Compiled By Umar Dalha Funtua. Copied By Aminatu Hassan Oum-Deed at. [8/5, 8:19 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~* *Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat) *Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat) *Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare. *Godiya*---- Ga Allah subhanahu wata'ala daya bani rai da lafiya na rubuta maku wannan littafin mai dinbin fad'akarwa da nishadantarwa, yanda nafara lafiya ina rok'on Allah yasa in k'are lafiya. *Jinjina*--- ga 'yan Golden Pen writers association Allah ya k'ara hada kanmu ya qara mana zaqin hannu ya bamu ikon rubuta abunda zai amfani al'umma baki daya. *Matashiya*--- wannan labarin qirqirarre ne banyi da niyyar cin zarafin kowa ba duk wanda ya ci karo da abunda yayi daidai dashi yayi haquri. Page *_~1~_* • ∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆• Tsoro na Allah tsoro na muhadu dashi ahanya saboda ko ba komai dai ni nasan bana iya kallon cikin kwayar idanunshi,wani mugun kwarjini yakeman ta bangare guda kuma tsareni da idanunshi masu rikitar dani dayakeyi aduk lokacinda zamu hada hanya. dukda an bashi shedar tinda ake dashi ba'a taba ganin miskili ta bangare guda kuma kamilin saurayi aduk fadin unguwar ba irin shi. Unguwar da take cikeda 'ya'yan masu kudi 'yan gata, 'ya'yan masu fad'a aji a fad'in Nigeria, da yawa yawansu ma ba a qasar sukeyin karatu ba ta wani bangare kuma sha'aninsu sukeyi da 'yan matansu 'ya'yan k'usoshin gwamnati irinsu amman duk da haka acikinsu Ya Ameen daban yake. mata dayawa suna sonshi amman shi Sam basa gabanshi Aikinshi da kasuwancinshi kadai yasanya gaba, acewarshi har yanzu ba'ayi yarinyar dazai tsaya b'ata ma kanshi lokaci akanta ba, kai shi soyayyar ma gabaki dayanta bai yarda da itaba. Menene abunso a jikin mace? Kullum tambayar da ya keyi ma kanshi kenan. (Nidai nace bakaje hannu baneba lol🤣) """"""***************""""" Ahankali nake takawa cikin natsuwata da tafiya ta mai ban sha'awa da burgewa, ni ahakan ma gani nakeyi sauri nakeyi saboda aiken da ummata tayiman kasuwa banaso na rasa adaidaita din da zai kaini duba da yanayin unguwar tamu, akwai drebobi har guda uku acikin tanqamemen gidan namu ko nace nasu amman dukda haka ummana ta haneni da shiga motocin domin kaini inda zani, a cewarta in tsaya matsayina na diyar mai aikin gidan mara galihu saboda gudun wulaqanci dukda cewa su drebobin ba zasu wulaqantani ba kasancewar mu dasu duk matsalar mu daya na wulaqanci da muke fuskanta daga matar gidan, A wajen mai gidan da babban yaron gidan ne kawai muke samun sassauci amman ba daga su ba mudin da dabbobin dake gidan gonar bangare daya daga cikin gidan duk daya muke awajen iyalan gidan in kacire mutum uku rak cikin mutum bakwai daga cikin gidan watau Ya ameen Babban Dandan Gidan a maza, afnan watau autar gidan dashi kanshi kuma uban gayyar watau mai gidan Alhj Mustapha Dambulan Ban aune ba naji nayi karo da mutum kasancewar saurin da nakeyi kuma da son kaucewa idanun drebobin saboda banaso su yiman tayin kaini din, lokaci guda kuma nayi baya zan fadi bankai ga kaiwa qasa ba naji an janyoni dakarfi har na fada faffadan kirjinshi da yake cike da haiba, lokaci guda dad'edd'en kamshin turarenshi da ke kara taimakawa wajen rikitar dani ya yiman sallama a hancina. "Subhanalla" nace ina mai ja baya dasauri amman dukda haka damtsen hannuna na cikin nashi ba tareda ya sakeni ba, "yi hakuri don Allah yaya..." "Shiiii🤫" ya katseman hanzarin bashi hakuri da nakeyi, cikin isa da rashin son magana dinnan nashi ya bude baki dakyar yaceman "is ok ya wuce amman nan gaba ki dinga kula, bakyau ana tafiya ana tinani" ya fada ahankali yanda nikadai zan iyaji dukda dai cewa dama haka yanayin maganar tashi take don in ba saninshi kayiba saima ka dauka maganar zuci yakeyi labb'anshi ke motsawa Sakina yayi tareda zagayeni ya wuce kaman ma ba shine ya gama magana ba yanzu Girgiza kaina nayi yayinda har yanzu ban koma normal ba bugun zuciyata ya qara gudu lokaci daya kuma ina kokarin daidaita numfashina domin ji nayi kaman ya wuce tare da numfashin nawa, juyawa nayi nabishi da kallo har ya shige dan madaidaicin apartment din nashi da yake cike da kyau da qayatuwa a bangare guda na gidan. Ci gaba nayi da takawa mamakin shi fal araina, na godema mahalicci na da ba aunty sauda ko nihal ce wannan tsautsayin ya faru akansu ba da na kade har buzuna,bani kadai ba ma har ummata da take cen tana masu iyakar iyawarta cewa zasuyi na bangajesu na daidaita kafada ta da tasu ubanwa ya haifeni, oh "Allah ya soni" na fada afili ina mai sauke ajiyar zuciya daidai lokacin da na daidaita kaina ta gefen titi ina mai tafiya tareda waige waigen Inda zan hango abun hawa saboda inaso nayi sauri na amsoma ummana aikenta kada mukara yin laifi akan wanda mukayi dasafe wajen Hajiya matar gidan da muke aikatau. _Muje zuwa Wannan shine mafari_ ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:20 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~* *Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat) *Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat) *Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare. Page ~2~ •∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆• *Ya kamata musan wannan gidan dakuma rayuwa dake gudana agidan* _Wacece wannan yarinyar da takema kanta ikirarin marar galihu?_ _Wanene Ya Ameen?_ _Wanene Alhaji Mustapha Dambulan?_ """""""""""""""**********""""""""""""""" Alhaji Mustapha Dambulan asalinshi dan jihar Katsina ne A wani Local Government da ake kira kankiya, su shidda ne awajen mahaifinshi da mahaifiyarshi da suke zaune cikin rufin asiri daidai gwargwadon abunda Allah ya hore masu, mahaifinsu Alhaji Isuhu da mahaifiyarsu Hajiya zuwaira suma duk yan asalin karamar hukumar kankiyar ne. Alhaji isuhu manomi ne rikakke, kuma irin attajiran qauyen nan ne saboda yana noma ga kiwo yanayi, kuma ta bangare guda yana ba mutane jari sudinga sana'a suna raba ribar, akalla mutanen da yake wannan kasuwancin dasu sunkai mutum goma koma fi, sannan yana kasuwanci na auduga da kamfanin saqa kaya dake Lagos inda dakanshi yake siyen auduga da wadda yake nomawa ya hada yakai kamfanin a bashi kudinshi yazo ya sake juyasu kafin kakar audugar ta dawo. Yaranshi maza biyu ayayinda mata suke su hudu dukda cewa ya aurar da guda biyu manyan yanzu saura biyu ke gareshi a gabanshi. Dukda yake mutumin karkara Allah ya bashi matukar tinani hankali da basira, saboda alokacin karatun boko baiyi yawa ba azamaninsu amman ahaka yace insha Allah 'ya'yanshi duka mata da mazan sai sunyi tinda shi Allah bai bashi ikon yi ba, matan na gama makarantar primary yake aurar dasu ga wadanda sukeso saboda shi babu tsarin auren dole ko hadi a rayuwarshi tinda yace shima ba'ayi mashi dole ba wannan shi yasa yake zaune da matarshi kwaya daya rak kuma uwar 'ya'yanshi duka guda shiddan,ayayinda mazan kuma suke wucewa gaba da primary Allah ya taimakesu kuma suna gamawa suka samu aiki tinda alokacin ko baka gama secondary ba ma in kaso zaka iyayin aiki kuma abiyaka albashi mai tsoka saboda alokacin kudin sunfi daraja ba kaman yanzu ba. Aisha itace zuwaira tafara haihuwa daganan sai Fatima mai bimata sai kuma Auwalu daganan sai aka haifi Mustapha. Haihuwar ta tsaya mata kusan wasu shekaru masu dan dama inda har sun gama makarantar primary dinsu sannan Allah yabata haihuwar 'yanbiyu mata aka barmasu sunansu watau Hassana da hussaina. Kyawawa ne gabadaya gidan jajir suke ga hanci masha Allah wannan shiyasa ma yayinsu mata sukeda manema har Allah yasa aka aurar dasu sai kannensu mata da ake gab da aurar dasu suma kwana kusa. Aikin da auwalu da Mustapha suka samune yayi sanadiyyar barowarsu mahaifarsu suka dawo cikin garin katsina ayayinda shi auwalu ya dogara da aikin da yakeyi kawai shikuma Mustapha dayake shi ya gado mahaifinsa sak Allah yayi mashi zafin nema sai yake hadawa da kasuwanci ya saro kaya ya dinga sararwa ga masu shaguna inda nan danan Allah ya yi mashi ludufi abun ya bunkasa kawai sai ya fara gininshi a unguwa mai kyau saboda shi bayada ra'ayin zama gidan gwamnati ayayinda shi yayanshi auwalu bai damuba ganin cewa a albashinsu ake cire kudin Ganin ya gama gidanshi dan madaidaici yasanya yaso iyayenshi su baro karkarar sudawo maraya, sukau suka kafe kai da fata alambaram bazasu bar mahaifarsu da danginsu sukoma wani wuriba subar noma da kiwonsu, saidai fa in aure zaiyi ya sanya matar acikin gidan, yayinda shikuma yace lallai ba aurene gabanshi ba yanzu ma shirin qaro karatunshi yakeyi a qasar waje amman tinda yayanshi yasamu wadda yakeso ya aura yasanya ta acikin gidan alabasshi sai su warware ahankali. Lokaci daya akayi bikin auwalu da yan biyu inda su aka ajiesu anan cikin garin kankiya shikuma Mustapha alokacin ya ma dade da tafiya k'aro karatunshi, amman a gidan da Mustapha ya gina nan auwalu yasanya matar tashi maisuna Zainab alokaci guda kuma yana cigaba da aikinshi na gwamnati. """""""""""""""**********""""""""""""""" Mustapha ya kammala karatunshi cike da nasarori ayayinda arzikinshi na Nigeria ya cika ya tumbatsa saboda koda yaje karatunshi baibar kasuwanci ba sai ya koma saro kaya irin na kasar wajen masu masifar kyau yana turowa kuma asaukake inda yakeba babban amininshi da sukeyin kasuwanci tare yana saida mashi yana tura mashi kudin yasake saro wasu. Gininshi ya farayi tanqameme acikin unguwar GRA yayinda shikuma Auwalu yake layout amman gini ne na fada aji domin fintinkau yafi wanda auwalu ke ciki ya gina apartment guda uku manya aciki yayinda shifa ya kafe akan sai ya maido iyayenshi birni suma suzo su huta tinda suma sun kawo karfi komai zasu iya yima iyayensu harma su taimaka ma 'yan uwansu mata da suke gidan mazajensu da suka fara tara zuri'a Ganin ya kammala gininshi ga kasuwanci ya habbaka ya gina manyan store store na kayan masarufi da kuma kayan electronics sai kuma motoci daya fara shigo dasu daga qasar waje manyan 'yan kasuwa da 'yan siyasa na siye ta bangare guda kuma bai daina kasuwancinshi na qasar waje ba inda har ya zuba hannun jari a wani babban kamfani a China dayake saqa atamfofi da k'era wayoyin hannu. K'arin girma sosai ya samu saboda karatunshi da ya qaro inda ya hada digree dinshi na farko da na biyu afannin qere qere da kasuwanci wannan shi yasanya gwamnati tarayya tafara bashi kwangila ta gina gidaje da masana'antu abundai sai Sam barka ba'a cewa komai addu'ar iyayenshi tana binshi tinda Mustapha mutum ne nagari maison kyautata ma duk wanda Allah ya hada shi zama dasu kuma baya kyamatar talaka ko mara shi duk daya ne awajen shi saboda yasan Allah ne mai azurtawa kuma yana azurta wanda yaso alokacinda yaso. Wannan kenan *KUBRA* d'iya ce ga hamshaqin d'an kasuwa Alhj Nura, Alhj Nura tare suke kasuwanci da Alhj Mustapha dukda ba tsaranshi bane ko kusa amman dai shi harka ta kasuwanci babu ruwanshi da wannan ta bangare guda kuma yana damawa a siyasar qasar babban dan kwangila ne da Allah ya azurtashi da makudan kudaden da shi kanshi baisan iyakarsu ba saboda yafi Alhj Mustapha kudi nesa ba kusa ba, kubra kyakkyawa ce dukda bazata gwadama Mustapha komai ba, ahaka Allah ya hada jininsu suna soyayyarsu dukda ita taganshi tace tana sonshi wanda hakan tasa Alhj Nura yima Mustapha magana, baiyi qasa aguiwa ba ya amince duba da yanzu iyayenshi babu abunda sukeso dagani irin iyalanshi kada girma ya cimmashi ahaka batare da ya tara zuri'a ba. Kubra na da wani hali na kyamatar talaka da marar galihu inda Mustapha bayason wannan halin har yana mata magana akai irin yadda yaga in yaje fira gidansu tanama ma'aikatansu bayajin dadi sai yake dan tsawatar mata lokaci lokaci, to tana dai kokarin kiyayewa saboda irin son da take mashi saboda Mustapha kyakkyawane ajin qarshe ga naira ga Hutu dukda bazai nunama mahaifinta komai ba. Acikin haka ne Allah yasanya akayi auren Mustapha da amaryarshi kubra suna zaune kalau, wannan tasa ya jama yan aikinsu kunne ya gaggaya masu halinta saboda su kula kuma suna kokarin kiyayewa. Dangin Mustapha kaf sunason kubra (kundai San yanda akeson mai kudi) iyayenshi girma ya kamasu yayinda mahaifinshi ya koma ya zauna ya barma qaninshi duka hidimominshi tinda 'ya'yan sun kawo karfi, saidai fa Mustapha ya gyara masu gida ya maidashi na zamani tinda sun k'i baro mahaifarsu ya sanya masu masu aiki da masu gadi da dreba guda daya mai suna iro suna kula dasu tinda yanzu babu sauran kowa a gabansu in ka dauke jikokinsu yaran Aisha da Fatima harma da yan biyu dake zuwar masu Hutu kuma tinda akwai ma'aikata suke kula dasu don dai hajiya zuwaira girma ya kamata don ma dai jikin nasu ba irin namu bane ba 'ya'yan yanzu. Mustapha yaba 'yan uwanshi kaf jari kuma dukansu ya tattara su bayan aurenshi sukaje qasa mai tsarki suka sauke farali harma da wasu daga cikin ma'aikatanshi dayake ya bude babban kamfanin markada qarafuna a jihar legas yayinda ya dauki ma'aikata daga jiharshi ta haihuwa dakuma saura daga saura jihohin nigeriya Ahaka Allah ya azurta kubra da samun diya mace kyakkyawa aka sanya mata suna Nafisa suna cemata feena daga ita sai Al'ameen suna ce mashi Ameen sai saudatu ana cemata saudat sai mai sunan Hajiya zuwaira suna cemata Nihal saikuma namiji data haifa Yusuf ana ce mashi Abi sai autarsu mai sunan maman Hajiya kubra watau bilkisu ana cemata Afnan. Yara ne sun taso cikin gata da kulawa,kuma ga karatun arabi dana boko gabaki daya Allah ya basu saboda mahaifinsu mutum ne mai tsantseni yaran wasuma ya tsaya ya kula dasu bare nashi, Sam bayason abunda zai bata mashi tarbiyya da karatun 'ya'yan nashi, wannan ce ta sanya ya tattara kan 'ya'yan nashi ya tafi qasar waje dasu bawai don ya raina tashi qasar ta haihuwa bane a'a saidai kawai irin yanda yanzu karatun kasar namu ya tabarbare acen yasanyasu makaranta mai kyau da ta Haddar alkur'ani dasauran litattafai, ahaka nafisa tasamu miji a cen qasar ta Dubai inda akadawo nigeriya akayi bikin kasancewar shima dan nigeriya ne iyayenshi yan asalin garin zariya ne,amman acen yake kasuwancinshi dama karatu ya kai shi kuma ya gama harma ya fara aiki da wani kamfanin kera takalma da abaya irin na mata. Gabadayansu sun gama karatunsu inda mohd Al'ameen ya karanta fannin kasuwanci da fasaha (watau dai ya gaji mahaifinshi) ya hada masters dinshi ya jona yanaso yayi doctrine dinshi ita kuma sauda tayi degree na biyu yayinda Nihal da abi suka kammala degree na daya itakuma afnan tana aji na biyu secondary wannan ne ya sanya Alhaji Mustapha ya tattara kan iyalanshi ya dawo qasarshi ta haihuwa domin qasar ta amfana da ilimin da 'ya'yan nashi suka samu Amman sun baro afnan gidan aunty feena domin karasa nata karatun, suma su Nihal da abi zasu koma idan sunso su cigaba amman alhaji yace sai sunyi aure tukunna domin ya gaji da ganinsu haka zaga zaga dasu ba aure. Inda moh'd Al'ameen ya wuce qasar america domin karasa karatunshi daya dauko ta fannin fasahar zamani domin kasuwanci ya iya harma ya fara da taimakon mahaifin nashi Hajiya kubra tana nan da halinta dakuka Santa dashi tin farko saima abunda yaci gaba domin mahaifinta Alhj Nura Allah yayi mashi rasuwa bayan haihuwar Nihal aka raba masu gadonsu, kasancewar ta na diya daya tilo ta mallaki dukiya da qadarorin da suka kara mata girman kai da dagawa domin yanzu bata jiran Alhaji wajen komai saboda itama ta mallaki dukiyarta ta agani afada wannan shi ya qara sangarta 'ya'yanta dukansu in ka dauke yaAmeen da afnan da bama ta qasar gabaki daya saidai tazo Hutu Gida na nunama sa'a alhaji mustapha ya qera masu a garin abuja suka tarkato daga gidanshi na katsina, ya ba yayanshi alhaji auwalu da ya tara zuriya shima da matarshi Zainab abun dai sai sam barka yayinda ya sake siyan fili ya k'ek'ara ma iyayenshi gida a cikin kankiyan tunda tsufa ya kamasu kuma sunki barin mahaifar tasu ya kuma Gina masu gidan gona Inda aka cigaba da kiwon dabbobi kama daga su kaji,talo talo dawisu,shanu,awakai da duk wasu nau'in dabbobi da kuka sani ya kuma bada ana masu noma tinda itace tushen arzikinsu shiyasa basu yada ta ba. 'Yan uwanshi mata duka ya gina masu gidaje ya qara masu jari kuma duk shekara sai wasu sunje hajji su da iyalansu ya dauki nauyin karatun 'ya'yan gaba dayansu kuma sunayin karatunsu cikin kwanciyar hankali wasu ma ya fiddasu qasar waje suna karatun tinda Allah ya hore mashi yanzu duk fadin Nigeria babu dan kwangila sama dashi,ya gina ma'aikatu yana daukar ma'aikata ga sana'ar motoci da qarafuna duk ya nayi,kudi dai ko ta wacce hanya juyasu yakeyi wannan shine silar arzikin Alhaji Mustapha Dambulan din kudi kenan inda ya tara tarin masoya da mahassada arayuwarshi. YaAmeen ya dawo daga karatunshi hankali kwance da tarin Alkhairai,qasar ta amurka taso rikeshi saboda kaifin hankali da hazakarshi, amman ya qiya saboda irin tarbiyyar mahaifinshi dakuma kishin qasar tashi nigeriya. *Wannan Kenan Yanzu Aka Fara* 🌹🌺~Oum-Deedat ce~🌺🌹 [8/5, 8:20 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~* *Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat) *Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat) *Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, qanwa daya tamkar dubu,Allah ya barmu tare. Page ~3~ •∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆• Muje zuwa....... Ahankali zanmaku wacece "Suhan" ya labarinta yake kuma me ya kawosu irin wannan gida dayake cike da tarin gadara, shagwaba, mutumci, halarci,dakuma miskilanci """""""""""""""""***********""""""""""""""" Cikin hanzari na siya abunda duk nasan anada bukata na baro kasuwar da tarin idanu yayiman yawa, adaidaita na hau tare da fada mashi sunan unguwar da zai kaini. yayinda muka isa nace mashi ya ajiyeni nesa kadan da gidan, sanin danayi cewa YaAmeen yana gida, kuma zai iya tambayata dalilin dayasanya driver bai kaini ba, tinda shikuma ya hanani hawan okada, acewarshi drebobin basuda amfani in har wani acikin ahalin gidan zai dinga hawa hayis, (oh ko su wanene ahalin gidan oho😵) Ilai kuwa yana qofar gidan zaune bisa darduma, yana shan daddad'ar iskar dake busowa ta sanyin marece dakuma flowers dake busowa, a lokaci daya kuma yana latsa iPad din dake hannunshi, dagani wani abu muhimmi yakeyi,cikin sanyinshi da halinshi ko wayar ma sai an yi mata Jan aji da yanga?🙄 Suf suf na wuce, wuf na shige ta tamqamemen gate din dake kofar gidan mai double, saboda har ga Allah yanzu nidai kunyarshi nakeji tun abunda yafaru dazu dani akanshi,wai nice yau kwance a k'irjin yaAmeen...k'irjin da kowa ke mararin ganin mamallakiyarshi shi, k'irjin da mata da yawa keson kasan cewa bisa shi, ni nayi imani in ka kadauke kannenshi nice ta farko da na fara kwanciya bisa shi, nima fa a tsautsayi ne ba yin kaina bane ba tinda ko magana zamuyi bana yarda in kusanci inda yake kawai ina tsayawa ne ta inda zan iya jin maganar shi Shima kuma yana k'ok'ari wajen ganin ya ma baya ga duk wata d'iya mace da ba muharramarshi ba. ( yo wa ma zai iya rungumewa wannan sarkin 'yan miskilan🤔) Da wannan guntun tinanin nashige sashenmu damin isarma da ummarmu aikenta, nima inyi maza in hada ma aunty Nihal fruit salad d'in da ta ceman tana so,wanda saboda tsabar isa da taqama saidai tayiman text din in hada mata d'in. Shi kau ta bangarenta yana lura da ita tin sa'adda napep ya ajiyeta da sand'on da takeyi kada ya ganta, bata san ta riga ta makaro ba, murmushi yayi mai kama da an sanyashi dole, domin shidai lamarin yayinyar na bashi dariya, shidai har ga Allah ba shiga lamarinta yakeyi ba, amman ya kula mahaifiyarta na iyakar kokarinta wajen bata tarbiyya, ko motocin gidan ya kula mahaifiyarta ta hanata hawa. bai gasgata ba saida ya tambayi malam mudi shugaban drebobin gidan yabashi tabbacin hakan, shikuma ya gargadesu da matsa mata kada su sanya ta bijirema umarnin mahaifiyarta, matar da yake girmamawa fiyeda tinanin kowa, yana sonta har cikin ranshi yake tausaya mata saboda ya kula akwai wani sarqaqqen Al'amari mai girma tattare da ita, matar da kuma duk duniya mahaifiyarshi batada wadda take wulaqantawa irinta, amman ko menene ya sanya ta nace ma zaman gidan? Oho! Dukda lokuta da dama yasha taddata bangaren masu aikin, ya sanya su kebe ya yi mata tayin barin aikin shi zai kula da ita da duk bukatunta batare da kowa ya saniba Amman ta kan ce mashi " karka damu muhammadu komai lokaci ne". Iyakar abunda take fada kenan tayi mashi sallama tabar wurin "Huh" 😯 ya fada tare da guntsar iska ya fesar alokaci guda yana mai kad'a kafad'a "Haka ne umma kamar yadda kika fada Allah yasa lokacin yazo mana da Alkhairi" ya fada a fili yana mai mik'ewa tare da tattara shimfid'ar tashi. •••••••••••••••••••••••••••••••••••••••• Wanene Moh'd Al'ameen? 