no idea. " su sady kam haushin hubby ne ya kara cikata. Sai Kallonta take tana son ganin abinda tafi sauran mata da tayi mata zarra a rayuwa. Duk iya Kallonta ta kasa gano makusarta. Illa kawai ta ce, bata da wayewa a nata fassarar. Don da wuya kaga hubby cikin kaya masu nuna siffar mutun. Dressing dinta is decent. Shikam ya saki jikinsa da samarin sai hirarsu suke kwasa. Duk wani movement na hubby a kan idonsa. Sai 2oclock sannan taro ya watse kowa ya fara kama hanyar masaukinsa, masu tafiya a ranar sun kama hanyarsu. Su hubby sun so dawowa ranar but ba dama saboda walima da sheikh dawood al- maisani ya shiryawa su hayder na haddar alqurani da yayi a wurin sa, shida wasu matasa su biyar sai mata 2. Suraj ne ya kalli samarin da suka rakoshi har mota, bayan su hubby sun wuce masauki. " Ku mai ya hanaku joining din hayder?" Murmushi sukayi junaid na shafa kai. " nida shine dama mukayi joining banfi sati ba na gudu." Dariya su Hafiz suka sa tunowa da drama din. " as how" suraj ya tambaya still da murmushi a kan fuskarsa. Don yaran sun matukar burgeshi. " kana ji ko? Fist day da mukaje tun a fatiha an min gyaran tajweed yafi goma, a fatiha kawai, duk iya dagewata ranar ban samu wuce fatiha ba. Shima hayder yasha gyara. Duk kanmu a fatiha ranar muka kare. The next 3day hayder ya wuce ikhlas da kyar ni kuma ina nan a fatiha. In takaita maka 5 days nayi a fatiha, sannan na tafi ikhlas, lokacin hayder yana suratul nas. 1days ina ikhlas ranar na dauka zan shiga sabuwar sura amma Dan malaminka haka yayita dawo dani. In takaita ma gani nayi bazan iya ba kwana 7 a fatiha da ikhlas ina kuma mun fara shiga manyan sura. Malamin Dan gani kashenin tajweed ne, ko ja daya ka manta sai ka faro daga farko. Ai tun daga nan ban sake komawa ba." Dariya sosai suke masa. Hayder na daga gefe yana danna waya. " daka daure ai, da komai ya wuce." Suraj ya fada yana dariya " ina wane mutun. Sauka biyu fa mukayi kafin mu taho nan. Waye besan karatu irin na ibn kayyim memorial college ba.? Munje gasa yafi a kirga, muna winning.Amma dan malaminka kamar ya samu fresh meat." " don't insults my sheikh. " hayder ya fada yana hararar junaid. Murmushi junaid yayi, " sorry na manta kana wurin ai.?" Card hayder ya mikawa suraj 5oclck tare da masa sallama ya shige mota, don a gajiye yake, Allah Allah yake su je ya huta kafin su wuce gidan sheikh. Sallama sukawa suraj tare da godiya. Don wasu manyan gifts ne da akayi rapping dinsu, guda six ya basu, kowa da sunanshi a jiki.                  ******************* "Yanzu kiyi irin wannan catch din amma ki kasa sanarmin gaskiya banji dadi ba ko kadan"  ummu sulaim ta fada tana shafa lotion,. Tsaki hubby tayi " me kike son in gaya miki." " sorry na manta, na Yaya Yusuf ma saida magana tayi karfi mukaji. Amma dai kin San mu ba haka muke miki ba. Its un fair. Yanzu da wani mugun halinshi su sady suke fada da ya zakiji." Kafada ta makale tare da tabe baki " so what. Ke baki San kalan nacin mutumin nan bane, ba wai son shi nake ba, balle in damu don an fadi mugun halinsa." Nan ta kwashe labari Kaf ta fada musu. Baki suka rike suna mamaki. " kun masifar dacewa, sai kin ganku lokacin da kuka jero tare, don har picture na kashe muku baku Sani ba." Asiya ta fada yana murmushi tare da nunawa ummu sulaim pic din. " its true. Gaskiya yana sonki sosai, kar ki bari ya kufce miki hubby, zamanin yanzu ka samu Wanda zai soka haka yana da wuya. You're very luky, ji yadda Yaya Yusuf ya soki, yanzu kuma ga suraj. Ki gode Allah don ba kowa ke sanun hakan ba." Asiya ce ta kara da " gaskiya kam." Banza dasu hubby tayi ta ci gaba da shiryawarta. Don har lokacin bata jin natsuwa da lamarin ta da suraj. Hajiya ce ta shigo. Wuri ta samu ta zauna tana kallon hubby. " Ummi wane labari nake ji ne?" Kallon Hajiya hubby tayi cikin rashin fahimta. ummu sulaim tayi murmushi tana kallon hubby " na biki da muka kusa sha mana" Tsaki hubby tayi ta harareta. Asiya ce ta korowa Hajiya bayani dalla dalla kamar yadda hubby ta gaya musu. Ajiyar zuciya Hajiya tayi " ai ni hankalina bai kwanta bane, amma ba komai zamu ci gaba da addua. Allah ya zaba miki mafi alkhairi. Ki ci gaba da addua." " in sha Allah." Ta fada kanta a kasa. Ajiyar zuciya tayi bayan Hajiya ta fita. Dariya su Asiya suka sa baki daya suna tsokanarta.                 ****"**************  Hayder " Agric chiken" hubby ta fada tana murmushi. Kallon ta ummu sulaim dake kusa da ita tayi, ta kalli su junaid da suka sha jallabiyyoyi da nadi irin na larabawa. Murmushi tayi " Allah girma ba wuya, ni kaina bana gajiya da kallon yaran nan ina mamakin girmansu. Musamman hayder da junaid. Har gara junaid shi bashi da jiki, amma dubi hayder wa ze ce 19 going to 20 years.              ******************** Walima ta kayatar sosai. Hajiya tasha kukan farin ciki, hatta su Alhaji Jamil dasu hubby sai da sukai hawayen dadi. Jin yadda haidar ke kwararo karatun alkurani cikin kiraar kalun. Haka su Hafiz Bakajin komai sai kabbara, duk inda aka ja masa in ya amshe, sai yakai inda zaa ja wata, haka tambayoyi kan tajweed da tafsir, Abin masha Allah. Ya samu kyaututtuka da dama, bayan an kammala akaci aka sha sannan kowa ya kama gabansa. Rungume shi Hajiya tayi tana kuka, shima hawayen yake fitarwa na dadi. Burin hajiyarsa ke nan, ya samu yalwataccen ilmin addini. Kullun taga yara a wurin gasar alkurani takance ina ma wata ran inga hayder dina haka. Yana secondary school ansha zabansa ya wakilci school dinsu, hakan ya kara sashi son zurfafa ilmin addini,  alkawari ne ya daukarwa kansa duk wuya duk runtsi, yadda ya dage neman ilmin zamani, haka zai dage a kan ilmin addini koma, fiye. Shiyasa duk tsaurin sheikh ya daure ya cige batare da kosawaba don ya cimma burinsa. Kuma alhamdulillah ya samu ya taka mataki na farko da yake fata a rayuwarsa. Albarka kam yau hayder ya sha a wurin su Alhaji Jamil. Nan take ya tura ma yan uwansa da mahaifinsu. Alhaji Jamal na masallaci sallar magrib yaji shigowar sako wayarsa. Bayan ya kammala tasbihi da azkhar ya fito da wayar don ya duba. Gaba daya kiraar hayder ta fara tashi a cikin wayar, Wanda ya jawo hankalin liman, da sauran mamu da suka rage a masallacin. Hawayen dadi Alhaji Jamal ya fara ya dago yana kallon liman da ya masa zuru da ido. Wayar ya fara nuna masa, cikin rawar murya " Aliyu, Aliyu hayder. " liman da mamu suka zagaye Alhaji Jamal suna kallon hayder dake zubo kiraa cikin kwarewa da dadin murya. " Allahu Akbar suka fara fada. Har bidion ya kare. Alhaji Jamal na ta sharar kwalla. Murna suka dinga tayashi tare da fatan Allah yasa albarka a karatun, yasa ya zama mai anfani ga alummar musulmi. Nan liman ya fara kwararo falalar mahaddacin qurani da darajarsa a wurin Allah. Gaba daya imani ya kara cika zukatansu. Hakika a cikin zuriarka a samu mahaddacin qurani ko da guda daya ne, ba karamin falala bace ga wannan zuri'a. Haka ta faru da Alhaji babba da Hajiya Aisha. Suna tare a babban falo dasu Ahmad da iyalansa sun kawo musu ziyara. Kamar Alhaji babba bazai daga wayarba ganin sunan Jamil yasa ya duba. Duk Kansu sunyi farin ciki matuka. Hajiya Aisha kam har da kukanta ita ma.                  **************** Zaune suke a babban falon masaukinsu. Gifts din su hayder ne baje a falon, sai manyan jakun kuna da su hubby ke arranging din gift's din a ciki, bayan sun ciresu a kwalayensu. Saboda in sunce zasu tafi dasu haka zasuyi accupying  space da yawa. Wani hadadden box hubby ta daga, ya matukar burgeta yadda akayi rapping dinsa. Da ita kanta rapping sheet din. " wow!!!" Asiya ta fada tana karba daga hannun hubby. Sunan da Asiya ta gani an rubuta yasa jikinta daukar rawa, cike da son ganin abinda ke cikin rapper ta fara yagawa cikin sauri, da kaguwa ido ta zaro...   Gaba daya su hubby dake Kallonta cike da mamakin abunda ya fusata ta lokaci daya su kabi box din da kallo. Zaro wani hadadden box din turare da aka rubuta SHUMUKH ( The sprite of Dubai )da manyan baki sa a Kansan an rubuta ( Deserving The Highest)  Budewa tayi ta zaro kwalbar yar madai dai ciya mai kyau. Ga wani kamshin dadi dake tashi tun bata fesa ba  Tsaki hubby tayi, tana juya turaren a hannunta. " yanzu duk girman abun nan, abunda ke ciki kenan?" " wannan mayyar yarinyar ce ta bashi, nasrin take ko wace?" Asiya ta fada cikin jin haushi, tana tabe baki. Dariya suka mata " nama dauka wani Abu ne, yadda naga kin haukace lokaci daya, kina son ganin abunda ke ciki." Ummu sulaim ta fada still tana dariya. Hafiz ne ya ankare da abunda suke yi. Kwalbar ya amsa daga hannun ummu sulaim yana kallo. Kallon su junaid yayi " guys look hare." Gaba daya suka juyo suna kallonsa " oh my world. " junaid ya taso da sauri ya amshi turaren yana juyashi a hannunsa cike da mamaki. Rapper din da box suka dauka suka nufi wurin sauran guys din. " amma gaskiya yarinyar nan tana ji dakai. Kasan nawa kudin turaren nan?" Hafiz omer ya fada yana kallon hayder da duk abinda suke ko a jikinsa. Laptop dinsa ma yake daddannawa. Tabe baki yayi ya kalli amir da turaren ke hannunsa yana fesawa ya ci gaba da aikinsa. " nawa? Don gaskiya akwai kamshi ba karya ko nawa ne yaci kudinsa. Jabir ya karba yana kallo " 3,571 USD." " What?" Suka fada a tare. Dariya Hafiz omer yayi " da gaske nake yi. Ranar ba na baku labarin turaren da huzaifa ya siyo a Dubai ba? Har nake cewa zan yi oder don yamin dadi sosai. To shine wannan. Last month akayi launch dinsa. It's take them  3 years to create it. That why there called it deserving the highest. " " gaskiya yaci sunansa. Amma ban iya cire makudan kudi haka in sai just one perfume!!" Amir ya fada yana karewa turaren kallo Junaid yayi murmushi " tasan mutumin nata kan son kamshi, turaren komai tsadarsa zai saya in har ya masa. Hakan na nuna ta gama karantar mutumin nata. Don in kanason burge haider bashi turare ammafa designer mai dan banzan kamshi." Harararsa hayder yayi " what do you mean?" " nasan kaji dadin wannan kyautar. Kuma dama burinta kenan kaji dadi. Right? " " of course. " hayder ya fada yana kallon junaid dake masa murmushi Hafiz ne ya dan Sosa kai " da har ina cewa na samu turare?" " in kana ciki, mu buga oder kawai. Tunda bamu da wadda zata bamu." Hafiz omer ya fada Asiya dake gefe ta cika tayi fam, ganin yadda suketa koda turaren. Ta kallesu tana tabe baki " banda abinku meye abun burgewa a wannan turaren da har za a shekara uku wurin kirkirarsa? Ni wannan ko kyauta ban so balle insa kudina in siya." Gaba daya kallonta suke cike da mamakin maganarta. Alim ne yayi dariya don sun dade da harbo jirginta. " haba kanwarmu kema kinsan kin fada ne kawai, amma ba Wanda zai ji kamshin turaren nan ko ya ganshi, ya ce bai burge shiba." Junaid shima murmushi yayi " anya kanwarmu? Kodai kishi kike?" Baki ta tura " Allah ya kiyaye in tsaya kishi da wannan slender din." Gaba daya dariya suka kwashe dashi Hafiz omer ne ya harareta, kauda kanta tayi. Ido hudu sukayi da hayder dake aika mata da wani irin kallo mai kamada gargadi gargadi, harara harara. Zuciyarta ne ta fara rawa, don tunda suka zo banda gaisuwa ba abun da ya hadasu, ko kallon arziki bata samu ba. Da sauri ta dauke idonta don bazata jure kallon fire da yake aiko mata ba. Kwafa yayi kadan ya ci gaba da abinda yake yi. Jabir ne ya canza akalar hirar. Nanfa aka koma musun kwallo, su hubby suka ci gaba da parking din gift din. Asiya kam jikinta yayi sanyi, don haka tashi tayi ta nufi room din su Hajiya. Abdul fatta ne ya shigo, kusa da hayder yama kansa mazauni. " wash!!!! " sannu suka fara masa, tare da gaisuwa. Hubby ya kalla " suraj na jiranki a waje, nayi nayi ya shigo yaki,."  " OK" ta fada tana ci gaba da abin da takeyi. " na manta munada uwa a bakin murhu, kuka Samu wahala. Allah yasa muna shiga airport muka hadu da suraj. Yanzu haka tare da maaikatan company dinsu muke, zasuyi packaging din sauran kayan." Hafiz omer ne ya cabe da " haka nefa!!." Junaid ne ya fita ya shigo dasu. " amma dai kin San kin ajiye mutun a waje ko?" Harararta hubby tayi " na ajiyeshi ko ya ajiye kansa? Ko gayyatoshi nayi?" " ba kyau wulakanci, ki tashi kije, kar ya gaji da jira." " so what? " hubby ta fada Tashi ummu sulaim tayi, " muje in rakaki to." Ganin hankulan samarin ya fara kaiwa Kansu, duk da a hankali suke maganar yadda baza suji ba, yasa hubby mikewa. " bari in tambayi Hajiya tukunna.?" Baki ummu sulaim ta rike " to fah!!!" Ido hubby ta zaro mata tare da daga gira daya. " what? Ko kina tunanin zan iya fita ne ba tare da sanin taba." " no wai gani nayi nan ne, ba wani dadewa zakiyi ba. Its almost late." Ummu sulaim ta fada tana duba agogo. " dozen matter." Bayan ta gayawa Hajiya ta basu izni tare da jaddada mata karta Dade. Zaman gyalenta ta gyara, Suka fito. Suna zuwa dai dai corridor din wurin ummu sulaim ta juya abinta. Ko kafin hubby ta bude baki, har ta shige ciki da dan gudunta. Baki hubby ta sake tana kallonta, kafin tayi kwafa. " zamu hadu ne." Juyawa tayi tana scanning din wurin. Motar  Kangiwa air ways. Ta fara hangowa, daga gefe ta hangoshi tsaye jikin wata farar mota kirar Mitsubishi A hankali cikin takunta mai daukar ido, da natsuwa ta nufi inda yake. Tun fitowarta idonsa a kanta, ya kasa dauke idonsa. Sai yau ya kara kare mata kallo sosai. A cikin hasken fitulun da suka kawata wurin, ga kamshin furanni. Sanye take da material purple, yellow, blue, brawn. Sai mayafi purple Wanda har kana iya hango kitsonta back and front, daya kara fito da kyan fuskarta sosai. This is the first time da ya ganta ba zunbulelen hijab. Duk da yanzu dinma rigar bubu ce, wadatacciya har kasa, don ko takalminta bai iya gani, Sai dan tsininsa da yake hangowa. Dressing din ya matukar burgeshi, don ya bashi damar ganin daya daga cikin abunda yake fatan matarsa ta sunna ta kasance tana dashi. Gashinta da yake iya hango tudunsa ta bayan gyalen yayi kamar a cuci. Kanta a kasa, amma tana jin yadda idonsa yake a kanta. Gyara gyaleta tayi, ta kara jawoshi da kyau, yadda zai rufe gashinta.  Sallama ta masa, cike da nutsuwa. Murmushi ya sake mata " waalaikumus salam, barka da fitowa gimbiyar mata." " ya gajiyarka." Ta fada a hankali, kamar bata so. " alhamdulillah, mu kam ai mun saba, so ba wata gajiya, wannan Sai Ku mata." Shiru tayi tana wasa da yatsunta. She is uncomfortable, don ko yan matancinta bata yi wani tsayawa da samari ba. Zata iya cewa Yusuf ne kawai. Shidin ma ba ko yaushe ba. Don zata iya kirga zancen da suka yi alone, after all she known him. Wannan kuwa is total stranger. Tsayuwarsa ya gyara fuskarsa cike da annuri " nazo miki sallama ne, zan wuce tomorrow morning. Yaushe zaki wuce kankiya in kin koma?" Shiru tayi tana dan nazari " one week my be." " OK. In that case ina ga zanzo kafin ki koma, don nima yanzu haka Italy zan wuce. Ina sa ran dawowa nan da 3days." Kallonshi tayi kafin ta kauda idonta gefe. " OK. Allah ya kiyaye hanya." Yaji dadi sosai, daya kasa boyuwa a kan fuskarsa. "Amen na gode,." Shiru sukayi na dan lokaci. Ita ta kauda shirun. " zan shiga ciki." " OK. Sai nazo din." Harta juya tadan dawo " mun gode sosai da hidima." Ta juya ba tare da taji mai zai ce ba. Yana tsaye har ta shige ciki,. Murmushi yayi yana shafa sumar kansa. Allah yayi halitta a nan. Komai nata mai kyau. Ya fada a ransa. Lokacin ne maaikatan nasu ke kokarin saka manyan jakun kunan a bayan van din. Su hayder ne suka karasa wurinshi don su kara masa godiya.               ******************** Hajiya da ummu sulaim jirgin Lebanon suka hau zuwa Oregon. Don dubo ummu kulsum dake fama da laulayin ciki, shiya hanata zuwa graduation duk da suna kusa. So time din flight din su da safe 7:30. Su Hajiya Balkisu, Asiya, Hafiz omer, kuma jirgin Lego's. 1:15. Alhaji munir, jabir, junaid, haider, alim, da amir. Direct jirgin Kaduna 4:00. Alhaji Jamil da ashir sunbi jirgin abuja tun last night. Wuraren tarihi su junaid suka kai hubby don tunda su ummu sulaim suka tafi, taji garin ya fita a ranta gaba daya. Golden lake sukayi branching. In da kowa yasai abinda yake so na ciye ciye suka nemi wuri suka zauna suna ci suna hira, duk labarin school ne, da friends dinsu. Hayder kam gefe daya ya samu ya zauna yana kallon jamaar dake shige da fice. Yau shigar ash and black yayi yayi kyau sosai.  Hubby ta kalleshi tana tabe baki. " a karatun harda miskilanci ake kara koyar daku ko?" Kallon hayder suke yi da ke waya hankali kwance. Junaid yayi murmushi " ina kika taba jin an koyawa mutun miskilanci? Dama dai miskilin ne." " naga abin ya kara shaharane, na Sani ko harda shi ya koya." Dariya sukayi Amir yace "gaskiyarki Anty miskilanci ya karu, ni kaina shaida ne." Murya hubby ta dan daga yadda zai jiyota " agric chicken. " ya jita sarai ya mata banza, bai ma nuna ko alamar yasan dashi take ba. " agric chicken " ta kara daga murya. Haushine ya kama hayder musamman jin dariyarsu amir. Don ya tsani sunan. " arage dai a sami ta gobe, kowa na hira da dan uwansa, don mugun hali ka koma gefe." Ko kallon ta bai yi ba. Ya ci gaba da danna wayarsa. " Allah ya shiryi mai bakin hali." " amin" su junaid suka fada suna dariya. " Matar hayder ta banu, wallahi har tausayinta nake." Alim ya fada Tabe baki hubby ta yi " ita taga zata iya ai." " haka ne kam, tunda yanzu ma yan matan duk da sanin halin nasa suke kara manne masa." Alim ya fada Dariya junaid yayi " kasan mata da yawa na son muskilayen maza." " in ji wah?" Hubby ta fada tana tsareshi da ido. " kema fa kina ciki, naga Yaya Yusuf ma ai miskilin ne,." Junaid ya fada Harararsa tayi " in kana maganarka karka kuskira ka tsomani ciki." " afuwan." " in kun gama shirmen Ku tashi mu tafi." Hayder ya fada yana yin gaba Agogo junaid ya duba past 3. Da sauri suka mike suka nufi mota. Don isa airport don sunyi dama da Alhaji Munir da jabir zasu hadu a can. " waye yake shirmen? Allah ka shiga hankalinka, don kaga kayi tsawon kafa, bashi zai baka lasisin yimin rashin kunya ba." Juyowa yayi ya kalleta, ya juya ya ci gaba da tafiyarsa. " mai hali bai fasa halinsa." Ya fada a ransa Haushine ya kara kama hubby. Ta yi tsaki                ******************* Kallon sit din tayi, ta kalleshi. " dawo nan! Ban son sit din kusa da window" kallonta yayi ya kalli sit din, Ya kauda kanshi. " agric chicken!! Da kaifa nake magana, ka koma can sit din." Air piece ya sa a kinnensa tare da kunna kiraa ya kyara belt dinsa da zamansa da kyau. Haushi ya kuma hubby, ji take kamar ta kifa masa mari, ta rasa yadda akayi number din sit din su yazo a hargitse. su junaid ma kowa sit dinsa da ban dana juna, ita da hayder ne kawai sit dinsu ya zo daya. Tsaki tayi, ta gyara yadda zata wuce ciki, bata son window sit. Koda za su mata burking ta gayawa jabir amma see how she end of. Kafarsa ta take da karfinta kafin ta wuce. Ya jita sarai, don yaji zafi sosai, amma ko motsi be yi ba, balle tasa ran zai tankata. Wayarsa ce tayi kara, a yan gace ya duba, tare da answering din call din. Hatta hubby dake kusa bata iya jin me yake fada, saboda yadda yake maganar, cikin Jan aji da natsuwa. Sake baki hubby tayi tana kallon ikon Allah. Kallon ta yayi, tare da mika mata wayar. Wayar tabi da kallo, kafin ta amsa. Nasrin ce ke son mata sallama, don basu hadu ba a wurin walima, saboda tana jin kunyar Hajiya so bata xoba. Jininsu ya hadu, da hubby duk da ba wani dadewa sukayi suna magana ba. She respect her, don tasan matsayin Yusuf a wurin hayder. Haka tana jin labarin hubby sosai a bakin su Hafiz. Gani daya ta mata taji ta kwanta mata a rai. Hira sosai suka yi, har sai da akayi annausing  cewa jirgi zai tashi, kowa ya kashe wayarsa. Sannan sukayi sallama ta mika masa phone din. " she is nice girl. In baka shawara?" Ta fada tana kafeshi da ido. Kallonta yayi cikin muryarsa mai kama da anmasa dole " ina jinki?" Tabe baki ta yi tana dan rainin sense a gasan ranta. " mai zai hana ka nemi Asiya. She is the perfect choice for u. Kun matukar dacewa." Kallonta yake, girarshi ya dan Sosa ganin takai karshe. " thanks for the advice, keep it to your self, I don't need it." Harararsa tayi " wai kai me yasa baa abin arziki da kai ne?" Tsaki ta yi ta gyara zamanta. Tunawa tayi da assignment dinta na islamiyy da ta taho dashi don tayi, amma bata samu time ba. So yanzu da zaman banza bari ta dauko tayi, ko ta rage takaicin hayder. Tausayin Asiya take. Yarinyar na matukar sonshi..........   [03/03, 12:07] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 12       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Tattaunawa akan daya daga cikin wannan mau'du'in. Muhimmancin ilmin da namiji, da ya'mace, sai muhimmancin auratayya tsakanin maban banta kabilu. Da harshen larabci Tsaki hubby ta yi ta jerowa daya bayan daya. Ba wai larabcin bane bata iya ba, yanda zata jera point din. Sannan tana da matsala har yanzu wurin jera wasula. "Alhamdulillah" ta fada lokacin da aka fara raba abinci, don tana bukatar sake nazari, duk point din data dade da tanada sun watse. Hankalinta kwance ta dibi girki yadda ya kamata, ta kora da coca cola mai sanyi. Hayder ta kalla da ke shan tea. Ta tabe baki Book dinta ta dauko ta ci gaba. Takaici ne ya ishi hayder, yadda hubby ta cika masa kunne da tsakinta Littafin ya kalla don ganin me take rubutawa. Dariya ce ta kusa kamashi. " zero head, aikin yan kananan yara, amma ta kasa ta ishi mutane da tsaki." Ya fada a ransa Kallonta yayi yadda ta takar kare kamar gaske. Biron ya fige a hannunta, da sauri ta bishi da kallo, book din ya janyo ba tare daya ce mata komai ba, ya daura kan abin cin abinci, da zaka janyo mai kama da table ya fara rubutu. " ban son rashin mutunci, taya zaka wani fige Abu a hannuna, kana shigamin hanci da kudun dune fah." Ko kulata bai yiba, kallon rubutun take mai matukar kyau, a tsare. Kamar ingin ke rubutawa. " komai sai an masa yanga, rubutun ma ji yadda yake, kamar baya son yi." Sai da ya gama, ya ajiyemata a gabanta da biron. " please leat me sleep in peace. " ya fada yana tsareta da ido. " da yake na rike maka ido ba?" Kai ya kada tare da lumshe idanuwansa. Taji dadi sosai, yanda ya tsara mata bayanan dalla dallah. In gan taccen Arabic. A Jakarta ta tura book din " shishshigi kawai, ko an gaya maka na kasa ne?" Ya jita sarai, ya shareta. Don yasan albarkacin Yusuf take ci. Da ba dan haka ba da ko kusa bazata kara wargin shiga harkarsa ba. Yana respecting dinta ne saboda sanin matsayinta a zuciyar yayan nasa, da irin kyakykyawan zaman da sukayi, da duk lokacin da zaka zauna da Yusuf Ku dan dade sai kasan yadda ya damu da ita, haka ita ma. ta wani gefen kuma yana tausaya mata saboda rashin da tayi, Wanda maye gurbinsa zai mata wuya a rayuwa. Shi duk da jinin da suka hada da ita, kwata kwata baya jinta a ransa. Har mantawa ma yake da ita. ******************* Dawowarsu da one week aka shirya wasu hayder hadaden get together and babaque. A harabar gidan Alhaji Jamal. Abun ya kayatar sosai, yan uwa da abokan arziki duk sun hallara. Sir omer, da iyalansa, Jamil ma da nasa iyalan, Alhaji babba, shima da friends dinsa. Gidan ba masaka tsinke, kamar ana wani gagarumin biki. Mommy Hauwa da friend dinta Hajiya salwa suna zaune a falon mommy Hauwa, yan aikinta na faman hada gifts din da already anyi packaging dinsu a manyan buhu, suna fita dasu mota. Hubby ce ta shigo kamar an korota. Kallo daya mommy Hauwa ta mata taji gabanta ya fadi. Batayi tsammanin samun mommy a gida ba. So ganinsu a zaune yasa tayi kokarin saita kanta, tare da share hawayen da suka wanke mata fuska. " sannunku da gida." Ta fada tana wucewa dakinta da sauri, gudu gudu. Dukkansu da kallo suka bita. Mommy Hauwa ta ja ajiyar zuciya ganin ta shige. Hajiya salwa ta kalli mommy Hauwa dake kokarin yafa mayafinta. Bayan sammani ya fita da buhun karshe. " kina nufin tafiya zakiyi ba tare da kin je kinga halin da yarinyar nan take cikiba? Wai ke me yasa kike haka ne? Kina ganin ta shigo da irin wannan damuwar, ai kya je kiji abinda ya fusatata haka? In baki jata a jikinki ba kin san matsalarta,wa kike son ya miki wannan aikin. Bayan keda kike uwarta kina nuna ko in kula kan lamurranta. Shiyasa ta zabi zama da gwaggo sama da ke da kika haifeta." Murmushi mommy Hauwa tayi, mai kama da yake " bazaki gane lamarin Ummi ba ne." " ta ya zaki gane kuwa? Tunda baki jata a jikinki ba." Hajiya salwa ta fada tana nufan dakin hubby cikin jin haushin kawartata. Tana jikin Woodruff kayanta take fito dasu, ga akwatunana har biyu manya ta bude tana jefa kayan a ciki. Hawayene wani na bin wani a fuskarta. Sai Jan hanci take. Tausayinta ne ya kama Hajiya salwa. Hannunta ta kamo suka nufi bakin gadon hubby. Kuka mai karfi hubby ta fashe dashi ta daura kanta a cinyar Hajiya salwa. Hajiya salwa bata ce mata komai ba, sai shafa kanta da takeyi alamar lallashi. Ta bata damar tayi kukan ko taji saukin damuwarta. Mommy Hauwa ce ta leko, don taji shirun yayi yawa, gashi ana can ana jiranta. Kallonta Hajiya salwa ta yi " ki tafi kawai, zan isoki" juyawa mommy Hauwa tayi ba tare data ce komai ba. Amma ita kadai tasan damuwar da zuciyarta ke ciki. Mawuyacin Abu ne kaga kukan hubby, don ita sha yanzu ne, maganin yanzu. Kana gaya mata cuta ta gayama mutuwa, shike nan ya wuce a wurinta. Amma muddin kaga tana ma Abu kuka to ba karamin Abu aka mata ba. Sai da tayi kukanta mai isarta. Sannan tayi shiru, tana Jan ajiyar zuciya. " komai yayi zafi maganinsa Allah. Ki daina sama kanki damuwa irin haka, duk da bansan dalilin kukan ba na tabbata ba karamin Abu bane zai saki kukaba." Hajiya salwa ta fada tana mai mata kallon tausayawa. Kanta ta sunkuyar tana wasa da yatsunta. Don duk a kawayen mommy Hauwa tafi jin nauyin ta da ganin girmanta. Don Matar tanada mutunci sosai. Ga sanin ya kamata. " ki gaya min waye ya taba min ke?" Shiru tayi ta kara sunkuyar da kanta. Duk yadda Hajiya salwa ta so hubby ta gaya mata damuwarta amma ta kasa. Saboda nauyinta da takeji. " shi ke nan, ni zan tafi tunda ban kai matsayin da zaki gayamin damuwarki ba." Hannunta hubby ta riko " kiyi hakuri wallahi ba haka bane." " I understand. But waannan kayan fa da kika fara hadawa?" Kallon kayan hubby ta yi sannan ta sunkuyar da kanta " gobe zan koma kankiya." Kada kai tayi, tana jin jina sakaci irin mommy Hauwa. " ita matsala in ta samu ba guje mata ya kamata a yiba, fuskantarta za ayi don a maganceta, saboda guje mata kamar barin baya da kura ne." Ta fada tana mikewa. " na gode sosai, ki gaishe min dasu Faisal." Hubby ta fada cikin girmamawa " zasuji." Ta fada Tate da ficewa a dakin. A harabar gidan sukayi karo da Ummul khair da ummu sulaim suna shigowa. Gaisheta sukayi cikin girmamawa, sannan suka wuce ciki. A gogo hubby ta kalla 9:43 na dare. Tsaki tayi ta tashi ta ci gaba da hada kayanta. Kai tsaye dakin hubby suka nufa. Da sallama suka shigo. Dagowa tayi daga jera kayan da take cikin akwatin ta bisu da kallo. Tare da amsa sallamar." Me zan gani haka?" Ummul khair ta fada tana zama a bakin gadon. Ummu sulaim kam kujerar madubi taja ta zauna tana bin kayan dake wargaje da kallo. " abinda idonki ya gane miki." Hubby ta bata amsa " kar dai maganar waannan sakarkarun ne? yasaki kike son tafiya?" Tabe baki hubby tayi tana ci gaba da ninke kayanta. " ko kadan, lokacin tafiyar tawa ne yayi." " be kamata ki damu kanki ba, kan wannan maganganun shirmen, tun da kin San ba gaskiya bane. Ba komai yake damun munaya ba illah kishi da zugan su Anty samira." Ummu sulaim ta fada cikin takaici Hawaye ne suka fara bin kuncin hubby " ta Yaya bazan damu ba? Kina jin irin sunayen data dinga kirana dasu a cikin jamaa. Tun da nake baa taba min tozarcin da ya bakanta min rai ba irin na yau. In kece ya zakiji?" Kada kai ummu sulaim ta yi, cikin jin zafin abinda akawa yar uwarta. " a kwai ciwo kam, shi yasa na tsaya na basu nawa piece of mind din." " na rasa abin da ya kawo wannan maganar. Naga da safe har gaisawa kukayi da ita lafiyar Allah." Ummul khair ta fada " ki kyale abu, in har aka ce da munafurci a ciki. Anty samira yar uwata ce, amma Sam halayyarta basu min ba. Ta cika kananun magana da son hada wuri. Ina wurin munaya ke bamu labarin Ahmad ya kaiwa hubby su Arafat sun mata wuni. Da irin yadda yaran suketa labarin yadda ta kula dasu har basu so komawa ba. Munaya na ba su Anty samira labarin yadda take jin dadi, da yadda take son hubby saboda tana son yaranta. So na barsu suna ta hirar kin San munaya in kanason ka gama da ita to ki nuna kina son yaranta. Yanzu zaki ga mutunci. So ina ganin bayan na bar wurin ne suka zugeta." " in banda dabbanci tayaya zatayi tunanin ni hubby in rasa Wanda zan so sai Ahmad? Tsakanina da Ahmad mutunci ne, da ganin darajar juna. Duk cikin yan uwan Yusuf ba Wanda yake bibiyar rayuwata sama da shi. Su suna ganin kaman zuwan da yake yi kankiya wani abun ke kaishi. Wanda kuma wallahi ba haka bane. Ko da wasa ban taba ganin wani alama ko kadan sabanin zumunci da mutuncin dake tsakaninmu ba. Shi yasa nima nake mutuntashi nake ganin girmansa." " that's it. Wannan shine yasa suke ganin soyayya kukeyi. Don ni Anty samira ta so ta bugi ruwan cikina don taji wani Abu a bakina. Amma na nuna mata ban taba ji bama, har nake ce mata wannan ai tatsuniyar yara ce, ina hubby ina Yaya Ahmad. " Ummul khair ta fada cike da takaici. " amma dai kin San baki mana adalci ba in har kika ce tafiya zakiyi, bayan kin San biki nan ba wani lokaci aka sa da yawa ba, just 3weeks." Ummu sulaim ta fada tana kallon hubby " kiyi hakuri, gaba daya garin ya fita a raina. Kin San jiya salis har gidan nan yazo, ni na dauka abin arziki ya kawoshi,ba kunya ba tsoron Allah wai sona yake yi. Ido suka zaro a tare " wane salis din? Yaya salis?" Ummul khair ta tambaya harda sassarfar magana. " shifa!!!! Bama shi yafi ban haushi ba irin Engr Sahabi, harda wani shi ya dace ya maye gurbin marigayi. Mu rufawa juna asiri." Dariya su ummu sulaim suka sa. Haushi da takaici ya kara cika hubby. Cikin dariya Ummul khair ta ce " sai kika ce masa me to?" " bar dan iska, an gaya masa kwantai nayi? Ko kwantan nayi nafi karfinsa wallahi. In ba rashin kunya da rashin tunani ba tayaya yana abokin mijina, kawai don ya rasu ya wani zagayo. Sai ma kunji yadda yake wani kashe murya kamar in sanu muciya in ta dukan banza don haushi." Har lokacin su ummu sulaim dariya suke ma hubby. " kin San dama an ce da budurwa da bazawara, kamar kasuwa ce, da mai brush da Mara brush kowa ya gani ya gyasa sai ya lallabo, sai in yaga no go no go sai ya kara mai. So kadan ma kika gani. Shiyasa gara mutun yayi aurensa ya huta. " Ummul khair ta fada Harararta hubby ta yi " dama ke kam gara da aka hada dake, don naga kin fiye son aure da yawa. Ni kam ban shirya ba, ba kuma rana." " ai kuwa yanzu kika fara ganin irinsu Engr masu son rufa miki asiri." Ummu sulaim ta fada tana dariya. " zan kara ganin kafarsa a nan gidan, sai na tata masa rashin mutunci. Yanda gobe ko mai kama dani bazai kuma marmarin tunkara ba." " kar kiyi haka, tunda bakya son sa just find a way da zaku rabu a mutunce, yaci albarkacin Yaya Yusuf kodan mutunci da zumuncin dake tsakaninsu." Ummu sulaim ta fada " ya labarin hot guy?" Kallonta hubby tayi. " waye kuma hot guy? " Harararta Ummul khair ta yi " karki raina min hankali man. Bayan naji labarin komai." Tsaki hubby ta yi "sai ki je ki tambayi Wanda ya baki labarin. Kinfa fara raina ni, kar kiga ansa miki ranar aure ki shiga hankalinki dani." " Allah baki hakuri. Don Allah dan ban labarinsa mana? Yaushe ze zo, na kosa in ganshi" " ban Sani ba." Hubby ta fada Sun dade suna hira, har 11 na dare, sannan sukayi sallama da hubby ta rakosu har jikin mota. Sannan ta koma. Already lokacin an tashi daga get together da babaque din su hayder. Hubby na shirin kwanciya su mommy Hauwa dasu jabir duka dawo. Tana jin hayaniyarsu a falo taki fitowa, adduar bacci tayi ta gyara kwanciyarta. Sai da kowa ya kwanta, sannan mommy Hauwa ta nufi dakin hubby. Da akwatunan hubby ta fara karo. Kafin ta nufi gadon da hubby ke kwance. Bubbuga kafarta tayi, Wanda yasa hubby bude idonta, ganin mommy Hauwa yasa ta tashi ta zauna. Itama zama tayi a bakin gadon tare da kamo hannun hubby cikin nata. Cikin murya mai taushi " me ya faru kika dawo, dazu ba tare da an kammala abin da ya kai ki ba? Rai a bace? Ke da wa?" Ta jero mata tambayoyin a tare. Cikin damuwa ta fara zayyanowa mommy Hauwa yadda sukayi da munaya. Dasu Anty samira. Ajiyar zuciya mommy Hauwa tayi ranta ya baci sosai amma bata nuna ba. " wannan kayan fa?" Ta tambaya tana kallon kayan " gobe zan koma." Kada kai mommy Hauwa tayi " ki cire maganar komawa kankiya a ranki, don babu. Lokaci yayi da zaki tsaya ki zaba ma kanki mafita. Tunda kin nuna baki son karatu, to ki fito da miji mu aurad dake, don bazai yiwu ba karatu ba aure ba. Wannan yaron in har da gaske yake, to ki shaida masa ya fito." " bafa soyayya muke ba, just friend dina ne." Hubby ta fada da saurinta. Kallon ta mommy Hauwa tayi na dan lokaci kafin ta ce " shi kenan dama Hajiya salwa ta dade damun maganar tana son hada ki da Husain, ni na dakatar da ita, saboda sanin halinki, but zan gaya mata ta turoshi Ku dai dai ta. Hankalina dama bai kwanta da wan can yaron ba." Da sauri hubby ta diro daga gadon, " mommy wane Hussain din?" Harararta mommy Hauwa tayi " daya da kika Sani. Ki zama a cikin shiri daga gobe zuwa jibi zaki iya ganinsa a gidan nan. Ki natsu banda rashin hankali, kin dai San yadda muke da Hajiya salwa." Ta fada tana kokarin barin dakin. " don Allah mommy kiyi hakuri, wallahi ni dai bai min ba." Kallonta mommy Hauwa ta tsaya yi kafin ta kada kai ta fita. " innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Meke faruwa da rayuwata ne? Daga wannan sai wannan. Ina ita ina Hussain miskilin mutun number daya hatta ita hanta Hajiya salwa kullun cikin korafin miskilancinsa take, gashi da murdadden hali ya hadu da zamowarsa soja. Tun da suke haduwa dai dai da rana daya bata taba ganin dariyarsa ba, magana ma wannan ko gaishe shi sukayi sai dai ya daga maka kannu kawai. Bata manta hutun data taba zuwa gidansu lokacin tana SS 1 irin dukan da sukaci ita da kanwarsa salma kafin ta rasu. Saboda surutunsu,. Akwai ranar da har tsallen kwado ya sasu. Kwanansu biyu suna jinyar kafafu. Ita kanta Hajiya salwa shakkarsa take yi. Ta kasa barci, saboda damuwa da nema ma kanta mafita. At last ta gama tunanin abinyi. Ajiyar zuciya tayi. Tana Allah Allah gari ya waye taje ta samu daddynta.......... Sunday, tun da sassafe hubby ta tashi. Ta gama saka kayanta a mota. Sannan ta kira malan iro. Don ta shaida masa ya zama cikin shiri by 11 zasu wuce zuwa kankiya. Saboda daddy dinta baya yadda tayi driving zuwa wani gari. Sai 10 sannan mommy ta fito daga side din daddy. Dama hubby ta dade da shiryawa tana jiran tashin daddyn nata. Don tasan weekdays baya tashi da wuri. With full confidence ta nufi part din daddy tare da sallama. A falo ta sameshi yana kallon tashar CNN. Cike da faraa da jin dadi yake kallon tilon yar tasa. " ummina an har tashi?" Murmushi tayi tare da gaisheshi tana zama kasan carpet cike da ladabi. Kallonta yayi yana murmushi " sai inah? Da safen nan?" Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta. " ina son komawa kankiya yau. Kayi hakuri da ban sanar maka da wuriba." Kallonta yake yi yana karantar yanayinta. "  mun riga mun gama magana da Alhaji. Zaki ci gaba da zama damu a nan. Har Allah ya fito miki da miji kiyi aure. So ba maganar komawarki kankiya, u stay with us." Lokaci daya hawaye suka fara bin kuncin hubby. " please daddy kayi hakuri ka barni in tafi, nafi son zama a can don Allah. " Ajiyar zuciya Alhaji Munir yayi. " me muke miki da kike gudun zama damu Ummi?" Kar ta kada cikin muryar kuka ta ce "ba komai, bakumin komai ba." " so kamar yadda na fada ne, ba komawa kankiya. Sannan ki fito da miji cikin masu sonki Wanda hankalinki ya kwanta dashi.  Don so nake a hada dana jafar tunda Allah yasa ya fito da yarinyar da yake so. Kuka ta fashe dashi tana ba daddy hakuri, ita wallahi ba Wanda take so. " shi kenan dama mommynki tamin bayanin dan wurin Hajiya salwa. So in yazo naji yanda kukayi." " wallahi ni ban sonshi, don Allah daddy ka taimakeni ka gayawa mommy karta ce musu yazo." Tausayi hubby ta bashi, ganin yadda take ta risgar kuka, amma ba yadda ya iya dole a matsayinsa na uba ya sauke nauyin da Allah ya dora masa. Ya tuno da maganganun da sukayi da Alhaji kawu. Gyara murya yayi. " shi kenan zan gaya mata, amma bisa sharadi daya." Da sauri hubby ta rarrafo hannunta ta daura kan gwuiwowin Daddy tare da kwantar da kanta. " na yadda da koma wane sharadi ne. Matukar mommy baza ta turo min wannan monster din ba." Ta fada tana Jan hanci saboda kuka. " na baki nan da 2weeks ki fito  da miji, don gaskiya na gaji da ganinki ke ba aure ba, ke ba karatu ba. Sai gararanbar association" Da sauri ta dago cike da firgici da tsoron kalaman daddy. " kaji tausayina daddy don Allah. " ta fada cikin marairaice murya, baki na rawa ga hawaye nabin fuskarta. Tausayi sosai ya kara kama Alhaji Munir. Gyara zama yayi. " Ummi hakan shine soyayyar, kowanne uba yayin da yarsa takai munzali fatansa ya aurad da ita. Don shine mutuncinsa kuma mutuncinta, ballan tana ke da kin taba yin auren, kin San dadinsa da rashin dadinsa. Don wata kaddara ta gitta, baya yuwuwa ki yankewa kanki kin sake wani auren. Hakan na nuni da kina fushi kenan da hukuncin Allah. Bayan sanin kanki ne duk abun da ya samu bawa to kaddararsa kenan, ya kamata ya rungumeta hannu bibbiyu, yayi fatan ta zamo masa alkhairi duniya da kiyama. Wannan shine daya daga cikin alamomin musulmi na kwarai. Yadda da kaddara mai kyau ko akasinta. A yan kananan shekarunki bai yiyuwa mu ajiyeki muna kallo, ba muyi miki adalci ba, bamuyi wa kanmu ba. Don haka ki kwantar da hankalinki, ki natsu cikin masu sonki in akwai Wanda ya kwanta miki, ki shaida masa ya fito, kiyi aurenki, shine cikar kamalarki, in kinyi haka muma kin tsare mana namu mutuncin." Cikin kika " in sha Allah zan yi yadda kuke so." " Allah ya miki albarka, ya baki miji na gari, da Yaya masu albarka wa' anda zasuji kanki kema. In sha Allah bazaki taba dana sanin biyayyar da kikai mana ba. Ina alfahari da zamowarki ya a gareni. Na gode." Rungume mahaofin nata tayi. " na gode daddy da adduarku garemu. Ina alfahari da zamowarki iyaye na gari a garemu." Murmushi mommy Hauwa tayi ta dade tsaye a bakin kofar, amma basu kula da shigowarta ba. " in an gama tattaunawar tsakanin uba da yarsa, sai muje a ba ciki nashi hakkin." Murmushi hubby ta kakalo tare da ficewa daga dakin. Da kallo iyayen suka bita cikin tausayawa. " akwai rikici fa!!! Sai kinayi kina bata baki." Murmushi mommy Hauwa tayi " ummin ce wani lokaci Zuma ce, sai da wuta. Kasan tun sassafe har ta sa kayanta a mota? Gani kawai take data zo ta kallalameka zaka barta ta tafi." Ajiyar zuciya Alhaji Munir yayi " kema da naki laifin ai. Ban son ki kara mata maganar Hussain tunda ta furta bata son sa shike nan." " Allah ya zaba mata miji na gari, amma gaskiya naso wannan hadin. " " mata kenan, kibar yarinya ta zabi wanda ranta keso. Kedai naki ki bita da addua." " ai shi kenan, na farko ma ya akayi, balle na biyu. Allah ya mana jagora." " amin" Alhaji Munir ya fada, a tare suka nufo part din mommy Hauwa don yin break fast kamar yadda suka saba. Already su jafar, jabir, junaid sun halkara saman dinning table suna jiran iyayen nasu. Toilet direct hubby ta wuce ta wanke fuskarta. Sannan ta nufo dinning din.                 ******************* Kwance take saman gadonta, sai sakawa da kwancewa take. Lallai ta yadda da maganar  da hausawa ke cewa mutuwa mai tonon asiri, tabbas haka maganar take, dabadon mutuwa da yanzu tana tare da mosoyinta, wata kilama harda da ko ya. Tunanin yadda zata iya zama da wani mijin ba Yusuf ba take.  "Yanzufa dole in auri wani? Dole yadda Yusuf ya sanni shima haka." Runtse idonta tayi hawaye mai zafi na bin kuncinta. Don ba abun dayafi daga mata hankali irin hada shinfida da wani ba Yusuf ba. To ita yanzu waye zata fitar? Hashim, suraj ko Munir. Kai no!!! Ba dai  Munir ba, yaron da suka taso tare tasan kuruciyarsa yasan nata. After all ya mata yaro da yawa. Hashim kuma gaskiya tana tsoron zama da kishiya, don bata tashi ta ganta a gidansu ba. Balle yadda ake fadin hatsabibancin matarsa, gaskiya bazata sa kanta a shiga uku ba. Suraj yes!!! Zata iya aurensa don ta lura yana matukar sonta, sai dai tana ganin kamar ajinsu ba daya ba, zai yi wuya aurenta dashi. Don difference din is Claire. Agogon dakinta ta duba 1:6 pm mikewa tayi ta dauro alwala, bayan ta idar da sallar azhahar ta dora da salatul istikhara, 2 rakaat. Rakaar farko fatiha da suratul khafirun, rakaa ta biyu fatiha da ikhlas. don neman zabin Allah Bayan ta idar tayi tasbihi, da istigfar ta karanta adduar istikhara. Allâhumma inni astakhiruka bi ilmika wa astaqdiruka biqudratika wa as’aluka min fadlikal-azimi, fa innaka taqdiru walâ aqdiru wa ta’lamu walâ a’lamu wa anta allamul ghuyubi. Allâhumma in kunta ta’lamu anna hâdhal amra (  bukata   ) khayrun li fi dini wa ma-ashi wa aqibati amri faqdir-hu li wa yassir-hu li thumma barik li fihi wa in kunta ta’lamu anna hâdhal amra(  bukata )  sharrun li fi dini wa maâshi wa aqibati amri fasrifhu anni wasrifni anhu waqdir liyal-khayra haythu kâna thumma ardini. Wani natsuwa taji yana ratsata. Tana cikin ninke sallayar Aisha tayi sallama. Yar da sallayar tayi da gudu ta rungumeta tana mai matukar farin cikin ganinta. Cike da farin cikin ganin juna kamar ba jiya suka rabuba. Aisha ta kalli hubby " sis meya faru? Kar dai maganar jiya ce, tasa kikayi zuru zuru haka? Kamar wadda ta kwanta cuta." Tabe baki hubby ta yi " abubuwa sun kwabe, dama na rasa abokin shawara. Na gode Allah da kika zo at right time " " tare da Yaya Ahmad muke, yazo ya baki hakuri, baiji dadi yadda kukayi dasu munaya ba. Muje in mun dawo sai mu tattauna." Tsaki hubby ta yi " wallahi ban son ko ganinshi. Da zaki taomakeni ki ce masa bananan." Harararta Aisha ta yi " laifin wani dai baya shafar wani. Meye laifinsa a cikin rikicinku? Ki tashi muje don sauri yake, mu samman yabar aikinsa don yazo ya baki hakuri,  muje." Ba yadda hubby ta iya, haka ta zunbulo hijab dinta har kasa. Don Ahmad ya wuce ta masa wulakanci, saboda girma da mutuncinsa da take gani. Tabbas laifin wani baya shafar wani. Sosai ya nuna rashin jin dadinsa, tare da bata hakuri. "Ba komai, yariga ya wuce" ta ce masa. Ya mata godiya sannan sukayi sallama ya tafi.                 **************** Shiru sukayi kowa da abunda yake sakawa, bayan hubby ta gama zayyanowa Aisha matsalarta. Nisawa Aisha ta yi " maganar su daddy gaskiya ne, lokaci yayi da zaki yi settling. Ni ina ga ki ba suraj dama ya turo. Gayen ya hadu, kuma yana sonki.after all da ganin alamunsa zai yi riko da addini." " kayya dai!!! Baka ganewa a fuska" "Haba ke kuwa, kina ganin tabon sallah a goshinsa, ai kinsan ko ba komai yana yinta." " Allah yasa." Hubby ta fada " naga alama kamar hankalinki yafi kwanciya da Dr Hashim. " Aisha ta fada tana dariya. Harararta hubby tayi tare da Jan tsaki. " ni kam duk cikinsu ba wanda nake jin wani Abu a kansa. Sai dai kawai zan iya cewa na danfi ganin dama damar suraj, duk da dinbin matsalolin da nake hangowa." " in haka ne, mai zai hana ki ba Hussain dama, wata kila in kin fahimce sa, kiga sabanin zatoki, kin San duk muskilancin mutun yakan dagawa matarsa kafa. Sai ki sha mamaki irinsu. Musamman akayi dacen yana sonki. Kuma kamar mommy hankalinta yafi kwanciya dashi." " ina!!!!! Bada ni ba. Auren soja sa mutun ya shirya." Dariya Aisha ta yi " nifa kike zagi da wayau." " kinga zaki iya ne ai." Hubby ta bata amsa tana murmushi " to koda Engr Sahabi za ayi." Duka hubby ta kai mata " Allah ya kyauta." " maganar gaskiya dai ko suraj ko kuma salis. Don salis yayi gaskiya bashi da aibu." " ke a tunaninki zan iya auren abokin Yusuf? Ko kadan don haka ki saka zancen wani salis a dustbin. " " halacci ke nan aboki in ya mutu ko ya saki matarsa ka aura." " Allah ko? To baa kaina ba. Don ni ko Wanda ya San Yusuf ban iya aura, don ina ganin kamar naci fuskarsa ne. Gara min bare inyi maneji." " Allah ya zaba miki mafi alkhairi" " amin." Hirar bikin su Aisha suka fara, da yadda ya kamata komai ya kasance. Sai 5pm Aisha ta masu  mommy sallama, hubby ta rakota compound dinsu, in da driver gidansu Aisha ke jiranta. Tsayawa sukayi jikin motar, suna maganar fita da zasuyi gobe saboda wasu shirye shirye daza su fara. Wata hadaddiyar fox jeep ce ta shigo compound din. Baka wuluk sai daukar ido take, gashi tasha tilted da bazaka iya ganin wanda ke ciki ba. Da kallo su hubby suka bi motar. Aisha ta kalli hubby, hubby ma aishan ta kalla. Suka sake maida hankalinsu kan motar data parka kusa da motar su Aisha.......... Toh!!pa!!!! Suraj, ko Dr Hashim, Munir, ko Engr Sahabi, ko kuma salis... Wani hadadden half cover shoe army green  ya fara musu sallama, bayan kamshin da ya cika hancinansu, da kofar driver ta bude. Sanye yake da shadda mai matukar daukar ido, light green, kanshi na sanye da hula damanga, army green. Yayi matukar kyau ga kamshi, kamar ya fito daga shagon turare. Aisha ta kalli hubby " wannan hadadden guy din fah!!!" Da yake bata taba ganin shiba sai labarinsa da take ji. Tabe baki hubby ta yi " suraj" ta fada a takaice, a hankali yadda bazai jiyo suba. Fuskarsa cike da faraa ya nufo in da suke tsaye, Cikin takunsa na kasaita. " u are lucky sis. Please don't let him go." Aisha ta rada mata kasa kasa. Sallama ya musu, Aisha ce ta amsa masa fuskarta dauke da murmushi. " what a lucky day. " ya fada yana kallon hubby da kanta ke sunkuye. Yau daya tun haduwarsu dataji nauyinsa. Aisha ce ta gaisheshi, cikin mutunci suka gaisa. Sannan hubby ta gaishe shi. Murmushi yayi  yana karewa hubby dake sanye da dogon hijab har kasa brown kallo. Ta masa kyau sosai duk da ba wani kwalliya ce a fuskarta ba. " to hubby sai goben in mun hadu." Aisha ta fada tana kokarin shigewa mota. Kallon hubby yayi yana murmushi " baki gabatar min da kawar tamu ba, har zata tafi." Hannun Aisha hubby ta kamo. " Aisha Jamal Yusuf zubair Oregon, sister din su hayder, my Best friend and also sister. " " masha Allah, best friend ya kike, ya hidimomi." Murmushi Aisha ta yi " lafiya kalau, kazo lafiya." Nan fa hira ya barke tsakanin Aisha da suraj, don shi mutunne mai saurin sabo, da alama yana da son hira. Hubby dai yar kallo ta zama, sai mamakin Aisha take yadda ta sake dashi kamar sun dade da sanin juna. " I have to go, nice to meet u." Aisha ta fada tana murmushi Shima murmushin yayi " nice to meet u too friend. " sallama sukayi da Aisha ta shige mota suka yi gaba. " bismillah." Hubby ta fada tana yin gaba. Binta yayi da sauri  suka jera. Shuke shuke ne na fruit, sai kujeru singles kusan guda biyar. Wurin hirar su jabir ne da abokansu. Wurin yayi kyau. Daga wurin kana hango duk abin da ake a conpound  din, kamar yadda kaima ana shigowa zaa hangoka. Sai da ta tabbatar ya zauna computable,. " bari in shiga gida 2 min, kar suga na dade." Murmushi yayi " no problems, ko kwana kika ce inyi, ai an gama balle 2min." Takunta mai matukar burgewa da daukan ido, duk da dogon hijab din amma yakan iya ganin yadda take yi, cikin natsuwa, da yanga, wanda yasan is naturally. Har ta bacewa kallonsa murmushi yayi tare da sauke ajiyar zuciya. Allah ya sani yana matukar son yarinyar. Akwai hankali da natsuwa. Ba irin rawar kan nan na matan zamani. Shi da badan ma yaji ta taba aure ba, a bakin da baya karya. Da ba zai taba yaddaba. Tanada karamin jiki, kuma jikinta nada kyau sosai. Don shi a yadda yake bata bazata wuce 20 zuwa 21 years ba. Wayarsa dake faman ringing ya duba tare da answering. A cikin natsuwa take takowa, dauke da wani kyakyakyawan trey golden. Ruwan faro, sai 7live da cups, sai wani bowl mai dauke da danbun nama. Anyi celling din shi da leader Da sauri ya tashi ya amshi trey din. Kujerar kusa dashi ta jawo zuwa gabansa, ya daura trey din a kai. " thanks. " ya fada yana Mata murmushi mai kayatarwa. Shiru sukayi na dan wani lokaci. Shi ya katse shirun " naje  kankiya jiya baki koma ba.?" Cike da natsuwa, " I won't back to kankiya. " Murmushi yayi " I known, Alhaji kawu ya min bayani. " Ido ta zaro tana kallonsa cike da mamaki. " meya fada maka?" Juice din ya tsiyaya, sai da ya yi sipping tukunna, idonsa a kanta, fuskarsa cike da annuri. " Notting much, ya tambayeni yadda mukayi dake, I tell him kinyi accepting dina as a friend. So murmushi yayi irin nasu na manya." Ya fada yana daga mata gira daya. " then he told me in turo magabatana nan da 2 weeks." " what." Ta fada da dan karfi, idonta a waje. That means kenan duk abin da yake faruwa da saninsu. Dariya ya yi " am so happy, jiya ko bacci ban iya ba, saboda dadi.  Kamar yasan na matsu Kwarai in ga na ajiye iyali. Wannan shine dalilin zuwana don in ji naki raayin. " do u really accept me as your husband? " Kanta ta sunkuyar tana wasa da tsinken dake hannunta. Zuciyarta na faman bugun uku uku.  wannan shi ake kira abun yazo, in ji mai tsoron wanka. " please ina son ji daga bakinki,. Kin yadda kin amince, zaki zama uwar yayan suraj kangiwa?" Sai da taja numfashi tukunna, kanta a kasa " if that is what they wanted, it's OK by me." " ba abunda suke soba, ke meye naki raayin? Zanfi farin ciki, ace ke kikayi accepting dina da kanki, ba wai under  pressure from you're parent ba." " I accept. " ta fada tana kara sunkuyar da kanta. Farin ciki wurin suraj baa magana. " Alhamdulillah, in sha Allah bazaki taba yin dana Sani,da zamowa ta miji, kuma uban yayanki ba. Zan baki farin ciki, iyakar iyawata, In sha Allah. Na gode sosai da kika bani dama in shigo rayuwarki." Hira sukeyi cikin natsuwa, duk da yawancin maganar shi yake bata labarin daya dangan ce shi, da family dinshi. Yaji dadin yadda ta fara sakin jikinta dashi, duk da ya lura tana da kunya sosai,. Yau ma kamar yafi na ko yaushe. Shigowar motar Alhaji Munir, yasa gaba daya hamkalinsu ya koma kansa. Mikewa yayi. " bari in je in kwashi gaisuwa." Ya fada yana nufar motar Alhaji Munir. Da driver ke kokarin bude masa Kofa. Tun shigowarsu ya lura dasu. Sallama ya masa, tare da kokarin durkusawa don gaisheshi. Da sauri Alhaji Munir ya tareshi, tare da mika masa hannu. Cikin jin kunya, da nauyinsa ya mika masa nashi, sukayi MusaBaha. Suraj yaji dadin yadda Alhaji Munir ya tarbeshi,cikin mutunci. Duk da haduwarsu ke nan ta farko ba,. Already sun San juna, sun sha haduwa a maban- banta wurare. Ajiyar zuciya hubby ta sauke, lokacin da suraj ya isa wurin daddynta. Sai yau ta kare masa kallo. Tabbas bashi da makusa, ya hadu. Sai dai tasan bai kama kafar Yusuf dinta ba.  " madam bari in kama hanyar kauyen mu." Suraj ya fada yana murmushi. Tashi tayi ta rakoshi har jikin mota. Tare da masa fatan sauka lafiya. Har ta  juya zata tafi. " ji mana." Ya fada yana bude kofar motar. Dawowa tayi ta tsaya. Wata hadaddiyar leader ya mika mata " please ba don ni ba, don Allah ki yi anfani da ita, bana jin dadin rashin waya a hannunki, ko ba komai zanji muryarki, wani abun ma zakifi sake jiki, ki min magana. Next week Saturday in sha Allah parents dina zasu zo." Gadiya ta mishi, da alkawarin zatayi anfani da ita kamar yadda ya bukata. cike da farin ciki suraj ya bar gidansu hubby. Sai bayan da ta idar da sallar magrib ta dauki leader din ta nufi dakin mommy Hauwa. A zaune ta sameta tana jan tasbaha. Sai da ta jira ta gama sannan ta mika mata leader din. " meye wannan." Mommy Hauwa ta tambaya " nima ban Sani ba, shi ya bani." Ta fada kanta a sunkuye. Kada kai mommy Hauwa tayi tare da bude leader. Kwalin waya ne ta fara cin karo dashi. A hankali ta fito da kwalin ta bude. Ido mummy Hauwa ta zaro, baki a sake tana juya wayar, tare da kara karanta sunan waya.  Goldvish (18 carat white gold & 120carat of vvs---1 graded diamond)  Mommy Hauwa ta kalli hubby da itama idonta na kan wayar. Tana ganin kyawawan waya bata taba ganin wayar data burgeta ba, kamar wannan. Gata yar dai dai, so cute. " Ummi wannan ai customize phone ne?" Mummy Hauwa ta fada tana juya phone din. Junaid ne ya shigo da sallama. " evening Anty. " ya fada yana zama kusa da hubby. " evening brother, daga ina?" " hayders house. " " aikin ke nan." Hubby ta fada "Mommy Hajiya na gaisheki, wai ya taji shiru." " or I totally forget. I call her." Mommy Hauwa ta kalli hubby, tare da mika mata phone din. " kin tabbatar dai kina son shi ko?" Kai hubby ta sunkuyar cike da jin nauyin mommy Hauwa. " naso Kwarai Ku dai daita da hassan, amma tunda kin ga bai miki ba, shi kenan, Allah ya musu  zabi na alkhairi." Junaid ya amsa da " amin." Shima ya yaba phone din. Leader ya bude wani kwalayen ya fito dashi. Daya smart watch, da yan perfumes ne different colours. Kananan kwalabe masu kyau. "Woow!!! This is our collection." Junaid ya fada yana murmushi. Mommy da idonta ke kan set din perfume din ta ce " kamar Yaya?" Sunan ya nuna mata. ( 7 friends for ever collection) sai ainihin sunan turaren caron poivre.  " kai junaid ban son karya, yaushe kuka fara kasuwancin da har zaku fara collection na kanku.?" Mommy Hauwa ta fada tana harararsa. Dariya yayi " da gaske mommy wannan turaren mu mukayi, design dinsu, sannan mu muka zabi ingredients din da muke son a hada mana dashi. Mu muka yi exporting dinsu to Nigeria. Its our oder" " yaran nan kun fara bani tsoro fah!!" Mommy Hauwa ta fada tana tsare junaid da ido. Dariya yayi " kar kiji komai mommy. Neman halas dinmu fa muke yi. Kin ga waannan ko wanne da kamshinsa da ban. Its made from expensive ingredients, zakiji dadin su sosai." Harararsa hubby ta yi " in mommy ta yadda ka dauka nima yadda zanyi. Please stop lieying. Luke at is very care full its expensive perfumes. How do you people have that kind of money to do all this in short time. ?" Kada kai mommy Hauwa tayi alamar gamsuwa da maganar hubby. Murmushi junaid yayi. " it's OK. Amma kar Ku manta muna da irin su don Harris da business tycoon Alhaji omer Yusuf zubair, har kwa tambayemu in da muka samo manyan kudi?" " haka nefa!!!." Mummy Hauwa ta fada tana kallonsa. " dama na shigo in gaya muku amaryata ta iso." Ya fada yana murmushi " Amarya kuma?" Hubby ta tambaya "Mai kafa hudu ba." Ya fada yana dariya ganin kallon da mommy Hauwa ta masa. Murmushi suka yi tare da masa Allah ya sanya alkhairi. Tare suka fito compound din. A jikin motar suka samu jafar da jabir, suma suna kallon new car din kanin nasu. Cike da mamaki  mommy Hauwa ta ke bin motar dake gabanta da kallo  2008 BMW 7 Series. " masha Allah brother, mota tayi kyau, Allah ya sa alkhairi, ya sa daka da alkhairin dake tattate da ita, ya kare ka daga sharrin dake tattare da ita." Su jafar suka fada, suna rungume dan uwan nasu, cikin farin ciki. " ameen, na gode." Ya fada yana murmushin jin dadi. Su mommy Hauwa ma sun tayashi murna da addua. Duk da zuciyarta na cike da tambayoyi. " yarona fah?!" Mommy Hauwa ta tambaya " power bike, da safe ya ce min zaizo ya nuna miki, da tare zamu taho, Alhaji babba ya kirashi." Tabe baki hubby ta yi " Allah ya kyauta, banda shirmen hayder me zaiyi da power bike." Mommy Hauwa ta fada " ra ayi." Jafar ya fada yana dariya "Sai kin ga power bike din yayi kyau sosai." In ji Junaid " mako dai!!! Me mutun zaiyi da wani mashin in ba mako ba." Hubby ta fada tana hararar junaid Ido ya zaro " kin San kudin bike din nan, kike cewa mako? Yafi kudin motar nan da kike gani nesa ba kusa ba." Dariya hubby tayi " Haba yaro karka raina min hankali mana." Kallon jabir junaid yayi " gaya mata brother. " " is true bike akwai masu tsada sosai, duk da bansan irin wanda ya siya ba, amma zai iya kasan cewa yafi motar tsada." Jafar ya fada  "Aprilla ( Italian motorcycle brand )" daga jafar har jabir kallon junaid suka yi cike da mamaki. " wow!!! Har kasa na kosa inga bike dinnan, kwanan nan friends dina na musu  tsakanin aprillia da kasawaki." Murmushi junaid yayi " zakuwa ka ganshi yayi kyau sosai," Mommy Hauwa dake saurarensu murmushi tayi " ina ruwan yarona, komai nashi daban." Jabir ne ya amsa da " I love the boy, he have a taste, komai nashi unique. Kam" " gobe zaa bani Amarya in dana." Hubby ta fada Murmushi junaid yayi, tare da amsar key din a hannun jafar ya mika mata.  " it all yours sis." " thanks u are the best. " ido su jafar suka zaro cikin wasa " what about us." Dariya su hubby suka yi " jealousy. " junaid ya fada yana dariya " I love u all. " hubby ta fada tana shigewa ciki da gudu, kamar wata karamar yarinya. Da kallo suka bita. Mommy Hauwa ta kada kai " Allah ka shirya, naga ranar da Ummi zata San ta girma." Murmushi dukan su suka yi cike da son yayar tasu.......... [04/03, 18:15] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 3       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Baka jin komai sai karar cukula da plate. Mommy Hauwa ta kalli Alhaji Munir. " sai ga yaronka da zukekiyar mota." Murmushi Alhaji Munir yayi " na ganta Allah ya sa albarka." Ajiye spoon dinta tayi " haka ma zaka ce? nifa abun ya fara bani tsoro, har yaushe suka fara business din, da zasu samu manyan kudi haka?" Murmushi still Alhaji Munir yayi " ki kwantar da hankalinki. Shi kasuwanci sirrine, kashi casa'in na arziki yana kasuwanci. In Allah ya sa maka albarka sai kiga cikin lokaci kadan ka zama wani Abu. Kamar yadda suka fara nasu cikin nasara. Shekara uku da wani abu, ai ba yanzu bane." " ehhhmm!! Haka dai kace." Junaid Alhaji Munir ya kalla " kai baka mata bayanin kasuwanci naku bane?" " na gaya mata, kawai bata yadda bane." Alhaji Munir ya kalli mommy Hauwa "duk abun da suke yi is under our watch." " shi kenan ai!!! Allah yasa albarka." "Amen "  suka fada baki daya. A nan Alhaji Munir ke shaida musu za a je tambayar auren jafar, yana son nan da 5month a hada dana hubby gaba daya. Kallon jabir mommy Hauwa tayi " kayi kokari nan da lokacin ka fito da taka a hada in huta. Don na kosa in dinga ganin yan dagwai dagwai a gidan nan." Dariya suka yi gaba daya, banda jabir dake faman Sosa keya, yana murmushi kasa kasa. " tu kunna dai mommy. " " ba wani tukunna, ni da zaka bani zabi dana hada ka da kawar amir, Zainab. Yarinyar akwai hankali da natsuwa. Ina son yarinyar. Don haka nake fatan ko kai ko junaid ya auro min ita." " lala!!! Ban dani." Junaid ya fada yana dariya " nima aa!" Jabir ya fada Alhaji Munir ya kalli mommy Hauwa " wai ke me yasa bakya son zaman lafiya ne? Ki barmin yara su zabi abinda suke so." " ai shi kenan, Allah baku hakuri." Ta fada tana yamutsa fuska Dariya hubby keyi kasa kasa. Ita ta rasa wannan son hada zumunci na mommy. Gashi duka are in vain. Harara mommy Hauwa ta maka mata. Ba shiri ta Mike ta nufi dakinta, kafin mommy ta kai mata mangara, bayan ba ita takar zomon ba.                ***********"******* "Lafiya meya samu kafar?" Ummu khulsum ta fada tana zama kusa da hubby. Hubby da ta cika tayi tam. Don bata kaunar ko kwarzane a jikinta. Ta nunama ummu khulsum in data kuje har yayi jini kadan. " subhanallahi garin Yaya?" Tsaki hubby ta yi " wannan dan banzan yaron ne, ya so yabi ta kaina da gwangwanin banza mashin dinsa." Baki ummu khulsum ta rike. " kar ki gayamin har yanzu kina nan kuna shirmenku." " bar miskilin banza, sai na masa dukan kawo wuka, tukun na zai shiga hankalinsa dani, in farfasa gwangwanin banza kowa ya huta." Ummul khair dake shigowa ta fashe da dariya, jin hubby na maganar yima hayder duka. Itama ummu khulsum dariyar tayi. " gaskiya kam, don ya gama raina ki, wata kila in kin nuna masa tsohon kashi ya shiga hankalinsa." Ummu khulsum ta fada tana dariya " kai uhtee!! Wannan ai zuga ne! Ina hubby ina hayder? Loma biyu kawai zai yi da ke, ko in ce hadiya daya. Ki daina shiga harkarsa kawai. Don yanzu kosu Yaya Ahmad ai basa ce zasu bugeshi ba, balle ke mace." Ummul khair ta fada " laifinta ne ai, yayi ta hon taki matsawa, da ba dan na janyeta ba da ya karairayata, yadda ya taho da gudun nan." Ummu sulaim ta fada tana shigowa da fist aid a hannunta. Harararta hubby ta yi cikin fushi, da jin haushin maganarta " duk filin compound din nan ya rasa inda zai bi sai ta inda nake tsaye?" " Allah ya shiryeku, ke son girma shi son girma da raini. Sai kuyi tayi, wanda ya gaji ya sake." Ummu khulsum ta fada Zama ummu sulaim ta yi ta na ma hubby dressing din inda ta kuje. " daga yau da dorinata zan dinga zuwa gidan nan. Don ni bazan dauki rainin hankali ba. Dukan tsiya zan masa ko ya shiga hankalinsa. Don yaga yayi tsawon kafa, bashi zai bashi lasisin raina na gaba dashi ba. Don duk ta gina ne bata shigaba. Agric chicken kawai." Dariya sukayi gaba daya, banda hubby dake cika tana batsewa. Ummu sulaim ta ce " ke yanzu ko cewa akayi ki bugeshi sai ki buga?" Harararta hubby tayi " mai zai hana. Ki zuba ido ki gani, ya sake shiga gonata kiga yadda zamu kwashe." Hayder ne ya shigo da sallamarsa, wucewa dakinsa yayi ba tare daya ko kallesu ba. " tabdijamm!!! Anty khulsum bai fa gaishe kiba, ya wuce." Murmushi tayi tana kallon hubby " ina zai gaisheni, bayan yanzu gani yake shine gaba damu, ya kwace girman Hajiya kuma ta goya masa baya." " tabdijamm!!! Allah ya ragewa aya zaki, da anyi karamin yakin badar a gidan nan." Hubby ta fada Ummul khair dariya tayi " ba abunda zakiyi ko ke din ce,. Don Hajiya ta daure masa kafa, harda wani shine uba, kuma yaya a garemu. Can u imagine, ke hatta su Yaya Ahmad shakkarsa suke. Don wani abun in yanayi har mamaki yake bani. Karfi da yaji ya kwace girman ya dora ma kansa." Tabe baki hubby tayi " Ku kuka so, wallahi." Hayder ne ya fito da niyyar fita. Hubby ta mike ta tareshi " dutse halan ka taka dasu ko? Kasan Allah duk randa ka kuskura ka kara aunani da gwangwanin  mashin dinka, sai jikinka ya gaya maka, sannan in fasa gwangwanin banza kowa ya huta." Kallon up and dawn ya mata tare da tabe baki ya bi ta gefenta ya wuce abinsa. " miskilin banza, dani kake zan cen." Ta fada tana zama. Su ummu sulaim kam dariya hubby ta ba su yadda ta dage adole tana masifa. Hirar zumunci, da na shirye shiryen biki suka kafa. Duk da already an gama duk kan wani shiri daya da ce. Lokacin bikin duka duka saura 10days.              ********************* " kayi hakuri, kafi kowa sanin halin mahaifinka, wajen kafiya, munyi iya kar kokarinmu amma abun ya ci tura. Don haka ka daure ka amince da zabin sa shine zaman lafiyarka. Don ban taba ganin bacin ran Yaya ba irin wannan karon, har cewa yayi nida hajiyanka mune masu daure maka kafa, shiyasa kake son bujirewa zabinsa." Cikin tashin hankali, suraj ya zo ya tsugunna a gabanta. " nasan kinyi kokari, amma sanin kanki ne ke kadai zaki iya sakko da daddy kan raayinsa. Na amince muddin ya yarda na auri zabin raina, zan auri doctor ita ma. Ko don in faranta masa rai." Kada kai Anty tayi " ka kasa ganewa ne kawai. Amma wannan karon is different da sauran time din. Kafi kowa sanin mahaifinka ba zai aminta da auren bazawara ba, after all ba wani ilmi tayi mai zurfi ba. Sannan babban matsalan status din is far different." Suraj da yake cike da tashin hankali da damuwa. Idon nan ya kada yayi jawur, shi kansa ya manta rabon da yasamu natsatsuwa da isashshen bacci. tun kan yakai maganar hubby gaban mahaifin nasa. " wannan ba hujja bace Anty. Musulunci ya ce mu auri mata don kyanta, ko don kudinta, ko nasabarta, amma sai aka horemu da auren maabociyar addini. Me yasa  Ba a ce mu zabi maabociya dukiya da nasaba ba? Saboda wannan iyakarsa gidan duniya. Bazawara kuma, kun manta manzo SAW ma da bazawara ya fara. Kinga kenan nima nayi koyi dashi, meye aibu a nan?" " ba aibu, suraj. Amma kasan halin mahaifinka fiye da kowa. Gobe in sha Allah zan je in sameshi, ka cigaba da addua, don ita ce kawai mafitarmu a yanzu." Duk da tashin hankalin da yake ciki, bai hana bayyanuwar murmushi a fuskarsa ba, don duk cikin dangin mahaifin nasa ba wadda yake saurarawa sama da kanwartashi. In ya tuke ita kadai ke iya lallabashi. " na gode Anty Allah ya biyaki da gidan aljannah. " Murmushi tayi, tana mai fatan nasara. Zuciyarta cike da tausayin suraj, don ta tabbatar yayi nisa a son hubby.                ***************** shakuwa ce ta shiga tsakanin hubby da suraj, don yanzu takan sake dashi a waya, susha hirarsu. Suraj mutun ne mai saurin sabo, ga ban dariya some times,. Satin daya yi alkawarin zuwan family nashi, basu samu zuwa ba, saboda uncle dinsa da ragamar tafiyar ke hannunsa baya kasar. So sai aka daga zuwa next week. Yanzu haka kwana uku kacal ya rage.               ******************** Zaune yake a gaban mahaifin nasa. Kansa a kasa, zuciyarsa na faman bugu, don ya tabbatar yau zai samu duk kan amsarsa, in ma nasara da akasinta. Jikinsa yayi sanyi sosai ganin fuskar mahaifinsa daba wani annuri a tattare da ita. Sai dai duk da haka bazai yi saurin karaya ba. Kallon da mahaifin nasa ya masa, yasa hantar cikinsa kadawa. Gyara zama Alhaji saad kangiwa yayi. Cikin dakakkiyar murya  wadda ba wasa ko wargi a cikinta ya ce " na samu sakonka, sai dai ka sani ban lamuta ba, bazan taba yadda ka auro min yar talakawa ba," da sauri suraj ya dago yana kallon mahaifin nashi baki na rawa " Allah daddy babanta nada arziki dai dai gwargwado." Bai karasaba Alhaji saad kangiwa ya tareshi " rufa min baki, mutumin banza. Waye Alhaji omer Oregon, ballantana shi? Ina yaron sane? Me na sama ya ci balle na kasan?. Na gama magana, yanzu haka yan aike sun dade da isar da sakona ga iyayenta. Don haka kar koda wasa inji ance an sake ganinka tare da yarinyarsu. Bakai ba ita. Sannan maganar aurenka da doctor nan da sati mai zuwa, ya rage naka kaje Ku tsara yadda abubuwan zasu kasance ko kar kaje, ba fashi. Don na lura da take yakenka in na ci gaba da zuba maka ido, mutuncina zaka zubar." Fadin tashin hankalin da suraj ya shiga a lokacin bazai faduba. Gaba daya jinsa yake kamar a sama yana plotting. Ga kirjinsa da ya masa nauyi kamar an daura dutse. Kallon mahaifin nasa yake. Gani yake kamar an canza masa shi. Mahaifinsa mai matukar son sa, da son farin cikinsa, yau shine da kansa yake son fatali da duk wani farin ciki na rayuwarsa. Don rabuwa da hubby tamkar rabuwa da wani bari na jikinsa ne. " tashi ka ban wuri, kar ka manta nasa matakan tsaro a kanka, koda wasa ka kuskura kayi gigin tsallake umurnina, tamuce ni dakai." Da kyar ya kawo kansa part din hajiyansa. Rungumeta yayi, ya saki kuka kamar wani karamin yaro. Tasan dama zaayi haka, don daga kanta aka fara, Tausayin tilon yaron nata ne cike da ranta. Taso Kwarai  mahaifin ya masa adalci ya auresu gaba daya, amma yaki. saboda wani ra'ayi Mara tushe balle makama. Lallashin suraj ta yi, tare da nuna masa muhimmancin biyayya ga iyaye, sannan ta kwantar masa da hankalin in har hubby rabonsa ce, to ba makawa sai ya aureta, in kuwa ba rabonsa bace to no matter how baza ka sameta ba. " I promise u, in har ka kwantar da hankalinka, bayan aurenka da doctor, zanyi iya yina in ga ya barka ka auri zabin ranka kaima. Amma hakan bazai samu ba, sai ka natsu ka nuna masa kayi naam da zabin sa." Kallon hajiyansa yayi, da jajayen idonsa da suka kara kan kan cewa. " kina ganin baza suyi kokarin aurad da ita ba, kafin lokacin?" Ajiyar zuciya tayi " shiyasa na ce ka dage da adduar ai. Sai kaga komai yazo da sauki." " shikenan. Amma tayaya zan tari Habiba da wannan maganar? Dama da yaya na samu ta saurareni." " yanzu kam na tabbata bayani ya isa ga iyayenta. Nasan zata nemi Karin bayani daga bakinka, then sai kayi anfani da hikimarku ta maza, ka bata baki, tare da shaida mata matsayarka." " na tabbata gani zatayi kamar yaudararta zan kuma yi. I can tell her. " " u have to tell her, this is the right thing." " I will try." Ya fada in low voice.                 *********** Zaune suke a falon Alhaji babba, bayan sun sallami bakinsu. Alhaji kawu ne ya kalli Alhaji babba, fuskarsa cike da bacin rai da damuwa Zai yi magana, Alhaji babba ya katseshi. " kar kace komai. Nasan abun da ciwo. Amma karka manta kullun cikin yima yaranmu addua ta gari mukeyi, mu dauka hakan wani alkhairi ne a garesu baki daya. Sannan ina neman alfarma kamar yadda na nema a baya, in har Habiba bata da wani tsayayye to ina son a hada da Abdul majid ko abdul Karim, kamar yadda na bukata a baya." Ajiyar zuciya Alhaji kawu yayi, tare da kai kallonsa kan Alhaji Jamil, da abokan Alhaji Munir su biyu, sai Alhaji Jamal, da abokan shi kansa Alhaji kawu su biyu dake falon. Ya maida kansa kan Alhaji babba. " bamu bukatar sake mai maita wannan kuskuren. Don haka koma da wanne ne a ciki na amince. Zuriata da zuriarku tamkar Abu daya ne, ko da dana bukaci a bata dama, ganin ita a yanzu bazawarace musulunci ya bata damar zabar abokin rayuwarta. Sai dai yanzu iya sanina duk masu son nata matasa ne, marasa aure, bana son a maimaita yar gidan jiya. daya ne mai iyali, shi kuma akwai dalili daya dazai hana in bashi auren Habiba. Dama mun so a hada dana dan uwanta,." Murmushi Alhaji babba yayi irin na jin dadi. " alhamdulillah wannan Abu ya min dadi. Ban son ko kadan Habiba ta fita daga zuria ta. Shiyasa tun farko na bukaci ka yarje min in hada ta da daya daga cikin jikokina. Don haka ba fashi, nan da lokacin da akasa auren, muna fatan su samu fahimtar juna." Duka yan falon addua sukayi da fatan alkhairi. Taro ya watse kowa na cikin farin ciki da annashuwa, kamar ba wani abun bacin rai daya faru. Abokan Alhaji Munir suka fara masa bayanin abunda ya faru, kafin ya koma gida, Alhaji kawu ma ya mayar masa da yadda abubuwan suka kasance. Ran Alhaji Munir ya baci sosai.  Addua yayi Allah yasa haka ya zama mafi alkhairi garesu baki daya. So koda ya koma gida mommy Hauwa kawai yama bayani, sannan ya bukaci datayi shiru tukun na, har suji daga bakin Alhaji Jamal kan wanda zaa hada dashi. Mommy Hauwa bata ji dadin wannan lamari ba, duk da dama ta dade da hasaso hakan. Don wata aminiyarta ta shaida mata akwai yar abokin kangiwa da akeson a hadasu tun shekaru biyu da suka wuce, ya ki. So ta dauka maganar ta wuce ne,ko kuma sun hakura tunda shi ya nuna baya so. Fatan alkhairi tama yarta da kudurce kara dukufa da yi mata adduar zabin nagari........ Yau ne Alhaji Jamal ya Tara iyalansa, da yaransa maza. Ahmad, Abdul Karim da hayder. Abdul fatta bai samu zuwa ba, saboda yanayin aikinsa. Alhaji Jamal ya kalli iyalan nasa bayan ya tabbatar da duk hankalinsu na tare dashi, don jin abun da yasa ya tarasu. " ina son tsakanin Abdul Karim da Abdul fatta daya daga cikin su, ya auri Habiba don maye gurbin dan uwansa, bai kamata ina da samari a gida ba ace nabar irin wannan natsatstsiyar yarinyar ta fita daga zuriata. Don haka na tara mu a nan don muyi shawarar wanda ya dace ya maye makwafin marigayi a cikin su biyun nan." Kallon kallo aka fara tsakanin matan, su Ahmad dai Kansu na kasa. Mmn Yusuf ce tayi karaf ta cafke da " Abdul Karim din dai, don wannan karon bazan taba yadda amin abinda aka min wancan karon ba." Da ido Alhaji Jamal ya tsareta " ko zaki gayamin abinda kike ikirarin an mikin?" Cikin jin haushi ta ce " in maye ya manta, ai uwar diya bazata manta ba. Wan can karon naji Yusuf da kansa yaki nafisa, ka daure masa kafa, to a wannan karon an samu akasi, don Abdul fatta da kansa ya bani damar zaba masa mata, kuma na zabo masa, har sun aminta da juna. Don haka abi wani sarkin ba dai yayana ba." Still idon Alhaji Jamal a kam Mmn Yusuf. " Allah ko? Duk da yaushe akayi hakan bani da labari?" Ya tambaya Shiru tayi tana dan ture turen baki. Numfashi ya ja " gidana ne, yaya nane, nike da ikon kafa doka a gidan nan kuma dole abi. Don haka ki bini a hankali" Hajiya ce ta amshe da " aa gaskiya ta fada, kamar yadda kake da iko da Abdul itama tana dashi, a matsayinta na uwa. Ya kamata a mata uzuri, tunda ya samu mata, ba matsala Allah ya sanya alkhairi yasa ayi damu." Harara Mmn Yusuf ta dallawa Hajiya, murmushi Hajiya tayi. Don bata manta gashin kuman da sukawa hubby a wan can karon ba, bata fatan ta kuma kasan cewa a kalkashinsu kuma. Ita hakan ma dadi ya mata. Alhaji Jamal ya maida kallonsa ga Abdul Karim da ke zaune gefensa, kansa a kasa. " to Abdul Karim magana ta dawo gareka, ya kake gani? Zaka iya cika min wannan burin nawa ko kai ma ka samu wadda kake so?.'" Shirune ya biyo baya, kowa idonsa na kan Abdul Karim, yana jiran yaji mai zai fada. Mmn Yusuf ce ta katse shirun da " a bashi lokaci yayi tunani ai ko?" Harararta Alhaji Jamal yayi, dauke idonta tayi tana fadin " Allah baku hakuri da ga fadar gaskiya." Mmn samira da tun da suka zauna sai yanzu ta yi magana. " ka bashi lokaci yayi nazari tukunna." Da tsananin mamaki Hajiya tabi Mmn samira da kallo. Bata taba tunanin ko a mafarki Mmn samira zata samu second true akan hada Habiba da daya daga cikin yaranta ba. Ganin yadda suke zaune kai a hade, sama da shekara talatin. Kin yadda su hada ido Mmn samira ta yi, duk yadda Hajiya taso su hada idon. " zan cen banza, ba maganar shawara a ko aa, kawai nake son ji." Alhaji Jamal ya fada, don shma jikinsa ya fara sanyi da lamarin iyalan nasa. " ka bashi lokacin kamar yadda suka bukata, sai dai ina son Ku Sani Habiba, bawai ta rasa manema bane, so karkuyi tunanin wai kunyi favoring dinta ne." Hajiya ta fada Dariya Mmn Yusuf tayi " munga alama ai.?" Ta fada cikin gatse. " ya isa haka!! Ban kiraku don Ku daga min hankali ba, don Ku baa taba abun arziki daku. Kaje na baka nan da rana ita yau, ina jiran amsa daga gareka, sai dai karku manta baku kadai bane yayana, in Ku kunki min wannan alfarma akwai masu bukata ido rufe, sai dai an ce so so ne amma son kai yafi. Ku tashi Ku tafi." So ko a cikin gida, gaba daya Mmn samira daukewa Hajiya wuta tayi, ganin haka Hajiya ta fita a hanyarta. Sai dai mamakin Mmn samira har yanzu bai barta ba. Ita kam ko a jikinta, don ta tabbata koda Abdul Karim ko bashi hubby bazata rasa mijin aure ba. Da badon yadda take kin sauraran masu sonta ba da tun tuni ta dade a gidan mijinta. Addua da fatan alkhairi ta bi lamarin dashi, sannan ta sata cikin adduainta na musamman.                 ******************* Koda suraj ya kira hubby ya mata bayani, don ya tabbatar bata da labarin abinda ke faruwa. Bata wani nuna masa damuwarta ba, duk da deep down she is broken. Ba wai tana son shi bane, aa, amma shine mutun na biyu data bashi damar shiga cikin rayuwarta. Tattara komai tayi ta ajiye a gefe, don dama bawai auren bane a gabanta. Ta wani fanninma dadi taji, don ta dan Shana kafin su kara bijiro mata da wani zan cen aure." Su ummu sulaim da sauran friends dinta suma abin bai musu dadi ba, amma suka bita da fatan alkhairi.              ***************** Abdul Karim Jamal Yusuf zubair Oregon. Kani ga Ahamad, Shi ke binshi a dakinsu. Ya yi degree dinsa na farko Dana biyu a Malaysia, in da ya karanta architecture yanzu haka yana aiki da ministry of works abuja. Yana da rufin asiri dai dai kwargwado  Kyakyawa ne,  duk gidan in ka dauke Yusuf da hayder to ba ya shi.  Dan gayune na karshen zamani, cikakken womanizer, amma a boye yake alamuransa. Sai sigari da yake busawa time to time, wannan kam kowa ya San dashi. Yana son wayayyar mace mai ilmi, don duk yan matan da yake muamala dasu wayayyune, wanda ilmi da kudi suka zaunama. Burinshi duk in da matarsa ta fita a San yes ya iya zabe, ya kere sauran maza. Hubby no way!!! She is alliterate, sannan bata waye ba ko kadan, ba irin Matar da yake muradin ajiyewa a gidanshi bace. Yasan she is beautiful and wealthy, amma shi is not his type.               ******************* Hidima ake ba kama hannun yaro. Yau gidan kamar an yashe, duk suna wurin lunching. daga iyayen amare sai  tsoffi da suke ganin wurin ba wurin zuwansu bane.  Hajiya ce sai manyan aminanta biyu, Hajiya Balkisu da Hajiya Fatima. Suna zaune a falon hajiyar ana hirar duniya. Daga can suka fara jiyo magan ganu na tashi daga tsakar gidan da ya hada part dinsu. " lafiya kuwa?" Hajiya Fatima ta fada tana kallon kafar falon. " muryar Hajiya kaka ne, Allah yasa lafiya." Hajiya ta fada tana mikewa don ta gano abinda ke faruwa. Kafin ma ta isaga fita Hajiya kaka da kanwar Mmn samira, Hafsat suka iso bakin kofar Hajiya. " ina kike, yar ayi ba yar a rababa. Dama tun da naga kina shishshigewa yarinya nasan kin kulla tuggun cuta. Ita kuma da yake sakarya ce, Mara tunani take biye miki, kina cutarta. To wallahi bazata sabuba. Bazan taba yadda da wannan hadin cutar ba eheee!!!." Gaba daya su Hajiya suka fito don jin ba'asin zance. " lafiya dai ko Hajiya? " Hajiya Balkisu ta tambaya, don bata gane kan maganganun da Hajiya kaka ke fada ba. " ina fa lafiya, ana son cutata, a cuci zuriata. Ta ya zaa dauki second hand a ba jikana, babban abun ma Mara haihuwa? Yarinyar da shekara kusan hudu ko batan wata bata taba ba, har mijin ya koma ga Allah baiga kwansa ba, saboda an asirce shi, an hanashi auro wadda zata Haifa  masa yaya. Shine ni ake son a lallaba a cuci jikana ko? To wallahi bazai taba yiyuwa ba, matukar ina raye. Ni da nake fatan ganin yayan jika zaa min sagegeduwa don rashin imani." " Haba hajiya!! Ba girmanki bane, koma menene, ki bari a warwareshi a tsanake, be kamata kina daga murya haka ba, kefa babbace." Hajiya Fatima ta fada cikin murya mai taushi, ganin yadda Hajiya kaka ta hakikance tana zuba ruwan balai, ga bakinta sai kunfa yake fitarwa. Hafsa ce ta amshe da "haka dama ake fakewa da cin girma a cuci mutun. Ai gaskiyar Hajiya kaka ne, tana son yadda ta mallake yaya Amina, sai abunda ta ce, ta mallake mata dan da take ji dashi. Gara tun wuri ki sake lale, a nemi wani sarkin." " ni kike gayawa wannan maganar? Ki Sani in Hajiya kaka ta fada na kyale, ke kam gidanku zanci, har kina da bakin da zaki gayamin zan cen banza? Ina abun yake?" Hajiya ta fada cikin fushi da bacin rai Yan uwan Mmn Yusuf dake tsaye suna kallon ikon Allah. Innani ta ce " meye laifin Hajiya a wannan magana? Sai ki jira Alhaji Jamal shida yake son hadawar kuyi dashi. Amma gaskiya wannan ba dai dai bane. Agi ta harari innani " zancen banza kenan!!! Ai maganar Hajiya kaka a kan hanya take. Karki yarda haka ina ji ina gani, jikana har ya koma ga Allah banga kwansa ba, baya ga mallakeminshi da akayi, baya ganin kowa da gashi in ba su ba. Me ake da wannan hadi? Ko cuta? " " ta ina zan yadda da wannan danyan hukunci? Shima Abdul Karim din ya ce bai so, don haka babu dole. A kara gaba, a sakarma jikana mara yayi fitsari, kar inji kar in gani, in fa ana son zama lafiya." " wai gaya muku a kayi neman kai ake da ita ne da kuka, ishi jamaa da tashin hankali? Yau ya ce baya so, dubunsa nanan na jira. Meyayi zafi? Ko an ce dama dole sai jikanki ya aureta, sannan zata ci gaba da rayuwa.? Hajiya Balkisu ta fada rai a bace. " ya dai rage naku, in gaskiya ake son kullawa, ba cuta ba, ai itama ta haifi namijin, shi ya aureta mana. Amma da yake ba Allah a ciki, zaa cuci dan kishiya." Hafsat ta fada tana barin wurin. " aiko fadi ki kara, na haifi da daya tamkar da dubu, ke kanki kinsan hakan." Hajiya ta fada Ido Hajiya kaka ta zaro " to in kin cika yar halas, cikin Uwale da ubale, shi ya aureta. Amma ba jikana ba." Murmushi agi tayi " gaskiyarki Hajiya kaka tunda Allah ya raba yaba kowa, kinga tuwona maina kenan. Kai wannan abu yayi kyau." Ta fada cikin izgili Iska Hajiya ta busar daga bakinta, ta sauke ajiyar zuciya, ta dade rabon ranta ya baci irin na yau. Murmushi tayi. " na gode da shawararki, in sha Allah gobe iwar haka Habiba ta zama mallakin Aliyu hayder, zan nuna miki tabbas nidin yar halasce,. In kin cika ki nemowa jikan naki wadda tafi Habiba a gobe." " gasu nan kamar jamfa a Jos, takin ce dai baa so. Tunda kun janye falillahil hamdu, aniya bi aniya. " ta fada ta juya ta nufi part din yar tata tana faman surutai.                     **************** Sanye take da ankon cotton material milk sai design dark blue, dinkin riga da skert 8picess yasha adon dark blue less da yazo da material din. Dinkin ya zauna das a jikinta, tasha make-up yau kan make-up sosai ta tsaya aka mata, ga daurin head irin wanda ake yayi, gashinta da yasha gyara ya fito sosai yayi tim a bayanta. Karamin gyale ne, Mara nauyi dark blue da takalmi da jaka to match. Tayi mugun kyau, kai kace ita ce amaryar. Kana ganinta kasan tana cikin farin ciki, ga abokansu da sukayi secondary tare sunzo, sai kashe selfie suke ana shafta baka jin komai sai karar sautin DJ da dariyarsu Kasan cewar wurin duka mata ne, yasa hubby sake jikinta. Daga inda suke tsaye da Anty samira yana iya hango hall din, da jamaar dake ciki. Tun yana fahimtar abinda Anty samira ke fada har ya daina jinta. Gaba daya hankalinsa ya koma kan wata hadaddiyar yarinya da yake hangowa daga inda yake tsaye. Ba abunda ya kara tafiya dashi irin dirin jikinta unique, kamar murmushinta da dariyarta. Gaba daya wani irin yanayi ya tshinci kansa a ciki, mai wuyar fassarawa. Ya hadu da mata iri iri, yayi muamala dasu, amma bai taba cin karo da irin abunda idonsa ke hango masa ba. Ba abunda ya kara tayar masa da hankali, irin lokacin data tashi ta nufi wani table din dake kusa da inda take zaune. Takunta da yadda jikinta ke juyawa. Ajiyar zuciya tare da wani nishi gaba daya ya sauke lokaci guda. Da sauri samira ta kalleshi. Rufin asirinsa yana sanye da dark glass a idonsa. Da ta gama dagoshi. " lafiya ahehh!!! Ina magana kayi min Shiru?" Kanshi ya shafa, yana kokarin saita natsuwarsa. " ba damuwa in kin dawo ma karasa maganar, I have to go. " ya fada cikin rawar murya " are u OK?" Ta tambaya tana tsareshi da ido, ganin yadda ya koma lokaci daya. "I'm OK." " shi kenan sai mun hadu a house, ka kwantar da hankalinka, komai na hannun Hajiya kaka, nasan she will handle it." " thanks sis, shi yasa nake sonki da yawa." Dariya tayi cike da jin dadi. " in dai ina raye ba mai makala maka abinda baka so." " thanks " ya fada yana murmushi. Cikin dabara ya daddauki picture din yarinyar da gaba daya ta tafi da imaninsa. Har Anty samira ta juya zata tafi, ya kirata, yarinyar ya nuna mata " waccan fah, gani nake kamar na santa, a wani wuri.?" Kallonta takai kan yarinyar, sannan ta kalleshi. Ganin ba wani alama a tattare dashi, he ask normal yasa ta tabe baki tare da Jan tsaki. " habiban da ake son manna maka ce, kasan bawai kwalliya take yi ba, kullun tana lullube kamar Matar liman, shi yasa ba lallai ka ganeta ba." " what." Ya fada da karfi. Ganin hankalin Anty samira ya dawo kansa tana masa kallon tuhuma, ya dan wayance. " good for her. Ni na wuce." Ya fada cikin basarwa. Da ido ta bishi har ya fice a wurin. Allah yasa ba sonta ya fara ba, don ta lura da canjin yanayinsa. Musamman yazo don su tattauna hanyar da ya dace yabi ya kubucewa auren hubby, amma gashi ko gama maganar basuyi ba ya kawo excuse, ya tafi. Bari zasu hadu a gida koma menene taji. Allah ma yasa Hajiya kaka ta aiwatar da abunda ta ce zata aiwatar, A wuce wurin.  Tafiya yake, amma gaba daya hankalinsa da tunaninsa yana kan hubby. Tabbas yaso ya cuci kanshi, bai taba tunanin haka yarinyar take ba. Wannan ai irinsu ne ake kira matan Niima. Murmushi yayi yana shafa tattausar sumar kansa. Tabbas yayi mata, ta nunawa saa, irin Matar da ko a mafarki bai yi zaton zai ci karo da ita ba. A tunaninshi is just fairy Tell ne kawai. But its real. Yanzu kam baiga wanda zai hanashi auren hubby ba. Sauri yake ya isa gida, don ya samu su tattauna da Mmn samira da Hajiya kaka, don yasan dukansu are against the marriage. " Habiba Abdul Karim Jamal Yusuf zubair Oregon " ya fada yana murmushi. ga picture dinta daya bude yana kallo, yaci saa kuwa lokacin tana murmushi, kyawawan hakoranta farare masu dauke da siririyar wushirya sun fito tar, saboda zooming din da yayi lokacin da zai dauka, abinka da babbar waya, kamar yana gabanta ya dauka...........   [04/03, 18:17] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 14       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau " amma gaskiya mutanen nan basu da mutunci. Yanzu duk yadda kuke da Hajiya Amina, da abunda zasu saka miki kenan." Hajiya Fatima ta fada bayan sun koma falon Hajiya. Hajiya Balkisu ta karba, bayan ta rike haba irin na mutun yaga abun mamaki. " ai ni kam jikina yayi sanyi, dama an ce baa ba kishiya amana, ko ba dade ko ba jima, sai ta dagaki sama ta nana da kasa, ki ganta sumi sumi, da ita kamar bata yiba. Shiyasa kullun nake gayawa Hajiya ta yi taka tsantsan, amma sai tace ai anzama daya. Mutanen yanzu baka taba sanin zuciyarsu. sai abu ya sameka." Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke " tun da dama Alhaji yayi maganar nan, na lura da take taken su, amma ban dauka abun yayi zafi haka ba. Ni a tunanina koda Habiba kwantai tayi, ita mai rufamin asiri ce, Ashe ni ban Sani ba, burun burun ake min. Allah na gani alkhairi nake nufin dukkansu dashi, ya rage nasu yanzu." " to ke da kika ci alwashi, ba tare da dogon nazariba, abun fah da kamar wuya!!! kina ganin hakan zai yiyu?" Hajiya Fatima ta fada " nima abinda na gani kenan, kin San a girme Habiba ta girma hayder tayaya zakiyi, wannan hadin. Da kin barta kawai baki amsata ba." Murmushi Hajiya ta yi " she karu ba komai bane face numbers. Hayder dai ni na haifi abuna, in sha Allah ba niba har su sai sunyi alfahari da auren hubby da hayder. Alhaji yaso su da alkhairi sun bujire, ni kam zan amsheshe da hannu bubbiyu. Ko ba komai tuwona maina kamar yadda suka fada. Ina son Habib tamkar yadda nake son yayan cikina,. Kamar yadda duk duniya a yanzu, banda mijina, bani da kamar Hauwa. Nasan kuma in sha Allah hayder yayi mata, irin Matar da nake masa fatan samu, zuwa gaba  in sha Allah zaiyi alfahari da zamowarta mata a gareshi, kamar yadda itama zatayi alfahari da zamowarsa miji gareta." " Allah yasa albarka ya kade fitina." "Amin" Hajiya da Hajiya Fatima suka amsa. " bamuga ta zama ba!!! Auren auta." Hajiya Fatima ta fada tana murmushi " ba zama kam, yanzu meye abun yi?" Hajiya Balkisu ta tambaya " eh!!! To!!! Maganar neman gidane zai zama matsala, saboda kurewar lokaci, don so nake a hada bikin gaba daya a wuce wurin. " " wannan ba matsala bane, yanzun nan zan kira kanin megidana, harkar gine gine, yake yana bada haya. In ji ko akwai available. " Hajiya Balkisu ta fada tana lalubo wayarta. Murmushi Hajiya Fatima ta yi tare da rike baki " ammafa ya kamata kafin mu fara gudanar da komai, aji ta bakin maza, tukunna." " haka ne kam, amma dai buga muji maganar gidan, don in sha Allah ba fashi auren nan." Hajiya ta fada tana kallon Hajiya Balkisu.                 ****************** A tare suka sauke ajiyar zuciya, kada kai Alhaji Jamal yayi ya juya zuwa part dinsa. Hayder da kansa ke faman juyawa, ga wani bugu da zuciyarsa keyi kamar zata faso waje. Bakin ciki, da takaicin magan ganun da  Hajiya kaka ke yi. Wanda duk akan kunnensu shida Alhaji Jamal. Suna tsaye suna magana, suka fara jin hayaniya, da sauri suka nufo part din matan, jin muryar Hajiya kaka yasa Alhaji Jamal Jan birki, ganin haka shima hayder din ya kasa shiga. Ba abunda ya kara daga hankalin hayder irin furucin Hajiya. " in sha Allah gobe iwar haka Habiba ta zama Matar Aliyu hayder. " me hakan ke nufi? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, allahumma ajirji fi musibayi wakhlufli khairan minha. Ya furta a saman labbansa. Da kyar yake daga kafarsa, ya nufi part din su Abdul Karim, yayi sa'a ba kowa a dakin. kwanciya yayi dafe da kansa, dake barazanar tarwatsewa. Yana jero adduai a saman labbansa. Alhaji Jamal na shiga part dinsa ya kira Hajiya Amina (Mmn samira) a wayarsa. Zama yayi Yana huci cike da bacin rai da damuwa. A hankali ta tako zuwa cikin dakin, daya daga cikin kujerun dake kusa dashi, tama kanta masauki. Tare da gaishe shi. Shiru ya mata ba tare daya amsa gaisuwar tata ba. Ido ya zuba mata, wanda ta kasa jure kallon da yake mata ta maida kallonta gefe. " meke faruwa a gidan.?" Ya jeho mata tambaya Cikin alamun rashin gaskiya ta kalleshi tare da kauda idonta " ba abinda ke faruwa, ko wani ya fada maka wani abu ya faru ne?." Takaici ne ya cika Alhaji Jamal ganin yadda take son raina masa hankali " ba gayamin akayi ba, da kunnena naji duk abinda Hajiya kaka ke fada." Tabe baki tayi " meye laifi to don ta fadi gaskiya?" Baki sake Alhaji Jamal yabi Mmn samira dashi cikin tsananin mamaki. He can believed Mmn samira ce da kanta.  " kin ban mamaki, ban taba tsammanin haka daga gareki ba, ko don kusancin dake tsakaninki da Hajiya. Sannan da dai nawa ne? Koyana so ko bayaso jibi in sha Allah zaa hada danasu Aisha, kun dade baku daga hankalinku ba." Wani kallo Mmn samira ta zuba masa, da tun aurensa da ita bata taba masa ko makaman cin saba. " kamar yadda yake danka, haka zalika yake dana, haka kurun bazan zauna a ci gaba da cutata ba, abin baima tsaya kaina ba, sai an hada da yarana? Abdul da kansa ya ce baya sonta, banga dalilin da za'a masa dole ba, shima a barshi ya zabi abinda yake so kamar sauran yaran. Tayaya za'a jona masa bazawara?, bazawarar ma juya? Sannan a ce kar in yi magana?, ina kallo a cukeni a cuci dana. Naga in da namijin ne itama tana dashi, in gaskiya ne, shi ya aureta man. Za'a zo a kitsa maka abu ka hau ka zauna, Nasan duk ita ce mai wannan kinbibin hadin, don haka ta hada da danta badai dana ba." Alhaji Jamal mamaki gaba daya ya cika shi. Tabbas abin ya wuce inda yake zatonsa. Mmn samira zai ce tunda ya aureta bata taba daga masa murya ba irin yau. Don haka mamaki da bacin rai yasa ya kafeta da ido. Kin kallonsa tayi sai data kai inda taso kaiwa sannan ta yi shiru tana huci da huhhura hanci. " shi Abdul Karim din da bakinsa ya ce miki baya sonta?" Ya tambayeta " so sai ma, kaima ya kamata kasan baya sonta tun ranar daka taramu a nan. Don da yana sonta nan take zai amsa maka." Kada kai Alhaji Jamal yayi " shi kenan tashi kije." Haka ta fice a dakin tana faman hura hanci. Da ido ya bita yana mamakin mutanen duniya, Tabbas in da ranka kasha kallo. Fita yayi, ya nufi gidan Alhaji babba.                     **************** So koda Abdul Karim ya iso gida, bai samu shiga wurin Mmn samira ba. Don ya samu compound din gidan cike da abokan Ahmad sai engrn Sahabi da salis. Gefe kadan kuma su Hafiz omer, junaid, amir, alim, da Hafiz ne suma jikin motar amir suna nasu hirar. Direct wurin su Ahmad ya nufa, bayan bayan ya paka tashi motar. an gaggaisa ya dale motar salis dake kusa data Ahmad in da wasu na jingine a jiki, wasu na kan kujerun roba. Kasan cewar Abdul Karim ya saba da yawancinsu, kusan duk ana tare, yasa shima ya shiga aka ci gaba da hirar dashi. Duk da deep down his heart tunanin hubby ne dankare a ransa, da son sake sakata a idonsa. A hankali get man ya wangale kofar get din. Motoci ne suka fara shigowa dan kare da mata. A hankali ta sawo kan motarta cikin compound din. Wanda gaba daya hankalinsu Ahmad yana Kansu. Ita da yusra ne a gaba, sai mutun biyu, kawayenta na islamiyya, da suka mata kara, sai humaira ta uku. Hira suke sha da dariya don akwai daya mammy mai ban dariya a cikinsu. A kusa da motar ummu khulsum ta faka tata motar. " dadina da zuwa gidan nan akwai hadaddun samari, mai powder ta dan miko min in dan murza, kafin na fita ko nayi ciniki."  Dariya suka kwashe dashi suna kallon mammy data hakikance sai sun bata powder. Yusra ta mika mata " gashi Allah ya kawo kasuwa, musha biki." Murmushi tayi ta amsa tana " amin." Tsaki hubby ta ja, hango su Engr da suka kafe motarsu da ido. Kallonta yusra tayi, tare da kallon su Engr tayi dariya " gafa muta nenki?" " na gansu, ban son gaishesu wallahi, dana San suna gidan nan ba abunda zai shigo dani yanzu." Hubby ta fara " gaisuwa ai dole, ko baku gaishe suba ni sai na gaishesu don na hango new catch dina." Mammy ta fada tana murmushi " wanne a ciki?" Dayar ta tambayeta " anki gaya miki, salon amin snatching. " dariya sukasa jin salon data amsa din. " wannan shine riga malan masallaci, tun kan catch din yazo hannu, ana tsoron snatchers. " yusra ta fada, tana balle murfin motar ta fita. Hubby ta Gyara zaman gyalen after dress dinta tayi da kyau. Kamar ta sani ana gama lunch zaa taho ta dora after dress dinta a kan kayan. Fitowarta yayi dai dai da isowar su junaid, gaisheta sukayi, cikin mutunci tare da tambayar kayan lunch. Key ta mikawa hafiz, akwai abubuwa a but, in kun kwashe a kawo min key dina. "Sai Anty!! Allah ya bar mana ke." Hafiz omer ya fada yana murmushi. Dole ta inda su Ahmad da tawagarsa zasu wuce, zuwa part din su Hajiya. Tun suka doso idon salis, engrn da Abdul Karim na kan hubby, harta iso. Yaya Ahmad ta fara gaisarwa, kafin ta musu jam'u cikin sitiriyar miryarta mai zaki, da dadin sauraro. Sauran ma gaishesu sukayi, suka wuce ciki. A jiyar zuciya dukan su suka sauke a tare. " engr wai ya maganarku da hubby ne ta kwana?" Daya daga cikin abokansu ya tambaya Murmushi Engr Sahabi yayi " Ku tayani da addua, yarinyar akwai kafiya wallahi, ina nan ina kokarin shawo kanta, sai dai lamarin suraj kangiwa dake nemanta yasa jikina ya fara sanyi." " haba faduwar gaba, asarar namiji, sai dai in dama ba sonta kake yi ba." Daya daga ciki ya fada " kasan irin son da nake mata kuwa? Ina sonta fiye da yadda labbana zasu iya misaltawa, ina sonta, ina son halayyarta, after all duk Wanda ya samu wannan ya gama dace da mata tagari, I known how happy she made my friend, when they are together. Ya fada yana smiling " gaskiya kam ta hadu ba karya. Amma ya kamata kai da salis daya ya hakura ya marama daya baya, ta haka zakufi saurin shawo kanta, akan dukkan Ku kuce kuna sonta at the same time. " Kallonsa Engr Sahabi yayi " do'sen matter, an ce kasowa dan uwanka abinda kake sowa kanka, duk kanmu muna da reasons da yasa muke son aurenta, Duk Wanda ya samu a cikinmu we are happy. Abinda kawai zai bakanta mana shine, wani can daga waje yazo ya aureta." " haka ne kam. Amma ina ganin kamar da wuya ta amincewa dayanku." Dayan ya fada " we keep on trying." Salis da sai lokacin ya samu bakin tofa nashi ya fada. " ammafa duk laifin Ahmad ne! Naga suna mutunci sosai, da zai shiga maganar da komai yazo da sauki." Daya ya fada Harararsa Ahmad yayi " ka rufa min asirina, kai da bakinka kace muna mutunci? Hubby duk Wanda zai mata maganar aure yan zunnan duk mutuncin da kukeyi zaku bata. Ni kuma I don't want that." " nifa ban gane maka ba? Ina da question mark da yawa a kanka? Anya!!" Salis ya fada yana tsare Ahmad da kallo Murmushi Ahmad yayi. " koma dai menene kowa tashi ta fishshe shi." Kowa dake wurin ido ya zubama Ahmad da yake ci gaba da danna wayarsa, kamar bai San abunda suke yi ba. Engr ya kalli salis " dama na fada maka ai! Ko ban fada ba?" Salis ya sauke ajiyar zuciya " ka fada kam" ya fada a takai ce. " kai amma yarinyar nan tayi kasuwa, kana ganin yadda kangiwa ya haukace a kanta? Kusan a sati in bai zo garin nan ba yazo sau biyu, da da sai ya kwashe fiye da 2month bai shigo garin Kaduna ba, duk da iyayensa na cikinta." Daya ya fada yana jin jina kai " shawara!!; Ku samu manyanta da maganar don kowa yasan matsayarsa, tunda ta wurinta ba nasara, nasan in sha Allah su za suyi nazari sosai kan abun." Daya ya fada " ka kawo shawara mai kyau, nima nayi tunanin haka." Salis ya fada Abdul Karim kam ya zama photo,sai kallonsu yake one after the other. Shi a tunaninsa hubby rasa mai aurenta tayi, yasa daddy son hadashi da ita. Yanzu ya gane manufar daddyn akan son dayansu ya auri hubby. In har abokan Yusuf zasu so su maye gurbin Yusuf saboda sanin kyawawan halin hubby, ina ga su kannensa. Shi duk zaman Yusuf da hubby bai da wani cikakken labari a kai, don lokacin da akayi yana Malaysia, in yazo Hutu yawanci yana Lego's gidan uncle omer zuwanshi gidan Yusuf sau daya, zuwansa bayan auren, da yaje ganin daki, tare dama yayansa Allah yasa albarka. Saboda bai samu damar zuwa lokacin bikin ba. Sai lokacin yake tuna tarba ta karamci da hubby ta musu a lokacin, shida arif fist born din Alhaji omer. Da yadda sukai tayiwa yayan nasu dariyar ya auro Small girl, gashi da alamar bata waye ba, saboda zunbulelen hijab data sako har yana Jan kasa, "ga gida har gida, amma ba mata" kalaman arif ya tuna a lokacin. Kalaman yaya Ahmad ne suka dawo masa bayan fitowarsu daga part din Alhaji Jamal " a matsayina na dan uwanka, shawara daya zan baka. Karka kuskura ka bijirewa wannan auren, ka karbeshi da hannu bibbiyu, na tabbata zakayi alfahari dashi. Karka biyewa kyale kyale, kyawun zuciya da addini shine abun lura. Hakika daddy ya maka zabe mai nagarta, wanda duk cikinmu ba wanda ya dace da hakan. Damarka ce wannan, in kayi wasa ta kufce maka, na tabbata zakayi dana Sani mara iyaka, lokacin da ba zai maka anfani ba." Amsar daya bashi a lokacin ta dawo masa. " in haka ne mai zai hana kai ka aureta, naga kana da space na mutun uku, a gidanka. Ko ba komai kai ka taba aure, kaga bazawari da bazawara kenan. Kunfi mach ma,." Murmushi Ahmad yayi masa " kai din saurayine? Karka dauka bansan duk sharholiyar da kake yi a abuja da Lego's ba? Gara ita ta hanyar auren sunna ta rasa budurcinta, kuma ga jininka. Kai fa? Allah kadai yasan yawan matan da kayi tarayya dasu. Kaga kenan kai ne baka dace da ita ba. Da kake fadin in aureta, Wait and see ka ce baka so ka gani." Kunyar Ahmad ce ta kamashi a lokacin, bai taba tsammanin yasan abinda yake aikatawa a boye ba,no wonder ko waya sukayi ya dinga masa waazin yaji tsoron Allah, ya tsare dokokinsa, kar yaga ba idon yan'uwa, ya aikata duk abinda yaso, yasan Allah na kallonsa, kuma yana jiran dukkan bayi a mada kata. Ba abunda yake boye a gareshi game da bawa, don haka ka yawaita tuba, tare da nisantar miyagun ayyuka. Kallon sa yakai kan Ahmad dake faman daddanna wayarsa. So da kaunar dan uwan nasa yaji ya kara ratsa zuciyarsa. In sha Allah zai karbi auren hubby da hannu bibbiyu, sannan zaiyi iya kokarinsa ya kyara tsakaninsa da mahaliccinsa. Ya tabbatar Ahmad na son hubby sosai, sai dai ya kasa gane abunda yasa ya zabi ya hakura, don ya tabbata daya gayawa daddy yana sonta ba wanda zai sakosu a ciki. Kamar Ahmad yasan shi Abdul Karim ke kallo, ya dago suka hada ido, murmushi ya masa da kallo mai nuni da kaga maganata ko?" Lumshe ido Abdul Karim yayi tare da jin son hubby na kara ratsa zuciyarsa. Allah Allah yake dare yayi ya samu Daddy ya shaida masa ya amince da auren hubby, don bazai iya jira har nan da 5days ba, kamar yadda daddy ya diba masa, don yayi shawara ba....... har yanzu guy din nan bai daga waya ba fah!!?" Hafiz ya fada bayan ya sauke wayarsa daga kunne. Tsaki ashir yaja, bayan ya share bakinsa da tissue, yana ture plate din gabansa. " Ina kuke tunanin ya shiga?" Kafada Hafiz ya daga " I don't known, tun dazu dai da muka rabu dashi a gidansu alim, kan daddy na nemansa, bamu sake ganinsa ba. Gashi  ko picking calls din ma bayayi. " " duk rainin hankalin hayder, baya kin daga waya. Maybe daddy ya aikeshi ne." Inji Hafiz omer " kai I don't think so. I'm filling some thing is wrong " junaid ya fada " kun tambayi su Yaya Ahmad? Ko sun San inda yake?" " they don't known where he is." " let me trace his number. " junaid ya fada yana fito da wayarsa a pocket. " a kwai dan iska, da kasan da tracing din ka barmu cikin damuwa." Amin ya fada " I totally forget, sorry. " For some second junaid ya dago yana kalonsu. " I can believed yana cikin gidan nan."  " are u sure? " kai ya kada. " OK Le's cheek Abdul part. Don nan ne kawai bamu duba ba." Ashir ya fada yana mikewa tsaye. Dai dai lokacin hayder ya fito daga part dinsu Abdul. Da kallo suka bishi, kallo daya sukawa juna suka tabbatar some thing is wrong with him. Wurinsu Ahmad ya isa, suka gaggaisa, ganin yanayinsa duk suka shiga tambayarsa lafiya? Murmushin karfin hali yayi " I'm not filling fine. " ya fada cikin muryarsa mai dadin sauraro da Jan aji. Rungumeshi Ahmad yayi, yana tambayar abinda ke damunsa. Kansa ya nuna masa,. " kasha magani ko muje hospital? " ta tambaya cikin nuna tsantsar kulawa.  " no I'm ok. I take a drug. Fatan samun sauki sukai ta masa. Kafin ya nufi cikin friends dinshi. " what is wrong with u?" Junaid daya tareshi tun kan ya iso, ya fara tambayarsa. Kamar yadda ya fadawa su Ahmad haka suma ya gaya musu. Duk da junaid bai yadda da abunda ya fada ba, amma ya bashshi a hakan. Kayan ciye ciye ne burjik a wurin, don duk abinda aka ci a wurin sai da ta diba musu, a kyawawan containers. Ba suba har su Ahmad ma sun samu. Cake din daya hango a gefe, ya janyo. Cake din ya burgeshi da gani zai yi dadi. Duk da cake ba cimarsa ba ce, musamman cup cake, amma wannan ya bashi shaawa. Sai da yakai daya bakinsa ya gutsura bayan yayi bismillah. Ya kalli Hafiz omer da tun dazu yake kallon hayder yana karantar yanayinsa. " ina cuka samu wannan delicious cake din?" Amir ne ya amsa shi da " Anty hubby, kasan jiya da muka rabu dakai gidan mommy Hauwa muka je, so mun samu tana aikin cake din, kamshi ya ishemu, kasan hali, ta hanamu dandane, wai na lunch ne, baa ce taba kowa ba. She promise us, zata ajiye mana namu after lunch, she keep her promise." Ai kafin amir yakai aya hayder ya furzar da cake din bakinsa, ruwan dake hannun Hafiz ya fige, ya fara kuskure bakinsa dashi. Kallonsa suka tsaya yi baki bude, cike da mamaki, duk da sun San ba shiri tsakanin hubby da hayder amma sun San abun bai kai haka ba. Dariya Hafiz yayi " na banza, don na tabbata wani ya wuce ciki." " Allah ya kyauta. Naga ranar da zaku daina wannan abu kai da Anty. Ko ba komai ai you have to respect her, she is elder, and aur friend sister." Hafiz ya fada " a kwai abunda ke damun kwakwalwar yaron nan, Ku barshi kawai." Hafiz omer ya ce " waye yaron?" Hayder ya fada yana kallon Hafiz omer Dariya Hafiz omer yayi tare da daga hannun serenader " sorry. " Junaid dai na daga gefen hayder yana kallon ikon Allah. Duk da bai ji dadin yadda hayder yayi ba, amma ko a fuska bazaka gane hakan ba. Kiraye kirayen sallar da suka jiyo, yasa suka nufi masallaci don gudanar da alwala da sallar magrib.                ******************* Da sallama suka shigo, su Anty samira da munaya, sai sauran yan uwansu da suka dawo daga wurin lunching, basu kai ga shiga part din Mmn samira ba. Suna tsaye a harabar wurin ana maida yadda akayi, a wurin lunching, Su hubby suka shigo. Kadan daga cikinsu suka amsa musu sallamar. Ganin yadda suka kuresu da ido, yasa su hubby suka gaishesu in jam'u. Har sun wuce samira ta ce " kai Allah mun gode maka, yanzufa yan matama kwantai suke, balle zawarawa, shiyasa sai kiga ana neman likawa jamaa dole." Ta fada da karfi yadda su hubby zasu jiyota. " oho!!! Kuma!! In ta wuce kan mijina, ta fada kan kowama, bai daman ba." Munaya ta fada tana hararar bayan hubby. Basu kai ga jin karashen maganar ba, suka shige, duk da su yusra basu San kan zancen ba, sun dauka hira kawai suke, amma ita hubby ta San da ita suke. Ranta ya baci amma bata da lokacin batawa a Kansu. Koma mai zasu ce, sun dade basu fada ba.                 ***************** Alhaji Jamal bai shigo gidan ba sai to 12am. Allah yasa Hajiya ranar ita keda girki. Hakan ya bata damar tattaunawa da mijin nata, a tsanake. Abdul Karim kam bai samu shiga wurin Mmn samira ba, ana idar da sallar isha'i, suka fita da arif daya iso daga legos, lokacin da suka shigo gidan already late. Anty samira ma data kirashi hakuri kawai ya bata, kan zasu hadu da safe. Hayder ranar raba dare yayi yana addua. Tare da kai kukansa ga mahaliccinsa. Don har ga Allah baya jin son hubby ko digo a zuciyarsa. To yarinyar da ko soyayyar yan uwantaka bata hadasu ba, ina ga soyayyar aure? Hankalinsa ya dan kwanta, ganin har ya bar gida, zuwa in da suke kwana, saboda baki, Hajiya bata masa maganarba. Yana fatan Allah yasa kunnensa ne bai jiyo masa dai dai ba.                 ******************* Tagumi mommy Hauwa ta zabga bayan ta gama jin bayanin bakin Alhaji Munir. Gaba daya lamarin ya isheta ya daya, amma kullun a kazo maganar aure sai ran kowa ya tashi, mu samman wannan karon. Ajiyar zuciya mommy Hauwa tayi tare da kallon maigidan nata. " da kamar wuya, wai hurguwa da auren nesa!!! Wannan hadin gaskiya bayyi ba, kowa yasan tsakanin hubby da hayder kamar masu ganin hanjin juna, tun tasowarsu, har zuwa yanzu. Sannan hubby ita take gaba dashi a haife, ta ina zaa fara wannan danyen aikin? Kudai canza dabara gaskiya, kar azo ayi abinda za ayi dana sani." Zama Alhaji Munir ya gyara, tare da fuskantar mommy Hauwa da kyau. " kin ban mamaki, ban taba tunanin wannan magana zata fito daga bakin kiba. Har kin manta da halaccin yar uwarki gareki? A tunanina ko yayayyen yaro Hajiya ta bukaci hada Ummi dashi bazaki ja da ita ba, balle danta na cikinta. Meye sharuddan da ya can -can-ci a ba namiji aure? Wannene hayder bai cika ba? Ban zama butulu ba, bazan taba manta alkhairi Hajiya da mijinta ba, kai harda su Alhaji babba, irin karamci da mutunci, da soyayya da suka nuna min, tun haduwata da omer, har zuwa jajur cewa da sukayi wurin ganin na aureki, har zuwa yanzu. Ni ko mai zan musu in biyasu? Babu!!! Na dade ina rokon Allah ya bani ikon saka musu da abunda suma zasuji dadi  komai kankantarsa. Auren Ummi da Yusuf ba karamin dadi ya min ba, duk da kalubalen da ni kaina nasan dasu. Haka ma yanzu ina son ki Sani, daga ke har Ummi ba shawararku nake nema ma. Umurni nane dana mahaifina, gobe in sha Allah bayan sallar jumaa zaa daura auren Ummi da hayder. Don haka duk abunda ake bukata ki natsu ki rubuta, gobe in Allah ya kaimu aje a siya. Don Sunday zata tare dakin mijinta, kamar sauran yan uwanta." " bana kin hadin nan, kamar yadda kake fada, hasalima nafi kowa murna. Abu daya zuwa biyu ke damuna. Sanin halinsu, sai nake ganin zaman nasu kamar da wuya a samu yadda ake so." Mommy Hauwa ta fada tana sauke ajiyar zuciya " addua zaki bisu dashi, ita suke bukata. Lokacin da zasu shirya kina ina? Karki manta ko ba komai yan uwan juna ne! Aure ya wuce duk inda kike zato. In sha Allah sai kin ce gara da akayi. Hakika nayi dacen suruki daya tamkar da dubu., hayder yarone, amma mai halin manya. Ke kanki abunda kika sani ne, ba yarinta a tare dashi, sai kamala, da mutunci, da sanin ciwon kai,da sanin ya kamata, Ga kamewa." Murmushi mommy Hauwa tayi " hakane kam, sai dai yarinyar taka fa zaa sha fama." " don't mind her, barni da ita. Su gwaggo da tawagarta na nan isowa gobe, a gyara part din can su sauka a ciki, don gayya zatayi, kamar yadda ta fada min a waya. Tayi farin ciki sosai da jin wannan maganar." " ai fa? Bikin mutuniyarta, don ma lokacin yazo a kure." " haka ne!!; Ummi da gwaggo kam ai sai Allah, don ma ba kiji yadda take murna ba, ke kyace an mata albishir da gidan aljannah. " " mutuminta ne Hayder, abun ya zama mata biyu. Takwara da balarabenta." Mommy Hauwa ta fada tana murmushi Murmushi Alhaji Munir yayi, tuno drama din gwaggo da hayder. Gwaggo akwai son hira, ga jininsu ya hadu sosai da hayder, hayder ba Hausa sosai, gwaggo ba larabci, so in kaji hirar dole kayi dariya, mu samman yadda yake takar karewa sai yayi Hausa, in ya kakare gwaggo na dariya zata murda nata larabcin ta masa bayani yanda zai gane. In kana kusa, ba kayi wasa ba har fitsari sai kayi a wando, don dariya." Hayder daga turanci, French, sai larabci sune manyan yaren da yake ji in yanayi kamar a bakinsa aka kirkiro. Hausa yana jin duk abinda zaka fada, mayar wane sai a slow. Don gidansu gaba daya baa wani yare banda arabic. Friend da sauran yan uwa da basa ji, sai dai suyi turanci. A school nema ya samu ya ji hausar don a gida ko iyayensu mata basu isa suyi musu Hausa ba, dokar Alhaji Jamal ce, dole a kiyaye a zauna lafiya.             ********************** Yauma tun daga sallar asuba, Alhaji Jamal bai dawo gidansa ba. Hakan yasa basu hadu da Abdul Karim ba. Koda ya shiga cikin gida, Hajiya kaka bata samu damar mayar masa da yadda akayi ba, saboda yana tare dasu arif. Anty samira kuma suna part din yara matan gidan. Ko da sukaje gaishe da Hajiya ita ma bata nuna masa komai ba. She act normal kamar yadda ta saba, duk da taji zafin jin cewa baya son hubby.                   ***************** Part din Alhaji Jamal ta ja hayder don gidan ba masaka tsinke da jamaa. Duk da faduwar gaban da yake, bai yadda ta gane tashin hankalin da yake ciki ba. Bata kawo komai ba, ganin ya dan fada mata, ta daukeshi matsayin stress. Kallonsa tayi cikin natsuwa. " meye matsayina a wurinka? Da sauri ya dago yana kallonta cike da far gaba. Sunkuyar da kansa kasa yayi, yana jin zuciyarsa na karyewa. Saboda tuno girman matsayinta a wurin shi. " matsayinki gareni ya wuce yadda labba da harshena zasu bayyana, kamar yadda girman hakkinki a kaina ya girmama, har musulunci ya mana umurnin kyautatawa gareku,  saboda girman matsayinku, ya sanya aljannarmu a kalkashin kafafunku, wanda sai kun daga kafin mu samu damar shiga aljannah, wadda take burin duk mai imani." Murmushi Hajiya tayi, tana kokarin maida hawayenta. " ina neman alfarma a gareka, zaka iya mun?" " umurni kawai zakiyi, bakya bukatar alfarma a gareni. Ni da duk abunda na mallaka muna kalkashin ikonki ne, duk abinda kika ce, matukar bai kauce wa shariar Islam ba, an gama." Hawaye mommy dake kokarin mayarwa suka fara bin kuncinta. Hakika hayder ya cika dan halas da daya tamkar da dubu, abin alfaharinta. Hakika tana daya daga cikin iyaye masu saar yaya a duniya. ba abunda zata ce sai Alhamdulillah. " an taba mutuncina, an yi challenging dina in har na cika yar halas in aura ma ummi." Tayi shiru tana goge hawaye Da sauri ya taso zuwa inda take zaune, rigarsa yasa yana share mata hawayenta, bai damu da kwalin da ya samu wurin zama a fararen kayan jikinsa ba. Ya fara lallashin Hajiya. " in wannan ne ki kwantar da hankalinki, na miki alkawarin zan auri Habiba, kamar yadda kika bukata." " na gode hayder Allah ya maka albarka, ya baka yaya na gari, ya baka abinda bazai kareba, ya karemin kai daga dukkan sharri." "Amen "ya fada " ka je ka fara shiri, don in an sakko masallaci zaa daura auren. Sunday zata tare, already an samu gidan da zaku zauna, yanzu zan je mu gani, bayan daurin aure sai kuje kuma, in akwai gyare gyare ko wani abu da ake bukata. Sauran kayan lefe duk zanyi in sha Allah sai kayi alfahari da wannan auren." " na gode sosai, amma ki bar min kayan lefen zanyi da kaina, in kunyi estimate din amount din kwa gayamin in bayar." " shi kenan." Hajiya ta fada a part din ta barshi, don ya kulle tunda ba kowa. Tana fita ya hada kanshi da gwuiwa ya saki wani marayan kuka. Rabonsa da ya samu kanshi cikin irin wannan tashin hankali da bakin ciki, har ya manta. Sai daya sha kukanshi, ya shiga toilet din daddy ya wanke fuskarsa, ya nufi masaukinsu. Zuciyarsa cike da tsana da jin haushin hubby. Adduar yaye bakin ciki yayi ta maimaitawa saman labbansa har ya isa. Sultan guise inn dake kusa dasu. Don tunda aka fara biki, shida su Hafiz omer sukayi kaura zuwa can.                ****************** Gida yayi kyau, well polished. daga Hajiya har su, Hajiya Balkisu gidan ya burgesu.  Duplex ne, falo biyu a kasa, kowanne da toilet dinsa. Sai kitchen, store, sai dan karamin daki a karamin falon. Sama kuma dakunan bacci ne guda uku da falo daya. Kowanne  bedroom da toilet dinsa. Gidan akwai fili sosai, da motoci kusan goma zasu iya parking, yasha interlock. Ga shuke shuke na fruit da flawers, sai dakin maigadi da toilet. Gidan na Unguwar malali ( sami close) sabon ginine baa dade da gama shi ba. Yaji finishing na zamani, komai high quality standard na gidan. Nan take Hajiya ta biya kudin 2 years bayan sun koma office din kanin mijin Hajiya Balkisu. Kiran mommy Hauwa Hajiya tayi ta shaida mata an samu gida, ta turo masu furnitures din su auna.                 ***************** Kuka take harda birgima, su Hajiya salwa sun sha lallashi har sun gaji.  Da bulala mommy Hauwa ta shigo dakin, kan hubby tayi gadan gadan cikin fushi. " dan gidanku, me yasa shi da ya gaya miki, baki masa wannan haukar ba? Sai mu da kika raina? Ana lallashi kina kara botsarewa." Da sauri Hajiya tunba ta tare mommy Hauwa " haba ki bar yarinya ta yi kukanta! Taya zaa bugeka a hanaka kuka? Don haka karki fara dukanta. Hubby da tun shigowar mommy Hauwa da sharbebiyar bulala, ta boye bayan salamatu. " don Allah karki bugeni, na daina, amma ki cewa daddy ya aura min koma, wane ne, ko kuturune, ko makaho, duka na yadda amma banda hayder don Allah..,........     Not Edited.......[05/03, 14:03] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 15       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Murmushi mommy Hauwa tayi, duk da dunbin tausayin yar tata. " hayder din dai da baki so, shine. Gara ma ki kwantar da hankalinki, don ba abunda zaa fasa." " kiyi hakuri, kiwa iyayenki biyayya, matukar sunyi don Allah ba don wani abu na duniya ba. To in sha Allah zakiyi alfahari da hakan. Ballantana Sani kanki ne, duk abunda su kayi, sunyi ne don maslahar, da kuma kyakyawan manufa." " Allah rainani zai kara yi." Hubby ta fada tana kara sake kuka. Duk yadda su Hajiya suka so daure dariyar data taso musu kasawa sukayi. Cikin dariya Hajiya salwa ta ce " banda abinki Ummi, yanzu kuma ai ke ce a kasa. Maganar raini duk bata taso ba, dole ki masa biyayya don aljannarki na kalkashin kafarsa. In kina neman aljannah to dole ki ajiye komai ki rungumi aurenki." Ta bude baki zatayi magana mommy Hauwa ta buge bakin. " rufawa mutane baki, ana magana kina mayarwa, kamar saoinki. Allah ki shiga hankalinki dani. Shi bai yi kukan bai son kiba, sai ke? Yana yaro dashi son kowa kin Wanda ya rasa, an hadashi da uwar mata." " aa Hajiya Hauwa!!!! Yarinyar tawa kike kira uwar mata, duka duka nawa ummin take? In kyau ne, nima ai baa nunama diyata ba." Dirin shigowar motoci gidan ya sa hankalinsu ya koma can. Hubby zamewa tayi daga jikin salamatu ta shige dakinta, kuka ta saka iya karfinta ta fada saman gadonta, ta ci gaba daga inda ta tsaya. Su gwaggo ne, da tawagarta. Lallai kam gwaggo tayi gayya kamar yadda ta fada. Kun San mutanen karkara da son zuwa bikin nesa!  Balle sun samu motoci available. Direct part din da aka gyara musu aka wuce dasu. Tare da cikasu da kayayyakin abinci, da na sha, da duk wani Abu da zasu bukata.                ****************** Hafiz omer ya samu a reception. Da sauri ya nufo hayder ganinsa a hargitse. Rungumeshi hayder yayi yana sauke ajiyar zuciya. Cike da tashin hankali don bai taba ganin hayder a yanayin da yake ganinsa jiya zuwa yau ba. Na yanzu is worse. " what is happened? Don't Tell me is notting, tun jiya na lura some think its not right? Hafiz omer ya fada yana dan bubbuga bayansa. Sakinsa yayi, tare da Jan numfashi. Hafiz omer ido ya zuba masa cike da damuwa. " ka gaya musu, a kwai daurin aure a sultan bello masjid, after sallar jumaa."  " daurin auren wah?" Hafiz omer ya tambaya. Ko kafin ya karasa tambayar hayder ya wuce sama, zuwa dakinsa. Da kallo Hafiz omer ya bishi, yadda yake hada steps 2 to 3, ya haye. Kai Hafiz omer ya kada tare da cewa " Allah ya kyauta"  wayarsa ya Ciro ya shaidawa su junaid. Don  duk a tunaninsa daurin auren daya daga cikin yaran abokan daya daga cikin  daddies dinsune. Yana shiga direct toilet ya wuce, wanka yayi tare da dauro alwala, duk da lokacin, ba lokacin nafila bane. Bayan ya shirya cikin daya daga cikin kayan da suka dinka don fitar bikin su Ummul khair. Shadda ce, mai matukar kyau da tsada milk color. Duk da dan fadawar da fuskarsa tayi,   yayi kyau  sosai. Time ya duba to 1pm daga hannu yayi, ya karanto suratul fatiha x7, sai  karshen suratul bakhara. Sannan ya fara jero adduar jagorancin ubangiji, game da lamarinsa da hubby, ya bashi ikon yima iyayensa biyayya.             ******************** Zamewa tayi daga kan gadon, ta kifa kanta cikin pillows ta saki kuka mai tsuma rai, har numfashinta na shishshidewa. Gwaggo ta matso kusa da ita, cikin tausayawa, da sanyin jiki. " haba takwara, aure an riga da an daura. Balarabe dan uwanki ne, kin san shi, kin San daga inda ya fito. Yanzu ba abinda ya rage face kiyi biyayyaya ga Allah da manzonsa. Kiyiwa iyayenki, da mijinki biyayya." Maganar gwaggo ta kara sa hubby kara fashewa da kuka, ji take kamar gwaggo ta watsa mata ruwan zafi, jin tace wai hayder mijinta. Dago fuskarta data jeme, tayi ja, ido sun kunbura, don kuka, cikin dasashshiyar murya da bata fita sosai ta bude baki zatayi magana, ko harafi daya ta kasa furtawa. Sai hadiyar zuciya take. "Ayya har yanzu kukan ne, bai kare ba? Ki bar kukan nan haka zai cutar dake. Aure ne an rigada an daura, ba mu da abin yi, a yanzu. Na fahimce ki, kiyi hakuri da abinda iyayenki suke so, in sha Allah zakiyi alfahari da hakan." Inna shatu ta fada tana shigowa dakin. " Allah na tsaneshi?" Hubby ta fada cikin dashewar murya. " to sai me in kin tsaneshi? Mu muna son sa, kafaffiya. Mommy Hauwa ta fada Harara gwaggo ta watsawa mommy Hauwa. " ana lallaba yarinya kina neman ballo wani ruwan?" Daukar abunda ya kawota tayi ta ficewarta.                ******************* Gaba daya mamaki ya cika su Ahmad da daukacin jamaar da suka San gidan Alhaji Jamal. Daurin aure kam yayi jamaa sosai. Abdul Karim gaba daya hankalinsa ya tashi, ganin abun yake kamar almara. Haka ta kasance gasu junaid da sauran abokan hayder. Da kallo suka dinga binsa. He act normal, amma deep down his heart, shi kadai yasan yadda zuciyarsa ke suya. Duk yadda suka so jin Karin bayani daga bakinsa, basu samu ba. Haka sukaita gaisawa da abokan su Alhaji Jamal da sauran family and friends. Kowa na masa Allah ya sanya alkhairi. Rungumeshi Ahmad yayi, yana masa congrat. Abdul Karim dai ya kasa ko kwakwkwaran motsi, sai bin hayder da kallo yake, da sauran iyayensu da kakanni kowa ka kalla yana cikin matukar farin ciki, da anna shuwa. A haka suka dungumo zuwa main house.              ******************* A tsakiyar bedroom din Mmn samira, Hajiya Fatima, da wasu mutun biyu da suka mata rakiya, suka ajiye kwalayen sweet, dabino, da biscuit. Buda daya daga cikinsu ta rangada har sau uku. "Cika alwashi sai dan halas, taka haye baya i'yawa. Allah yayi, alkawarin Allah ya cika, mai kyashi, da hassada sai kallo. Da daya tamkar da dubu, farin wata sha kallo, yaro mai halin dattako, kyau baa fika ba, haka ma arzikin baza a gwada dakai ba, balle ilmi da aiki dashi. Na Habiba Allah ya yarda." Guda ta kara sawa. Hajiya Fatima ta kalli Mmn samira, da yan uwanta da suka zuba musu ido suna kallon ikon Allah. " ki kwantar da hankalinki, Habiba yanzu haka ta zamo mata ga Aliyu hayder. Wannan goron albishir ne, da kuma godiya." Kallonta Mmn samira tayi, ta kalli kayan sweet din dake tsakiyar dakinta. Cikin sanyin jiki ta kauda kanta. " Allah sanya albarka." " amin in da gaske kike." Daya daga cikin matan da suka zo da Hajiya Fatima ta fada " alhamdulillah tun da an barmin jikana. Meye kuma na bita da kulli?" Hajiya kaka da ta shigo ganin abinda ke faruwa ta fada. " babu kam!" Hajiya Fatima ta fada tana juyawa don barin dakin. A bakin kofa suka ci karo da Abdul Karim na shigowa, a hargitse. Kallo daya ta masa ta dauke idonta suka wuce, zuwa part din Hajiya. Jikin Mmn samira yayi sanyi, tabbas bata kyauta ba, bata taba tunanin Hajiya zata zartar da wannan hukuncin ba, nadama da dana sani su suka lullube zuciyarta. Da bata bi zugar su samira da hajiyanta ba, da duk haka bata faruba. Koda Abdul Karim bai auri hubby ba, da ta kwantar da hankalinta an rabu cikin mutunci da ganin kimar juna. Amma yanzu wa gari ya waya. Ta bata da matar da take iyaka kokarinta na kwato mata hakkinta, ba tare da laa kari da zamowarta kishiyarta ba, kasan cewarta mara baki. Shihowar Abdul Karim ya dawo da ita daga dogon tunanin data tafi. " me yake faruwane mama?" Ya fada bayan ya zauna kusa da ita. Hajiya kaka ta amshe " meko ke faruwa, banda Allah ya kubutar mana dakai daga auren juya, second hand. Ai sai  Ka godewa Allah. " Wani kallo ya zubama Hajiya kaka kafin yakai kallonsa kan Mmn samira, da jikinta ya kara sanyi. Daya daga cikin kannen Mmn samira ta fara koro masa bayanin duk yadda abun ya kasance. Kai ya rike, hawaye na bin kuncinsa. " kun cutar dani wallahi, koda na ce ita ba irin matar da nake so ba ce, ai ban ce bazan aureta ba ko? Haka kurun Ku yanke min wannan danyen hukuncin. Ai da sai Ku bari satin da daddy ya diba min su cika kuji matsayata ko? Kun San yadda nake sonta? U have no idea?" " innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Yanzu Abdul mu kake cewa mun cutar dakai? Me yasa tun farko ka ce baka sonta, ina kai da bakinka ka gayawa yar uwarka hakan. Shine don ka raina mana hankali zaka zo ka canza managana, salon kasa a mana dariya. To tun wuri ka cireta a rayuwarka, don ta zama mallakin kaninka." Hajiya kaka ta fada Idonsa da suka kada su kayi jajur ya daga ya sauke su kan Hajiya kaka. " ina samiran tazo ta gayamin gidan uwar da na ce mata ban son hubby? Ya fada yana waige waige " ya rage naku kuma, aikin gama ya gama. Ni kaina sai da na bada shawara aka ki saurarata. Yanzu wa gari ya waya? Hakuri kawai zaka dauka, aikin gama ya gama, ka dauka Dama can ba matar ka ba ce." Cikin yan uwan Mmn samira ta fada. Mmn samira kam ta kasa cewa komai. Sai Karin nadama, da dana Sani dake nukur kusarta. " idona idon samira, sai naci mutuncinta, munafuka kawai." Abdul Karim ya fada yana barin dakin cikin fushi da bakin ciki. " a kan wata banza can kake kiran, yar uwarka da munafuka? Ko Anty babu?." Hajiya kaka ta fada tana bin batansa da kallo.                 ****************** Ko kafin su iso main house, su Hafiz sun kira daukacin friends dinsu dake garin Kaduna, sun shaida musu daurin auren hayder da walimar da zasuyi a gobe Saturday after magrib. Suna isowa sun samu wasu daga friends din har sun iso. Kowa cike da mamaki, misamman wa 'anda su kayi secondary school tare. Direct part din Hajiya suka nufa, bayan gaisuwa, hayder yasha albarka, sannan suka shiga part din Mmn samira, sai part din Mmn Yusuf. Wadda itama daga baya taga rashin dacewar abunda sukayi. Ko ba komai tana jin hayder a zuciyarta kamar yadda take jin yayanta. Da tasan abun a kansa zai kare, da ta amince Abdul fatta ya auri hubby, in yaso a hada da nata zabin. Gidansu bubby suka dun guma, don gaisawa da su mommy da sauran yan uwan hubby kamar yadda al'ada ta gada. Sun samu tarba mai kyau, kamar a hadesu, musamman gwaggo data zage su kayi ta kashe hotuna da su hayder. Bakinta har kunne, don ji take tafi kowa murna da wannan Abu. " yanzu da wannan Ummi ke kira da yaro? Wannan ai sai ya sabata a wuya ya kaita, Zaria ya dawo, baiji komai ba." Inna Maryam ta fada Hajiya salwa ta yi dariya " kin San yaran yanzu akwai saurin girma, kamar ana basu takin zamani. Kalli su junaid? Wa zai ce Ummi ce yayarsu?" " babu kam!!" Inna maryam ta fada Yau kam hayder yaga kara da karamcin katsinawa. Duk da dayawansu ya sansu. Amma yaji dadin karamcinsu gareshi. Sun sha pictures kam, kamar ba gobe.                   ***************** " don Allah sake trying number din hubby, shirun yayi yawa." Humaira ta fada tana kallon Aisha " ina ga kuje gidan Ku gani, don nasan lafiya lafiya hubby bazata kai yanzu, bata xoba, kuma bata kira ba. Ga number dinta baya shiga." Aisha ta fada Ummul khair ta mike," muje " harararta Aisha ta yi " kin manta dokar rashin fita, a kanki ko?" " share don Allah, sharf sharf zamu je mu dawo, ba tare da kowa ya farga da bana nan ba, in har ba Ku kuka fada ba."Ummul khair ta fada tana daukar mayafi. " ba ruwana wallahi." Aisha ta fada Ummu aiman ce ta shigo. "Ke kuma sai ina?" Ta fada tana kallon Ummul khair dasu yusra " Hubby's house. " ta fada a takaice. " zauna kusha labari. U can believed what is happened in this house. " Ummi aiman ta fada tana zama kusa da Ummi sulaim. " me ke faruwa?" Suka tambaya a tare. Bowl din hannunta ta mika musu cike da sweets masu dadi, da tsada. Kowa ya zabi Wanda ransa ya masa. " an daura auren hayder da hubby, dazu bayan sallar jumaa. This is the sweets for their wedding. " Ummu sulaim ne ta mike da sauri, baki na rawa, ta kalli yayar tata " ba kyau irin wannan wasan." Murmush tayi " ina wasa da ke ne, da zan maki karya? Go and ask." Kuka Asiya ta fashe dashi. Cike da tashin kankali suka juya kan Asiya. Mayafi Aisha ta jawo, suka fice ita da Ummu sulaim dasu yusra. Suka nufi gidan su hubby. A compound din suka hadu dasu junaid. " ta tabbata.? Ummu sulaim ta fada hango su hayder cikin kaya na alfarma, sai kashe pictures a keyi. " lallai abun da kamar yuwa." Aisha ta fada Duk yadda suka so jin yadda abun ya faru ya ci tura, don su kansu su Hafiz ba su san takamai mai meya faru ba. Ummu sulaim duk da ita ce gaba da hayder to tana matukar shakkarsa. Don haka kasa tambayarsa tayi.  Allah ya sanya alkhairi suka musu, tare da shigewa ciki. Hubby na zaune da daurin kirji a baikin gadonta, bayan hajja kolo ta gama turareta da wasu itatuwa masu matukar kamshi, fatarta sai glowing take. sai da Hajiya salwa ta tsaya a kanta sannan ta yadda a mata gyaran jikin. Don tana jin nauyin matar sosai. Da gudu gudu suka shigo, ana rige rige. Hubby na ganin su Aisha ta taso da gudu ta fada jikin ummu sulaim, tare da sake sabon kuka. " oh!!! Ni yau Allah na gode maka, wai ke bazaki gaji da kukan nan haka ba? Tun safe kina abu daya." Hajja kolo ta fada tana har hada kayan kyaran jikin dake baje a tsakar dakin hubby. Sai da ta dau some second kafin ta rabu da jikin ummu sulaim, kama hannunta tayi suka zauna. Suma su Aisha sukama kansu mazauni, bayan sun gaishe da hajja kolo. Kallon hubby sukeyi cike da tausayawa ganin yadda ta koma lokaci daya. " kun ga yadda rayuwata ta kare ko? A rasa wanda zaa hadani dashi sai kanin kanin bayana, wanda a haihuwar kaji, nayi jika, da tattaba kunne dashi. Yaron da na tabbata na taba goyashi a bayana, wace irin rayuwa ce wannan?" Ta fada tana hawaye. Aisha ta dafa ta " kiyi hakuri, koma me nene, na tabbata akwai babban dalilin da yasa sukayi haka." " ki rungumi kaddararki, Allah yayi hayder shine mijinki, duk da dunbin masu sonki, Allah yasa akayi dashi, alhalin ba Ku kuka sasanta kanku ba, hakan na nuni akwai hikima mai girma a tare da wannan lamari. Duk mu nan waya taba kawo hakan a ransa? Ko da wasa, amma Allah cikin hikimarsa gashi ya tabbata. Just accept the true, and deal with it." Yusra ta fara Harararta hubby ta yi da kunburarrun idonta. " don bake aka aurawa wannan karamin yaron ba, kya ce inyi hakuri mana!!!" Rungume hubby Ummul khair ta yi tana murmushin maganar hubby " na dade ina fatan haka ya kasance tsakaninki da hayder. Duk lokacin da kuke drama dinku, kuna burgeni, ina ma ina nan in muku zaman daki. Ko ba komai zan sha kallo." Da sauri hubby ta banbareta a jikinta, tana kai mata duka " ban yafe miki ba kuwa, Muguwa." Gaba dayansu dariya suka sa. Ummul khair ta tabe fuska " nama dauka zaki ce, zakimin tukuicin takwara." " in baki rufe min rubabben bakin kiba, zan fasa miki shi wallahi. Allah ya tsare ni, Bakinki ya sari guntun kashinki da haihuwa da wannan dan yaron." Hubby ta fada tana huci Hajja kolo dake faman dariyar su hubby, ta kalli hubby still tana dariya " yaro man kaza, waya gaya miki namiji na kadan? Zako kisha mamaki." " barta kawai, ran da muka ganta da turtsi billi, tayi mana bayani ai.?" Ummul khair ta fada tana dariya Ai da gudu tabar dakin tana dariya, saboda hubby da tayo kanta........ Dariya su ummu sulaim suke wa hubby da Ummul khair. " na rasa yadda akayi, yarinyar nan ta rainani da yawa." Hubby ta fada tana kwafa. " gaskiya Ummul khair ta fada. Kun matukar dace wa. Nima nayi missing din drama dinku wallahi. A ture batun wasa. He is the perfect match for u. Sai dai wannan karon sai kinyi a sannu, don nasan ba canzawa zakiyi ba, in ba haka ba kyaci na jaki, don karayrawyaki zai yi, daga ke se shi, ba mai karbarki." Yusra ta fada tana dariya Tsaki hubby ta ja. " Allah ya kyauta me jiya tayi, ballan tana yau." " wan can karon an turguda kafa, wannan karon kam tabbas, in baki bi a hankali ba, karyaki za'a yi. Bana kusa balle in zo zaman jinya." Aisha ta fada " kun zo kumun jaje ne? Ko kunzo Ku kara bata min rai ne? Ku nuna min kuna bayan dan uwanku?" Hubby ta fada cikin bacin rai. " sorry sister, ba nufin mu haka ba. Amma To tell u the true, we a happy for u." Ummu sulaim ta fada Hajja kolo dake kwasar dariyar drama dinsu,  ganin abun nasu bana kare bane, ga lokaci na ta tafiya. ta kalli hubby tare da mika mata hadin da tayi a wani bowl "gashi, ki shiga ki shafe jikinki da wannan." Hararar bowl din tayi, "banda na dazu kuma har da wani, nafa gaji gaskiya, dazu haka kikai ta dirzar min jiki, kamar kin samu kayan wanki, ni kam bazan sake ba,." " Aisha kira min Hajiya salwa a falon Hajiya Hauwa. " ya kolo ta fada tana kallon Aisha Karba tayi ta wuce toilet tana kun kuni. " kunyi a banza, asarar kudi, da wani abun kukayi da yafi muku." Ta shige toilet din. " Zuma sai da wuta." Humaira ta fada Hajja kolo ta ce " ai abubuwan hubby sai a hankali, Allah ya bashi ikon hakuri da ita." " miskili kafi mahaukaci ban haushi, shine dai dai da ita, dama kuma ai sun saba, wanda yaji wuya ya sake." Aisha ta fada " ya maganar walima, zaki samu zuwa ko ya zaa yi?" Yusra ta tambayi hubby bayan ta fito. " I don't no." Ta fada " yanzu kam ai sai da izinin mijinta, in ya yarda mai zai hanata zuwa, tunda duk na gida ne." Hajja kolo ta fada Yamutsa kumburarriyar fuskarta tayi " lallai kam zaa rube a gida, in har sai na tambayi wannan yaron zan fita." Dariya sukayi Aisha ta ce " da ko baki kyauta mana ba. Kin manta ke kikayi paganizing komai? Sannan ki ce bazaki ba? Meye a ciki don kin tambayeshi? Naga durkusawa wada ai ba gajiyawa bane." " kin san in ba kya wurin ba zaiyi  armashi ba." Ummu sulaim ta fada Banza hubby ta musu, don duk haushi suke bata. Don ta lura dadi ma sukaji an aura mata kanin bayanta. " ki shirya don Allah, zan ma Hajiya magana, sai ta turo a daukeki." Aisha ta fada tana fita daga dakin. Baya su yusra suka rufa mata, bayan sun ma su hubby sallama. " ko Janeway zaa kawo, ban zuwa ko ina." Ta fada tare da bin bayansu da harara. Dariya humaira, da zata zauna da hubby tayi. " aikin banza harara a duhu." Harara hubby ta aika mata. " kema tashi ki bisu." Harararta ta rama. " nima sai ki kawo Janeway ai, ki fita dani. Zama daram, har sai randa muka mikawa hayder matarsa. Robar humra ta jefeta dashi. Gwalo ta mata " oho!!! Dai."                   ****************** Su hayder daga gidan su hubby,  mai furniture da mommy Hauwa ta hadasu dashi suka dauka, zuwa gidan da zasu zauna. Duk kansu gidan ya musu kyau. Komai a tsare. Mai furniture ya gama aune aunensa yayi gaba.  " don Allah hayder ka bani wuridin da kake yi, nima in fara." Hafiz ya fada Dariya sukayi, banda hayder da ya harari Hafiz. Dafa Hafiz  amir yayi. " nafi kowa bukatar wuridin nan." " gaskiya you're very lucky, you bit the whole kangiwa, in just few day's. " Hafiz omer ya fada " gaskiya na maka murna, kun balain da cewa." Daya friend dinsu ya fada " ka bude mana hanya, nima kaga yanzu ba wanda zai ce min nayi yarinta, in na daddago aurena." Hafiz omer ya fada tana murmushi. " dama kai akawa auren ai da an huta, da tsince yaran jamaa da kake yi." Alim ya fada yana dariya Duka Hafiz omer ya kaima alim. " ko ina sai kun nuna hali ne?" Junaid ya fada yana musu inkiya da ido, saboda basu kadai bane, akwai some friends da bazasu so susan sirrin su ba. " bar dan banza, in masge shi." Hafiz omer ya fada cikin wasa Sai kusan magrib suka bar gidan. Sun tsaya tsara yadda komai zai kasan ce, ya bada tsari da ma'ana.                 ******************** Zaune suke a babban falon gidan Alhaji babba. Dau kacin iyayensu maza, suna wurin, sai Alhaji kawu da aminansa biyu. Kowacce sanye cikin kaya na alfarma, tasha lullubi da manyan mayafi, sai kamshi daya cika falon tamkar shagon perfume. Nasiha mai ratsa jiki, Alhaji babba ya musu, bayan ya gama Alhaji kawu ya amsa:--- Ku qudurce a ranku zaman ibada zakuje. Kuma ku sama ranku sabida Allah zaku zauna da mazajenku, ku yadda da qaddara kowane iri a cikin rayuwarku. In har kuka riqe haka to bazaku shiga shahun masu cewa " duk wacce tace namiji ubane xata mutu marayainiya ba. komai talaucin mijinki, ko kaushin halinsa,  ko kananun shekarunsa, ku rungumi abinku, ku yi ta mai addu'a, domin wata kamarshi ma take nema bata samu ba. Ina dada Jan kunnenku, da  kusani, mijinki abin tausayi ne, abin lallashi ne, abin tarairaya ne, gareki domin shine mahadin rayuwar ki, kuma aljannarki. Kuji  tsoran Allah, kar Ku zama masu yawan buri da son duniya, kwata kwata duniyar kwana nawa ne, kina tabbacin xaki maimaita shekarun ki na baya? Sannan in kin sameta, kina da tabbacin lokacin da zaki moreta? Duk halin da kike ciki a gidan mijinki ki godema Allah, domin akwai wacce ta fiki matsala, amma tana godiya ga Allah. Ki tuna Allah da kansa yace " bayan tsanani sauqi na zuwa" kuyi haquri da mazajenku, babu abunda haquri baya haifarwa. Musanman a wannan lokaci.  in kin tuna Allah da kansa yayi magana akan haquri. To ashe ko ba qaramin abu bane. In kikayi riqo dashi zaki samu riba mai tarin yawa. Domin Allah yana tare da mai haquri, Kuma haquri haskene. kuji tsoran Allah kar wayewa da ilimin boko, ko yawan shekarunki, yasa ki dinga ganinki dai dai da mijinki. Hakika shine gaba dake, Allah ne ya bashi wannan matsayin, don haka Ku kiyaye. Allah ya muku albarka, ya Baku yaya na gari, ya sanya yalwa da tsoron Allah cikin rayuwarku." Gaba daya suka amsa da "amin" banda amare da jikinsu ya kara yin sanyi. Kowacce kukanta ne ya karu. Sauran iyayen ma albarka suka sa musu. Sannan aka fito dasu, Kowacce aka nufi, motar da zaa kaita gidanta da ita. Ummul khair da Aisha, abuja aka nufa don kaisu dakunansu. Sai ummu sulaim kano, sai hubby malali. Hubby tayi kuka kamar ranta zai fita, ga kewar su Aisha, sannan abun da take ganin kamar wasa, yana neman zama gaske, koma ya zama gaske. Gida yayi kyau, ba karya, su mommy Hauwa sunyi matukar kokari, fiye ma da last time. Don komai sabo suka zuba mata, High quality dakunan bacci biyu da falo biyu. Sai hayder da ya gyara nashi bedroom din da babban falon gasa, sai small bedroom dake kasa. Fadin haduwar gidan hubby kauyan cine, ko a turai sai haka. Bikin yar gata da autan Hajiya, ai kuma kunsan baa magana. Nasiha sosai su Hajiya salwa suka karawa hubby. Sannan suka tafi, a kabar hubby da kawayenta biyu. Humaira da Khadija. Hira humaira da Khadija ke yi, hubby kam tana kashin gide, a hadadden Italian bed dinta. Tayi nisa cikin duniyar tunani. " don Allah Ku tashi muje, mu dan zaga gidan, na dade banga gidan daya burgeni irin wannan ba." Khadija ta fada, tana mikewa. Tashi humaira tayi, dama zaman ya isheta, hannun hubby ta kamo. " please tashi muje." Mikewa tayi suka fito ko ina sun shiga a sama dakin hayder ne kawai suka samu a rufe. Suka sakko kasa, nan ma sun shiga ko ina, kafin suka yi branch a kitchen. Katon kitchen ne, yaji cabinet, ka naurorin girki na zamani kala kala, wasu ma su humaira basu san anfaninsa ba. Fridge humaira ta bude, mai 2 door, " na dade ina ganin irinsa a TV, yau gashi ina ganinsa a fili. Gaskiya kitchen din nan yafi ko ina kyau." Murmushi Khadija tayi. " ai nima abun ya burgeni. Na dade banga kitchen daya burgeni irin wannan ba. Ai in a gidan nan nake, kullun ina nan." Kallon TV dake manne a bangon kitchen din tayi. " Irina kam, ai kullun sai na babbaka girki." Humaira ta fada. " mayyar series ba!!! Balle ga TV a kitchen ai kam sai abunda Allah yayi." Dariya humaira tayi. " masha Allah, komai yayi kyau. Allah ya bada zama lafiya, nan da 9month muzo suna." Tsaki hubby ta yi, tana maka mata harara, ta fita. " komai barazanar Amarya, sai ansha manta." Khadija ta fada tana dariya Sallamar da sukaji  yasa su fitowa. Mata biyu ne, yan uwan  mommy Hauwa suka shigo da jerin akwatuna, na auren hubby.   Sai da suka jera mata su tsaf a dakinta. Sannan sukai mata sallama. Ganin mota free, ga dare ya fara yi yasa su humaira binsu. Tare da ma hubby fatan alkhairi.                ******************* Mota kusan hudu suka shigo, harabar gidan. Su hayder ne da 6 best friends dinsa. Sanye yake da kananan kaya. Blue Jens, sai White shirt mai gajeran hannu. Kafarsa sanye da sandal farare,. He look handsome. Tsayawa sukayi suna kallon gidan, kowa da abunda yake sakawa. Hannu junaid ya mikawa hayder. " dud Allah ya sanya, alkhairi ya baku zama lafiya, Ni kam ina daga nan." Ya kalli su Hafiz " I'm wetting for u hare." Ya fada yana shigewa motarsa. Dariyar Hafiz omer yayi " kai kam Allah yayi matsoraci." " naji sai kun fito." Junaid ya fada A hankali suka taka zuwa kofar da zata sadasu da cikin gidan. A bakin kofar harder yayi burki, juyiwa yayi yana kallonsu. Hannu ya mika ma ashir dake rike da ledojin kaza, fresh fruit, yeghout, sai chocolate. Mika masa yayi, yana masa kallon tambaya. Murmushin gefen baki hayder yayi " na gode, Allah tashemu lafiya." Baki bude suka tsaya suna kallonsa. Gira ya daga musu " what?" " kana nufin baza mu shiga ciki ba? Ko ya?" Amir ya fada cike da mamakin hayder. " na hutar daku, sai da safe." Hayder ya fada yana shigewa ciki, tare da murzawa kofarsa key. " kam biji, biji iskar sanyi. Amma yaron nan yama raina mana hankali." Hafiz ya fada yana rike baki. Dariya Hafiz omer ya saka, har yana rike ciki. Suma dole suka tayashi, don abun da haushi, da mamaki. " in kun gama tsayuwar sai kuja, akwalar kafafunku, mu tafi." Amir ya fada yana yin gaba. " garama da bamu shiga ba, da da wane ido zamu kalli Anty hubby, a ce mune yan siyan baki? I wander how she feel, about all this thing. " Hafiz ya fada " its true, nima na dade ina wannan tunanin." Alim ya fada " abun da kamar wuya, ina imagining yadda wannan zaman zai kasan ce." Ashir dake kokarin shiga motar da suka zo da ita ya fada. Dariya Hafiz omer yayi " ehhhimmm hayder ne fah!!! Muna nan daku, tsaf ze bi da ita." Junaid ne ya leko da kansa, " zaku zo mu tafi? Ko zaku tsaya, shiga abinda bai shafe kuba." " I Wonder. " ashir ya fada Haka suka ja motocinsu kowa ya nufi makwancinsa. Malan idi, ya maida get ya rufe. A kan kunnen hubby suka shigo, tashi tayi, ta murza key a kofarta, tabar key din a jiki. Wanka tayi, tare da shirin bacci. Maganin da Khadija ta bata na ciwon kai, ta dauko ta bude fridge dake bedroom din, ta dauko faro. Tasha, adduoin kwanciya barci tayi, taja lallausan bargonta ta lullube, saboda sanyin ac. In no time bacci yayi gaba da ita. Saboda gajiya, ga rashin isashshen bacci. Hayder kitchen ya wuce,  ajiye komai a muhallinsa. Sannan ya wuce bedroom din sa. Wanka yayi, tare da shiryawa cikin kayan bacci Mara sa nauyi. Baya tare da yunwa, don haka shima yabi lafiyar gado. Abubuwan da suka faru ne, suka fara dawo masa kamar majigi. Nasihar su Alhaji babba ta tsaya masa a rai. Sai tunowa da dan uwansa, da yayi. Ajiyar zuciya ya sauke, yana tuno ziyara ta karshe da dan uwan nasa ya kai masa, lokacin bai wuce saura sati uku kacal  yabar duniya ba. Magan ganun da sukayi a lokacin suka fara dawo masa, kalma by kalma. Hawaye suka fara zarya a kuncinsa. Adduar da ya saba ma dan uwan a duk lokacin da ya tunasa, yayi. Tare da kara gyara kwanciyarsa. Ya fada tunanin yadda zata kaya shida hubby.......   [05/03, 14:06] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 16       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... A hankali ta fara bude idonta, da sauri ta mike, tana dauke da adduar tashi bacci a harshenta, da labbanta. Ganin gari har ya fara haske, toilet ta nufa da saurinta. Bayan ta idar da sallah, ta zauna tana azhkar, tare da adduoin da bata samu ta tashi cikin dare kamar yadda ta saba ba. Kanta ta daura a jikin gadon ta fada duniyar tunanin. Bata san ta ina zata fara wannan zamanba. Abu daya ta Sani, bazata taba yadda wani abu ya shiga tsakaninta da wannan yaron ba. yan zuma ya ta kare da rainin hankalinsa, balle yaga gadon baccinta. After all he is her younger brother kuma brother din Yusuf. Ko da yake tasan ko giyar wake yasha shima ba zai tunkareta da wannan ba. Murmushi tayi, tama tsaya tana bata hawayenta a banza. Zaman gidan nan bai sake da tana zama da brother dinta bane, sannan ta huta da damuwar masu cewa suna sonta, da kuma su gwaggo dake son tayi aure. Yanzu kunnenta shiru. Shi kuma zuwa gaba yana da right da zai yi aurensa kamar kowa, don ita dama ba auren bane a gabanta. Zama dashi tamkar Katanga ce da zata bata kariya ta fanni biyu. Masu sonta da iyayenta. Murmushi ta kara yi, " I have my freedom, I will do what I want. " Hayder kam yana dawowa masallaci, muraja'a ya zauna yi, bayan ya kammala azkhar. Sai to 8 tukun ya nufi toilet yayi wanka, ya shirya cikin wasu kananan kaya shirt da trouser masu kyau da asalin tsada. Ya gyara sumar kansa, mai matukar laushi da daukar ido. Kamshi kam baa magana, kamar wanda ya fito daga kamfanin turare. Hajiya ya kira, suka gaisa, tana tambayarsa hubby, ya amsa da lafiyarta kalau, nasiha ta kara masa sosai, sannan sukayi sallama. Alhaji Jamal ya kira suka gaisa. Sannan ya nufi kitchen don samawa cikinsa abun da zai ci. Gidan shiru bakajin karar komai, sai na naurar sanyaya daki, dake tashi. kamshin turaren wuta, da sanyin ac dake bada wani kamshi, mai sanyaya rai. Ya shaka yana lumshe ido. Don kamshin ya masa dadi. Jin gidan shiru, ya tabbatar bata tashi ba, ruwa ya sa a kettle. Ledojin daya shigo dasu jiya ya dauko, kidney kebab ya juye a plate ya sa a microwave. Jin gina yayi da cabinet din kitchen din yana bin kitchen din da kallo, ya masa kyau matuka. Ina ma a ce shida nasrin ne da wannan hadadden gidan, sannan suna a matsayin maaurata. Gabansa ne ya fadi, tunowa da nasrin. Ya zataji in ta samu labarin aurensa? Yasan ba karamin tashin hankali zaayi da ita ba. Don yarinyar tana sonsa matuka, shima zuwa yanzu, ya tabbatar yana jin wani abu dangane da yarinyar. Ajiyar zuciya ya sauke, abinda ke kara daga masa hankali, wane irin zama zasuyi shida hubby. Baya sonta, ya tabbatar itama haka, kawai biyayya ce, da rashin madafa. Zai bata lokaci yaga iya gudun ruwanta. Ta hakane, zai gane matsayin aurensu a gareta. Karan kettle ne ya dawo dashi daga dogon tunanin daya tafi. Cup ya dauko ya hada black tea. French bread ya dakko yayi slicing dinsa, ya shafa butter, jerasu yayi a bread toster. Ya dauko trey kenan da zai jera break fast dinsa, yaji wani kamshi ya doki hancinsa. Duk da turarensa daya gauraye kitchen din bai hanashi jin kamshin daddadan turarenta ba. A bakin kofa tayi burki. Tana sanye da doguwar riga, ta material da mayafinsa. Ba ko pawder a fuskarta, amma tayi kyau sosai, sai glowing fatarnan keyi. " nan dama akafi auki." Ta fada under her breath Ya jita, sarai ya share. Sai da ya jera komai kan trey din, kafin ya dauka zai fito. Ganin zai wuceta ba alamar zai kulata. Tayi murmushi cikin tsokana " agric chicken ba gaisuwa." Kallon sama da kasa ya mata ya wuce abinsa. Murmushi tayi " dani kake magana, a sannu zan gyarama zama yaro." Ta wuce cikin kitchen din, don wata mahaukaciyar yunwa take ji. Tea ta hada mai kauri, ta zuba cake a plate ta haura falonta dake sama. " good for u, Ashe ka gane, zamane na kowa yayi ta kansa." Ta fada tana murmushi "******************* Ranar gaba daya cikin baki, yan ganin daki, hubby tayi shi. Sai yamma lis ta samu kanta. Hayder kam tun haduwarsu a kitchen da safe basu sake haduwa ba. Hakan ba karamin dadi ya karawa hubby ba. Next day yan secondary school dinsu suka kawo musu ziyara, Nan ma tasha hidima. Sai dai taji dadin still yadda suka nuna mata respect. Ta dauka aurenta da hayder zai sa su kara rainata, sai taga sabanin haka. Mazan na tare da hayder a main falo. Matan suna falonta na kasa. Taji dadin wannan ziyara, don da yawansu tunda aka gama basu sake haduwa ba. Sai to 6pm sannan suka tafi. Sai da ta kyara ko ina tsaf tukunna, ta nufi bedroom din ta, wanka tayi, ta shirya cikin English Ware's Riga da skirt masu matukar kyau. Sun zauna a jikinta tsaf. Wayarta ta dauko tana son kiran gwaggo. Kusan 20miss calls ta gani, abin haushin tana kokarin kira, ta tuna, dazu suna waya da yusra kudinta ya kare. Datanta ta kunna don siyan kati true bank, but network is bad. Hijabinta ta zunbula ta Zari 2k a bag dinta ta nufi falo. Direct falon hayder ta nufa, yana kashin gide a 3 sitter ya rufe idonsa kamar mai bacci. Kamshin turarenta ya masa sallama. Bai ko motsa ba balle, ya nuna yaji shigowarta. Tunda ba sallama tayi masa ba. " agric chicken. " ta fada tana kallonsa, ko motsi be yi ba. Bubbuga kujerar tayi kadan, ta kara daga murya "agric chicken." Tsaki tayi ganin ya mata banza buga kujerar tayi da karfi, tare da ware murya " agric chicken, kana jina fah!!!." Idonsa ya bude a hankali, ya sauke su a kanta. " kanaji ina maka magana kamin banza, don wulakanci." Ta fada tana harararsa. Agogonsa ya kalla 6:35. Lokacin sallar magrib ya gabato. Mikewa yayi ya zauna da kyau. Ganin bashi da niyyar mata magana, haushi ya kara kamata. Sai aika masa da uwar harara take. Ta mika masa kudin " recharge card nake son ka siyo min, mtn na 1500, airtel na 500." Kallonta yayi ya kalli kudin da take mika masa. " karba mana." Ta fada cikin kaguwa, da jin haushi. Mikewa yayi, har zai fita, ya dawo, ya karbi kudin, a aljihun gaban shirt dinsa ya saka ya fita. Da harara ta rakashi. Ganin ya nufi sama yasa ta fito da sauri, " agric chicken ina kuma zaka? Yanzufa zanyi anfani dashi, kake shigewa ciki." Ko waigota be yiba, ya haye abinsa. " oh!!! Allah," ta fada tana dafe goshi. Sai da ya dauro alwala, ta gabanta ya wuce, tana kara jaddada masa, yanzufa take son anfani dashi. Kwafa yayi, bayan ya fita, tare da busar da iskar bakinsa, don ransa a bace yake, da yabi ta zuciya ba abinda zai hanasa mangareta, watan ita a matsayin Senior tazo ke nan, She want to boss him rawn. "A sannu zanyi maganinki" wata zuciyarsa ta fada. Har akayi sallar ishai, ba hayder ba alamarsa. Hubby takaici kamar tayi yaya. Don ta samu ma wasu daga cikin wanda suka mata miss calls, sun sake kiranta. Tana son magana da gwaggo. Still rashin kyan network ya hanata, samun damar siyan kati ta waya. Hayder bai shigo gidan ba sai 9:24 lokacin har ta gaji da jira, ta kulle kofarta. Zagi kam yashashi. Don ranta ya baci sosai. Kota kanta hayder be biba, shima shirin bacci yayi, yayi kwanciyarsa. ***************** Hannu ta mika masa " ina kudina?" Black tea dinsa ya ci gaba da sipping " agric chicken, da gaske kazo da rainin hankali, taya zan aike ka, baka siyo, abinda na aike kan ba, sannan baka dawomin da kudina ba?" Kallonta yayi. " dan aikenki ne ni?" Ya fada yana kafeta da ido. Gefe ta kauda kanta. " wa zan aika, banda kai? Ko bayan kai akwai wani yarone a gidan?" Smacking yayi, still yana kallonta. " ba recharge card ba money, karfi yaci, in kina dashi kuma bisimilla ki kwata." Ido ta zaro. " tabdijan!!! Kana neman fitina wallahi, kasan kudina ba zai yi ciwon kai ba, don seka biyasu." Wuceta yayi, ya fita a gidan. Kwafa tayi, bedroom ta koma, ta sake dauko wasu kudin, taba malan idi ya siyo mata. ******************** Ta windon bedroom dinta ta leka don ganin abinda ke faruwa. Tsaki taja. " kuruci dangin hauka, wa annan ne zaa kira da masu hankali, har a dauki aure a basu." Ta fada tana kwabe baki. Tun da dama naga ana kafe- kafe da aune -aune, nasan za'a rina. Tsayawa tayi tana kallon yadda suke buga basketball din, sai ife, ifensu daya karade gidan. Kitchen ta nufa, ta daura abincin dare. Wanda tun zuwanta, daga ita sai malan idi maigadi take dafa abincinta, sai ko in sunyi baki. Hayder da kansa yake dafa abinda zai ci, baya damuwa da rashin sa masa abinci da takeyi. In takai abinci falonsa to su junaid ne sukazo, ko bakinsa maza, a nan kam tana kokari, don duk abunka in kazo baxaka gane irin zaman da sukeyi ba. Abinci kuwa, zata dafa taba bako, batajin kyiwar girki, in ba lokacin cin abinci kazo ba, zata kawo maka juice, ruwa, da snacks. Wannan koyarwar gwaggo ne. Bata yadda bako yazo ya tafi baisha ko ruwa ba. In ma yaki sha. Ta dinga mita, har sai mutun ya kurba. A cewarta mugun bako ne, zai zo ka kawo masa abu yaki ci, ko sha. Sai kusan magrib suka bar gidan. Yauma 9 ta wuce taji dirin bike din hayder alamar ya dawo kenan. Kwanciyarta ta gyara tare da lumshe idonta. Tana jin kewar Yusuf. Tabbas mutuwa mai tonon asiri, da yanzu tana tare da masoyinta, mutuwa ta mata yankan kauna, a dai dai lokacin da tafi kowa bukatarsa. Ya tafi ya barta, cikin gwagwarmayar rayuwa. ***************** Yau kwana biyar ke nan, da tarewar hubby. Tana zaune a falonta na kasa. Indian series take kallo a tashar zee world. Nocking din da taji, yasa ta mikewa, ta zura hijab dinta dake kusa da ita. Hajiya kaka, da samira ta gani. Cikin faraa ta tarbesu, tare da masu iznin shigowa. Kitchen ta nufa don kawo musu abin motsa baki,. Da kallo Anty samira kebin falon. Iyakar haduwa ya hadu. Gaba daya tunda ta shigo daga get, jikinta yayi sanyi, ga wani kishin hubby data ji ya kara darsuwa a zuciyarta. Ta rasa me yasa yarinyar ke darata a komai. Yadda take jin labarin haduwar gidan, har yafi yanda ake labarinsa. Hajiya kaka ta rike baki, tana kallon Anty samira. " aljannar duniya, ki ce Hajiya ta tatse Jamal tas. Don wannan dukiya da aka zuba a nan, yafi karfin arzikin Munir." " ehemmm!!!! Kema kya fada, duk anyi ne don muji haushi." Anty samira ta fada cike da kyashi " sunyi ta banza kuwa, don baa taba canzawa tuwo suna, har gobe a tuwonsa zai zauna." Hajiya kaka ta fada Hubby ce ta shigo da babban trey dauke da cups juice, water, cin cin da cake. Ajiyewa tayi a center table din dake gabansu. Sannan ta zauna. Hajiya kaka ta fara gaisarwa cikin ladabi, sannan ta gaishe da Anty samira. Hajiya kaka ce ta kalli hubby, duk da katon hijab din da take sanye dashi, bazai hanaka ganin kyanta ba. Fuskar nan sai walkiya da daukar ido take, ta kara haske tayi kyau. " masha Allah, yarinya, ke kam kakarki ta yanke saka, na dauka zanzo in ganki, cikin damuwa, an hadaki da kanin bayanki, sai naga sabanin haka. Bako jin nauyi kinyi tarayya da yaya, kuma kina yi da kani, kanin ma na bayanki. Kinyi kokari matuka." " me ko zai dameta, ta samu santalelen yaro, ana tsotseshi." Samira ta amshe Gwaggo ta kara da " koda yake haka ne, kin san in mutun yayi kwantai, koma wa yazo ba damuwarsa bane, shidai ya jishi dakin aure kawai. Ni kam Allah ya tarfa min alam nasharaha." Hubby kam kanta ta sunkuyar, zuciyarta na tafasa. Bawai dama ta manta abinda Anty samira ta mata bane, kawai dai ganin ita ta tako har inda take, bai kamata ta wulakanta taba. Sannan tasan tsaf sune, Ummul aba' is na aurenta da hayder. Darajar sun tako har gidanta, da darajar furfura, shi yasa ta daga musu kafa. Koba komai suna sama da ita. " ai kam na tausayawa yaron nan, da yarintarka, a dauki uwar mata a hadaka da ita. Ban taba ganin irin wannan lamari ba. Koda yake sunfi kusa." Bataji karar shigowar power bike din saba. Sallamarsa kawai sukaji. A hankali ya tako zuwa cikin falon. Sanye yake da lallausan yadi fari, half jamfa mai gajeren hannu, yayi kyau sosai, ga kamshi na musamman dake tashi a jikinsa. Kujerar kusa da hubby ya zauna tare da daura kafa daya kan daya, ya jingina hannunsa mai dauke da phone dinsa a hannun kugerar, daya hannun yana shafa sagensa, zuwa gemunsa. Idonsa kar akan su Anty samira. " babiba." Ya fada da wata irin murya daya sa hubby saurin dagowa ta kalleshi, cike da mamaki. Lokaci daya ya canza mata kamar ba hayder din data Sani ba. " go inside. " ya fada yana mata wani irin kallo. Bata san lokacin da ta mike ta nufi stairs ba. " hayder wane irin abu ne haka? Bako gaisuwa, ka zauna zaka nuna mana kai ka zama mai gida, mai bada umurni? Ko ni baka gaishe ni ba, ai ka gaida Hajiya kaka ko?" Anty samira ta fada cike da jin haushi. Kallonta yayi,tare da murmushin gefen baki. "A addinance sallama ya kamata nayi, kuma nayi dazan shigo. Duk da ba dole bace, amma amsata dole ne, cikinku waya amsa min sallamar? Babu?, kuna nan kuna cin zarafin yar mutane." Cikin fusata Anty samira ta mike " in kana rashin mutuncinka karka yadda ka gangaro kaina! Don naga alamar kanka na rawa.? Murmushi yayi mai sauti " duk wanda ya siya, dole a siyar masa, bazan dau rashin hankali a gidana ba. Ba yadda zaa yi, Ku tako har gidanta,. sannan kuci zarafinta. In a da kunyi, to ni bazan dauka ba, matukar ba zumunci zai kawo mutun ba, to bana nemansa a gidana, in ba haka ba tamuce ni dashi." Hajiya kaka ce ta fara sallalami " ta tabbata! Ta tabbata! Wallahi ta tabbata. Kaima har an wanke an baka? Yo in ba an wanke an baka ba, a gabana bako kunya da ganin darajar furfura, kake kunfar baki don an taba tsohuwar matarka. Ina abun yake? Kake wani kafafa..." " naji kina baki taba ganin aure, irin namu ba? Kin manta da auren manzo Allah, Annabi Muhammad SAW da Nana Khadija?  Yana dan shekara 25 ita tana 40years.  aurenta biyu, da yara biyar. Kafin ta auri Annabi Muhammad SAW. Kin ga ashe ba sabon abu bane, koyine da manzon Allah SAW. After all ke ce silar hakan, banga kuma dalilin zuwa ki tozartata ba, bayan ke kika ja, abinda yasa aka aura mata yaron." Hajiya kaka da ranta ke bace, ya zaayi kamar hayder ya zauna yana gaya mata magana, hankalinsa kwance, kamar mai magana da saansa. " baka cewa ni na daura auren, mara kunyan banza." " ko baki daura ba, ai kinyi sila. Ke daba dan darajar zamowarki kaka ba ta wani bangaren kuma furfurar da kike ikirari, da koda kudi aka ce ki tako kafarki gidannan bazaki fara ba. So leave us in peace. " " ka rika wallahi, hayder Hajiya kaka kake ciwa fuska? Yanzu zaka iya yiwa Hajiya babba haka? Saboda mun tako gidanka, maganar nan bazata tsaya a nan ba, sai na kai kararka, ai gaba ma da gabanta. " samira ta fada cikin bacin rai. " nan kika fi auki dama, an girma baa san an girma ba. Karki fasa kai karar tawa. Amma ki sani bama keba, duk wanda ya kara yunkurin cin fuskar matata, ko da dai dai da bakar magana ne, he will answer to me." Takaici ne, ya kume Anty samira, tana jin labarin rashin mutuncinsa, amma bata taba tsammanin yakai haka ba. Don ko da tana gida, ba wani shiri sukeyi ba. Kamar yadda bayayi da mahaifiyarsu, haka ita ma, Karin jin haushin yadda yake treating din mamanta, yasa bata shiga harkarsa. Hajiya kaka ta kalla. " tashi muje, kafin ya rufemu da duka kuma, don naga abun nasa ya yi yawa.' Mikewa Hajiya kaka ta yi, Cike da sanyin jiki, ga takaicin hayder, a cikin jikokin nata ma, shi bai kai saan dan autan subama. Still yana zaune kafa daya kan daya, sai faman shafa sajensa, yake da kyawawan zara zaran yatsunsa, farare Sol dasu. Kai ka rantse maganar arziki yake furtawa, yadda yake maganar cikin yanga da Jan aji. Idonsa kar a kansu. A fusace suka bar gidan. Tsaki yaja,. Tunowa da drama daya tarar anayi a main house. Abdul Karim da Anty samira, da kyar aka janyeshi yana sai ya mata dukan tsiya, sanadinta tasa ya rasa muradin zuciyarsa. Sai a nan ma suka ji, wasu kulle kullen data hada duk don taga auren hubby da Abdul Karim bai tabbata ba. Da badan shi, da ya janye Abdul Karim ba, da abun ba karamin kazanta zai yiba. Don su Hajiya sun kasa, gashi ba maza a gidan. Cikin ikon Allah sai gashi ya shigo. Ya tausayawa Abdul Karim, duk da shima tawani fannin yana da nashi laifin. Mikewa yayi ya nufi upstairs, don dama wani documents yazo dauka. A last step suka hadu da hubby dake rungume da hannu, cikin damuwa da bacin rai. Duk abinda suka fada kan kunnenta, shine dai bata ji mai yake fada musu ba, saboda a cikin natsuwa yake maganarsa, amma daga amsar da suke bashi, tasan ba maganar arziki ba ce. Babban abinda ya kara kona ranta, da yace ta tafi, ita kuma sokuwa, har dabin maganarsa, sai bayan ta tashin ta dinga jin haushin kanta. Wuceta ya so yayi, tai saurin tare hanyar, kallonta yayi, ya koma ya jingina da jikin karfen benen, ya nade hannayensa duka biyu a kirjinsa. Ya zuba mata fararen idanuwansa. " meye sunan abunda kayi? " ta tambaya tana kallon hannayensa dake sarke a juna. Ganin bashi da alamar amsa mata yasa ta kara jin haushi, don ta tsani tayi magana ya mata banza, gashi ta lura halayyarsa ke nan. " abunda kayi, baka kyauta ba, koba komai sune gaba damu, dole muyi hakuri da duk abunda zasu fada mara dadi. Karka manta Hajiya kaka tamkar uwa take gasu Hajiya. Please don't do such thing again. " Wani kallo ya mata data kasa tantance na menene. Ganin zai bangajeta, yasa tai saurin bashi hanya, da ido ta bishi har ya shige bedroom dinsa. Ajiyar zuciya ta sauke. " oh!!! Allah wannan wane irin yaro ne. Ke nan rashin mutuncin nasa kowa ma bai bari ba kenan.? Maganar ummu khulsum ce ta dawo mata. " rashin mutuncin hayder sai dai in baka shiga gonarsa ba, amma komai girmanka, bazai daga maka kafa ba. Don haka kibi a hankali, kika fusata shi, wallahi zaki gane baki da wayau, abin da ya miki da, nafila ne dana yanzu, don yanzu yana ganin kina kasanshi, matsayin matarsa, bazaku kwashe da dadi ba. Don haka ki kiyaye, Ku zauna lafiya, banda raini."  Tana kokarin tuno da ansar data ba ummu khulsum a lokacin. ya fito, ganinta yayi still a wurin. Wuceta yayi ya sauka daga steps din, cikin gudu- gudu, sauri - sauri. Hubby ji tayi kamar ta tade kafar tasa ya fadi. Ganin tsayuwar bazai mata ba, ta nufi falo, ta dauki trey din data kawowa su Anty samira ta nufi kitchen dashi.                  ****************** Tana kitchen taji shigowar mota, a tunaninta baki su kayi. Hayder ne ya shigo kallo daya ya mata ya nufi kofar da zata sada ka da waje, ya bude tare dama malan idi bismillah. Malan idi ne ya shigo da wasu manyan ledoji a hannunsa. Gaisheta yayi cike da ladabi, sannan ya ajiye. Haka ya dinga shigo da ledoji da kwalaye har ya gama, sannan ya kalli hayder dake rike da cup din juice " oga an gama." Hannu ya daga masa, cikin sauri yabar kitchen din. Kallonsa tayi, takai kallonta ga shirgin kayan da malan  idi ya shigo dashi. Juyawa tayi ta ci gaba da aikinta. Bebi ta kanta ba, ya fara ciccire ko wanne, yana sa su a muhallinsu. Nama ma mahaka ya jera su tsaf a deep freezer. Anyi shilling dinsu a kananan mazubi da white rapper.  Juice, drinks, da bottle water duk ya jerasu a store. Duk abinda yake yi tana jinsa, bata ko kalli inda yake ba. " in kin duba, akwai abunda babu let me know. " ya fada yana kokarin barin kitchen din. " wai kai baka iya gaisuwa bane?" Dawowa yayi da baya, yana kare mata kallo. Harararsa tayi " wannan kallonfa?" Hada rai yayi cikin miryarsa mai kama da an masa dole ya ce " ni dake waya kamata ya gaishe da wani.? Baki ta bude cike da mamakisa, ta amsa masa da " kai ya kamata ka gaisheni, after all kai kazo ka sameni, kaga kenan kai zaka gaisheni." " sau nawa kika shigo kitchen din nan, da safe kika ganni, kika gaisheni?" " taya zanyi dama in gaisheka? Karami ai shike gaida babba." Smacking yayi, tare da shafa sajensa.  Idonsa kar cikin nata. " shi yasa ai ban gaisheki ba, kin san yanzu abin ya juye. Ko da ban gaishe kiba, balle yanzu, da nake samanki." Ya fada yana gwada mata da hannunsa, daya daga a saman kanta. " Allah ya kiyaye, in zamo a kasan ka, in mafarki kake, gara ka farka, har gobe ina nan a matsayin yayarka. Dole kuma ka bani wannan girman." Ta fada cikin bacin rai " keep dreaming. " ya fada yana barin kitchen din. " kam bala'i, me wannan yaron yake nufi? Kar dai auren da yake ganin an daura musu, yasa kansa ke rawa. Lallai kam zai sha mamamki." Haka har ta gama aikinta tana tunanin maganarsa. Ta idar da sallar ishai ke nan tana ninke hijab din da tayi salla dashi. Ya shigo dakin tare da sallama. Gabanta ne yayi mugun faduwa, don tsawon sati dayan nan da kawota gidan, ko sau daya bai taba gigin shigowa dakinta ba. Hasalima da daddare  kafin ya dawo ta rufe dakinta. Da kyar ta hadiye yawun bakinta tana binsa da kallo. " lafiya malan? Meya shigo dakai nan.? Dakin yabi da kallo, komai tsaf, gwanin shaawa, ga kamshi mai dadi na tashi. Lallai su mommy Hauwa sun kashe money, ya fada a ransa. Don shi kansa dakin ya burgeshi sosai. " me kike tunanin zai kawoni dakinki?" Ya fada yana isa wurin dressing mirror dinta. " koma menene, ka gaggauta ficewa a dakin nan. Kuma ya zama fist and last da zaka shigomin daki." " really.? " ya fada yana daddaga turarukan dake wurin, yana gani, tare da kaiwa hancinsa ya shinshina ya ajiye, ya dauki wani. Tsayawa kawai tayi, tana kallon ikon Allah Don abun nasa ya fara daure mata kai. Kirjinta sai dukan tara tara yake, don bata san da wadda yazo ba. " gobe Hajiya zata aiko miki da yar aiki, in kuma bakya bukata ki kira, ki shaida mata." Ya fada Ajiyar zuciya ta yi, tare da ajiye hijab din a mazauninsa. " OK, naji sai da safe." Ta fada tana nuna masa kofa. Juyowa yayi ya jingina da jikin dresser din hannunsa duka biyu dafe da gefe- da gefen dressen. " I will travel tomorrow. " ya fada idonsa a kanta. " Allah kiyaye hanya." Ta fada, still tana nuna masa kofa. Kudi ya Ciro a aljihun rigarsa. Bunch din 1k ya ajiye mata. Ya juya zai fita. Sunansa data kira yasa ya juyo, yana kallonta. Kudin ta dauka, ta nufi inda yake tsaye. Mika masa tayi " I don't need you're money. " kudin ya kalla, sannan ya kalleta, juyawa yayi yatafi ya barta da kudin a hannu. Kiransa ta fara, amma ko waigowa beyi ba. Tsaki ta ja, tare da komawa ciki ta murzawa kofarta key.                  **************** Washe gari, jirginsu hayder ya tashi zuwa Paris, shida Hafiz, da amir. Hajiya ta kawowa hubby yar aiki, mai suna Mariya, ta ji dadi sosai, don dama zaman gidan ya fara isarta. Musamman yanzu da yan ganin daki suka fara sauki. Kwanan hayder biyar da tafiya, hubby ta koma islamiyarta. Ko da ta gayawa hajiya maganar islamiyya, tambayarta tayi hayder ya sani? Ta  ce mata eh!! Kawai. Ce werta no need da zata tsaya har sai ta tambayi hayder, No way. Islamiyyar daga 10 to 12pm, kafin ta tafi, sun gama komai na gyaran gida, tayi saa Mariya bata da kyuiwa, akwai aiki. Tana dawowa zata daura musu lunch. Dadinta ba nisa tsakaninta da school din.                   ***************** Zaman gidan Alhaji Jamal yanzu ya sauya salo, duk yadda yaso yaga ya sasanta iyalan nasa, abun ya faskara. Don haka ya kai kararsu wurin Alhaji babba. Alhaji babba da kansa ya tako har gidan dan nasa. Nasiha sosai ya musu, tare da rokonsu dasu manta duk wani abu daya faru, su yafewa juna. Sannan ya shaida musu ya ba Abdul Karim da Abdul fatta nan da 2month kowannensu ya fitar da Matar aure. Hakan ne ya kawo dan sassauci. Musamman tsakanin Hajiya da Mmn samira. Sai dai Hajiya ta Riga tayiwa kanta alkawarin bazata taba sake mata kamar da ba. don an shata ta warke. Kuma maciji baya sarin mumini sau biyu a rami daya. Yanzu tasan yadda zata zauna da kowaccensu. Dama Mmn Yusuf kowa yasan inda ya ajiye dan uwansa.                 ****************** Satinsu hayder biyu, suka dawo cike da nasarorin abinda ya kaisu. Sunyi saukar safe. Main house ya fara isa yaga Hajiyansa kafin ya nufi gida. Ko da ya shigo gidan, bai ga motar hubby ba, bai kawo komai a ransa ba. Malan idi ne ya shigar masa da kayansa, Tare da masa sannu da zuwa. Karar TV da yaji a falon hubby na kasa yasa shi nufar can. Cikin sallama ya shiga. Mariya dake zaune a kan carpet tana kallon Hausa film. Ta amsa tare da gaisheshi cikin Ladabi. Ta dauka bako hubby tayi, don bata san shiba. Ta ce " Anty bata nan." Kallonta yayi yana juya maganar a ransa. Cikin muryarsa mai dadi, cike da muskilanci ga hausar sai a slow ya ce " ina taje." " ta tafi makaranta, amma ta kusa dawowa." " makaranta, makaranta, ya fara juya Kalmar a bakinsa, kamar mai son gano maanarta." Jin yana ambatar makaranta, Mariya ta dauka bai gane bane, don taji hausar tasa wani iri, da ganinsa kuma ba bahaushe bane. Ta ce " makarantar islamiyya, nan kusa ne, ba nisa, yanzu zata dawo." Wucewa tayi da sauri, ita a dole zata kawowa bako ruwa, kamar yadda hubby ta umurceta in anyi baki. Ranshi a bace ya haura sama. lokaci yayi da zai takawa yarinyar nan burki. Yan zune ya kamata tasan waye Aliyu hayder..............   Kuyi hakuri, weekend bazaku jini ba, saboda hidimomi da nake dasu. Sai mun hadu Monday in sha Allah.   [07/03, 17:22] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 17       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... NOT EDITED Allah Allah Mariya ta ke hubby ta dawo, ta gaya mata wani balarabe yazo. Bata ji dadi ba data dawo dauke da ruwa ta samu baya nan. Hubby koda ta dawo ta samu malan idi na goge bike din hayder bata kawo komai ba, ta nufi cikin gida. Ko Jakarta bata ajiye ba, Mariya ta fara bata labarin zuwan balarabe. " Anty baki ganshi ba, mai kyau sosai. Na ce yanzu zaki dawo, kafin in shiga in dauko masa ruwa, ya tafi." Gaban hubby ne ya fadi, hayder ya dawo. Jakarta ta dauka tayi sama. Wunin ranar basu hadu ba. Da yamma su junaid suka zo, sun shiga sun gaisheta kamar yadda suka saba. Abubuwan sha ta tura Mariya ta kai musu, kafin ta tafi gida. Don in tazo da safe sai 5 take komawa gida. Yauma a wurin basketball ta jisu, har kusan magrib, sannan suka nufi masallaci. Yau hubby tun magrib ta rufe dakinta, don har lokacin tana cikin jimamin yadda hayder zai yi reacting kan maganar zuwa islamiyyarta. Ana sallar ishai, ya nufo gida, yau ko tsayawa karatun da yake dauka bayan sallar ishai bai samu ba. Dakin hubby ya nufa, amma ina yajita a kulle. Kwafa yayi, sannan ya nufi nashi dakin.                   **************** Da sauri -sauri, gudu -gudu, kamar yadda ya saba saukowa daga steps ko hawa. Dinning table din da hubby ke zaune tana break fast ya nufa, kujerar da take facing dinta yaja ya zauna. Kirjinta sai faman bugun tara-tara yake yi, mu samman kallon da yake binta dashi, yasa jikinta yin sanyi, ga wani faduwar gaba da take ji. Daurewa tayi, ta ci gaba da cin abincinta. Tambayar daya watso mata ne, ya sata saurin dago ido tana kallonsa. Shima idonsa a kanta. " ina kika je? Jiya na dawo, bakya gida?" Tabe baki tayi, tana juya dankalin da fork din hannunta. " meye damuwarka, don na fita?" Shiru yayi, yana karantar yanayinta. " da izinin wa? Kika fita?" Kallonsa tayi tare da waro ido waje, cikin mamakinsa. Musamman yadda yayi tambayar, Tamkar uba a gaban dansa. " don zan fita sai na tambayi wani?" Ta fada, tana kai dankali bakinta. " yes, tunda ba zaman kanki ki keyi ba ba?!" " Allah hayder ka fita a idona! Kai har ka isa, inki fita, sai na tambayi izininka? Ka sani duk lokacin da naji fita, fita zanyi." Ta fada cikin daga murya kadan. Jingina yayi, sosai a jikin kujerar. " ki sake fita bada izinina ba kiga, yadda zamu kwashe, karki rainamin hankali, nasan aure nasan kuma yadda yake. So be careful." " baka isa ba hayder kayi kadan! Ka kafamin doka da oder." Tashi yayi, ya nufi kitchen " let see." Ya fada yana shigewa ciki. Yana falonsa yaji tashin motarta. Lekawa yayi, ai kuwa fitan ta sake yi. Murmushi yayi, " yaro bai san wuta ba, sai ya taka." Ya fada yana gyara zamansa, ya ci gaba da aikin da yake yi a system.               ********************* Yau makarantar batawa hubby dadi ba. Don yau basuyi darasiba ko daya. Ilah waazi da aka musu. Daya shafi mata yan wuta, da dalilan shigarsu wuta, kamar hadith's din da yazo na cewa mafi yawan yan wuta mata ne, kuma sun shiga wuta ne, saboda yawan butulcewa mazajensu, da mazansu zasuyi shekara da shekaru, suna kyautata musu, duk ranar da aka samu sabani, sai ta ce meka taba min. Sannan malan ya gangaro kan sauran dalilan dake sa mata shiga wuta. Sannan ya kara musu da muhimmancin, sallah ga mace, sannan biyayya ga mijinta.  Da yawaita sadaka. Da yawansu sai da suka zubar da hawaye. Hubby samun kanta tayi, da tambaya. "Shin koda auren dole akawa mace, in batayi biyayya wa mijin ba, zata shiga wuta." " so sai ma, muddin an daura mata aure da mutun, dole ne, ta masa biyayya koda bata sonsa. In ba haka ba tabbas azabar Allah zata tabbata a gareta." Takai tacciyar amsar da malan ya bata kenan. Jikin hubby yayi sanyi, tsoro da fargaba duk sun cika zuciyarta. " mafita kawai take tunanowa kanta. Don bazata yadda haka kurun ta jawa kanta shiga wuta ba, gara in ma rabuwa ce, to su rabu. Don bazata iya masa biyayya ba." Wata daliba ce ta shigo da sallama, bayan an amsa mata, ta shaidawa muallim ana neman Habiba Munir a office din principal. Nan take muallim yaba hubby izinin zuwa amsa kira. Gabanta na faduwa, haka ta nufi office din principal. Tana tunanin dalilin kiran. Gabanta ne yayi mugun faduwa, ganin hayder zaune, a daya daga kujerun gaban table din principal din. izinin shigowa principal din ya bata, tare da nuna mata kujerar dake facing din hayder, alamar ta zauna. Kanta a sunkuye, ta zauna, ba tare data yadda ta kalli hayder ba. " gaishe da principal din tayi, cikin rawar murya." Fuskarsa dauke da murmushi " malama Habiba, haka ake, Ashe kinyi aure shine baki gaya mana ba? Da badan mai gidan yazo da kansa ba, da bamu sani ba, Baki kyauta ba gaskiya." Kanta a sunkuye, still muryarta na rawa " ayi hakuri. " " ba komai malama Habiba, gashi mai gidan ya ce daga yau bazaki sake zuwa ba, da sai in ce muna binki, shinkafa kaza. Na biki da bamu ci ba." Da sauri ta dago ta kalli hayder, ido hudu su kayi da juna, da sauri ta dauke idonta. " naji dadin ganin maigidan naki, hakika ki gode Allah, nasan hayder tun kuruciyarsa, ni na fara koyar dashi ilmin addini, shida sauran yan uwansa. Allah yasa albarka a aurenku, ya baku zama lafiya da zuria tsarkakakkiya." Nasiha sosai ya musu, kafin ya shige gaba hubby na bayansa, har Hall din da ake waazi. Nan yasa hubby ta musu bankwana. Basu ji dadin barin hubby islamiyya ba. Don sun saba da ita, saboda son jamaarta. Hubby naji tana gani haka, hayder ya tasota a gaba har wurin da tayi parking din motarta. Hannu ya mika mata alamar ta bashi key. Harara ta watsa masa kafin ta wurga masa. Da mamakinta ya cabe key din. A hankali yake murza sitiyarin, cikin kwarewa, har suka iso gida, ba wanda ya tankawa dan uwansa. Hubby takaici ne, ya cikata, data san abinda zai aikata mata kenan da ta hakura da zuwa makarantar har sai tasa Hajiya ta roka mata shi, tana matukar son makarantar, akwai koyarwa sosai, don ita dai, bazata taba iya tambayarsa ba. Yana tsaida motar tayi cikin gida. Juya kan motar yayi ya fita. A falonta ta tarad da Mariya da yusra, ai da sauri ta ajiye jakar suka rungume juna, suna murnar ganin juna. Tare da ihun murna. " baki da kirki ko kadan!!! Sai yanzu kika tuna dani?" Hubby ta fada suna zama a 2 sitter din falon. Kunne yusra ta kama, tana murmushi " tuba nake, tun da muka dawo daga abuja banda lafiya, shiyasa ban zo ba. Sai satin nan na fara fita." " ayya shine ko a waya baki fada min ba? Ai da nazo dubiya." Hubby ta fada tana murmushi Ido yusra tadan zaro. " ina ni ina fito da Amarya a dakinta. Ko Aisha sai jiya nake gaya mata." " to ya jikin? Duk da banji dadi ba da baki fada min ba, ko ba komai ai sannu tana da dadi." " sorry. Ya amarci?" Yusra ta fada tana murmushi Harara hubby ta mata, " yana wurin amaren asali." Mariya ce tama hubby sannu da zuwa, sannan ta bar falon. " su waye kuma amaren asali, ban da Ku?" Yusra ta fada tana dariya " su Aisha zaki tambaya." Ta fada Murmushi yusra tayi " har dake, kinga yadda kikayi kyau, kikayi fresh? Gaskiya amarci ya karbeki, kodai mun samu ne?" Duka ta dada mata a cinya. Da sauri yusra tasa hannu tana sosawa, saboda yanda dukan ya shigeta. Hararar hubby ta yi " daga fadar gaskiya, sai ki tafasamin cinya?" " wai ki dawo hankalinki ne, don na lura kamar kin kume, a ciwon nan." Hubby ta fada tana harararta " bakya kallon madubine halan? Amma duk wanda ya ganki ai yasan kin canza. In kuma mune baa son musan sirrin ai shikenan. Shi din ai dan duma ne baya boyuwa, da kansa ma zai bayyana kansa." Tsaki hubby ta yi, " zako Ku Dade kuna jira." " don Allah kar ki mana bakin ciki. Ki bada hadin kai sosai nan da 8 to 9month muzo suna." Yusra ta fada tana fuskar tausayi " Allah ya tsare ni, in ce na haihu da wa? " da kallo yusra ta tsare hubby Har hubby ta tsargu da irin kallon da take mata. " kallon na lafiya.?" A jiyar zuciya yusra tayi, tare da kyara zamanta. " family planning kike yi hubby? "  ido hubby ta zaro. " wane irin family planning kuma?" Ta tambayeta " gani nayi, in ba family planning kike yi ba. Mu muna da kyautata tsammanin in sha Allah kema ki samu rabonki, ki huta gorin rashin haihuwar da ake jifanki dashi. Tunda ko dama can ance miki komai naki is normal." Murmushi hubby ta yi " zan so hakan, amma situation din, da nake a yanzu, ba maganar haihuwa a gabana." Kallonta yake cike da tambayoyi. Ganin kallon da take mata, yasa hubby mikewa, "muje ki canza kaya, ki tayani mu daura girki." A tare suka nufi sama, ta bata wasu kayan ta canza, sannan suka nufo kitchen. Fried rice, pepper chicken da coslow. Suka hada. Yusra na kallon ikon Allah, yadda hubby ta zubawa kowa, har mai gadi, bataga  ta ware na maigidanba. Kasa shiru tayi, " banga kin zuba na hayder ba?" Murmushi hubby ta yi " in ya dawo zai nemi abinda zai ci." Da mamaki yusra ke kallonta. " ta yaya zaki dafa abinci, amma ace ba kwanon mijinki? Anya hubby? " " karki damu, kema kinsan halin hayder, shi yafi son hakan." Hubby ta fada tana daukan trey din data zuba musu nasu a ciki. " Allah ban yadda da ke ba." Yusra ta fada tana tsareta da ido. " shi kenan naji, mu ci abinci tukunna, sai muyi magana." Kada kai yusra tayi, ta dau trey din ruwa da drinks tabi bayan hubby. " hubby kiji tsoron Allah, ki rike aurenki da muhimmancin. Kar kibi, soye soyen zuciya, hakika zata kaiki ta baro. Menene laifin hayder? Kamar yadda kikayi biyayya, shimafa biyayyar yayi. Amma ace yayi cefane ya ajiye miki, amma ki dafa ki kasa bashi? Har sai lokacin da ya dawo sannan zai samawa kansa abin da zai ci? Bisa dukkan alamu hakkinsa ma na aure  ba bashi kike yi ba. A haka kike tunanin Allah zai barki? Hakkinsa ma kawai ya isheki." Ajiyar zuciya hubby tayi " bazaki gane ba wallahi, its very difficult for me." " ehmm!!! Kin zabi kiji kunyar lahira data duniya ko? Fine." Yusra ta fada Shiru hubby tayi tana jin jina lamarin. Gaskiya yusra ke fada, amma gaskiya abin da kamar wuya, ita da hayder? Kai ina, bazata sabuba, wai bindiga a ruwa. " ko zaki cemin ke baki da sauran filling ne?" Yusra ta jeho mata tambayar tana tsareta da ido. Ido hubby ta zaro, tare da yamutsa fuska. " a yanzu dai kam babu." Murmushi yusra tayi. Cikin ido sosai ta kalli hubby. " wallahi karya kike, ba yadda za'a yi ki ce baki filling, muma da bamu taba auren ba, ya muka kare, balle Ku da kuka san dadin abun. Ko matan da kike ganin suke kin kara aure, don mazansu sun rasu, ko sun rabu, zaki samu 80%  sun manyanta. Amma mace da kuruciyarta da komai, ta ce bata filling? Wannan tatsuniya ce kawai.  Ki daina cutar dan uwanmu ki barshi ya mori kuruciyarsa. Haka kurun, ga mata komai yaji, amma zaki hana ruwa gudu." " sai kiyi kuma ai." Hubby ta fada " Allah ya shiryeki, tunda na lura kin zama mai kunnen kashi, baa isa a gaya miki gaskiya ba." Yusra ta fada cikin bacin rai, tashi tayi ta yafa mayafinta, tare da daukar hand bag, " ni na wuce, sai wani jikon." Agogo hubby ta kalla, 5:23pm " tun yanzu? Ki bari dan can anjima sai ki yafi, please. " " nop!!!! Akwai inda zan biya, kafin in koma gida. Nama manta ban gaya miki ba, an sa bikina, in 1 month time. " Tsalle hubby ta fara, tana murna, tare da rungume yusra. " congratulation, I'm so happy for u. Woww!!! What a greet news." " thanks. " yusra ta fada tana murmushi. " aminu ko halil?" Hubby ta tambayeta cike da murna. " halil." " what a nice choice, kun dace, sosai wallahi. Allah ya kaimu lokacin." Hubby ta fada. Har mota ta rakota, sujayi sallama cike da kewar juna, Ta tafi.            ********************** Tana kwance a 3sitter dake falonta na sama. Jira take 9 ya cika taje ta kwanta, kafin hayder ya shigo. Don yanzu ta riga ta karanci lokacin dawowarsa. Rabin hankalinta na kan series din da ake nunawa, a tashar starlife, Rabi ya tafi ga tunanin waazin da aka musu dazu a islamiyya da kuma magan ganunta da yusra. Kamshin turaren da taji ya bugi hancinta, yasata dago da idonta, da sauri, ta kalli kofar falon.......... Gabanta ne ya fadi, kokarin tashi zaune ta fara, tunowa da kayan dake jikinta, yasa ta koma ta kwanta. Sanye take da aimless gown red. Roba ce, tabi jikinta sosai, kanta ko dan kwali babu, illah kama gashin da tayi donut dashi. A hankali ya karaso cikin falon, hannunsa daya dauke da mog, dayan kuma wani kwali ne, karami. Sanye yake da jallabiyya fara Sol, mai gajeren hannu. Zama yayi a kujerar da take facing nata, Ya daura kwalin kan center table. She is uncomfortable, mu samman da taji, an dau lokaci bai ce mata komai ba. Kasa hakuri tayi, duk da yadda zuciyarta ke faman biting. " what bring u hare?" Ta fada idonta na kan TV. Kafarsa daya kan daya, yana sipping Green tea, da yasha kayan kamshi, hankali kwance. Ganin bashi da niyyar tanka mata, yasa ta daga kai ta kalleshi, ido hudu sukayi. " am talking to u, wai me yasa ka gama raina nine." Ta fada a lamar ranta ya fara baci. Murmushin gefen baki yayi, sai da ya kara sipping Green tea dinsa, sannan ya kalleta, idonta a kan TV. " tunda kika tako gidan nan, a matsayin matar Aliyu hayder ai raini ya kare." Ido ta zuba masa, cike da mamakin maganarsa, shi din ma ita yake kallo. Murmushi tayi. " kai a tunaninka hubby ta shigo gidan nan don zaman aure? Uhimmm!!! Lallai kam, bude kunnenka da kyau kaji.  u are a big dreamer. I came to your house as your big sister, babu dadi babu kari. Har zuwa time din da zaka samu abokiyar zama, u are free to married your choice." Murmushi yayi har tana jin sautin mirmushin nasa. " I don't understand u" Harara ta watsa masa " bafa da Hausa, ko wani yare nake maganar ba,? Ina nufin dani dakai kowa yayi harkarsa, don't inter fare in my matters, nima I'm not inter fare in yours. That all." " yanzu na gane. Lokacin da zan wani auren, ke kuma inyi ya dake?" Ya fada still idonsa a kanta. " ina nan a matsayin sister dinka, mana." Ta fada Gira ya daga yana tabe fuska, " what about our parents?" " ba zasu sani ba, we just pretend." Tabe baki yayi, yana jijjiga kai, a hankali. " hakkokin igiya ukun dake kanmu fa? In mun boyewa iyayenmu, zamu iya boyewa Allah ne?" Ganin alamar nasara yasa hubby mikewa ta zauna da kyau. Gaba daya tama manta da kayan dake jikinta. Burinta kawai ya amince da bukatarta. " innalillahi wa inna ilaihir rajiun." Hayder ke maimai tawa a zuciyarsa. Wani shock yaji, lokaci daya, da wani abu dake bin duk wani bargo da gaba na jikinsa. Lokaci daya hankalinsa ya tashi. Ba wani lafiyayyen namijin da zaiga hubby a lokacin hankalinsa bai kai kololiwar tashi ba. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da dauke idonsa a kanta. Hubby Sam bata lura da kallon da yake binta da shiba. " wannan ai abu mai sauki ne,! Na yafe duk wani hakkina dake kanka, kaima sai ka yafe hakkinka dake kaina, kaga shi kenan an zauna lafiya.?" Kallonta ya kara yi, murya a shake, da kyar ya iya fisgo haruffan bakinsa. " kinyi tunani me kyau. Ashe zero Head din, wani lokaci yana ja." Da mamaki take kallonsa, gani tayi ya canza mata lokaci daya, amma bata kawo komai ba. Illa haushin zero head din daya fada. " amma kasan ban son rashin kunya ko?" Idon da suka canza kala ya zuba mata. For some time, ya kauda kansa. " lokacin baccinki yayi." Harara ta watsa masa " na fika sani ai. Ba mu gama magana ba. Ka yafe din ko yaya.? " in ban yafe ba, yazakiyi da ni.?" Ya fada idonsa can tv, kamar mai kallo, nan ko shi kadai yasan halin da ya ke ciki. " you have your girlfriend right? U love her. Me and u a not in the same page,  We never love each other. So what is the big deal? " ta fada cikin kosawa " let me think about it. Zamuyi magana gobe, zan gaya miki abinda na yanke." Ba haka taso ba, amma ba yadda ta iya, dole ta bashi lokaci, she hope he accept her idea. Mika mata kwalin da ya zo dashi yayi, " from Ummul khair. Nasan zata miki anfani sosai." Ya fada tare da gyara zamansa. Amsa tayi tana jujjuya kwalin. Gaba daya ta manta da Ummul khair ta ce mata, taba junaid sako ya bata, tun ranar da aka kai Kowacce gidan mijinta. Ta manta shaf da maganar sakon, bata tambayi junaid ba, da taga shiru bai kawo mata ba. Sai yanzu ta tuna. Mikewa tayi zata tashi, da sauri ta koma ta zauna, tare da rungume hannayenta duka biyu a kirjinta. Zuciyarta na faman dakan tara tara. " innalillahi. " ta fada a ranta. Kunya da jin takaicin kanta ya kamata. Idonta takai kan hayder TV yake kallo kamar bai san abinda takewa ba. Ganin hankalinsa na kan TV, yasa ta kwasa da gudu zuwa bedroom dinta. Da jikin kofar ta jingina, tana sauke ajiyar zuciya. A hankali ta isa gaban madubi. " la haula wala kuwwata illa billah." Ta fada ganin yadda kirjinta ya fito sosai a cikin rigar, hatta nippule dinta kana iya hango shatinsu. A tsaye suke char, kamar sa tsole maka ido. Su ba manya ba ba kuma kanana ba, Masha Allah.  Kunya da takaici ne suka cikata. Tabbas hayder ya gama ganeta tsaf, tana can tana shirmenta. No wonder taji muryarsa ta canza, lokaci  daya. " Allah ya isana." Ta fada tana shigewa toilet. Wani wawan ajiyar zuciya hayder ya sauke. Da ido ya bita, har ta shige bedroom dinta. Sannan ya dauke idonsa, tare da kara kashingida a jikin kujerar, don baya jin yana da sauran kuzarin da kafafuwansa zasu dauki gangar jikinsa zuwa bedroom dinsa. Kanshi ya dafe da hannu daya. Yasha ganinta ba hijab, amma bai taba tsayawa ya kare mata kalloba. No wonder, shi abun na daure masa kai yadda samarinta ke nunawa a kanta. Abin har haushi yake bashi, yaga me tafi sauran mata da suke nuna hauka a kanta haka? Tunawa yayi, da week din aurensu yadda suraj kangiwa ya zo ya sameshi, lokacin yana masallaci yana daukar karatu. Rokonsa ya fara, harda ko nawa yake so, zai bashi ya saki hubby. Murmushi yayi a lokacin " bazan iya abinda kake son inyi ba.?" Tsugunnawa yayi, yana rokonsa " nasan baka son Habiba, kamar yadda na kwana da sanin bata sonka. Don haka ina rokonka ka saketa. Daga million daya, zuwa billion zan baka in har zaka mun wannan alfarmar." Tsugunnawa hayder yayi shima. " kayi hakuri, tabbas bana sonta, iyaye suka hada mu, bani kuma  da ikon rabuwa da ita. Baka da kudin da zaka bani don in saketa, I have my on business, my on earning. Kudinka bazai sani in sabi mahaliccina ba. In saketa don ka aura, haramun ne, don haka bazan yi don in faranta maka ba. Shawarata a gareka shine ka rungumi kaddara, kamar yadda muka runguma da hannu biyu." Tashi yayi, ya barshi a wurin, yana mai jin tsananin tausayinsa. Tunowa yayi da Abdul Karim, yaya Ahmad, duk da shi bai bayyana nashi soyayyarba, amma ya kwana da sanin dan uwansa na son hubby. Salis da Engr Sahabi. Tabbas yaso hubby ta auri salis, don duk inda kamilin mutun yakai salis ya kai. Yana mutuntashi, da ganin girmansa matuka. Kamar yadda ya kwana da sanin matsayinsa a wurin Yusuf. Ajiyar zuciya ya sauke, tunowa da irin son da Yusuf yake mata. Magan ganunsa suka fara dawo masa one after the oder. Musamman haduwarsu ta karshe, bazai taba manta wannan lokacin ba. Kamar yadda abubuwan da suka faru a lokacin ba zasu taba gogewa a ransa ba. Mutun baya taba gujewa kaddararsa tabbas haka abin yake. Tunanin maganganunta na yanzu suka fara dawo masa, Murmushi yayi yana shafa sajensa a hankali. Duk da baya sonta, shi ba jahili bane, yasan tanada hakki a kansa, daga lokacin da aka daura aurensu, kamar yadda yake da hakki a kanta. Dama ya daga mata kafa ne yaga iya gudun ruwanta. Yanzu ne zaa fara wasan. Don ba zai taba yafe hakkinsa ba. Ama tsayinsa na lafiyayyen namiji, wanda yake ganiyarsa. Ba zai iya hakuri ya zuba mata ido ba. Ganinta a yanzu ya kara masa son kasan cewa da ita. Mikewa yayi, ya kashe komai, ya nufi bedroom dinsa, wanka yayi, tare da shirin bacci. Gaba daya daren baccin hayder kadan ne. Daya rufe idonsa surar hubby ke yawo a danuwansa. Dole ya tashi ya fara nafila.                ****************** Sai da tayi shirin kwanciya, sannan ta dauko kwalin ta bude. Dariya tayi ta daga bulalar tana kallo. " ya Allah ka shiryi Ummul khair. " ta fada tana Ciro karamar takardar dake ciki. " special gift to my beloved sister. Karki raga masa ko kadan, naji su Anty ummu khulsum na cewa ki bishi a hankali.  In ya miki ba dai dai ba, Zaneshi zakiyi sosai, jikinsa ya gaya masa, ba daga kafa, in ba haka ba rainaki zai yi." Dariya hubby tayi tunowa da ranar da hayder ya aunata da bike dinsa. Watan Ummul khair bata manta maganar bulala ba. " yar banzan yarinya, zamu hadu ne." Maida bulalar tayi ta ajiye. Maganar hayder ce ta fado mata. " nasan zata miki anfani sosai. " me yake nifi? Haka taita kokarin hasaso abinda maganar ke nufi ta kasa, don haka, ta tattara ta watsa tunanin a kwandon shara.               ******************* Da safe basu hadu ba, kamar yadda suka saba tashi, kusan a tare. Don hayder baccin da bai samu da daddare ba, yake ramawa. Hubby kam abun ya mata dadi, don bata shirya fuskantarsa ba. Har yanzu yana jin kunyar yanda ya ganta. Sai bayan sallar la'asar ya sameta a falon ta na kasa, ita da Mariya. Shigowarsa Mariya ta fita, bayan ta gaishe shi. Yanzu kam ta San shine mai gidan, saboda yawan ganinsa da takeyi. Sannan tasan duk baki mazan da sukeyi iyakarsu falon gasa, amma shi sau da yawa tana ganinshi ya sauko, ko zai hau. Zama yayi, tare da mikar da kafarsa daya kan center table din gabansa. Sun kai 15min ba wanda ya tankawa dayansa. Kunya da haushinsa ne suka hana hubby magana. Cikin muryarsa mai kama da anmasa dole, don sanyi, da yadda yake fitar da haruffan bakinsa. " I accept, amma ina son muyi a rubuce, kar daga baya ki canza magana." Murmushi tayi, nan da nan farin ciki ya cika ranta. Mikewa tayi da sauri ta nufi of stairs, minti kadan sai gata da pepper da pen, Mika masa tayi. Kallon pepper din yayi, ya kalleta. " ke kika bukata, don haka ke zaki rubuta." " OK. Me kake son in rubuta?" Ta tambaya tana kallonsa Tabe baki yayi, yana shafa sagensa, alamar ya zama masa jiki, yin hakan. " fist ki fara jero hakkin mata a kan mijinta, then hakkin miji kan matarsa. U write kin yafe duk kan hakkokinki dake kaina. Then sai kiyi sign. I will write my on, sai kowa yayi sign. Sai muyi photocopy kowa da nashi. Then shi kenan." Zama tayi, ta fara jero su, kamar yadda ya bukata. Duk da wasun ta kanji nauyi da kunyar rubutawar. Hakkin mata a kan mijimatarsa::;- 1. Ya biya ta Sadakinta na Aure. 2. Ya kula da Addininta. 3. Ya daukin nauyin cinta, shanta, suturarta, har da kayan kwalliya nata. 4. Ya ba ta hakkinta na aure. 5. Ya dauki nauyin kulawa da lafiyarta. 6. Ya daukin nauyin karatunta musamman ma na Addini. 7. Ya nuna mata soyayya a fili. 8. Ya rika mu’amala da ita a cikin sauki kamar karamar yarinya. 9. Idan ya shigo gida ya rika sakar mata fuska da fara’a. 10. Ya rika yaba mata idan ta yi abin kirki tare da yi mata Addu’a ta fatan Alkhairi. 11. Ya rika sauraron korafe-korafenta da shawarawarinta. 12. Ya rika yafe mata idan ta yi masa ba dai-dai ba, kuma yana gyara mata cikin hikima. 13. Ya rika yin kwalliya da ado domin ta gani ta ji dadi. 14. Ya ba ta lokaci na musamman a lokutansa domin yin hira da ita kawai. 15. Ya rika cin abinci tare da ita. 16. Ya ringa taimaka mata wajen aiyukan gida musamman idan ta samu rauni na laulayin ciki ko na rashin lafiya tare da tausaya mata. 17. Ya rika nuna damuwa cikin abin da ta damu da shi, da farin a cikin abin da take farin ciki da shi matukar bai saka wa Allah ba. 18. Ya girmama iyayenta da ‘yan uwanta. 19. Ya ringa yi mata kyuata ta musamman domin faranta mata rai. 20. Ya rika fita da ita wurare na musamman kamar ziyara ko wurin karatu ko wurin shakatawa. 21. Ya rika b oye aibinta. Hakkin miji a kan matarsa::;- 1 – Soyayya ta gaskiya. 2 – Tsare Amana Miji. 3 – Tausasawa miji da wasa da dariya da shi. 4 – Tsare sirrin miji. 5 – Ba za ta fita daga gidansa sai da izininsa. 6- Ba za ta yi azumin nafila ba sai da izininsa. 7 – Ta yarda ya sadu da ita duk lokacin da yake bukata, dan Annabi Mai tsira aminci yace duk matar da taki mijinta ya sadu da ita a duk lokacin da yake so, toh Mala’iku zasu ta la’antar taba zasu su daina ba har sai lokacinda ta yarda da shi. (BUKHARI/MUSLIM). 8 – Ta saurari mijinta kuma tayimasa biyayya matukar ba aikin laifiya umurceta dayi ba. 9 – Mace ta nisanci raina abin da mijinta ya bata, domin Annabi Muhammad mai tsira aminci ya ce “Mata zasu shiga wuta ne saboda kafurce wa mazajensu, wato raina alherin miji” (BUKHARI/MUSLIM) 10 – Ka da mace ta cutar da mijinta da magana ko da aiki. 11 – Mace tayi ado da kwalliya wa mijinta, saboda Annabi mai tsira da aminci yace “Allah kyakkyawa ne, kuma yana son kyakkyawan abubuwa, (IMAM MUSLIM YA RUWAITO). 12 – Mace ta tsare dukiyar mijinta da na ‘ya’yansa harma da na gidansa, dan Annabi mai tsira da aminci ya ce “Mace mai kiwo ce a gidanta, za’a tambayeta abin da ta kiwata. 13 – Mace tayi gaggawan baiwa mijinta hakuri a duk lokacin data ga yayi fushi, Tace masa, dan Allah kayi hakuri, ban san abin da na yi zai ba ta ma ka rai ba, ka yafe mi ni dan girman Allah. 14 -Mace ta yiwa mijinta dukkan irin aikin da ake bukata ayishi a gida. 15 – Mace ta kyautata halayenta ga iyalan mijinta. 16 – Mace ka da ta yi abokantaka da mugayen kawaye, sai su hallakar da ke baki sani ba. 17 – Mace ta zama mai tausayawa mijinta, kamar yadda uwa take tausayin ‘Danta. 18 – Mace ta zama mai Biyayya ga mijinta. 19 – Mace ta zama Abokiyar rayuwa ga mijinta. 20 – Mace ta kusanci dukkan abinda mijinta ya ke so. 21- Mace ta nisanci dukkan abin da mijinta ya ke ki. 22 – Ki yi murmushi a duk san da mijinki ya kalle ki. 23 – Ki yi masa addu’a a duk lokacin da zai fita, ki ce a dawo lafiya Allah ya bada sa’a. 24 – Ki yi masa addu’a kuma a duk lokacin da bakya ganinsa bayan bayanan. 25 – Idan mijinki ya dawo ki karbi abin hannunsa, tare da yi masa sannu da zuwa, dan girmama shi. 26 – A duk samda zakiyi magana da mijinki ki gaya masa magana mai dadi, mai tabshi, kada ki daga muryanki a kan nasa, kuma kada ki masa tsawa har ki harare shi. 27- Ki zama cikin tsabta da kamshi mai dadi duk lokacin da kuke tare. 28 – Ki sanya hijabi a duk lokacin da kuke tare da wadanda ba muharramanki ba. 29 – Ki sa lokaci idon ki, ki kuma shafa jan baki, kuma ki shafa turare, amma sai kuna tare dashi a gida dan mace bata shafa turare ko jan-baki ta fita anguwa dashi. 30 – Ki kaskantar da kai dan biyayyaa gare shi. 31- Ki san lokacin da yake dawowa dan kada ya sameki a cikin kazanta, ki kuma san lokacin cin abincin sa dan ki tanada ba sai ya zo yana nema ba. 32 – Bayan kin gama masa komi ki tambaye shi ko yana da wata bukata a gareki, dan mi biya masa ita. 33 – Kar ki nuna murnan ki idan wata hasara ta same shi, ki nuna masa kamar kece kika yi hasarsar. 34 – hakanan kiyi murna da duk wani alherin daya samu. 35 – Ki zama kamar matan sahabbai, yadda sukewamazajensu. Idan miji zai fita sai su ce a dawo lafiya, kar ka kawo ma na haram zamu iya hakuri dayunwar duniya, amma baza mu iyahakuri da azaba ba gobe lahira. Kallonta yake yadda ta Dage sai zuba rubutu take. Murmushin gefen baki yayi yana kada kai.  Mika masa tayi. " I'm don."  Ta fada tana murmushi Amsa yayi, yana bin abunda ta rubuta daki daki. Murmushi yayi. " Ashe ba zaman cika benci kike a makarantar ba?" Ya fada still idonsa a kan pepper din. Harararsa tayi, " just sign, ban tanbayeka dogon turanci ba. Koma mai zaka ce, ka dade baka fada ba." Kansa ya dago yana kallonta, mika mata hannu yayi, pen din ta sa masa a hannun. Tana watsa masa harara. Don taji haushin maganar daya fada. Badon tana son su rabu lafiya ba, da sun kwashi yan kallo. Ya daura pen din kenan zaiyi sign sukaji nocking, gaba daya suka kai kallonsu ga kofar shigowa.......   [07/03, 17:27] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 18       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... " just sign, let me cheek the door. " ta fada tana nufar kofar. Ahmad ne da iyalansa. Yaran na ganin hubby ta bude kofar suka dale jikinta, suna dariyar murna. Itama dariyar ta fara tana kara rungumosu jikinta. Murmushi munaya tayi. " ni dai aban hanya na wuce, na gaji da tsayuwa." Dariya hubby tayi ta daga jenior, tare da rike hannun ashraf suka shiga ciki, tana musu bisimillah. Da sauri hayder ya taso rungume dan uwansa yayi, tare da goga kumatun juna, kamar yadda suka saba. Sannan ya fara daga yaran sama suna dariya. Tasnim ya amsa a hannun munaya, sannan ya gaisheta. Jan dan uwansa yayi, suka nufi main falo. A kabar hubby da munaya da yara. Kitchen ta nufa, yaran na biye da ita, sai zuba mata surutu sukeyi. Kayan sha ta hada a trey taba Mariya takai main falo. Sannan ta dauki na munaya suka fito. Zama tayi bayan ta ajiye trey din. Sannan suka gaisa, cikin mutunci kamar ba abunda ya hadasu. " a mana afuwa, bamu samu zuwa ganin daki da wuri ba.?" Munaya ta fada tana murmushi Murmushi hubby ta mayar mata " ba komai, ai gashi kunzo yanzu." Gaba daya hubby ta kasa sakewa da ita, hakan yasa da yawan hiran ita da yaran suke kayansu, sai jefi jefi, munaya ke saka musu baki. Ita kanta kunyar hubby take ji, abinda ya Jamata rashin zuwa tun tuni kenan, sai yau da Ahmad ya matsa mata tukunna. Mariya ce ta shigo, tama hubby sallama, lokacin tafiyarta yayi. Kallon ta hubby tayi. " Mariya yau kam, zaki min hakuri, zuwa dare sai in sa a mayar dake gida."  Kada kai Mariya tayi " to Anty, amma zaki kira mama ko? Don kartaga shiru."  Phone hubby ta dauka zata kira mmn Mariya. " ki barta kawai ta tafi, I will help u" munaya ta fada Ba yadda hubby ta iya, ta sallami Mariya ta tafi. Kitchen suka nufa, nan idon munaya ya raina fata. Da kallo takebin ko ina na kitchen din. " woww!!! Gaskiya Anty hubby gidanki ya burgeni ba kadan ba." Munaya ta fada tana kara kallon kitchen din. Murmushi hubby tayi " na gode." " me zamu dafa?" Hubby ta tambayeta. " abun dadi, kin san nayi missing din girkinki sosai." Munaya ta fada tana murmushi Murmushi hubby tayi, tunowa da old-time. Book ta mikewa munaya "  duba mu gani, ko akwai abunda zamu iya yi a ciki." Wani hadadden drawer hubby ta bude, ba komai a ciki sai chocolate kala kala, da kwalayen Lipton, green tea, black tea, English break fast, flavour tea gasunan kala kala. Chocolate ta zuba a plate, ta nufi falo inda su jenior ke kallon cartoon. Ta basu, ta koma wurin munaya, da ruwan ido ya hanata tsayawa a kan girki daya. Suna aiki, suna hira jefi jefi. Munaya ta kalli hubby dake soya rice. " Anty hubby don Allah kiyi hakuri ki yafe min abinda ya faru, wallahi sharrin shaidan ne, da zugar su Anty samira. Sai rikicin aurenki da Abdul Karim nake jin komai, na makircin da take kullawa a kanki. Kunyarki ta hanani zuwa gidan nan. Don Allah kiyi hakuri. " Murmushi hubby tayi, tare da sauke ajiyar zuciya. " na dauka kinfi kowa sanin halina, a lokacin sama da ita? Saboda nafi kusa da ke a kanta. Na dauka ko wani ya fada wannan maganar a kaina, ke me bada shaida ce gareni. Bazan boye miki ba naji zafin abinda kika mun a cikin jamaa, wanda da ni dake ne, bazan damu sosai ba. Amma ba komai na yafe miki, komai ya Riga ya wuce. Sai dai ina son kisa a ranki. Hubby bata taba son wani ba, bayan Yusuf. Tsakanina da Ahmad mutunci ne, da ganin girman juna, Nothing more." " kishine ya rufe min ido, a lokacin. An sha kawo min gulmar, ban taba daga kai ba, sai lokacin. I'm sorry " " ba komai ya wuce. I understand." Hubby ta fada Hira suke yi, suna dariya kamar ba abinda ya taba faruwa. Dama can akwai shakuwa tsakanin hubby da munaya. Munaya bata da matsala, barta dai da son class, komai nata irin na big class take yi. Hayder ne ya leko, ya shaida musu sun wuce masallaci, har da yaran. Suma lokacin sun kammala komai, hubby na wanke kayan da suka bata, munaya na goge -goge. Sai da hubby ta shirya musu abinci a dinning din main falo, nasu kuma, suka haura dashi falon sama. Wanka sukayi bayan sun idar da sallah. Wani hadadden arebian dress hubby taba munaya tasa. Sannan suka nufi falo don ba ciki hakkinsa. Santi kawai munaya ke zubawa. " Allah kinji da dinki, ina ma ni na iya girki haka. Munyi missing abincinki sosai wallahi. " murmushi hubby tayi. Don a zamanin baya sau da yawa gidanta munaya take zuwa suyi girki ta dauka zuwa gidanta. Expectially weekend's. Wani lokaci kuma, hubby ke girkawa ta aika musu. Bayan sun tattara wurin. Munaya ta dauko Jakarta. Mikawa hubby wata Leda tayi. " gashi kowanne da yadda zakiyi anfani dashi, suna da kyau sosai. Tun daga Niger aka kawomin su." Amsa hubby tayi, tare da godiya. Don bazata iya ce mata tabar kayan ta ba. Ko ba komai ta ajiyewa  Aisha ko su ummu sulaim. Duk wandda Allah ya kawo ta. Wani tablets ta fito dashi, guda biyu tasha daya ta mikawa hubby daya. " ki sha wannan ki gani, a kwai aiki. In ya miki next time in zaa kawo min, zan ce a kawo kwali biyu." Kai hubby ta kada " ki barshi kawai Maman junior in zaa kawo miki, a kawo mana tare." Ta fada don karta dagota. " no. Kin san kalan kyansa.? U have to try it." Munaya ta fada tana ballo tables din daga gidansa. Ganin hubby tana mata wasa da hankali, yasa ta bata rai. " Allah sai kin sha, ke matsalata dama dake kenan. Dole mutun ko yana da kyau ya kara da wanka." Ruwa ta zuba a cup ta mikawa hubby. Dole yasa hubby amsa. Ruwa ta kurba, tare da jefa tablet din a baki, da niyyar ta ma munaya wayau ta ajiyeshi a bakinta for some second taje ta zubar. Tana jefawa a bakinta ya wuce. Ido ta zaro. Tare da  fadin " innalillahi wa inna ilaihir rajiun." A kasan ranta. Dariya munaya tayi, ganin yadda hubby keyi da fuska. " bafa shi da wani taste," ta fada don a tunaninta, ko taste din ne baima hubby ba. Hira suke yi sama, sama, munaya ta kalli hubby. " wai Anty hubby bakya gajiya da wannan zunbulelen hijab din ne? Tun da muka zo kike ta fama, har girki duk dashi, ko zafi bakyaji? Kamar wata matar malan." Murmushi hubby tayi, ba tare data tankawa munaya ba. " au!!!! Sorry, ashefa matar aramma ce. Amma don Allah adinga cirewa ana shan iska. Ni ina zan iya?, sallama Allah- Allah nake in idar in cire." Murmushi hubby tayi kawai. Sai after 8 su hayder suka shigo. Yau ne rana ta farko da hayder ya saka abincin hubby a bakinsa. Shi din ma don gudun kar Ahmad ya gano, irin zaman da sukeyi ne. Yasa shi zuba soup din kaza. Ahmad kam santi yayi ta zubawa. Tare da gayawa hayder yadda sukayi missing girkin hubby. Shi kansa bai san ta iya girki haka ba. Yasan dai duk lokacin da ta kawo, kamshin girkin na kayatar dashi, amma bai taba marmarin dan danawa ba, duk da santin da yake jin su Hafiz nayi. Sai after 9 su Ahmad suka musu sallama. Set din sarkar gold mai kyau da girma yaba hubby. A matsayin gudunmawarsa. Godiya sosai ta masa. Tare da cika yaransa da kayan zaki, Leda guda. Suka rakosu har mota. Cike da kewar juna suka rabu, suna daga musu hannu. Suna shigowa hayder ya wuce sama, ba tare da sun cewa juna komai ba. Duk da taso ta tambayeshi maganar takardar yarjejeniyarsu. Amma ganin yadda ya hade fuska, yasa itama ta shareshi. Kayan da suka ci abinci dasu ta tattara, tare da gyara wurin.  Sai da ta wanke su tsaf, sannan sauran abincin ta sasu a containers ta sa a fridge. One this about her. Bata son barin ko cokali, ya kwana ba tare data wanke ba, Matukar anyi anfani dashi. Direct toilet ta nufa, ruwan sanyi ta sakarwa kanta, Saboda yadda take jin jikinta. Hadadden man culachum, ta shafa sama- sama, tare da sanya kayan baccinta, Aimless da boom shot. Fink colour. Gashinta ta kama ta nade shi, kafin ta saka hula pink. Shigewa cikin duvet dinta tayi tare da karanto adduoin kwanciya bacci. Juye- juye ta fara, tana jero tsaki. " haka kurun ina managing kaina, tazo ta tsokalomin fitina." Wata zuciyar Hubby ta fada. Tana kara Jan tsakin. Zuciyarta ce ta fara mata wasi- wasin anya kuwa tasa key a kofarta? Don shigowarta Allah -Allah take ta shiga toilet ta watsawa kanta ruwa. Ganin ta kasa samun natsuwa yasa ta sakko ta nufi kofar, cike da kasala, da nauyin jiki. Tana kokarin kai hannunta kan kofar, yana turo kofar tare da shigowa cikin bedroom din. Sanye yake da kayan bacci, marasa nauyi, Riga da dogon wando. Light blue. Ido hubby ta zaro tana binsa da kallo, don bata taba tsammanin yanada karfin zuciyar da zai sake shigo mata bedroom ba. Matsawa tayi, ganin jikinsu na neman gogar na juna. Hakan ya bashi damar murza key din, tare da zareshi daga jikin kofar. Zuciyarta ta fara dukan tara- tara, " what bring u hare at this time? " ta fada tana mai hadiye yawu dakyar. Don a tsorace take, smacking yayi, yana kara jingina da kofar, hannunsa duka biyu nade a kirjinsa, kamar yadda ya harde kafafunsa biyu. Daga inda take tsaye tana iya hango faffadan kirjinsa dake bude, ga six pack dinnan sun fito sosai masha Allah. Kana ganinsa kasan akwai karfi, yadda damtsen hannunsa suke a murde, ga jijiyoyi sun fito  sai daukar ido suke,  jikinta ne ya dau rawa ganin kallon da yake binta dashi, yasata tunowa da kayan dake jikinta. Da sauri ta juya don ta sa hijab dinta. Bataji takowarsa ba, sai ji tayi an kwace hijab din. Da sauri ta waigo sukayi ido hudu. Jikinta na rawa kamar yadda muryarta ta dau rawa. Wurga hijab din yayi can gefe. " what come over u." Ta fada cikin rawar murya. Murmushi yayi, tare da daga mata gira. " laifine don miji ya shigo dakin matarsa?" Ya fada in husky tone. Zuciyarta ne ya kara tsananta bugawa. Kallonta sosai hayder keyi tare da furta " fatabarakal lahu ahsanul khalikin." A kasan zuciyarsa. Wani irin filling ya ke fisgarsa zuwa gareta. Duk da ba abin daya shigo dashi ba kenan. Hannunta ta hada duka biyu, jiki na bari. " don Allah ka fita, koma meye zamuyi magana da safe." Bakinta yake kallo zuciyarsa na saka masa abubuwa da yawa kanta. A hankali ya fara takowa zuwa gareta. Ganin haka yasa ta fara ja baya, still hannunta a hade, tana mai maita " please please. " gaba daya ta gama rudewa da yanayinsa. Ritsata yayi, lokacin da takai bangon dakin. Hannayensa duka biyu yasa ya dafe bangon dashi, ya sata a tsakiya. Zuwa lokacin hubby sumane kawai batayi ba don tsananin fargaba, don gaba daya ya canza mata, kamar ba hayder data sani ba. Fuskarta ya dago da daya hannunsa. Da sauri ta runtse idonta, don bazata iya kallon cikin idonsa ba. Cikin karfin hali " please hayder don't do this to me, I'm your sister, Please." Murmushi yayi, har tanajin sautinsa a kunnenta. A hankali yakai bakinsa kan nata. Gaba dayansu wani shock ne ya ziyar cesu a tare, ga hubby kan tsananin tsoro, ne ya kara cika mata zuciya. Datse hakoranta tayi, taki bashi damar samun abinda yake so. Tana jin sautin murmushinsa a kan fuskarta. Gaba daya ya rungumota jikinsa, yayin da daya hannunsa ya fara yawo a jikinta. Still bakinsa na kan nata, yana lasan labbanta a hankali kamar yaro ya samu alawa. Kokari ta fara don ta kwace jikinta, amma ko gezau, hannunsa da taji a kirjinta, yasa ta bude baki, don tayi ihu. Hakan yabashi damar zura harshensa sosai cikin bakinta. Duk yadda hubby taso kwatar kanta ta kasa, tun tana dan turjewa, har itama sakon ya fara kaiwa ga kwakwalwarta. Abinka da an dade baa haduba, ga aikin munaya. Gaba daya tsayuwar ta gagaresu, dagata yayi cak, zuwa saman bed dinta. Sunkai tsawon lokaci, suna sarrafa juna. Hayder yakai kololuwar bukatuwa da ita, yana gaf da cimma burinsa. Tunanin basuyi nafila daya dace suyi ba, ya masa birki, duk yadda yaso yayi ignoring din abun ya kasa. Dole yadan janye daga hubby yana sauke ajiyar zuciya, Tare da gangameta a jikinshi sosai. Kara narkewa tayi a jikin nasa. Don gaba daya tunaninta ya dade dayin kaura daga jikinta. Gaba daya hayder ya gama rikitata da salonsa. Daga ita har shi ajiyar zuciya suke sakewa a hankali. Iskar bakinsa, ya hura mata a fuska. Far tayi da idonta, wanda ya kara mata kyau. Kar idonta ya sauka a kan hayder. Kamar ringing din bell haka taji a tsakiyar kanta. Ido ta zaro, tare da mikewa da sauri. Kokarin sauka daga bed din tayi, zuciyarta na zafi, da kuna, takaici, da haushin kanta duk sun cika zuciyarta a lokaci daya. Kara tayi, tare da janye duvet din dake tattare a gefe, ta rufe jikinta, tare da yin toilet da gudunta. Yana daga kwance yana kallonta, gaba daya jikinsa ba kuzari. Murmushi yayi ganin tayi toilet da gudu. Tana sa key din kofar, ta jingina tare da fashewa da wani irin kuka, mai cin rai. A zaune take dirshan tana kuka iya iyawarta. A hankali ya tako zuwa jikin kofar, kwankwasawa yayi, yana kiran sunanta. Daga inda yake yana jiyo sautin kukanta. Yakai 15 min a tsaye, yana faman kwankwasawa, taki budewa. " ka fitar min a daki, ban son ganinka, mugu sai Allah ya sakamin." Ta fada cikin muryarta data fara dashewa don kuka. " just open the dam dor." Ya fada in high tone " anki din. Da in kwana da kai gara na kwana a toilet." Ta fada Ranshi ya fara baci, yanzu kam. " in kin so ki shekara a ciki." Ya fada cikin bacin rai " yafi min ganinka ai, mara kunyan banza. Tun mutun bai tafasa ba yana son ya kone." Murmushi mai ciwa yayi " ni kike gayawa wannan maganar, don na nemi hakkina a wurinki? In kin isa ki fito ki gaya min face to face mana." Ya fada cikin bacin rai Tsaki hubby tayi. " duk maitarka wallahi bazan fito ba. Kuma An fada din kayi abunda zakayi. Mara kunyan yaro. Kwalelen kare da hantar kura, nan gani nan bari, kar kuma in kara ganin kafafuwanka a dakin nan, in ba haka ba duk abinda na maka, kai ka siya da kudinka." Shi abinma dariya ya fara bashi. Wannan shine, ga tsoro ga ban tsoro. " ki jika kisha in kin isa!! Keep that in mind da kanki zaki kawomin kanki, ina shararren wurina. Bana bukatar sake zuwa dakinki. Wannan shine alkhawarin hayder to u." " Allah ya kiyaye,." Ta fada tana Jan tsaki. Murmushi yayi, " zamu hadu ne, very soon, zakiyi bayani." Ya fada yana maida kayansa. Sannan ya fita zuwa dakinsa. Wanka ya sake, sannan yayi shirin bacci. Daya rufe idonsa moment dinsu yake gani a idonsa. Murmushi yake ta sakewa cike da nishadi, don shi kadai yasan garar daya kwasa, duk da bai kai inda yaso ba, amma he's happy. A haka har bacci ya sace shi. Hubby kam, jin fitarsa, yasa tai saurin fitowa ta sawa kofarta key. Toilet ta koma, tayi wanka, tare da Dirje jikinta sosai, tanayi tana hawaye, tuno da yanayin da suka kasance ita da hayder. Ihu ta sake tare da durkushewa a wurin. Abune da ko a mafarki bata taba kawawa ba, ta dauka ko giyar wake hayder yasha bazai tunkareta da bukatar shiba, but she is mistaken. Tabbas ta yadda namiji ba kunya, tunda har ya iya shafawa idonsa toka. Allah ya isa tafi kwando dubu, ta jawa munaya da hayder. A ganinta da badan tablet din munaya ba, ba abunda zai sa tayi losing control dinta irin haka. Yau gaba daya bacci kaura yayiwa hubby. Tunanin rayuwa, da tunanin Yusuf su suka tsaya mata a rai. After all mamakin hayder da karfin halinsa. Tabbas sai ta dau babban mataki a kansa, in har tana son ta zauna lafiya...... Yau da farin ciki hayder ya tashi, rabon da ya tsinci kansa cikin farin ciki haka, tun kan aurensa da hubby. Har ya gama break fast, ba hubby ba alamarta. Dama ya kwana da sanin ganinta zai masa wuya kam. Murmushi yayi daga gani na mugunta ne, ya kara kai kallonsa steps din. Key din bike dinsa ya dauka yayi gaba. Sai da ya dan tsaya typing a wayarsa, yayi sending tukunna, ya tada bike dinsa, malan idi ya wangale masa get, tare da kwasar gaisuwa. Ya fice abinsa. Tana tsaye daga window taga fitarsa. Tsaki taja. " jishi sumi sumi, kamar in an sa masa hannu a baka bazai ciza ba." Ta fada tana sake labulen. Sannan ta dau hijab dinta ta zunbula, ta sakko donta nemama kanta abin da zataci. Sun gama gyara gidan, tare da sa turaren wuta, mai matukar kamshi. Ta haura sama donta dauko wayarta data manta a bedroom dinta. Miss calls ne, sai sms. A hankali ta fara bin sms din. Har tazo kan wani un save number, kamar bazata budeba wata zuciyar ta ce ta bude tagani. " ki shirya kije ki gaida su mommy, Hajiya da Hajiya babba, Hayder "  tsaki taja duk da taji dadi, don ta dade tana son zuwa, amma saboda sai ta tambayeshi, yasa ta gwammace taita zama a gida. Cike da murna da doki ta fara shiryawa, cikin wani rantsatstsen less light yellow, dinkin doguwar Riga, taji aikin da stones. Light blue na hijab mai hannu, da shoe and bag light blue. Tayi kyau sosai.  gida ta kai Mariya, sannan ta wuce gidan Alhaji babba. Tarba Sosai ta samu, tayi saa Alhaji babba na gida. Turaruka masu tsada da kamshi, ta kawo musu. Ta dade tare dasu, sannan ta musu sallama, nasiha sosai suka kara mata. Gidansu ta wuce, a harabar gidan taci ta tarad da su junaid. Ranta bai so ba don yanzu dukansu haushinsu take ji. Da faraa suka gaisheta. Dole haka ta saki fuskarta ta amsa musu, tare da shigewa ciki. A kofar shiga falon mommy Hauwa sukayi karo da hayder dake fitowa, Da sauri taja baya. Tsayawa yayi, yana kallonta. Kin dago kanta tayi, don haushinsa dosai ta keji, da kunyar ya gama ganeta. Murmushi yayi tare da furta " sorry " a kasan makoshinsa. Ya bi gefe ya wuce. Da harara ta raka shi, har ya bacewa ganinta, sannan ta shige ciki da sallamarta. Mommy Hauwa na zaune a falo da jafar hubby ta shigo. Tana arba da mommy Hauwa a zaune da gudu ta je ta rungumeta. Dariya mommy Hauwa da jafar suka sa. Jafar ya ce " yar halas taki anbato, yanzu dama mijinki yake cewa kina nan zuwa, Ashe ma har kin iso." Harararsa tayi, jin ya kira hayder mijinta. Dariya yayi, don bai gane dalilin harararba. " harara daga zuwa? Allah ya baki hakuri." " nayi fushi da kai da jabir. Don haka karma ka kulani." Ta fada tana turo baki cikin shagwaba. Kunne ya kama " tuba mukeyi sis, jiya muke maganar zuwa wurinki da jabir.'" Harararsa tayi " ba wani nan!! Don ka ganni ne, shiyasa. Amma na tabbatar kun manta dani kwata kwata, ba zuwa ba waya. " Mommy Hauwa ya kalla, yana mata alamar tasa baki. Dariya mommy Hauwa tayi. " karka sani a ciki, ba ruwana." " kai mommy!! Kina wurinfa muke maganar zuwa gidanta." Ya fada cikin shagwaba, kamar wani karamin yaro. " zan rama, very soon. "  ta fada " very sorry, muna nan zuwa, da zaran jabir ya dawo zamu zo." Ya fada cikin miryar lallashi. " ina nan ina jira." Ta fada Mommy Hauwa taji dadin ganin yadda hubby ta kwantar da hankalinta, tayi kyau ta murje. Duk inda hubby ta gilma idon mommy na kanta, cike da jin dadi. Hubby taji dadin yadda mommy Hauwa ta sake da ita, suka sha hirarsu, cikin hikima ta dinga tambayar hubby game da zamanta da hayder. Hubby nuna mata tayi komai normal ba wani problem. Sai after 2 sannan tai sallama da mommy ta nufi main house. Duk da bataji  dadin rashin ganin daddy dinta ba, saboda tafiya da yayi. Part din Mmn samira ta fara zuwa, kamar yadda ta saba. Sun gaisa, cikin mutunci, hubby bata nuna mata komai ba. Sai dai ta lura jikin mmn samira yayi sanyi, kusan kamar ma kunyarta take ji. Bata dade ba, ta nufi part din Mmn Yusuf. Itama kadaran- kadahan, ba yabo ba fallasa. Kamar all times, har yau ta rasa abinda ta tsarewa matar. Shin kaso dan mutun Ashe yakan zama laifi? Meye laifinta don ta nuna tsantsar soyayyar danta? Da wannan tunanin ta nufi part din Hajiya. Zo kaga murna, kamar waanda suka shekara basuga juna ba.  Hajiya ma taji dadin ganin hubby. Sai washe baki take, cike da farin ciki. Da kanta tama hubby jagora zuwa part din Alhaji Jamal. Shima yayi farin ciki da ganin hubby. Sai 5pm Hajiya ta ce, ta tashi ta tafi yamma tayi, badon taso ba, haka ta ja motarta zuwa gida. Cike da kewar yanuwanta.                ****************** " Salamu alaikum, malan idi yau ba redio ne.? Wani dattijo dake cikin keken guragu ya fada, bayan ya iso wurin da malan idi ya kafa kujerarsa a wajen get din gidan. " yau kunne nake son ji, bana son hawan jini ya kamani tun yanzu. Don na lura jin abinda ke faruwa a kasar nan ba abunda zai kara ma mutun sai hawan jini." Malan idi ya fada cikin dan bacin rai. " shi yasa in ba a wurinka ba, ba ruwana da redio." Gurgun mutumin ya fada Kallonsa sosai malan idi yayi. " me ya kawoka kuma yanzu? Nafa kusa fara maka rashin mutunci, baka tashi zuwa wurina sai kaji kamshin girkin hajiya na tashi, ka dai daici an kusa gamawa, ka wani lallabo, kai baka koshi ba, ni ban koshiba." Marairaice fuska gurgun mutumin yayi. " bama haka da kai. Kasan ance duk Wanda yaci shi kadai, zai mutu shi kadai. Ci bibbiyu yafi albarka." "Ai sai kayi, gaba don yau Hajiya bata nan." Malan idi ya fada yana harararsa Dariya gurgun mutumin yayi " ina fa jiyo kamshi, tun daga dakina. Nakuma san daga gidan nan yake fitowa. Don ni yanzu saboda lakantar kamshin girkin Hajiya, nakan iya ban banta kamshin Jan zakara, da farin zakara, yau kam kamshin kifi na jiyo." Dariya sosai malan idi yakeyi " lallai abin naka, babbane. To da gaske bata nan. Wannan gurkin oga ne, don shi kadai ne a ciki." " haba ai nasan daga gidan nan kamshin ke fitowa, don duk Unguwar nan ba inda zaka jiyo kamshin girki, mai sa miyau tsinkewa sai gidan nan. Allah ka mana arziki, mutun ya dace da matar data iya girki, ai ka more zaman duniya. irin matan nan ko ruwa suka dafa maka dadinsa da ban ne. Ashe shima alhajin gwanine a girki. Yau zamuci ma ban bance Wanda yafi wani." "Kaga tashi kayi gaba abinka, ban san sa ido. In kuma ka yadda oga yajika kana yaba girkin matarsa ba ruwana" " gaskiya na fada ai!! Inda ni  na samu ina kwasar girki haka ai  bazan koma  kauye ba.  ko bazasu biyani ko sisi ba, in dai zan kwashi girki bani da matsala." Dariya malan idi yayi, don yasan mutumin nasa, kan girki. " Allah ya shiryeka. Yau dai bamu da kwano a gidan nan. Don haka kai zaka kawo mana naka abincin muyi maneji." " sai fa manejin kam." Gurgun mutumin ya fada yana tabe baki   Hango motar hubby yayi, malan idi ya tashi da sauri ya wangale mata get, gurgun mutumin kam sai wangale baki yake yana daga mata hannu. Sallama ta musu, bayan ta dan sauke glass, ta wuce ciki.              ******************** Tun 4 hayder ya dawo, kitchen ya nufa, bayan ya rage kayan jikinsa. Daga shi sai  short nicka da singlet. Irish ya soya, da onion source, dayaji attaarugu da kayan kamshi. Sai catfish daya gasa.  Hubby na shigowa, sama tayi. Don ta tabbatar yana gida ganin bike dinsa a compound, sannan gidan a bude, ga kamshin girki dake tashi. Key tasawa ta kulle kofarta. Wanka tayi tare da dauro alwala, don magrib ya gabato. Ta dau takardun islamiyyarta ta fara mura jaa. Yana jin shigowar motarta. Dai dai lokacin da ya fito ta kofar kitchen din, ita kuma tana shiga ta falo. Malan idi ya kira ya mika masa plate cike da chips, roasted fish and Onion source. Washe baki malan idi yayi, yana godiya. Don yau ya fitar da rai da abincin gidan, ganin uwar  dakin nasa bata nan. A wani square plate ya hada nasa kwanin shaawa. Ya sa rapper din Leda  ya rufe, ya daura a kan deepfreeze. Daki ya koma ya watsa ruwa da sauri sauri, ya daura alwala.  