'Da na biyu wajen Alhaji Mustapha Dambulan, kuma d'a mafi soyuwa a zuciyar Alhajin,ko dan ya gado shi ne ta fannin harkokinshi? Ko dan shine yaro mafi sauki tareda jinkai da taimakon na qasa dashi? Ko don shine kadai baya daukar irin zuga da halin mahaifiyarshi? Sau dadama ma yana mata nasiha wasu lokuttan dukda yasan ba ta dadin rai suke rabuwa ba, dukda yasan ba dauka takeyi ba, amman yana fata wani lokaci tagane gaskiya kuma tadawo kan hanya. Kyakkyawan namiji ne ingarman namiji ka fasalta duk wani kyakkyawa da kasani tau YaAmeen ya wuce shi d'an boko ne na bugawa a mujalla kuma dan gayu ne, mutum ne maison tsafta yana da ladabi sosai, bayason bacin ran iyayenshi, matashin mai naira ne domin wasu daga cikin abokanshi kan mashi laqabi da yaro da kudi..., miskili ne na gidan gaba sau dadama yana kallo anayin abu amman yakasa tankawa saboda k'yashin magana da Allah yayi mashi, kokuma yayi kaman ma baisan anayi ba, bashida business da mata mace komin kyaunki komin haduwarki Baki kai ya kalleki ba, yana da shekara talatin da biyu a duniya, idan an mashi maganar aure kaka zuwaira wadda suke kira da Hajiya kan ce akyaleshi komai lokaci ne, yayinda Alhj isuhu kan matsanta da maganar, ita ko Hajiya kubra tana ganin an matsanta ma d'and'anta ita har yanzu ma bataga matar da ta kwanta mata ba da zata iya barin d'and'anta mafi soyuwa a wajenta ya aureta ba ta zame mata suruka a ganinta har yanzu cikin masu cewa su a son YaAmeen din da wad'anda iyayensu ke son had'a su dashi har yanzu arzik'insu bai kai mata wanda zata iya had'a zuriya dasu ba,balle tana ganin Al'ameen dinta saurayi ne na nuna ma tsara, yaro ne da kowacce budurwa kan so ya zame mallakinta. Tanason suruka 'yar babban gida, 'yar masu naira, masu fad'a aji a fadin duniya. bama Nigeria kadai ba, in haka ta faru ita fiye da burinta ya cika saidai abunda ba'a rasa ba, tinda kishiyace mata ke gudu ita kuwa tasan ta wuce wannan level din koma kawo wannan tinanin a ranta batayi. Dukda halin YaAmeen na miskilanci hakan bai hanashi tausayi da jin qai na talaka ba, sau da dama ma zaiga su saudat na wulaqanta masu aikin gidan ya tsaya ya tsawata masu, saboda akwai ma lokacin da ya taba marin nihal saboda ta watsama wata mai gyara mata daki ruwa, (tin ma suna farkon dawowa k'asar, kafin zuwan su suhan gidan) saboda tayi mata mopping din daki, bata kunna air conditioner ba ta sanya mata room freshner shine ta taddata harabar gida ta watsa mata ruwa, akayi sa'a akan idanun YaAmeen din ne,aikau batayi aune ba ta ji saukar mari a kuncinta, wannan ne ya sanya sukejin tsoronshi, saboda ko sun fada ma hajiya kubra bata mashi fad'a sosai saboda irin son da take mashi. Da wannan ne ma'aikatan gidan suke samun salama indai yana qasar idan kuma yayi tafiya suke kaffa kaffa saboda sanin halin 'yan gidan. ======================= Da sallama na shiga tanqamemen falon da ya lashe kujeru saiti hudu acikinshi,dukda nasan babu mai jina kuma da wuya ma ka tadda wani a falon, shima a hakan wai an ginashi ne saboda sauke baqi, dukda hajiya kubra ta mai dashi na sauke baqin da sukazo daga kauyen su alhajin, amman batare da saninshi ba.dukda babu kowa dake zaman falon, dukda haka sai na shareshi kullum nayi mopping, wannan shiyasa kullum nake kwana da uban ciwon jiki, wani corridor mai zurfin gaske nabi, banyi wata tafiyaba na tadda kofar falon Nihal da saudat din, kwankwasawa nayi dukda nasan bazan samu amsa ba amman haka dokar take garemu dukkanmu ma'aikatan gidan, kuma ko ma a musulumci haka dokar take shiyasa ma abun baya b'ata man rai. sallama nayi tura qofar ahankali na shiga cikin salon tafiya ta (kamar ta masu akwai😜) falo ne madaidaici jere da kujeru kyawawa kalar sararin samaniya dukda cewa komai na falon haka yake, kama daga su labulaye Chinese carpet dakuma tiles din da ke malale a dandamalin falon. K'ofofi biyu ne rak cikin falon, karkatawa nayi nabi ta gefen haguna inda zai sadani da asalin dakin Nihal din, hannuna dauke ba bowl na ceramic cike da fruit salad daya sha madara da zuma, nayi sallama a dakin bayan na murd'a handle din dakin. Kwance na hangota nutse cikin gadonta da zan iya cewa yafi auduga taushi (🤔 oh ko ina suke samun irin wadannan katifun?) Ni kuma nace kaji suhan da k'auyanci😉. Hannunta rike da waya k'irar Samsung a hannunta tana waya ga wata ahannunta daya k'irar iPhone tana latsawa,dagani dai da wannan dan gayen saurayin nata takeyin waya. "Aunty Nee gashi" nafada ahankali saboda kada tace nayi mata ihu a kunne, ko kallona batayi ba balle tayiman magana,dama nasan hakan zata kasance, in kuma ban mata maganar ba ba zata sha ba, kuma nayi laifi, sai an hukuntani, wannan ce ta sanya nake cemata gashi tinda ni ke qasa da ita kuma nema nakeyi. Takawa nayi na ajiye mata a kan wani qaramin stool dake gefen gadon mai kyau kaman da gold aka qerashi tsabar kyau, na juya da nufin ficewa a d'akin. "Hey" abunda naji tace kenan cikin maganarta mai cike da shagwaba-shagwaba gadara gadara, isa isa, tinani na ya katse lokacin da naji tace "ki wanke mun toilet dina" abunda tace kenan ta cigaba da wayarta saboda nidai banajin me take cewa a wayar saboda munada dan tazara. Gaba na ne ya fadi tino danayi naga text din aunty saudat a waya ta,itama tanason meatpie dashi zatayi dinner gashi kuma yanzu lokaci yakusa qure wa inda Allah ya taimakeni ma akwai means meat a fridge..... "Ko bakiji bane?" Ta fad' a sound so harsh "To aunty" nace tareda shigewa toilet din wanda nidai a iya dubana na tsanaki babu abunda toilet din yayi, saboda dasafe na wankeshi kuma ita kadai take using abunta kawai tsabar mugunta da son sanya aikin. Agurguje na gama mata na fito tareda shigewa kitchen din da yake main falour din na gasa ma aunt saudat meatpie din tareda hada mata meant juice,saboda nasan k'a'ida duk dare saita sha shi,wai saboda batason tayi k'iba. Fitowa nayi tareda zuwa na sake wanka, nayi alwala na kabbara sallah tinda anriga anyi magriba ban tashiba saida akayi issha'i, na fito da niyyar zuwa inyi serving dinsu wajen cin abincin da ummata ce ke girka masu wai basu iyacin abincin kowa dagani sai na ummana shiyasa ma mu dakinmu daban ko acen boys quarters din masu girkama 'yan cikin gida abinci da gyara masu sashensu, wannan ka'ida hajiya kubra ce ta sanya ta dole dukansu suke haduwa, wajen yin breakfast da dinner ko da kuwa Alhaji Mustapha na nan hardashi ake haduwa wajen cin abincin Ummana ce ta katseman hanzarin barin sashen namu da nakeyi "mamana ga abincinki nan kizauna kici naga yau kaman a gajiye kike ni zanje na zuba masu abincin" ta fad'a tana mai kallona cike da tausayawa saboda tasan irin yanda yaran gidan ke gallaza man ta wajen sanyani girkinsu da aikace aikacensu na babu gaira babu dalili, "No umma banason ayi maki abunda zai bata maki rai, ko kinje zasu maki wulaqanci ne kiyi zamanki yanzu zan dawo ai YaAmeen yana nan basa min wulaqanci sosai in yana wajen jiya ya dawo k'asar kinsan" nafada ina kamo hannuwanta, gyada man kai tayi tareda cewa "Allah yayi maki albarka d'iyata yanda kikeyi man Allah ya baki maiyi maki kema ya baki miji nagari, kicigaba da hakuri watarana sai labari" "to umma nafada" tareda wucewa ina cemata "kije kici abinci kisha magani ki kwanta yanzu zan dawo insha Allah" "to" tace tareda komawa dakin namu, nikuma na wuce dasauri domin nasan suna cen suna jirana. Ilai kuwa a zaune na tadda su a dinning area din dayake yakusa girman wani qaramin gidan, kaitsaye kitchen din da yake cikin dining area din na shiga tareda kinkimo manyan warmers da plates plates nazo ina jerawa, har na gama na fara serving dinsu ko kallon fuskokinsu banyiba, saboda nasan ko kalla nayi saqon harara ne zan samu, masalan daga 'yan matan gida buyu kyawawa da suke jin Kansu babu ya su a fadin Nigeria, shagwaba kawai suke zubawa, yayinda Hajiya kubra ke biye masu tanata murmusawa irin na manyan hajiyoyi da suka yarda kuma sukejin sunkai ko ina, labarinsu ya baza ko ina a fadin qasar tamu, abie ne ke latsa waya abunshi ta bangare daya yanada kyalkyala dariya, shi ko YaAmeen baima wajen, ahaka na gama serving nasu nayi masu sallama zanbar wajen, Ya shigo fuskar nan tashi murtuk kaman kullum yake takowa cike da izza da kamala kai kace dandan sarkin kano ne sanusi lamido🤪 "Suhan zo kiyi serving YaAmeen" dayake itama hajiyar haka take kiranshi dashi......"No am ok green tea kawai zansha" ya fada kaman bayason magana yayinda sauran qannen nashi duk suka natsu suna cin abincin su bayan sunce "bigboo u are welcome" "OK ki jira mu gama ki tattara wurin" ta fad'a tana mai faracin abinci, "to Hajiya na fad'a ina mai dan rissinawa irin na biyayya sannan na juya na wuce babbanb falo domin jiran su gama din tinani fal araina, " Saudat had'a man Lipton din" naji ya fad'a daidai lokacin da nake idasa ficewa daga dining area din. Sun shafe awa biyu kafin duk suka tashi tareda yima juna sallama hajiya ta haye sama inda abi ya shige sashenshi suma su nihal suka shige nasu sashen sai kuma Allah ya kaimu. Tattara plates din nayi nakai kitchen na juya zan koma dauko sauran, naga ya shigo da wasu bance komai ba saima dukar da kai danayi na jaye na bashi hanya ya wuce cikin kitchen din nima na fice dan dauko wasu, ahaka ya tayani kwashe kayan dukda hankalina bai kwantaba saidai nasan cewa hajiya na iya saukowa taganshi aiko da na kade har buzu na, bansan me yasanya shi aikata hakan ba yau lokutta dadama naga ko kallo ban isheshi in ka cire 'yan kwanakin nan da yake yawan bina da ido, shima na dauka hakan na da nasaba da tausaya wa duk wani mai aiki ne na gidan daidai da masu sharar lambu, nikau ta bangarenta baisan wata irin kacha bace yake sanya wa yana daure illahirin jiki da jijiyoyon jikina ba,ba bazai hantareni ba amman ko kallo ban isheshi ba, babu fuskan tambayan yasanya naja bakina na tsuke, na isa wajen sinc din ina dauraye abun da suka b'ata naji maganar shi a bayana don har ga Allah na dauka ya fita. Wannan tasanyani zabura na juyo mamaki fal a raina wanda har saida ta bayyana fuskana Wace irin mai sa'a ce yau ni?🤩 ni suhan ce yau YaAmeen ke cewa zaiyi magana dani? Tau wacece irin magana? Kodai wani laifin nayi mashi? Kodai bai hakura ba dazu dana tureshi? Ko dai........"Ko baakijii ba ne? Nace inaso muyi magana" ya fada hankali kwance da maganar nan tashi ta rowa da muryarshi mai kama da goge a cikin kunnen 'yanmata "Too yaya" na fada a ahankali cikin dardar tareda juyowa na fuskanceshi zuciyata kaman za tayo tsalle ta fito waje, saboda tsabar kad'uwa Guntun murmushi yayi iya lebo shi aganinshi nan ya k'okarta hakan sai tasanya kyaun shi ya k'ara fitowa afili kasancewar ba halinshi bane ko da murmushin amman ko baiyi ba kyaun shi na d'aya daga cikin abunda ke fizgar yanmata. Kallona yayi na tsawon second biyu, gamida gyara jinginar da yayi da cabinet ya motsa bakinshi ahankali kaman mai maganar saidawa ya fara da cewa......... ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:20 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~* *Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat) *Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat) *Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare. *Page* ~4~ °^^^^^^^^^^^^° "Ajinki nawa a makaranta?" Ya jefa man tambayar bazata. A d'an firgice na dago ina kallon shi, gami da ɗan zaro idanu na, da sau da dama na sha jin ana cewa kaman na mai jin barci amman suna da girma sosai,tambayar ce ta zo man a bazata, ko da alama ban taɓa kawo tinanin magana makamanciyar irin wannan zata iya shiga tsakaninmu ba; "na'am, ni?" Na Maida mashi da tambaya a ɗan firgice kuma cikin sigar mamaki, Shiru yayi na wani lokaci, kaman ma baya da alamar sake tanka mani, nikuma alokaci guda tambayoyi suka ziyarci kwanyata, har banma san mun shafe kusan minti biyu a haka ba, Yayinda shikuma ya kafeni da idanunshi masu kama da na wanda soyayya taci ta cinye😜 "Banjin akwai wani da nake magana dashi a kitchen dinnan da ya wuce ke; Ai ina tinanin mu biyune kadai a nan ko?" Ya faɗa a gajiye kaman, wanda akeyi ma dole, "Na gama makaranta. " Na fada a gajiye ciki-ciki ina mai gyara tsayuwata, Tare da janyo hijabi na, na rufe gefen fuska ta, saboda kallon da yake yi man yana distracting din attention dina; Jina nakeyi kaman a gaban miliyoyin mutane, kai gara ma ace a kotu nake, da sainafi sake wa, Da ace a gaban mutum nake kaman YaAmeen muna magana dashi one on one. 'Yar guntuwar dariya yayi, "Wow kina fadin har kinyi degree da masters, A hakan nan yanda kike yar mitsitsiya?" Ya fada yana mai nuna ni da duk kan hannun shi yana sama da ƙasa da su saitin Inda nake tsaye, Da wani yanayi, wanda nidai nakasa ganeshi; don bazance zaulaya ba don nasan ba halinshi bane yin hakan. Sai a lokacin nagane kuskuren danayi,dan zaro idanu nayi alamar wayyo Allah, Gami da Jan sauran hijab dina, na ruge fuska ta ruf, ina dan mai sakin ɗan k'aramin murmushi; A hankali nace, "am sorry secondary nake nufi yaya" "OK good " ya fada a gajarce, Yana mai ƙara nazarinta, ko buƙatar da yake da ita zata samu karb'uwa awajenta? "Ina so kici gaba da makaranta, domin zaman ki a haka kina wahala ba abune mai dad'i ba; ko babu komai ilimi yanada dadi, zaki taimaki kanki ki taimaki ummanki" Ya tsagaita yana mai zura mata idanu da ke taimakawa wajen ƙara ruɗa ta; Domin yaga yanda zatayi, Nikau bansan lokacin da nabude fuskata ba gabaki daya, ina mai sakin murmushi har siririyar wushiryar dake saman hakora na ta bayyana. "amman kije ki shawarci ummanki, kuma ina so maganar ta tsaya iyakar ni, da ke, da ita; Don bana so wani ya sani kaf gidan nan, idan ta yarda sai ki kawoman takaddunki, da kuma zabin makarantar dakikeso kiyi da abunda kikeson karantawa, kibar sauran maganar a hannuna. Kome zamu ji, ko zaku gani, Ku kauda idanunku gabaki daya, Babu ruwanku a ciki, Ni nace zan yi, kuma insha Allah zanyi;" Yana gama fadar haka ya juya, Yana mai barin tanqamemen kitchen din, da kai ka rantse da Allah ba'a Nigeria yake ba. Dakallo na bishi, a yayin da kwalwa ta ta cunkushe, "tabbas tabbas mafarkina zai tabbata, tabbas lokaci yayi; Alhmdllh naketa faɗa, a cikin raina, saboda na ma rasa tinanin da zanyi, bayan wannan; Juyawa nayi, gami da ci gaba da aiki na. A gaggauce na gama na rufe kitchen din, gami da barin part din baki daya zuwa namu, Amman zuciya ta cike da tarabbabi, domin nasan halin umma ta, Sannan ni na san kafin in dosheta da maganar, Sai nayi nazarin abunda zance mata tukunna, Don na san ta da gudun duniya da abunda ke cikinta balle wulaqanci irin na hajiya kubra. Ko da na isa part din namu, Na tadda umma ta, tasha magani amman takasa yin barci, saboda taga na dade har wajen karfe goma da wani abu, Alla Alla take yi, ya kasance lafiya, Gashi ko abinci na ma ban ciba, ina shiga kuwa na taddata zaune bisa sallaya. Allah sarki umma ta, Mace kamila mai gudun duniya, Mace mai ibada, da rashin hayaniya, Amman dukda wannan halin nata, hakan baisa Hajiya kubra ta ɗaga mata ba, Ni gani ma nakeyi kaman babu wad'anda ta tsana irin mu acikin masu aikin dake gidan, Wanda munfi mu goma sha wani abu, ummata ce ta katseman saqa da warwarar da nake tayi cikin zuciya; "lafiya dai ko mama na?" ta faɗa tana mai miƙewa a hanzarce, sannan ta ci gaba da magana cikin dan firgici kaɗan; "Naga dare yayi sosai, ya kamata ace yanzu kin kwanta ki huta hakanan" Ta faɗa cikin sanyinta, mai sanya ni natsuwa, duk da a ɗan firgice take; Kome nake yi, ko ban fad'a ba, son da ummata keman yafi wanda nakeyi mata, Duk da kau a duniya babu wadda tafi soyuwa a raina kamanta, Tinda ita kadai na sani, ita kadai na tashi na gani , ita ce uwata, itace ubana, ita ce yayata, abokiyar shawara ta kuma, ta fanni daya kuma abokiyar wasa ta; "Ina hankalinki yake ne ummina? Ina ta magana kinyi shiru" ta faɗa tana kamo hannuna, bansani ba ashe har ta nade abun sallar ta iso inda nake tsaye daga bakin ƙofa a tokare. "Umma saida najira suka gama sannan na wanke kayayyakin kinga gobe in Allah ya kaimu mun rage aikin;" na faɗa, ina mai kama mata hannu nima, muka zauna gefen katifar tamu dake yade a tsakiyar dakin. "ga abincin ki tau, maza kici ki kwanta, kinga karmu makara gobe dasafe in Allah ya kaimu banaso kullum muke b'atawa hajiya rai;" ta faɗa tana jawoman kwanon abincin. Kwanon silver ne amman tsaf yake, kaman sabo sai sheqi da walwali yake yi, kaman yau aka budeshi a leda, Allah sarki ummana akwai tsafta, dakin namu ma sai k'amshi yake yi, an goge tiles dinnan sai daukar ido yake yi, abunka ga fari, dakinmu tsaf yake babu tarkace da karikitai, in ka cire katifarmu, sai labulaye da wani teburi a gefe, inda muke ajiye daddumar sallah tamu, da sauran litattafan addini himili guda, kasancewar ummata tayi karatun addini mai zurfi, sai take k'araman duk bayan sallar subhi, akwai wardrop ta bango a dakin, wannan shi ya tak'aita mana tarkace, tinda ba yaro ke garemu ba, kwata kwata ma babu yaro a gidan, kowa da locar ta inda ni biyuma ke gare ni, kasancewar guda uku ce a dakin, amman ajere suke, sai ummata ta dauki daya, tabar man biyu saboda ni budurwa ce zan fita karikitai. Abincin naci, naje na daurayo bakina na cenza kaya zuwa kayan bacci, muka kwanta umma tayi mana addua muka shafa kowa ya juya cikeda tinani kala kala. Nikam ta bangare na banyi bacci ba, amman ummana tayi baccinta saboda maganin da tasha, kuma ko ba hakaba, ita bata kwanciya da damuwa ko haushin wani a ranta, takance ba'asan gawar fari ba hakanan kaje lahira da haushin wani duk abun da gaƙuri bai bayar ba ai rashin shi baya badawa. Gari na waye wa muka gama komai, kama daga salla, karatu, da wanka; zuwa karfe bakwai, kowa yayi shirin fara aiki kaman yanda yake a al'adar gidan namu. Amman mu bamu kai ga fita ba, sabo da ƴan cikin gidan ma basu kai ga tashi ba, kuma ina so in yima umma ta maganar karatu na; sai dai ina zullumin tunkararta da maganar, sabo da na san halin umma ta sarai, wani d'an qaramin yak'i ne gabana, Amman duk da haka hakanan zan daure in tunkareta da maganar domin ga dama ta samu, kuma ko ba komai hakan ci gaba mu ne ni da ita baki daya, fata na dai da addu'a ta Allah ya ɗora ni akan ta, ta yadda ta amince mani, sabo da wannan karon ina tsoron YaAmeen ya ji haushi ya janye burin taimakon mu a ranshi, saboda ba wannan ne karo na farko ba da umma ta ke daƙile shi akan duk wani burin taimaka mana da yake yi, Wanda shi a ranshi har ga Allah taimakon ummana din ne kan ingiza shi ga hakan saboda rashin hayaniyarta da biyayyar ta ga iyayen nashi. ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:21 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~* *Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat) *Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat) *Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare. *Page* ~5~ °^^^^^^^^^^^^° Bayan mun gama karyawa ne, muna zaune a ɗaki ni da umma ta,Tana yanke farcen ta na hannu, Yayin da ni kuma nake zaune gefen katifar tamu da littafin hisnul musleem a hannu ina karantawa. Rufe littafin nayi tare da maida shi ma'ajiyar shi, na dawo na zauna daf da ita, tsawon second biyar na dauka ban iya cewa ƙala ba, tabbas abinda nazo mata dashi ni kaina na san mai girma ne, to sai dai ba yadda na iya, shahada nayi na bude baki na a hankali nace; "Umma don Allah ina so muyi magana dake" cike da mamaki ta ɗago idanun ta tare da tsare ni da su, take guntun tunani yazo a ranta, wacce irin magana ce wannan da maman tata bazata iya tunkararta kai tsaye da ita ba? Koma dai menene tana fatan ɗiyar tata ba zata zo mata da wani abu akasin tunani nata ba; "ina jin ki mama na" ta bani amsa tana mai dakatawa daga yanke farcen gami da sauke hannun kan cinyoyinta. "Umma don Allah ki saurare ni kuna ki fahimce ni, wannan karon izinin ki nake nema; ki duba halin da mu ke ciki na rashin sanin madafa, dama ce ta zo mana da zamu fita daga cikin wannan ƙangin bautar da mu ke ciki, dama ce da zata sanya mu dogara da kanmu har ƙarshen rayuwarmu." Tinda na fara magana ta tsira man idanu ba tare da tace kanzil ba, sai dai ni bazan iya karantar abunda ke cikin zjciyar tata ba; Ganin yanda ta kafe ni da idanu ya sanya ni sauke kwayar idanu na ƙasa ina mai murza yatsu na suna bada sauti ƙas, ƙas. " Uhm, ina jinki mama na, wannan wacce irin dama ce? Ina fatan dai zaki zo mani da buƙatar da kika san zan iya amincewa da ita, ba wadda kika san za ta iya sanyawa ranki ya ɓaci ba" Tinda ta fara magana bugun zuciya ta ya ƙaru, fargaba da zullumin yadda zata ɗauki maganar suka baibaye ni, dakyal na bude baki na cigaba da cewa; "Umma jiya ne Ya Ameen yace ya kamata in koma makaranta domin yana so mu zama masu tallafar rayuwarmu da kanmu, kuma yace in nemi izinin ki na bashi takaddu, da kuma zaɓin makarantar da nake so, tin jiya nake zullumin tunkarar ki da maganar, domin ban san yanda zaki kalli abun ba, wallahi umma ba nice nayi mashi magana ba, shine da kan shi ya same ni kitchen ina wanke wanke ya man maganar; Idan dai ba idanu na bane suke man ƙarya ba, wannan. Karon kallon da ummar tawa take man ya cenza salo, ya rikiɗa ya koma kallo ne mai cike da gargaɗi da kuma tuhuma; kafin ta bude baki ta cigaba da Cewa "Masu gadi ma da drebobi ban hanaki magana dasu ba? Balle Al'Ameen ɗanɗan masu gida? Miyasa kike son cenza hali ne Hauwa'u" A firgice na ɗago ina mai kallon ta cikin tsananin firgici damuwa fal a raina, yau ni ce umma ta ta ke kiran sunana kai tsaye; me ya sanya ni? Me ya kai ni? Me ya ja mani? "tsabar son zuciya da hangen gaba" zuciya ta ta bani amsa, tini kwalla suka soma shatata daga idanu na, wanda tini kalar su ta juye daga farare tas zuwa jajaye; Hannun ta na kamo gami da runtse su sosai sannan naci gaba da magana ba tare da damuwa da goge kwallar ba, gara na barta ta zuba ko zanji saukin raɗaɗin da zuciya ta keyi mani, "Don Allah umma kiyi haƙuri, wallahi tallahi bani na mashi magana ba, iskeni yayi har kitchen, kuma daga ni sai shi muka yi maganar, umma kiyi haƙuri in na bata maki rai insha Allah bazan sake ba" Na Faɗa wani tuƙuƙi na taso man daga cen ƙasan rai na, "Ni baki ɓata man rai ba Mama na, gani nayi kawai kaman baki gudun wulaƙanci daga wurin hajiya Babba ne, sanin kanki ne da ta ita ne ma da yanzu mun bar gidan, sabo da Alhaji ne kawai muke zaune har yanzu, tau minene yasa ba zamu kiyaye ba? Tabbas kinsan idan hajiya taji zaman mu a gidan nan ya ƙare kenan, zata ce ne mun mallake mata yaro gashi har yana wahala akan mu, kinsan kuwa ni bani son abunda zai haɗa ni da su dukkan su balle rayuwa ta ta ɓaci hakanan" Kuka na naci gaba da yi duk da na ji ta kai aya, Amman zuciya ta na kwadaito man samu ne gashi umma ta na lasa man ɗanɗanon rashi a baki, ban gama maganar zucin da nake ba naji ta cigaba da cewa "idan ya sake maki maganar kice mashi na hana ki, kuma nace mun gode da halacci da irin ƙoƙarin da yake yi a kanmu Allah ya ƙaro buɗi da arziƙi" Tana gama faɗar haka ta zare hannun ta ta fice a ɗakin, ita kanta cen ƙasan zuciyar tata bata yi mata ɗaɗi, kukan da suhan ɗin ke yi mata yana taɓa mata rai, sai dai babu yanda ta iya wulaƙanci abu ne da kowa ya kamata ace ya guda ba ma ita kaɗai ba, suhan ɗin yarinya ce dududu bata wuce shekara ishirin ba, bata fata wani abu ya shiga tsakanin ta da Al'Ameen, a matsayin ta na babba ta san abu ne mai sauƙi, domin daga tausayi komai ke chanza wa, dukda ta san Al'Ameen ɗin ya fi ƙarfin ɗiyar tata, sai dai ita ba zata so hakan yayi sanadiyyar ɗan zaman da suke yi a gidan ya zo ya gagare su ba. Ni kau tinda umma ta fice ta bar ni a gurin zaune, fashe wa na kuma yi da kuka tare da faɗawa na kwanta kan katifar tare da kifa kai na, na saki wani irin kuka mai tsuma rai, maraici bai yi ba, mahaifi daban ne a rayuwa, yanzu da yana da rai ko kusa bazan fuskanci irin wannan rayuwar ba, tabbas ummata akan gaskiyar ta take, Hajiya babba muguwar mace ce, yanzu zata sanya a ɓatar da kai a doron ƙasa indai ka nemi shiga gonar ta. Dukda yace shi kadai zai yi hidima ba tare da ta sani ba, wannan tunani shi ne, Hajiya mace ce mai cikakke iko, komai akeyi a gidan a tafin hannun ta yake, akwai 'yan gulma masu kai mata rahoton duk abin da yake faruwa a gidan; Ko ba haka ba ma ni mai ya shiga kaina? Mu da muke a ɗosane, sauran ma'aikatan gidan ma duk sun fimu galihu, me yasa nake hangen gaba ne? ALLAH ne kaɗai yasan yanda zai yi da mu, mu bar mashi komai, karatu na ba dole bane, ni cikakkiyar marainiya ce da ban ma san ya kalar mahaifi na take ba, ban taso na ganshi ba, ban taso naji umma ta na maganar shi ba, kuma bata so ina mata maganar shi, shin mai zai sa in ci gaba da damun kaina? A hankali na rage sautin kukan nawa, gami da goge hawayen, lokacin da idanu na suka kai kan agogo dake maƙale a bangon ɗakin namu, 09:30am, a hanzarce na tashi na shiga bayin dakin namu na wanke fuska ta, ban damu da in shafa ma fuskan komai ba, wa zan ma kwalliya? Rai na a cunkushe yake; Ƙofar ɗakin namu na fito na tadda umma ta tana tattara sharar tsakar gidan da su sauran ma'aikatan dama basa yi sai ita ko ni, sun ma bar mana mu kadai, a cewarsu ai dama aikinmu ne mu share tsakar gidan tinda ni ke sharar cikin gida, hakan ma baya damunmu in da sabo mun saba. Wata daga cikin amintattun Hajiyar ce ta zo wucewa zata shiga ɗakin nasu da ke kallon namu, watsa mana wani irin kallo tayi gami da cewa, "maman Suhana sannu da aiki, Hajiya babba tana neman ku, ya kamata ku tafi domin sun tashi tun ɗazu" "To uwani, mun gode,an tashi lafiya ko?" umma ta ta maida mata cikin sakin fuska, domin duk kwakwarka ba zaka iya karanto ɓacin rai a fuskan umma ta ba, ko da kayi don ka ɓata mata rai tana tura maka aniyarka ne a wuce wurin; taɓe baki tayi gami da cewa "lafiya" ta shige ɗaki abun ta, muna iya jiyo tashin sauti tsokin ta a hankali. Juyowa Ummata tayi ta kalle ni cikin sanyi ta tace "Mama na wuce kije gani nan zuwa, sai dai kada ki manta da maganar mu kinji ko?" "To umma" nace gami da juyawa na shiga ɗakin ɗauko hijab ɗina. ******************************* Yau dai haka na wuni yin aiki sukuku,duk wata hanya da zata haɗa ni da Ya Ameen na toshe ta, ina gama aiki na na koma sashen mu na kwanta yayin da umma ke can tana aikin abincin ranan su, bata bari in taya ta, sabo da Hajiya magana take yi, cewa take kowa yayi aiki shi, ƙarar ƴar mitsitsiyar waya ta rakani toilet ce ta katse man tunanin da nake ina ta juye juye bisa katifar tamu; Massage ne ya shigo man aunty saudat naso in raka ta shopping, wannan ne ya sanya na miƙe gami da shiryawa domin dama na saba dukan su biyun nice ke raka su, duk lokacin da muka dawo suna kwashe tsofaffin kayan nasu su bani kasancewar su basu da jiki ni kuma ina da ƴar murjewar jiki, dukda sun girmeni sai size din namu yazo daya, haka kuwa aka yi muna dawowa ta tattara tsofaffin abubuwa da bata so ta bani wanda ni a waje na kaman sababbi suke. ******************************* A haka sai da na shafe kwana uku ina wasan ɓuya da Ya Ameen, sabo da bana so magana ta ƙara shiga tsakani na dashi balle ya tado da maganar karatun nawa, ni a ganina in yaji shiru yasan umma bata barni bane kawai, Daman abunda na sani shine halin yaya Al'Ameen, ba zai man magana ba indai ba nice nayi mashi ba, wannan tasa na saki jiki na ci gaba da ayyuka na yanda ya kamata, na cire ma raina komai da tsammanin zanyi wani karatu a rayuwa ta, na sani dama sau daya take zuwa a rayuwa, ni tawa damar ta zo kuma nayi sake da ita shikenan kawai duk yanda Allah ya so yayi dai-dai ne. Tafe yake cikin salon tafiyar shi ta ingarman namiji, dan ƙwalisa, ga natsuwa, kamala cike da kwarjini; tabbas Al'Ameen ya kai namijin da za'a kalla a sake kallon shi, fuskar shi cike take da annuri dukda kasancewar shi ba ma'abocin murmushi ba, hakan bai hana tsantsar kyawonshi fitowa ba. Fari ne tas yana da tsawo daidai misali jikin shi ya dace da murzazzar fatar shi da take cike da gargasa kwance luf kai ka rantse bata taba shan zafin rana ba, yana da dogon hanci sosai domin ya dauko kyaun mahaifin shi da mahaifiyarshi duk a cikin su shiddan ya kere su a kyau da haske dukda suma suna da nasu kyaun, bakin nan nashi kuwa kaman gidan tsutsa gashi kalar maroon mai haske, kai kace jambaki ya shafa sannan ya goge, sam baya da girma sai dai sajen da ke gewaye da fuskar ya ƙara ƙawata fuskar, sam baya da sanƙo wannan ne yasa gyaran fuskar ya fitar da ainahin kyawon fuskar dimpul din shi na dashe das a gefen fuskar shi na hagu wanda tasa ko bai motsa fuskan ba kana iya hango kwarin shi kwance a kan fuskar shi, Ya Ameen ba dai miskilanci ba. Sanye yake da farar riga T-shirt ta polo da farin wando na lallausan jins ɗan kamfani gucci watau kayan botique, ƙafar shi Sanye da farin takalmi samfurin adidas, ni kaina mai Rubutun takalmin ya tafi da imani na, hannun shi riƙe da wayar shi samfurin Apple Phone, tare da sun glass ɗinshi sai makkulin motar shi ƙirar Benz, yana ɗan kaɗa shi a hankali. Waya yake amsawa cike da natsuwa yake taka wa a hankali, kai da ganin shi kai kasan ba RAGGON NAMIJI bane. (littafin Maman mamy) Falon ya shiga da sallama ɗauke a bakin shi Amman in ba kai da kake kusa dashi ba ba zaka san yayi magana ba, kai tsaye wajen da hajiya kubra take hakimce ya dosa, a hankali yake taka wa sai dai cikin zafin nama, irin na cikakke namiji, katse wayar yayi daidai lokacin da ya isa daf da inda take zaune saman sofa. "MOM" Ya faɗa daidai lokacin da yake zama kusa da ita, "Good morning Son" ta faɗa cikin murmushi mai nuna isa a duk lokacin da tayi shi, sam ba zata iya ɓoye son da take yi ma yaron nata ba, "Morning Mom, How Was Your Night" ya faɗa yana mai ɗan zamewa ya kishingiɗa a saman sofar, "Great dear, Hop there is nothing wrong?" ta maida mashi da tambaya. "Nothing Mom But i want to enrout to china today" ya faɗa da ƴar damuwa a fuskar shi, "Wat? Hop dai lafiya son" "Lafiya Ƙalau Mom, kayan da nayi order ne an samu matsala ne wajen shipping nasu so i need to go there, domin in san matsalar da aka fuskanta sabo da kaya ne na manyan kudi, gashi costomers sai magana suke yi sun ƙagara a basu kaya" "Well Allah ya kiyaye hanya, fatan dae kayi report wajen aiki?" ta faɗa tana dafa kan shi kaman ƙaramin yaro; "Yes Mom ba wani matsala bari naje sai munyi waya, yanzu muka gama magana da Dad ma shima yana hanya Amman ba zamu hadu ba sai dai na dawo, ban san tsawon lokacin da zan dauka ba acen" ya faɗa a gaggauce yana mai miƙewa gami da gyara zaman rigar shi a jikin shi, bai jira cewarta ba ya fice daga falon, yayin da ita kuma take bin shi da kallon ƙauna irin na uwa ga ɗanɗa mafi soyuwa a rayuwar ta, tana mashi addu'a da fatan nasara domin dai ita idan akwai abunda ta tsana a rayuwar ta tau bai fi ganin ɓacin ran Al'Ameen din ba. ***** A bakin dry centre na gidan muka haɗu ina shanya cottons na goge goge, aikina nake don ni har ga Allah ma ban kula da tahowar shi ba, tinani na ya tafi ga tinanin da ya zame man abun ci, abun sha, a kullum watau tinanin mahaifi na. Ƙamshin turarenshi ne ya man sallama, yayin da idanunu na suka gaza juyawa su kalleshi, gaba daya naji an zare man lakkar dake jikina, jinin jikina ya katse ya ci gaba da gudu cikin jiniyoyin jikina, domin dai in ban manta ba kwana uku kenan rabon da in sanya shi a idanu na, ni na ma dauka ko baya ƙasar ne kwata kwata ma; Tinani na ne ya katse daidai lokacin da ya matso daf da inda nake tsaye "Hey what are u doing here?" Haka naji kunnena ya faɗa man, ɗan rusunawa nayi a hankali nace "Ya Ameen ina kwana?" "Lafiya" ya bani amsa a taƙaice cikin salon maganar shi da ke ƙara mashi kwarjini a idona, "ya maganar mu ne ta rannan banji kince komai ba" ya faɗa yana mai tsare ni da idanun shi masu ƙara ruɗa ni, ɗan kauda fuska ta nayi, sabo da bana so mu haɗa ido dashi. "umma ta ta hana ni tace kuma nayi maka godiya ga irin ƙoƙarin da kake yi a kanmu Allah ya saka da alkhairi" na faɗa ina mai sadda kai ƙasa domin nima na san abun ba zai yi mashi daɗi ba; "its ok" Ya faɗa yana mai wucewa ba tare da ya tsaya ƙara jin wani abu da zai fito daga bakina ba, Ni din ma banyi niyyar ƙara tankawa ba, sabo da na san bani da kuma abun cewa. Kwalla ce ta taru a idanuna, nayi saurin goge ta ina mai fiƙi fiƙi da idanu,amman wata ke ƙara zubowa, shikenan na rasa dama ta, na rasa buri na, umma tafi so muyi ta zama cikin wannan ƙangin na bauta, Mu fa ba bayi bane da aka siyo a kasuwa, muma mutane ne kaman kowa, Ya Ameen yayi iya ƙoƙarinshi akan mu, sai dai duk yanda naso in karanci halin da zuciyar shi ke ciki akan fuskar shi, bai bani damar hakan ba, kallo na na maida ta saitin da yabi ya wuce, ko burbushin shi ban hango ba, sai dai Ƙamshin turarenshi irin na maza da suka amsa sunansu ya bar mani, "Nagode ya Ameen ko a haka ka bar mu mun san kaso taimaka mana na faɗa a fili ina mai durƙushewa, gami da sakin wani maraya kuka. Ba mu ba kawai, duk wani mai aiki dake cikin gidan yana ƙoƙarin taimaka mana, sam baya so duk wani dake ƙarƙashin shi yayi kukan baya kyautata mashi, Tabbas da duka masu arziki na duniya irin halin shi garesu da abubuwa sunyi ma mabuƙata sauƙi a rayuwa, duk da cewa halin mahaifin shi ya dauko, sai nake ganin ya ma fi mahaifin nashi kula da al'amurran mu a cikin gidan *Dukka buri na ya wargaje* *Mafarki na ya tafi* *Allah kai ne gata na* *Ka duba lamurra na* ****************************** ~Oum-deedat ce~ [8/5, 8:21 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain✍🏽~* *Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat) *Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat) *Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare. *Fage ~6~* °^^^^^^^^^^^^^° Tsawon kwana uku na shafe ban sake jin ɗuriyar Ya Ameen ba, hidimomi na nake yi hankali kwance. Yau gidan mun tashi da hidimomin aikin abinci, Alhaji Mustapha ne zai yi baƙi, abokan kasuwancin shi daga waje ne zasu zo. Abinci kala goma Hajiya Babba ta bamu umarnin muyi, mu duka ma'aikatan an rarraba ma kowa nashi aikin, masu gyara gida na yi, masu gogewa nayi, mu da mu ke aikin abincin mun hallara mu duka a babban kitchen ɗin gidan. Wannan karon harda su Aunty Saudat da Aunty Nihal ne a kitchen ɗin, sai dai banga amfanin su ba, yo eh mana basu da amfani domin kowaccen su kujera ta ja ta zauna suna latse latsen su,sai dai su bada command ɗin yanda zamuyi, wanda a zahiri ma mun fisu iyawa, salon iya yi ne kawai. Haka muka kammala abincinciccikan duk mun jigata; wannan ce tasa bayan mun gama jejjera abincicikan bisa tangamemen dining table ɗin da yake gefe guda a cikin falon sashen baƙin, na wuce sashen mu domin yin wanka da gyara jikina. Zuwan su yayi daidai da gama shiryawa ta, kiran Hajiya Kubra ne ya shigo waya ta, tare da bani umarnin zuwa sashen na baƙin domin taya su zuba abincin. A falon muka haɗu da Alhaji Mustapha ɗin da na kwashe watanni ban sanya shi a idanuna ba domin baya yawan zama; Durƙusawa nayi har ƙasa na gaida shi, yayin da ya amsa man cikin fara'a da sakin fuska, tare da tambayar umma na ko muna cikin ƙoshin lafiya. A ɗarare nake zuba masu abincin domin harda Hajiya Kubra zaune a wajen saboda baƙi ne abokan hulɗarsu na kasuwanci kuma ita ma tanada share a ciki, wannan ce tasa nake yi a hankali domin kada inyi laifi wajen Hajiyan. Gama zuba masu abincin yayi daidai da wanzuwar daɗaɗɗen ƙamshi, lokaci guda mamallakin ƙamshin ya bayyana fuskar shi ɗauke da maɗaukakin murmushin da ban taɓa ganin yayi irin shi ba; Sanye yake da lallausan farin tissue yard har kana iya hangen fara ƙal ɗin singlet dake jikin shi, kanshi babu hula hakan ya bayyana kwantaccen sumarshi luf da ita bisa kanshi har sheƙi take yi, hakan ya ba gyaran fuskar shi damar ƙawata fuskar shi da take ɗauke da madaidaici saje, ƙafar shi na Sanye cikin wani cover ɗin takalmi ɗan ƙasar italy sai sheƙi da walwali yake yi. Cikin hanzari yake takowa cike da kwarjinin shi, lokaci guda yana fadin "am so sorry wallahi na samu tsaikon jirgi ne" ya faɗa daidai lokacin da ya isa gare su yana mai jan daya daga cikin kujerun ya zauna. Da hannu Hajiya tayi man nuni da in serving ɗinshi, aiko ba ɓata lokaci na duƙa daidai saitin inda zai iya jin me make faɗa, saboda bana so in damesu saboda har wasu sun fara cin abincin; "Me za'a zuba maka Yaya?" Na faɗa ba tare da na bari mun haɗa idanu ba, "fried chicken with mixed fruit" ya faɗa shima yana kauda kai gefe cikin salon shi na miskilanci wanda ni na kula ma kwata-kwata shi haka halinshi yake; Ban ƙasa a guiwa ba kuwa nayi maza na zuba mashi, nuni yayi mani da ido da na bar wajen daidai lokacin da nake miƙa plate ɗin gaba shi, na daga ƙafa cikin sauri na bar falon domin wasu daga cikin baƙin sun fara tsare ni da idanu, ina tunanin shima abunda ya kula dashi kenan. ******************************* Bansan ya suka ƙare da baƙi ba, domin ni na fita batun su tinda dai na gama masu abin da zan masu, hutu aka bamu cikin gidan na kwana biyu domin family ɗin zasu yi wata tafiya da mu kanmu yan cikin gidan bamu san ina zasu ba, saƙon Alhaji Mustapha ne ya iso mana, dama duk in zasu yi tafiya koda ta yini ɗaya ce ya kan mamu alkhairi irin nashi da ya saba. Kudi ne masu yawa ya bayar a rarraba mana koda zamu buƙaci wani abu baya nan. "Allah sarki, Allah ya saka ma Alhaji da alkhairi ya ƙara buɗi na Alkhairi" umma ta ta faɗa lokacin da saƙon namu ya iso gare mu, su kau sauran ma'aikatan ƙananan maganganu suka hau yi, wai sun fi so Ya Ameen ya basu kyauta saboda shi bai Iya kyauta ba da yawa yake bayarwa. Kaji butulci irin na ɗan adam, mu dai bamu damu ba ai ance ma raina kaɗan ɓarawo ne, kuma ko ba haka ba umma ta tana da wadatar zuci abu kaɗan ke isar ta a rayuwa hakan ce tasa nima na tashi da irin wannan tarbiyyar. ******************************* Sun shafe kwana biyar babu su a cikin gidan hakan ce tasa muka samu sauƙin tsangwama da walwala acikin gidan, dama ba mu ke aikin abincin ma'aikata ba iyaka ayi mukai kwano in mun gama ci mu dauraye, iyakarmu gyaran dakinmu sai ko umma ta da take share tsakar gida, domin ita bata son ƙazanta Sam bata iya zama cikin ta, yayin da su kau sauran basu damu ba kitchen ɗin girki kawai suke share wa. Wani lokaci nakan shiga lambun gidan insha iska ko in katso gwaba ko Apple in ci idan nayi marmarin hakan, umma ta bata hanani domin ta san ko babu komai ba kullum muke samun irin wannan damar ba, hanani sake wa da sauran ma'aikatan kawai ta hanani shima mafi yawancin mazan ne, nima ban damu ba saboda da irin wannan tarbiyyar na taso ta rashin sake wa da maza. Shugabar ma'aikata mata ce ta leqo ɗakin namu, lokacin ina toilet wankan ƙa'ida na idan na tashi baccin rana ƙarfe uku wanda sake wa yanzu ya zame man kaman nafila cikin ƴan kwanakin nan da sukayi basa nan. " Maman Suhana Hajiya ce tayo waya, tace a faɗa maku ku gyara masu sashen su duka, Suhana ta gyara na Alhaji ƙarami da na Abie domin dukkan su gobe suna hanya idan Allah ya kai mu" Dam!! Naji gaba na ya ruguje ya faɗi, daidai lokacin da na fito ina goge kai da towel ɗina na wanka, shi kenan zasu dawo, shi kenan walwala zata ragu, Abunda zuciya ta ke ƙissima man. "To Talatu, insha Allah yanzu zamuje mu gyara, Amman gyaran zai kai goben tun da kinga yanzu marece ya riga ya kawo jiki" Ummata ta faɗa tana mai kallon Talatun, Talatun ta amsa mata da cewa "To shi kenan Maman Suhana ai ba damuwa gaskiya aikin da yawa, ku fara ɗin zuwa da safen kwa idasa" ta faɗa tana mai ficewa a ɗakin, da kallo na bita, matar kam kaman ta Allah to sai dai fa fuska biyu gareta, domin ita ce ta gaban goshin Hajiya babba a gidan Amman bata bari a sani,; nima na san hakan ne ta dalilin a cikin gidan nake nawa aikin kuma harda ɗakin Hajiyar nice ke gyarawa. Haka kau aka yi tuƙuru muka hau gyaran cikin gidan, ko ina yayi ƙal, ya rage gyaran ɗakin Abie ne da ya Al'Ameen ya rage, shima idan aka yi Magriba zanje na gyara na Abie, na Ya Ameen ne sai goben Saboda na san halin wannan sarkin ƴan tsaftan, tsaf zan gyara Amman yana zuwa zai ce baiyi ba. :::::::::: Washe gari tin da duƙu-duƙu na tashi gami da shiryawa na leƙa ɗakin Shugabar ma'aikata na amso makulli, an ma ci sa'a domin bai barin makullin ɗakin shi a hannun kowa wannan sarkin ƴan tsarin. Yanda yake na daban, haka ma part din nashi yake, komai dake shashen daban yake da sauran abunda ke cikin gidan, ba wasu tarkace amman an narka dukiya wajen;saitin kujeru ne a falon farare ƙal masu kwalliyar golden haka jefi jefi a jikin su, golden tiles ne malale a falon da ya ƙawatu da wani makeken chinese carpet da ya lashe fin rabin falon bayan su babu komai sai center table na zallan glass fari tar dashi mai haɗe da tumtum irin na gidan sarauta guda biyu tsakiyar falon, akwai stools suma kwara biyu tsakanin kujerun, sai saitin kayan kallo ƴan kamfani Samsung haɗe da Italian Tv stand, up White ne fentin falon yayin da ya dace da cottons masu matuƙar kauri suma kalar golden, sai na'urar sanyaya ɗaki da water dispenser dake maƙale a saƙo guda na falon. Kai kanka in ka kalla sai ka sake kallo, iya tafiya da imani falon ya tafi da nawa. Corridor ne gefe guda daga bangon hagu da ke falon, idan ka bishi shi zai sadaka da ɗaki ɗaya tal acikin shashen da yake mamallakin shashen, sai ƙofar ɗan ƙaramin kitchen da yake ta cen ƙuryar Corridor ɗin da yake ɗauke da madaidaicin dining area a ciki, kitchen din ya tsaru kaman na wata macen komai na aikin gida akwai shi ciki, sabo da Ya Ameen ya iya girki, in ƴan miskilancin nashi suka taso shi ke girkawa da kanshi yaci abun shi ko kuma in yayi baƙin shi yakan dafa masu abinci simple kuma ya wanke dishes ɗin da kanshi. Yanda falon ya tsaru sai naga ma kaman bedroom ɗin yafi ƙayatuwa, shima komai upwhite ne da kwalliyar golden, saɓanin toilet ɗin da yake kalar sararin samaniya da fitilu farare, sai ya zamana abun burgewa da ban sha'awa. Zagewa nayi na gyara ko ina na ƙalƙale, shi tas na kunna boner ta ruwan ƙamshi, take part ɗin ya ɗauki ƙamshi mai sanyaya rai, sannan na kunna na'urar sanya ɗaki domin ƙamshin ya kama ko'ina,bayan na gama na kashe komai na janyo part din na kulle gami da mayar ma da Mama Talatu makullin. ******************************* Ƙarfe biyar sakaliyya suka iso gidan, yayin da dukka mu ma'aikata muka fita taro su da yi masu barka da zuwa, harda umma ta baiwar Allah da take sanye cikin zurmemen hijab ɗinta, wanda bata ma lafiya kwance take zazzaɓi ne rau a jikin ta, Amman hakan bai hana ta fitowa ba, tinda haka aka saba kafin su shiga part ɗin nasu sai an gaggaisa da kowa tare da jin lafiyar kowa, wannan doka ce daga Alhaji mustaphan wanda a haka dole suke tsayawa suna zuzzunɓura baki suna aika mana da harara su sun dawo a gajiye amman baza'a bar su su shiga ciki su huta ba. Hakan baya damun Alhajin domin ya saba da halinsu tsaf halin mahaifiyarsu ne hakan ta saba masu dashi, halinta ne tin kafin ya aure ta kyamar talaka, masu aiki, sai dai yana tausaya masu har faɗa yana masu a lokutta da dama yakan ce "ku shiga taitayinku kuma ku natsu kusan inda yake maku ciwo, faɗi baya dauwama, haka ma wuya, kuma aure zakuyi ba kuma kusan gidan wanda zakuje ba" Hajiyar kan amshe da cewa "a'a alhaji ka rinƙa faɗar alkhairi a bakinka fa, yaran nan fa kai ka haife su" Wannan karon da Afan mutuniyata aka dawo, sai aunty Feena da yaran ta guda biyu ɗan shekara shidda mai suna Ayan sai ƴar karama da ba zata fi shekara biyu ba Nasreem. Aiko tana hangoni tayo kaina da ɗan gudun ta, maimakon in ce mata oyoyo sai itace ta rigani cewa "oyoyo aunty suhan sai kuma gaki" ta faɗa tana ƙyalƙyala dariya gami da daka tsalle ta rungume ni sai kace wata 'yar yarinya, Afnan ba zata kai tsara ta ba, ko ba komai zan iya bata shekara uku haka, riƙe take da hannun Ayan, hakan ce tasa nima murmusawa gami da tsugunna wa bayan na bamɓare ta a jikina; tsugunna wa nayi na cicciɓi Ayan din ina cewa a hankali "aini fushi nake yi da ke, ko waya Afnan kinma manta dani kwata-kwata, sweet Ayan ne kaɗai nawa ni, shi da nasreem. Ƙyalƙyalewa tayi da dariya," Allah Aunty suhan ba haka bane, karatu ne yayi zafi Amman Allah Allah nake lokacin zuwan mu hutu yayi inzo inga ya kika koma, na san kina nan kin ƙara kyau abunki". Murmushi nayi ina cewa nima nayi missing ɗinki Autan Hajiya, ya kamata kuje ki huta hakanan". Ashe bamu sani ba duk hankalin su ya dawo kaina Alhaji da Aunty Feena sai murmusawa suke yi, ita aunty Feena ɗaukar da nayi ma Ayan ce ta burge ta kunsan mai ɗa wawa, yayin da su kuma su Aunty Nihal haushi ya cika masu rai, Afnan ɗin na basu haushi, tana zubda masu daraja, wai ace House maid ce take yi ma haka?, dubeta ita kuma dalla har da wani daukar Ayan salon ne ta shafa mashi datti. Tsoki suka yi cikin rai, su kuma sauran ma'aikatan haushi ne ya cika masu rai na fifita ni da Afnan ɗin keyi akan su,basu yi la'akari da cewar su sun girma ba sun manyanta. Gogan naku na gefe jingine da motar shi, ya harɗe ƙafafu yana ta kallon su, bai ko murmusa ba Amman dai sun burge shi cikin ranshi, shi yasa yake masifar son Afnan ɗin ita ce ƴar gaban goshinshi, saboda ko kusa ba halinta daya da sauran yayyen nata ba. Mu kuwa hankalin mu ma bai kai kanshi ba da yake gefe yana ta zuba mulki da miskilancin har aka gama gaggaisawa muka juya zuwa shashen mu su kuma suka nufi cikin babban apartment ɗin nasu, har sun kai babbar ƙofar da zata sada su da cikin gidan, Afnan ɗin ta juyo gami da kwalla man kira, "Aunty suhan.!, in na gama hutawa ina nan shigowa ki ajiye man abun daɗin nan" ta faɗa cikin ɗaga murya gami da yin ɗan tsalle ta kashe man ido daya, bata jira cewa ta ba ta shige cikin gidan riƙe da hannun Ayan yaro ɗan gayu ɗan hutu gashi mulmul dashi, hakan ce ta sanya kallo ɗaya yaron ya shigar man a rai tin Wancen zuwan da sukayi, tin kafin ma ayi mashi ƙanwa ne; murmushi nima nayi gami da ƙada kaina "hooo Afnan ba dai rigima ba" na faɗa a fili ina shige wa shashen namu, ko ba komai zan ɗan samu sassauci zuwan Afnan ɗin domin tana ɗebe man kewa, tin umma na hanani har ta haƙura ta barni domin ta kula cewa halin Afnan ɗin ya banbanta da sauran ƴan uwan nata. ********** "huh...." ajiyar zuciya yayi tare da guntsar iska ya fesar, a hankali ya fara taka wa gami da nufar nashi apartment ɗin domin ya gaji over, makullin dake hannun shi yayi using ya buɗe sashe nashi; Turus ya ja ya tsaya, wani sas-sanyan ƙamshi ne ya bugi dogon hancin shi, lokaci guda ya maida kallon shi bisa kowanne lungu da saƙo na falon, kaman dai an cenza komai?, Amman inaaaa..... Su ɗin dai ne, hmmmm? 🤔 Wanene yayi wannan aikin? Ta bayar kanshi yake Amman ya kasa lalubo amsa. Jiki a sanyaye ya nufi Corridor ɗin da zai sada shi da bedroom ɗin nashi, still dai nan ma haka, aah! Mamaki bai gama cika shi ba sai da ya murɗa handle ɗin ɗakin ya shiga.; gadon shi an lailaye shi da zanin gado mai kyau da yayi order daga dubai bai iso ba sai da baya nan, hakan ce ta sanya Talatu buɗe ɗakin ta ajiye a cikin wardroop, ni kuma da nazo gyara na gani na yaye na sama duk da baiyi dauɗa ba na shimfiɗa na saka Wancen cikin laundry basket. A hankali ya taka kaman mai tsoron ɗakin, gami da isa bakin gadon ya zauna a hankali. Taushi da sulbin zanin gadon gami da ƙamshin da suke tashi daga saman gadon ne suka sanya shi sulale wa ya kwanta bisa gadon sosai yana mai kallon POP din dake saman ɗakin, ajiyar zuciya ya sauke a jere har sau uku gani da furta "Suhan" a hankali domin kuwa ya san wannan aikin ba na kowa bane sai ita....... ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:22 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI ƘARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven, No pain, so Magical Our creative golden pen, Be hold our words, A production of our pen, savour Our worlds for it cause u no pain✍🏽~* *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Gaisuwa ga ƴan golden pen, expecially ~Yaya Umar Dalhat Funtua~ muna godiya da ƙoƙarin editing, na baka kyautar wannan Page ɗin, kayi yadda kake so dashi. Allah ya ƙara haɗa kawunamu ameen* *Page ~7~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Haka kau aka yi, ina gama sallar magariba sai ga afnan saɓe da Nasreem a kafaɗa, riƙe da hannun Ayan tana jan shi a hankali, sallama tayi fuskar ta cike da annuri da fara'a ta shigo, yayin da ta ajiye Nasreem bisa katifar tamu, ta janyo Ayan shima ta zaunar dashi, wutsil yaro ya haye kan cinya ta da nake zaune bisa dadduma. "ku ji mu da yaro dan Allah, sai san jiki kaman mage" Afnan ɗin ta faɗa tana mai kama baki alamar mamaki, murmushi baiyane a saman kyakkyawar fuskar ta, lokaci ɗaya ta maida duban ta wajen umma ta da take zaune itama bisa tata daddumar domin bata tashi idan ta gama sallar magriba har sai ta kammala isha'i; "umma ina yini ya kwana biyu ya jiki-jiki, dan ko ba'a faɗa ba naga kaman baki lafiya" ta faɗa cike da girmamawa, Afnan yarinya ce mai cike da natsuwa, biyayya da girmama na gaba da ita ko da kuwa ta fishi da komai, shi yasa rayuwar ta da ta Ya Ameen ta kusan zuwa daya bambancin kawai shi akwai ɗan miskilanci a al'amuran shi in ya so, saɓanin ita mai walwala ce da zaulaya in taso, ta ɓangare daya kuma ga sangarta idan taso gami da shagwaba sabo da ita ce auta, tana da wani hali guda ɗaya da yake burge Alhaji mustapha, hakan ce tasa idan tazo mashi da buƙata ba dai ya Musa mata ba, yakanyi duba na tsanaki ga buƙatar tata, halin kuwa shine *manyance* watau tana da tinani irin na manya, lokutta da dama Alhajin kan zauna yayi magana da ita ta tsanaki idan ya je cen ko kuma idan ita tazo nan. "lafiya ƙalau Afnan, kun iso lafiya ko,? Ya gajiyar tafiya? Kunsha hanya, maimakon ki zauna ki huta Alabasshi idan mai duka ya kai mu kin shigo ku sake gaisa wa, shine kika kwaso yara kuka taho, kika rabo su da umminsu kika zo nan dasu kina kwasar masu sanyin nan" umman ta wa ta ƙarashe tana mai duban afnan ɗin tare da miƙa ma Nasreem ɗin hannu alamar ta taho, ai kuwa ba musu yarinyar ta muƙe cikin salon tafiyar ta irin ta ƴaƴan turawa ta isa wurin umman tawa tare da ɓangala mata dariya, cikin gwarancinta take ta mata jagwalgwalon surutun su irin na yara; Afnan ce ta amsa mata da cewa "Ai umma ba zama in har banzo mun gana da aunty suhan ba, in wanke laifi na sannan in sake kafa wani gwamnatin domin naga Ayan yana neman kwace man fada, don ma na san ba zaki barta ba da cen ɗakina muka tafi muka sanya labule Alabasshi sai ta kwana cen da safe ta dawo" murmushi kawai umman tawa tayi alamar ba zata bari ba, sannan ta maida hankalinta kan Nasreem ɗin lokaci daya tana cewa "to kiyi maza ki gama kinsan ba daɗewa za'a neme ki sabo da yaran da kika taho dasu" "toh umma insha Allah" Afnan ɗin ta faɗa tana maido hankalinta kaina da nake ta wasa da hannun ayan, son yaron ya shiga raina sosai na rasa dalili, kuma ni ba mugun daɗi ma nake da mahaifiyarshi ba duk da dai cewa tafi su Saudat kirki ko don ta girmesu ne, ta fisu hankali shi yasa? Oho "Aunty Suhan kinga yanda kikayi shar abunki? Hutu ya ratsa ki wallahi kin ƙara kyau fatar ki sai sheƙi take yi minene sirri?" ta faɗa muryarta cike da zaulaya, ni sai ma ta bani kunya wallahi, sunne kaina nayi cike da kunyar umma ta da take zaune wajen, kuma tana jiyo duk abun da muke faɗa, ita kau Afnan na lura da ko ajikinta ma........" ba wani nan afnan kece zan cema haka Allah" na faɗa cikin murmushi, har cikin raina ina ƙaunar afnan ɗin, sabo da ko ba komai zuciya tana son mai kyautata mata, Afnan ɗin na son mu har cikin ranta, bata gudun mu ko kyamatar mu kaman yanda sauran suke yi, hakan ce tasa daga ni har umma ta muka sakankance mata muka saki jikin mu da ita. "Humm,,, haka dai kika ce Aunty na, ya Maganar karatu kin ƙarashe kuwa?" ta jefo man tambaya cikin halin ta na manyance; Lokaci guda gaba na ya ruguje ya faɗi, saurin saisaita kaina nayi domin kada ta fahimci wani abu, sannan nace mata "har na gama fa Afnan" "wow, har kin kammala aunty suhan?, wane course kika karanta ne?, na fa dade rabo na da nigeria wlh" ta maido man tambaya cikin tsammanin samun amsa daga gare ni, hakan shi ya ƙara ruɗani har firgici na ya fito fili cikin inda inda na mayar mata da cewa " Secon. dry school fa na.. ke nufi Afnan" zaro idanu tayi jin abunda na faɗa "meh😳" ta tambaya cikin son jin ba'asi "eh" na mayar mata ina mai gyaɗa mata kai kaman ƙadangaruwa, "look aunty suhan kibar wasa, ni na san umma ba zata hana ki ba, kuma nasan tinda Ya Ameen yana ƙasar ba zai sa maki ido kina zaune baki aikin komai ba kuma ke ba karatu kike yi ba" (kuji Afnan ɗin nan ma, wai bata aikin komai🙄) ta mayar mani cikin ɗan ɓacin rai, sabo da na kula hakan baiyi mata daɗi ba. Tsam umma ta tayi tana mai son jin amsar da zan bata, yayin da ni kuma nayi ƙasa da kaina ina mai cije laɓɓa na kamar zan huda su, alama nake yi mata da tayi shiru, Amman kaman ma bata san ina yi ba, cigaba tayi da cewa "kinga kin girmeni, Amman kina nan kina kallo zanzo in gama makaranta ta, na fiki ƙananan shekaru amman na fiki sanin abunda zai amfane ni nan gaba, gaskiya in wani ya baki shawara tsaida karatun ki daga iya Secondry bai kyauta ba, sabo da dashi ne zaki tallafi rayuwar ki nan gaba har ma da ta umma" tana kai aya naji kaman in zunduma da gudu, kaman in ɗora hannu a kai🙆🏻 in ta zunduma ihu😵 "afnan ya kamata mu bar maganar karatun nan hakanan shi komai da kika gani muƙaddari ne, idan da rabon inyi nan gaba sai kiga Allah ya kawo wani sanadin" na faɗa ina mai son ta fahimci umma ce ta hanani, ta kuwa fahimta domin naga ta dan zaro idanu waje sai kuma ta gyaɗa kai gami da cewa "tau ai shikenan Allah ya kawo aunty Suhan, dama zuwa nayi in tambayi umma don Allah ko zata barki ki raka ni siyayya zuwa gobe insha Allah ba daɗewa zamuyi ba" ta maida maganar tata kan umma ta da take ta jijjigar Nasreem har ta samu tayi bacci, "Allah ya kai mu" umma ta bata amsa cikin yanayi da na kasa karanta, Sam ba zata iya nuna ma Afnan ɗin ɓacin ranta ba domin ko babu komai maso uwa tau lallai yaso ɗanta, Afnan ɗin na daga cikin mutanen da take ganin girman su duk da ƙarancin shekarun nata kuwa,. Miƙewa Afnan ɗin tayi gami da gyara gyalen dake saman kafaɗar ta, tana mai cewa "To umman mu, aikau godiya nake yi bari muje sai da safe kinga ma kuwa ta maganar ki har sunyi barci, bari in kai Nasreem ɗin in dawo in ɗauki Ayan ɗin, tinda ban iya ɗaukarsu su duka" "a'a bari Mama na ta ɗaukar maki Ayan ɗin ai ba kin ta jigila ba tinda ga wadda zata iya taimaka maki, kuje ta kai maki shi, sai da safe ki gaida hajiyan da yayar taku" umma na ta mayar mata cikin ɗan murmushi, "to umma aikau na gode, aunty na taso muje aiki ya ganki na ɗaukar wannan gabjejen saurayin haka gashi yayi bacci ya ƙara nauyi, ko in goya Nasreem ɗin muyi kama kamar Ayan ɗin" ta faɗa cike da zaulaya da son sanya ni dariya da ta kula kaman walwala ta duk ta tafi, tinda aka yi maganar karatu, aikau ta ci nasara murmusawa nayi ina mai Miƙewa tare da faɗin "ance maki kowa ma raggo ne irin ki, da sai munyi ma yaro na kama kama?" na mayar mata cikin nima tawa zaulayar daidai lokacin da muke ficewa daga cikin ɗakin a tare. Ko da muka isa muka kwantar dasu sai da tace zata rako ni, nice na hana ta, ganin dare yayi, nima ina komawa nayi sallah na kwanta tinani fal cikin raina na Afnan ɗin da ƙarfin hali, ko ma dai miye ina fatan ta bar maganar karatun nan haka nan, bana son Abunda zai jawo man matsala da umma ta muna zaman zaman mu lafiya ƙalau, tinda na kula har cikin ranta ba son maganar take ba. ~~~~~~~~~~ Bai san lokacin da bacci ya kwashe shi ba a haka, sabo da sanyi da tsaftar ɗakin gami da taushin zanen gadon, sai dai farka wa yayi yana mai jiyo kiraye kiraye sallar magrib na tashi a laud speaker ɗin masallacin da ke gefen gidan nasu, a kasalance ya tashi gami da cire kayan, ya faɗa toilet domin yin wanka da alwala, mamakin yarinyar yake yi sosai, a ina ta iya irin wannan tsaftar haka? Gashi komai a nutse, ta ajiye komai inda ya kamata, hatta da towels ɗin wanka ta cenza mashi wasu, ta dauraye waɗanda suka yi dauɗa ta shanya a ɓangaren shanya na toilet ɗin, ta kwashe tarkace robobin shower jel da hand wash liquid soap ɗin duk ta zuba su a shara taje ta zubar, toilet ɗin ƙar, kaman an cenza komai na ciki ya koma sabo, shi kanshi cikin jin daɗi yayi wankan, ya fito yana mai jin daɗin jikin shi da ƙamshi da jikin nashi yake yi, shi ya siyo product ɗin Amman ta zaɓi waɗanda suka dace ta ajiye mashi. (yo Al'ameen wannan ai aikin Suhan ɗin ne a cikin gidan ko baka sani ba?) Bai sha mamaki ba sai da ya buɗe wardroop ɗaukar kaya,, ya tarad da komai ta ware mashi wajen shi ta kimlace su, ta kwashe duk wasu tarkace masu datti ta zuba a laundry basket; cikin natsuwa ya shirya gami da taje sumar kanshi tayi luf abun ta, ya fesa turare, gami da zura Jalla biya, ya fito yana taka wa cikin salon tafiyar shi ta ƙaƙƙarfan namiji, domin zuwa sauke farali sallar magariba. ******************************* Washe gari ma da nake nawa aikin, haka Afnan ɗin tazo tana taya ni, rabi surutu rabi tsaukana, yo eh tsaukana mana zance, tinda da ta fara shara ko goge goge sai ta duƙe ko ta faɗa kan sofa tace "wash wlh aunty suhan na gaji da yawa, gaskiya kina ƙoƙari" na kan yi dariya ince "Afnan kenan, miye na gajiya a nan?, aikina ne fa" A haka muka gama tana mai ƙara tuna man da cewa ƙarfe biyar fa na yamma zamuje shopping ɗin nan don Allah inyi shiga ta kece raini, (Lol🤣 Afnan kenan) Ƙarfe biyar tayi daidai da shiryawa ta, doguwar riga na sanya irin dubai abaya ɗin nan, da Alhaji mustapha ya taɓa yo man tsarabar ta, abayar na matuƙar karɓa ta, baƙa ce sosai har ƙasa sai dogon wando daga ciki, haɗe take da gyalenta, saboda haka sai Kaga dama sannan ka sanya hijab, kwalliyar golden ne jikin ta da adon wasu duwatsu farare daga sama har ƙasa, wannan shi ya ƙara ƙawata rigar, banyi wata kwalliya ba sosai domin ni ba ma'abociyar shafe shafen nan bace rambatsai. Hoda kawai na murza, sai kwalli da na zizara ma idanu na, haɗi da shafa lipstick mai ƙamshin Apple shima fari ne da ɗan sirkin Light pink haka, parking ɗin gashina nayi, tini ni dama ba ma'abociyar kitso bace sabo da gashina irin na asalin Fulani ne, mai taushi da sulbi, ga yawa da tsawo, wanda saidai in wanke shi kawai in shafa mashi mai in haɗa shi in ƙulle hakan ya wadatar dashi, turare irin namu na mata mai taushin ƙamshi na fesa haɗi da shafa humra ƴar Sudan da aunty saudat ta bani kwanaki cikin kwalimar ta, sai ƙamshin ya haɗe ya bada wani ni'imtaccen ƙamshi. (ka ganni kaman ba yar aiki ba😅) Afnan ce ta shigo cikin saurin ta tana cewa "Aunty Suhan maza ki fito, ga yaya cen yana jiran mu na lallaɓo shi, zai kai mu kinsan halin nashi baya son jira, ɗan oya oya ne." Turus ta ja ta tsaya lokaci guda mamaki fal bisa fuskar ta, lokaci guda ta shiga taɓa hannuwa, 👋🏻 sannan ta shiga faɗin "Aunty Suhan wannan kyau haka? Dubeki dan Allah kaman wadda zata je gasar kyau, kina da irin wannan kyaun haka kike boye wa?" jan hannuna ta shiga yi tana faɗin masha Allah wannan ai ni sai ma inji kunyar jerawa dake wlh abu kaman ƙyanƙyasar inji? " ta ƙarashe da zaulaya Ja nayi na tsaya ina cewa "Afnan Allah in kwalliyar tayi yawa bari in rage, yo ni wa zan ma kwalliya har haka?" murmushi ta sake yi, da ya riga ya zama ɗabi'arta, "ke wasa fa nake maki, Ya Ameen ɗin ne zai tsaya wani jiranki? Har ma fa ya shiga mota mu kaɗai yake jira, kuma yace in na ɗaɗe zan ga wayam, saidai idi dreba ya kai mu" ta shiga faɗi tana mai sake jan hannu na, ni kuma na shiga binta kaman raƙumi da akala. A tsakar gida muka haɗu da umman tawa, tana shigowa dan shirya zuwa girkin dare cikin gida, da addu'a da fatan dawowa lafiya ta bimu, sannan ta mana gargaɗi da mu kula da kanmu ƴaƴa mata muke, to muka amsa mata gami da jerawa da Afnan ɗin kai ka rantse ƙawaye ne, domin Afnan ɗin ta taddoni a jiki, saidai ɗan tsawo ne kawai zan nuna mata, ba kowa ne ma za'a gaya ma na girme ta ba ya yarda. Bayan motar ta buɗe mani na shiga, wani sanyi ne mai ratsa zuciya ya mani sallama, ban san lokacin da na ja mun fashi ba, gami da runtse idanu na ba sannan na saki ɓoyayyar ajiyar zuciya, mota ce mai suna mota, na tabbata ban taɓa shiga mota makaman ciyar wannan ba, duk kuwa da tarin motoci na alfarma da suke gidan. Tada motar da yayi, shi yayi sanadiyyar dawowa ta cikin hayyaci na, daidaita kaina nayi cikin sanyin magana nace mashi "ina yini Yaya" duk da bana iya hangen shi sosai bayan shi kawai nake iya gani don ta saitinshi nake zaune sai ayan da ya kwanta bisa cinya ta, ina iya hango motsawar shi da motsawar bakin shi ta cikin mirror dake maƙale na driver, "lafiya" ya bani amsa a taƙaice, ban kuma cewa komai ba, sai wasa da na shiga yi da ayan, yana bani labarin school ɗin su a hankali, ina jiyo Afnan ta cika shi da surutu da take zaune gidan gaba wani abun ya amsa mata, wani kuma yayi murmushi kawai ya share ta. A haka muka isa tanƙamemen super market ɗin da ya haɗa komai, komai na kayan more rayuwa ana saida shi a ciki; ɓalle murfin motar nayi naja hannun ayan muka fita, yayi daidai da fitowar Afnan ɗin tana cewa "Yaya kai ba zaka shiga ba?" girgiza mata kai kawai yayi yana miƙa mata ATM ɗin nashi gami da cewa "30mnt na baku kuma, kuyi maza ku fito ina jiran ku, ina da nawa uzirin rigimar ki ce kawai bana so Lil" (da yake ya kan ce mata Lil wani lokacin) "OK Bigboo, insha Allah, ta faɗa tana mai ƙamewa cikin zaulaya, zagayowa tayi gami da kama hannun Ayan tayi gaba ni kuma na bita a baya kaman wadda kwai ya fashe mawa, tinda sanyin ac da ƙamshin motar Yaya suka bugeni naji komai nawa ya kwance, kaman an zare man lakka, lallai Ya Ameen daban ne, komai nashi ma daban yake; Ban san mun isa ba saida naji Afnan ta girgiza ni tana cewa "Aunty suhan lafiya dai kuwa? Ko baki lafiya ne?" ɗan murmushi nayi na shiga girgiza mata kai, ina mai cewa "a'a Afnan babu komai kawai dai wajen ne ya burge ni, mu shiga kada mu cinye lokacin mu anan" Nacewa Afnan ɗin tayi saidai in taya ta zaɓe, haka kau aka yi, duk Abunda na zaɓa sai ta ɗauki biyu, kama daga kayan shafa, kayan maƙulashe, kayan sawa da su eaner wears, Ayan ma da Nasreem ta ɗaukar masu kayan ciye ciye sabo da su basa buƙatar komai. Haka muka fito masha Allah gaskiya wurin yayi kyau ya ƙayatar dani, haka nake faɗa ma afnan ɗin a hanyar mu ta komawa motar Yayan. "Ta bangaren shi baya so tinanin yarinyar kan nushe shi a lokutta da dama, sai dai yakan danganta hakan da tausaya masu da yake yi, dubeta don Allah gwanin burgewa yanzu, kaman tayi ta dauwama a haka, ya kula tin shigar ta motar tashi, kashin turarenta ya bayyana kanshi, ƙamshi mai cike da kwantar da hankali, yana so tayi karatu, yana so ta tallafi rayuwar umman tata, yana so su samu ƴanci, sai dai me yasa?, me yasa umman tata take da wani irin tinani, me yasa ta nace ga rashin son tallafa masu da yake yi? Ya haƙura, ya haƙura tin ma kafin ta fara zargin ko yana da wata manufa tashi ta daban akan su, Suhan yarinya ce mai cike da natsuwa, mai cike da kamewa, tana da gudun abun duniya, wannan kaɗai ya isa ya yaba ma mahaifiyar tata, ta nan fannin kuma ta ciri tuta, ta kai a yaba mata gaskiya, kuma yana ganin ƙoƙarin ta, tayi aikin ta na uwa ta haɗa harda na uban ma; "Huh" ya guntsi iska ya fesar, yana saisaita kanshi ga barin kallon ta tin ma kafin ta ankara don baya son raini ya shiga tsakanin shi da ita. 