ash color din jallabiyya yasa ya nufi bike dinsa, cikin sauri yabar gidan don karatowar lokacin sallah. Sai da ta idar da sallah tare da azhkhar, ta fito don daukan cake. Don bata jin yau zatayi wani girki. Kamshi ne ya doki hancinta, duk da na'urar fitar da kamshi amma kitchen din a kwai kamshin girki. Idonta ne ya sauka a kan plate din hayder. Murmushi tayi tare da ajiyar xuciya. " tsuntsu daga sama gasashshe." Ta fada tare da daukan plate din tayi dakinta. Key tasa ma kofarta, don ta gama fita kuma, sai in Allah ya kaimu gobe. Abincinta taci hankalinta kwance. Gashi yayi mugun dadi, rabon dataci gashin kifi irin haka, tun zamanin school, Da take cinye masa abinci.               ****************** Koda hayder ya dawo, yaga babu plate babu dalilinsa. Murmushi kawai yayi, ya bude oven ya dauki wani fish din. Irish ya fito dashi a freezer yayi fraying. Tsaf ya hada plate dinsa ya nufi falo. Yana kallon  huda tv, yana cin abincinsa cike da natsuwa. Nasrin ce ta kirashi, wani kayataccen murmushi yayi, tare da daga wayar. Sun fi 30min suna waya, kafin sukayi sallama.                ***************** Kamar a mafarki, hubby ta fara jin kukan mage ta window dinta. A tsora ce ta tashi zaune, tana raba ido a duhu, jikinta sai bari yake, in akwai abinda take balain tsoro to mage na ciki. Inuwar abu taga ya gilma ta windonta. Da yake ciki akwai duhu, waje akwai hasken fitila. Ta jikin labulenta tana iya ganin inuwar abu na kaiwa da komowa. Still kukan mage ne, ba imagining take ba. Ai da gudu ta duro daga gadon, har tana buge kafa. Daga jikinta, har zuciyarta bugawa suka fara yi. Musamman jin magen ta tsananta kuka, na yanzu ma yafi mata kama dana jariri. Da gudu ta fito a dakin, daya dakinta da tunda tazo, ko sau daya bata taba kwana a ciki ba ta shiga, tare da danna key. Ajiyar zuciya ta fara saukewa tana dafe da kirjinta, dake bugawa kamar zai fito. Adduoin ta fara jerowa, daga ta kai wannan ta cafko wannan,.  Kwanciya tayi, still a tsorace take, tana son tashi ta kunna ac amma tsoro ya hanata kwakwaran motsi. Windows din da yake a Jere suke dana bedroom dinta. Magen ta dawo ta nan, kamar tasan hubby ta gudu a can. Kuka ta fara tare da yakushin window din. Kamar tana son budewa. Ai a 360 hubby ta fito a dakin. She have no idea kawai tsintar kanta tayi a dakin hayder. Da sauri ya dago kai yana kallonta, da gudu ta karaso kan kujerar da yake zaune, ga system a gabansa,. Zama tayi a kusa dashi, tare da sakalo hannunta a nashi. Jikinta sai bari yake. " ikon Allah, lafiya?" ya fada  Kofa take nuna masa, still tana makale da hannunsa. Ganin ta kasa magana, yayi yunkurin tashi, yaje ya ga meye. Da sauri ta janyoshi tare da kara kan kameshi. Bakinta na rawa " mag, mage ce." " mage?" Ya fada yana kallonta. Kai ta kada masa. Alamar eh! " OK. Sakeni in je in ganta. But how come mage a gidan nan?" Ya fada yana kokarin raba hubby da jikinsa. " please don live me along. I'm scared" ta fada baki na rawa " what I don't understand shine, a cikin dakinki kika ga magen, ko ya akayi?" Ya fada yana tsareta da mayun idonsa. " a window na, tana son ta shigo." Tsaki yayi, tare da harararta. " na dauka ma dakin naki ta shigo ai! Kike rawar jiki haka." Sun kai 10min ba Wanda ya kara tankawa dayansa. Zuwa yanzu hubby ta fara samun natsuwa, koba komai tasan she is safe known. Kallonta yayi, ya kalli hannayenta dake sakale da hannunsa daya. " sakar min hannu malama." Ya fada in his husky voice. Da sauri ta saki hannun tana dan tura baki.  Haushinsa, da haushin kanta, ya kamata lokaci daya. Matsawa tayi, ta takure wuri daya, tare da daura kanta a kan hannun kujerar. Da yake kujerar mutun uku ma zasu iya zama a kai. Kallonta yayi, yana tabe baki. Sanye take da night dress riga ce dukanta bata kai gwuiwarta ba. Mai dan karamin hannu. Pusher pink da drawing din apple a gaban rigar. Kanta ko dankwali babu, Ta kamashi da ribbon.  Kansa ya dauke, ya ci gaba da aikinsa. Hannunsa yayi tapping a dai dai, kan hubby da ke bacci, hankali kwance. Ido ta bude a hankali ta sauke su a kanshi. Gaba dayansu sai da gabansu ya fadi.  " go to your room, zan kwanta." Ya fada yana mai goge gashin kansa, alamar daga wanka ya fito. Sai lokacin ta lura daure yake da White trowel, sai karamin da yake goge kai dashi. Da sauri ta kauda kanta. " don Allah ka barni in kwana a nan, tsoro nake ji." Ta fada cikin siririyar muryarta. " no!!!! U can sleep here.?" Ya fada yana tsareta da idonsa. " I sleep right hare, I won't disturb u." Ta fada, cikin yanayin ban tausayi. " what u say yestaday?" Ya fada still idonsa a kanta. Gabanta ne ya fadi, tunowa da karansu na yestaday night. Kanta ta sunkuyar tana wasa da yatsunta. Sai da yayi shirin baccinsa tsaf, sannan yakai kallonsa kan hubby data dungule wuri daya. " Habiba. "  ya kirata in high tone. Dagowa tayi ta kalleshi, tare da kauda idonta. " bafa zaki kwanamin a daki ba. Ki tafi toilet dinki ki kwanta. Amma ba nan ba." Kwal kwal tayi da ido,  cikin rage murya da lallashi. " Allah tsoro nake ji. Kayi hakuri ka barni in kwana a nan please. " Daure fuska yayi, kamar bai taba dariya ba, kallo daya hubby ta masa jikinta ya kara daukar mazari. Tafi kowa sanin halinsa, in yaso rashin mutunci. Tunowa da school tayi, Ita kuwa a yanda take jin tsoron fita, ko yankata zai yi, ba inda zata. " I say get out!!! Tun kan in dagaki in watsaki waje." Ya fada ransa a bace Takowa tayi a hankali zuwa inda yake hannu ta hada " don Allah hayder kayi hakuri, ka barni a nan, kaifa dan uwana ne, bazaka so abinda zai cutar dani ba." Shiru yayi yana kallon yadda jikinta ke rawa, hatta muryarta rawa take. Murmushi ne yakusa kwace masa. The mighty hubby ke bashi hakurin ya barta ta kwana a dakinsa. Wonder shall never end. Rai ya kara hadewa " on one condition. " kai ta daga masa baki na rawa " meye condition din?" Ajiyar zuciya ya sauke a hankali. " u do what I ask u to do, without a guying. In ba haka ba I will trow u out. " Kauda kanta tayi, saboda kallon da yake mata, she can handle it. Hawayene suka fara bin kumatunta. She never been so helpless like this. " please hayder don't do this to me, I'm your brother wife, please. " ta fada tana durkushewa a wurin, tare da sakin kuka mai tsuma rai. Idonsa ya runtse, yanajin tausayinta, tare da jin kukan har tsakiyar kansa. Bai taba tausayinta kamar lokacin rasuwar Yusuf da kuma yanzu da take gabansa,  so Helpless.  Dan uwansa ne ya fado masa a rai, gaba daya yaji hankalinsa ya tashi. Jingina yayi da bangon dake kusa dashi, still idonsa a rufe, ga jijiyoyin kansa sun fito sosai. Sun kwashe 12min a haka, kafin ya bude jajayen idonsa. Still tananan a durkushe a wurin. Sai ajiyar zuciya ta ke saukewa da Jan hanci. Dagata yayi cak, ya nufi Kofa da ita. Hubby kam ganin zaiyi waje da ita yasa ta fara kokarin saukowa, amma ta kasa. A wajen kofarsa ya sauke ta. Tare da zuba mata jajayen idonsa. " go." Ya fada a takaice. " juyawa tayi, da nufin tafiya dakinta, cikin Jan kafa. Daga idon da zatayi, sukayi ido hudu da magen tsugun ne a kofar dakinta ta zubo mata manyan  Golding eyes dinta. Ai a 360 ta kwasa ta koma dakin hayder tana ihu, magen ta rufa mata baya......... [08/03, 20:31] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 19       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Da gudu ta banko kofar, har tana bangajeshi. Baki bude yake kallonta, gaba daya ta fada jikinsa, ta gankameshi, jikinta na matsanancin kyarma. Kyakyawar runguma ya mata, yana buga bayanta a hankali. Kanta ta gara cusawa a kirjinsa. Tana Jan numfashi da kyar.  kaman zata shide haka numfashinta ke fisga da kyar. Sun dade rungume da juna. Jin yadda take sauke numfashi, tare da ajiyar zuciya, jikinta ya rage rawa sosai. Yasa ya dago fuskarta idonta kam a rufe, gani take in ta bude magen zata kara gani. Iskar bakinsa yadan hura mata a fuska " its OK. Open your eyes. " ya fada in husky voice yana ci gaba da hura mata iskar bakinsa. Kara runtse idonta tayi, tanajin iskar bakinsa mai kamshin strawberry na sauka a kan fuskarta. Gaba daya tsigar jikinta ya fara tashi. A hankali ya zareta daga jikinsa, resting chair din ta kara komawa, ta dungule wuri daya. Jin alamar taba kofar yasata saurin dago kanta. Hayder ne yasa key, fridge ya nufa, ya zuba ruwa mai sanyi a glass cup ya tako inda hubby ke dungule ya mika mata. Jin mutun a kanta yasata dagowa, ganin yana mika mata cup din. Ta mike ta zauna da kyau tare da amsar cup din, don tanada bukatar ruwan ko don kuka, da tayi. Tsaf ta shanye sannan ta mika masa cup din. Kwanciya ta kara yi, tare da runtse idonta. Daga nan tana jiyo yanda magen ke yakushin Kofa, kush- khush- kush, tare da kukanta. Ajiyar zuciya ta sauke. Hankalinta ya fara dawowa jikinta, don tasan koma menene ba ita kadai ba ce a dakin. Yana tsaye daga jikin window idonsa na hango malan idi dake baje a kofar dakinsa, yayi shinfida yana kwasar bacci. Tsaki yayi a zuciyarsa yana furta " ji wai nan a dole me gadi? Mai gadi da aka Sani da sintiri cikin dare don ya tabbatar da tsaro, amma shi ke kwasar bacci hankalinsa kwance." Kallonsa yakai kan hubby, yasan harda  sanyin ac yasata dungulewa haka. Takowa yayi, zuwa inda take kwance " Habiba!! " ya kira in sweet low voice. Kanta ta dago ta kalleshi, hannunsa ya mika mata. Kallon hannun tayi, mai matukar haske da laushi, dogayen yatsunsa kwanin shaawa. Kallonsa tayi, alama ya mata da ido. Kanta ta dauke tare da mikewa ta zauna. Ganin bata da alamar kama hannun nasa, da kansa ya kamo nata hannun, tsigar jikintane ya yi wani yar!!! Tare da shock daya ratsa jikinta lokaci daya. Lumshe idonsa yayi, saboda shock din daya ratsa jikinsa. Bata da zabin da yafi ta mike, kamar rakumi da akala haka ya ke rike janye da ita. A tunaninta wajen zai kara turata, amma sai taga sabanin haka. Toilet ya nufa da ita, suna shiga wani kamshi mai sanyaya rai ya daki hancin hubby. ya kalleta yana shigar da idonsa in sexy way. " kiyi alwala, I'm waiting for u outside. " Kallonsa take ido waje, don yanzu ta fara tsinkewa da lamarin Hayder, gaba daya gani take kamar ba shi ba. Ba karamin aikinsa bane ya kulleta a toilet din. Yana juyawa, da sauri ta riko hannunsa. " wait please. " baki ya Dan tabe, ya jingina da kofar. Cikin Sauri- sauri tayi alwalar. Kallonsa tayi, matsawa yayi daga jikin kofar, da sauri ta wuce zuwa cikin dakin. Hakan ya bashi damar yin nashi alwalar. Woodruff dinsa ya bude, wani alkabbarsa  mai hade da hula, ya dauko. Carpet din sallah mai matukar kyau da laushi, ya shimfida. Sannan ya mika mata rigar, Kallonsa tayi, cike da fargaba da tsoro. " nayi sallah." Ta fada muryarta na rawa.  Murmushi yayi, yana ajiye mata rigar a saman cinyarta. " I known. This one is special." Ya fada in sexy voice dinsa, yana murmushin gefen baki. Gabanta ne ya fadi, da sauri ta dago tana kallonsa. " don't forget our agreement? " ta fada, muryarta na cracking Murmushi yayi, har tana jin sautin numfashinsa. " kin San na ce miki no a guying, ko I will trow u out, just do as I say." Ya fada yana tsareta da idonsa. Idonta ne suka ciko da kwalla, mikewa tayi a hankali ta saka rigar, kamar mai sharan kasa, yadda ta mata tsawo, da fadi baki daya. Su Kansu hannayen sun mata yawa sosai. Kallonta yayi, tare da Jan hannunta, har kan daddumar, She have no choice. 2 rakaat sukayi, ya musu addua sosai, tare da dafa kanta ya karanto adduar da manzo  S.A.W ya umurci ko wanne ango, da gabatarwa kafin yaje ga iyalinsa. Allhumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha ala'ih, wa'auzu bika min sharraha wa sharra ma jabaltaha ala'ih. Kwanciya tayi kan carpet din, zuciyarta da jikinta rawa kawai suke, don ta tabbatar yau Allah ne kawai zai kwaceta a hannun hayder. Tun jiya take tsoron randa zai rutsata don ta lura abun nasa ba sauki. Dagata yayi, tare da rungumota jikinsa, yana Ajiyar zuciya. Dagata yayi cak zuwa saman bed dinsa. Kokarin cire alkabbarsa yakeyi, ta cukui kuyeta, tare da nade kanta a ciki. " Habiba don't make it had for us." Ya fada yana rage kayan jikinsa.  Hawayene wani na bin wani, maganar ummu sulaim ne suketa kara kaina a ranta " kamar yadda Allah ya kaddara Yaya Yusuf ya sanki matsayin matarsa, haka ya kaddara hayder shima ya sanki a matsayin matarsa, so take heart and deal with it. Duk yadda kika kai ga gujewa hakan it won't work." Ko kafin ta tuno amsar data bata a lokacin,. Sai jin  hayder tayi, yana kokarin zare rigar a jikinta. Karfinta tasa tana kokarin hanashi, amma ina hakan bai samu ba. Karfi ba daya ba. Yana zare alkabbar tana dira kasa daga gadon. Kofa ta nufa, burki taja, ta tsaya. Zuciyarta na bugawa. Tare da wasi wasin, ta fita su kara da mage?ko ta tsaya hayder yayi yadda zai yi da ita. Don tasan bazai taba barinta ba. Kanta ta kifa a jikin kofar ta fashe da kuka mai cin rai. " how can she help her self know? " Bataji takowarsa ba, sai jinsa tayi ya rungumota ta baya, yana sauke Ajiyar zuciya. Ta bashi tausayi sosai, amma gaskiya baya jin zai iya hakura da ita, don wani filling yake ji, Wanda bai taba experiencing ba, a rayuwarsa. Ji yake in har bai rabeta ba, tabbas zai shiga matsala. Ta wani fannin kuma, zai sauke hakkinta dake kansa, duk da bata da bukatar hakan. Wuyanta ya fara kissing, a hankali, shivering ta fara, tare da kokarin zame kanta. Juyo da ita yayi ya hadata da kofar. Yana ci gaba da kissing wuyanta, zuwa ear loop dinta Gaba dayansu jikinsu yadau kerma lokaci daya. Kanta ya dago, yana kallon kyakyawar fuskarta, data jike da hawaye. Idonta a rufe, don batajin zata iya kallonsa. Bakinsa yakai kan nata, like last time she denied him access to har mouth. Labbanta ya ke tsotsa a hankali, hannun daya na tallabe da fuskarta, dayan na zaga duk kan sassan jikinta. Jikinsa ya mata katanga a jikin door din. Tun tana kokarin avoiding, har gaba daya jikinta, ya fara amsar sakon ninsa. Dagata yayi bridal style zuwa bed din, tare da sweching  light. Wasanni masu zafi ya fara aika mata, Wanda ta kasa control din kanta, ta fara maida masa. Gaba daya daren hayder ya hana hubby sakat, Tun tana dauriya, har ta gaza, ta fara masa kuka. Yana kwance hubby na rungume a jikinsa, Yana jin saukar hawayenta. Shi kanshi hawayen yake zubarwa for 2 think. Fist tunowa da Dan uwansa, second godiya ga Allah bisa niimar bashi hubby a matsayin mata. Yau ya kara tabbatar da maganar Yaya Yusuf, Yau ya kara tabbatar da dalilin da yasa Yusuf ke matukar kaunarta, Yanzu ya gane abunda sauran masoyanta ke hangowa a tare da ita. Bai taba tarayya da ko wacce irin mace ba, a rayuwarsa. Amma yasan she is special, unique and different from others. Hubby tunanin Yusuf ne, dankare a ranta, gani take tamkar taci amanarsa ne, tare da takaicin kanta, yadda ta kasa control din kanta, da har hayder ya samu dama a kanta, So ita yanzu da wane ido zata kalli hayder? Hayder kanin bayanta? He is know controlling her. She is know his real wife. Ya zatayi da wannan katuwar kaddarar?  Alarm dinsa ne ya kada 4am, Yana son tashi, amma baya son disturbing nata,. Kanta ya ke shafawa a hankali. Tare da tuno maganar Yaya Yusuf mai kama da wasiyyah, last ziyara daya kai masa Cyprus.               ******************** Zaune yake a harabar apartment dinsu. Wurine mai yalwar hasken fitilu, da furanni masu kamshi, Wanda su suka zuba kujeru don hutawa da daddare, in sun dawo. Idonsa a sama yana kallon taurari, tare da girmama, girman halittar Allah, da tasbihi a kasan zuciyarsa. Baiji takowarsa ba, sai dafashi da yaji anyi, da sauri ya juya, don a tunaninsa junaid ne, ko ashir, amma ga mamakinsa yaga Yusuf. Murmushi sukawa juna, Yusuf ya zagayo, ya zauna a kujerar dake fuskantar hayder. " na dauka ka dade da bacci, saboda gajiya." Hayder ya fada yana murmushi Shima murmushi yayi " baccin yaki zuwa. Me kakeyi kai daya a nan" Yusuf ya tambaya. " muraja'a and looking at star's. " ya fada a takaice. Murmushi Yusuf yayi, yakai lallonsa sama, yadda stars din suka fito sosai, ga wata da alamar ya kusa 10 to 11 days. " tabbas kallonsu kansa mutun ya kara tsoron Allah da sanin girmansa." Hayder ne ya amsa da " sosai brother" ya fada a takaice " you no what, duniya bata da tabbas,  dole mutun sai yanayi yana garanbawul din imaninsa." Yusuf ya fada still idonsa na kallon sama " ga mai imani ya dauketa, bata da tabbas, ga Wanda ta aura gani yake matabbatace da zai aikata abinda yaso," Murmushi Yusuf " shin duka duka, farin cikin guda nawa ne? Me ye kesa bawa farin ciki a duniya, da har zai salwantar da lahirarsa a kanta?....... Murmushi hayder yayi. "  dukiya!!!Mufi yawan mutane suna halaka ne don son duniya da kuma son hutu da jin dadi a duniya. Shuwagabannin masu rayuwa cikin hutu da jin dadi suke jawa alummarsu halaka don irin fasadin da suke aikatawa a bayan kasa.da yawan mutane na ganin jin dadin duniya shine ka samu kudi. Sun manta da ko kanada kudin, sai Allah yaso kaji dadi dasu. Sannan dukiya kan zama fitina ga maabocinta, don dayawan mutane ita ke halakar dasu, kota wurin nemanta, ko kuma ta wurin gudanar da ita. Dukiya kan kawo shagala da lamuran duniya, ga Wanda ba Allah a zuciyarsa. Mutun zai iya yin komai, don kawai ya tara abin duniya, I mean everything kisan kai, cinamana, zalunci, yaudara duk don yaji dadi a duniya. Kasan abinda yafi daure min kai?" Kallonsa Yusuf yayi, tare da kada kansa. Ajiyar zuciya harder yayi, " ka gama tara dukiyar, amma baka tanadi lokaci, da kwanakin da zaka zauna ka moreta ba." Murmushi Yusuf yayi. " rigima ke nan.  Duniya ke nan, yanzu kananan lokaci kadan ka gushe. Shin wane ayyukane na lada da bayan mutun ya gushe zai kawo masa lada?" Still idon hayder a sama, murmushi yayi. " bayan mutun ya mutu, ayyukansa sun yanke, abunda zai ci gaba da wanzuwa na lada kona kankare zunubi ga bawa, shine da na gari, dazai ci gaba da yi masa addua. Sai sadakatul jariyyah. Kamar gina masallatai, Gina rijiyoyi, tallafawa marayu. Da sauran ayyuka masu gudana." Ajiyar zuciya Yusuf yayi, tare da gyara zamansa. " ga mutumin da kejin kamar rayuwarsa baza tayi tsayi ba, kuma bai mallaki Dan da zai masa addua ba? Mai zai yi, bayan sadakatul jariyyah.?" Kallonsa hayder yayi, cike da alamomin tambaya, saboda yanayin da Yusuf yayi tambayar. Hannun Yusuf ya kamo cikin nashi "1. Ayyukan mutum anan duniya suna tare da shi a duniya da lahira. Makomarsa na tattare da ayyukans a nan duniya. 2. Duk abin da mutum ya fada ko ya aikata anan rayuwa za'a rubuta shi a nuna masashi ranar kiyama kamar yadda ya fada ko ya aikata su. 3. Kotun ranar kiyama kotu ne wanda ayyukan mutum basa boyewa. Hatta da kansa zai iya yiwa kansa hisabi don kasancewar ayyukansa a fili suke. Baya bukatar wani shaida wanda zai tabbatar da ayyukan da ya yi. 4. Bautar Allah shi ne abinda ake gabatarwa kafin a sami kaiwa ga kusanci ga Allah da kuma sanin girmansa. 5. Dare shi lokaci mafi muhimmanci wajen samun kusanci ga Allah. 3. Massalaci shi mahallin da aka fi samun kusanci da Allah. Kuma sallah ce mafi girma daga cikin abidu. Don haka ne ma ake kiranta mirajin mumini. Rashin da baya rage komai ga bawa, sau da yawa ma yakan zama alkhairi ga bawa." Hannunsa Yusuf ya kara kankamewa tare da dan bubbuga hannun da daya hannunsa, Kallonsa hayder keyi, yana nazarinsa. " tun da kazo na lura da canji sosai a tattare da kai, don Allah ahee!! Meke faruwa.?" Murmushi Yusuf yayi, tare da Jan numfashi. " yanayin rayuwane kawai. I wish ni kaina nasan abunda ke damuna, I want to ask u a fervour. " " ask everything u want, in sha Allah zan maka." Hayder ya fada still idonsa a kan Yusuf Murmushi Yusuf yayi " na gode sosai da soyayyarka gareni, duk a yan'uwana kai ka zama mafi soyuwa a gareni. Ina sonka saboda Allah, fiye da yadda nake son kaina. Ina rokonka ko bayan bana raye ka kasance mai yawan yi min addua, Don kai kadai nake ganin kani kuma da a gareni." Idon hayder ne suka cicciko da kwalla, saboda yanayin da Yusuf yayi maganar, cike da rauni. Rungumeshi hayder yayi gaba dayansu hawaye suke fitarwa a idonsu. Sun kai lokaci mai tsawo rungume da juna, kafin suka saki juna. " na maka alkawari, matukar ina numfashi, in sha Allah zan kasance mai yawan maka addua. Kamar yadda ban taba ma kaina addua ba tare da na sakaka da sauran yan uwanmu ba." Murmushi Yusuf yayi still yana rike da hannun hayder. " na gode, hakika kai dan uwane na gari, ina alfahari da kai. A another fervour!!! Ina son ka kulamin da Habiba. Don bayan son Allah da manzonsa, da baa hadashi da komai. Iyayena da kai, sai kuwa Habiba. Habiba tamkar wani bangarene na jikina, bana son rashina yasata shiga wani hali, zan so ka maye mata gurbina, don nayi imanin zaka kulamin da ita, fiye da yadda zan kula da ita." Kallonsa hayder keyi idonsa na zubar da hawaye, wnnan wasu irin kalamai ne ahehh dinsa keyi, tamkar mai barin wasiyya. Mu samman yanayinsa dake sanya tsoro a zuciyarsa. " aheeh!! Wannan wane irin magana ce mai kama da wasiyya?" Hayder ya fada cikin raunin murya. Murmushi Yusuf yayi tare da jingina sosai a jikin kujerar. " ka dauketa a matsayin wasiyya hayder.  Ina son bayan bana raye ka auri Habiba,  Habiba mace ce ta gari, abin alfaharin kowanne miji daya dace da samunta, duk yadda zan maka bayani bazaka gane me nake nufi ba, sai zuwa gaba. " Mikewa hayder yayi zuwa kusa da Yusuf, tsugun nawa yayi, hannunsa duka biyu yasa ya dafa gwuiwowinsa dasu. " don Allah karka karya min zuciya, zan iya daukar komai, amma banda irin wannan kalaman naka. In sha Allah zaka ci gaba da rayuwa damu har tsufanmu, kaga aurena kaga yayana, kamar yadda in sha Allah kaima very soon Habiba zata Haifa maka naka. In wani ciwo ke damunka please don't hide it. Ba cutar da bata da magani." Kanshi Yusuf ya safa, yana kokarin maida hawayensa. " bawa baya wuce kaddararsa hayder. Allah yasa ina da rabon ganin aurenka in ga yaranka. In har hakan alkhairine gareni. Ina maka fatan samun maratus saliha, kamar yadda na dace. Shi yasa nake tsoron haduwata da Allah, don duk wani jin dadi, da kwanciyar hankali na duniya alhamdulillah na samu,. Kudi, mata ta gari, lafiya, kwanciyar hankali. Lahira kuwa, kaga baka da tabbas din karbar ayyukanka na alkhairi." " ka Sani mutane kashi uku ne, a duniya: 1. Daga ni'ima zuwa ni'ima, 2 daga ni'ima zuwa azaba,( Allah ya tsaremu) 3 daga wahalar duniya, zuwa azabar lahira, (Allah ya tsaremu). Ina maka fatan jin dadi, duniya da kiyama." Hada hannunsa hayder yayi " don Allah kabar wannan maganar haka, ka fara tsoratani da gaske." Karamar dariya Yusuf yayi. " shi kenan, Allah yasa mu cika da kyau da imani. Gobe ni zan wuce, Oregon. " " amen, na dauka zamu kwana biyu a nan." Hayder ya fada yana mikewa tsaye. Tashi Yusuf yayi, yana murmushi. " no!!! Zan je ziyara Oregon one day, in koma gida,." " please ahehh! Ka kara ko kwana daya ne." Hayder ya fada cikin fuskar shagwaba. " no way, I miss my wife already, I have to go." Yusuf ya fada yana tafiya zuwa apartment din " u love her too much ahehh!!" Hayder ya fada cike da kishin hubby, gani yake Yusuf yafi sonta a kanshi. " I love u more." Yusuf ya fada yana dariya " if u say so." Hayder ya fada cikin muryar tausayi. Juyowa Yusuf yayi, ya kalleshi yana dariya. " ina adduar Allah ya kawo karshen yar tsamarka da my wife. " " ta cika son girma da yawa." Hayder ya fada yana kwallo da wani karamin dutse. Kallonsa Yusuf yayi yana murmushi " kai kuma ka cika raini ba? Bansan me yasa ka rainata haka da yawa ba." " bata jin magana, ba kokari a school, ga dan banzan shagwabar tsiya. Ni Tun dawowarta daga kauye, yadda take behaving take ban haushi, shiyasa bana shiga harkarta, amma duk ban tsira ba, ta tasani a gaba da mugunta. Tayaya zan wani girmamata." " kafa rama koma me ta maka, kaga kunyi 50-50 don haka sai kayi hakuri. In don kifinka da ta cinye ne, zan biya, a zauna lafiya. Ko ba komai ai ta girmeka, gashi kuma tana matsaya yin matata, bana jin dadin yadda kake treating dinta." Yusuf ya fada Kunne hayder ya kama " sorry, yanzu kam ai ina gaisheta in mun hadu." Dariya Yusuf yayi " good for u." Ya fada yana shigewa ciki, a baya hayder ya biyoshi, a kofar dakin hayder sukayiwa juna sai da safe, hayder ya shige dakinsa, shi kuma ya wuce nashi masaukin dake gaba da dakin Hafiz...              ********************* Ajiyar zuciya harder ya sauke. Jin numfashin hubby na sauka a hankali, tare da ajiyar zuciya ya bashi tabbacin tayi bacci. A hankali ya gyara mata kwanciyarta, ya mike ya nufi toilet. Addu'o'i sosai ya jerowa dan uwan nasa, kamar yadda ya saba, tare da masa fatan samun rahamar Allah, ya roka masu zama lafiya shifa hubby da zuria masu albarka. Yana wurin har aka kira sallah. Sai da ya tashi hubby sannan ya wuce masallaci. Rashinsa a dakin ya bata damar tashi a natse, duk jikinta yayi tsami, a hankali ta taka zuwa cikin toilet dinsa. Ruwa mai zafi ta sa, ta gasa jikinta tare da yin wankan tsarki, Dana sabulu.  Kokari take ta maida hawayen dake kokarin fitowa. Duk yadda taso manta abinda ya faru dakika kadan da suka wuce, abun yaki fita a ranta. Gani take kamar a mafarki, lokaci kadan zata farka. Amma wasa wasa mafarkin yaki karewa. Taso tafiya dakinta, amma still tana tsoron fita. Rigar daya bata jiya, ita ta dauka tasa tayi sallah. A wurin ta kwanta, minti kadan bacci ya yi gaba da ita.. Sai to 7 hayder ya shigo gidan. Dagata yayi ya mayar kan gadon, bayan ya gyarashi tsaf. Bai saba baccin safe ba, don haka computer dinsa ya dauko ya fara aikinsa kamar yadda ya saba. Har 9:39 kafin ya kashe, ya nufi kitchen don sama musu abinda zasuci. Karar rufe kofar ne, ya farkar da hubby. Dakin tabi da kallo, kafin ta mike. Sakkowa tayi, ta nufi dakinta, zuciyarta cike da tsoron kar su hadu da mage. A bakin Kofa ta tsaya, tana lellekawa, sai da ta tabbatar ba komai, tukun ta shiga dakin. Key take kokarin sawa amma sai taga wurin wayam, ba key a jikin door din. Wanka tayi, ta shirya cikin atamfa Holland mai kyau, dinkin Riga da skirt sunyi mata cip, komai masha Allah. Kwalli kawai ta shafa, ta gyara packing din gashinta. Feshe jikinta tayi, da turarenta mai kamshi, dan da nan dakin ya dauka, dama ga kamshin humra data sa a jikinta. Higab dinta ta zunbula ta nufi kasa, don yunwa takeji, har tana ganin jiri- jiri. Mamaki sosai tayi, ganin Mariya harta gama gyara komai, ta sa mata turaren wuta, gidan gaba daya ya dauki kamshi. A kitchen suka hadu da Mariya. Da faraa ta ce " Anty ina kwana?" Murmushi ta mata "lafiya kalau, ya mamanki?" " ta ce in gaisheki." Mariya ta fada " ina amsawa, sannu da kokari'" hubby ta fada tana kokarin jona kettle. Murmushi Mariya tayi. " Anty akwai abinda zan kama mikine? Ko inje in gyara falon sama?" Kallonta hubby tayi, tana murmushi. " ki bari muci abinci, sai in tayaki" " na gama cin abinci kenan, na wanke plate din kika shigo." Mariya ta fada Kallonta hubby tayi, ganin iya gaskiyarta ta fada, yasa ta ce taje ta share falon. Cup ta dauko, ta zuba madara, sugar  da Millo. Tana jiran ruwan ya tafasa. Kamshin turarensa ne, ya fara mata sallama. Bata juyoba don bata da courage din fuskantarsa after what happen. Rungumota yayi ta baya, tare da daura kansa a kafadarta. " good morning. " ya fada in husky voice dinsa. Jikinta ne, ya dau rawa. She can believed what hayder do to her, Ta kara yadda mazan yanzu kunyarsu rageggene. Hijab din ya cire, a kan dogon kujerar da aka tanada a kitchen din ya wurga. Tare da juyo da ita, Kanta a kasa. Hannunsa yasa ya cire ribbon din kanta, gashin ya baje a bayanta. Ya zubo da kadan ta gaba gefe daya, Wanda ya sauka har kirjinta. " u look good, karki kara samin wannan abun, in har ba baki bane a gidan. Hubby kam tsabar takaici ne, ya hanata koda kwakwaran motsi. Mamakin karfin halin hayder take yi. Batayi aune ba, sai bakinsa taji a cikin nata. Kokarin tureshi ta fara, amma ina ya mata kyakyakyawan rukon da bazata iya kubu cewa ba. Sai da ya gaji, don kansa ganin tsayuwar na Neman gagararsu, yasa ya saurara mata. Hannunta ya kamo, suka jero zuwa main falo, A kasa ya shirya musu kayan break fast. Sai da ya tabbatar ta zauna, sannan yaje ya sallami mariya, don yau bayi da bukatarta a gidan. Cike da karfin, hali, da tusawa zuciya dangana hubby ta ke cin abinci a hankali. Gaba daya idon hayder na kanta, tausayinta yake ji, ganin yadda gaba daya tayi sanyi, kamar ba hubby ba. Shi kansa yasan bai kyauta mata ba. Amma ba yadda ya iya, dole su rungumi kaddararsu. Gefensa ta dan kallah. " kai ka kawo mage gidan nan?" Ta fada da muryarta cike da rauni. " nop." Ya fada yana Kallonta Shiru tayi, ba tare data yadda da abinda ya fada ba. Don ta tuno da kalaminsa na cewa ita da kanta zata kawo masa kanta, yana shararren wurinsa. In ba shi ya shigo da magen ba ta ina ta samu ta shigo? Ganin alamar bata yadda ba yasa ya gyara zamansa. " look habibi, da gaske bani na shigo da ita ba, magen gidan barrister ce, dawowana masallaci naji suna tambayar malan idi koya ganta.  jiya  aka kawota, sun tashi da safe, basu ganta ba. Shi kanshi malan idi bai San ta shigo ba.  Ina shigowa mukayi karo da ita a kofar falo, shine na dauketa na mika musu ita." Ajiyar zuciya hubby tayi, tare da Jan Allah ya isanta ga mamallaka magen. " magen is so cute!! Kinga picture din da na mana tare." Ya fada yana murmushi tare da bude wayarsa don ya nuna mata picture din.  Haushine ya kama hubby, bata San lokacin data balla mai harara ba. Murmushi yayi yana nuna mata picture din. Tashi tayi ta nufi, sama da gudunta. Da ido ya bita yana murmushi, tare da shafa sajensa. Kiss yama magen tare da furta " your the best. "......... [08/03, 20:33] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 20       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Ya Tattare kayan da sukayi break fast, ya gyara wurin. Kwanciya tayi, hawaye wani na bin wani. Kuka sosai ta sha, kafin bacci yayi gaba da ita.                ***************** Alhaji Jamal ya kalli hayder " munyi waya da jamil, Ku aika masa da CV dinku." Dariya hayder yayi " daddy mu kam mun yafe, waye zai tsaya wani bata lokaci aikin government. " Ido Alhaji Jamal ya dan zaro " kana nufin baza kuyi ba kenan? To su sauran da suka karanta medicine haka zasu bari ya tafi a banza,? ina dama anyi karatun ne don taimakon alumma?" "A kwai hanyoyi da yawa na taimako, yanzu dai karatu zamu koma, tukunna" Hayder ya fada yana murmushi Kai Alhaji Jamal ya kada kai, Allah ya taimaka." " amen Daddy. Gobe in sha Allah zan zo muje kaga store din." Hayder ya fada yana kai kofin shayi bakinsa. " haka ne, na manta ne ai da yau na dawo da wuri, da munje, amma ba damuwa Allah ya kaimu goben." " amen. " hayder ya fada " ya yarinyata? Ba wani matsala ko?" Alhaji Jamal ya tambaya yana kallon hayder. " lafiya kalau." Ya fada cike da jin nauyin Daddy Murmushi yayi " Allah ya muku albarka, a ci gaba da hakuri, kasan mata zama dasu sai da hakuri, da kuma juriya." Murmushi hayder yayi kanshi a kasa. " ko akwai abunda kake bukata?" Alhaji Jamal ya tambayeshi " ba komai," hayder ya fada yana murmushi Murmushi Alhaji Jamal yayi. " na manta Ashe da dan kasuwa nake magana." Dariya hayder yayi. " karamin dan kasuwa dai." Ahmad ne yayi sallama ya shigo, daddy ya gaisar, sannan suka gaisa da hayder. " kun tashi daga kanana yan kasuwa, kun fara zama manya. " Ahmad ya fada yana murmushi Murmushi Alhaji Jamal keyi cike dajin dadi, " haka ne ko Ahmad? " Alhaji Jamal ya tambaya " Daddy sai kaje kaga manyan stores din da suka shake da kaya, sannan zaka yadda da maganata." Ahmad ya fada yana hada shayin,. " shi yasa nayi maganar aikin government aka ce min aa. Allah yasa albarka." Alhaji Jamal ya fada "Amen" suka amsa gaba daya. Hira suka ci gaba da mahaifin nasu, gwanin sha'awa, har wani lokaci kafin suka fito kowa yayi hanyarsa.                   **************** Hubby sai 1:30 ta farka, da sauri ta daura alwala don yin sallar azahar.  Tun kafin ta idar takejin nocking, tana idarwa ta sakko don ganin ko waye. Tasha mamakin ganin Abida. Fuska ta sake sosai tana mata sannu da zuwa. Falo ta kaita, tare da cikata da kayan ciye -ciye, tunda bata samu tayi girki ba. " Anty hubby ina wuni." Abida ta fada tana mai sakin fuska Mamaki sosai ya kama hubby, don tunda take da Abida, bata taba ce mata Anty ba. Sau da yawa in sun hadu, ita take jira ta fara gaisheta. In ma ta gaishetan a wulakance zata amsa. " lafiya kalau, ya mai gidan da Abdul?" Hubby ta tambaya " lafiya kalau, Abdul yana main house." Ta fada tana murmushi " ayyah! Shine baki zomin dashi ba?" Hubby ta fada cikin rashin jin dadin ta. " ya samu su jeniour a gidan, shiyasa yaki yadda ya biyoni." Ta fada cikin jindadi. " yasu mommy? " hubby ta tambaya jin daga main house take. " lafiya kalau. " ta fada a takaice. Shirune ya biyo baya, don hubby bawai ta saba da ita bane, asalima tana daya daga cikin wanda suka takurawa rayuwarta a zamanta da Yusuf. Tana mai mamakin ganin yadda ta sakko lokaci daya. Kallonta take a kai -kaice, kamar ba abida ba, duk yanga da gayun nan babu, tayi wani iri kamar wadda ta taso daga ciwo. Abida kuwa kallon hubby take, cike da shaawarta, a yadda tai tunanin ko tarbar arziki bazata samu ba, saboda abubuwan da ta mata a baya, amma sai taga sabanin hakan. Yanzu ne take nadamar abubuwanda ta ma hubby, gashi baa je ko ina ba, gashi tana ganin saka mako. Don yanzu wulakancin da kannen mijinta suke mata karema bazai ci ba, gashi  baya ganin laifin kannen nasa ko kadan, in Abu ya hadata dasu  A gabansu zai ci mutuncinta. Gashi bata da ikon kai kararsa gida. Saboda ita tace taji ta gani. Ba yadda ba ayi ta auri dan uwanta Khalil ba taki, karshe sai Ai'ra aka aura masa, an bata zabin ranta da sharadin komai ya faru ba ruwan kowa a ciki. Takuma ji ta gani. Wanda sai yanzu take gane kuskuren data tafka ma kanta. Ajiyar zuciya ta sauke, da har tasa hubby juyowa ta kalleta. " hayder fah?" Gaban hubby ne ya fadi, cikin yaken karfin hali ta kalli Abida " ya fita." Kai Abida ta kada tana kokarin maida hawayen da suke kokarin zubowa a idonta. Jikin hubby ne yayi, sanyi, tashi tayi taje ta daura musu abinci. " gidanku yayi kyau sosai." Abida ta fada tana murmushi Murmushi hubby tayi " na gode. Kiyi hakuri na sha'afa, bakizo ganin daki ba, muje ki gani." Hubby ta mike tayi gaba Abida na biye da ita. Murmushi Abida tayi mai ciwo " kuyi hakuri duk kanku ba wanda naje dakinsa, sai ke da nazo yau. Bikin ma da yaya ya bari naje! Shi yasa duka programs din baku ganni a wurin ba." Kallonta hubby take cike da mamaki, don har ga Allah bata lura da rashin zuwan Abidan ba, saboda dama can in sun hadun ma ranta sai ya baci, da bakar magana, da kallon banza. Tama manta da ita.  " amma dai baki kyauta ba, bikin kannenki guda amma baki raka kowacce cikinsu ba? Ko bakije na kowa ba ai kyaje na Aisha. " Bakinta tadan ciza tana kada kai. " ni kaina nasan ban kyauta ba, amma ya na iya tunda bani nake iko da kaina ba? A hakan ma yayi kokari da ya banni nazo har 3 days a Jere, duk da ba dadewa nakeyi ba. Ni kaina kullen sa na damuna, na rasa yadda zanyi, gashi ba wanda zan kai kararsa ko na samu sassauci. Iyayensa kuma da na musu maganar budan bakin hajiyansa sai cewa tayi " wai so nake ya barni in ta yawo a gari kamar wata akuya? Ta inda take shiga ba tanan take fita ba, nayi nadamar kai kararsa wurinsu. Duk da ba wannan bane karo na farko da hakan ke faruwa ba." Ajiyar zuciya hubby tayi cike da yausayin Abida. Abida ta ci gaba da cewa " haka lokacin dana kai kararshi, daya hanani fita aiki, baban ya min tatas ba kunya ba tsoron Allah ya goyi bayan dansa. Daga karshe yace in har na matsu lallai dole sai nayi aiki, to inzo zai bani a company dinsa. Ba yadda na iya, haka na ajiye aikina, na koma ina aiki a company din, sai da na share wata biyar ko sisi baa taba biyana ba, danayi complain bakiji bakar magana da daddyn Abdul ya gaya minba. Hakan yasa na ajiye musu aikinsu. Tun daga nan muke takun saka dashi, har yau dinnan da nake miki magana." " Allah ya kyauta, ki ci gaba da addua, sai kiga komai ya dai daita, da yardar Allah. " hubby ta fada cikin muryar tausayawa Murmushi Abida tayi, tana zama a daya daga kujerun kitchen din. " duk abunda ya faru dani, ni na siya da kudina. Da nabi maganar Daddy da duk haka bata faruba, Daddy yasan Alhaji sammani farin sani, don haka ya nuna baya son in auri danshi, don wani lokaci, yaro kan dauko halayyar uba, kwabo da kwabo, koda bazan auri zabin Mmn Yusuf ba, to in kawo wani, amma ba jinin Alhaji sammani ba. Lokacin so ya rufemin ido, babban kuskuren dana tafka shine, duk abinda ke faruwa a gidanmu, ba wanda bana kwashewa in gaya masa. Yasan masu adawa da aurena dashi, yasan yan ba ruwana, Shiyasa yanzu sai abu ya faru a yan' uwa, amma yayi mursisi, ya hanani zuwa, in nai magana yace mai zanje inyi a wurin wanda baya kaunarsa. Kiri- kiri yana son rabani da yan 'uwana, rabon da wani nawa ya kai min ziyara ya kai 4month, sai dawowar hayder. Saboda wulakancin da yake musu, haka kannensa sun sha fada da Aisha, ita ce dama mai kokarin zuwa min akai akai. Daga baya ita din ma ta dauke kafarta, don bazata juri wulakanci ba. Nasan banda hakkin iyayena, har da hakkinki, na musguna miki da nayi, yake bibiyata. Kannanen mijina zagi, wulakancin da cin mutunci ba wanda basa min, jiyama karamarsu harda yun kurin dukana." Ta fada idonta na zubar da hawaye Cike da tausayawa hubby ta fara bata, baki har ta samu tayi shiru. " ba abunda yafi karfin Allah, ki dage sosai da tashi da daddare kina kai kukanki ga Allah, in sha Allah komai zai wuce." " na gode sosai Anty hubby, har naji zuciyata tayi min sanyi, da na samu na fitar da abinda ke damuna ." Hira suka ci gaba, cikin kwanciyar hankali, hubby na bata shawarwarin yadda zata bullowa lamuranta. Abida taji dadi, don duk yan uwanta ba wanda zata iya budewa cikinta. Saboda gudun abinda zai je ya dawo. Sai 5 Abida ta tafi, bayan hubby ta cikata da kayan kwalliya, turaruka, da materials har guda 4. Godiya tayi sosai, cikin sanyin jiki tabar gidan hubby. Duniya kenan? Kaji tsoron Allah kaji tsoron mutun. Tunowa da yadda soyayyar Abida da mijinta yake, kafin auren. Kamar zasu cinye juna, don so da kaunar juna da sukeyi, ko yaushe suna tare, ko unguwa taje, yana biye da ita. amma duka duka auren da baifi 2²/¹ years ba, amma rigingimun dake  cikinsa yafi farin cikin yawa.                ******************* Tana tsaye a gaban mirror. Sanye da kayan bacci Riga da wando dogo, pitch color, sunyi mata kyau sosai,   gashinta ta kama tare da saka hula mai raga -raga. Ta kara feshe jikinta da turare. Kwanciya tayi, tare da jero Addu'o'i kwanciya bacci. Duk da zuciyarta ta kasa natsuwa, don tun a wurin break fast da suka rabu da hayder, bai dawo gidan ba, gashi har fast 9. Damuwarta rashin key din dakinta, ta tabbatar shiya kwashe keys din, har da na daya dakin duka. Sai 9:30 ya shigo gidan. Direct dakinsa ya nufa sai da ya gama shirin baccinshi sannan ya nufi dakin hubby. Sanyin AC tare da kamshin turaren wuta suka fara masa sallama, lumshe idonsa yayi, yana jin dadin kamshin nan, yana son turare a rayuwarsa, ya lura itama maabociyar turare ce, sosai. Hangota yayi, cikin duvet ta dukun kune. Murmushi yayi yana shafa sagensa ya nufi gadon. A hankali ya rab'a gefenta ya kwanta cikin lallabawa kar ta farka ya jawota jikinshi ya rungume ta tsam a faffad'an k'irjinshi sai sauk'e ajiyar zuciya yake yana shafa bayan ta da gashin kanta, a hankali,Kamar a mafarki hubby ta ji ana shashsha fata. Ido hudu sukayi da hayder da already idonsa ya fara sauya kala. Da sauri ta runtse nata, jikinta ya dauki rawa zuciyarta na bugawa, don bata manta wuyar data sha a hannunsa ba. Ganin ta farka ya kara mishi kwarin gwuiwar ci gaba da aika mata da sakwanninsa, masu matukar rikitata. Ganin yana Neman wuce gona da iri, tai saurin janye jikinta, tana zaro ido  cike da tsoro ganin abin da yake da niyar aikata mata ta k'amk'ame jikinta, baki na rawa tace. "a,a Please hayder ka barni wallahi ban da lafiya, har yanzu jikina ciwo yakeyi." dariya ya d'anyi ganin duk ta rud'e sai karkarwa take bakinshi ya kai kan nata ya fara bata hot kiss. Gaba daya jinkin hubby ya sake,  Bata da sauran karfin da zata kwaci kanta. Kansa ya dago yana kallonta. Muryarshi can kasa  " yaushe na tashi daga agric chicken na koma hayder? " ya tambaya yana sake mata wani killer smile. Kasa cewa komai hubby tayi, don gaba daya ya kashe mata jiki, da salonsa. Murmushi yayi ganin sai karkarwa take, bakinshi ya kai kan k'irjinta ya rink'a juyata, ita kuwa a hankali ta rink'a mik'a tare da ruggume shi, hakan ya kara masa kaimi wurin ci gaba da abunda ya fara. Sai da ya tabbatar ta samu gamsuwa yadda ya dace, haka shima, tukun ya tsahirta mata jawota jikinshi yayi sannan ya ruggume ta yana maida numfashi da lumshe ido yana mai sa mata albarka. Ganin tana kokarin yin bacci, hayder ya dago kanta, dake kwance a kan kirjinsa. " tashi muje muyi wanka, ba kyau mutun ya kwanta yayi bacci ba tare da ya gusar da najasar jikinsa ba, ana son ko alwala mutun yayi kafin yayi bacci. " Hannunta ya daura a kansa. Hannunta tai niyyar cirewa a cikin gashin nashi, ko tunanin me tayi, kuma sai ta fasa. Massage ta fara masa a kan, cikin natsuwa, lumshe idonsa yayi, saboda jin dadin abunda take masa. Cikin husky voice dinsa " meye planning dinki, a kan rayuwar aurenmu?" Shiru tayi kamar bazata tanka masa ba. Sai can ta sauke ajiyar zuciya " ka riga ka gama rusa min duk wani plans dina. Sai dai ka sani gangar jikin Habiba kawai zaka mallaka, banda zuciyarta. Shiyasa na maka kwadayin ka auri zabin ranka, in da zaka samu kyakyawar kulawa da soyayya." Murmushi yayi ba tare daya bude idonsa ba. Sun dau lokaci shiru ba wanda ya kuma cewa komai, kafin ya ce " ban rusa miki plans don wani abuba, illa don in taimakeki. Nasan bazaki iya cika sharuddan ba." Harararsa tayi " waya gaya maka hakan.?" Idonsa ya bude, kallonta yayi yana smacking tare da daga mata gira daya. " I'm not a kid!!!  Allah ya halicci ko wanne mutun da filling, matukar baligi ko baliga, lafiyayyu, zasu ci, mai kyau, su sha mai kyau, the next thing shine bukatuwa ga dayansu, Baki isa ki kare kanki daga wannan ba, no matter how u try. Koda na amince da sharuddanki, nasan zuwa gaba kadan bazaki jure ba. Hakan ma kinyi kokari." " is not true!!!" Ta fada tana harararsa Dariya yayi. " karki zo kina reaping dina a banza. Kinga ai gara a wuce wurin. Ban damu ki bani zuciyarki ba, kamar yadda kema ban son kisa rai da tawa zuciyar. Amma duk wani hakki naki, in sha Allah zanyi iya abunda zan iya." Rankwashi ta zuba mishi a kai, da sauri ya mike, " ouch!!!!" Ya fada yana shafa sumar wurin. " what? " ya fada yana daga mata gira. " for saying I'm going to rep u." Ta fada tana gyara kwanciyarta. " ba kyau mugunta, kin san dai yanzu ina da hanyoyin ramawa da yawa? So be care full. "  Banza tayi dashi, kwanciya yayi, ya jawota jikinshi. " na tambayeki dazu baki bani amsa ba. Meya faru aka daina kirana da agric chicken? Na dawo hayder? " ya fada yana murmushi Tureshi tayi, tare da juya mai baya. Juyo da ita, yayi tare da dago fuskarta. Murmushi ne a kan fuskarsa, gira ya daga mata daya. Duka ta kai masa a kirji, yayi saurin tike hannun, yakai bakinsa  kiss ya mata tare da bin hannun yana kissing. Cikin rawar murya ta ce " please agric chicken let me sleep. " tana kokarin kwace hannun. Dagowa yayi ya kalleta, fuskarsa dauke da murmushin mugunta. " agric chicken never sleep at night. They spend the night eating and play, so let us play. " Bata fuska tayi, don har ga Allah ta gaji, bacci kawai take bukata a lokacin already past 12am. " agric chicken ka ce, I'm not a agric chicken, U are. So go to your room and play alone. " " u are agric chicken wife, u also a agric chicken. " ya fada yana kara shigewa jikinta. " please hayder!! " ta fada cikin muryar tausayi " I'm in the mood, please let me be. " ko kafin ta kara cewa komai ya zira bakinsa cikin nata.                 ******************* Yau ma hubby da tsamin jiki ta tashi. Bayan ta gasa jikinta tayi sallah, komawa tayi ta kwanta. Tambayoyine fal ranta. Tana mamakin hayder, wanda yasa har take zargin anya bai saba ma'amala da mata ba? Saboda wasu salon nashi, ko ita da ta shekara hudu a gidan miji, bata taba sanin su ba.  Yawan bukatarsa ya fara bata tsoro. Tasan Yusuf ma yana da yawan bukata, amma ko kadan bai kai hayder ba. Baccine mai dadi yayi gaba da ita. Hayder daga masallaci ya wuce main house. Saboda nemansa da daddy keyi.                 ******************* Da sauri sauri take hada break fast din, Mariya na gyaran gida. Sai 10 ta samu ta kammala. A dinning table din main falo ta jera nasu, bayan ta zubama, Mariya da malan idi nasu. Sama ta haura don ta samu tayi wanka. Shiryawa tayi cikin wata pitted grown na less ash and pink, mai kyau da asalin tsada. Tayi kyau sosai, ba wani makeup tayi ba, just powder, kwalli, sai wet lips. Fuskarnan sai daukar ido take, bata tsaya daura dan kwali ba, karamin gyale ta yafa pink, tare da kara feshe jikinta da turaruka. Kujerar dinning din ta janyo, tama kanta mazauni. Plate dinta ta gama hadawa da abinda take da muradi. Irish with liver source, sai pray eggs. Ta hada tea.  Ta fara ci kenan taji takun hayder tare da kamshin turarensa daya cika hancinta. Sanye yake da farar shadda,  dinkin zamani ya zauna a jikinsa sosai, sharddar sai daukar ido take, ta kara fito da hasken fatarshi sosai, Very handsome. Kujerar dake kallonta ya ja ya zauna. Idonsa na kanta, ta masa kyau ba kadan ba. Ko don bai saba ganinta da karamin gyale bane? Wayarshi dake faman ringing ya daga, tare da gyara zamansa sosai a cikin kujerar, idonsa a kan hubby da tun shigowarsa bata dago idonta ba, illah abincinta data ci gaba daci,. Tana jin yadda idonsa ke yawo a jikinta. Hakan yasa ta kasa dago idonta ta kalleshi, ta riga tawa kanta alkawarin biyayyar aure, dai dai iyawarta. Zata tursasa zuciyarta wurin kokarin kyautata masa komai kan kantar hakan. Sai dai har lokacin tana jin jina, yadda zata sakko da kanta kasa gareshi,. Gaishe shi take son yi, amma ta kasa yin  hakan. " antashi lafiya? " ya fada still idonsa na kanta. Sai da ta hadiye abincin bakinta kafin ta amsa masa " lafiya kalau. " ba tare data dago ta kalleshi ba. Tana mamakin irin wannan kallo na hayder, kamar ta tsole idon nasa ta huta, haka take ji. " kinyi kyau. " ya fad in husky voice dinsa yana bubbude wormers din dake table din. " wow!! all this for agric chicken.?" Ya fada yana smacking. Harararsa hubby tayi, karaf idonsu ya hadu, gabanta ne ya fadi, lokaci daya, Karin kamarsu sosai ta gani da Yusuf. Murmushi gefen baki hayder yayi, ya rungume hannunsa tare da jin gina da kujerar. " a zuba min in har ana son inci!" Ya fada da wata irin sansanyar muryar da hubby bata taba jin yayi magana a irin sigar ba. Kallonsa tayi, ta kalli wormers din. Abincinta ta ci gaba da ci, wayarsa ya fito da ita yana latsawa. Har hubby ta kammala break fast dinta, mikewa tayi, tare da daukar plate da cup din da tayi, anfani dasu, ta nufi Kofa. " Habiba " taji ya kirata. Tsayawa tayi, ta juyo a hankali tana kallonsa. " I'm serious." Ya fada yana kai kallonsa ga  wormers din. Juyawa tayi ta tafi, abunta, "saban salo! Ka da Allah yasa kaci mana, da wake serving din naka?" Hubby ta fada a ranta tana Jan tsaki. Tare da ganin laifinta in the first place data dafa abincin ma dashi. Tsaki ta kara ja ta nufi kitchen. Wanke plate da cup din tayi, ganin Mariya bata kitchen din tayi tunanin ko tana gyaran falon sama. Freezer ta bude ta fitar da nama, don yasha iska kafin lokacin daura abincin rana yayi. Mariya ce ta shigo da womers a hannunta, ta ajiye tare da komawa ta tattaro sauran. Budewa hubby tayi, ga mamakinta komai bai diba ba. Tabe baki tayi. Ta rufe wormers din. Mariya ta dawo da sauran plate's din. Har hubby ta ce ta samu robe ta juye ragowar sai kuma taga kamar bata kyauta ba. Tashi tayi, ta dau plate ta diba masa abincin, dai dai yadda take tunanin zai iya cinyewa. Ta jera a wani kyakyawan trey, ta dauka ta nufi falonsa. A zaune ta sameshi ya daura kafa daya kan daya, yana daddanna waya. Da sallama ta shiga, Dagowa yayi ya kalleta, tare da amsa sallamar. Ya ci gaba da abinda yakeyi. Haushi ne ya kama hubby, ganin yadda ya shareta, ji take kamar ta juya ta koma. Karamin tsaki taja tare da dan harararsa kasa kasa. " in ajiye a dinning din ko in kawo maka nan?" Ba tare daya dago ba yace mata " kawo nan." A hankali ta taka zuwa in da yake, a gabansa ta ajiye trey din. Tare da mikewa ta tafi. Hannunta ya kamo ya dawo da ita. " saurin me kikeyi?" Ya tambaya yana ajiye wayar a gefen, Side table. A kan carpet din ya zauna, tare da mata nunin ta zauna. Ba tare data so ba ta zauna. Idanunsa dake kashe mata jiki, ya zuba mata " kamata yayi in  mace ta kawowa miji abinci, ba  ta dungura masa ta tafi ba, tsayawa zatayi ta tabbatar yaci, tana mai masa hira mai dadi. Kinga koda gishiri, ko barkono yayi yawa, duk bazai jiba, saboda zamowarta a tare dashi." Dauke kanta tayi. " in da so da kauna a baki ma sai a bashi." Ta fada tana tabe baki kadan " wow!!! Kice  randa nasrin ta shigo gidana zanga tarai raya?" Ya fada yana smacking " sosai ma kuwa, mu samman in tana sonka." Ta fada tana kallonsa Sagensa ya shafa da Zara zaran yatsunsa, Fuskarsa dauke da murmushi. " amma dai bazakiji haushi ba ko, don kinsan ina son mace data iya soyayya sosai, don ba kunyarki zamuji ba." "Allah ya kiyaye!! Haushin me zanji?" Ta fada tana tabe baki. Gira ya daga, yare da tabe baki. " haka ne fah! Thanks for the food." Ya fada yana janyo trey din " za muje kankiya anjima, in kina da sako?" Ya fada yana kai chips bakinsa. Murmushi ne ya kufcewa hubby " da gaske?" Ta tambaya. Kai ya daga mata, tare da lumshe idonsa. " in shirya mu tafi tare?" Ta fada cike da zumudi. Kada kansa yayi. Bata rai tayi " please! " " nop" ya fada a takaice Kwabe fuska tayi, kamar zatayi kuka. " don Allah fah? Just one week." Ido ya fito dashi " one week. " ya maimaita. Kada kai tayi. " u are not serious. " ya fada in low voice " don Allah?"  Ta fada tana hada hannayenta biyu. " ni kuma ki barni da wa?" Ya fada yana tsareta da ido Baki ta dan tura kadan. " kai kadai mana! Me zai kama ka?" Ta fada cikin muryar lallashi. " mage zata kamani, ina tsoro gaskiya." Ya fada yana smacking. Takaicine ya kama hubby, bata San lokacin da ta rarumo pillow din kujerar kusa da ita ba, ta jefeshi da shi. Tashi tayi, cikin fushi zata fita. Da sauri ya tareta, tare da janyota jikinsa. " sorry. " ya fada yana dariya Duka ta kai masa a kirji. " please kuje dani, nayi missing gwaggo sosai." Ta fada " I'm sorry, not today." Ya fada yana dago da kanta, Kwace kanta tayi, tana kokarin barin jikinsa, Idonta ya ciko da kwalla. Wai yau ita hubby ke rokon hayder yana mata yanga? Duniya kenan juyi juyi, abun da kake ganin da wuya sai kasha mamakin saukinsa da yuwuwarsa in Allah yaso hakan. " look Habiba, bani kadai zan tafi ba, muna da yawa, kuma bazan so tafiya dake a cikinsu ba, ki bari zuwa next week sai in kai ki."  Kallonsa tayi, tare da kauda kanta tana sauke ajiyar zuciya. Kai ta kada masa, alamar amincewa. " good!! Amma a ranar zamu dawo." Ya fada " aa!! Sati zanyi." Ta fada kai ya kada a hankali " shi kenan an fasa zuwan." Haushine ya kama hubby, ganin yadda ya hade rai a dole oga" wai meyasa kake min haka ne? Don kaga ina rokonka shine kake min wulakancin." "Da week din daya wuce kika tambayeni zan iya barinki, but not now." Ya fada yana tashi a wurin, tare da daukar wayarsa dake ajiye a side table ya zura a aljihu, bayan ya duba time. " meye ban banci?" Ta tambaya idonta a kansa. Murmushi yayi mai sauti " tambayata ma kikeyi? Ke kanki kin san difference din." Harararshi tayi, ta mike, ta bar masa dakin don ta lura abun nashi harda rainin wayo. Rungumota yayi, jikinsa. Kiss ya fara manna mata a wuyanta. Tana ko karin zamewa. Sukaji sallamar su junaid. Gaba daya suka shigo falon, saboda ganin kofar a bude, Ganin hayder rungume da hubby, suka juya da sauri suka fita. Tsaki hayder yayi, ya juya yana kallon hubby dake kokarin kwace jikinta daga nashi, cike da jin kunyarsu junaid da takaicin yadda suka samesu. Kiss ya mata a samman labbanta, da goshinta, ya saketa. Da sauri tabar falon. Murmushi yayi yadau wayarsa ya fita. "Lafiya kuka juyo haka da sauri,"  amir dake daga bayansu  ya tambaya. Kai Hafiz ya shafa yana kallon junaid dake masa warning da ido. Murmushi yayi. Gamo mukayi Hafiz ya fada yana komawa jikin mota ya tsaya. Cikin rashin fahimta amir yake mai maita gamo- gamo. " gamo wane iri?" Ya tambaya yana kallon junaid. " kyale dan iska, mu jirashi a nan." Ya fada yana hararar Hafiz dake dariya kasa- kasa Hayder ne ya fito, hannu ya mika musu suka gaisa. Hafiz na ci gaba da dariyarsa. Harara hayder ya aika masa. " daga yau in zaa shigomin gida a tabbatar na bada izinin shigowa, ba daga sallama a fado min gida ba!" " masu gida manya!! ayi hakuri. " Hafiz ya fada yana bushewa da dariya. Murmushi amir yayi " ka mayi kokari, in nine a bakin get zamu dinga haduwa. ba abinda yafi aure dadi, kalli yadda hayder ya canza, in just one month!." Mortar hayder ya shiga, gaba kusa da junaid dake sit din driver. " kan ku akeji, let go" Ya fada " kullun nazo gidan nan da kwadayin aure nake komawa gida. I have to get married soon."  