😂 ********* A haka muka isa gidan Afnan ta kama man kayan muka shiga dasu ɓangaren mu, don ta nace cen zamu ajiye kayan ta fitar ma da kowa nashi, a cewarta rabon mu yau ya rantse don duk siyayyar nan da aka yi, cikin kudin Yaya ne, shi yasa ta zage ta ɗibar mana son ranta tinda ba nata aljihun bane yayi kuka, ina jiyo ta tana cewa "Yaya ina so muyi magana, fa wallahi" amsa mata yayi yana cewa "To my Lil, mu bari zuwa dare in na dawo sai mu tattauna, yanzu dai ina da muhimmin uziri kinji auta" ya faɗa yana mai murmusa mata, "OK yaya, as u said bye-Bye, sai ka dawo, a dawo lafiya" ta faɗa tana mai manna mashi ɗan ƙarami peck a kumatu sannan ta sake ɓalle murfin ta fito, na kula ɗabi'ar turawa ta kama su, har basa jin komai su rungumi juna, ko sumbatar juna a goshi, ko kumatu a gaban bainar jama'a, Ni kau tini nayi nisa da ragowar kayan da Ayan saɓe a kafaɗa ta. Haka ta wawware ma kowa kayanshi, harta umma ta, ta ɗauko mata atamfofi masu shegen kyau ƙwara uku, da less guda biyu, sai hijabai masu ruwan kayan guda uku, da takalma ƙwara biyu, masu kyau zubin na manya, Godiya umma ta ta shiga yi da faɗan na biye mata ta kaso kuɗi da yawa, wannan ai ɓarna ce, "ba komai umma wallahi Albarkarku kawai muke nema" Abunda tace kenan sannan tayi ma umman Alƙawarin za mu kwashi kayan namu da nata masu buƙatar ɗinki, mu kai ma telan dake ma gidan ɗinki, umman taso ta hana ta a cewarta hakan ma ya isa zamu bada nan cikin unguwa ayi mana, ba sai ta ƙara yin wata hidima ba, Amman Afnan ɗin ta nace ai babu komai wallahi duk yi wa kai ne. Nima ta ware man nawa kayan, wanda sai da tsoro da firgici suka kama ni, rabi da kwantan siyayyar ma ni tayo ma wa, kai ni afnan wacce irin ƙauna take yi mani har haka?, "Godiya na shiga yi mata tare da faɗin sunyi yawa ta rage" ɓata fuska tayi tana cewa"ga duk kan alamu watan ɓatawarmu yayi, ai in tazo Nija bata da ƙawar da ta fini, don me zan maida hannun kyauta baya, banga yanda nake yin kyau ba idan nayi kwalliya? dama maƙasudin siyayyar nice, sabo da bata yo man tsaraba ba da zata taho" godiya muka shiga yi mata ni da umma ta, lokacin da take kwasar nata kayan da basa da wani yawa sai kayan ciye ciye kawai. Sallama muka yi da ita, tare da mani Alƙawarin gobe zata shigo musha fira in na gama ayyuka na na cikin gida, har bakin sashen namu na raka ta, ina mai walwala da annuri a fuska ta, domin duk wanda yace yana son ka ai ya gama maka komai a rayuwa, ina ganin sauran ma'aikata ana ta zunɗe na, to suma dai da zata wuce sai da ta gaida su, ta masu ɗan Alkahiri a cikin kuɗin da ke pos ɗinta, Amman duk da haka baiyi masu ba, masu mugun abun ganin wannan tarayya tamu ta watse suka ƙudura, masu gulma suka naɗa, domin a gaban su muka shiga da leda niƙi niƙi, Amman sunga ta fito da guda ɗaya tal a hannu, ita ma ba'a cike ba, ashe yau Hajiya Babba da labari kenan, wai don ma basu san Yaya Al'ameen ne ya kai mu ba, wai ni Allah ai da kashin mu ya bushe daga ni, har mahaifiya ta, a haka dai na tura masu aniyarsu, na juyo salin alin na shige namu ɗakin tare da turo ƙofa, domin ɓoye kayan namu, sabo da wasu daga cikin su ƴan ganin kwam ne, zasu iya leƙo wa ko don ganin wainar da ake toyawa a cikin ɗakin. *************************** Ƙarfe tara da rabi daidai, Afnan tayi sallama sashen Yayan nata, izini ya bata ta shiga daga ciki, kai tsaye kujerar da yake zaune kai yana latsa laptop ɗin shi ta nufa, sanye yake da 3quater ruwan kunun kanwa, watau army green, da fara ƙal ɗin singleti, sanyin falon madaidaici ne, har yanzu gyaran da Suhan ɗin ta yi ma ɓangaren nashi yana nan, tinda ba yara ke akwai ba a sashen, ba yawan abokai ya cika ba, (yo wannan miskilancin nashi zai bar shi yayi abokai ne?) fuskar shi tar cikin haske da yake fitowa ta laptop ɗin, lallai Yaya Al'ameen ƙaƙƙarfan namiji ne, hakan ko ya samo asali ne da jim ɗin da yake zuwa akai akai, a sashen motsa jiki na gidan, kyakkyawa ne na gaske, cikin kalar fatar shi fara tas tas da ita. Murmushi yake bin ƙanwar tashi da shi, har zuwa lokacin da ta iso wajen nashi, hannu ya miƙa mata tare da zaunar da ita dab da shi yana mai faɗin "Lil wannan magana dai wace iri ce, da har aka bata muhimmanci haka?" Kallo ta bishi dashi, tana mai ƙara jin ƙaunar yayan nata cikin ranta, shi kaɗai ne zai zauna da ita ya fahimci damuwarta, har yayi mata maganin ta, in ka ɗauke aunty feena da dama ita wannan kaman uwa ta ɗauke ta, tinda a hannun ta ta taso. " yaya so nake muyi wata magana mai muhimmanci, dafatan zaka saurare ni, kuma ka fahimce ni, kayi ma maganar tawa kyakkyawa duba na tsanaki, don Allah" Na ɗaya daga cikin dalilan da yake sanyawa yana ƙara jin ƙaunar ƙanwar tashi fiye da kowa a cikin ƴan uwan nashi kenan, manyance da natsuwa tsara zance ga kuma girmama na gaba da ita, "Yaya wata Alfarma nazo da ita, dafatan zaka taimaka ka biya man wannan buƙatar, na sani duk gidan nan babu wanda zan tun kara ya saurare ni, kaman kai, kuma na san zaka iya shi yasa na zo wurin ka Yaya" ta katse mashi tinanin shi, cikin marairaicewa. Murmushi yayi yana mai tattara dukkannin natsuwarshi zuwa gareta, "ina jin ki Lil wannan wace ALFARMA ce kike buƙata gare ni haka da kike ta kwana - kwana haka?" ya faɗa cike da murmushin da ke ƙara ƙawata mashi fuskar shi, tare da fiddo zallar kyawon fuskar tashi, dimfull ɗin shi yana mai ƙara nutsewa cikin kuma tun nashi. " Yaya Maganar SUHAN ce" ta faɗa cikin tarabbabin yanda zai amshi maganar tata....... "Ehem!, ina jin ki Afnan me Suhan ɗin tayi ne?" ya amsa mata fara'ar fuskar shi na raguwa, abun da ya ƙara tsorata Afnan ɗin kenan cikin in ina tace "maaaganaaar... Kara.. Tun,,, ta Yaaaya".... ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:22 PM] Aminatu Hassan: 🌹 *_BAN FI ƘARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u no pain✍🏽~* *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ _*Jinjinar ban girma ga mai gida na, Abbu-Deedat. Nagode da irin goyon bayan da kake bani da irin yadda kake ƙarfafa mani guiwa, a duk al'amurran da na sanya gaba. Godiya marar adadi Allahu ya bar ƙauna ya raya mana Ahmad Deedat🥰*_ _*Page ~8~*_ °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° "Look afnan✋🏻" ya katse ta daga inda indar da take yi, sannan ya ɗora da faɗin "Na riga nayi duk iyakar ƙoƙarin da zan iya yi akan issue ɗin karatun yarinyar nan, tin ma kafin ke kizo, saboda haka bana jin zan iya maida kaina acikin al'amurran su, tinda har mahaifiyar ta bata son al'amarin karatun nata, zai fi kyau muma mu dakata hakanan, mu barta tayi ma mahaifiyar ta biyayya Allah ya sani mun riga mun yi iyakar iyawarmu" ya ƙarashe maganar cikin wani yanayi na ƙunar rai lokaci guda yana ɗan ƙutawa gami da janyo laptop ɗin tashi ya buɗe, ga duk kan alamu yana nufin ya gama magana kenan. Shiru falon yayi, in baya ga ƙarar Ac da take bada sanyi ƙaɗan-kaɗan baka jin komai, ita kanta Afnan ɗin shiru tayi kaman ruwa ya cinye ta, ta rasa minene tinanin umman suhan ɗin akan ɗiyar tata, amman dai koma minene ita bazata bar lamarin haka nan ba, za tayi iya yi ta tinda ta kula babban burin suhan ɗin kenan, don dai Allah yayi ta da kawaici da biyayya ga na gaba da ita. Muskutawa ta sake yi ba don ta gaji ba, sannan ta marairaice dama abunka da auta an saba shagwaba "Na sani wlh yaya na, sai dai ba zamu bi ta kan umman ba, ita ba sanin daɗin abun tayi ba, Yaya Pls, don Allah ba don ni ba, ka taimaka mani, bana so ma ta gane da sa hannuna" shiru yayi mata na wasu daƙiƙai, sannan ya nisa tare da faɗin "Toh Naji, yanzu ya kike so ayi?" tini fara'ar fuskar ta ta dawo, afnan kenan baiwar Allah, yarinya da kyakkyawa zuciya. "Yauwa Big boo" ta fada cike da jin daɗi sannan ta kamo hannuwa shi ta riƙe su gam, sana ta ɗora da faɗin " Dady, Dady zaka yi ma magana, shine kaɗai zai iya sawa umman suhan ta yarda, ba tare da samun wata matsala ba, Pls my Lovely yaya" shiru yayi sai daga bisani ya nisa gami da faɗin "Is OK dear, Consider it done, kar ki damu ina so ki bar maganar nan a hannuna zamu san yanda zamuyi, ni kaina ina tausayin Rayuwar su, mutane ne da suka cancanci a tausaya masu don ga duk kan alamu sun fi sauran ma'aikatan shiga halin damuwa, masalan ita umman suhan ɗin" ya faɗa cike da basarwa kai kace ma bashi ne yayi maganar ba, saboda bazaka taɓa kawo ma ranka cewa miskilancinshi ma zai bar shi fahimtar wani abu ba. Miƙewa tayi tsaye, gami da yin wani ɗan tsale cike da annashuwa, "Nagode Yaya, na gode Allah ya saka da Alkhairi ya bar ƙauna, I love u sooo much, Good night Swt Yaya" ta faɗa tana mai nufar ƙofa domin fita, saboda dare yayi, da murmushi ya bita, wannan zuciya ta Afnan da kyau take, tabbas shi ya san ko ba daɗe ko ba jima sai sun yi alfahari da yarinyar "Ameen" ya furta a hankali cikin salon san kauda tinanin abun a ranshi, domin aikin da yake yi Afnan ɗin ta shigo, mai muhimmanci ne. ××××××××××××××××××××××× Washegari bayan mun kammala aikin mu, mun dawo sashen mu munyi wanka wajen ƙarfe biyu na rana, aiken Hajiya Kubra ya iske mu, ni da umma ta wai tana neman mu, har ga Allah gaba na sai da ya faɗi, domin har jin daɗi nake inje in kammala aiki na tana sashen Alhajin ta yanda ma babu abin da zai haɗa ni da ita, sai dai wajen zuba abinci. Ummana ce ta amsa da cewa gamunan zuwa, lokacin da ƴar saƙon ta fita ne ta juyo da kallon ta gare ni da nayi fiƙi fiƙi da idanu, ina ta tinanin laifin me kuma muka aikata yau, saboda duk idan aka yi mana irin wannan kiran to fa ba lafiya ba. "ki kwantar da hankalin ki mama na, insha Allah lafiya lau, babu abin da zai faru sai alkhairi" da to na bita domin in kwantar mata da hankali saboda yanzu umman tawa sai a hankali ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba, don ko jiya dakyar muka yi bacci, ciwon zuciyar ta ne ya kusan tashi. Hijabi na na ɗauko na sanya gami da wucewa gaba umman tawa na biye a baya na, babu mai cewa ƙala har muka isa babban sashen gidan, ta bangare guda kuma zuciya ta na luguden duka, domin na san rashin mutucin Hajiya Kubra sosai, fata na dai kada al'amarin ya shafi umma ta, ko minene dai ya tsaya iya kaina. Sallama muka yi daga bakin ƙofa, Mama Talatu ce ta amsa mana daga ciki tare da faɗin "ku shigo mana, kuka tokare daga bakin ƙofa kaman wasu baƙi" shiga muka yi, ina gaba Ummana na baya; zaune muka iske ta bisa ɗaya daga cikin sofar da suka yi ma falon ƙawanya, gefe na samu da niyyar zama ƙasa ta dakatar dani, "a'a Suhana, ku shiga dai daga cikin falon Hajiyan, tana daga ciki tana jiran ku" "Toh Talatu" Ummana ta amsa mata. Kai tsaye falon muka shiga tare da sallama, waeh Aljannar duniya kenan, tsayawa fasalta kyaun falon da dukiyar da aka narkar ma ɓata lokaci ne, kawai ka fasalta shi da duk falo mafi kyawo da ka taɓa gani a Rayuwar ka. Zaune take, hakimce cikin isa, izza da taƙama (Hajiya Kubra ba dai ji da kai ba) ko amsa mana sallamar da muka yi bata yi ba, sai ma cen gefe ɗan nesa da tayi mana nuni saman carpet din da ya lashe fin rabin falon tayi, bamuyi ƙasa a guiwa ba muka zauna, muna mai gaisheta cikin ƙan-ƙan da kai, shima bata amsa ba, sai ma shiru da ya biyo bayan hakan na tsawon wucin gadi, sannan ta nisa cike da gadara ta fara faɗin "ina so ku nisanci ɗiyata Afnan, domin duk abubuwan da suke faruwa cikin gidan nan tin zuwanta a kunne na suke, na hana ta taƙi bari, ina so ku sa ta tayi nesa daku, domin ko alama bana son zuwa sashen masu aikin nan da take yi, kuma na san ɗiyarki ke janta" ta faɗa tana maida duban ta kan umma ta da kanta ke sunkuye, sannan ta cigaba "kunsan ko alama ba da son raina kuke zaune a gidan nan ba, saboda har yanzu kin ƙi ki faɗa mana asalin daga inda kuke, daga ke har ɗiyar taki bamu san asalin ku ba, sannan ki shirya bayyana mana komai da ya shafe ku idan ba haka ba, ba jin zaman ku a gidan nan zai cigaba da ɗorewa, bazan lamunci a mallake man ƴaƴa ba idan kunne yaji...... " ta ƙarashe tana mai ajiye maganar cike da gadara, ko ɗar bata ji ba, duk cin mutumcin da tayi mana bata gani ba, wannan ai tozarci ne, ko ba'a faɗa ba, na san mama Talatu da uwani ne suka kawo wannan gulmar, watau ita dai duniya haka take kana barci ana maka mun shari, idan da sabo ma mun saba jin ire-iren wannan tozarci daga gurin Hajiya kubran, muryar Hajiyan ce ta katse man tinanin da na Lula "Kuna iya tafiya Maryama, Amman kada ki manta da buƙata ta a gare ki" Cikin mutuwar jiki muka taso muka fito, tabbas idan raina yayi dubu ya ɓaci, a bakin ƙofa muka haɗu da afnan ɗin, tana yi man magana amman ni Sam hankali na ma baya kanta, murmushi kawai nayi mata na raɓa ta na wuce, juyowa tayi da niyyar binmu, na sanya hannu na dakatar da ita gami da girgiza mata kai, sannan na sanya ƙafa cikin sauri na bi umma ta da har ta kusa ficewa a babban falon. Wucewa Afnan ɗin tayi zuwa cikin falon Hajiyan, tare da zama cikin tashin hankali don ta san halin mom ɗin tata sarai "Mom me kika yi masu? For God sake me kika faɗa masu?" ta faɗa kaman zata yi kuka, "ke dallah saka rai shashasha, me kika gani jikin waɗancen faƙiran da har kika liƙe masu, har kina ɗaukarta kuje siyayya tare? Su fa ƴan aikin mu ne, ko kusa ba tsararki bace, bata da wani amfani wajenn mu in ba tayi mana aiki ba mu biya ta, ko kaya sai mun sanya mun cire sana muke basu su sanya, Amman wai kece yau kike haɗa kanki dasu, har kike zuwa ɗakinsu ki zauna, to ahir ɗinki wlh in ba haka ba zan saɓa maki fiye da tinaninki wallahi" ta ƙarashe tana mai nuna zallan ɓacin ranta ga autar tata "mom, ni fa banfisu da komai ba, in fact ma, babu Wanda yafi wani wurin Allah sai wanda yafi tsoron shi, so ni gaskiya momy baki kyauta mani ba, ai su ɗin ma ƴan adam ne, wanda ya halicce mu ya bamu, suma shi ya halicce su, kuma bai manta dasu ba" ta ƙarashe cikin matsanancin ɓacin rai, domin ga alama mom ɗin tata magana marar daɗi ta faɗa masu, kuma akan ta ne, mom ɗin ce ta amshe da cewa "au haka kika ce? Ashe ba zaki dena ba kenan? Maza ki shirya kayan ki, in kin fita ki kirawo man Nafeesa kuzo ku koma inda kuka fito domin bazan lamunci wannan iskancin naki ba wallahi, kada in saɓa maki" Fashewa tayi da kuka gami da barin part ɗin ma gaba ɗaya, cikin gudu ta sashen yayan nata, ta tarad dashi dawowar shi kenan daga office, don ko takalma ma bai cire ba, faɗa mashi tayi cikin kuka mai fidda zallan ɓacin rai, cikin tashin hankali ya janyo ta gami da rungume ta ya shiga shafa mata baya, cikin sanyin shi mai haɗe da miskilanci yake faɗin " Is OK Lil, is OK, tell me what is happening ne, me ya same ki? Ina ke maki ciwo?" cikin wani sabon kukan ta zayyana mashi komai dake faruwa da Abunda mom ɗin tasu tayi, zaunar da ita yayi yana mai faɗin "is OK Afnan, kinsan halin mom sarai, no, bai ma kamata ki ɓata ma kanki rai ba hakanan, ko ni da kika ga ina gaya mata gaskiya ba saurarena take yi ba a times, sai muyi mata addu'a insha Allah zata gyara halin ta, kiyi shiru babu inda zaku koma sai hutun ku ya ƙare, Amman ina so kema ki ɗan ja baya da su, saboda kada ki dinga ja masu ɓacin rai wajen mom ɗin, kin gane ko? Gyaɗa mashi kai tayi tana mai faɗin "na gane Yaya, amman wlh maman Suhana ba lafiya gareta ba, ina gudun ɓacin rai ya sanya wani abu ya same ta, gashi na baro Phone ɗita ɗaki balle in kira su na basu haƙuri" ta ƙarashe faɗi tana goge kwalla da ke saman fuskanta kwance shaɓe shaɓe. Is OK, kwanta nan ki huta,bari in shiga in watsa ruwa, sai in fito mu san abun yi,; ya faɗa mata haka ne don ya san rikicin Afnan, tana iya cewa zata kuma zuwa sashen nasu, kuma shi ba zai so hakan ba, gara ace ta ɗan ja bayan dasu, ta bar mashi komai a hannun shi insha Allah shi zai daidaita komai. Ni kau muna fita na kama umma ta muka nufi sashen namu, ina kallon mama Talatu murna fal cikin ranta, ga duk kan alamu ma laɓe tayi mana, domin taji Abunda Hajiyan zata faɗa, dama ita ta kai mata gulmar, kuma tayi ta zuzuta Hajiyar tana ƙara ma labarin gishiri, har cewa tayi Afnan ɗin sai ta kai ƙarfe sha biyu a ɗakinmu, kuma wai kuɗi take kashe mana sosai muke yi mata wayau, kuma yanzu na fara jin kaina daidai da su Nihal, saboda irin sutura da afnan ɗin wai ta siyo mun daga cen ƙasar wajen. Lafiya muka isa ɗaki, duk da umman tawa na ƙoƙarin dannewa, tinda ta lura da kwallar da nake share wa akai, akai, Amman hakan bai hana ta kwantawa ba, ba tare da ta furta ko uffan ba, nima bazan tada maganar ba, saboda maganganu ne marasa daɗin ji, to kenan ma tana nufin ƙilan bama da asalin kenan?, me umma ta ke nufi da ɓoye mana salainmu da take yi? Me hakan ke nufi,? Ganin ta samu barci ne, ya sanya nima komawa gefen ta na kwanta ƙasa, nayi matashi da katifar tamu, ina fata in ta farka komai ya wuce guri ta, ina fata kada ta tashi da :a in rai, domin kafin ta kwanta saida na ɓalli maganin ta na bata, na ƙudurce a raina zan nisanci Afnan ɗin, ba tare da na bari ta zargi wani abu ba, sai dai don mu tsira da mutumcin mu. Afnan ɗin ce ta roƙi Yaya Al'ameen ɗin da ya ara mata wayarshi ta kirani, sai kuma ta manta bata riƙe number ɗin wayata ba, dole ta sanya ta haƙura da niyyar in mun haɗu cikin gida zata sake bamu haƙuri dangane da Abunda mom ɗin tata tayi mana. Ta ɓangaren Hajiya kuwa, ko da ta tuntuɓi Aunty feena da maganar komawa, cewa tayi gaskiya ita ba yanzu ba, duka ma yaushe tazo? Kuma wannan dalilin ma bai kai Abunda za'a ce an koma saboda shi ba, ai tinda an ja kunnen Afnan ɗin shikenan bazata kuma maimaitawa ba,; su kuwa su Aunty saudat da sauran ma'aikatan gidan daɗi suka ji, wai ko ba komai an nesa ta ni da afnan, dama ƙaryar tawa ta Afnan ɗin ce (oh🤔 wai ko ma yaushe Afnan ɗin ta dawo, duka duka?) Haka Ya Ameen ya ta lallaɓa Lovely sister ɗin tashi har ya samu sukayi kwana uku da faruwa Al'amari, dama Alhaji mustapha yayi tafiya, duk wainar da ake toyawa bai sani ba acikin gidan, wannan ce ta sanya bayan ya dawo Al'ameen ɗin ya kuduri niyyar tunkararshi da maganar karatun suhan ɗin, a ganin shi wannan ce kawai damar da zai yi amfani da ita wajen ceto suhan ɗin da mahaifiyarka a halin taskun da suke ciki. ********************** Ƙarfe takwas daidai 08:00pm yayi sallama falon abban nashi, tafiya yake cikin salo shi na cikakke ɗa namiji, duk da yana da sanyi, wannan ce ta ƙara ƙawata tafiyar tashi, murmushi Alhaji mustaphan ke bi shi dashi, har ya ƙara so ya zauna kujerar dake kallon ta Alhaji mustaphan. Ɗan sunkuyar da kai yayi alamar girmamawa tare da faɗin "ABBA barka da dare" miƙa mashi hannu Alhajin yayi suka yi musabaha, "barka ka dai Son, ya aiki ya jama'a?" Abban ya faɗa fuskar shi cike da annashuwa, "Lafiya ƙalau Abba , an dawo lafiya.?? " ya faɗa cikin girmamawa, "Lafiya ƙalau Son, ina fata dai lafiya? Al'ameen ɗin ne ya amsa da" Lafiya lau Abba, wata magana ce nazo muyi idan ka da lokaci". "To to to, bismilla ina jinka Al'ameen ince dai ko lafiya ko?" Alhajin ya faɗa cikin dattako, lokaci daya yana mai ajiye kofin coffe da yake sha a hankali, ya tattara duk kan natsuwarshi ya ɗora ta kan mafi soyuwa daga cikin ƴaƴan shi. Natsuwa Ya Ameen ɗin yayi tare da warware mashi komai da ake ciki, dangane da karatun suhan ɗin, sai dai bai faɗi Abunda mahaifiyarshi tayi ba, sannan ya ɗora da faɗin "Abba kuma ina so asamu wasu masu aikin da zasu mayi gurbin su, Kaga dai ita maman yarinyar ba cikakkar lafiya gareta ba, kowa kuma ya sani, sannan idan Allah yayi ita kuma Suhana makaranta zata tafi, Kaga akwai nbuƙatar wasu madadin su, sannan bana so mom ta san da hannuna ko na Afnan a ciki, ka shige mana gaba wajen ganin ka daidaita komai wajen hajiya" Murmushi Alhaji mustaphan yayi irin nasu na manya, sannan ya ɗora da faɗa ya aka yi ba'a faɗa mashi hakan ba tun farko? Ai da yanzu ma yarinyar tayi nisa a karatu, ko ma ya tura ta cen wajen Aunty feena tayi karatun ita da Afnan ɗin, Amman ko yanzu babu matsala, babu Abunda zai gagara da izinin Allah, wasu ma an temakesu balle waɗan da suke ƙarƙashin su?, shi ɗa ai na kowa ne, kuma baka san mai amfanar ka ba nan gaba. "Babu komai Al'ameen, ka bar maganar a hannuna insha Allah da kaina zan samu ita mahaifiyarka tata, zan kuma roƙe ta wannan alfarmar in har na isa tayi man" Alhajin ya faɗa cikin son ƙarfafa ma Al'ameen ɗin guiwa ga temakon da yake son yayi, ko bayan ba ranshi, shi ya san ya bar wanda Al'umma zasu amfana dashi, ya san ya bar ma dadi, ko ma yace mafi yi, domin Al'ameen ɗin yaro ne irin wanda kowanne uba yake da burin ace ya mallake shi, a matsayin magaji. Cikin jin daɗi da godiya yayi ma Abban nashi sallama gami da cewa "bari in barka haka nan Abba, ka huta na san ka gaji, a tashi lafiya, sai da safe" ya faɗa yana Miƙewa da niyyar barin ɗakin, da kallo Alhaji mustaphan ya bishi yana ƙissima wani al'amari da zai faru nan gaba ƙaɗan akan ɗanɗan nashi mai girma, tabbas yana da buri da fatan hasashen nashi ya zamo gaskiya. Murmushi yayi yana mai janyo kofin coffe ɗinshi ya cigaba da kurɓa cikin dattako gami da faɗin "Allah shi kaimu Son" _Toh fa Fans, magana ta girmama, lamarin ya kai kotun ƙoli, ko ta yaya Alhajin zai yi domin shawo kan maman Suhana?, Kudai kuci gaba da bin Alƙalamin Oum Deedat domin ta warware maku zare har abawa_ _~Oum-Deedat ce~_ [8/5, 8:23 PM] Aminatu Hassan: 🌹 *_BAN FI ƙARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u nopain✍🏽~* *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Fans ina jin daɗin comment ɗinku, hakan na ƙara man ƙwarin guiwa, nagode akafta* _*Page ~10~*_ °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Takowa ya cigaba da yi a hankali cikin salon tafiyar shi ta ingarman namiji, daf dani ya sunkuyo ta yadda zan iya jiyo shi, sannan ya shiga faɗin "pray for your mom, yanzu ba kukan ki take buƙata ba, sannan ki tashi daga wajen ki koma bisa chair kin tare hanya, wani zai iya bugeki" Abunda ya faɗa kenan a gaggauce ya koma inda yake zaune ya sake zama. A hankali na tashi ina mai haɗa hanya cikin jin juwa da ke neman yin haji-jiya dani, kujerar dake kallon tashi na zauna tare da juyar da kaina daga saitin shi, ta yadda ba ma zamu iya haɗa idanu ba. Akai Akai yake ɗaga idanu yana kallon kyakkyawa agogon dake hannun shi samfurin Apple, sai kuma kiran da akeyi mashi Akai Akai yana latse wa. Ƙarar buɗe ƙofa ce ta dawo da hankalin mu duka wajen, zabura muka yi mu duka biyun wanda a tare muka isa ga likitan da ya fito daga cikin ward ɗin "likita umma ta ta farfaɗo? Kaddai kace man ta mutu dan Allah" na faɗa ina mai matso wani sabon kwallar, "ummanki lafiya lau ta farfaɗo amman mun yi mata allurar barci saboda ta sake samun hutu, zaki iya shiga ki ganta nan da anjima idan ta farka" ya faɗa man yana mai maida hankalin shi kan yaya ameen ɗin da yake tsaye ta gefen mu, "a'ah yallaɓai ashe baka shiga office ɗin ba? Sai ka zauna waje?" dan guntun murmushi yayi sannan yace ma Ya Ameen ɗin "to muje sai in maka ƙarfin bayani ko" ya wuce gaba Ya Ameen ɗin ya bishi a baya, da idanu na raka su har suka shige office ɗin sannan na sauke ajiyar zuciya lokaci guda ina mai hamdala gami da sanya hijab ɗina na share dukkan ƙwallar dake kan fuskata, muskutawa nayi sannan na maida duba na kan mama Talatu dake tsaye tana binmu da kallo da kuma naɗe dukkanin motsin mu cikin fai-fain ta na gulma, ɗan taɓe baki nayi kaɗan ina mai rayawa a cikin raina "dukkan ku zaku gama ne, zaku gaji ku bari, ai Hajiya Kubra ba'a mata gwaninta. *************** Likita ne ya zauna a kujerar sa gami da nuna ma Al'ameen ɗin kujerar zaman patient," Bismillah yallaɓai ga wuri zauna" bayan ya Ameen ɗin ya zauna ne sannan ya muƙa mashi hannu suka sake yin musabaha gami da ƴan gaishe gaishe, dama sun san juna don shine family doctor ɗinsu, kuma a asibitin ne suke da file, Dr. Ashafa kenan kwararren likita ta kowanne fanni. "Yallaɓai garin yaya haka kuka bar matar nan cikin irin wannan hali? Abun yayi tsanani, zuciyar ta ta kusa ta buga, ta daɗe da ciwon zuciya duk da bincike ya nuna tana kan drugs, sai dai ba wasu masu ƙarfi bane, ba zasu yi tasirin hana zuciyar kumbura ba, gaskiya ba dan kunyi gaggawar kawo ta nan ba da abun ya munana, a dinga kulawa pls" ya sauke maganar tare da ɗora dukkanin idanun shi da natsuwarshi akan Al'ameen ɗin don jin amsar da zai bashi. "Dr wallahi ban san abun yayi worse haka ba, ban ma san wane asibiti suke zuwa ba, na dai san bata da lafiya Amman ban san me ke faruwa da ita ba, yanzu ya jikin nata? Ba zamu iya ganin ta yanzu ba, ina da uzuri ne tin ɗazu ma ake kira na" ya sauke maganar da gani dai cikin hanzari yake don ya ƙagara ya tafi "No babu wani damuwa yanzu mun shawo kan matsalar, sai dai gaskiya a kula, a dena yawan ɓata mata rai, in da hali ma adena bari tana aiki mai yawa da zai iya gajiyar da ita, yanzu ma zaku iya shiga ku ganta, sai dai zaku barta anan ne, ka san tsari asibitin ba'a zaman jinya" ya faɗa yana mai sake miƙa ma Al'ameen ɗin hannu dan musabaha, shima Al'ameen miƙa mashi yayi yana faɗin "Nagode Dr. Ashafa, sai dai alfarma zakuyi mana wannan karon, ita wannan yarinyar ɗiyarta ce, so ko mun koma da ita zata tashi hankalin ta ne, zata damemu da kuka, ku barta ta zauna wajen ta har muga yanda jikin zai yi, ni zan je, idan na taso daga office zan dawo inga yana yin jikin ko da Abunda ake buƙata" "OK shikenan yallaɓai" likitan ya faɗa, sannan suka juyo a tare suka fito domin shiga ɗakin da umman tawa take; ya ameen ɗin ne ya tsaya yana faɗa mana mu shiga muga jikin ta har da mama talatun domin ita zata koma ne gida. A tare muka shiga ɗakin da shi da mama talatun, likitan ne yake shaida mana banda hayaniya, kada kuma a tada ta har sai dai ita ce ta tashi dan kanta, kuma kada a bata komai taci, akwai sinadari abinci da ake bata ta iskar oxygen ɗin da yake maƙale a hancin ta. Duk iya rashin imanin mutum sai ya tausaya wa umma ta, kwance take tayi fayau da ita, numfashi take sauke wa a hankali, babu Abunda ke motsi jikin ta, jawo kujera nayi ta roba mai kyau na zauna yayin da na ƙure ta da idanu hawaye na ɗiga ɗis-ɗis saman hijab ɗina. Juyawa suka yi suka fita har mama Talatu da Ya ameen ya yafito da hannu, kuɗin taci ya bata tare da mata godiya sosai yace ta koma gida sai ya dawo, dawowa yayi ɗakin tare da kira na domin shi wucewa zai yi, a baya na bishi zarai-zarai har muka fita harabar asibitin da har mama Talatu ta samu abun hawa, ina kallon ta tana leƙowa taga shin ina zamu, sai dai ta makaro dan mai motar ma har yaja sunyi gaba, naso nayi mata godiya Amman ba komai ai bana ma fatan mu daɗe asibitin, zan yi mata idan mun koma gida. "Is OK Suuhaaan" ya faɗa a hankali bayan ya daidaita tsayuwarshi bakin motar sannan ya juya ya jingina da ita sosai, "Comon goge wannan hawayen naki, kukan ya isa hakanan, ki yi mata addu'a sannan ki guji ɓacin ran ta, a mamadin mahaifiya ta ina mai ƙara baku haƙuri, na san ita ce sanadi, Amman insha Allah komai ba zai ƙara faruwa ba" ya faɗa yana mai ƙoƙarin haɗa idanu dani, ni kau sauke kaina nayi ƙasa ina mai bin umarnin nashi na share fuskar tawa gami da jan majina a hankali na shiga faɗin "Mungode Yaya babu komai wallahi, dama umma ta tana da wannan ciwon, nima dashi na taso na ganta, ba Hajiya bace sila, Mungode da karamci Allah ya saka da Alkhairi" na faɗa ina mai ƙosawa da tsayuwar, ba zan iya jure tsayuwa wuri ɗaya dashi ba, kwarjini yake man, gani nake duk ya cika wajen, Al'ameen ɗin daban ne, akwai kamala da haiba tattare dashi, komai nashi da yake yi cikin hankali da natsuwa yake yin shi, daidai da magana kaman baya son yi, muryar shi, ƙamshin turaren shi na ƙara rikitar dani, bana son irin yanayin da nake shiga a duk lokacin da muka kasance mu biyu a wuri ɗaya, kula yayi da irin yanda duk nabi na takura, motsa bakin shi yayi a hankali ya shiga faɗin "ki koma wurin umman, zan je aiki in dawo tin ɗazu ake jira na babu Abunda zaku buƙata, akwai komai a ɗakin kuma akwai drinks a fridge zan sa a kawo maki break fast ki tabbata kunci don na san baki ci komai ba, sai na dawo" Ya faɗa, bai jira cewa ta ba ya faɗa mota gami da yi mata key, janyewa nayi na bashi hanya, ya zo yawuce bai ko kalli inda nake tsaye ba (hoooo Al'ameen miskilanci) ******************************* Mama Talatu kuwa na isa gidan sashen Hajiya kubran tayi, ta iske bata tashi ba Amman don tsabar san gulma sai da ta jira ta, bayan ta fito ne take tambayar ta ya bata ganni ba? Ban shigo aiki ba,me yake faruwa, "yo Hajiya ina ko zaki ganta? Ai bama su gidan gaba daya" cikin isa take kallon talatun, "ke Talatu bana son munafunci, faɗa man gaskiya me yake faruwa ne a gidan? Ta faɗa cikin gadara lokaci guda tana mai zama kan ɗaya daga cikin sofa na alfarma da sukayi ma falon ƙawanya, sanye take cikin wani ɗanyen lace mai azabar kyau, dama hajiya Kubra ba dai kyau ba, naira ta kwanta mata ta ko ina sai sheƙi take yi da walwali, nan mama Talatu ta kwashe ƙarya da gaskiya har faɗa mata take yi cen ta baro Al'ameen ɗin ai muna tare. Ranta ko in yayi dubu ya ɓaci, au ta hana taraiya da afnan shine muka koma ma Al'ameen? Al'ameen ɗin nata da take ji dashi tamkar tsoka ɗaya a miya, me hakan ke nufi? Dakatar da mama talatun tayi gami da miƙewa cikin takon isassu ta fita daga sashen zuwa sashen Alhaji da take barowa da sanyi safiya, Afnan ce ta fito tana kallon mama Talatu, ashe ta zo fitowa taji suna magana shine ta koma da baya take jin duk abubuwan da mama talatun ta faɗi ma mom ɗin tasu "mama kiji tsoron Allah fa, ashe ke ke hadda sa fitina tsakanin hajiya da masu aikin gidan nan? Kina shugaba baki so a zauna lafiya, to wallahi kema ba zaki ci gaba da zaman gidan nan ba muddin kika yi sanadiyyar barin su suhan ɗin gidan nan". Tana kaiwa aya bata jira cewar mama talatun ba ta koma ɗakin nata da gudu tana mai rarumar wayar tata gami da kiran Ya Ameen ɗin, tsaf ta kwashe komai ta faɗa ma gayan nata yanda taji mama Talatu na faɗa ma Hajiya, tare da faɗa mashi yanzu zata bar gidan zuwa asibitin ta taya ni zama, koma minene ya faru ai su ne sila; Dakatar da ita yayi gami da cewa ta bari sai ya dawo baya son wata matsala kuma, shi zai jawo hankalin hajiyar ta bar zancen bari ma ya faɗa ma Alhaji komai kafin Hajiyar ta isa. Da yake da tazara sosai tsakanin sashen nata da na Alhaji, lokacin da ta isa har Al'ameen ɗin ya kira Alhajin ta iske yana waya da Al'ameen ɗin ta nemi waje kusa dashi ta zauna, tana ta cika da batsewa, bayan ya gama wayar ne ya maida hankali shi kan Hajiya Kubran, da murmushi ɗauke kan fuskar shi ya shiga faɗin "uwargida ran gida, lafiya dai ko naga kin dawo, wannan kwalliya ai sai dai ace in biya" ya faɗa cikin zaulaya da murmushi a kan fuskar shi. Fuska a tamke take cewa "Alhaji ba wannan ba, yaron nan Al'ameen...." Dakatar da ita yayi ta hanyar ɗaga mata hannu gami da cewa "Abunda Al'ameen ɗin yayi shine daidai, ai suma mutane ne, ko kuma zai ƙyale ta ta mutu ne cikin gida yana kallo? Mutane su samu abun faɗa a gari? Kada in kuma jin kince komai akan zancen nan kuma anjima ku shirya ku duka muje a dubo ta, Allah ya bata lafiya shine fatan mu. Sannan ina so ki sanya a nemo maki wasu ƴan aikin da zasu zauna mamadin su, abarsu su huta hakanan ita yarinyar ta kula da mahaifiyarta." Yana zuwa nan a zancen ya miƙe gami da gyara zaman babbar rigar shi yana mai kallon ta sannan ya cigaba da cewa" Ni zan fita sai na dawo, kada ku manta ku shirya fa, sannan idan Allah ya kai mu gobe Asabar mu dukkan mu zamu je kankiya mu gaishe da su Alhaji tinda kowa yana ƙasar ki faɗa ma yaran ma su duka su shirya" da kallo ta bishi har ya fice, ita kanta ba tin yanzu ba ta san Alhajin kaifi ɗaya ne, dukkan isar ta da zartar da hukuncin ta, tana yi ne akan ƴaƴan ta kawai da masu aikin gidan sai kuma abokan kasuwancin ta. Amman Alhajin gagarabadau ne a wajen ta, duk abin da take taƙama dashi ya fita shi tsayayye namiji ne a cikin gidan sa, dukkanin hukuncin da ya yanke ya yanku kenan, ba shan ruwa ba ƙetare hanya. ****** Ƙarfe biyu Al'ameen ɗin ya koma gida bayan salla juma'a gami da yin wanka ya shirya, Afnan ya kira a waya ya sheda mata ta fito su tafi, aikau ta saɓo Nasreem ta kamo hannun Ayan, Afnan kenan sarkin ƴaƴa, ko MOM ɗin tasu bata faɗa mawa ba don ta san hana ta zata yi, biyawa suka fara yi, suka yi take away da sauran tarkace, sannan suka wuce asibitin kai tsaye. A ɗakin suka taddani zaune bisa kujera, na kifa kaina jikin gadon umman tawa da har yanzu bata farfaɗo ba, ban ma ko ji ƙarar buɗe ƙofar tasu ba, na yi zurfi cikin tunani, ƙamshin turaren shi ya sanya ni sauri ɗagowa, ilai kuwa su ne shi da afnan, sanye yake cikin dakakkiyar shadda fara ƙal, yau juma'a tu babbar rana, fuskar nan tashi fayau, idanun shi tarwai cikin farin glass ɗinshi mai kama da medical glass, idanun shi ƙyam a kaina, kallo yake man mai cike da ma'anoni da tuhume tuhume, tabbas na san laifi na, take away ɗin da ya sanya aka kawo man, tin bayan fitar shi da safe, yana ajiye bisa stool ɗin ɗakin ko taɓa shi ma banyi ba har gashi yanzu Ƙarfe uku saura; ba'a magana da ƙarfi ya sanya bai ce an komai ba, sai ma ɗan ƙutawa da yayi ya ajiye sauran ledojin da suke hannun shi ya fice gaba ɗaya a ɗakin. Gaisawa muka yi da afnan sosai kaman babu abin da ya faru, na shiga tambayarta sauran mutanen gidan, "suna gaida ki da mai jiki" ta furta ba dan taji daɗin ƙaryar da ta furta ba. Hannun Ayan na kamo ina cewa "zo mana Ayan in ba faɗa mi ya kawo gaba?" cikin ƙarfin hali har da ɗan murmushi na na yaƙe. Text ne ya shigo wayar afnan, Ya Ameen ne yake cewa lallai ta sanya ni inci abinci, shi ya wuce sai anjima zai dawo kuma lallai kar suyi hayaniya a ɗakin nan su tada umman tawa. _Kuyi manage da wannan please bana ɗan jin daɗi ne ku taya ni da addu'a fans_ ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:23 PM] Aminatu Hassan: 🌹 *_BAN FI ƙARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u nopain✍🏽~* *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ 🤸🏻‍♀💃🏻💃🏻 Kuzo ku taya ɗan ku Deedat murnar cika shekara uku cif a duniya, ina fatan Allah ya Albarkaci Rayuwar shi, ya shirya shi shirin addinin islam, ya bashi rayuwa mai Albarka, ya bashi ilimi mai yawa mai amfani, ya cika mashi burin shi na zama Soja😄😆 ya bamu ikon tarbiyyantar dashi. AMEEN ya Rab, Deedat yana gaida dukkan fans na *BAN FI ƘARFIN TA BA* _*Page ~9~*_ °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Mu kau cikin ni da umma ta, babu wanda yayi runtsawar kirki, kowa da abunda yake saƙawa cikin rai, har gara ma umman tawa, tana ƙoƙarin ganin ta kau da komai, sabo da shawarwarin likita da ya bata na tayi ƙoƙarin ganin bata riƙe abun ɓacin rai a zuciyar ta ba. Ni kuwa Allah Allah nake gari ya waye, domin na yanke shawarar ƙundunbalan tambayan umman tawa ainihin labarin mu, da asalin mu, lokaci yayi da zata dena ɓoye mani komai, na mallaki hankalin kaina, yaci ace ta fito ta fayyace mana komai kowa ya sani, ko zata fita a zargin da mafi yawancin ƴan gidan ke mana, a kan kunnen mu mun sha jin ma wasu ƴan ƙanana maganganu akan umman tawa da ni kaina ma, kai wasu ma cewa suke yi ni shegiya ce bana da uba, tinda haka suka ganta tazo gidan a wahale ga ɗiya duƙu-duƙu kuma taƙi faɗin wacece ita da kuma ainahin daga ina take. Alhaji Mustapha kuma ya kafa dokar kada wanda ya tambaye ta, har sai ta gaji dan kanta ta faɗa, a cewarshi babu kyau shiga rayuwar wani, kuma hakan zai tada mata tsohon mikin dake ranta, gida dai nashi ne, tau tinda haka ne ya bata izinin zama har iya lokacin da take so, kuma tinda aiki tazo nema a zaɓa mata marar wahala a bata har sai ta murmure. Ciwon umman tawa ya so ya tashi cikin dare, amman cikin ikon Allah abun ya taƙaita, ban so ace zan tada mata maganar da safe ba, gudun sake faruwar tashin ciwon nata, tau sai dai babu yanda na iya, wannan karon haƙuri na da kawaici na yazo ƙarshe, ba zan iya jurar ganin irin wannan rashin mutuncin ba daga wajen Hajiya kubran; da haka na samu bacci ya ɗan figeni har zuwa asubar farko da kiran sallah ya tashe ni. ******************************* Ya Ameen yana shiga ɗaki waya yasa ya kira Afnan ɗin domin sheda mata yanda sukayi da Dad ɗin nasu, "Hello yaya" ta furta daga cen ɓangaren cikin muryar bacci "My Lil bacci kike yi ne?" ya tambaye ta cikin muryarshi mai daɗin sauraro a hankali, "eh Yaya na kwanta, lafiya dai ko? Ko wani abu kake buƙata? Ta tambaye shi tana mai tashi zaune da ƙara gyara ma Ayan dake gefen ta kwance bisa gadon nata lulluɓinshi," No Lil, ina dai son faɗa maki ne munyi magana da dad ne akan maganar waccen yarinyar, Amman tinda kin fara barci mu bari zuwa safe ki same ni part ɗina kinji, Good night dear" ya faɗa yana mai datse kiran ƙit, domin ya san halin zumuɗinta yanzu tana iya cewa ta taso ta taho, shi kuma baya jin ma zai iya doguwar magana yanzu ya gaji so yake ya kwanta, yana da muhimman ayyukan da zai aiwatar gobe, murmushi ya saki na gefen baki, wanda yayi sanadiyyar ƙara ƙawata fuskar tashi cikin hasken ƙwai mai launin dark blue na dare dake falon. Miƙewa yayi cikin salon tafiyar shi mai cike da aji, ya shiga bedroom ɗin nashi domin yin shirin bacci, kayanshi kawai ya cire ya faɗa toilet ɗin da baya gajiya da shaƙar daddaɗan ƙamshin da suhan ɗin ta sanya mashi har kawo yanzu. ------------------- Bayan mun kammala komai na Al'adar mu, kama daga sallah, wanka, sai muka zauna karatu ni da umman tawa, muna gamawa ne naga umman na ƙoƙarin tashi na dakatar da ita ina faɗin "Umma ina so zamuyi wata magana dake don Allah" na faɗa ina mai rufe littafin umdatul-Ahkam ɗin gami da maida shi ma'ajiyar shi, na sake muskutawa domin girman maganar, ba zan ɓoye ba zuciya ta kaman tayo tsalle ta fito nake ji ta ƙirjina, masalan ma da naga irin kallon da umman tawa ke bina dashi, mai cike da ma'anoni daban daban, komawa tayi ta zauna domin saurarar ɗiyar tata, da kanta yake duƙe kaman tayi ma sarki ƙarya, "Ehn ina jinki mamana, sauri nake yi domin kinga lokaci ya fara ja. Sake sunkuyar da kai nayi ina mai komawa kalar tausayi maganar tayi ma baki na nauyi, shahada nayi lokaci guda na shiga faɗin "Umma ki duba girman Allah ki faɗa mani asalin mu, wanene mahaifina? ina ne asalin garin mu, umma ke kanki su wanene mahaifan ki? Umma kin fi so mu zauna a gidan da ba'a san darajar mu ba? Kin fi so mu zauna ana wulaƙanta mu, ana zargin ki, ni kuma ana sheganta ni? Kada zuciya ta tafara yadda da maganar su fa!, na bani da asali, bani da mahaifi umma! Umma su nan ɗin ba dangin mu bane, basu san zafin mu ba, ƴaƴan su ma basa so su raɓe mu, suna kyamatar mu, suna ganin sun fimu umma, bazan iya jurar aci maki fuska a gabana ba, saboda kina ɓoye mana wani abu, kinƙi ki fito ki faɗa ma kowa mu ɗin su wanene ciki kuwa harda ni...... " marin da ta sauke man a kan fuska ta har guda biyu, su sukayi sanadiyyar datsewar maganar tawa, ɗif nayi dafe da kunci, kaman ruwa ya ci ni, yau ni ce umma ta ta buga, yau ni ce durƙushe gaban mahaifiyar tawa ina faɗa mata malaman da suke barazana ga lafiyar ta, ba zan iya tuna lokacin da umma ta ta ɗauki hannu ta bigeni ba, saboda ita mace ce mai san yin hali, Sam bata da zafi; kuka na fashe dashi lokaci guda ina mai ƙanƙame jikina, yanda naga ta hassala kaman zata rufe ni da suka. "Ashe ke shashasha ce hauwau ban sani ba?, ina tarbiyyar da na baki? Ina kika kaita, nan ɗin da kike ganin ana wulaƙanta mu, ya fiye mana cen, in kika koma kashe ki zasu yi, nace kashe ki zasu yi! Ni ma ba zasu barni ba, saboda ke nake zaune nan, dan ki tsira da mutuncin ki, ki tsira da rayuwarki yasa nake zaune nan, nima abun yana man zafi, Amman ko me zasu yi mana ba zasu iya kashe mu ba, zaki mutu ne muddin kika yarda kika koma cen" kwalla ce ke shata ta a idanun umman tawa, abun da ya ƙara matuƙar firgita ni kenan, rarrafawa na shiga yi ina mai zuwa inda take na rungume