Amir ya fada lokacin da suke barin gidan. Dariya suka yi. " ka samu Abba kawai  da maganar, nan da yan watanni ka shiga daga ciki kai ma." Hafiz ya fada yana dariya Tsaki amir ya ja " na masa magana, yestaday sai kunga yanda ya taso min kamar zai hadiyeni. Wai su saifullah basu yi maganar aure ba sai ni. Shiyasa gaba daya kartin banzan nan sun fara ban haushi." Dariya su Hafiz suke harda kyakyatawa. Hayder kam murmushi ne kwance a kan fuskarsa. " har na tausaya maka, gashi banga alamar sunada niyyar yin aure nan kusa ba." Junaid ya fada "Barsu hajiyan gano, zan je in samu, dolen su suyi,." " ka daure kayi masters din da Abba ke son kayi mana, kana dawowa kayi aurenka." Hafiz ya fada Kada kai amir yayi " ina!!! Da Sana'a ta ni ba komai zan nema wurin wani ba, auren nan shi nake so yanzu. Bayan nayi, na ci gaba da karatun tunda dama akwai niyyah." " kaida ko budurwar baka da ita, kake maganar aure.?" Hayder ya fada yana kallon amir ta mirror " hajiyata zata zabo min nima. " ya fada yana murmushi Dariya sukayi. " to in ta zabo maka wadda bata maka ba kuma fa?" Junaid ya fada yana dariya " take your time guy, kar kyallin fuskar hayder ya rudeka kayi gaggawar da zakayi dana sani." Hafiz ya fada "Say something mana." Junaid ya kalli hayder Tabe baki hayder yayi "what can I say." " irin jinger da kake sha wurin antynmu, ko ya shiga hankalinsa." Hafiz ya fada Tabe baki yayi " Ku barshi yayi aurensa in yana raayi." " thank u broth." Amir ya fada yana murmushi...........  [09/03, 10:41] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 21       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Wata uku kenan cif da bikin hubby da hayder,  suna zaune lafiya, kowanne na kokarin sauke hakkin dan uwansa dake kansa, dai dai iyawarsa. Har zuwa lokacin ba wani maganar soyayya a tsakaninsu, sai dai akwai shakuwa mai ban mamaki. Hubby ta kwantar da hankalinta, duk da dayawan lokaci, tana shiga damuwa. Tunowa da zamanta da Yusuf wanda gaba daya sunyi hannun riga da zamanta da hayder. Sai dai dama bata da higher expectation a kansa. Yau su hayder suka tafi kasar India, shida Hafiz omer. Kayanta take hadawa, zuwa gidan Hajiya kafin ya dawo. Taso zuwa gidansu, amma yaki yadda. Har yanzu a tsorace take da gidan, gani take magen gidan barrister zata kara kawo mata ziyara. Mariya ce ta dauka mata akwatin, ita kuma ta dauki Jakarta, Suka fita. A gida ta sauke Mariya ta wuce gidan Hajiya. Cike da farin ciki Hajiya ta tarbeta. " yanzu nake kokarin kiran wayarki," Hajiya ta fada tana kallon hubby da faraa a fuskarta. Cikin shagwabe fuska hubby ta zauna a kusa da Hajiya, tare da daura kanta a cinyar Hajiya. " tun dazu na keson in fito, na jira sai da Mariya tazo, yau ta makara bata zo da wuri ba." " ya gidan? Ba dai matsala ko?" Hajiya ta tambaya. Kai hubby ta daga mata. Sun dade suna hira hubby na kwance a cinyar Hajiya. Shiru Hajiya taji, tana magana hubby bata amsa taba. Kanta ta sunkiyo tana kallon fuskar hubby da tayi wani gaske, sai glowing take, kamar ka taba jini ya fito. Murmushi tayi ganin hubby tayi bacci. Tashi Hajiya tayi ta gyara mata kwanciyarta, da yake 3 sitter ce, kujerar. Ko ba komai yanzu, hankalinta ya fara kwanciya da zamansu hubby. Kara kallon hubby tayi, tayi kiba kadan, ta murje, kirarta ya kara fitowa sosai, kamar yadda kirjinta, yadan kara habaka. Tayi haske gwanin sha'awa. Masha Allah ta fada cikin jin dadi.                  ****************** Zaune suke a reception na hotel din da suka sauka.  Ya kara cika, yayi kyau na ban mamaki. Yana sanye da black Jens da light green shirt mai dogon hannu. Kafarsa sanye cikin cover shoe black sai daukan ido yake. Jingina yayi jikin kujerar tare da runtse idonsa. Gaba daya kewar hubby ta lullube shi, bai taba tunanin zaiji kewarta haka ba. Moment dinsu yake tunowa. Bai san lokacin da murmushi ya subuce a kan fuskarsa ba. Kallonsa Hafiz omer yake, yana kallon yadda hayder ke faman shafa sage, ido a rufe yana murmushi. Duka ya dada masa a cinya. Da sauri ya bude idonsa, da suka fara canza color. Gira ya dagama Hafiz omer " lafiya. " Kallonsa Hafiz omer keyi, " kai zan tambaya? Nasrin ko antynmu ake tunani haka? Irin wannan smiling " Harararsa hayder yayi " ban son sa ido." Ido Hafiz omer ya fito dashi tare da nuna kanshi " nine dan sa idon." Da ido hayder ya amsa shi, tare da mikewa, let live that place. " Gyara zama Hafiz omer yayi " u can go, I'm enjoying my self hare." "Allah ya shiryeka Hafiz, a dai dinga tsoron Allah." Hayder ya fada yana hararar Hafiz " amen, jeka." Hafiz omer Ya fada yana murmushi Kada kai hayder yayi, ya nufi lifter da zata kaishi room dinsa. Gaba daya Allah Allah yake yabar wurin. yan mata ne gasunan sun sha matsatstsun kaya, wasun ma bai sake da tsirara ba, sai kai kowo suke a kansu. Wayarsa ya dauko, zai kira hubby sai kuma ya fasa, to in ya kira ya ce mata mene? Tun da yazo da su kayi waya da Hajiya taba hubby suka gaisa, ya shaida musu ya isa lafiya, bai sake kiranta ba, haka itama batayi tunani kiranshi  ko sau daya ba. Iyaka ya kira Hajiya. Hajiya kuma, a tunaninta suna waya da juna. Nasrin ya dannawa kira, ringing biyu ta daga, cike da jindadi.               ******************** Yau gaba daya main house a cike yake, da yayan gidan mata. Saboda sa ranar bikin Abdul Karim da Abdul fatta da akayi, nan da 3month. Hubby dasu Aisha, ummu sulaim, Ummul khair. Sun lume a dakin Hajiya. Don tun bikinsu, wannan ne zuwansu gida na farko. Baka jin komai sai dararrakunsu da shewa. Ummu aiman ta shigo cike da faraa " wai yaran nan me kuke ci a dakin ne, kowa na waje, Ku kun kunshe kanku a daki, kun ishi mutane da ife -ife.'" Dariya suka sa " an dade baa haduba, so hirar zumunci muke yi." Aisha ta fada Zama ummu aiman tayi " in zumuncin ne, Ku fito ayi shi gaba daya mana? Ba Ku ware kanku ba." " wannan hirar tamuce, bama son saura suji." Ummul khair ta fada. Harararta ummu aiman tayi " ai dama nasan ke kam sai addua. A dai dinga son jamaa, don jamaa rahama ne." Kallon ummu sulaim, aiman tayi, "ke kuma Anty samira na nemanki." Baki ummu sulaim ta tabe " banni ina nan ina kallon Matar hayder. Don Allah ko ni kadai nake ganin abinda nake gani?" Ta tambaya tana kallon su " me kike kallo." Ummul khair ta fada tana kwantowa kusa da ummu sulaim Hubby ta nuna da yatsanta. Dariya Ummul khair ta bushe dashi. " tun tuni nake son inji wani ya fara maganar, kar inyi nawa yayi zafi, kunsan nafi kowa daukar laifi a gidan nan." Ta fada tana dariya. Harara hubby ta aika mata, ganin duk sun zuba mata ido, sai taji tadan muzanta. " kallon na lafiya ne?" Ta fada Gaba daya suka sa dariya " Kinga yadda ki kai wani kyau, ki kayi jiki. Gaskiya gaba daya auren yafi karbarki." Aisha ta fada Tsaki hubby tayi " saboda ni ce marainiyar wayonku ko? Kowacce bata kalli kanta ba sai ni?" Hubby ta fada tana huhhura hanci Ummu aiman ta dawo kusa da hubby " Anty hubby dan gaya min anya, ba ajiyarmu a nan?" Ta fada tana daura hannunta a kan plat Tommy din hubby. Hannunta hubby ta buge. " Allah ya kiyaye!!! Ki dai tambayesu, banda ni.?" Ta fada tana harararta Dariya sukayi " Allah ban yadda da ke ba. Tun da na kawo miki favorite chocolate dinki naga kin ajiye baki shaba, na sa miki ayar tambaya?" Ummul khair ta fada tana kallon hubby " don ban sha chocolate ba, bashi zai nuna komai ba, just bana jin sha a lokacin ne kawai." Ta fada tana harararsu P - test, Ummul khair ta fito dashi a Jakarta, "gashi a gwada, in har Anty hubby bata da komai, in zama agwagwa." Dariya suka yi, hubby da haushinsu ya isheta, ga faduwa da gabanta keyi. " zako ki zama abun da yafi  agwagwa kuwa. " Ummu sulaim dake kallon hubby tana dariya. " ke Ummul khair meye naki na sauri? In ma shine, ai baya boyuwa." " kunfa samin besty a gaba!!!" Aisha ta fada " Ummul khair naga alama sai na miki wankin babban bargo kafin kibar gidan nan. In har baki fita daga idona ba." Hubby ta fada ganin yadda Ummul khair ke binta da kallo tana dariya " Allah ya huci zuciyar Amarya a gidan Aliyu hayder. "  mikewa hubby tayi ta nufeta gadan gadan. Waje Ummul khair tayi da gudu tana dariya. Binta hubby tayi sai da ta tabbatar ta fita a dakin ta dawo, tana huci. " karku ja mana asara, da kananan cik' kunanku kuke wannan guje -gujen." Ummu aiman ta fada tana kallon hubby Harara hubby ta aika mata, ta zauna a bakin gadon kusa da Aisha " da yake a ruwa ake sha ba." Hubby ta fada tana duba wayarta Da kallo dukan su suka bita, baki sake. Ummu aiman ta zaro ido " kar dai duk kayan aikin nan, komai masha Allah, rowarsu akewa kanina."  Banza hubby ta mata, don duk haushinsu take ji. Tabe baki ummu sulaim tayi, tana mikewa, " meye naki na damuwa Anty sulaim? Komai wayon Amarya sai ansha romonta, balle na yadda da kanina." Ta fada tana barin dakin Ummu aiman ma baya ta rufa mata, tana hararar hubby, Don har ga Allah ta yadda da abinda hubby ta fada. Aisha data tsare hubby da kallo, kallonta hubby tayi, ta harareta tare da Jan tsaki. " kallonfa? Me kike jira baki bisu ba?" Murmushi Aisha tayi, hannun hubby ta kamo ta kurawa hannun ido, idon hubby ta gwale tana kallo, buge hannunta hubby tayi, " ban son iskanci, likitancin naki a kaina zai fara?" Murmushi Aisha ta sake yi. " alhamdulillah ki yadda ko karki yadda tabbas kina da ciki." Ido hubby ta zaro tana kallon Aisha, kirjinta na bugawa da sauri da sauri. A take wani tashin hankali ya shigeta. Amma tai saurin saita kanta. Dariya tayi. " wasa kikeyi." Daure fuska Aisha tayi " bamu taba wannan dake ba, abin farin ciki ne, amma naga kina kokarin denied, bayan abunda kike nema ne, shekara da shekaru. I'm very happy for u." Ta rungumeta cike da farin ciki. Tureta hubby tayi " u are joking right? " " I'm not joking, in baki yadda ba, kije any   hospital a gwada." Aisha ta fada tana mikewa. Har takai kofa hubby ta kira sunanta, juyowa tayi, tana kallonta. " please don't tell anybody." Murmushi Aisha tayi ta fice a dakin. " innalillahi wa inna ilaihir rajiun. I'm finish." Hubby ta fada tana shafa flat Tommy dinta. Gaba daya jikinta da zuciyarta sun dau rawa. Tunani ta fara don ta gano amsar ta da kanta. Zata iya tuna tun bayan haduwarta da hayder batayi mensuration ba. A tunaninta juyin da yake mata ne, don wani lokacin sai tayi 2 months bata yiba. A yan kwanakin kam tafi son Abu mai ruwa -ruwa, yawanci yanzu bata cika cin Abu mai nauyi ba, amma ta danganta hakan da son kartayi gaining weight. Chocolate da sauran kayan zaki ma a kwanakin bata ko sha'awasu. In banda wannan bata jin wani canji a tare da ita. It can be possible, 4 good years tayi da Yusuf, ko batan wata bata taba yi ba, duk irin magun gunan da tasha don tayi  conceiving, amma shiru. Amma a ce yanzu wai she is pregnant, "pregnant with hayder." Ta fada kasan ranta, tana dafe kanta " no it can be." Ta fada hawaye na bin kuncinta. " ina zan kai wannan abin kunyar ni Habiba." Kwanciya tayi ta ci gaba da kukanta. Jin kamar an tunkaro dakin, tai saurin share hawayenta tare da rufe idonta kamar mai bacci. Murmushi Hajiya tayi, ganin hubby na bacci. Ta dauki abinda zata dauka ta fita.                ******************** " don Allah Anty hubby da gaske, maganar da kika fada dazu?" Ummu aiman ta tambaya bayan ta rutsa hubby a daki ita kadai, don abun na cin zuciyarta. Kallonta hubby tayi cikin rashin fahimtar kan zancen " wace magana kenan?" " ina nufin da gaske ba abunda ya shiga tsakaninki da hayder har yanzu?" Ta fada tana tsare hubby da ido. " ba kyau bin kwakwafi Anty aiman.? Hubby ta fada tana murmushi Harararta ummu aiman tayi " kiji tsoron Allah, kar ki cutar min da kani, kin san girman hakkin miji a kan matansa? Me yasa kike son halakar da kanki, kan wani dalili naki mara tushe? Ko kina tunanin kinfi iyayenmu sanin abinda ya dace ne? Da suka hada ki da hayder?" Baki sake hubby take kallon ummu aiman, kai ta kada tana jin jina, son kai irin na Anty aiman. " sannu mai dan' uwa." Hubby ta fada tana tashi don tabar dakin. Da sauri ummu aiman ta rikota " ba haka nake nufiba, kinfi kowa sanin, akwai mutane da yawa da suke zuba muku ido, suga yanayin zaman naku, ba nason a samu kofar da wani zai samu abin fade, amma kiyi hakuri, tabbas bai dace in muku shishshigi cikin lamarin aurenku ba, I'm sorry. " ta fada cikin sanyin murya. " its OK." Hubby ta fada tare da fita ta nufi falon yara inda su Aisha suke. Da kallo ummu aiman tabi hubby.  Hajiya ce ta shigo dakin, ganin ummu aiman a zaune ta kalleta" ke kuma lafiya kike zaune ke kadai a nan? Ina sauran yan' uwan naki?" Ajiyar zuciya Ummu aiman tayi " nida Anty hubby ne, yanzu ta fita."  Kai Hajiya ta kada tare da bude woodruff dinta, don ta dauki kayan da zata sa, fito warta kenan daga wanka. " amma Hajiya kina ganin zaman Anty hubby da hayder ba wani matsala?" Ummu aiman ta fada cikin sanyin jiki Barin abinda take yi tayi tana kallon ummu aiman " me yasa kike wannan tambayar?" " dazu muke tsokanarta a kan tana da ciki, shine take cewa wai  in ba a ruwa zata shaba ba." Shiru Hajiya tayi, tana nazarin maganar. Juyawa tayi ta ci gaba da shirinta, ba tare da tace komai ba. Ganin haka, yasa Ummu aiman barin dakin. Shiryawa take amma tana nazarin maganar ummu aiman. Ita tana nan tana murna, ganin kamar hubby nada ciki, a she shirmen banza take? Kada kai tayi, yaran yanzu sai Allah ya shirya. Hubby son girma, hayder son girma, watan an rasa mai sauke nashi? In sun san wata ai basu san wata ba. Ta wani gefen kuma tana kwakwkwanton maganar ganin, daga hayder din har hubby, sunyi kyau, sun murje abinsu, alamar kwanciyar hankali, Koma menene she will find it out. Washe gari su Ummul khair, kowacce ta koma dakinta. Gaba daya hubby ta shiga damuwa, gashi ta rasa hanyar da zata bi ta fita, at lest ta je ko hospital ne, amma ta rasa dabarar da zatawa Hajiya. Gashi nauyi da kunya, ya hanata ta amshi P -Test din Ummul khair.                  **************** Kwanan su hayder goma, a kasar India, kafin suka nufo gida Nigeria. Hajiya tasa hubby da mai aikinta, suka gyara dakin hayder, don tun da yabar gidan ba kowa a ciki. Tare da turara, turaren wuta,  Hajiya na sane da dawowar hayder a ranar. Abunda ya kara sa jikinta sanyi, bata ga hubby na wani shirin tarbar mijin nata ba. Ya kamata tayi mata maganar zuwa share gidansu, da goge- goge, tunda sun dade basa gidan, gashi an fara sanyi. Amma hubby bata yi mata maganarba, itama share wa tayi. Hubby kam bata da masaniyar dawowar hayder. Mantawa ma wani lokaci take dashi, sai in ta tuna da damuwarta tukun take tuno da musabbabin. Girki na musamman Hajiya tasa hubby ta mata, aka zuba a wormars masu kyau da daukar ido. Suna zaune a falon Hajiya, wurin 8:9 na dare. Hubby na sanye da cotton material, dinkin bubu, mai shape. Yayi mata kyau sosai ya zauna a jikinta, material din irin mai sharking din nan ne, saboda full stones. Shima Kamar yadda jikinta ke rawa, in ta motsa, haka yake sharking, tare da daukar ido. Sai gyalensa da ta rufe  kanta dashi. Simple makeup ne a fuskarta. Tana kwance a cinyar Hajiya kamar yadda ta mayarma Hajiya cinya filo. Suna kallon news. Tare da hira jefi jefi. " ni kam Ummi, kin shanye abinda na baki, ko yauma ajiye min shi ki kayi?" Baki hubby ta turo, cike da shagwaba, don ji take in tana tare da Hajiya, kamar tana tare da gwaggonta ne. " zan sha anjima." Bata rai Hajiya tayi " tashi ki dauko min, haka jiya kikayi, karshenta sai zubarwa akayi." Tashi hubby tayi taje ta dauko kofin mai cike tugudi, wanda yaji kayan kamshi. Zama tayi tana sha tana bata rai. Don harga Allah yanzu bata son Abu mai zaki, ji take har tsakiyar kanta. Mikawa Hajiya tayi " na koshi." Karba Hajiya tayi ta duba cup din, ganin tasha ba laifi ta ajiye shi a kan side table. Sallamar da suka ji, yasa su maida kallon su bakin kofar, Hajiya dauke da fara'a, yayin da hubby zuciyarta ke faman dukan uku- uku........... Rungume juna sukayi da Hajiya, tana "oyo-oyo auta, bakin India." Hubby kam daskarewa tayi a wurin tana kallonsu, tasan girman soyayyar dake tsakanin Hajiya da autan nata, bata hada son sa da kowa, cikin yayanta. Har lokacin zuciyarta rawa take, ganin yadda hayder ya kara haske, da ciki. Sanye yake da kananan kaya. Trouser army green da White shirt, mai layi- layin army grean color. Hannunsa daure da black  I phone watch. Ga wani kamshi, mai dadi da sanyi daya cika dakin. Zama yayi kusa da Hajiya, suka fara gaisawa, da tambayarsa hanya. " "alhamdulillah tafiya tayi riba." Ya fada yana kallon Hajiya yana murmushi. Lallausan gashin Kansas, da yasha gyara, sai daukar ido yake, ta shafa " Masha Allah, Allah yasa albarka a abunda ake nema." " amen." Ya fada yana kai kallonsa kan hubby, da gaba daya take kokarin jawo jaruntarta. Ido hudu sukayi. Cikin rawar murya " ka dawo lafiya." Smacking yayi, " na sameku lafiya." Ya fada still idonsa na kanta. Don wani kyau yaga ta kara masa, daga zaunen da take, yana iya hango komai mu samman kirjinta daya kara cikowa. Shigar tata ta burgeshi sosai. Maganar Hajiya ya dawo dashi hankalinsa. Murmushi yayi, yana shafa sajensa. Harararshi hubby tayi, kasa- kasa. Don ta lura bashi da kunyar kallo, gashi ta kasa tambayarsa abun da yake kallon, kullun ya tsareta da mayun idonsa. Hajiya ta kalli hubby " ki shiryawa auta table. " Tashi tayi, don ta nufi dinning. " no barshi tukun, kisa a warmer in munje gida naci, yanzu ban jin yunwa." Ya fada yana kwanciya tare da daura kansa a cinyar Hajiya. " I miss this very much. " ya fada yana lumshe ido. " daga kai har matarka in kun karsa min cinya kun huta, kun mayarmin da cinya kamar filo."  Kara gyara kwanciya yayi, cikin shagwabar da yasa hubby sake baki tana kallon ikon Allah, duk da ba yau ta fara ganiba, amma a tunaninta ya girma yanxu. " ki daina barinta tana kwanciyamin a cinya. It's ally for me. " Dariya Hajiya tayi. " kai ma yaranka na xuwa, ban sake yadda ka kwanta min a cinya." " kai Hajiya, autanki ne fah? Su ma  suna da cinyar mama ai." " tawan dai zaku bar musu, suma su Mora." Ta fada tana murmushi Hubby kam kunya ne ya kamata, musamman irin kallon da Hayder ke mata a kai- kaice, yasa ta kasa sakewa. Mikewa tayi, zata koma dakin Hajiya. " ki dauko akwatinki, mu tafi." Ya fada " aa hayder! Ku kwana a nan, gobe in sha Allah ido na ganin ido, sai Ku tafi, tunda baa gyara gidan ba, gashi yanzu an fara sanyi, akwai kura. Nasa an gyara maka dakinka." Ba haka yaso ba, " OK, bari in je inyi wanka, sai in ci abincin." " Ummi debo masa ruwan zafi, a toilet dina. Na manta baa gyara water hitter din dakin ba." Tashi hubby tayi, ta nufi dakin Hajiya. Shi kuma, ya dau wayarsa ya shaidawa driver ya shigo masa da kayansa."                 ******************** Ta gama hada ruwan tana kokarin fitowa falon, shi kuma yana sawo kai dakin. Matsawa tayi, ta bashi hanya. Kallon kallo, a ka tsaya yi, tsakanin hubby da hayder. Ganin bashi da niyyar bata hanya " Hajiya na falo, bari in wuce." " and so." Ya fada yana daga mata gira Kokarin bi ta gefenshi tayi ta wuce. Jefa jakar hannunsa yayi kan bed din, ya jawota zuwa jikinsa. A tare suka sauke ajiyar zuciya. Kara rungumeta yayi a jikinsa. Yayi missing everything about her,. Ga wani filling dake fusgarsa, Allah -Allah yake ya dawo gida, gashi Hajiya ta rusa masa plans, sai yanzu yayi regretting turota, da tana gidansu, ba abinda zai hanashi nemar ma kanshi natsuwa a yanzu. Da kyar hubby ta kwace jikinta, tayi falo da saurinta.  Dafe kirjinta tayi " thanks to Allah. " Hajiya bata falon. Jingina yayi da bangon dakin, yana maida numfashi. Ya dade a haka, kafin ya lallaba ya shige toilet. Yana jin jina, yadda yau zai iya bacci ba tare da ya sauke damuwarsa ba. Don ganinta gaba daya ya kara rikitashi. Hajiya tasha mamakin ganin hubby kwance a falo. Kai ta kada ta nemi wuri ta zauna. Sanye ya fito da kayan bacci farare. Yayi kyau, sai kamshi ke tashi. Direct dinning table ya wuce. Kallo daya hubby ta masa, ta dauke kanta. Ido suka hada da Hajiya, kunya ce ta kamata. Da sauri ta mike ta nufi dinning table din, don tayi serving dinsa. Ko don ta cire zargi a zuciyar Hajiya Hannayenta yake bi da kallo, yadda sukayi kyau, sukayi wani haske, kamar ka taba jini ya fito. Kallonsa ya kai kan fiskarta, ta kara haske sai glowing take. Bakin nan yasha pink wet lips. Harararsa tayi kasa- kasa. Jin ya kamo hannunta, yana murzawa a nashi. Wani shock ne gaba daya ya xiyarcesu, Hajiya ta kalla, ganin hankalinta gaba daya yana kan nta news. Yasa tasa daya hannun da nufin banbare hannunta. Duka hannun biyu, ya rike yana murzawa a hankali. Kiss ya mata a hannun, sannan ya saketa, ganin yadda take a tsorace. Abincin ya masa dadi, amma darene, don haka kadan yaci, ya hada green tea. Ya koma kusa da Hajiya yana sha suna hira sama - sama. Mikewa hubby tayi ta shige dakin Hajiya, wanka tayi, ta sa kayan baccinta, tare da feshe jikinta da turare masu sanyin kamshi. Tayi kwanciyarta. Tsayawa Hajiya tayi, tana bin hubby dake sharar baccinta hankali kwance da kallo. " Ummi, Ummi." Hajiya ta fada tana dukan kafar hubby kadan. Bude ido hubby tayi mai cike da bacci, tana kallon Hajiya. Daure fuska Hajiya tayi. " oya tashi ki wuce wurin mijinki, bazaki kwana min a nan ba." Ido hubby ta zaro, tare da shagwabe fuska tana turo baki. Zatayi magana Hajiya ta katseta. " tashi kafin ranki ya baci, bada ni zaayi wannan rashin hankalin ba." Mikewa hubby tayi, tana tura baki. Zani ta daura akan kayan baccin, tare da zunbula hijab dinta. Hajiya na kallonta, bata ce komai ba. Sai da tazo zata fita, ta kirata. Dawowa tayi, Flack's Hajiya ta mika mata, irin 5 liter electric Flack's, wanda zaka jona shi da wuta, kamar kettle. Kallon Flack's din tayi, ta kalli Hajiya cikin rashin fahimta. " kije dashi, ko zakusha tea."  Dauka hubby tayi ta wuce, cikin sanyin jiki. Ajiyar zuciya Hajiya taja tare da shirin baccinta ta kwanta. A hankali ta tura kofar ta shiga. Kwance yake yana juyi, gaba daya hankalinsa a tashe yake, tunanin yadda zai fito da hubby daga dakin Hajiya yake yi, don gaskiya bazai iya hakuri ba. Yaji an bude Kofa an shigo. Ajiyar zuciya yayi, tare da fesar da iskar bakinsa. Wani dadi ne ya ziyarci zuciyarsa tare da furta " alhamdulillah" a saman labbansa. A kan table ta ajiye Flack's din. Dakin tabi da kallo, a tunaninta yayi bacci, ganin wuta a kashe, sai hasken fitilar waje dake hasko dakin. " wannan Flack's din kuma fah?" Ya tambaya yana tashi zaune. Gabanta ya fadi, jin maganar kamar daga sama. " Hajiya ta ce in taho dashi, ko zaka sha tea." Murmushi yayi yana shafa kansa. Tare da godewa Hajiya a ransa. " ta kyauta kam, kamar tasan ina da bukatarsa sosai." Kofar fita hubby tayi, da sauri ya tsayar da ita. " ina kuma zaki?" Ya tambaya yana kallonta " wai zan kawo maka kayan tea din ne." Ta fada Smacking yayi, Tare da mika mata hannunsa. " I have them already, let me show u." Dawowa tayi ta tsaya, ba tare data mika masa hannunba. " ban son Jan aji, I know you Miss me." Ya fada yana jawota ta fada saman jikinsa, in da ya mata kyakyakyawar runguma. " please hayder, Hajiya nanan, she can hear us."  Hayder kam bama ya jinta, hijab din da zanin ya zame ya watsasu gefe. Gaba daya jikinsu, rawa yake, hubby kam harda na tsoron kar Hajiya ta jiyosu. Don dakunan a Jere suke da juna. Hayder kam tsabar bukatuwa, yasa yama manta da Hajiya can hear them. Hajiya kam ranar kwanan dakinta, bai samu ba, sai dakinsu ummu sulaim ta kwana. Hankalinta kam yanzu ya kwanta, dama abinda take da bukatar tabbatarwa kenan. Tunaninta da wane idon zata kalli Hajiya, don ta tabbatar ba abinda zai hanata jiyosu, kasan cewarta mutun mara nauyin bacci. A gogon gefen gadon ta kalla 4am dai dai lokacin da hayder ya fito daga toilet din. Jallabiyya ya zura, tare da shinfida dadduma ya kabbara sallah. Tashi tayi, duk jikinta yayi tsami.  Tsaki tayi a hankali, taga alama ciwon bacci sai ya kamata in batayi da gaske ba, a ce mutun baya gajiya, a dare sai tayi wanka ya kai  hudu- biyar. Duk don karta kwanta da najasa, amma sai ya San yadda yayi, ya bata mata wankanta. A hankali ta bude dakin ta fita, dakinsu Ummul khair ta wuce, ga mamakinta, mutun ta gani kwance a kan gadon ummu sulaim. Da sanda ta nufi dakin Hajiya. Ganin bata dakin ta sauke ajiyar zuciya. Toilet ta wuce, ta tsarkake jikinta, tare da dauro alwala. Hand rayed tasa ta busar da kanta. Ta maida kayan baccinta. Sai da tayi sallar asuba, sannan ta dale gadon Hajiya, taja bargo nan da nan bacci yayi gaba da ita. Hajiya na kallon hubby, murmushi tayi tana binta da kallo, yadda take sanda abin ma har yaso yaba Hajiya dariya. Wai nan ita a dole mai wayau. In dauka kamar a dakinsu ummu sulaim ta kwana. Hubby na fita, ta tashi ta dauro alwala ta kabbara nafila. Sai to 9, ya shigo gidan tun daga fita sallar asubah. Ba kowa a falon, kai tsaye yayi dakin Hajiya. A gadonta ya hango hubby lullube da bargo, tanata bacci, hankalinta kwance. Karasawa yayi dai -dai fuskarta, lallausan hannunsa yasa yana shafa fuskarta a hankali, gyara kwanciyarta tayi " lazy bone." Ya fada yana sumbatar goshinta. She look beautiful, sai yanzu ya kara karewa fuskarta kallo,ta kara kyau, tayi haske kamar ka taba jini ya fito, bakinta ya kai idonsa da zagayen bakin ya kara bifowa sosai,. Bakinsa ya kai ya sumbaci labbanta, sannan ya fita. A falo suka ci karo da Hajiya tana shigowa. Rungumeta yayi, tare da gaisheta. Cike da faraa Hajiya ke amsawa, tare da tambayar gajiyar hanya. " alhamdulillah. " ya fada yana nufan dinning table. Yana fita, ta mike, tare da kai kallonta kan agogon dake makale a bangon dakin yana kallonta, After 9. Da sauri ta sakko daga gadon, cikin sauri sauri ta gyara gadon, tare da gyara dakin. Wanka ta shiga, bayan ta fito ta shirya cikin wani red Chinese dress, mai matukar kyau da santsi.  Riga da wando. Simple makeup tayi, cikin sauri take shiryawa don ko Hajiya bata gaisar ba.  Red Vail ta yafa, Wanda ya dace da kayan, ta feshe jikinta da turaruka bayan deodorant da humra, ta tasa a jikinta. Cike da jin nauyi ta gaishe da Hajiya. Cike da faraa take bin hubby da kallo. " masha Allah, wannan kwalliya tayi kyau. Kamar mai zuwa gasar sarauniyar kyau?" Hajiya ta fada dariya hubby tayi " tsarabar China da junaid ya kawo min." " ya kauta, sunyi kyau, suka kuma tarar da kyan."  Hajiya ta fada tana mikewa " maza kije kici abinci, gashi can har ya huce." Ta fita a falon Gaba daya idonsa na kanta, tunda ta fito, kamshin turarenta ya fara masa sallama, gaba daya shigar tata ta matukar burgeshi, kayan sun mata matukar kyau, kamar don ita aka halittasu. Kasa dauke idonsa yayi a kanta. Takunta da yadda jikinta ke juyawa, gwanin sha'awa ya zuba ma ido, yana tasbihi a ransa. " ban son kallo." Ta fada a hankali tana Jan kujerar dinning din daya, ta zauna. Smacking yayi " its my property. " ya fada in his husky voice Gug din kunu ta jawo ta zuba a cup. Ta kai bakinta, Still idonsa a kanta. Harararsa tayi, ji take kamar ta makeshi, wannan murmushin rainin hankalin da yake binta dashi. " kayan sunyi kyau, ina imagining dinsu a jikin My Nasrin." Ya fada Sai da ta hadiye kunun bakinta cikin tabe baki. " in kana so, sai in cire ka kai mata." Jingina yayi da kujerar sosai, yana shafa sagensa. " ya zama second use." Tabe baki tayi " good for u." Waina da soup din kayan cikin, data zuba zata ci, ya janye gabansa. Kada kai tayi, ta zuba wani. " ki shirya da wuri."  Kai kawai ta daga mishi. Mariya ce ta shigo, ita da mai aikin Hajiya. A nan take shaidawa hubby tun safe Hajiya ta sasu suka je gyaran gidan, dawowarsu ke nan. Hubby taji dadin hakan.               ******************* Hajiya da Hajiya Balkisu, suna zaune a falon Hajiya suna hira irin ta aminan juna. Don zuwan Hajiya Balkisu kenan bata dade ba. Hubby ta fito rataye da Jakarta. Ganin Hajiya Balkisu yasa ta rusuna tana gaisheta. Cike da faraa take amsa mata, tare da tambayarta mai gidan. " yayi, tafiya ne, shine aka zomin kwana biyu, Jiya ya dawo. So zasu tattara suyi gidansu." Hajiya ta fada cike da jin dadi. " Masha Allah, mun gaisa da hayder din ai yanzu da zan shigo." Sallama hubby ta musu, cike da kewa Hajiya ta sallameta, part din Mmn samira da Mmn Yusuf taje ta musu sallama, ta fito already hayder na cikin motarta driver sit yana jiranta.               ******************* " kinga ikon Allah ko? Wannan shine rabo ajali." Kallon  rashin fahimta Hajiya kebin Hajiya Balkisu dashi. " ban gane maganarki ba." Hajiya ta fada Baki Hajiya Balkisu ta rike " kar dai ace, baki hango abinda na hango ba, duk kwana kin nan da kukayi tare?" Zama Hajiya ta gyara, tana fuskantar Hajiya Balkisu da kyau. " kin kara Sani a duhu." Cike da mamaki Hajiya Balkisu ke bin Hajiya da kallo " zaki ce min baki ga alamun ciki a tattare da Habiba ba?" Kara gyara zama Hajiya tayi " ciki fa kika ce?" Ta tambaya " sosai ma kuwa ciki." Hajiya Balkisu ta fada With Confidence " kinsan ni in ba laulayi naga mace nayi ba, bana ganewa, sai kuma in ya fito."  Hajiya ta fada " lallai kuwa, amma tabbas ciki ne jikin Habiba. " Da sauri Hajiya ta tashi ta rungumeta Hajiya Balkisu cike da farin ciki. Dariya Hajiya Balkisu tayi. " auta ya girma, mun kusa zama kakan nin asali." " kai!!! Na so in zargi hakan, amma ganin ba wani laulayi take ba, na dauka kawai cikar daki ne, da kwanciyar hankali. Ashe abin farin ciki ne? Wai!! Allah na gode maka, daka nunamin wannan rana ta farin ciki. Yau ina masu kiran Ummi juya? Yanzu kuma mai zasu fada kenan?" " barsu tukun, Lokacin maida martani na nan zuwa, very soon." Hajiya Balkisu ta fada tana murmu .........   [09/03, 10:43] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 22       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Shiru kake ji, sai kira'ar sudais dake tashi a redion motar. Mariya na baya, tana faman kalle kalle. Sai hubby dake WhatsApp da Aisha, gaba daya hankalinta na kan wayarta. Jin tsayawar motar, yasata saurin dagowa, kallon kofar gidan da sukai parking tayi, sannan ta maida kallonta ga hayder cike da Neman Karin bayani. Kauda kansa yayi, ba tare da yace mata komai ba. Garar rufe kofar motar da taji, yasa tai saurin kai kallonta ga Mariya da already ta fita a motar. Zagowa tayi tanama su hubby sai gobe in tazo. Cikin sanyin jiki, hubby ta daga mata hannu, ba tare da ta samu ko kalma daya da zata furta ba. Allah - Allah take suje gida ta aiki mariyan ta siyo mata P-Test, ta samu tayi pregnancy test, ko ta samu natsuwar zuciya. Amma lokaci kadan hayder ya rushe mata plan dinta. Ajiyar zuciya tayi, jin ya harba motar a titi. " a kwai gobe" ta fada a kasan ranta, duk da ba haka taso ba. Suna gaf da shiga unguwarsu, wayarsa tayi kara. Dagawa yayi, cikin husky voice dinsa yayi sallama Shiru yayi yana sauraron mai maganar. Kafin taji yana cewa. " koma menene Ku bari sai da yamma." Shiru yayi can kuma ya danyi tsaki " i say in the evening. " -- " OK." Yana Karya kwanar layinsu, malan idi da gurgu na zaune a waje. Suna hira. Hango motar na zuwa gurgun ya washe baki. Malan idi, kakarmu ta yanke zaka, uwar dakinmu ta dawo." Da sauri malan idi ya mike, shima yana washe baki. " ai kuwa, sune, dama tun da naga yau ana share share, nasan su oga na hanya." Da sauri ya wangale get, tun kafin ma su iso. A bakin get din Hayder ya tsaya suka gaisa da malan idi, tare da tambayarsu ya hanya? Hayder ya tambayeshi lafiyarshi da kuma gidan. " komai lafiya, yallabai. Sai rashinku na kwana da yawa." Murmushi hayder yayi tare da amsa gaisuwar gurgun mutumin dake ta washe baki. Shiga yayi, yayi parking. Malan idi ya shiga musu da jakun kunansu. Dakinta direct ta wuce, komai tsaf a gyare sai kamshi ke tashi. Kayanta ta shirya ko wanne ta maida shi, inda ya dace. Sannan ta nufo kitchen don daura abincin. Cook Book, ta dauko tana dubawa. Kamshin turarensa ya tabbatar mata da dosowarsa kitchen din. A bakin Kofa ya jingina tare da dafe kofar da daya hannunsa. Juyowa tayi, tana kallonsa, " me kake son a dafa?."  Shafa sajensa yayi da daya hannun still yana kallonta, Ba tare daya ce komai ba. Haushi ne ya kama hubby, yana daya daga cikin abinda ke hadata dashi, sai kayi magana yasan dashi ake, amma sai yayi maka banza. Tukunya ta dauka ta zuba ruwa. Ta daura a kan cooker gas, tana kokarin kunna a shana, bataji takowarsa ba, sai dai taji an rike mata hannu. Hannun ta kalla, kafin takai kallonta kanshi. A shanar ya amsa, ya ajiye a gefe. " an hutashsheki." Ya fada yana shinshina wuyanta. " please hayder, kasan dai baza a zauna baa ci abinci ba, ko don su malan idi. " ta fada muryarta na rawa Juyo da ita yayi, ya ci gaba da romancing dinta. Ta bude baki zata yi magana. Ya daura yatsanshi a bakinshi alamar tayi shiru. " ta rasa wane irin fitinan nen yaro ne, wannan. Ya dawo kenan, yanzu zai hanata sakat da fitinarsa. " kina son ki batawa Hajiya yaronta." Ya fada in his husky voice.  Yana kara rungumota jikinsa. " dama can, tasan halin yaronta, shi yasa ta masa aure kafin ya fara tsince yaran jamaa."  " banda sharri!!! Ke kika gayyatoni, ni kuma na amsa, meye lefina?" " da yaushe na kiraka?" Ta fada tana dago kanta yanda zata ga fuskarsa sosai. " Hajiya kanta, ta yaba kwalliyar da aka min, shine naga ya kamata na bada tukuici. Kin ga ke kika bani goron gayyata." Ya fada yana smacking " banyi don kai ba, da har kanka zai na fasuwa. Nayi don radin kaina ne? Ta fada tana harararsa. " really. " ya fada yana daga mata gira. " really!!! Ka jira Nasrin ta shigo, na tabbata zatayi don kai, amma banda hubby." " kina son Nasrin din nan, naga a lama." Ya fada " yes!! I like her, she is a nace girl." Murmushi yayi cike da jin dadi. " thanks. " ya fada " amma kaman baka damu da ita ba? Do you really love her? " ta tambayeshi " why do u ask?." " gani nayi tunda kuka rabu, har yau baka taba daukar kafarka kaje ka ganta ba. Bayan an ce garin masoyi baya nisa, in har son da kake mata na gaskiya ne, yaka mata at least by now kaje ka kai mata ziyara." Smacking yayi tare da tabe baki. " kika Sani ko irin namu tsarin kenan?" Ya fada yana shafa gashin kanta. " ba wani nan, _a kwai katon question mark a kan son da kake mata.? Ta fada " zaki rakani.?" Ya fada yana daga mata gira " no." Ta fada tana kada kai. " why." Ya fada " ask one of your friend. " " ke nake son ki rakani." Ya fada cikin very low voice " no, in capital NO " " u are jealous of her." Harararsa tayi. " Allah ya kiyaye, da ina kishi bazan ce ya kamata kaje ba." " OK." Ya fada yana tabe baki. " kinsan yanzu zance ba sai kaje wurin budurwa ba, true phone and you're system, u communicate and see each other. I'm not like your stalking boyfriend's, every ware u go, the followe u." " that how its suppose to be." Ta fada " in my case is different. In ina son ganinta I just tell her, in no time zaki ganta a Nigeria. To tell u the true, ban taba daukar kafata naje wurin mace ba." Tabe baki tayi. " there love u, more than you love them. Amma hakan bashi zai hana ka kula da mai kula da kaiba. Koda yake laifinsu Ne, da zasu tsaya zubar da darajarsu da Allah ya musu, saboda so. Nama rasa me suka gani da basu gani a sauran maza ba, suke wani makale maka? Farin ko dogon hancin? " Murmushi yayi har tana jin sautinsa " ke da kike ikirarin bakya son Aliyu hayder bakya iya resisting dina, how do you expect them to resists me?" Nocking suka fara ji, sai lokacin hubby ta tuna a inda suke. Da sauri ta mike, gyara kwanciyarsa yayi, ya daura kansa a kan hannayensa biyu, fuskarsa na kallon sama. Ta gafen ido, yake kallonta tana kokarin sa riga, cikin sauri. Still nocking din aka ci gaba dayi. " wait. " ya fada yana mikewa, ganin tana kokarin fita. Kauda kanta tayi, smacking yayi, tare da zura jallabiyyarsa da short nicker. Sai da yazo zai fita, ya rada mata a kunne " go and cherk your self in the mirror. " Haushi ne, ya kamata, kamar ta mangare keyarsa. Dama a cike take da maganarsa ta dazu. Bai dade ba, sai gashi da manyan ledoji, masu tamarin Eat More restaurant. Still tana tsaye a inda ya barta, sai cika take. Tabe baki yayi. Ya wuce cikin kitchen din. Ya ajiye ledojin. Sauran kayansu dake watse a tiles din kitchen din ya tattara. Hannunta ya kamo, ya damka mata. Da gudu- gudu, ta haura sama. Dariya yayi, yana shafa tattausan sumar kansa. Don yasan ya tsokano rigima yau. Toilet ta wuce, madubi ta kalla, yadda gashinta ya wani baje, tare da wargajewa. wanka ta fara, tana tuno maganar hayder, hawaye ne suka fara bin kumatunta. Ita kanta ta rasa wannan fitinar. Kamar wani magnet haka take rasa duk kan kuzarinta, matukar zai bukaceta, bata iya resisting, ya san weak point dinta, wannan wani sabon babi ne na  rayuwarta, da 'da bata San da shiba. Tana kokarin fitowa yana shigowa. Ta gefensa tabi zata wuce. Rukota yayi da sauri. Masifa ta fara masa, don abun ya fara isarta, duk makullan dakinta, da toilet duk ya kwashe, bata da wani privacy a gidan. Dagata yayi cak, zuwa cikin barf da hannu daya ya riketa, ya kunna shower. Kokarin kwacewa take, don tayi alkawarin ta daina biye masa, tunda abun harda gori. Amma baa je ko ina ba, ya sakata a saiti. Midik kakeji Harararsa tayi, " ban yafe ba wallahi, mugun yaro." Ta fada tana nufar woodruff. Dariya yayi, yana ci gaba da goge kanshi da karamin trowel. Lotion dinta ya dauka ya fara shafawa. Duk harare -hararen da hubby ke binsa dasu yana kallonta. Shi dariya ma take bashi. Sai da ya gama, tare da fesa turarukanta. Still tana gaban woodruff, ta rasa kayan da zata sa, don ta kubutar da kanta, tun kafin yaga bayanta. Duk kayan data dauko sai taga bai yi ba. Tsaki tayi, tana jin haushin Aisha da ta sata yin irin wannan banzan dunkunan. Tasan har dasu ke ja mata murxuwa a wurin hayder. Wata tsohuwar rigar material dinta ta hango, mai zuwa da hijabinta. Musamman ta siyesu zuwanta umra, don zuwa masallaci. "Ban wuri," ta fada cikin siririyar muryarta, tana harararsa. " let me help u." Ya fada yana matsa lotion din a hannunsa. " na rokeka don Allah ka barni in shirya a tsanake." Ta fada tana kwace lotion din a hannunsa. Tabe baki yayi, tare da dage kafada, ya fita a dakin. Da harara ta rakashi.                  ***************** 3 cutter da armless shirt na kamfanin NIKE farare, sun masa kyau, kitchen ya wuce ya dauki Leda biyu, ya nufi waje. Malan idi ya samu yana alwala. Ya mika masa tare da juyawa ciki. Godiya malan idi yayi, yana Allah Allah ya idar da alwala yaga abinda ke cikin ledar din. Saboda kamshi daya cika hancinsa. Sai da ta idar da sallah, sannan ta sakko. A falonta na kasa ta sameshi, ya baje a carpet, yana kwasar girki.   Ledar din ta fara bubbudewa, shawarma taci karo da shi, a wani Small paper bag. Zama tayi tare da yin bisimillah ta fara ci. Idonta ta lumshe, saboda dadin daya ratsa mata kwanya. Tunda ta sauko, idonsa na kanta, ganinta da hijab, tabe baki yayi, ganin yadda take cin shawarma tana faman lumshe ido. Wunin ranar gaba daya haka hayder ya takura hubby, da fitina iri iri, sai yamma ta samu kanta, da su junaid suka kawo musu ziyara.            ********************** Ya dawo daga main house kenan, sun dan tsaya da malan idi. Bayan sun gama magana wayarsa ya zaro daga aljihun Jens dinsa. Kan bike dinsa ya zauna yana waya. Ledar din hannunta, take shillawa, tare da rere wakar film din Mariya. Ganin hayder a zaune saman bike dinsa. Jikinta ya dau rawa, mu samman da ta tuna da gar'gadin hubby. Ledar din data shilla take kokarin dawo da ita ta boye cikin hijab. Batai aune ba, sai ji tayi ta harde, dan dogon takalmin dake kafarta, ya turgude, sai gata a kasa, ledar tayi can gefe. Ko motsi beyi ba, yana ci gaba da wayarsa. Kallonta yayi, ya kalli leader din. Ya kauda kansa. Da sauri ya kara kai idonsa kan ledar din. P-Test  ya hango daya ya fito daga ledar din. Daga inda yake, yana iya karanta jikin dan dogon searchet din. Da sauri ta mike, ta dau leader din. Tare da dauke wanda suka zubo din. Gaishe shi tayi, ta wuce da sauri kamar munafuka. Kai kawai ya daga mata. Gaba daya hankalinsa ya kasu kashi biyu, ganin ya ma daina gane me nasrin ke fada, yasa ya mata sallama.               ******************** "Kin tabbatar ba Wanda ya gani ko?" Hubby ta fada tana tsare Mariya da ido. Kai Mariya ta daga mata. Da sauri hubby ta dauki leader din tayi sama. Har washe garin ranar hayder na jira yaji hubby tace masa wani Abu, amma shiru. Bayan ya tabbatarwa kansa she is pregnant. Ganin tsinkayen datayi anfani dasu har hudu, amma suna nuna she is pregnant, Duk da boyon data musu bai hanashi bin ciko su a kasan dustbin din toilet dinta ba. Farin ciki a wurin hayder baa magana, ranar ko bacci bai iya yi ba. Sai mika godiyarsa ga Allah tare da nemama yayansa gafara da rahamar Allah. Hubby kam ranar tasha kuka, da tunanin mafita, rashin zuwan hayder gareta a ranar ya mata dadi, don ya bata damar nazarin abinda zatayi next. 11 dai- dai, hayder ya fito daga dakinsa. Hubby na zaune a gaban mirror. Kanta ta kifa, tana faman saka da war wara. Kamshinsa ta jiyo, tai saurin dago kanta. " ki shirya ki sameni a waje, zamu je wani wuri." Ya fada yana juyawa, ba tare da ya jira mai zata ce ba. Cikin sanyin jiki, ta dauko hijab dinta, kalan da zai shiga da atamfar dake jikinta. Ta saka, tare da daukar jakarta, Already dama shiryawarta kenan. Yakai 5min a cikin motarta, sai gata ta fito. Gaba ta bude ta shiga, yaja suka tafi. Ba Wanda ya tankawa dan uwansa. Kallonsa tayi, sannan takai kallonta kan ginin da suke tsaye a gabansa. Sultana specialist hospital. Kallonsa ta kara yi, bai ce mata komai ba, bai kuma kalleta ba, balle ta sa ran samun karin bayani. Hasalima fuskarsa ba annurin da zata samu damar tambayarsa dalilin zuwansu hospital. Don haka tasa a ranta halan a cikin yan uwane wani ba lafiya, suka zo dubiya. Fita tayi ta bishi a baya, yana gaba, tana biye dashi suka shiga cikin hospital din....... Afwan. Rayuwa ba kai kake tsarawa kanka yadda kaso ba, sai yadda Allah ya so kuma ya tsara. Tafiya ce un expected ta kamani, shi yasa kuka jini shiru. Yau na dawo, ga gajiya, amma dunbin comments dinku yasa bazan iya shareku ba, kodon kauna da kulawarku. Shiyasa na daure na muku typing at leas in nuna muku how happy I'm. Na gode da kauna, da kulawarku. Love u all, thanks. Kujera ya nuna mata a Reception din, ba tare da yace mata komai ba. Bata da zabin daya wuce ta zauna. Zama tayi tana binsa da kallo. Ya koma mata kamar ba hayder data sani ba. Wani kwarjini na ban mamaki taga ya kara mata a idonta. Wayarsa ya Ciro, ya kira wata number. Minti kadan sai ga wani balaraben doctor ya fito daga wani corridor, wuyansa rataye da abun auna numfashi. Rungume juna sukayi, tare da hade kumatu, as usually gaisuwarsu. Sun danyi magana kafin, suka dawo da kallonsu kan hubby, da rabin hankalinta na Kansu, rabi na kan yan matan dake gefenta. Tun shigowarsu gaba daya hankalin yan matan, yayi kan hayder. " I known this guy." Dayar ta fada. " kai guy din nan ya hadu karshe, I like this guy." Dayar ta fada Still idonta a kan hayder " natuna!! You known Hafiz? Dayar ta tambaya. " wane Hafiz kenan." " our nebour." " na ganeshi, Wanda ya dawo daga Cyprus ko?" " yauwa shi. Friend dinsa ne, ina yawan ganinsu tare." Dayar ta fada. Ganin hubby na magana da doctor din da suke tare da hayder yasa sukayi shiru. Gai sawa hubby sukayi da Doctor sabir. Jagora ya musu har office dinshi. Katon office ne, mai kyau da tsari. Kujeru biyun dake gaban table dinsa ya nuna musu, cike da faraa. Sun dan dau lokaci, suna hirarsu da hayder, kafin wata nurse ta shigo, dauke da file a hannunta. Cikin girmamawa ta gaisheda su hubby kafin ta mikawa doctor file din ta fita. Doctor din ya dago yana kallon hubby cike da faraa a kan fuskarsa. Tambayoyi ya fara jerowa hubby, kallon hayder tayi, taga gaba daya hankalinsa na kan wayarsa. Gabanta ne ya fadi, cikin karfin hali, da rawar murya ta ke amsawa doctor din. Waya ya dauka ya kira wata nurse din. Minti kadan sai gata. Wasu fararen takardu, da yayi rubutu a kai ya mika mata. Tare da kallon hubby ya ce " madam kuje tare, akwai wasu test da za su miki yanxu." Jiki a sanyaye hubby tabi bayan nurse din. Zaune take, bayan ta dawo daga wurin da aka dauki jini, da fitsarinta. Tana kallon hayder da yayi balance a kujera suna hira, sama- sama da Doctor din. Duk yadda taso su hada ko ido ne abu ya faskara. Jikinta yayi sanyi, Bata so hayder yasan tana da ciki ba. Don ta gama yankewa kanta hukuncin zubar dashi, don da kunya a ganta da cikin hayder a jikinta. Bata san ya zata iya shiga jama'a da wannan abun kunyar ba. Ta rasa yadda akayi ya gane, tunda ita ba wani laulayi take yi ba, Aisha ce ta fado mata a rai, ta wani gefen kuma tana ganin Aisha bazata taba fallasa sirrinta ga hayder ba, tun da har ta shaida mata bata son ta gayawa kowa. Nurse din dazu ce ta shigo da envelope a hannunta. Doctor din ta mikawa, ta fita. Zaro farar takardar yayi ya kalla, yana murmushi. " congratulation ahehh!!!! She is 2month 2 weeks pregnant. Rungume juna sukayi ya na ce masa " thanks. " Hubby doctor ya kalla cike da faraa " congratulation uhtee!!!" Yake tayi tare da sunkuyar da kanta, cike dajin kunya. " zaki zo every month, don tabbatar da lafiyarki, dana beby din mu." Doctor sabir ya fada lokacin da ya rakosu har mota. Kai kawai hubby ta kada, tare da bude kofar motar ta shiga. Sallama sukayi da hayder sannan ya juya ya koma cikin hospital din, su kuma suka kama hanyar gida. Har suka iso gida, ba wanda ya tankawa dan uwansa. ******************* 10 o'clock dai dai, ya shigo dakin hubby, cikin shigar kayan baccinsa, sai kamshin turare ke tashi. Yau idonta biyu, fargaba da rashin sanin matakin da hayder zai dauka a kanta, da makomar cikin dake jikinta, wanda ta tabbatar yanzu zubar dashi, tamkar yakin duniya na biyu ne a gareta. Tana zaune a bakin gadonta, wani book din adduoi take dubawa. Ya shigo. Kallo daya ta masa, ta kauda kanta. Har lokacin fuskarsa ba walwala. Kusa da ita ya zauna tare da jingina da jikin gadon. Nazarinta ya tsaya yi, ganin har lokacin taki dago idonta ta kalleshi. Shi mamakinta ne ya isheshi. A tunaninsa murna zatayi a duk lokacin da ta samu wannan kyakyawan labarin. Amma ga mamakinsa sai yaga sabanin hakan. Tun ranar da tayi anfani da P- test din nan, ya lura gaba daya bata cikin walwala, da natsuwa. " me yasa baki gaya min kina da ciki ba?" Ya fada in his low voice, da ita kanta ba don tana kusa dashi sosai ba, bazata jiba. Shiru ta masa, ba tare data ce komai ba, tana kokarin maida kwallar data cika mata ido. " don't Tell me, u are not happy about it?" Ya fada yana tsareta da ido. Hawaye ne suka fara bin kumatunta. Dafe kanshi yayi tare da anbaton " ya Allah.'" sai kawai ta saki kuka mai cin rai, wani irin kunya ya rufeta shike nan yanzu ta tabbata matar hayder harda cikin shi a jikinta sannan kowa ya ganta yasan abinda hayder ya mata kafin ta samu cikin ace k'anin ta wai yau shine mijin ta kuma harda cikin shi a jikinta, ita duk a haukanta bata taba tunanin zata iya daukar ciki ba, da tayiwa kanta dabara, duk da baa wa Allah wayau. Yakan zartar da abinda yaso a lokacin da yaso. Cikin kukan ta matsa kusa dashi, idonta na zubda kallah tace "Dan Allah kayi hak'uri kar ka gayawa kowa please Na tuba, kasa ya zubar min da cikin ni banson haihuwa wallahi ni dai a zubar da cikin tun da ba wanda ya sani" Smacking ne kwance a kan fuskarsa, sajensa yake shafawa, yana kallonta. jawota yayi jikinshi cikin lallashi ya hada bakinshi da nata kissing dinta ya fara, jikinta gaba daya tayi sanyi, so bata yi wani yunkurin hanashi yin hakan ba. Tama san in yayi niyya ba yadda ta iya dashi. Sai da ya gaji don kansa, ya zare harshensa tare da gyara mata zama ya kwanto da ita kadan a jikinsa. Fuskarta ya dago ya tsare ta da ido cikin husky voice dinsa yace. " Kin san sanda cikin ya shiga ne? kinsan me zaki haifa ne? kinsan rayuwar da zaiyi? Ke kika halicce shi? Ko kyau tar da Allahu S. W. A ya mana kika raina? ki nitsu Habiba cikina fa kike cewa wai ince a zubar ciki da a da da kudima kin nema amma baki samu ba. Sai yanzu da Allah yaji kanki, ya tausaya miki, ya baki, kike neman yi masa butulci. May child!!! My own flesh and blood kike son in sa a zubar? kinsan wahalar dana sha kafin na sameshi, kin san irin tashin hankalin da na shiga, daga ranar da aurenki ya fado kaina, har ranar da kika shigo gidan nan a matsayin matata ta sunna? Kin san yaki da zuciyata da nayi don kawai in karbeki a matsayin abokiyar rayuwa? U have no idea. My blood my halal kike cewa a zubar me zaki gayawa mahalliccin mu? Ranar da bayi ke girbar ayyukansu?" Ya fada still idonsa a kanta. Idonta a rufe, don bazata juri kallon kwayar idonsa ba. kauda kanta tayi tare da cewa. "Bana so wallahi ko zan Haihu ba da kai ba, na yadda in haihu da koma waye da na haihu da kai, nace kanina ne mijina ko nace kaninah ne uban yarana?". Sosai zantu kanta suka bata mai rai, tureta yayi daga jikinsa. Idonsa cikin nata ya nunata da yatsa jikin shi har rawa yake yana fidda numfashi da karfi yace. " kar kiga Ina binki ina lallaba ki, saboda ke macece mai rauni da tawayan tunani, Ku mata akan biku a hankali dan a fahimtar daku amman na lura abin naki rainine, dan haka ya zama dole na gyara miki tunanin ki, zuwa yanzu, yaci ace na fi karfin ki kirani da yaro, tunda nayi abinda manyan mazan basu yi miki ba. Naga alamar baki tsoron Allah, sai tsoro da gudun surutun jama'a, da bazai anfaneki da komai ba. Sadaki aka biya, shaidu suka shaida. Ko kin dauka kowama sakarai ne, da zaiyi tunanin zan ajiyeki a gidana ina kallonki ba tare da wani abu ya faru a tsakaninmu ba? ki bude kunnenki da kyau. wallahi kar bakin ki ya kuma furta Kalmar zubda ciki a gidan nan. in kuwa kikayi gagganci furtawa, ko yunkurin aikata ba dai dai ba, akan cikina wallahi zaki gane kuskurenki, lokacin zaki san waye Aliyu hayder. Zan iya karawa da kowa akan cikina. Don shine farin cikina, cikar burin dan' uwana." Mikewa yayi ya fice a dakin, cikin bacin rai, da jin haushin hubby. Jikinta yayi mugun sanyi da kalamansa. " tabbas wannan babban butulci ne, ga niimar Allah a gareta. Sunje kasa yakai 6 duk don neman haihuwa. Bakar magana, wulakanci, cin mutunci, wanne ne bata fuskanta ba akan haihuwa? To meye nata na daukar zafi kan haihuwa da hayder? Surutun jama'a? A duniya ka isa ka hana jama'a surutu a kanka? Komai kayi abin magana ne, wani yaga kayi dai dai, wani yaga kayi kuskure. Baka taba burge jama'a. Tabbas farin ciki ya kamata tayi, yanzu ta tabbatar da kanta a matsayin cikakkiyar mace, mai haihuwa. Sabanin da da wasu ke lakaba mata juya, har ake kin aurenta don hakan. Tunowa tayi da Abdul Karim da Abdul fatta, wanda duk dalilinta na zamowa bata haihu da yayansu ba, yasa iyayensu mata kin yadda su aureta. Wanda ya zama sanadin aurenta da hayder. Tabbas yayi kokari, kuma yayi sadaukarwa. A matsayinsa na yaro mai jini a jiki, wanda yanmata ke rubibinsa, amma ya hakura ya amsheta a matsayin mata. Duk da shekaru 5¹/² years dake tsakaninsu. Sannan a matsayin bazawara, ba budurwa ba. Batayi tunani ba, Allah S.W.A ya mata gata, ya mata canji da hayder wanda a yan watan nin da tayi dashi, ba abinda ta nema ta rasa, abinci, sutura, kudin kashewa, duk wani abu na more rayuwa dai dai karfinsa yana yi. Komai nashi enough zai yi batare da gajiyawa ba. Kamar yadda ya dauke mata dukkan bukatunta na ya mace. Wanda a zamanin nan yana da wuya mutun ya samu wannan. Jiki a sanyaye ta tashi ta nufi toilet ta wanke idonta. Kara gyara jikinta tayi, tare da fesa turare mai kamshi ta nufi dakin hayder, don ta bashi hakuri. for the fist time. Don tun daga fist night dinsu, sai dai shi yazo dakinta, ko kuma ya dauketa zuwa dakinsa, amma badai da kafarta ta taka zuwa dakinsa ba. Ga mamakinta kamar yasan zata zo, dakin a kulle. Nocking tayi- tayi yaki bude mata, dole ta juya ta koma dakinta. Ran maza ya baci!! Kwance yake yayi rigin gine, kansa a kan hannayensa yana kallon ruffing din bedroom din. Tasbihi yake da istigfar. Ko zuciyarsa tayi sanyi. Don gaba daya ransa ya gama baci da hubby. " Ashe bawa zai iya zama mai butulci haka? Allah ya maka Niima ka butulce masa, wasu na nema ido rufe basu samu ba. Amma kai ka samu ka butulce! Bayan da da kudinka ka nema baka samu ba! Tabbas hubby bata sonshi, ko kadan. Yau ya kara tabbatar da hakan, Tunda har bata son hada jini dashi. Don karfin hali da rashin kunya har tana iya bude baki tace data haihu dashi gara ta haihu da wani. Wannan maganar ta masa ciwo fiye da sauran magan ganunta. Ta manta shima bafa sonta yake ba. Ba yadda ya iya, shi yasa ya rungumi kaddara. Duk da wasiyyar Yusuf na ya aureta, Sam bai yi niyyar aurenta ba, don yasan baya sonta, shi yasa ma yaja bakinsa yayi shiru, bai taba furtawa kowa ba, daga shi sai Allah, sai kuma dan uwansa. Don dama koda Yusuf din ya bukata bai amsa masa ba. Don yasan abun da kamar wuya. Kaddara tazo ta hadasu hakan yasa ya amsa da hannu bibbiyu duk da yana jin ciwon abun a ransa. Amma ya kudurta zai zauna da ita don Allah, zai kula da ita ya sata a farin ciki, don Allah, sannan ya cika muradin yayansa na ganin hubby cikin farin ciki ko bayan rayuwarsa. Yanaji ana nocking, yasan ita ce, amma bashi da muradin ganinta a lokacin. Tsaki yayi tare da gyara kwanciyarsa. Ranar gaba daya baccinsu ragaggene. Hubby kam tsabar nadama da danasani su suke nukur kusarta. Nafila ta kwana yi tana neman gafarar Allah, tare da ma Yusuf addua. Sannan ta nema musu zaman lafiya ita da hayder. Koba komai yanzu dole ta yadda ta amince. Shine miji kuma uban yayanta. Allah ne ya bashi girman, dole ta saukar da kanta ta nemi aljannarta. Ga hayder ma kusan hakan ce, sai dai shi addua yama yayan nasa, tare da adduar Allah ya sauki hubby lafiya, ya azurtasu da zuria masu albarka. ******************* Yau kwalliya sosai hubby ta zage tayi, musamman don oga hayder. Tayi kyau sosai. His favorite tayi masa break fast. Sai 10 ya shigo gidan. Sai da ya shirya cikin kananun kaya, ya sakko zuwa kitchen. Mariya ya samu tana goge goge. Da sauri ta durkusa tana gaisheshi. Rai ya hade kamar bai taba dariya ba, wanda yasa cikin Mariya kadawa don tsoro. " meye aikinki a gidan nan?" Ya tambayeta cikin kakkausar murya. Jikinta da zuciyarta gaba daya suka hau rawa. " wanke - wanke, shara, mopping, sai taya Anty aikin girki." Ta fada muryarta na rawa " good!! Daga yau ta kara aikenki dai- dai da wajen get, kika je sai na kakkarya kafafunki." Ya fada in warning tone Jiki na rawa Mariya ta amsa, tare da bashi hakuri. " bace min a nan." Ai kafin ma ya rufe baki tayi waje da gudunta..........    [10/03, 13:05] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 23       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... A falon kasa hubby ta tarar da Mariya ta rakube wuri daya sai rarraba ido takeyi, kamar wadda taiwa sarki karya. " kin gama goge kitchen din.? " ta tambayeta. Cikin rawar murya " aa, yallabai na kitchen din. " Juyawa tayi ta nufi kitchen, cikin takunta na natsuwa da daukar hankali, Zuciyarta na bugawa. Trey ne a gabansa yana jera bowls mai dauke da soup, sai cup din black tea da toasted bread. Wani kwarjini ya mata, da kyar ta lalubo natsuwarta, ta karasa ciki. Jingina tayi da cabinet tana mai fuskantarsa. " mun tashi lafiya." Ta fada cikin siririyar muryarta, mai dadin sauraro. For the fist time, sau da yawa shi ke fara gaisheta, ta fatar baki, ko rungumeta ya mata kiss a kumatu " morning. " . Kallonta yayi ya tabe baki, ba tare daya amsa mata ba, ya dau trey dinsa ya fita. Bata daddara ba ta bishi a baya har zuwa falonsa. Sai lokacin ya ga wormers din data jera a dinning. Ajiyewa yayi, yaja kujera ya zauna. Dafa kujerar kusa dashi tayi. " na dafa maka favorite dinka." Ta matsa tana bude masa wormers din. " thanks!! Take your food and live that place. " ya fada in warning tone Rufe wormer din tayi ta dawo kusa dashi. Tare da rike kunnenta biyu, kamar yadda takewa Yusuf in ta masa laifi. " nasan ban kyauta ba, na bata maka, I'm very sorry. " ta fada cikin muryarta mai dadi. Har cikin zuciyarsa yaji sanyi, tare da samun relive a zuciyarsa. Yasan yanzu ta sakko daga dokin shirmen nata. Tabe baki yayi ya ci gaba da cin bread dinsa. Plate ta dauka ta zuba masa abincin data dafa, taja kujera ta zauna, tare da janye plate din bread din ta tura masa daya plate din. Ganin bashi da niyar ci, yasa ta dibi kadan takai bakinta. " see!!! yayi dadi sosai." Dubanta yayi,  tare da ture plate din  " then eat." Bata rai tayi " please hayder, musamman saboda kai nayi fah!" " really!! " ya fada yana daga mata gira. Kai ta kada masa, tana shagwabe fuska. " don't cook for me again, because I'm not eated." Ya fada yana sipping din black tea dinsa. " why?" Ta fada a shagwabe Jingina yayi sosai a jikin kujerar, hannunsa yasa yana shafa sajensa, idonsa a kanta. " because I'm apred u poison me." Ya fada in his husky voice Ido ta zaro, tana kallonsa, cike da mamakin kalamansa. " ta yaya zakayi tunanin zan iya poisoning dinka. Haba hayder? Rashin imanin nawa bai kai nan ba. After all me kamin da zafi da har kake tunanin haka daga gareni?" Ta fada idonta ya fara kawo kwalla. Smacking yayi, yana shafa sajensa. " kin san in mace bata son namiji komai ma zata iya yi, balle yadda jiya kika kara tabbatar min how trueally hate me." " kayi hakuri I regret every word I say to u yesterday. How can I hate u, bayan kai din dan uwanane? Ko ba soyayya ai akwai so irin na yanuwantaka tsakanina da kai." Ta fada tana share hawayenta. Tabe baki yayi " it OK, ya wuce. Ki shirya haifawa hayder yara every year in sha Allah. This is your punishment, no family planing. " ya fada yana kallonta Kauda kanta tayi, tana dan tura baki " in ba wuya ba!" Ta fada " ko da wuya, daga yau zan fara saki a addua, kiyi ta zazzagominsu. Muga ta karyar son girma." Harararsa tayi " kamar wata akuya? Duk shekara? ina laifin after 5 - 5 years.?" Ta fada cike da shagwaba "We shall see." Ya fada " ka bari in nasrin ta shigo tai tayima duk shekara, tunda kana so." Ta fada tana kallonsa. Sagensa ya shafa, tare da murmushin gefen baki. " ke zaki Haifa min duk shekara. Ita kam matar so ce, 1 zuwa 2 sun isa." " watan nice banza, akuya in ta zazzago maka ya'ya ga injin mai jini! Saboda baka san ciwona da zafi na ba ko? Wallahi baka isa ba, tun wuri ka sani I'm not your engine. " ta fada cikin jin haushi Murmushi yayi da har dimples dinsa suka fito sosai. Tashi tayi ta dau plat din data shirya masa abinci, ta tura a gabansa. " dole ne in ci? " ya fada yana smacking " yes!!! Wataran sai na yakushe fuskarka, akan wannan murmushin rainin wayon." Ta fada Tabe baki yayi yana shafa sajensa, tare da kara balance a kujerar. Jawo kujerar tayi kusa dashi, ta debo abincin a spoon takai bakinsa. Bude bakin yayi, ta juyemasa. A haka har yaci da dan yawa. Ta kara debowa ta nufi bakinsa ya kada kansa. Ajiye spoon din tayi, ta tashi ta fara tattara wurin. " ke kinci abincin ne?" Ya tambayeta " nasha kunu." Kallonta yayi cikin rashin fahimtar meye kunun? Ci gaba tayi da tattara kayan. Hannunta ya kama, tare da janyota ya zaunar da ita a saman cinyarsa. " thanks for the food, its delicious. " Murmushi tayi, tana kokarin tashi, kara matseta yayi a jikinsa. Hannunsa yasa yadan dage rigarta yana shafa plat Tommy dinta, a hankali. Wani soyayyar abinda ke cikin yakeji yana ratsa shi. Lumshe ido hubby tayi ta kara lafewa a jikinsa. Jikinta ya fara sanyi, saboda yadda sakonsa kebin jinin jikinta. Wuyanta ya fara kissing a hankali, hannunsa na yawo a jikinta. Abunka da kwana biyu baa hadu ba, Gaba dayansu a bukace suke da juna. Juyowa tayi ta hade bakinsu wuri daya.                    *************** Tana gama girkin rana, ta sallami Mariya, kamar yadda hayder ya bukata, don a cewarsa yana takura. In ta gama mata aikinta in har yana gida ta tafi kawai, basai ta kai 5 ba. Cikin nishadi suka ci abinci, shi yajasu jam'in sallar azahar. Dakinta ta nufa don bacci takeji, jiya bata samu ta runtsa ba. Kayanta ta cire ta shiga tai wanka. Doguwar riga armless Mara nauyi tasa ta feshe jikinta da turare, ta kwanta. Har bacci ya fara daukarta ya shigo dakin. A hankali ya hau gadon tare da mata kyakyawan runguma. Minti kadan bacci yayi gaba dasu.                 ******************* " naga sako na gode Allah yayi maka albarka da sauran yan 'uwanka duka." Alhaji Jamal ya fada cike da jin dadi yana kallon hayder. " amen daddy." Ya fada  idonsa a kan TV da daddy ke kallon news. Kallon dan nasa yake cike da jin dadi, da alfaharin zamowarsa da a gareshi. Yara nawa ne masu irin wannan tunanin? A ce mahaifinka nada hali, amma kai zaka dauki dawainiyar duk wani kayan abinci na gidansa? Shinkafa, taliya, macaroni, semovita, cues -cues, madara, mangyada da sauransu. Yau kimanin wata na uku kenan duk wata haka hayder zaiyi karamin pickup na kayan abinci ya kawowa mahaifin nasa. Hakan ba karamin dadi yakewa Alhaji Jamal ba. Kamar yadda yake masa, haka zai siya ya aikawa  Alhaji babba duk da nashi baya kai na mahaifin nasa. Sun dan dade suna tattaunawa dan gane da business dinsu hayder din, kafin ya nufi cikin gida. A main kitchen ya samu Mmn Yusuf na aikin abincin dare. gaisheta yayi cike da faraa, itan ma cike da jindadin ganinsa take amsawa tare da tambayar hubby. Sun dan dade suna magana kafin ya wuce part din Hajiya. A bedroom dinta ya sameta tana nade kaya. Rungumeta yayi, tare da gaisheta. Dariya tayi tana jin dadin ganin autan nata. " ya Ummi? Ba wani Matsala ko?" Ta tambaya kamar yadda ta saba kullun in yazo, sai ta masa wannan tambayar. " lafiya kalau, tana gaisheki." Ya fada yana fadawa kan gadon Hajiya da karfinsa. " ina amsawa, akwai garin kununta da nasa aka mata, in ka tashi tafiya sai ka wuce mata dashi."  Ta fada " ba gida zani ba," ya fada yana gyara kwanciyarsa. Kallonsa hajiyan tayi " koma ina xaka ka tafi dashi, tunda baa kanka zaka daura ba." Ta fada " makaranta zani, ki bari gobe in sha Allah zan zo in karba." Kada kai Hajiya tayi " shi kenan Allah ya bada saa. Kunje asibiti dai ko?" Ta fada tana kallonsa. Kallonta yayi, cikin rashin fahimta " waye bashi da lafiya." Ajiye rigar hannunta tayi ta zauna a bakin gadon kusa dashi. " kar dai ka cemin daga kai har ita, baku fuskanci halin da take ciki ba? Ya kamata ka kaita taga likita, don tabbatar da lafiyarta da abinda ke cikinta. Sannan ba zaa rasa shawarwarin da likita zai baku ba, Ta wurin inganta lafiyarta, duk da ba wani laulayi take ba, amma dai kam ya kamata kuje." Kansa ya daura a cinyar Hajiya, cike dajin nauyinta. For the fist time in his life daya ji nauyin Hajiyan. " munje 2 days ago." " yauwa hakan yafi ai." Ta fada tana shafa sumar kansa. Murmushi yayi " na kusa zama daddy, ya fada in very low voice. " Dariya Hajiya tayi " na kusa zama kaka, dan' da namiji shine jika, abin cikin kwan dayafi kwan dadi." Kai ya dago cike da shagwaba. " yanzu sai fa kifi son shi, ko ita a kaina ko." Dariya Hajiya tayi " soyayyar autana ta dabance, albarkacin autana zasuci." Murmushi yayi, tare da kara kwanciya akan cinyar tata. " ya maganar makarantar naka?" Hajiya ta tambaya Tashi yayi ya zauna. " zan dan dakata tukun, dama nida ita gaba daya nake son mu tafi, itama ta fara nata karatun, amma yanzu ina ganin zan bari sai bayan ta haihu sai mu tafi." Murmushi Hajiya tayi " hakan ma yayi, Allah ya sauketa lafiya." " amen." Ya fada Murmushi Hajiya ta sake yi, ganin tsantsan farin ciki, tattare da autan nata. Hira sosai sukayi da Hajiya sai kusan magrib yabar gidan, ya nufi masallaci inda yake salla, tare da daukar karatun littatafan addini.              ********************* Dawowar hayder ya wuce bedroom dinsa, da mamaki yake bin hubby da tayi dai dai akan bed dinsa da kallo. Sanye take da kayan bacci silk red, karamar riga da boom shot, sun lafe sosai a jikinta. Kamshin turarenta dana dakin ya bada wani kamshi mai dadi, da sanyaya rai. Da sauri hubby ta sakko daga gadon, rungumeshi tayi, shima kamar jiranta yake ya kara matseta a jikinsa. Sun kai some minute sannan ya dago da kanta ya manna mata kiss a goshi, da saman labbanta. " bakiyi bacci ba?" Ya fada in husky voice  kai ta kada, cikin shagwaba ta kara makalewa a jikinsa. " ina kake zuwa ne, kusan ko yaushe baka dawowa sai after 9?" Ta fada cikin shagwaba " tadi nake zuwa." Ya fada yana kallonta kasa -kasa dariya tayi, " lokacinka ne ai, Allah ya bada saa."  Smacking yayi tare da dago kanta suna kallon juna. " bakya taya Nasrin kishi kenan." Ya fada " taga zata iya ne ai,." Ta fada " kamar Yaya?" Ya tambayeta " tasan kana da yan mata buhu - buhu amma still tana sonka. Tasan kuma bayan ita bazaka rasa wata a gefe ba." " banda sharri dai.!"ya fada yana Kallon yadda take motsi da bakin, cikin shagwaba take magana. A da yana daya daga cikin abunda ya tsani hubby saboda shi. Amma yau da ta fara masa salon shagwabarta sai abun yana burgeshi Kwarai. Lips dinshi ya daura a nata, batayi wata wata ba, ta cafke tare da sarrafa shi cikin bakinta, wani salo take masa da baisanta da shiba. Ai gaba daya sai ga malan hayder ya rikice. Sun dade suna romancing juna, kafin ya zareta a jikinsa. Wanka ya shiga, yana fitowa ya feshe jikinsa da turare, bai ma bata lokacin sa kayan baccinsa ba, ya nufi hubby dake kwance lamo, gaba daya jikinta ba kuzari. Ajiyar zuciya suka sauke a tare.               ******************** Hayder ne ya shigo, sai wasu mutun biyu, dauke da kwali. Sai da ya  basu izinin shigowa ganin hubby bata falon. A falonta na kasa suka ajiye fridge matsakaici mai kyau. Sai da suka jona komai intact sannan suka masa sallama suka tafi. Fita yayi, suka shigo da malan idi, rike da ledoji. Sannan malan idi ya fita. Bude fridge din yayi, ya fara jera fresh fruits: apple, orange, pear, grebs  peach, banana etc sai da ya cika fridge din da fruit. Sauran ya kwasa ya mikawa malan idi A hankali take sakkowa daga steps din. Yau gaba daya jikinta bata jin dadinsa, ga tashin zuciya, ko dan kunun data saba sha yau bata sha ba. Tana jin yunwa amma ta rasa me take son taci. Da sauri ta fada jikinsa. " morning. " ta fada tana zagayeshi da hannayenta biyu. " morning!!! Are u OK?" Ya fada cike da kulawa, ganin yanayinta Kai ta kada masa " tun asuba, sai yanzu? Shima tadin kaje?" Ta fada tana tura baki, cikin shagwaba kiss ya mata a goshinta " yaushe kika fara samin ido ne?" Ya fada " ba sa ido bane, ina son sanin inda kake zuwa ne?" " wurin sweet heart dina." Ya fada yana smacking " an jiman nan zan kira Nasrin, in bata bayani." Ta fada tana zama a kan daya daga cikin kujerun falon. " please karki kashemin aure, tun baa daura ba." Ya fada yana kokarin haurawa sama. Sai lokacin idonta yakai kan fridge din. Tashi tayi tana binsa da kallo, yayi mata kyau sosai, gashi yayi das a wurin, kamar dama don shi aka bar space din. Budewa tayi. Murmushi ne ya bayyana a saman fuskarta. Bunch din ayaba ta dauka ta koma ta zauna, TV ta kunna tana ci tana kallo, cikin ikon Allah taci sosai. Mariya ce ta shigo ta tattara bawon. Kwanciya tayi tana jiran sakkowarsa, don shi ma baiyi break fast ba, gashi har pas 11 .......... Wasu na complain na rashin yawan typing, wanda already nayi bayani. Amma nayi tunanin in har pages din baya muku yadda kuke so, mai zai hana in maida update dina every 2 days? Ina jiran ra'ayoyinku. Thanks Kallonsa tayi tana murmushi, yayi kyau, cikin jamfa da wando, farare. ta mikewa tayi tabi bayansa zuwa falonsa. Kujera ya ja mata ta zauna, kafin ya ja kujerarsa ya zauna. Fleet din vegetables chicken toll, ta janyo tare da cire rapper din ledar din. Taja karamin fleet ta sa masa ta tura gabansa. Sai da ta hada masa komai sannan ta kalleshi. Idonsa cikin nata " bisimillah!!!" Ta fada tana dan harararsa don ta tsani murmushin data sama na rainin hankali da yake mata, gashi ta lura ya zama kamar a jikinsa. " shukhran!." Ya fada tare da yin bisimillah ya fara cin abincinsa. Roll daya ta dauka tana ci a hankali, idonta na kan TV tashar CNN. Wani farin ciki hayder keji a ransa, tare da godewa Allah bisa niimarsa gareshi. Yau shine da iyali, ana tattalinsa da kulawa dashi, abinda bai taba tunani ba daga hubby, amma kwana dayan nan gaba daya ta canza, wani kulawa da tattali na musamman take bashi. In ya tuna nan da few months zai dauki danshi na kanshi, flesh and blood farin cikin baya misaltuwa a zuciyarsa. " meye matsayarki kan karatu?" Kamar daga sama taji tambayarsa. Juyowa tayi ta kalleshi idonsa baya kanta, Shagwabe fuska jin tayi shiru yasa ya dago yana kallonta. Hada ido sukayi, ya daga mata gira, yana gyara zamansa. " ni kawai ka mai dani islamiyyata." Ta fada cike da shagwaba Tabe baki yayi,  tare da sipping din green tea dinsa. " ba wannan nake magana ba." Ya fada in husky voice. Kara shagwabe fuska tayi, tana dan tura baki. " islamiyya kawai nake so." Shi dariyama taso bashi, yadda take yi, tare da burgeshi. lallai yana da aiki! Hubby akwai shagwaba ta karshe ma " Mace itace jigo na farko na gina al'umma, in aka samu rauni ko sakaci ta wurin bata ilmi da tarbiyya, tamkar an rusa al'umma ne baki daya. Ilmi ina nufin na addini, wanda zai daurata kan tafarkin tsira, wanda zata tarbiyyanci al'umma zuwa ga rabauta. Ilmin zamani shi zai kara haska mata rayuwa da abinda ta kunsa. Mace na bada ingantacciyar tarbiyya yayin da ta hada ilmi duka biyu. Rayuwarta data yayanta zakiga ta fita daban. Karki manta da, Hadisin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, wanda ya ke cewa ‘Dalabul ilmu faridatun ala kulli muslimin wa muslimatin,’ wato neman ilimi farilla ne ga dukkan musulmi na miji ne ko mace. Mace mai ilimi itace za ta san yadda zata tafiyar da gidanta da kyau idan tana da hankali. Mace itace uwa, ita za ta sa yaranta a kan hanya, har shi mijinta da kan sa ita kan koya masa dabi’u masu kyau. In kuwa ba ta da ilimi, ba ta san abin da ya kamataba tana iya zama masu  makauniyar jagora.  Ilimi ke sanya mace ta san yadda za ta tafiyar da kanta a kowane irin hali. Za ta zama wayayyiya mai basira." Shiru tayi tana sauraronsa cikin mituwar jiki. Ita kanta bata san dalilinta na rashin son karatun ba, to ita in ma karatun ne me zata karanta kenan? Secondary din ma ya takare balle university!! So kawai yake tayi ta kwaso masa carry over yana tsokanarta zero head. In ba haka ba, bata san ta inda zata fara ba. Ganin tayi shiru, ya kama hannunta zuwa 3 sitter din dakin. Zama yayi, ya kwantar da ita a jikinsa. Hannunsa ya tura cikin rigarta yana shafa cikinta a hankali, kiss ya mata a goshi. " think about what i say to u. Masu bincike na duniya  ma sun ce duk namijin da ka ga ya yi nasara a rayuwarsa, to akwai mace bayansa – ko uwarsa ko matarsa, I want u to be that woman. " Tura baki ta danyi, tare da kara shigewa jikinsa. " to ni inma nace zanyi karatun me zan karanta?." Ta fada a shagwabe Sunkuyowa yayi ya summaci dan bakin nata dake daukar hankalinsa, in tana shagwabarta. " ba komai bane matsalarki, illa rashin maida hankali, wasa ya miki yawa. Amma na tabbata in har zaki cire komai ki maida hankali, ba abinda bazaki iya karantawa ba." Murmushi tayi " ni dai da ka barni a islamiyyata, nafi jin dadi." " I will teach u, by my self." Ya fada " no my king ma haka ya ce, amma gaba daya karatun a shiririta yake karewa, haka ya hakura ya sani a islamiyya." Ta fada idonta na cikowa da hawaye Wani iri hayder yaji a ransa, da ya kasa fassara yanayin. Kasa ce mata komai yayi, mikewa yayi. Ganin yana niyyar fita ta tashi ta zauna " sai ina?" Ta fada Har yakai bakin Kofa, ya juyo yana kallonta. Smacking yayi " main house. " ya fada in his husky voice. Tasowa tayi " bamu gama magana bafa!" Ta fada tana fadawa tsakiyar kirjinsa, tare da zagayeshi da hannayenta biyu. " zamu karasa in na dawo." Ya fada cikin low voice don gaba daya jikinsa ya fara sanyi. " in zo muje please!!? " ta fada cikin marairai cewa, tana kallonsa. Gaba daya hayder ya shiga wani hali, wani felling ne ke fusgarsa, musamman yadda yake jin kirjinta na gogan nasa. Ga yadda take marairai cewa tana fari da ido kadan,. Abun ya tafi dashi, abinka da mai jiran kiris. Hubby tayi murmushi ta dauke fuska, tana mamakin hayder. Kara jawota  jikinshi yayi ya rungumota tsakankanin hannuwanta ya zura hannayenshi ya na shafo kirjinta  dake tsone masa ido,  yana lumshe ido yana fadin " I love them, they are so sweet and nice " Hubby kara shigewa jikinsa  tayi, tare da rumtse ido tanajin dadi yadda hannayensa ke yawo a jikinta.  hannuwanta tasa  tana shafo sumar kanshi shi kuma yana ta faman sunsunarta, yadda take massaging hair dinshi da soft hand dinta yasa yakara shiga mood da a hankali ya rinka yin kasa da hannunshi yana shafa ilahirin jikinta, yana isa wurin Tommy dinta ya rika shafashi yana dan kaiwa ga mararta kadan. Sunkuyawa yayi ya sumbaci plat Tommy din. Dukansu numfashi suke ta fitarwa, Idanunsa da suka canza colour, ya dago kanta yana kallon kyakyawar fuskarta, yadda take sauke numfashi, idonta a rufe, iskar bakinsa ya hura a saman fuskarta, tai far da idanta ta bude su a kansa. idanunsu na kallon juna yace " please I'm in mood"ya marairaice  yana kashe mata ido daya.   ido hubby ta zaro, duk da itama ya tsokanota a bukace take. ta bude baki zatai  magana ya hade bakinshi da nata ya cafko harshenta yafara tsotsa while hannuwanshi  a kan kirjinta  yana massaging dinsu nicely, Gaba daya hubby ta kasa hanashi don she's loosing her sense se numfashi kawai takeyi, kafafuwanta ne suka gaza daukarta ta tafi luuuu ya yi sauri ya tallabota. Dagata  yayi bridal style ya nufi  dakinsa da ita. Suna shiga ya ajiyeta saman bed. yasa hannu ya zage zip din rigarta, ya zage na skirt Yayi wurgi dasu, kissing dinta tundaga  up, to dawn.            *********************** Mita take cike da shagwaba na wankan da ya sata, bata shirya ba, ga lokacin daura abinci har ya wuce. Smacking yayi, yana shafa sajensa. " in har baa daina min irin wannan shagwabar ba, nima yanzu na fara sa mutun wanka a gidan nan." Harararsa tayi tana tabe baki " ka fadi gaskiya!? Dama can haka mutun yake." Rike gemunsa yayi kadan yana daga mata gira " koma meya faru laifin kine. As long as ana min haka, to mutun ya shirya." " haka kurun! Kullun mutun cikin ciwon jiki." Ta fada tana zura doguwar rikarta, hand dryer ta dauka ta fara busar da gashinta. " karfe daya baya amo, duk wanda ya sai rariya ai yasan zata xubda ruwa." Ya fada tare da manna mata kiss a kumatu ya fita. Da kallon rashin fahimtar zancensa ta bishi, har ya fice a dakin. Tabe baki yayi ta cigaba da abinda take. Dakinsa yaje ya canza kaya, ya dau makullin bike dinsa. Ya fice a gidan, cike da farin ciki. Yana daya daga cikin abunda yake burge hayder dan gane da hubby irin duk yadda zai zo da bukatarsa bata hanashi, koda sau nawa zai zo mata, sai dai daga baya taita mita tare da harare harare, ita a dole jikinta na ciwo, bai hana kuma in ya sake bijiromata ta mika wuya. A rayuwarsa yana son mace mai juriya, saboda yanayinsa. Ta nan kam sunyi mach.  Hubby kam sai da tayi sallar azahar sannan ta sakko da mamakinta ta tarar da Asima da Asiya, zaune a falonta na kasa, Mariya ta cikasu da snacks and juice. Da faraa ta karasa tana musu sannu da zuwa, duk da yadda kirjinta ya buga ganin Asiya, don ta dade tana tunanin yadda haduwar tasu zata kasance. Da faraa suma a kan fuskarsu suka gaisa, hubby na tambayarsu saukar yaushe? Asiya ce ta amsa da " jiya." A takaice tana karewa hubby kallo, ganin yadda ta kara kyau da cika, wani dan banzan kishi ne, ya turnike zuciyarta. A take idonta suka fara cikowa da hawaye. Hubby ta lura da kallon da suke binta dashi, musamman Asiya. Tausayin asiyan ne ya cika zuciyarta. Tare da jin kunya da nauyinta. Tashi tayi a san yayi, tare da ce musu bari tadan je kitchen ta dawo. Da kallo Asiya ta bita, har ta bacewa ganinta. Ajiyar zuciya ta sauke. Asima ta kalli kanwar tata cike da tausayawa. " ki kwantar da hankalinki, ki cire komai a ranki, ki nemi zabin Allah a alamarinki, sai ki samu sauki cikin rayuwa. Kar ki zamo mai kwallafa rai akan abun da baki da tabbas din samunsa." Kai Asiya ta kada. Tare da bin falon da kallo. Ya burgeta sosai, "ina ma gidanta ne da hayder." Wata zuciyar ta fada Girki hubby ta daura, ta dawo wurinsu, hira sukeyi cikin natsuwa da yake akwai shakuwa sosai tsakaninta dasu. Asima ta saki jikinta sosai sai ba hubby labarin wanda zata aura take, da irin dan banzan kishinsa, suna dariya. Asiya kam TV ta kurawa ido. Ta fada duniyar tunani. Itafa har yanzu bata cire rai da auren hayder ba. Amma ganin hubby a yanzu ya sanya tsoro a zuciyarta. Mai mace kamar hubby mai zai yi da irinta, ita kanta bata gajiya da kallon hubby koda can, saboda tana burgeta, komai nata masha Allah. Balle yanzu da gaba daya taga ta canza, ta kara kyau jinkin nan kamar auduga sai glowing yakeyi, ko ina ya kara cika, masha Allah. Duk da tasan yadda akayi auren hayder da hubby amma. Tasan koba dade- ba jima zasu dai daita kansu. Balle hubby ba irin matan da zaa iya dauke ido a Kansu bane." Dawowar hubby daga duba girkinta, ta kira sunan Asiya don tun dazu ta lura bata tare dasu. Juyowa tayi ta kalli hubby, sai yanzu hubby ta kara ganin ramarta. " kiyi hakuri, nasan irin son da kikewa hayder. Amma gashi yadda kaddara ta zo mana baki daya. In har kina sonsa har yanzu, pyete for your love, I'm happy to have u hare." Hubby ta fada tana murmushi Gaba dayansu baki sake suke kallonta, da mamaki. Ajiyar zuciya asima tayi " kin san me kike fada kuwa Anty hubby? Kishiya fa kike wa kanki tanadi? Duk da ba auren soyayya kukayi ba, ya kamata kina kishin mijinki, ba ke zaki ba da hanyar shigo miki da wata ba." Murmushi hubby tayi " asima kenan. Bazan yaudari kai na ba, nasan ko ba dade ko ba jima, hayder zai auro zabin zuciyarsa. Zan so ace wadda na sani ce, ba bare ba. Ko ba komai nasan irin son da Asiya ke masa, zanyi farin ciki ace ita ce zabin zuciyarsa." Ajiyar zuciya Asiya tayi " maganar gaskiya bazan iya kishi da keba. Na riga na yanke hukuncin ba daya daga cikin masoyana dama, zan manta da komai, in shafe babin a zuciyata. Dama bawai yasan zancen bane,  a yadda na fuskan ce shima he is not interested about me. So ki rungumi mijinki, ki kula da kayanki. U are very lucky in life, how I wish I was u!." Ta fada tana share hawayenta. Tausayinta sosai ya kama hubby, kusa da ita taje ta zauna,. " kar kiyi saurin fidda rai. Keep trying, I Will help u, like I say before. " ta fada cikin raunin murya. " bazan iya kishi da keba. Nasan hayder ma bazai iya hadaki da kowa ba. Me zai nema ga wata, bayan duk abinda yake bukata kin hada?" Ta fada tana kallon hubby ta kara da cewa " da wata ce, sai inda karfina ya kare!." Hannunta hubby ta kamo cikin nata. suna fuskantar juna "Fahimtar mutane gameda kyau ta bambanta, kamar yanda fahimtarsu a dandano ko kala ya bambanta! A yayinda a fahimtarka farar mace itace kyakykyawa, wani zaka samu Baqace jarumarsa, a yayinda kake son mace mai qiba, wani kuma siririyace zabinsa, ayayinda kake fifita doguwa, wani gajera tafi masa, duk sifar da tafi maka, to zaka samu wani baya sonta! A duk sanda ka samu macenda kake gani duk duniya ba kamarta, baka ganin aibu ko muninta, wani baida abinda ya tsana kamarta! Shin don bata da kyau ne? Ya akai ta maka kyau har ka zabeta, amma wani ya tsaneta yake ganin muninta? Shin to menene kyau?" Shiru tayi tana kallonsu, suma ita suke kallo da nazartar maganarta. Murmushi tayi ta ci gaba da cewa "A tunanina kyau qaryace kawai, tamkar hangen ruwane, ga mai jin kishi. Haka kyau yake gizo a idon masoyi, hakanan muni yake gizo da kawalwalniya a ido da qwaqwalwar maqiyi! A lokuta da dama, duk sanda muka kamu da son abu, zamuga duk duniya babu mai kyawunsa, ba abinda mukeso sama da shi, bamu ganin muni balle laifinsu, amma da zarar mun rabu, sai muga  abun ya koma mummuna abar kushewa, shin kyawun ya barshi ne, kokuwa ta ya sauya kamanni ne, kokuwa Kyau tsuntsune dake sauka akan mutum ya tashi a sanda yaso? A duk wannan tsawon kai kawon, MACE itace mai shan wahala akan kyau, akullum burinta ta gamsar da MAZA cewa ita kyakykyawace, dukda samun yardar mutane abune mai wahala mara yiwuwa, hakan ke kaisu ga shafe shafe (bleaching), feqe feqen haqora, aske gira, qarin gashi, qari/ciko a jikkunansu don cike wata gaba dakeda komada ko tawaya a tunaninsu da sauran salo don kama zukatan maza! Yar-uwa, a sanda kika soma bleaching don ki zama fara, ya zakiyi da mazan da ke son Baqar mace? Kokuwa kinga duk farar mace aureta ake baqa ke kwantai? Ya zakiyi in kika gama bleaching din kuma baki samu masoyi ba? Idan kikaje aka feqe haqorinki don kiyi wushirya, to ya zakiyi da wadanda basuson mai wushirya, kokuma masuson wushiryar su gujeki don ba kalar taki suke so ba? A sanda kikaje kina ta kankare kankare da aske aske da ciko, ya zakiyi da wadanda sukuma duk wadannan abubuwan basuyi musu ba, basu son masu su? Nawane baqaqen mata da kike kallo munana suke dakin mazajensu sunyi aure, nawane matayenda zakiga kaman aje filin tashe dasu don tawaya da muni, amma sun samu mazajen aure, suna dakunansu? Nawane kin fisu kyau da kamun kai, gashi sunyi aure amma ke baki samu miji ba? Yar-uwa ki sani WALLAHI KE KYAKYKYAWACE. Ki yarda da kanki, ki yarda kema mace ce, sai kifi burgeshi fiye da yadda zan burgeshi. "............   [10/03, 13:07] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 24       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Kallonta suke cike da gamsuwa da jawabinta. Hannunta dake cikin na hubby Asiya ta kara rikewa da kyau. murmushi tayi mai karawa fuskarta kyau da kwarjini. Asima zatayi magana Asiya ta dakatar da ita, da alama da hannu. " I agree with every word u say. Amma da gaske nake na hakura, shawara daya zan baki, no matter how the situation is karki kara cewa wata ta auri mijinki, at the end u regret it. Baki san kishiya ba!! My be don baki ganta a gidanku ba. Shiyasa. Mu da muka tashi muka ganta munsan illarta, da alkhairinta. Bana ma kaina fatan ta, in dai ba kaddara ba, wadda baka wuceta. Nasan ko baki son hayder yanzu, na lokaci kadan ne, tun da har kika so Yaya Yusuf, na tabbata in no time zaki samu zuciyarki cikin kaunar hayder. A halitta suna matukar kama, in kin dauke tsayi, da suffar karfi da hayder ya fi Yaya Yusuf. Sai ban bancin ido. Na Yaya Yusuf manya, na hayder madai daita. Sai dimples da Yaya Yusuf bashi dashi. Amma hatta muryarsu, da tafiyarsu kusan iri daya ne. Ta Yaya zaki iya kin son hayder bayan kamman nin da ke akwai tsakaninsa da Yaya Yusuf? Ga kuma jini da kuka hada! Halayyarsu wani zaki iya samu iri daya, wani kuma sabanin hakan. Hayder yana da zafi, sabanin Yaya Yusuf mai sanyin hali. Ki nutsu, ki rungume mijinki, ki rike aurenki. Kar kiba kowacce shegiya shigowa cikin rayuwarku." " abin harda zagi?" Hubby ta fada tana murmushi " baki san yan matan yanzu  bane shi yasa, bamu da dadi ko kadan. In mun shiga kokari muke mu fitar data ciki. Don haka ki rike wuta, ko wannan kodaddiyar kiyi kokarin mantar dashi ita." Dariya sukayi baki daya. " baki da kirki Asiya, Nasrin din ce kodaddiya? Bari ya jiki kina kiran Sweet heart dinsa da kodaddiya" Hubby ta fada tana dariya " ai ba karya nayi ba. Ke na lurama Sam baki kishi, bayan ansan mata da kishi, koda ko basa son abu, sukan nuna kishinsu." Asiya ta fada tana rike baki. Asima dake sauraronsu tana murmushi ta ce " ki barta very soon zakiji Anty hubby ta saka gajeren wando." Dariya sukayi gaba daya. " Allah ya kyauta." Hubby ta fada tana nufan kitchen. " kin san dama duk soyayya mai tsafta daga kiyayya ake farata, mun ji labarin naku mafarin, zamuga how u end up. " Asima ta fada tana dariya Asiya ta kalli Asima tana murmushi " na gode da shawararki uhtee, jhazhakallahu bi jannah." " ba komai, amfanin yan' uwantakan kenan. Muba juna shawarar da zata anfane shi, lokacin da yake cikin matsala. Allah yasa haka shine mafi alkhairi a gareku baki daya. Amma menene anfanin son maso wani?" " koshin wahala kam. Allah ka hadamu da masoyanmu na gaskiya." Asiya ta fada. " Amen uhtee!.." Asima ta fada dai dai lokacin da hubby da Mariya ke shigowa da wormers din abinci. A dinning suka jera komai kafin hubby ta kallesu tana murmushi " bisimillah " Mikewa asima tayi " kamar kin san kamshin abincin nan ya gama cika min hanci, Allah Allah nake a gama. Sam bana juriya yunwa yanzu." Asiya ma bayan Asima tabi suka zauna. Asiya ce tayi serving dinsu. Suna ci suna hira da dariya, gwanin sha'awa. " ban labarin new catch!! " hubby ta fada tana kallon Asiya Murmushi tayi " ba yanzu ba, sai komai yayi normal zakiji." Bata rai hubby tayi. Dariya Asiya tasa " bafa abinda kike tunani bane!! Na fi son sai komai ya dai daita, zanzo da kaina na baki labari, ba sai a waya ba. Nasan kuma zakiji dadi sosai!" Kada kai hubby tayi " Allah ya sa! Ya zaba mafi alkhairi." " Amen." Suka fada baki daya " kira junaid, ya kamata mu leka gidan Yaya Ahmed. " Asima ta fada tana kallon Asiya Tashi tayi, ta nufi jakarta, ta dau waya ta kirashi. " dama shi ya kawoku, amma bai shigo ba?" Hubby ta tambaya " eh! Sauri yake, su hayder na jiransa." Kada kai hubby tayi. Sun gama suka tattara wurin, tare da wanke kayan da sukayi anfani dashi, sunayi suna hira. Dakin hubby suka shiga, don gabatar da sallar la'asar. Sun sakko kenan junaid na sallama daga bakin Kofa. " yasu mommy? " hubby ta tambayi junaid cike da kewar iyayayen nata. " lafiya kalau, dady ne bai ji dadi ba kwana biyu, amma yaji sauki." Cikin damuwa ta ce " amma shine aka rasa wanda zai gayamin?" Murmushi junaid yayi " kiyi hakuri, kin san daddy in bashi da lafiya ba son a fada yake yiba." " duk da haka, ai ni ba bare bace, balle a kasa gayamin." Ta fada cike dajin haushi Ganin ranta ya baci, ya shiga bata hakuri. " it OK, ka gaishesu sai nazo!" Ta fada tana rakosu wurin motarsa. Ledar dake hannunta ta mikawa Asima dake baya. " godiya sukayi mata, junaid yaja motar suka tafi.               ********************* Hayder ta kira, tana son zuwa gida. Bai hanata ba, ya ce ta jirashi, zai zo sai su dawo tare. 5pm ta nufi gidansu cike da jin dadin yau zataga daddy dinta, don sun dade basu haduba sai a waya.              *********************** Ta fito wanka kenan idonta ya sauka a kan wata kyakyakyar traveling bag, pink a kan gadonta. Wurin ta nufa, tare da zage zip din, ajiyar zuciya tayi, don ta dan tsorata, tunda bata san da ita ba. Laffaya less ne masu kama da saree kusan guda 5, sai irin rigunan India da ake hadasu da jeans 3 masu matukar kyau. 2 set na Indian gold, sai Indian fashion, yankunnaye warwaro, besleet, zobuna, Indian perfumes, Sai riga da wando set 2. Murmushi tayi tasan aikin hayder ne, don shine ya dawo daga India kwanan nan. Zip din taja ta rufe ta dauke bag din ta mata wuri a woodruff dinta. Taji dadin kyautar don kayan sun burgeta matuka. Sai da ta gama shirin baccinta tsaf ta nufi dakin hayder. Kamshi mai dadine ya bugi hancinta, ga sanyin AC. Ba kowa a dakin, jikin mirror dinsa ta nufa tana kallon kayan shafansa masu matukar tsada. Idonta ne yakai kan turaren da Nasrin ta masa kyautarsa a Cyprus. Dagawa tayi tana juya kwalbar, tare da zare murfin tana shin shinawa. Da sauri ta zareshi a hancinta. " ouch!!!." Ta fada tana maidashi. Don ji tayi ya balain hawa mata kai, sabanin farkon ganinshi da kamshin ya mata dadi. "What are u doing with my special perfume?" Ya fada yana takowa inda take tsaye, sanye da rigar wanka, fara Sol.  Wai gowa tayi tana kallonsa tare da tabe baki. " turaren da yake wari!" Ta fada a shagwabe Ido ya zaro " turaren nawa ke wari.?" Daga ido tayi tana yamutsa hanci. Hannunsa ya kai ya dau turaren." Kinsan yadda nake sonshi kuwa?" Ya fada yana sashi a kan kirjinshi, dake bude. "Ina son shi sosai." Ya fada yana kashe mata ido daya, Tare da daga mata gira daya. Shiru ta masa tare da daukar wani turaren, Bufewa yayi zai fesa. Da sauri ta kwace a hannunsa. Mika mata hannun yayi ta bashi, ta makale kafada, tare da maida hannnta baya. " ban son warinsa." Ta fada a hankali cikin siririyar muryarta. Hannunsa duka biyu ya daga sama, kamar mai kiran sallah. " sorry!!!! Na manta fah! Yanzu kin zama tabani kaga sarki." Body lotion dinsa ya dauka, hannunta ya kamo ya danka mata. Kallonsa tayi, ta kalli lotion din. Gira ya daga mata ya zauna a chair din mirror. Murmushi tayi ta fara shafa mishi, cike da natsuwa, Lumshe ido. Mikewa yayi tare da  rungumota ta baya, ji numfashin shi na sauka kan wuyanta, tana juyawa kaman predator ya Kama bakinta da nashi bakin,  idanu hubby ta lumshe. hannunshi biyu yasa ya riko waist dinta tare da danneta da kirjinshi giving the access of her chest pressing he's chest then he's hand on her well shaped hips,  hannu biyu tasa ta zagaye west dinsa dasu.  baya baya ya dingayi har saida ya kai bakin gadonsa ya zauna, ya Kama bakinta gan kaman cikin nasa ba tare da ya Saketa ba,  he was pushing he's tongue deep that jikinta ya saki  bayan kanta ya rike da hannu daya sannan ya dora dayan hannu kan chest dinta not massag dinsu a hankali, cikin kwarewa. kaman ya samu sweet haka ya dinga shan bakinta, sakin bakinta yayi, ya zare bakinshi, cikin nata,  idanuwansu cikin na juna,   wani kiss ya Dan dora a kan lips dinta. A shagwabe hubby tace " please hayder let me sleep, jikina ba karfi." A kunnenta ya rada mata cikin husky voice dinsa.  " bari in baki maganin karin karfi, da kuzari." Kafada ta makale. " please mana!!!" Shima kwaikwayon muryarta da yadda tayi maganar yayi " please habiba.!!!!" Dan harararsa tayi " banson habiban nan, ka kuma san haka!." Hancinta ya lakace " I call u Habiba because it your name. " " call me Ummi kamar yadda su mommy ke kirana, in bazaka kirani da hubby ba." Ta fada Smacking yayi, " nafi jin dadin Habiba." Duka ta kai masa a kirji " ka gama rainani completely! Koda yake ba laifinka bane." Gira ya daga mata " who's fault? " tura baki tayi, cikin shagwaba " it's my fault." Still fuskarsa na dauke da smacking " u amazed me some time,!" Ya fada yana kara rungumeta a jikinsa. Ido ta lumshe cike da  kunya ta fara shafa sajensa daya kwanta gwanin shaawa. Ganin hakan ya kara lafewa cikin jikinta, ya fara aika mata da samun ninsa masu wuyar fassaruwa. Gaba daya kowa na kokarin faranta ran daya, na dogon lokaci, kafin suka sararawa juna, bayan kowan nensu ya samu cikakken gamsuwa. A kunnenta ya rada mata "Allah ya miki albarka, Rabbi ya cika miki rayuwarki da farin ciki." Lafewa tayi a kan faffadan kirjinsa, tanajin bugun zuciyarsa na harbawa kan nata, a haka suka dau lokaci kafin suka mike don tsarkake jikinsu. Daukanta yayi bridal style zuwa toilet din. A toilet dinma sun dade suna romancing juna, kafin sukayi wanka suka fito. Kwanciya tayi tana " wash Allah nah!!". Tana yamutsa fuska da tura baki. " wayyo jikina duk ciwo yake." Ya fada yana kwaikwayon maganarta, yana rike baya. Harararsa tayi, ta dau filo ta wurgeshi dashi. Chabewa yayi ya jefa mata kan fuskarta " lazy Bone's. " ya fada yana saka kayan baccinsa. Kwafa tayi " zaka dawo ne." Ta fada cikin dan jin haushin lazy Bone's din daya kirata dashi. Kunnensa duka biyu ya rike " afwan!!! Amin ko wanne horo amma banda wannan!! " yana murmushin gefen baki. " zaka ga lazy ganin idonka." Ta fada tana kara gyara kwanciyarta. Kusa da ita yazo ya kwanta, tare da janyota jikinsa. " I say I'm sorry ko.?" Kirjinshi ta fara shafawa a hankali. " naga kaya a bedroom dina?" Kiss ya manna mata a goshi," its for u" " na gode, Allah ya saka da alkhairi. " ta fada still tana shafa kirjinsa a hankali. Yaji dadin adduarta sosai. Mannata ya karayi a jikinsa, kafin sukayi adduar bacci,. A haka suna dan wasa da juna har bacci ya kwashesu.            ********************** Sun gama break fast, hayder ya mikawa hubby ticket. Amsa tayi tana dubawa, Dagowa tayi ta kalleshi. Yana jingine jikin kujera yana shafa sajensa. Fuskarsa dauke da smacking. Hade fuska hubby tayi, " no way?" Ta fada tana mikewa........... Kallonta yakeyi fuskarsa dauke da smacking, Ticket din ta ajiye a gabansa. Tare da zuba masa harara, baki ya tabe ya dauki ticket din yana kara dubawa. " gobe zamu tafi, pack your bag and get ready." Ya fada in husky voice dinsa " sai ka dawo!! Ba inda zani." Ta fada tana tura baki. " kar muyi haka dake! Kefa kika ban wannan shawarar to meye laifi don kin tayani na gyara kuskiren da kike ganin nayi?" " Allah kama gama rainamin hankali. Gotai gotai dani, zan rakaka zance? Bama a nan ba har Egypt, saboda bani da aikin yi? Ko ce maka akayi cewa tayi inje na gani?" Murmushi yayi mai sauti, " we shall see to it." mikewa yayi ya dau ticket dinsa, sama ya haura cikin gudu -gudu, sauri -sauri. Da harara ta rakashi, kafin tayi kwafa.                ******************* Yau gaba daya gidan bai mata dadi ba, daga ita sai Mariya, yau ko bakin ma da suka saba zuwa yau babu. Hayder kam tunda ya fita da safe har zuwa lokacin to 5 bai shigo ba. Dole haka hubby ta sallami Mariya ta tafi gida, don lokacin tafiyarta yayi. Tana kwance a kan sallayarta data idar da sallar isha'i. Tunani ne fal zuciyarta na rayuwa, sai lokacin ta fara tunanin magan ganun Asiya. Tabbas gaskiya ta fada mata. Don tasan ada ba wacce tafita kin kishiya. Tunowa da kishinta kan Yusuf, wanda ko kallon mace wadda ba muharramarsa ba, bata kauna taga yayi, balle magana. Yan matansa na family da wanda ta sani, gaba daya bata Shiga shirginsu, bata basu fuskama balle su kawo mata wargi. Tsaki taja, tunowa da yadda hayder ya dage maganar zuwa Egypt. Ita bawai kishin Nasrin takeyi ba, don tare ta gansu. Amma ta yaya don ya raina mata wayau, wadda bata san abinda  takeyi ba, ta rakashi zance. Ita a tarihima bata taba ganin inda mata take raka miji zance ba, ba kuma zaa fara a kanta ba. Lokaci yayi da zata kama mutuncinta. Tabbas ko bata sonsa, mijinta ne, uban yayanta. Duk wadda zai auro, ko tanason ko bata so, dole ya shafeta, ya kumayi tasiri a rayuwarta data yaranta. Sai ma tafi tasiri a kanta sama da yadda zatayi akansa shida ya aurota. Ya zama wajibinta ta sa su a adduarta, in alkhairi ne shigowarta rayuwarsu Allah ya tabbatar in ba alkhairi Allah ya masu canji na alkhairi. Cikinta ta shafo, da har lokacin ba alamar tasowarsa, sai tauri da wurin yayi. Wani dadi da natsuwa taji suna ratsata for the fist time. Tunowa da yadda Yusuf ya kwallafa ransa don ganin kwansa, A duniya. Kana naka Allah na nashi.wane irin farin ciki zaiyi in da ta samu ciki dashi? Wane irin so da tattali zata gani? Ta tabbata ko sarauniyar England bazata fita samun kulawa da tattaliba. Hakika soyayya wani jigone, a rayuwar aure, duk auren da babu soyayya, dole zaka samu akwai tawaya a tattare dashi. Duk jin dadi da kulawar dake cikinsa. Yanzu take jin son cikin jikinta, koba komai ta samu abunda zai sata farin ciki, da debe kewar masoyinta. Allah yasa namiji zata Haifa, ta nemi alfarmar koda hayder beyi niyya ba, yasa mata sunan masoyinta, balle a yadda shakuwar dake tsakaninsu ta San zai yi wuya ya kasa sa sunan." Kuka sosai yazo mata,. Bataji shigowarsa ba, sai kamshin turarensa. A hankali ya tako zuwa inda take kwance saman daddumar sallah tana kuka, don gaba daya zuciyarta ta karye. Zama yayi kan lallausan carpet din dakin, tare da daddagota, ya daurata a kan cinyarsa, yana tare da rungumota jikinsa. Kara shigewa jikinsa tayi. A hankali ya dinga lallashinta, cike dajin tausayinta. Ajiyar zuciya ta dinga saukewa tana lafe a jikinsa. Sai da ya tabbatar ta samu natsuwa tukun. " are u OK." Ya fada cike da kulawa. Kai ta kada masa. Dagata yayi suka shiga toilet. Dayake shigowarsa kenan yaji zuciyarsa ta kasa natsuwa, yayi dakinta, sabanin da da bedroom dinsa direct yake wucewa. A tare sukayi wanka, shiya taimaka mata ta shirya cikin kayan baccinta, masu kyau da laushi. Dakinsa ya wuce daure da towel dinta don ya shirya. Kitchen ya nufa don samawa cikinsa wani Abu don yunwa yakeji. Da yake bata cika ajiye masa abincin dare ba, saboda baya dawowa dawuri, in ma ya dawo baya bin takan abinci. Sau da yawa a main house yake cin abincin darensa, kafin ya wuce daukan karatu. Dakinta ya nufa da trey dinsa. Tana kwance a kan bed, still fuskarta akwai damuwa, da rashin walwala. Kujera ya jawo ya daura trey din a kai, ya zauna kusa da ita. chicken salad, sai natural fruits juice, Kallonta yayi, da yanayin data kasa fassarashi. Dagota yayi, ta zauna sosai, salad din ya diba, yakai bakinta. Kauda kanta tayi, tare da kada masa kai. Murmushin gefen baki yayi " ki ci, basai kin biya ba, tunda da kaina na baki." Kada kai tayi " na koshi." Ta fada " na dauka tsoro kikeji, kar ince sai kin biyani." Ya fada still da murmushi a fuskarsa. " da can ma da naci ban biya ba, balle yanzu!! In ina so ci zanyi, ba yadda ka iya dani." Ta fada tana gyara kwanciyarta. " kin dai manta, anma ba abincina da kikaci da baki biya ba." Ya fada yana cin salad din. " sai ka tunamin ai!!" " na school, kin biya da chocolate da sweet dinki. Food dinki dana friends dinki." Ya fada yana daga mata gira daya " right. ". Harararsa tayi. " ka biyani chocolate dina ai!! Tunda gasu nan a kitchen sai wanda nakeso in sha." Ta fada tana murmushi " kifina da kika ci, da chips, suma kin biya With high price. " ya fada yana smacking " ni ban biya ba! In don girkin da nake maka ne, bawai don in biyaka nakeyi ba malan." Ta fada cikin shagwabarta " really!!!! Ke adole kin dauka bulus kika ci? I keep it they intentionally. Its a trap!" Ya fada Tashi tayi ta zauna, Kallonsa take tana mamakin maganarsa. " why do u say that?" Ta fada tana rike habarta tare da daga masa gira duka biyu. Sagensa ya shafa yana Kallonta, smacking yayi " Allah ne ya soki, da mage ta koromin ke!! Amma da trap dina ya kamaki?" Kada kai yayi tare da hadiye sauran maganar yana dari ya kasa -kasa. Ido ta zaro cike da mamakin maganarsa. " hayder wane muguntar ka shirya min?" Ta fada tana tsareshi da ido. Tabe baki yayi " ki dauka dama kazar da kowanne ango ke kaiwa amaryasa ranar da zai tare da ita, Kikaci. Koda mage bata koroki ba, nayi niyyar amsar hakkina a ranar, Your under my plan, Allah ya kwaceki. Kika kawo kanki cikin salama." Rasa abinda zatace masa tayi, har ya gama ya fita da kayan binsatake da kallo. Dakinsa ya wuce, ya tsaftace bakinsa tare da kara fesa turare, na baki dana jiki. Ya nufi dakinta. Har lokacin tana inda ya barta. " please hayder me ka shirya yimin a ranar?" Ta fada " forget about it," ya fada yana yarfe hannu daya. "Amma kace ba kai ka turo min mage ba?" " yes!"" Ya fada yana kallon kwayar idonta. " ki gode ma Allah magen taimakonki tayi." Ya fada yana kwanciya kusa da ita. Hannu yasa zai rungumota ta bige hannun. " uchh!!! " ya fada yana yarfe hannu. " don't u dare touch me, again." Ta fada cikin fushi. " OK." Ya fada yana smacking tare da gyara kwanciyarsa sosai, kanshi na kallon sama, hannayensa duka biyu a hade kansa na tsakiyarsu. Kallonsa tayi, tana jin kamar ta mari fuskarsa, saboda haushin murmushi rainin hankalin dake kan fuskarsa. Kwanciya tayi ta juya masa baya. "Amma kinsan ba kyau juyawa miji baya ko?" Ya fada in husky voice banza tayi dashi. Tafiyar tsutsa ya fara mata a bayan. Hannunta tasa ta buge hannun again. " gobe flight din  rana zamubi ki tabbatar kin shirya kafin 11, don ta abuja zamubi. " sau nawa zan gaya maka, bazan jeba." " yes u tell me. But look!!! Bana son gardama do as i say." Ya fada in high tone. Shiru tayi, tana jin hawaye na kara cika mata idonta. " kar dai maganar tafiyan ce ta saki kuka dazu?" Ya fada still in high tone "Na tuno da masoyina ne, mai son farin cikina." Ta fada cike da takaici. " good for u!! Amma ki Sani kin aikata haram, da aurenki, kike tunani fast love life Dinki?" Ya fada in his husky voice " har kanada bakin da zaka fadi haka? Kai yanzu abinda kake shirinyi, a ina ka taba ganin anyi haka? Ina matarka ka rasa wanda zai rakaka neman aure sai ni? A ina ka taba jin anyi haka?" Ta fada still tana kallon gefe, ba tare data juyo ba. " its not a big deal!! Zaa fara a kanmu." " sai ka nemo Janeway ka jani ai!!!" Ta fada " no need for that, da kafarki biyu zamu tafi. A u jealous of her ? " " never." Ta fada "U love me, bakya son ganina da wata, zuciyarki zata buga, bazata iya dauka ba. Is that your reason?" Juyowa tayi tana harararsa " Allah ya kiyaye, in tsaya ina kishinka! Kawai I don't want to go with u." Tabe baki yayi, yana Kallonta. Murmushi ne ya kufce masa ganin yadda ta daure fuska, wai ita ranta ya baci. " just sleep! I don't want your trouble, bayan ina cikin farin cikin ganin sweet heart tomorrow. " Ya fada yana jawota jikinsa, tare da lushe idonsa. Kokari take ta kwace daga jikinsa ta kasa, dole ta hakura. Hannunsa na kan cikinta yana shafawa a hankali, har bacci yayi awan gaba dasu.              ********************* Duk yadda hubby taso kaucewa binsa Egypt abin ya ki yiyuwa. Hayder akwai naci da tsayawa kan maganarsa. Dole tana ji tana gani suka nufi Abuja daga nan jirginsu ya daga zuwa Egypt. Su mommy Hauwa sai a waya ta musu sallama, don daga gidan Hajiya direct suka wuce abuja. Da mamakin hubby tunda suka isa Egypt, yana tare da ita, in basa room dinsu a hotel din da suka sauka, to sun fita ganin wuraren tarihine, ko shopping. Shiru shiru taji ya mata maganar zuwa wurin nasrin taji shiru. Har ta kasa yin shiru, ta tambayeshi. Bai ce mata komai ba, in banda murmushi da yayi mata, ya share zancen Iya murzuwa hubby ta murzu a wurin hayder cikin kwanaki 14 da sukayi. In ka gansu gwanin shaawa baka taba cewa ba soyayya a tsakaninsu. Don wani kulawa da tattali suke ba juna na musamman. Satinsu biyu suka tattaro zuwa kasa Nigeria, kowa yabar gida - gida ta barshi. A dade anayi sai naija...........  [12/03, 12:42] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 27       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Da sauri ta kammala wankan ta fito, saboda amatullah data tashi taketa tsandara kuka. Da sauri ta dauketa tana jijjigata, kafin ta zauna a bakin gadon, ta fara shayar da ita, saboda kin shirun da tayi. Dakyar ta samu ta kama, tana Jan ajiyar zuciya. Hubby ma ajiyar zuciya taja, Tana shafa kanta. " sorry habty." Ta fada tana mata kiss a goshi Tsaye yake a bakin kofar, kwata kwata hubby bata san da shigowarsa ba, saboda yadda amatullah ta rikitata. A hankali ya tako zuwa inda suke cike da tsantsar son iyalan nasa. Zama yayi kusa da ita. " sabahul khair. " da sauri ta dago. Tattausan Murmushi  ta sake masa, cike dajin kunya da nauyinsa. " sorry banji shigowarka ba, Barka da safiya?" Ta fada cike da shagwaba Yana rike da kafar yana dan wasa da ita. amatullah da taketa wuntsilata a hankali. " princess dina ta iya rigima ashe?"  " lokacin tashinta yayi, ni kuma na shiga wanka." " shine baki jirani, muyi tare ba." Ya fada yana daga mata gira. " I think zaka wuce karatu, daga sallar asubah." Ta fada " waya gaya miki karatu nake zuwa?" Ya tambaya yana mikewa " a bakin Hajiya naji." Ta fada tana tsare shi da ido Smirk yayi, " bari inyi taking shower tunda anki jirana!! Ko in bari a sallami princess tukun aji dani." Ya fada yana kashe mata ido " in hakan ya maka!" Ta fada a takaice Har ya isa kofar toilet din, ya juyo " next month zamu tafi!! So ki fara shiri ." Shagwabe fuska tayi " ya maganar ziyarar kankiya, kano, abuja da na maka?" " zamuje amma tare!!" Ya fada yana shigewa cikin toilet din Ba haka taso ba, amma ba yadda ta iya, karta matsa ya hanata gaba daya, don yanzun ma saida Hajiya tasa baki tukun. Cikin wata dayan da sukayi, sun yishine cikin ziyarar yan' wa da abokan arziki. Ta gefe daya kuma suna cin amarcinsu.                    ******************* Kallon hubby Aisha tayi, ta kalli beby Amatullah. Ta kwashe da dariya, harda rike ciki. Kwafa hubby tayi, tana Jan dogon tsaki " ba laifinki bane, laifinane dana zo gidanki, kika samu damar min iskanci. " " sorry. " Aisha ta fada tana toshe baki Rungume Amatullah tayi a jikinta, tana jin son yarinyar a ranta, tare da tunowa da yaya Yusuf, da yanzu wannan kyakyawar yarinyar tashi ce? Rayuwa kenan? Wani baya haihuwar wani. " yanzu wannan kyakyawar bebyn taki da hayder ko." Harararta hubby tayi " bari in zo in bar miki gidanki, ina gadai kora da hali kike so kiyi min." " Allah ba haka bane Anty hubby!!! Kawai ina jin jina abun ne, in na tuna rayuwar secondary sch. Da yadda muamalarki da hayder take, cika bakin ki lokacin aurenku. Sai inga abin kamar almara, Jiya muka gama hirarku da humaira." " kice jiya muka gama gulmarku da humaira. " hubby ta ce " ba gulma bace wallahi. " ta fada " kun kyauta. Allah ya shiryeku." Hubby ta fada tana murmushi " muna labarin aurenta ne, shine zancen naki ya shigo, kin san itama iyayenta sun nace sai ta auri cousin dinta! Ita kuma akwai wanda takeso. Shine nake bata shawarar tayi hakuri ta bi maganar iyayenta, ta musu biyayya, kamar yadda kikayi, ke dama a lokacin kinada damar zabawa kanki abinda kike so, amma kika daure kikayi biyayya.  gashi tun baaje ko ina ba kin fara ganin alkhairi a rayuwarki." " nima dazu abinda na gaya mata kenan da mukayi waya." Hubby ta fada " dama tace zata kiraki, bata samu ta miki tsiya ranar suna ba, saboda jamaa, gashi tun daga lokacin baku haduba." " bar yar banzar yarinya. Naso ganinta kafin mu wuce, but wuraren ziyarar suna da yawa, ba isashshen time. " " haka ne, Allah yasa kin yiwa kanki dabara." Aisha ta fada tana murmushi Cikin rashin fahimta hubby ke kallonta. " dabara wace iri?" " kefa matsalata dake bakya saurin kawo wuta. Planning nake magana! Don't tell me bakije kinyi ba, kafin ki koma.?" Mararraice fuska hubby tayi " wallahi na manta, kwata kwata munyi maganar dake, yanzu meye abinyi?" "Yanzu kam sai dai in kun isa, sai kuje kiyi, in baki kunshi wani ba. Don naga alama hayder ba wasa." Aisha ta fada tana dariya Harara hubby ta jefa mata " bakinki ya sari guntun kashinki. Amma fah ina tsoron masa maganar, don ban san yadda zai dauketa ba." " haba!!! Kamar ba mace ba? Kalallameshi zakiyi, tuni zai amince, tunda duka saukin kune, kodon Ku samu natsuwar karatu nasan bazai kiba. Namayi mamamkin da bai miki maganar ba shi da kansa." Numfashi hubby taja " bazaki gane son yara irin na Hayder ba? Shi yasa nake tsoron masa maganar, a gefe daya kuma, ina tsoron daukar wani cikin." Dariya Aisha tayi sosai tana nuna hubby da yatsa " ke kike tsoron hayder!!! Wayyo!!! Duniya juyi juyi " Tabe baki hubby tayi " ya zanyi? Tunda Allah ne ya bashi girman dole na hakura na sadakar." " good for u!!! Kina burgeni!! Har ga Allah ina son halayyarki. So da yawa na kanji inama nice ke! Tabbas gwaggo ta ciri tuta. Dauraki a kan tafarki na gaskiya, Da jajir cewa wurin biyayyar aure. Shi yasa har gobe Mmn Yusuf na bakin cikin saken da tayi, na rashin yadda ki auri Abdul fatta. Gashi wadda ta zaba Masan baaje ko ina ba, kullun matsalar yau daban ta gobe daban. Yanzu haka tana Niger wai tayi yaji! Shi kuma yace wallahi bazai bar aikinsa yaje bikonta ba, sanda taga dama ta dawo dan kanta. Mmn Yusuf data kira yayantan a waya don ta basu hakuri, in kinji masifa da bakaken magan ganu, karema bazai Ciba. Harda gorin shi yarikesu tsawon shekaru, amma yarsa daya sun gagara rike masa. Alhalin sun san itace Mara gaskiyan. Har yaushe miji baya gari zaki dinga tara masa kartin banza, dasunan makotaka? Mu kanmu ranar da mukaje ganin daki, baya kasar matasa da yan mata sun kai shida muka samu a falonta sun baje bamai suturar arziki a cikinsu, har gara ita da Arabian dress a jikinta. Sun baje kayan abinci dana sha, ga kida kamar a club. Muda mukaje da niyyar kwana uku, kwana daya mukayi, sai gidan uncle omer muka karasa sauran kwanakin. Hakan ma wai yar uwarmu, da muka hada jini. Abin Sam ba dadi, ni kaina banso hadin ba, amma ba yadda ka iya." Kasa cewa komai hubby tayi, sai kada kai, tana godewa Allah da bata sake fadawa cikinsu ba. Don bazata taba manta izaya, da cin mutunci da tozarcin da suka mata ba. Da sunan bata haihuba. Gashi cikin ikon Allah ko bantaren magani bata sha ba, Allah ya bata nata rabon. Haka Allah ya kaddara bazata haihu da Yusuf ba, haka zai koma ga Allah ba tare daya ajiye kwansa a duniya ba, hakan na cikin kaddararsa da suka kasa ganewa, suka dauki karan tsana suka daura mata a lokacin. " Allah ya kyauta. " ta fada tana mikewa don gabatar da sallar la'asar la'asar, kafin hayder ya karaso.                 ****************** Yau su hubby suka iso kasar Cyprus, lefkosia town. A kusa da school din apartment din da zasu zauna yake, mallakin don Harris. 3bedrooms with toilets 1 falo with toilet, sai kitchen. Allah ya taimaki hubby mahaifiyar Mariya ta amince ta taho da ita, da sharadin sata a school. Hakan yama hubby dadi, don ta saba da ita, yarinyar ta iya aiki, ga son yara, bata da matsala ko kadan, sai dan rawar kai, wanda hubby bata daukeshi komai ba. Cikin sati daya suka kammala, duk wani shirye shiryen fara karatu. Haka ta bangaren bukatu na gida. A kusa dasu suka sama ma Mariya day school. Amatullah sun mata register da day care,dake cikin school din. inda hubby zata dinga ajiyeta kafin ta fito lectures, Mariya kuma tunda tana rigasu dawowa, zata kula da tsaftar gida da sauran aikace- aikace. Alhamdulillah hubby kam at first tasha matukar wahala, kafin komai ya dai daita. Hayder na matukar kokarin ware lokaci na musamman don kara fahimtar da ita abunda bata gane ba, duk da dunbin nashi karatun da business dake kansa. Yau watansu hubby uku a Cyprus. Tana kwance a falo, tana nazarin wani assignment da aka basu. Mariya da amatullah suna garden ta korasu don ta samu cikakken natsuwa. Kamshin turarensa ya tabbatar mata da dawowarsa, kafin sallamarsa ya shigo. Ya kara kyau da budewa, sanye yake da Jens blue da Shir gashin kansa da kyakyawan sajensa sai daukar ido suke. Da sauri ta tashi tare da taryansa. Dagata yayi yana juyi da ita, kafin ya sauketa suna dariya. " Allah matarnan kin kara nauyi sosai, meye sirrin ne? Don na lura nan da dan lokaci kadan dau kanki zai gagareni." Ya fada yana dukawa alamar gajiya. Bayansa take kokarin danewa tana dariya " kato dakai ka kasa dagani? Ai da kaji kunya wallahi." Ganin da gaske bayan zata hau yasa yayi ciki da gudu. "Allah bazan yadda ki karyamin baya a banza ba." Da gudu ta bishi, suka fara zagaye falon. Da ta kasa kamashi ta tsaya tana maida numfashi. Dariya ya fada mata shagwabe fuska tayi. " zamu hadu, Allah bazan yadda ba, sai ka goyani." " Rikicinki yafi na princess kwanan nan, ban kara goyaki." Ya fada yana smirk "Kwantar da hankalinka, lokacin da zaka goyani ma, ba wanda ya sani. Ta fada tana mayar masa da smirk dinsa Shafa kai yayi. Tare da karasowa inda take, dukawa yayi " oya!! hau." Murmushin mugunta ta masa " aa na fasa." Ta fada tana makale kafada. " Allah sai kin hau! Don bazan yadda kimin mugunta ba." Ya fada in husky voice dinsa Dariya tayi " ba yanzu ba, in my right time. " ta nufi kitchen don hada masa lunch. Yana kallonta harta shige, ya shafa sajensa yana smirk Books dinta ya dauka yana dubawa. Yaji dadin yadda take forming yanzu. Har ta gama hada dinning din, yana nazarin takardun. " wanka zaka fara, ko abinci?" Ta tambaya cike da kulawa Dagata yayi bridal style zuwa bedroom dinsa. Toilet ya wuce dasu, a tare sukayi wanka, bayan sun sha romance dinsu, suka fito, a shiririce suka shirya, suka fito dining. " ware is my princess, tunda na dawo banji motsinta ba.?" Dagowa tayi daga zuba masa abincin. " suna garden." Ta fada a takaice " jeki dauko min ita, I want to see her." Ya fada in husky voice Tura baki tayi, " ka gama cin abinci tukun." " no!" Ya fada in serious tone Tabe baki tayi tare da nufar kofar da zata sadata da garden din. Masha Allah, Amatullah ta yi wayau abinta. A zaune na ganta kan wani tattausan carpet ga kayan wasa baja- baja a gabanta, sai zillo da tsalle take daga zaune, tana dauko wancan tayar ta dauko wancan. Tasha riga da wando na blouse pink masu matukar kyau. Kanta an mata kakaba kanana dayasha molti color ribbons gashin har kafadunta baki wulik dashi. Mariya ce ta dauketa, ta kaiwa hubby dake tsaye dan nesa dasu, kafin ta dawo tana tattara kayan. Amatullah tana arba da hayder ta fara tsalle tana mika hannu ya dauketa, sai wangale masa baki take. Da sauri ya mike ya amsheta tare da cillata sama, yana dariya, itama dariyar take harda kyakyatawa. Ya Rungumeta yana " miss u my princess. " ya manna mata kiss a kumatunta. Hubby na tsaye tana kallonsu cike dajin dadi, inda sabo ta saba da hidimar hayder da amatullah. Bayan ya gama lunch, shiya taimaka mata tayi assignment dinta. Yana zaune kanta akan cinyarsa, yana shafa sumar kanta, kamar mai massage. Ta kalleshi cike da shagwaba " ya maganar da mukayi dakai jiya?" Kallonta yayi, ya tabe baki, sai da yaja fasali tare da sauke ajiyar zuciya " tun yaushe muka gama wannan maganar? Bana son kina taso da ita kuma." " please hayder!! Its just a matter of 2years." Ta fada cikin muryar ban tausayi " tun ba yauba na gaya miki, bana sha'awar family planing a rayuwata, koda duk shekara zaki haifamin, ina son kayana. So stop bringing the subject again and again." Ya fada Tashi hubby tayi ta zauna, ta kamo hannunsa, tana murzawa cikin nata a hankali. " kai kanka kaga irin wuyar da akesha!! Amma shine kake min fatan duk shekara? Saboda badaga jikinka zasu tsago su gito ba shiyasa zaka fadi haka. " ta fada cike da damuwa Harara ya zuba mata " duk abinda zaki ce, ni dai ina nan kan bakana. Ki gode Allah wani da kudi yake so bai samu ba, so in Allah ya baki ki amsa da hannu biyu ki gode masa. Har nawa kika haifa da kike maganar planning? In ke bazaki iya rainonsu ba, ina da inda ake maraba dasu. Wannan ya zama na karshe da zaki sake zuwa min da maganar family planing a gidan nan." Ya mike cike da bacin rai ya fita. Kanta ta daura akan hannun kujera, sai kuka. Ta rasa dalilin da yasa ya kasa fahimtarta. Yanzu haka a tsarge take da kanta, saboda wasu alamu data kasa tantan cewa,. Yanzu ta sake daukar ciki, yazatayi da amatullah? Ta gefe daya kuma karatunta. Ta bashi tausayi, amma baya jin xai yadda da kudirinta, Yana son yara. Zama yayi kusa da ita, tare da rungumota jikinsa. Cikin lokaci kadan ya lallashi abunsa. " shirya min Amatullah zamu FIta." Ya fada in husky voice " kai da ita kawai." Ta tambaya cike da rauni. Kai ya daga mata. A sanyaye ta nufi dakinta, ta hada dan bag dinta, da duk abinda zai bukata. Kafin ta kira Mariya ta kawo mata ita, ta shiryata cikin pink din roll-on.  Har mota ta rakasu ta dawo. Gidan suka sake gyarawa, tare da baza turaren wuta bayan sun kammala dinner. Ta idar da sallar magrib tana azhkar ta tuna da sauran p- test dinta da tazo dashi. Da sauri ta mike, ta fara duba inda take tunanin ta ajiye. Hamdala tayi data ganshi. Ta nufi toilet gabanta na dukan tara - tara. Safa da marwa take tayi, tana fanan kallon agogo jefi -jefi, tare da Jan tsaki. Falo ta dawo  kamar ance ta  daga labulen da zata iya hango compound din gidan. Gabanta ne yayi mugun faduwa...........Hayder ne a saman mota, kafafunsa na dan sarke da juna, sai waya a hannunsa. A gefensa Nasrin ce dauke da Amatullah tana jingine jikin motar, da alama hirar ta musu dadi, don daga inda take tana iya hango hakoran Nasrin dake waje, alamar dariya take. Shi kuma fuskarsa na dauke da lallausan murmushi daya fito da kyawawan dimples dinsa. Kasa jure kallonsu tayi, daboda zuciyarta da takejin yana bugawa kamar zai faso kirjinta. Duk iya yadda taso daurewa kasawa tayi, ta saki wani kuka, mai cike da kunar zuciya. Dakinta ta wuce har bata ganin gabanta sosai, saboda damuwa da bacin rai, Wannan shi ake kira abu goma da ashirin. Tana kukan targade ga karaya tazo. Sai da taci kukanta ta koshi, sannan ta nufi toilet ta wanke idonta. Agogo ta kalla to 11, amma har lokacin bai shigo gidan ba. Kwanciya tayi. Tunanin Yusuf ne, ya dawo sabo dal a zuciyarta duk yadda taso kauda tunanin ta gagara. Zuciyarta ta fara ba hakuri, tunda abunda ta dade da sanine, ko ba dade ko ba jima, dole sai hakan ta faru. The early the better. Allah ya bata ikon danne kishinta, yasa tafi karfin zuciyarta. Motsinsa da kamshin turarensa shiya shaida mata isowarsa. Da sauri ta rufe idonta, tare da gyara kwanciyarta kamar mai baccin gaske. Kusa da ita ya kwantar da Amatullah, ya manna mata kiss a goshi,. Shafa fuskar hubby yayi a hankali, tare da kai bakinsa kan nata, ya nata kiss. Sannan ya fita a dakin. Jin fitarsa ta bude idonta. Tana kallon Amatullah daketa baccinta hankali kwance. Kofarta ta murzawa key, ta dawo tai kwanciyarta. Don gaba daya ta tsinci kanta dajin haushinsa., ta wani gefe kuma tana ganin bata yi masa adalci ba. Hayder yasha mamakin jin kofarta a rufe, abinda bai taba faruwa ba, tun bayan shiryawarsu. Juyawa yayi ya koma dakinsa, kasan cewar yasan basu kadai bane a gidan balle ya tsaya yana buga mata Kofa. Iya tunanin abinda zai sa ta masa hakan, yayi amma ya kasa, maganar family planing ce ta dawo masa, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Allah yasa ba har yanzu tana kan bakanta ba, shiyasa ta zabi wannan hanyar don ta tursasashi ya mata abinda takeso. In ba wannan ba baiga dalilin da zai sa ta masa hakan ba. Gashi a bukace yake da ita, sosai. Wayarsa ya dauko ya fara  trying number dinta, swhech up!! Tsaki yaja yafi kwando dubu. Dakyar ya samu bacci ya daukeshi. Don ta riga ta gama saba masa da bacci a jikinsa. Ga bukatuwa dake tare dashi. Ta bangaren hubby kam, baccin ma kin zuwa yayi. Yanzu ne lokacin da zata kara kaimi wurin mallake zuciyar mijinta, ta hanyar data dace. don samowa kanta mafita, da saukin zama a cikinsu, in ba hakaba tana ji tana gani zata zama yar kallo, ko machine for producing children. Lokaci yayi da zata kara maida hankalinta kan karatunta, don tallafawa rayuwarta dana yaranta. Ko batayi don kanta ba, yanzu dole tayi don yaranta, kafin a dauko mata kishiyar da ta fita ilmi da wayewa. Yanzu ne ta fara ganin wautarta da tun tuni bata farga da hakan ba. Allah ma ya taimaketa kafin Nasrin ta shigo ta yi nisa, a nata karatun. Cikinta ta fara shafawa a hankali, tana hawaye, ikon Allah yanzu wata halittarce kwance a ciki, ba tare da ta farga ba. Ya makomar Amatullah yanzu? Ci gaba da shayar da ita zatayi, ko yayeta zatayi? Dole ta nemi shawarar doctor but how? Bata son kowa yasan da cikin, har sai ta tabbatar dashi, da kuma watanninsa. Kallon Amatullah dake ta baccinta hankali kwance tayi cike da tausayin yarinyar, tare da tausayin kanta. Tama gode Allah da ba wani laulayi na tada hankali take yiba, da ya zatayi da karatunta?. A gogo ta kalla 2:14am  sai lokacin Amatullah ta farka ta fara kukan neman abincinta. Daukarta tayi, ta shayar da ita, tare da sata a kafadarta tana jijjigata har bacci ya sake gaba da ita. Alwala ta dauro, ta kabbara nafila. 3 am dai dai hayder ya farka, alwala shima ya dauro, ya fara jera nashi nafilfilin, kamar yadda suka saba, duk dare. Yaso zuwa ya tasheta, amma baya son Mariya ta jishi yana buga kofa, ba mutuncin su bane, don haka ya share ta.                 ******************** Sai 7:23 ta fito daga dakinta, sanye cikin wata maron Arabian gown, mai adon gold stones and bits. Rigar ta bude sosai da wadataccen mayafinta. Amatullah ma tana sanye da riga da wando masu matukar kyau yellow and White, ta mata fakin din gashinta, ta daura mata hular kayan tafito a balarabiyanta sak, Sai kamshin sukeyi daga ita har hubby. Already Mariya ta tafi school, don 7 school bus dinsu ke zuwa daukanta, so in ta tashi sallar asuhah bata komawa, zata rage ayyukan gidan, kafin ta nemawa kanta abinda zataci, sannan ta shirya ta tafi. A school ake basu lunch. Kitchen ta nufa, don hadawa amatullah priso cream, a kujerarta ta sakata don ta samu damar yin komai a natse. Kamshin turarensa da dariyar amatullah taji, yasa ta juyowa. Ido hudu sukayi, da yasa gabanta faduwa. Yana sanye da black jeans da white shirt, sai hannunsa dake daure da silver watch. He look hansom. Dauke idonsa yayi a kanta, ya durgusa ya dauki Amatullah daketa mika masa hannu tana zillo tare da dariya irin ta yara. Dagata yayi, ya cillata sama kamar yadda ya saba, yana juyawa da ita, suna dariya. Kafin ya mata kiss a chic dinta. " an tashi lafiya?" Hubby ta fada cikin karfin hali da basarwa, don ganinshi ya kara sa taji kishin ya kara taso mata Takowa yayi zuwa inda take tsaye, tana juya priso din don ya huce, yadda zata iya bata, Rungumeta yayi da hannunsa daya, ya manna mata kiss a goshi. " what I have don to u? To deserve this kind of punishment? " ya fada yana daga mata gira " notting!" Ta fada in very low voice Kallon idonta yayi, for some time, yana karantar yanayinta. Ya kada kai " ban yadda ba komai ba, amma koma menene daga yau komai nayi, amin wani punishment din banda wannan." Harararsa tayi kasa- kasa. Smirk yayi don ya ga me ta masa " u see!!! Allah yasa ba maganar planning bace tasa ake min wannan horon? " Tabe baki ta yi, tana kokarin amsar amatullah a hannunsa. Kin yadda yarinyar tayi, ta kara makalewa a jikin hayder. " kinga princess ma tasan na fiki gaskiya." Ya fada in husky voice dinsa yana amsar abincin a hannun hubby. " Batayi niyyar musu break fast ba, amma wata zuciyar ta gargadeta, da kar ta biye kishin banza, yanzu ne lokacin da zata kara zage damtse ta kama mijinta a hannunta. Agogo ta kalla at lest tana da  sauran time, hakan ya bata damar daura musu break fast mai sauki. Cikin minti 30 ta kammala, ta jera komai a dinning.   [12/03, 12:44] Zulaihatu Aliyu: DA KAMAR WUYA                             Part 28       Written By Zulaihat Aliyu Misau        Wattpad@zulaihatualiyumisau     Not Edited....... Gaba daya haka suka gama break fast, ba armashi tamkar kurame, dama ita ce mai yawan kawo hira to itanma brain dinta ya dau caji. Shikuma nazarinta ya tsaya yi, jikinsa yayi sanyi, anma baya jin zata samu abinda take so. Sai da ya ajiyeta sannan ya nufi nashi Wurin daukar karatun. Zainab da Hafsat kawayene ga hubby. Tare suke karatu, duk kansu yan nigeria ne, zainab yar jahar kebbi, sai hafsat gombe, ta samu har sun rigata isowa. " ummu ama, yau kam kin buga latti." Hafsat ta fada bayan sun gama gaisawa. " yau da gobe kenan, ballantana kar Ku manta sai na sauke Amatullah a day care, kafin na karaso, amma kullun ni nake rigaku isowa, sai yau aka samu akasi." " shi yasa nake sara miki, mu kuwa ba cas- ba -as, shirya kanmu kawai sai kiga lokaci ya tafi." Zainab ta fada dai dai lokacin da lecturer dinsu ya shigo. Gaba daya yau hayder kasa gane kansa yayi, karatun ma baya shiga yadda ya kamata, Hankalinsa na kan hubby. Yau ya kara tabbatar da son hubby da ya gama mamaye ransa. Duk da bai furtawa kowa ba, amma alamu sun gama nuna kansu. Tunda rashin walwalarta kawai na rana daya da ya gani ya hanashi sukuni. Tunanin abinda zai mata, ya sata farin ciki ta manta da damuwarta ya fara, duk abinda yazo ransa sai yaga kamar bai yi ba. He is not a romantic person, yan matan suke binsa, balle yasan yadda ake lallashi, ya kira hafiz omer ya tambaya, yana jin tsoron iskancin hafiz din. bai taba jin son wata kwata kwacin yadda yake ji akan hubby ba a yanzu. Yana son Nasrin, amma jigon soyayyar tausayi da kyawawan halayyarta. Sabanin hubby da sonta ya fara shigansa a hankali, har yayi girman da yanzu yake ganin bazai iya ci gaba da adanashi, a cikin ziyararsa ba. Hubby na sonsa he is 100% sure of that, kamar yadda bai furta ba itama ta adanashi a nata zuciyar. Sai dai action din kowanne na fallasa sirrin zuciyarsa ga dan 'uwansa. Kyawawan halayyarta, rikon addini, tsafta, son jamaa, biyayya, da kawici. Kadan daga cikin halayyarta dake burgeshi. Ta bangaren hubby kam, tunanin yadda zata samu damar zuwa hospital ba tare da sanin hayder ba, shiya tsaya mata a rai. Sun fito daga day care kenan, ita da Zainab, don shayar da Amatullah kamar yadda ta saba in ta samu free time. " please umm ama, yunwa nakeji, mu dan biya cafeteria ko snacks in siya. " Zainab ta fada tana yamutsa fuska kadan. Dariya hubby tayi mata, suka nufi hanyar cafeteria. Pizza suka yi order sai coca- cola. Suna ci suna dan taba hira kan abinda ya shafi karatunsu, da exams din dake gabatowa. Wasu yanmatane su uku suka shigo. Sun sha kananun kaya, kamar yayan turawa, saboda tsabar belching ga uban Brazilian heir da suka sha kai ka rantse nasu ne, Ba laifi kowaccensu nada kyanta dai -dai kwargwado. Sai dai kallo daya zaka masu kasan kudi da duniyanci ya samu wuri. " mutuniyarki!" Zainab ta fada tana murmushi Tabe baki hubby tayi, tare da jan dan karamin tsaki. Kallo daya ta musu ta dauke kanta, tare da fatan musu shiriya, da sauran daukakin musulmi da sukabi hanyar da suka dauka. A table din kusa dasu hubby suka zauna. Bayan sunyi oder din abinda suke bukata. Dayar ta kalli ta kusa da ita. " ina mamakin yadda zakiga mace tana cika, tana wani fadi, ita a dole kasaitacciya, amma at long last sai abun ya baki mamaki in kinji wani abu daya dangan ceta. A lokacin sai ta baki tausayi, kiga Ashe a isar ma bata isaba." Tabe baki ta kusa da ita tayi, tana wani yamutsa fuska, cikin yauki " wannan zancen naki haka yake Merry. " Wadda aka kira da Merry, wanda asalin sunan maryam ne. Tayi murmushi tana kallon su hubby cikin kallon da suka kasa gane ko na menene. " duk wannan kafafar Ashe matar cushe ce, yaro nada wadda yake so, iyayensu suka aura masa ita. Kin san me? She is divorcee, his late brother wife. " " don Allah Merry? " dayar ta fada cikin mamaki tana kallon Merry Gira Merry ta daga mata,tare da yin fari da idanuwanta. " kin san jiya da idona na ganshi da yarinyar da yakeso, kamar zasu cinye juna don so da kauna. U know the sad of the story? " " what!! " dayar ta fada cikin gaguwa da son jin karashen zancen. " harda cute and beautiful angel dinshi. Kai jiya naga love, abun yamin dadi, tunda mu an toshe mana damarmu, wata ta samu ba kuma yadda mutun ya iya, matar cushe da bata da daraja, ina tausaya mata ranar da sweet heart dinsa zata shiga gidan nan. Don da ganinta gara namu duniyancin akan nata." " meye matsalanki, can su karata." Dayar ta fada in I don't care manner " ni ko nakeda matsala! Kinsan irin son da nake masa? Love at first site. Amma fa har yanzu ban hakura ba, sai  naga abinda ya turewa buxu nadi." " sai kiyi tayi ai, kamar shine autan maza? Let them be." Inji dayar " ko don abinda akamin, bazan taba bariba, ko ban shigaba, sai na tabbatar da wata ta shiga. I want to see her supper." Ta fada cike da mugunta da kyashi. Zainab ta kalli hubby da ranta ke a bace, amma tayi iyakar kokarinta wurin saita kanta, she can give them the room to insult her. Da ido Zainab ke mata alamar tayi cool down, and take heart. Har suka gama su Merry na kan zancensu. Dai dai wurin Merry hubby ta isa fuskarta dauke da killer smile " wow!! Kinfa burge, meye ban bancin naki da matar cushe? Gara ma ita iyaye suka cusata, kefa? I promise u no matter how u try u never enter that house, it belongs to hubby and her children. About that lady da kika ce kin gansu tare. I know every think about her, I don't have any problem with it. So ki kwantar da hankalinki. Bazaki  taba samun hayder ba, in sha Allah, har gaban abadan. Yaso kowa, ya auri kowa amma banda ke, bai daman ba." Cike da mamaki Merry ke kallon hubby, don a tunaninta hubby bata san da zaman Nasrin ba. "Husband snatcher!" Zainab ta fada tana Jan hannun hubby suka bar wurin. Da ido su Merry suka bisu, har suka fice. " wannan yarinyar yar rainin hankali ce, ki daina biye mata." Zainab ta fada tana Jan tsaki " ba yadda zaayi ka bugi mutun ka hanashi kuka, sai dai ni bana barin ta kwana, shan yanzu maganin yanzu." Dafata Zainab tayi " har yanzu baki gayamin abinda ya hadaki da ita ba." Tabe fuska hubby tayi, ta fara ba Zainab labari kamar haka " farkon zuwana school din nan da ita na fara karo. Ganinta bahaushiya yar Nigeria yasa na dan saki jiki da ita, don na ganta cikin shiga ta kamala, a lokacin. Ita ta nunamin wurare da dama a cikin school din nan. Kasan cewar ta rigani zuwa, a wurinta na samu bayanan topic din da akayi bananan. In zaki tuna ko lokacin da kuka zo tare muke da ita, lokacin bata hadu dasu sintia ba. Ranar da suka fara haduwa da hayder a ranar na fara ganin changes a tare da ita, na yawan tambayana shi, ko in ta rakani wurin shayar da Amatullah ta dinga yabonta, tana abu kazanta ma irin na babanta, kaza na babanta and so on. Abin na damuna amma ban taba nuna mata ba. Sai ya zama kullun ita ke jirana a parking space, bayan dan uban kwalliya da zataci, haka zata gaisheda hayder tana wani karairaya, da kakkashe ido. Satina biyu da fara zuwa, hayder ya gargadeni bani ba wannan yarinyar, baya son alakata da ita. Hakan yamun dadi, amma ta ya zan zame kaina bayan na bari ta shiga jikina da yawa? Abu na farko dana lura dashi, shine yar burun- burun taso shirya min. Idonta a bude suke tar, mission dinta ta samu kyawawa, wanda zasu kawo mata haske cikin sha'aninta. At first ta dauka banida aure sai daga baya, duk da haka tana ganin zata iya brain worshing dina, sai taga sabanin haka, don sau da yawa nakan zauna namata waazi kan abunda nagani tanayi ba dai -dai ba. Musamman ta fannin addini, dana lura tana amsa sunan musulman ne kawai. Ganin hayder ya kara tabbatar mata da zanyi wuyar damuwa, yanda take tunani, don mai irin mijina baya bukatar kowa a rayuwarsa. Sauda yawa zakiji tana kokarin bugar ruwan cikina taji how he is, in our multimonial bed?. " auzubillah!! This is haram, maryam. Its between me and him, no body eals. Zakiga ta cika kamar ta fashe. So tunda hayder ya gargadeni a kanta, na fara ja baya da ita. Abun bai mata dadi ba, don na lura gaba daya yanzu attension dinta ya koma kan mijina. Wannan ya kara sa na tsaneta, naji ta fita a raina kwata- kwata, ga halinta na rashin kamun kai, dana fara ganowa a lokacin. Rana daya na dauke mata wuta. Kusan sati tana bina ina shareta, cikin ikon Allah sai gashi mun hadu daku a cafeteria, Allah ya hada jininmu, ganina tare daku yasa ta kara daukan zafi. Washe gari na ganta tare da su sintia, tun daga lokacin muka fara yar tsama da ita. Hayder yasha cemin wai ta bishi har school, ranar dai na sameta har hostel na mata wankin babban bargo, to tun daga nan in ba a lectures ba bama haduwa, sai yau." " anyi yar iskar yarinya! " Zainab ta fada tana jin jina kai. " Allah ya shiryeta yasa ta gane, kina yar musulmai ki maida kanki tamkar taxi no gari, da sunan wayewa" " ta amma wacece yarinyar da tace taga mijinki da ita? Har kike ikirarin kin santa." Zainab ta fada cike da son jin karin bayani. " itace yarinyar daya kamata ya aura, kafin kaddarar  aurenmu aurenmu. Tana karatu a nan, suna tare  kusan 4years kenan." Hubby ta fada " very sorry! Is not easy kasan mijinka na soyayya da wata, koda ko baka son shi. Ta dauka baki sani bane ta kunna miki wuta a gida. Duk da bansan dangan takar aurenku da mijinki ba, zan baki shawara! Ki zage damtse ki rike gidanki da kyau. Don irinsu maryam ba karaman shaidanu bane. Ki dage da addua." " insha Allah, Thanks. " " ina kuka shigane tun dazu na dawo ina ta faman nemanku? Ga wayar ma bata shiga" Hafsat ta fada cikin jin haushi Murmushi sukayi " very sorry, muna daga day care muka wuce cafeteria," Zainab ta fada tana mika mata pizza da suka mata take away. " kun kyauta, kamar kunsan ina jin yunwa sosai." " ya jikin Islam din?" Hubby ta tambaya " taji sauki, sunma dawo da ita clinic din cikin school din nan. " " ya ka mata gobe muje mu dubata." Inji Zainab " haka ne kam! Allah ya kaimu goben." Inji hubby " amin." Suka amsa baki daya.                **************"*"**** Ranar hayder ya shirya musu romantic dinner, a wani 5star hotel dake kusa dasu. Don faranta ran hubby. Mariya da Amatullah suka saukesu a gidan friend dinsa. Hakan ba karamin dadi yayiwa hubby ba, don tun a Egypt rabon da su share din moment irin haka. Sai  past 11 suka koma gida, bayan sun dauki su Amatullah. Haka suka raya daren cikin so da kauna, duk da baki ya hanasu furtawa juna, sai zuciya da gabbai dake nasu aikin. Suna rungume da juna, cike da farin ciki, bacci yayi gaba dasu.               ****************** Zuwan hubby da su Zainab dubo Islam school clinic, yaba hubby damar nazarin clinic din. Ya hadu, ga kayan aiki irin na zamani, mamaki ta fara da yasa tun farko basu kawo Islam nan ba. Bayan 2days, daga school sun samu interval, ta wuce clinic din. Cikin 1hour 3omin result dinta a hannu, ta koma lectures ba tare data bude ba, don bata shirya gani yanzu ba, tafi son sai ta natsu tukun. Maryam Kabir kamba, yarinya ce yar shekara 21 a duniya. Haifaffiyar garin Abuja, mahaifinta Alhaji Kabir kamba dan majalisan dattawa ne, wanda ya dade ana damawa dashi a gomnatoci da dama dasuka shude. Maryam ita ce auta a yayansa. Sun shagwabata, shagwaba na karshe. Hajiya tumba mahaifiyar maryam mace ce mai son abun duniya, wanda neman kudinta yafi mata tsayawa kulada rayuwar yayanta. Kusan duka yaran tarbiyyan yan aiki ne. Maryam tun daga secondary sch idonta ya bude da bin maza, ga son kudi. Duk da kudin da ubanta ke sake mata. Shekararta 4 a kwakwalada amma ta kasa achieve din komai, makarantar ma sai ayi fiye da 2weeks bata leka ba, ganin hakan yasa mahaifinta yanke shawarar ta fita waje tayi karatun, a tunaninsa ko don tun farko ya hana ta yin karatu a wajene yasa bata maida hankali. Taji dadin hakan, don zata samu damar barje tsiyarta ba tare da an sa mata ido ba. Tare suka taho da Best friend dinta Regina. Ranar data fara haduwa da hubby taji hubby ta kwanta mata, tana son kulla alaka da ita, duk da ta lura hubby ba irin su bace, amma with time, sunyi irin hakan yafi a kirga, so wannan ma bazaiyi wuya ba. So koda suka hadu da Regina ta mata bayani, tare da setting plan dinsu a kan hubby. Zamanta da hubby na dan lokaci, ta gano tana da aure har da beby, amma hakan bai sanyaya gwuiwarta ba. Abu daya daya fara cimata tuwo a kwarya kan hubby shine, ta lura addini ya shigi yarinyar sosai, da zatayi wuyar samuwa. Yawan waazi da Jan hankalin da hubby ke mata, kusan ko yaushe ya kara sa ta fara kwakekwanto kan hubby. Ganin hayder ya rikita duniyar maryam don duk dunya ji tayi ba wanda ya kwanta mata, ya dace da rayuwarta sama dashi, ta gefe daya kuma ga hubby. Zata jefi tsuntsu biyu da dutse daya. Babban tashin hankalinta da hubby ta fita hanyarta lokaci daya. Hakan wani kalubale ne ga nasararta kan kudirinta a kansu. Sannan ta gefen hayder Sam ba sassauci. Ita a yanda ma ta samu labarinsa abun tsoro ya fara bata, sai dai tadau kudiri da babu komawa baya. Ganinsa da Nasrin yafi komai daga mata hankali, nan da nan ta koma neman karin bayani, alhamdulillah ta samu dai -dai abinda take bukata. Kalaman hubby sun sata, canza akalan plan dinta.  Dare nayi ta kira kawarta dake gida Nigeria ta labarta mata komai da taimakon da take bukata daga gareta. Dariya Nancy tayi " ki kwantar da hankalinki an gama, ki turomin da cikakken sunansa, sunan babansa da mahaifiyarsa, angama."......... Saida tayi sallar isha'i, tayi wanka ta shirya cikin wasu hadaddun English wares, riga da wando masu matukar kyau. Tama Amatullah wanka ta shiryata cikin kayan baccinta. Roll- on red. Reports dinta ta dauko ta warware, ta fara karantawa, tana jijjigata Amatullah dake goye a bayanta. positive, 4month pregnant. Ido tadan zaro cike da tsoro da mamaki, 4month ta maimaita. " no it can be." Ta fada tana ninke report din. Kenan tana komawa gidanta ta samu cikin, in tayi lissafi dai- dai, yanzu watan Amatullah 5 tana cikin na 6. " ya Allah!!! " ta fada tana sauke ajiyar zuciya, tare da tausayin kanta dana Amatullah. Tana maganar planning Ashe aikin gama ya dade da gamuwa. Duka 1 month kenan data fara jin changes a tare da ita, da yasa ta fara zargin kanta. Dakin Mariya ta nufa, don dubata, tun dawowarta school ta dawo da ciwon kai. Ta samu tasha magani har tayi bacci. Saita mata Ac din dakin tayi, ta kashe mata wutar dakin ta fita. A falo suka ci karo da hayder dake kokarin shigowa. Da sauri ta nufi she hannayensa ya bude ta shige, ya rungumesu daga ita har Amatullah dake bayanta. Kissing bakin juna duka fara kamar life defend on it. Kafin suka janye daga juna. Ta karbi jakar laptop dinsa. Kiss ya mannama Amatullah a goshinta, ai kuwa kamar jira take ta bude ido, baki ta bangale masa, tare da juye -juye, tana don taje wurinsa, hubby ta shigar mata da hannun cikin goyo. Showel din ta balle ya daga ta yana cillata suna dariya. " kaji dadi da ka tasar min ita!! Na samu na lallabata dakyar." Hubby ta fada cikin shagwaba, tana nufar dakinsa. Murmushi yayi, yabi bayanta dauke da princess dinsa. Ajiye bag din, ta wuce toilet ta hada masa ruwan wanka. A kadonsa ta samesu sai wasa yake mata tana bangala dariya harda kyakyatawa, Tana mamakin hayder, bata taba tunanin yana son yara haka ba, sai yanzu. " ruwan wanka is ready." ******************* Shiya kwantar da Amatullah tare da mata addua, kamar yadda suka saba ( A'uzu bi khalimatul lahi ta'matih min kulli shai'danin wa hammat wa min kulli ai'nuin lammat 3) Gira ya dagawa hubby dake kwance tana kallonsu, tare da kashe mata ido. Murmushi tayi tare da ware masa hannayenta. Hancinta ya hade da nasa, Ido suka lumshe a tare,Wani iri suke ji a jikinsu wanda bazai misaltu ba,kasa matsawa kowannensu yayi, a nutse ya daura lips dinsa saman nata tare da dorata a samansa shi yana kasa, bakinsu ya hade wuri daya ya kamo harshenta da nasa Yana tsotsa kamar zai cinye Mata Baki, hannunta ta kai kan sagensa da tafukan hannunta masu matukar taushi tana shafawa a hankali zuwa gemunsa tana Kara kissing dinsa sosai, Kirjinsu ya hade waje daya tare da gangarowa zuwa wuyanta Yana lasarta, a hankali ya zuge zip din rigarta, Jin hannayensa a saman a saman kirjinta yasa ta rudewa, tare da kaimasa nata sakonnin. Harshensa taji saman kirjinta wani shidewa ta fara yi, tare da zagewa wurin gigitashi da natsa salon. Bakajin komai sai nishinsu, da kurnani, sai kalamai na maabota shauki. Tana kwance a saman kirjinsa, bayan komai ya lafa, suna maida numfashi, duk kansu fuskarsu cike da farin ciki da annuri. Kiss yama goshinta, tare da kwantar mata da gashin kanta daya gama hargitsewa. " meye sirrin ne?" Ya fada in husky voice. Dago kai tayi tana kallonsa cikin rashin fahimta. Gira ya daga mata murmushi tayi tare da kara shigewa jikinsa, " kai ne sirrin." Ta fada a shagwabe " thanks. " ya fada yana smirk shafa lallausan fatar kirjinsa zuwa 6 pack dinsa take cikin salonta. " kullun cikin godiya ga Allah nake daya kaddari aure na dake, yanzu nake ganin anfanin biyayya iyaye, dana bijere musu kamar yadda na bijircewa wasiyyar dan uwana, da na tabka babban kuskure a rayuwata." Ya fada cikin sanyin jiki, da raunin murya. Da sauri ta dago, tana kallonsa. Jin ya ambaci wasiyyar dan'uwansa, me hakan ke nufi?. Tashi yayi ya zauna, tare da jingina da jikin bed din. Tana kwance a kan cinyarsa fuskokinsu na fuskantar juna. Kallo sukewa juna mai cike da ma'anoni masu yawa, Masu wuyar fassaruwa. " me kake nufi da wasiyyar dan'uwanka?" Ta fada cike da raunin zuciya Ajiyar zuciya yaja, tare da kamo hannayenta duka biyu cikin nashi, yana dan murzawa a hankali. " in zaki iya tunawa, 3 weeks before rasuwan ahee! Ya kawo min ziyara." Kai ta kada, don ta tuno, da tare ma zasu zo, haihuwar Anty samira a lokacin yasa bata bishi ba. Numfashi yaja, tare da fesar dashi tunowa da moment din na matukar dawo masa da mutuwar tamkar lokacin abun ya faru. " A ranar da yazo mun tattauna abubuwa da dama, sannan ya bammin wasiyyu guda 3, biyu kam na amsa masa, kuma Alhamdulillah ina iyaka kokarin ganin na sauke wannan alkawarin dana dauka. Dayan ne dai duk yadda yaso, ban amsa masa ba, don nasan da kamar wuya, wurin yiwuwarsa." Jin yayi shiru, tare da lumshe idonsa, ita kuma ta kagu taji duk da sanyin da jikinta yayi. " meye abu daya daka ki amsa masa a lokacin?" Ta fada idonta a kansa " aurenki." Ya fada tare da bude idonsa ya sauke a kanta. Tashi tayi ta zauna, taja bargon ta dan rufe jikinta dashi. Baki na rawa tana nunashi ta nuna kanta " auuure niii daaa kai?" Smirk ya mata " of course, ahee!!! Ya rokeni da na aureki, don ya tabbatar zan kula dake yadda ya kamata. Baya son bayan mutuwarsa rayuwarki ta tagayyara, yana fatan ki kasance cikin farin ciki da walwala, Amma gaskiya a lokacin ban amsa masa ba. Duk da abun na cikin raina yana damuna, amma a lokacin nasan bazan iya cika masa wannan kidirin nasa ba." Cike da mamaki hubby ke kallonsa. Kara matse hannunsa yayi cikin nata " yanzu kin kara yadda aure na dake mukaddarine? don ban manta kalmarsa ta karshe a kan hakan, dana rakoshi airport zai wuce Oregon. Kafadata ya dafa yana murmushi " na rokeka alfarma kaki min, ka sani Allah na cika burin bayinsa ta inda baa zato, a lokacin da yaso. Bazan matsa maka kan abinda baka ra'ayi ba, don muma ba wanda ya matsa mana. Duk abun da kake gani da wuya, a wurin Allah mai sauki ne. Zuwa gaba zaka gane soyayya da gatan da nama. Karike a ranka Yusuf na sonka so mai girma." Ina hawaye yana hawaye haka muka rabu, ina tsaye ina kallonsa, har ya bacewa ganina." Hawayene kebin kuncin hubby, ganin hakan yasa hayder shiga damuwa da tashin hankali. Lallashinta ya fara in romantic way. Duk da shi kansa daurewa yake, amma kewar dan' uwan nasa fil ta dawo masa, shi yasa bai taba maganar da kowa ba. " me yasa baka taba gayamin hakan ba?" Ta fada cikin dasashshiyar murya " ko don babu digon kaunata a zuciyarka?" Ta sake furtawa tana kafeshi da idonta da suka kada sukayi ja. Lashe labbansa yayi, " ban taba maganar da kowa ba, tsakani na dashi ne, sai mahaliccinmu, sai ke yau dana furta miki." " ajiyar zuciya taja, tare da mikewa ta nufi toilet don ta tsarkake kanta. Meye anfanin gaya matan da yayi? Tunda bai gaya mata a lokacin da ya dace ya gaya mata ba! Tabbas da tasan da wannan maganar ko ja bazatayi ba zata aureshi, kodon son cika muradin masoyinta. Amma shi da yake ikrarin yana sonshi, ya gagara cika masa. Wacce irin kiyayya yake matane har haka? Me ta taba masa mai zafi har haka? Tunanin da suka cika zuciyar hubby kenan. Jiki a sanyaye yabi bayanta. Rungumeta yayi a jikinsa ganin kamar fushi take dashi. " I'm so sorry!! Abinda ya wuce ya wuce, nasan kuma bai wuce kiruciya da rashin fahimtar juna ba. Ina so ki sani a yanzu soyayyarki ta gama mamaye zuciyar hayder, kece duniyarsa wanda Allah ya sanya farin cikinsa a cikinta, ke kika zamo min tamkar Zara cikin dubban mata, U are my every thing. Don Allah kar kiyi fushi dani." Ya fada cikin husky voice dinsa Tare da shagwabe fuska Dagowa tayi tana kallonsa, zuciyarta na bugawa, a hankali. " I love u so much. " ya fada idonsa cikin nata. Kallonsa take cike da so da kauna, wani dadi na ratsa zuciyarta. " I love u too." Ta fada cikin muryarta mai sanyi da dadin sauraro. Bakinsa ya kai kan nata, ya lalubo lallausan lips dinta suka fara aikawa jina hot romantic kissing, kamar zasu cinye juna. ****************** Bedroom din hubby ya shiga, dauke da Amatullah dake makale a kafadarsa. " habitty what take u so long eh!!!!" Ya fada in husky voice dinsa yana shigowa. Daskarewa yayi daga bakin kofa yana kallonta baki sake. Dariya tayi, tare da hure masa ido, bayan tayi dage sosai. Kaftawa yayi, ya saki murmushi " is that u." Ya fada yana kai hancinsa kan gashinta da yasha gyara sai kanshi da daukar ido yake. Juyawa ta fara a gabansa in romantic way. Runtse ido yayi jikinsa na tsuma yana kara godewa Allah bisa duk kan ni'imar da yayi masa. " don't kill me please. " ya fada muryarsa na rawa. Dariya hubby tayi tana kara kashe masa ido da salonta na Jan hankali. Tuni goga hayder ya dane network, kwalliyar da hubby tayi na kananun kaya (English wares) robber skirt and top da sukai asalin kamata ko Brazer bata bukata ba, gasu nan a cike kamar sa tsone idon oga hayder. komai masha Allah, ga gyaran gashi, yau na musamman tayi da makeup. " ba dama mutun yayi kwalliyarsa sai an bata masa." Ta fada tana tura baki, cike da shagwaba Smirk ya mata " kema kinsan abinda kikayi ai? abinda kika nema aka baki, right? " ya fada yana kashe mata ido Duka ta kaimasa a saman faffadan kirjinsa,. Ya rike hannun, tare da mirginawa ta koma kasansa. " u say u want to talk to me? " ya fada yana shinshina wuyanta. Lumshe ido tayi, tana maida numfashi. " let me show u." Ta fada cikin rashin kwarin jiki. Dagata yayi Ta mike, da ido ya bita tana takunta mai tafiya dashi. Amsar takardar yayi ya bude. Ido waje yake kallonta, murmushi tayi tare da shafa cikinta, da yadan tasa kadan, don in baka lurabama bazaka ganeba. Hamdala yayi tare da daga hannu yana godewa Allah. Ya tashi sai ji tayi ya sureta ya fara zagaya dakin da ita, cike da farin ciki. Dariya take, tana ya sauketa. Kukan Amatullah da suka farkar da ita da hayaniyarsu ya dawo dasu hankalinsu. Sauketa yayi, ya dauki princess dinsa ya fara mata rawa, suna celebrating sun kusa samun new beby. Ranar hubby taga so da tattali, sosai yake nuna farin cikinsa mara misaltuwa, a kan cikin hubby. Da yamma ya dauketa zuwa wani special clinic don neman shawar -warin yadda zasu kula da Amatullah, da abubuwan da ya dace taci. Sun yanke shawarar Jan bakinsu suyi shiru. They want to surprise there family. Koda suka yi waya da Aisha take tambayarta maganar family planing, ce mata tayi, tayi babban. Daga karshe ta shashantar da maganar. Kula sosai hubby ke samu, a wurin hayder, haka ya hadata da wata doctor musamman take zuwa har gida ta dubata tare da bata shawarwari. Ta ci gaba da shayar da Amatullah yarinyar tayi girma da wayau abunta. Watanta tara ta fara takawa. Ta bangaren karatun hubby abin masha Allah, ta dage tare da taimakon Allah duk sakamakonta na 2 section din da sukayi sunyi kyau. Maryam kam tana nan sai faman tura kudi ma Nancy take, kan hayder amma shiru ba nasara. Gashi zuwa lokacin soyayyar hayder ta kara nunkuwa a ranta. Haka zata bishi school ta tsaya daga nesa tana kallonsa kamar photo, don bata da ikon zuwa inda yake, tun tanar da ya sauke mata tagwayen maruka, da warning take tsoronsa. Nancy kam kasuwa ta bude, sai tatsar maryam take, da sunan zuwa wurin malan alhali harkar gabanta kawai takeyi. Sai in maryam ta kirata kan aiki bai ciba har yanzu. Sai tace zata canza wurin wani malamin ko zaa dace. Haka zatayi ta mata bill na abubuwan da malan yace a siya na kayan aiki. Ita kuwa wawiyar jiki na rawa duk inda kudi suke zata nemo ta tura mata. A na haka list din Wanda aka kora saboda rashin maida hankali, da rashin samun makin da ya dace ya fito. Sunan maryam na daga ciki, hakan ya balain daga mata hankali. Dole tana ji tana gani, ta tattaro zuwa kasa Nigeria, da niyyar sake komawa Cyprus koba the same school ba. Tama dawowa, hajiyanta ta hadata da wani dan ambassador na kasar France, ganin kudi yasata saurin amincewa da maganar aurensa, ba tare da bata lokaci ko bincike ba. Ranar wata Monday su hubby suna lectures ciwon nakuda ya kamata, daga nan aka wuce da ita school clinic. Zainab ce ta kira hayder ta shaida masa. In no time sai gashi ya iso. Wannan karon ma tare suka shiga labour room, da yake su sunma fi son mijin mace na wurin. Tun 4 na yamma sai 11 na dare hubby ta santalo beby girl dinta again. Mai kama da hayder tamkar Amatullah. Murna a wurin hayder baa magana. Hada hubby da beby din yayi ya rungume a jikinsa, yana jin sonsu da kaunarsu na ratsa duk wata gaba ta jikinsa. Hajiya na tsaka da baccinta, taji wayarta na ringing, ganin auta, yasa gabanta ya fadi, don bai taba kiranta a wannan time din ba. " lafiya auta?" Ta fada murya irinta mai bacci daya shiga fargaba. Dariya yayi " mun samu karuwa!" Ya fada still yana dariya Ajiyar zuciya Hajiya tayi " Wane irin karuwa? Kar ka cemin Ummi keda ciki ka kirani a wannan tsohon daren?" " ta haihu dazun nan! Mun samu Amatulrahman." Ya fada cike da jin dadi. Ai tuni bacci yayi kaura a idon Hajiya, ta gyara zama " an gaya maka haihuwar wasa ce? Ban son rainin hankali meya faru ka kirani?" " Allah da gaske nake, gata ki tambayeta. " ya mikawa hubby dake kwance wayar yana murmushi Ko gaisawa basuyi ba Hajiya ta katse hubby dake kokarin gaisheta " da gaskene abinda auta ya fada min?" Kada kai hubby tayi cike da kunya, kamar Hajiya na kallonta, sai da ta kara tambayarta sannan ta iya ce mata "eh!" Ta mika masa wayar. " amma yaran nan bakuda hankali, har ayi cikin ya kai haihuwa amma Ku kasa gayawa kowa, sai bayan an haihu?" Hajiya ta fada cikin fada da jin haushin abunda sukayi. Don bataji dadi ba kiba ko basu gayawa kowa ba sa gaya mata. Hakuri hayder ya fara bata, cike da damuwa, bai dauka abun zai mata zafi haka ba. Cikin daren Hajiya ta fara kiran jamaa tana shaida musu haihuwar hubby. Hubby na zaune tana shan tea, kiran Aisha ya shigo wayarta. " hello besty." Ta fada tana murmushi " ba wani besty! Ai ni kin gama ban mamaki, wannan kyakyawan labarin, amma sai injishi daga sama." Ta fada cikin jin haushi " Allah ya huci ran besty." Ta fada tana murmushi " yar rainin sense, shiyasa da muke maganar da Ummul khair kan maganar babban planning, tayi dariya ta ce " yanzu haka in kin bibiya Anty hubby ta kuma kunsan wani cikin ne, ta fake miki da babban tayi" ina cewa ina ba haka bane." " tuba nake! Ya yarona?" " gayi can, yanzu na senda shi wurin nanny dinsa. ina bebymu?" Ta fada tana washe baki, kamar ba ita ta gama korafi ba " gata nan, tana bacci. Na tura muku da pictures in kin kunna data zaki ganta." " ok. ina beby Amatullah? " Aisha ta tambaya " tana wurin daddy dinta." " na kosa inga new beby, how she look? " ta fada cikin kaguwa. " like u." Hubby ta fada tana murmushi " sai munyi waya, bari inga picture din bebynmu, I hope kin hado dana beby Amatullah?" " yes!" Hubby ta fada tana sauke wayar a kunnenta Kafin su hubby su iso gida, daga hospital, harsu Mariya da hafsa,Zainab sun gyara mata gidanta tsaf, sun saka turare, ko ina na tashin kamshi, dakin hayder ne kawai basu shiga ba. Hatta girki sun kammala. Hubby taji dadin abunda suka mata. "Madallah da aminan kwarai" hubby ta fada tana murmushi " dont meantion, we are know sisters right? " inji Hafsat Kai ta kada tana murmushi " right. " 8:41 sai gasu Hajiya da gwaggo, Anty samira sun iso. Basu kira kowaba, don haka su hubby basu san da zuwansu ba, sai ganinsu sukayi. Zo kaga murna wurin waannan bayin Allah. " da kungaya min inzo in daukoku daga airport. " hayder ya fada yana gefen Hajiya dake rike da Amatullah " Abinda kuka mana, muka muku, kuji in da dadi." Gwaggo ta fada tana harararsu. " mun bada hakuri fah!" Inji hayder " ko don wannan zukekiyar bebyn kwayi hakuri, Ku yafa musu." Anty samira dake rike da bebyn ta fada tana murmushi Ranar haka suka kwana cikin farin ciki, hubby na makale jikin gwaggo. Haka duk nisan Cyprus bai hana yanuwa da abokan arziki zuwa duba hubby da beby dinta ba. Haka su junaid duk kansu sunzo kusan a tare, kwanansu biyu suka koma. Satin hubby biyu da haihuwa su gwaggo sukayi haramar komawa gida. Anty samira dai dama kwananta biyu ta koma tare dasu ummu sulaim. Hubby taso gwaggo ta zauna mata, rike baki gwaggo tayi " kafata kafar Hajiya, ina zan iya da rashin kunyarku ta yaran zamani, wancan karon ma ya muka kare, balle yanzu da abun naku ya kara shahara? Ma dawo shekara mai zuwa ganin wani bebyn." " haba gwaggo, wannan wane irin fatane?" Ta fada cike da shagwaba tana tura baki. " fata ko gaskiya!! Miji na nanike dake kamar cungum ta ina zaki kasa haihuwa duk shekara.? " gwaggo ta fada tana tabe baki Dariya Hajiya tayi " keda takwarar taki?" " yo!! Me nace? Zamane dai banyi, Allah miki albarka da kika dauke Amatullah, kafin shekara ma dawo wani sunan. Ban zama inga wannan fitsara, kina nan ma ya muka kare, balle bakyanan?" Dariya kawai Hajiya tayi. Don itama bata bayan zaman gwaggon. Don hayder yanzu bata ido ce ta isheshiba. A gaban kowa yake nuna soyayyar matarsa. Garama ita tana dan kawaici da kunya, daba haka ba. Hajiya taji dadin hakan sosai. Tafiya da Amatullah dasu Hajiya sukayi ba karamin daga hankalinsu hubby yayi ba, musamman hayder da Mariya. Don har hawaye hayder yayi, Mariya kam kuka riris. Tafiyarsu gwaggo da kwana biyu, su mommy Hauwa da Alhaji Munir suka iso, ganin jika. Sunji dadin ganin yaran nasu. Albarka sosai Alhaji Munir ya dinga saka musu. Haka mommy Hauwa baki yaki rufuwa don farin ciki. Ummin tace wai da yara har biyu? Ikon Allah. Haka suka maida hankali kan karatunsu da kula da Amatulrahnan. Soyayyar hubby da hayder sai dada bungasa take, suna kula da juna, da gudun bacin ran juna, da nunawa juna tsantsar soyayya. Hayder ya riga hubby kammala nasa karatun, hakan yasa ya kara maida hankali wurin karatun Islam, da dama kusan a tare yake yin kayansa. Zuwa lokacin yayi nisa sosai a littatafan hadith, fighu, tafsir da sauransu. Alhamdulillah, Beby Amatulrahman nada shekara daya da wata biyu, hubby ta kara samun wani cikin. Na wannan karon mai matukar laulayi. Allah ma yasa Mariya ta kammala secondary sch dinta, kula da Amatulrahman ya koma hannunta. A wahalce haka hubby ta kammala nata karatun. Lokacin cikinta na cikin watana 7 amma har lokacin tana laulayi, sai dai bai kai farkon cikin ba. After one month suka tattaro zuwa gida Nigeria. Hubby tasha mamakin ganin gidan da hayder ya tsantsara musu a lamido crescent, Unguwar rimi. Gidane na gani na fada. Suna Jere dana junaid, komai iri daya. Zuwa wannan lokacin business dinsu hayder ya kara bunkasa, saboda sabon salo da suka zo dashi na dabarun kasuwanci. Zuwa lokacin kowa ya fara cin gashin kanshi. Sabanin da da sukeyi a tare. Ansa ranar auren junaid da Asiya, abinda ya faranta ran hubby sosai, tare da dunbin mamaki, koda yake ta dade da fara ganin alamu daga garesu, sai dai bata zurfafa tunani ba. Wata uku masu zuwa ****************** "please tell me, what happen between u and Nasrin? I want to know." Hubby ta fada tana narkewa a jikin hayder Hancinta ya lakace " its all your fault " " my fault? how?" Ta fada tana mikewa zaune Smirk ya mata " by stolen my heart." Ya kashe mata ido Murmushi ta masa tare da kiss a lips dinsa. " parents dinta sunki amincewa tayi aure nesa dasu, she is the only child da suka haifa. She love me so much, sun yadda ta aureni but da sharadin zan koma Egypt da zama. Abunda bazai taba yiwuwa ba, I can live my parents because of her. So mun dade ana ta jayayya, at last suka ce lallai se dai ta auri dan uwanta, tunda naki amincewa da sharadinsu. She come to me, so I advice her tayi hakuri ta musu biyayya tunda sun kafe kan hakan. Ni kuma bazan taba yin abinda suke so ba. Nasha wuya sosai kafin ta hakura zata aureshi. Yanzu haka 6 months kenan da akayi bikinta." " baka kyauta ba, da sai ka dinga zuwa kana dawowa ai!" Hubby ta fada Harararta yayi " kina dona kuwa?" Ya tambaya in husky voice Dafe saitin zuciyarta tayi " sosai ma" tana kashe mishi ido " ta ina zan iya yanke wannan danyen hukuncin, bayan kin bararraje a cikin zuciyar, baki bar space ko kadan ba." Ya fada yana smirk " kar kasa kaina yayi kato fah?" Ta fada cike da shagwaba "Kin riga kin gama da hayder Habiba, baya iya kallon ko wacce mace sai ke. A sonki bana ji bana gani. Don haka ki kwantar da hankalinki, zuciyar hayder taki ce da yaranmu. Haka gidan hayder belongs to u and our children's, sai kaddara da baa fata." Rungumeshi tayi tana kissing nasa every ware " haka zuciyar Habiba taka ce only u, no one but u, till my last breath. " Kara matseta yayi a jikinsa, cike da farin ciki, suka fara romancing juna daga nan suka wuce..... ****************** Wannan karon beby boy hubby ta santalo, mai kama da ubansa sak. Farin ciki baa magana, yaro yaci sunan Yusuf. Hubby ta ci gaba da kula da yaranta, har lokacin Amatullah tana wurin Hajiya. Anyi bikin junaid da Asiya. A lokacin akasa na Ashir da aina, Hafiz omer da Zainab kawar hubby. Yusuf nada 3 month business Trip India ta kama hayder. Gidan Hajiya suka kai mata Amatulrahman, suka nufi kasar India. Kwanansu biyar a kasar India, suna soyewa, a haka kuma yake samun time na abinda ya kaishi. Hajiya ta kirasu, suje su duba Hajiya kaka, su Abdul Karim sun taho da ita ba lafiya. Abdul Karim ya kira, nan yake gaya masa hospital din da take, duka anan cikin Mumbai ne. Bayan ya dawo daga meeting, suka shirya zuwa duba Hajiya kaka. Sun sha mamakin samunta ita kadai, sai rarraba ido take a gadon asibiti kamar agogo. Tana ganinsu ta fashe da kuka. Duk sun shiga damuwa bisa halinda take ciki. Tun safe dasu Abdul Karim da matarsa sailuba, suka zo suka dubata har zuwa lokacin 7 na yamma basu kara lekota ba, tsawon 3 days daaka kawota haka suke mata, in sunzo da safe, sai gobe kuma su dawo dubata. Kasan cewar hospital din baa bukatar mai jinya, hatta abinci su suke ba majinyata. Shiyaba su Abdul damar banzatar da Hajiya kaka. Alhalin yawanci kowanne mai jinya, zaka samu akwai wani na kusa dashi a wurin, har zuwa lokacin bacci, kafin su tafi, su dawo da safe. Ciwon zuciya ke damun Hajiya kakan, hakan yasa Mmn samira tattara yan kudadenta don samawa mahaifiyarta lafiya, ta turo Abdul Karim da matarsa don suyi jinyarta, don itama hawan jini yasata a gaba, yan kwanakin. Da ita zatazo da kanta. Tunda suka zo kowa ya kama gabansa, in gari ya waye sun duba Hajiya kowa keyin hanyarsa. Don yanzu sosai halin Abdul Karim na muamala da mata ya shahara har kowa yanzu ya sani. Ita kanta sailuban abinda take yi kenan, kuma duka sun sani, har lokacin ko batan wata bata taba yiba, bata so ta tsufa da wuri, shiyasa take shan maganin planning. A cewarta Hubby ce taci gaba da kula da Hajiya kaka, da safe kafin ta taho saita tana dar mata abinci na musamman wanda zai mata dadin ci, da saurin narkewa, ta taho mata dashi, haka zasu zauna susha hira har yamma, kafin hayder yazo ya dauketa su tafi. A haka har akama Hajiya kaka aiki, alhamdulillah an samu nasara duk da sai a hankali, tunda ya hada da girma. Hubby tunda take zuwa sau biyu suka hadu da sailuba, wadda takewa hubby kallon raini da kishi, don taji labarin komai, kuma har yanzu tasan akwai son hubby a zuciyar mijinta. Sun hadu da Abdul Karim da dan dama, don tunda yasan hayder na zuwa, yake kokarin biyosa suzo, ko kuma lokacin da zasu tafi, shi kuma zai zo. Saboda ciwon Hajiya kaka yasa suka kara kwanaki a India. Saida aka sallameta suka rankayo gida Nigeria gaba daya, suka bar Abdul Karim da matarsa a can, cewarsu akwai abunda suke, basu kammala ba. Kuka sosai Hajiya kaka tayi, tana ba su hubby hakurin, abunda ta musu, tare da shi musu albarka da zuriarsu. " nasan nayi kuskure, amma duk laifin samira ne data zugani, gashi ta kai dan uwanta ta baro, meye anfanin wannan aure na Abdul Karim? In banda takaici." Tabe baki hayder yayi " baki mana komai ba, illa ince abinda kika min banda kudin da zan biyaki dasu. Kin gama min komai, tunda kika zama sanadin aurena da Habiba. Allah ya saka miki da mafificin alkhairi, ya baki lafiya. " " amin! Allah ya riga ya kaddara Habiba matarka ce, Allah ya raya muku zuria." Ta fada tana share hawaye. Zuciyarta cike da dana sani da nadama ******************* Sun dawo ba dadewa hubby ta fara aiki a hospital din doctor sabir. Lokacin arziki da budi kota ko ina haka suke bulbulowa a rayuwarsu hubby Duk wani hidima na yan'uwa, da dangi kusan hayder ya dauke, kowa matsalarsa ta tashi hayder! Ya koma tamkar shine babba a gidan, duk abunda babban yaya yakamata yayi, shi yake gudanarwa. Ta fannin taimako kuwa baa magana, don shi mutun ne mai matukar sirri, baka taba sanin ayyuka na alkhairi da yake gudanarwa. Yanzu haka yana da katafaren gida, mai kama da boarding school, inda yake ba tsofaffi mafaka, wanda basu taba haihuwaba, ga tsufa ya kamasu babu mataimaki. Wanda ya danka shi kalkashin kulawar malaminsa sheikh Ahmad al- kanawiy. Haka masallatai da rijiyoyi ya Samar ba adadi, sadakatul jariya, gareshi da dan' uwansa. Haka taimakon marayu, wanda hadin hannune shida abokanshi, sai hubby da tayi joining dinsu. Shakuwa da kaunar juna, shine tsakanin hubby da yayyen mijinta, musamman ummu sulaim da Aisha, haka anintarta da yusra da humaira ya kara bunkasa, a gefe daya ga Zainab data shigo family duk ta sanadiyyarta. Sai Hafsat. So da kauna sai abinda ya karu, tsakanin Hubby da oga hayder, kullun ka gansu kamar sabon aure. Rayuwa tamasu hubby dadi, sai dai duk yadda rayuwa take lallai tana zuwa da nata jarabawar iri iri,. Yusuf na wata 6 hubby ta sake samun wani cikin, fatan Allah ya sauki hubby lafiya, ya kara dankon kauna tsakaninta da oga hayder, ya raya su Amatullah da kannenta masu zuwa........ Anan na kawo karshen littafina mai suna DA KAMAR WUYA. Na gode da kauna da soyayyarku gareni, musamman masu kokarin yin comments da masu voting duka, Allah yasaka da alkhairi, ya bar kauna. Jhazhakallahu bi Janna to all of u. Sai mun hadu a littafina na gaba KYAN DAN MACIJI