ta, ture ni ta shiga yi, jeki, je ki nemi mahaifin ki, ƙila zakiyi sa'ar ganin kabarin nashi, ƙila zai iya tashi ya faɗa maki komai, Hauwa'u ban tsammanin akwai ranar da har ke zaki iya zuwa ki sanya ni a gaba ba, ki titsiye ni sai na faɗa maki wacece ke ba, na ɗauka na gama maki komai, na ɗauka na ishe ki komai, ban tsammanin zaki gaji da zama a inda na zaɓa mana rayuwa ba, nace kashe ki zasu yi, muddin kika yarda suka san kina nan da ranki, jeki jeki ki nemo dangin mahaifin ki, ki nemo dangi na, Amman ni kar ki ƙara tambaya ta game da su, kar kuma ki sake ki dawo inda nake, kuma duk Abunda ya same ku ke ce kika siya da kuɗin ki, kar ki ƙara tambaya ta abunda ya shafe su; Ta shiga ƙara ture ni daga jikin ta tana mai share kwallar da take ta ambaliya a fuskar ta. Ƙara ƙwaƙume ta nayi, ina mai sakin gunjin kuka lokaci guda ina mai faɗin "Umma kiyi haƙuri ki yafe man, ki gafarce ni umma, nayi maki laifi, na aikata maki ba daidai ba umma, na cutar da zuciyoyinmu umma, bansan haka ba, bansan komai ba umma ki yafe man" shiru naji lokaci daƴa kaman ma bata numfashi, A firgice na ɗago, domin in ga me ke faruwa, abunda idanunwa na suka gani ne ya sani sakin razananiyar ƙara da sai da ta cika ilahirin sashen namu. Jikin ta gaba ɗaya ya saki, kaman wadda ta mutu bata numfashi Sam, "umma ki tashi" na shiga faɗi lokaci ɗaya ina mai jijjiga ta "umma ki tashi don Allah na bari, umma ki yafe man, umma kar ki mutu ki barni don Allah, umma ban da kowa sai ke, ke ce uwa ta ke ce uba na umma, ke ce komai nawa umma, kar ki mutu ki barni a cikin gidan nan umma, zan mutu nima in biki wallahi muddin kika barni, umma basa son mu basa ƙaunarmu, kar ki barni ni ɗaya a cikin gidannan" kuka ne gami da majina suka bi suka haɗe a yalwataciyar fuskar tawa, bama ta su nake yi ba, balle in mai da kai wajen share wa, gunjin kuka na nake yi mai cike da ruɗani kala kala, yayin da umman tawa take sharaf a jikina babu alamar numfashi tattare da ita, kwantar da ita na shiga yi lokaci guda ina mai girgiza kaina "umma ta bazata mutu ta barni nan ni kaɗai ba, bansan kowa ba umma sai ke" haka nake faɗa yayin da na tashi na fice da matsanancin gudu zuwa nemo wanda zai duba man ita, a tsakar gida muka haɗu da sauran ƴan aikin gidan da duk sun jiyo kuka na sun fito hankali tashe, hannun uwani na shiga ja ko sauraren ta banyi ba ina faɗin "mama uwani Kuzo ku duba man umma ta kar kuce man ta mutu, kar kuce man bata da rai, kar ku kashe man ita" mama Talatu Kuzo" na saki hannun mama uwani da nufi mama Talatu da gudu itama na shiga jan ta, ina mai sake sakin kuka mai tsuma rai, "me ya samu maman Suhana ɗin ne wai? " mama uwani take tambaya ta, ban iya bata amsa ba, domin naga sun yi tsaye sun ma ƙi shiga ɗakin, hanyar waje na nufa da gudu cikin kuka ina kwala ma baba idi kira, yazo ya duba ban umman tawa. Tin daga nesa ya hango ta, Ya Ameen ne da ya fito daga part ɗin nashi cikin shirin zuwa wajen aiki, suit ce sanye jikin shi kalar royal blue, ya matuƙar yin kyau cikin sanyin shi yake takawa da niyya zuwa ɗaukar motar tashi, ya hango ta tayi hanyar fita waje cikin matsanancin gudu, kuka ma take yi, duk ta cukuikuye hijabin tata kaman mahaukaciya, lelleƙawa nayi banga kowa ba, ga dukkan alamu ma basu baro sashen nasu na maza ba da yake cen gefe guda da namu Amman da tazara sosai, juyowa nayi da gudu zan koma sashen namu wajen umman tawa, kuka nake bil haƙƙi da gaskiya ni a tunani na umman tawa ta mutu ne, karo naci da mutum ba tare da sanin ko wanene ba na shiga jan hannun shi, idona ya kulle, bana ganin kowa bana ganin komai, umma ta kawai nake kira, lokaci guda Naji an kama man hannuwa duka an riƙe aka shiga girgiza ni, "ke ki natsu, natsu nace, ki faɗa man me ya sami umman taki? Tana ina ne?" amon murya shi ta bugi dodon kunne na lokaci guda na wara idanuna akan shi, shi dai ne, Ya Ameen ne riƙe dani ni suhan, yana girgiza ni, hannuwa na duka cikin nashi, duk da firici da halin kuka da damuwa da nake ciki, bai hanani jiyo ƙamshin turaren shi ba da kuma taushin hannuwan nashi da suke cike da wani sanyi mai ratsa zuciya, "umma ta, ba zata mutu ba, Ya Ameen kaje ka duba man ita don Allah, bata numfashi, bansan haka ba da ban mata maganar ba, kada ta mutu ta bar ni ni ɗaya cikin gidan nan bansan kowa ba sai ita duk duniyar nan" Na faɗa cikin kuka ina mai durƙushe wa kan ƙafafu na, gami da sake sakin wani marayan kuka mai ban tausayi ga mai sauraro, durƙusa wa yayi shima gami da kamo dukkanin damatsan hannuwa na ya miƙar dani "is ok, ya isa hakanan, ba zata mutu ba insha Allah muje in ganta" ikon Allah, maimakon ni da ke jan hannuwan waɗanda nake son su taimaka man, wannan karin wanda yake son taimaka man ɗin ne ya shiga jan hannuwa na, kaman makaho da ɗan jagora haka yake janye da hannuwa na, duk da nasan babu kyau hakan, ina jin babu daɗi a jikina duk kuwa da halin da nake ciki, Amman banyi yunƙurin janye hannun nawa ba, saboda da taimakon shi ne nake tafiya, jikina babu kwari Sam, kukan da nayi ya sanya har wata juwa-juwa nake gani, ƙala bance ba, na shiga bin shi kaman wadda bata san hanyar ba, har muka iso bakin ƙofar ɗakin da yake danƙam da ƴan kallon umma ta, dukkan su ma'aikata ne, Amman babu wadda tayi yunƙurin zuwa kusa da umman tawa ma da take yashe a tsakar ɗakin, duk sun tokare wasu daga ciki, wasu kuma daga bakin ƙofar dakin, wannan ƙiyayya har ina? To fa! Turƙashi, Alhaji ƙarami ne riƙe da hannuwan Suhana yana janye da ita? Me hakan ke nufi? Ita har ta kai ma tsayin wadda Al'Ameen ɗin zai ruƙo ya shigo da ita har cikin ɗakin ta? Take redio masu amfani da jini suka fara naɗar ƙarya da gaskiya, darewa suka shiga yi suna bashi hanya tare da ƙoƙarin gaidashi, ko kallon inda suke baiyi ba, domin shima sun bashi matuƙar mamaki, sai dai Al'Ameen ɗin ba irin mutanen da ke shiga sabgar da babu ruwan shi bace, hannuwan nawa ya saki yayin da yake kamo na umman tawa yana mai ƙoƙarin jin pulse ɗinta. Miƙewa yayi tare da maida kallon shi kan mama talatin dake tsaye tana recording ɗin duk wani motsi namu a ɗakin ko babu komai yau Hajiya Babba da labari kenan. "Mama ku kamo ta a sanya ta a mota muje asibiti, bari in fiddo motar" ya faɗa cikin sanyi halin shi mai cike da miskilanci, maganar ma kaman baya son yi, sannan ya juya inda nake tsaye yana faɗin "Muje" a taƙaice, lokaci guda ya shiga takawa da niyya barin ɗakin. Har yanzu kuma kuka nake, sai dai sauti kukan ya ragu sai dai kwalla da taƙi ta tsaya, bin shi na shiga yi a baya har zuwa parking lot da yake cike da motoci na alfarma; motar shi da tafi kowacce haɗuwa a wurin ya shiga tare da juyo ta daidai saitin da nake tsaye, sannan ya sanya hannu ta ciki ya buɗe man ƙofar gaba ta mai zaman banza, ganin da yayi ina ƙoƙarin shiga baya, banyi musu ba na shiga na zauna ina mai share kwalla ta akai akai, daidai lokacin da mama Talatu da mama uwani suka kamo umma tawa kaman matatta suka buɗe baya suka sanya ta, ya fita ya gyara masu sannan ya umarci mama Talatu da take shugaba ta shiga mu tafi tare da ita, yayin da mama uwani ta juya zuwa sashen namu tana mai taɓe bakin an mata buƙulun shiga haɗaɗɗiyar motar da take ɗauke hankalin duk wani dake zama sashen masu aikin. Horn yayi mai gadi da fitowarshi kenan daga makewayi, ya rugo da gudu ya shiga wangale tangaman gate ɗin, lokaci guda yana mai ɗaga ma uban ɗakin nashi hannu, ( da yake Al'Ameen ɗin mutumin shi ne sosai da sosai) shima mamaki fal cikin ranshi, ganin suhan ɗin a gaban motar Alhaji ƙarami da mama Talatu a baya sai wata mata da take kwance da bai iya tantance wacece ba bayan motar kaman matatta, Allah dai yasa lafiya ya faɗa yana mai furzar da dattin asuwaki daga bakin shi sannan ya shiga rufe ƙyauren gate ɗin da take turawa da ƙarfi saboda nauyin shi. Motar ya harba bisa titi, yayin da ya ƙara speed ɗin motar, mu da muke cikin motar gani muke tamkar baya gudu, Amman a zahiri gaskiya gudu yake wanda ya wuce ƙa'ida ma, hakan ce tasa nake ganin nawar tashi kaman in ƙwace tuƙin nake ji. Lokaci lokaci yakan juyo ya ɗan kalle ni da nake ta sharar kwalla gami da jan majina a hankali, tin kafin mu isa asibiti yayi masu waya gashi da patien emergency, aikuwa muna isa aka turo ɗan gadon ɗaukar marasa lafiya tare da gungura ta zuwa emergency ward, ɗaga ƙafa nayi da niyyar bin bayan su suka dakatar dani ta hanyar ɗaga man hannu, wannan ne ya sanya hankali na ya ƙara tashi fiye na da baya, ganin umman tawa kaman gawa sai yanda aka yi da ita, sake durƙushe wa nayi wurin ina mai sakin wani tsumammen kuka da ya karaɗe ilahirin reception ɗin, Ya ilahi, na shiga furta wa a fili ina faɗin "Ya Rab sa'idnee ya Allah" mama Talatu bata yi yunƙurin zuwa inda nake ba, kaman yanda shi ma gogan naku bai yi yunƙurin hana ni ba, sai ma waje da ya samu ya zauna ya tsura man idanu yana mai ƙara nazari na, lokaci guda ya miƙe tare da nufi inda nake durƙushen cikin sakon tafiyar shi mai kama da ta saraki..... *Fans Kuzo kuci cake ɗin deedat, fa u are All invited* ~_Oum-Deedat ce_~ [8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~11~* **********'********************* Kusan yini afnan tayi mana ita dasu Ayan, tafiya tayi wajen ƙarfe shidda saura, bayan ta sake bani haƙuri, na nuna mata haba ya wuce ai babu komai. Ya Ameen bai dawo ba har misalin ƙarfe shidda da wani abu kuma umma ta bata farfaɗo ba, hankali na ne ya tashi, office ɗin likitan na koma ya ƙara kwantar man da hankali, cewa yayi lafiya lau idan ta farka zata samu ƙarfi sosai, da wannan ne na samu naji ɗan sauƙi, babu abin da ke tadani kusa da umman tawa sai salla, ko abincin da afnan ta sanya ni inci, kaɗan na ɗan tsakura, ita ma da taga ba zan iya ci bane sai ta haƙura ta ƙyale ni. Ƙarfe bakwai daidai ya shigo bakin shi ɗauke da siririyar sallama da ni ƙaɗai na jiyo shi, kaina da yake duƙe bisa gadon umman tawa na ɗago a hankali na ɗora idanu na akan shi, idanun mu ne suka sarƙe cikin na juna nayi sauri janye nawa, kujerar da nake zaune kai na miƙe gami da tura mashi domin ya zauna. Dakatar dani yayi ta hanyar ɗaga man hannu da na lura sana'ar shi ce, watau maganar ma wahala take bashi, da ido nake bin shi har ya zauna kan sofar dake ɗakin ƙwara ɗaya tal doguwa 3seater, "ya jikin umman? Har yanzu bata farka ba?" na tsinkayi muryarshi yana jefo man tambaya cikin muryarshi mai daɗin saurare, ɗaga mashi kai kawai nayi, domin har ga Allah kwarjinn shi na hana ni sukuni, ƙamshin turaren shi duk yabi ya cika man hanci." OK" ya faɗa cen iya leaɓɓa, zaro wayar shi yayi ya cigaba da latsawa kaman ma baya cikin ɗakin. Sallama aka yi, gami da shigowa baki ɗaya, Alhaji Mustapha ne da iyalanshi baki ɗaya suka iso ta ƙarƙashin jagorancin Afnan da tace ta san ɗakin, miƙewa nayi cikin hanzari tare da masu barka da zuwa na ba Alhaji Mustapha kujerar da nake zaune, Gaishe su na shiga yi su da Hajiya kubra da take tsaye gefen Alhaji cikin isa da taƙama, "lafiya" Hajiyar ta amsa mani tana mai nufar kujerar da Ya Ameen yake kai ta zauna, tana mai sakar mashi murmushi yaƙeda wani irin kallo mai cike da ma'ano ni daban daban; Shi kau Alhajin amsawa yayi cikin sarkin fuska, yana mai tambaya ta jikin umman tawa, amsa mashi nayi ina mai ɗan murmushi iya fuska ta. Aunty feena ce ta ja kujerar da na bama Alhaji domin ya zauna sai bai zauna ɗin ba, gaishe ta nayi itama ina mai sa hannu na ɗauki Nasreem da take saɓe a kafaɗarta, ta ko wangale man baki tana wasa da hijabin jikina, Amsawa tayi cikin sakin fuska da har saida ta bani mamaki, (Lallai mai ɗa wawa inji Hausawa) jikin umman tawa ta tambaya na amsa mata kaina duƙe ina ɗan yaƙe, Allah ya bata lafiya, da Allah ya kyauta ta shiga yi man, Ameen mun gode na shiga jerawa Afnan da Ayan ne suka nufi wajen Yayan nasu tin shigowar su, dama ita ta hannun daman shi ce, Nihal ce ta dire wata ƙatuwar ledar da suka shigo da ita a hannu suna ta cin magani ko tanka man ba suyi ba, balle kuma in samu arziƙi tambayar jikin umman tawa, Angode na shiga faɗi lokacin da Alhajin ya ke faɗa man su zasu wuce Allah ya bata sauƙi. Da ameen na bishi ina mai masu rakiya har bakin ƙofar motar da suka zo da ita, wata danƙareriyar mota ce duk yawan su ta kwashe su tsaf, gaskiya motar ta haɗu iya haɗuwa, Nidai ba zance ga sunan motar ba, Amman Alhajin ne da kanshi ke tuƙawa. Hajiya Kubra ce ta kalli ɗan nata cikin wani yanayi na ɓacin rai Amman tana ƙoƙarin dannewa ne saboda kada Alhaji ya gane "Son ko zaka zo muje ne? Zamu yi ma su Hajiya siyayya ne gobe insha Allah zamu tafi cen mu duka muyi masu week end" ta faɗa tana mai gyara zama ta cikin motar, "No mom ina da uziri yanzu gaskiya, akwai inda zanje mai muhimmanci, zamu haɗu gida wajen dinner kawai" ya faɗa a dake cikin miskalancin shi, lokaci guda yana latsa wayar shi kaman ma ba da mom ɗin tashi yake magana ba; saboda ya kula da hajiyar ko jikin umman tawa bata tambaya ba, hakan bai mashi daɗi ba kuma ya kula ko Alhajin nasu ma hankalin shi bai kai wajen ba. "OK Al'ameen kayi ƙoƙari dai ka dawo kafin diner ɗin saboda zamu tattauna yanda tafiyar zata kaya" aAbban nashi ya faɗa cikin murmushi yana mai tada motar tashi, Saboda ya ji daɗin yanda ya iske Al'ameen ɗin a asibitn, ko babu komai ya san zasu samu kulawa da ta dace, kuma ya san tausaya war ɗanɗan nashi ga na ƙasa dashi. Juyawa muka yi ni da Ya Ameen ɗin muka shige asibiti n akan idon Hajiya Kubran, Cikin ɓacin rai da hajiyar ta kasa dannewa ta shiga faɗa tana faɗin "Amman Ahaji hakan ya dace ace kaman Al'ameen yana zaune suna jinyar ƴar aiki tare wannan yarinyar? Haba Alhaji, ya kake maida mu baya ne? Gaskiya Sam banji daɗi ba, iske shi fa nayi zaune hankalin shi kwance, shi ko iskar da take tasowa daga jikin su ma bai ji gurɓatacciya ce" Alhajin ne ya Dakatar da ita cikin ɗan ɓacin rai da yake ɗan taso mashi na halin Hajiyar "Ya isa Hajiya, kibar wannan maganar, wannan shine abun da ya dace kowanne shugaba yayi, na tsayawa tsayin daka ya tabbatar da lafiyar duk wani da yake aiki ƙarƙashin shi, ina Alfahri da Ameenun yana abunda yake dacewa" ƙutawa tayi cikin ɓacin rai da ƙudurce ɗaukar mataki akan al'amarin. Afnan da take cen baya sai zumɓura baki take yi tana ƙunƙuni, Saudat ɗin ce ta hamɓare ta gami da cewa "village gal, ai dama ke kullum kina bayansu kullum" Aunty Feena ce ta dalla mata harara gami da cewa a hankali "kedai kin cika baƙin hali Saudat" Shigarmu ɗakin yayi daidai da farfaɗowar umman tawa ta shiga motsa hannun ta gami da ƙoƙarin buɗe idanun ta. Cikin hanzari muka isa bakin gadon a tare, gami da furta sannu umma, lafiyar ki ƙlau? "Jiddah! Jiddah, kina ina? Matso nan Suhan, hannuna na saka cikin nata ina mai murmushin farin ciki da ke taho wa da ƴar kwalla ta," Gani umma, gani kusa da ke" na shiga faɗi ina mai durƙusa wa na ranƙwafa daidai kan ta ina mai rungumo ta cikin jikina "Hauwa'u ki yafe man kinji, na hana ki cikar burin ki, ki kira Alhaji ƙarami ki ce mashi na yarda da karatun ki, kiyi haƙuri da sannu kuma zaki san su wanene dangina, ahalina kuma, kiyi ma su Hajiya biyayya su ɗin iyayen ki ne, amanar ki na hannun su ko da bani da rai" ta ke faɗa cikin zafin ciwo idanu ta na a kulle har yanzu Kuka na fashe dashi ina mai furta "umma ni zaki yafe mawa, nice sanadin tashin ciwon nan naki umma, kiyi haƙuri umma, na dena tambayar ki komai wallahi insha Allah" Runtse hannuwa na tayi cikin nata tayi shiru a hankali tana mai sauke numfashi a hankali a hankali da gani bacci ne ta samu. Kasaƙe yayi yana ta kallon uwa da ɗiyar tata cikin tausaya wa ta ɓangare guda kuma yana mai sakin Sirrin murmushi har dimple ɗinshi ya loɓa, Ajiyar zuciya ya sauke lokacin da yaga umman ta samu bacci, ko ba komai zai samu sauƙi da zuciyar shi take yi mashi na kukan da afnan ɗin take yi, ya tsani kuka, ya tsani kuka masalan na mace mai rauni, yanzu zai ruɗe ya rasa inda zai sanya kanshi. Tasowa yayi a hankali,, ya tako har zuwa gaban gadon da ya koma ya zauna bayan da yaga ɗiya da uwa suna magana cikin shauƙin so, ledar da Nihal ta ajiye ce ƙasa gaban gadon umman tawa ya shiga buɗewa, kayan ciki ya shiga fiddowa a hankali a hankali, yana jera su bisa kyakkyawa locar da take ajiye gefen gadon, kayan tea ne, sai ruwan gora, da plax sai mug na shan tea, sai kayan marmari da su cake da sauran kayan ciye ciye da marar lafiyar zai iya buƙata. Da gani dai wannan siyayyar ta abban shi ce, dan ko kusa ya san halin mom ɗin tashi ba zata iya tsayawa yima ƴan aiki soyayya ba. Sai da ya tabbatar da ba zasu buƙaci komai ba sannan yayi mata sallama a gajarce ya fice yana mai ja masu ƙofar, da idanu na bishi har ya wuce, tabɗi Ya Ameen Matarka zata sha miskilanci na raya a rai na ina mai miƙewa domin komawa inda ya tashi dan in samu in miƙe ƙafa ta, da kallo na shiga bin wajen da ya tashin, kaman yana wajen zaune, ƙamshin turaren shi yana nan liƙe kaman nan ya fesa shi, ajiyar zuciya na shiga sauke wa a hankali a hankali ina mai furta Alhamdulillahi! ****************************** Bai shiga babban part ɗin ba saida ya koma nashi yayi wanka ya kintsa sannan ya nufi part ɗin hajiyar cikin takon shi kaman na saraki; Sallama yayi ya shiga, duk sun hallara a dining table suna cin abincin da sai dai aka yi ma mama Talatu umarni da ta girka shi ita da mama uwani, kujera ya ja guda ɗaya ya zauna saitin abban nashi, Mug ya ɗauka gami da haɗa cofee, domin bai jin zai iya cin komai a wajen, tsaftar umman Suhan ɗin ce kawai ya yarda da ita. A hankali ya ke shan cofee ɗin yayin da Alhaji yayi gyaran murya duk suka maida hankali su akan shi, " Gobe idan Allah ya kai mu zamu tafi kankiya, kaman yanda muka saba in mun yi haɗuwa irin wannan, Hajiya ki rubuta list ɗin abubuwan da za'a buƙata da wanda za'a kai ma su Baba ɗin, sannan ku Saudat da Nihal sanin kanku ne cewa idan muka je sai anyi maku maganar fidda mazaje, idan kuna da tsayayyu ku tura su cen kankiya su gaida kakannin naku kafin mu taho, zan yi ma yaya Auwalu magana sai yazo su gaishe su tare, sannan kai kuma Al'ameen idan an amshi list ɗin ka tabbatar ka haɗa komai cikin daren nan dan ina kyautata zaton da safe zamu wuce don na riga nasa anyi booking flight. Ina fatan babu mai magana ko?" ya faɗa yana mai maida kallon shi kan Hajiya Kubran da take zaune tana ta cika tana batsewa," Alhaji shi Al'ameen ɗin baka ce ya fidda mata ba, don na gaji da ganin shi zaune haka nan, tsararrakin shi har sun yi aure, wasu ma harda ƴaƴa, don haka shima yayi gaggawa fidda wadda yake so, in mun duba munga cancantar ta, sai a haɗa bikin da na su Saudat kawai" Ɗan murmushi Alhajin yayi yana mai maida kallon shi kan Al'ameen ɗin da ya kafe mom ɗin tashi da idanu yana ɗan murmusawa, shi da ya gano ta, watau tana gudun ya so yarinyar cen dake asibiti tare da maman ta, humm Hajiya kenan, yana fatan Allah ya shirya da mom ɗin tashi ta gane annabi ya faku, koma dai minene shi dai ai ba za'ayi mashi auren dole ba, ba kuma za'a ƙayyade mashi lokacin auren shi ba, duk tsiya dai sai ya samu wadda tayi mashi, kuma har yanzu baya tinanin ya dace, duk cikin ƴan matan da suke cewa suna so shi, shi fa ba suyi mashi ba, bai yarda da natsuwa da inganci shi ba, don duk irin ƴaƴan hamshaƙan masu kuɗi ne, masu ɗabi'a irin ta mom ɗin tashi watau wulaƙanta na ƙasa dasu, Sam basu san babu ba basu kuma san daraja ɗan adam ba, abin da umman tashi bata sani ba shine, duk wacce ya auro cikin su ya kawo mata ba zasu taɓa daidaitawa ba, saboda halin su ɗaya ne, isa, taƙama, izza da son mulki, wa zai bi wani? Murmushi ya ƙara saki daidai lokacin da yaji Dad ɗin nashi na faɗin "Tau kaji fa Son, Mom ɗin ka na nuƙatar suruka" "Amman sai inga ai shi namiji ne ya kwantar da hankalin shi ya zaɓo wadda tayi daidai da ra'ayin shi, kada ya je yayo zaɓen tumu dare, kinsan matan yanzu ɗin yanda suke" ya faɗa yana mai maida kallon shi kan Hajiya Kubran. "Haka ne Alhaji, sai ya duba cikin lokaci, in bai yi yanzu ba, sai yaushe? Ko so yake ayi mashi tare da Afnan ne? " Ta faɗa tana mai goge baki da soft tissue dake ajiye gefe da gefen dining table ɗin, miƙewa tayi tare da faɗin Al'ameen ɗin ya biyo ta domin su rubuta Abunda za'a buƙata tare, gami da ficewa ta haye sama nata. Al'ameen ɗin ne ya bita a baya, tare suka isa falon yayin da ta wuce bedroom ta ɗauki wata jotter mai kyau ta zauna ta shiga zana abubuwan da za'a buƙata cikin isa da taƙama, yayin da suka baro Alhaji Mustapha ɗin da sauran ƴaƴan nashi yana jin damuwoyin su, domin shi mutum ne mai yawan jiɓintar Al'aamarin iyalan nashi, dama kuma haka ake so, haka ya kamata ace ko wanne mai gida yana ma iyalanshi, komin girman shi kuma komin matsayin shi. Bayan Hajiyar ta gama rubuta komai ne ta miƙa mashi, gami da cewa ya duba in da wani abu sai a ƙara, dubawa ya shiga yi cikin halin ko in kula da isar da mahaifiya tashi take ta zubawa, babu komai ya faɗa mata gami da miƙewa don barin ɗakin. Dakatar dashi tayi, tare da ce mashi ya zauna zasu yi wata magana ne, zaunawa yayi bisa sofar dake kusa da tata ya bata dukkain natsuwar shi, domin shi mutum ne mai biyayya da son gamawa da iyayen nashi lafiya, shiru ne ya biyo baya na ƴan dakiƙu, domin ta san abun da zata zo ma ɗan ɗan nata ba lallai ya ɗauka ba domin ita ta haife shi, ta san halin shi sarai. "Al'ameen watau na lura ka fiye shiga Al'ameen Suhan da maman ta, bana so fa raini ya shiga tsakanin ku, kuma da me suka fi sauran ma'aikatan gidan nan ne da kafi basu cikakkiyar kulawa, ko dan Kaga mahaifi ka ya ɗaure maka wutsiya ne? Tau fa ka sani ni bazan lamunta ba, tinda Alhaji ya ce a ƙyale su da aikin gidan, da ta samu lafiya ka faɗa masu su tattara su koma cen inda suka fito tinda ba zata faɗi ainahin daga ina take ba ita daƴar tata, kuma ina so ka samo mana kuku cikin ma'aikatan company ɗinka guda biyu, wanda ka san sun ƙware sosai, saboda Sam girkin talatun nan baya man daɗi" ta faɗa cikin muryar ta, da ta koma ta mulki gaba ɗayanta. "Mahaifiyar tashi ya tsura ma idanu har saida ta kai aya, ba tare da ya katse ta ba, sannan ya muskuta ya gyara zama," Mom ina so ki sani, ni duk cikin ma'aikatan nan babu wanda na fifita, duka matsayi su ɗaya ne a wuri na, mom rashin lafiya tafi gaban komai, kuma ko da sun bar aiki, bana da hurumin korar su, kin manta ne dad yace gidan shi ne? Kuma ya basu izinin zama har zuwa lokacin da suke so, ko kuma suka gaji dan kansu, babu wanda zai hana su tafiya, so mom ina ganin wannan maganar yafi da cewa ku tattauna ta da dad, duk hukuncin da ya yanke a kansu is better" ya faɗa kan shi tsaye, domin Al'ameen ɗin mutum ne da yake kai tsaye, watau babu munafunci ko ɓoye-ɓoye a al'amurran shi. Sannan ya cigaba da faɗin "maganar kuku kuma zan magana cikin ma'aikatan sai a turo su ko zuwa da safe ne" ya furta cikin salon miskilanci shi, tare da miƙewa ya bar ɗakin ranshi a cunkushe, bai san sai yaushe ne mom ɗin tashi zata bar halin ta ba, bai koma gidan ba ma ga baki ɗaya sai da ya tabbatar ya haɗa komai da aka bashi list, sannan ya kai ma Aunty Feena, domin yin packaging ɗinsu ko wajen mom ɗin tashi bai koma ba ya wuce part ɗinshi kai tsaye. Yana kai kafaɗar shi bisa gadon nashi, tinanin su yayi mashi sallama, kenan umman tata ta bata dama domin tayi karatun? To ko Dad ɗin yayi mata magana ne? Allah sarki umma baiwar Allah, har yanda take ma ba cikin hayyacin ta ba, maganar ta Suhan ɗin tabi iyayen shi, abun da shi kuma Mahaifiyar tashi ta gaza fahimta, me suka tsare mata? Menene ɓata fi su dashi ba? Koda yake ya lura akwai ƴan zuga cikin Al'amarin, dole ya taka masu burki, dole ya gargaɗe su indai suna son zama cikin gidan, ba zai lamunci munafunci da haɗa husuma ba, hakanan su sanya ma bayin Allah karan zuƙa ba tare da sunyi masu wani abu ba daidai ba. Yayi Alƙawarin taimaka ma Suhan ɗin domin jin ta yake kaman Afnan ɗinshi, da ƙaunar da Afnan ɗin ke mata da sanyi halin ta da kuma tarbiyyar da ta samu daga wajen umman tata, sai kuma halin da suke ciki da musguna masu da Mahaifiyar tashi ke yi, su suka ƙara mashi ƙaimi wajen ganin son ya taimaka masu bil haƙƙi da gaskiya, baya jin wani abu dangane da Suhan ɗin illa wani narkon tausayinta da ke malala cikin zuciyar shi, yarinya da ita, ba tafi shekara ishirin ba Amman tana fuskantar wannan waƙi'ar, wannan halin da suke ciki kan ƙara jefa zuciyoyin su a damuwa da shi kuma baya jin zai iya lamunta. A haka ya samu bacci ɓarawo ya sace shi, zuciyar shi fal da tinanin halin da umman ta Suhan ɗin take ciki. ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~12~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Washe gari kuwa tin da safe kowa ya shirya a gidan, wannan umarnin Alhaji Mustapha ne domin yana so su isa da wuri domin ticket ɗin safe aka samu, aika Afnan yayi tayi kiran Ya Ameen ɗin da shi kaɗai ake jira bai fito ba, sai gashi kuma cikin takun shi na ƙasaita da sanyin shi da kan ƙara mashi kwarjini a fuskar jama'a Sanye yake cikin wani lallausan yadi kalar sky blue, an mashi ɗinki Abuja style, da gani dai yana son ɗinkin, rigar iya rabin cinya ta tsaya bata kai guiwa ba, hakan ya ƙara fiddo da asalin kyawon halittar da Allah yayi mashi, kan shi babu hula sai dai gyaran fuskan da kan ƙara ƙawata fuskar tashi. Takalmin shi da hankachip ɗin da ke hannun sau ciki, shi duk kalar kayan ne sai zuba ƙamshi yake yi. Cikin ɗan sassarfa ya isa ga Lahajin dake tsaye da alama jiran shi yake yi ya fito. Gaida dad ɗin nashi ya shiga yi cikin girmamawa, yayin da Alhajin ya miƙa mashi hannu don suyi musabaha, na daga cikin halin Alhajin ne sauƙin hali da sauƙin kai, hakan kan ƙara mashi shaƙuwa da ƴaƴan nashi fiye ma da mom ɗin tasu. Matsawa yayi ga Hajiya Kubran da fitowar ta kenan cikin shigar wani ɗanyen boyel mai taushi da walƙiya, ɗan rungumo ta yayi cikin murmushi mai ƙara ƙayata kyakkyawar fuskar tashi, amsa gaisuwar tashi ta shiga yi cikin jin daɗi da ƙauna ga ɗanɗan nata, duk da bata manta ƙin yarda da maganar tata da yayi da a daren jiya, Amman ta bar ma zuciyar ta, ta kuma sha Alwashin ganin zargin ta da hasashen nata bai zama gaskiya ba. Sauran ƙannen nashi suka shiga gaida shi yayin da ya duka yana ma Nasreem wasa da miƙa ma Ayan hannu sukayi musabaha yana mai gaida yayar tashi cikin sakin fuskan da sai yana cikin family ɗinshi ne kawai zaka ganta. Shafo kanshi tayi tana faɗin "Brother fatan ka tashi lafiya" ta faɗa cikin murmushi da kan ƙara nuna tsantsar ƙaunar ta ga ƙanen nata. Alhaji Mustapha ne ya kauda masu gaisuwar da suke yi cikin cewa "Al ameen ina ganin ya kamata mu zo mu wuce ko kasan da ƙarfe 08:00am ne lokacin tashin flight ɗin. ɗan sosa kan shi ya shiga yi da ɗan makullin motar shi da ke hannun shi sannan ya shiga faɗin" Dad ina ganin ni ba zan biku ba sai dai ko zuwa gobe ko jibi ne zan iske ku cen ɗin, saboda aikin construction ɗin nan naga yana neman tsayawa, Eng ɗin ne naga yana san sanya shiririta dan yaga na cika mashi cikon kuɗin shi, and Bilal ma yace man yau zai iso ina jin ma sun taso yanzu, Ga kaya da kamfani zai fitar yau ina so inje ayi komai gabana, kasan yanzu rashin gaskiya ta yawaita" ɗan murmusawa Alhajin nashi yayi, sarai ya fahimci Ya Ameen ɗin baya son bin nasu ne, May be dan yana gudun maganar da Hajiyar tasu ta taso ita ne jiya, tana iya zuwa ta zuga Granny Zuwaira akan zancen; ɗan ƙara murmusawa yayi yana faɗin " is ok Al ameen Amman wanne kamfani ne zai fidda kaya yau?" (Domin Al'ameen ɗin shine manager ɗin duka kamfanonin Alhajin duk da shima yana da nashi) "Eh sabon na costimetics ɗin nan ne" Ya shiga faɗi da ɗan guntun murmushi akan fuskar shi yana mai son Alhajin nasu ya yarda da uziri nashi, "Tau ba matsala for now, Amman dai ina fatan zaka je cen ɗin cikin lokaci, Kaga ka kwana biyu ba kaje ba, duk da kuna waya, ya kamata kaje kaima Kaga lafiyar kakannin naka" "to Dad" ya bashi amsa yana mai buɗe mashi gidan baya ya shiga ya zagaya ya buɗe ma Mom ɗin tasu, da bata ƙara tankawa ba don duk ya tushe mata plan ɗin nata, amman ba komai, ai bata ma jin sai tayi kamun ƙafa da wani akan al'amari yaron nata, duk isar ta da dukiya ta, ita ta haife shi in ya san wata ai bai san wata ba; Mota biyu sukayi ɗaya Alhaji Mustapha da Hajiya kubra sai driver kawai, sai kuma ɗayar da ta ɗauke Aunty feena da yaran nata sai Saudat, Nihal da kuma Abie da ya hakimce a gaba. Kai tsaye motar shi ya nufa, bayan yaga ficewa mitocin daga cikin harabar gidan nasu, restaurant ya fara tsayawa ya siya abun break fast sannan ya wuce Asibiti da ya kwana tinanin su duk da son kauda tinanin nasu da yake yi daga cikin ran shi, sai dai baya iyawa, sau da dama shi karan kanshi kan shiga tinanin kan shi da kanshi, tabbas ya san yana tausayin na ƙasa dashi, da marasa galihu, da ƴan aikin nasu, tau sai dai yana mamakin kan nashi, su salon yanda yake tausaya masu ma daban ne, amman ya kan alaƙanta hakan ne da rashin lafiya da take damun Maman Suhan ɗin. Sallama yayi daga bakin ƙofa, tsam na tashi daga kan kujerar da nake duƙunƙune tin bayan da na gama sallar asubahin na kuma komawa na kwanta domin in ɗan rutsa, don cikin dare umman tawa ta farka, cikin ƙarfin hali irin nata har fira muka ɗan taɓa tana kara jaddada man maganar karatun nawa, da kuma roƙo na akan in bama dukkan Abunda zan gani a rayuwa ta ta gaba baya. Daga ciki na buɗe mashi, ina mai janyewa na bashi hanya domin ya wuce. Kai tsaye ya shiga har bakin gadon umman tawa, yana mai ajiye manyan ledojin take away da yayo mana; ɗan rankwafawa yayi daidai saitin gadon umman tawa, yana mai kallon bugawar lumfashin ta. "ta samu bacci ne?" ya jefo man tambaya yana mai janyo kujerar gefen gadon ya zauna idon shi cikin nawa, "Eh ta samu bacci, Amman ta farka cikin dare jikin da sauƙi, don har ma fira mun yi" na faɗa ina mai ƙoƙarin janye nawa idanu, tinani na ke yi, shi wanne irin mutum ne? Mutum mai daraja irin ta Ya Ameen da ba ko domin arziƙi shi ba da na iyayen shi, shi mutum ne daban ko cikin matasan garin na Abuja akeji dashi, shine yake bamu kulawa haka? Gaskiya ya cencenci a yaɓa mashi, ya cencenci a girmama shi, da dukkan iyawa. "Hop dai bata wahalar da kanta ba wajen magana? Kin dai san dokar likita, ki dinga kula" ya faɗa yana mai kauda idanu shi daga gare ni da har yanzu nake rakuɓe daga bakin ƙofa, kwarjini shi baya bari in sake a duk lokacin da nake gaban shi. "To zan kula insha Allah" na faɗa a hankali iya fatar baki, miƙewa yayi cikin halin ko in kula da tsayuwar da nake tayi, sannan ya shiga faɗin "Dictor ya shigo?" Lokacin da ya shiga ta kowa a hankali zuwa ga bakin ƙofar domin ficewa, amsar da na shiga bashi ce ta sanya shi ja ya tsaya ga barin ficewa, hakan ce ta sanya muke tsaye gaf da gaf, duƙar da kaina na shiga yi, bazan iya jurar haɗa idanu nashi ba, idan ma zan kula da jikina wata ƴar kyarma nake yi a hankali, me ke damuna ne ni Suhana? "Bai shigo ba yaya, Amman Nurse ta shigo sannan tace idan ta farka a bata abinci mai sauƙin nauyi, sannan mu kira ta, in kuma likita shigo shikenan" "Is OK Let Me Check On Him" Ya faɗa cikin salon turanci shi da yake kama da na turawan amurka da nake kallo a Tb ɗin babban falon gidan, ficewa yayi cikin salon tafiyar shi ta jarumin namiji, idan yaso komai cikin zafi zafi yake yin shi, idan kuma yaso kai kace wahainiya ce ke tafiya masalan ma idan yana jin ƴan miskilancin. Office ɗin likatan ya shiga yayi daidai da isowar shi kenan Dr Ashafa ne yayi azamar miƙa mashi hannu yana faɗin "Yallaɓai ba dai har ka shigo ba? Gaskiya waɗannan patient ana ji dasu, Fatan dai jikin na maman tamu da sauƙi? Ya faɗa cikin murmushi da san ɓoye wani abu acikin ran shi;" Zamu iya zuwa ka duba Dr saboda ina so idan jikin nata ya samu sauƙi kayi discharge nasu, zanyi tafiya ne kuma bana son barin su anan babu mai kula dasu, gara su koma gida" ya maida ma da likita amsa cikin ɗan ɗaure fuska, bai san me Dr ɗin ke nufi ba, Amman ya kula tin jiya da yanda yake kallon Yarinya da take ta fama da jinya mahaifiya tata, ko menene ma nashi na damuwa? "OK to shikenan muje rana ya daɗe" likita ya faɗa yana mai ɗan sanya shakku a ranshi, Amman dai koma minene ai zai fahimta, gaba Al'ameen ɗin yayi Dr Ashafa ɗin yana biyo shi a baya tare da kayan aikin su na likitoci Sake shigowa naga sunyi shi da likitan, watau sai da ya kira likitan kenan? Haka na cigaba da rayawa a rai ina mai janye idanu a ga barin kallon su, bakin gadon suka ja suka tsaya, hakan yayi daidai da farfaɗowar umman tawa. "Ƴan mata zo ki taimaka ma umman ki ta tashi zaune kinji, zamu auna ta ne" likitan ya faɗa yana mai waiwayowa ya kalle ni da nake zaune ina aikin binsu da idanu da nayi nayi ga barin kallon su Amman na kasa, Ya Ameen ɗin yayi kyau, wani abu ke taso man cen ƙasa rai duk lokacin da ya bayyana inda nake, tasowa nayi a hankali na kama umman tawa ta zauna sosai, shi kau gogan ko kallo na ma bai yi ba, kaman ma bai san ina ta wurin ba, ya koma mani Yaya Al'ameen ɗin da na sani tin cen baya, da baya ɗaukar wargi, fuskar shi Sam babu walwala saɓanin yanda ya fita ba daɗewa. Aune aunen su na likitoci ya shiga yi, sannan ya ɗago yana mai faɗa ma Ya Ameen ɗin komai normal, za ta iya cin komai, kuma ta kula da shan maganin ta akan lokaci, zamu iya tafiya gida, Amman nan da sati ɗaya mu dawo a sake gwada ta a gani, dokoki sosai aka shinfiɗa ma umman tawa, sannan aka hana ta cin wasu abubuwa da dama; wayyo likita, bai san ma abincin sai wanda aka ga dama aka bamu ba, in kace ba zaka ci ba sai yunwa ta kashe ka babu mai sani. A haka na kama umman tawa muka fito, bayan motar na saka ta, ta ɗan kwanta na koma na kwaso sauran kayan da suke mallakin mu, har da take away ɗin da yayo mana da ko kallon shi banyi ba, balle in buɗa inga Abunda ke ciki. Har zan shiga bayan ya tsattsare ni da idanun nan nashi masu rikita dani, sannan ya mani alama da in shiga gaba, haka kuwa aka yi shiga nayi na takure, masalan ma ga umma ta acikin motar kuma idanun ta biyu ba bacci take yi ba. Kai tsaye naga mun nufi hanyar kasuwa, ban da hurumin tanka wa balle in tambaya me zamu yo a kasuwa, ƙila uzirin shi ne zai kai shi; parking yayi bakin tanƙamemen suoer market ɗin da yake bakin kasuwar, fita yayi ya shiga ba dadewa sai gashi ya fito yaron shagon na biye dashi a baya, hannun shi niƙi niƙi da kaya, but ya buɗe mashi tare da Sanyawa ya rufe, ya zagayo ya tada motar muka shiga cikin kasuwar, nan ma soyayya yayi sosai, cikin ni da umma ta babu mai tankawa, kowa da abunda yake saƙawa cikin rai. Gida muka nufa kai tsaye, yayin da yake parking ya yafito mai gadi da hannu, cikin hanzari ya iso inda muke ƙoƙarin fitowa daga cikin motar; umarni yayi mashi da ya kira mama talatin a sashe namu na masu aiki, aiko ya ruga cikin hanzari, sai gashi da mama talatun ta taho cikin sauri, umarni yayi mata da ta kama man umman tawa mu kai ta ɗaki mu kwantar, yayin da ya kirayi mai gadin da isa da yake tsaye yana gyaran flowers da suka taimaka wajen ƙayata gidan, kayan yace su kwashe su shigar mana dashi cikin ɗakin mu, yayin da ya ja motar shi yana mai barin gidan. Kai tsaye ɗakin namu muka nufa da umman tawa da take ɗan iya taka wa a hankali a hankali, kwantar da ita muka yi, yayin da su isa suka shisshigo mana da kayan namu suka fice suna ma umman tawa sannu da Allah ya kyauta, ina kallon mama talatun tana jinjina kai tana mai ƙare ma niƙi niƙinbkayan da ta gani tare da mu, ta dai san wannan aikin Alhaji ƙarami ne, wato dama ya ƙi bin su Hajiya Babba ne domin ya tsaya bauta mana kenan ko? Wai menene haɗin shi da mu ne? Su dai basu ga wata alama da ke alamta masu akwai wani abu tsakanin Suhana ba da Alhaji ƙarami ɗin balle ace dan ita yake yi? Koma minene zata yi ƙoƙarin sanar da hajiya ɗin, me hakan ke nufi ne? Ya kamata hajiyar tayi wani yunƙuri akai wallahi, ita ta ma ga sanyar Hajiyar wannan karon akan yanda ta santa da in ta ƙi abu duk yanda zata yi akan taga bai faru ba ta sani, tana cike da tsantsar mulki da kuɗi, naira shegiya ce, mai maida tsoho yaro ta maida yaro babba. (Humm🤔🤔 Ya Allah kayi mana tsari da Hassada, ƙyashi, ganin gari da munafunci ameen ya Rab🤲🏻) Bayan duk sun fita ne, na gyara komai a ɗakin na adama komai inda ya kamata, kayan ciye ciye ne da basu da illa ga masu ciwon zuciya irin wanda likita ya bada umarnin aci, su ne ya kwaso mana su sosai da sauran kayan buƙatu har da kayan marmari ma da zasu yi ma mai rashin lafiya daɗin ci, gyaran ɗakin nayi nayo wanka na shirya kaina cikin baƙar doguwar riga mara nauyi na tattara gashi na na ƙulle cikin ribom sannan na ɗaura ɗan kwalin rigar a bisa kai na, nayi kyau daidai misali, sannan na ɗauko ledar take away ɗin da yayo mana tin asibiti na buɗe da niyyar zuba mana muci ni da umma ta, lafiyayyen chips ne da plantain, sai soyayyen ƙwai da miyar kayan ciki, sai ƙamshi take har yanzu da sauran zafin shi, saboda mazubin na glass ne, da gani dai abincin zai yi tsada, sai dai baya cuwuwa ga umma ta saboda farin mai da aka yi using wurin suyar, kaina kaɗai na zuba mawa na fidda sauran ga ƴan uwa na ma'aikata da har yanzu sun gagara shigowa yi mana koda sannu saboda tsabar hassada, Abunda na san zata iya ci wanda likita bai hana ta ci ba na zuba mata, saida na tabbatas taci na ɓalli maganin ta na bata tasha sannan na gyara mata kwanciyar ta, na koma gefen katifa na zauna ina ya ƙunar abincin ahankali Fira mukeyi jefi jefi da umman tawa da take bina da kallon tsantsar ƙauna ga ɗiyar tata, addu'a dai kam Al'ameen ya sha ta daga bakin umman tawa, godiya take jerawa wanda hakan ne ta sanya ni ɗan murmusawa a hankali dai ina ci gaba da cin abinci na; Sallama yayi daga bakin ƙofar ɗakin yayin da umma ta ta bashi izinin da ya shiga daga ciki, lokaci ɗaya tana mai umartata da shinfiɗa mashi darduma. Kasa tashi nayi, domin jikina babu hijabi babu gyale, gashi rigar mai bin jiki ce ta fidda duk surar jikin dake Sanye da ita, kuma a zahiri bai kamata ya ganni haka ba, saboda shi ɗin ba muharrami na bane, hakan ce ta sanya na shiga bin ko ina na jikina da kallo kaman mai son gano wani abu. "Hauwa'u dake fa nake magana fa, nace ki shinfiɗa mashi darduma ya zauna kin bar shi tsaye" umman tawa ta faɗa tana mai yunƙuri tashi, a haka ta samu ta zauna daidai domin Nidai na gagara koda motsi balle in taimaka mata har ma nayi mashi shimfiɗar Hankalin shi ya maida kanta da take ajiye plate ɗin abincin kaman mai tausayin ƙasar, ta shiga miƙewa a hankali, lura da yayi da Abunda take ɓoyo ko ji ma kunya ne ya sanya shi kauda kanshi gefe, ya maida hankalin shi kan umman tawa yana mai ɗan sakin guntun murmushi iya laɓɓa, ko me take ɓoyo? Wannan mitsitsiyar yarinyar ma, da yake kyautata zaton garin jiki ne ya kwashe ta, ita har tana ganin ma ta cika ta kai mace, ƙara murmusawa yayi daidai lokacin da take shinfiɗa dardumar ɗan nesa kaɗan da katifa tasu. "Nagode" ya faɗa iya maƙoshi maganar tana mashi wahala, yana mai zama ya tanƙwashe ƙafafun shi irin zaman salla, lokaci guda yana mai gaida umman tawa, cikin sakin fuska ta amsa mashi, sannan ya ƙara mata ya jiki da Allah ya sauwaƙe. Godiya ta shiga jera mashi da kuma fatan nasara da cigaba a rayuwa, harma da iyayen shi, hakan ce ta sanya shi jin daɗi, yana mai ƙara ƙaunar matar da son taimaka mata da duk ahalinta. Ikon Allah, abikan aikin mu da tin ɗazu suka kasa leƙowa su ga jikin umman tawa su gaida ta, sai gashi ɗaya bayan ɗaya yanzu da suka ga shigar Ya Ameen ɗin ɗakinmu suna shigowa gaida ta da ganin ƙwam, kowa ya fita kuma sai ya ƙara da abin da ya gani gaba. Sake natsuwa yayi yana mai ɗan yin gyaran murya a hankali, sai da ya maido kallon shi inda nake rakuɓe bisa katifa gefen umman tawa, sannan ya saki wani ƙayataccen murmushi ganin ta sanya hijabi da shi bai ma kula da lokacin da ta ɗauko shi ba, haƙuri ya shiga ba umman tawa, da mata Alƙawarin hakan ba zata sake faruwa ba, ya faɗa mata afnan ce ta sanar dashi komai; ɗan faɗa umman tawa ta shiga yi tana faɗin hajiyar ta isa ne ya sanya tayi masu faɗa, ai ba wani abu bane, gyara ne take so ayi, kuma mun ɗauka insha Allah. Haƙuri ya ƙara bata sannan ya shigo mata da maganar makarantar tawa, ta bacin yardar ta ta ƙara bashi, sai dai tana mai shawartar shi da yayi komai a hankali kada ran hajiyar ya ɓaci, ya alƙawarta mata komai ya wuce kuma babu abin da zia faru insha Allah. Maida kallon shi yayi yana mai cewa "Ki ɗauko man takaddun naki in gani ko, don mu san ta yanda zamu ɓullo ma al'amarin" ya faɗa yana mai kauda idanun shi daga kaina kaman ma ba dani yake magana ba. Miƙewa nayi cikin ɗan sanyi gami da nufar wardroop ɗin tawa, gami da janyo ƴar ƙaramar folder da takaddun tawa suke na miƙa mashi. Amsa yayi yana dubawa, mamaki fal a ranshi na yanda yarinyar take da ƙoƙari, gashi dai makarantar masu hannu da shuni tayi, saboda Alhaji Mustapha ne ya sanya ta a makarantar har ta gama, kafin abubuwa sukayi mashi yawa ya tafi wani aiki ƙasar Indiya daidai lokacin da Jarabawa tasu ta fito wannan shine ya sanya ya shafa'a da karatun yarinyar koda ya dawo kunsan mnyan mutane, ita kuma Hajiya Kubran bata tina mashi ba, a cewar ta hakan ma ya isa, wa yace ƴaƴan masu aiki na makarantar jami'a (🤔🤨😏 ke kika hana ko Hajiya Kubra) Takaddu sunyi kyau ya shiga faɗi da ɗan murmushi shi irin na miskilai, kai kace ma bai yi ba, sannan ya miƙe dasu a hannun shi yana mai cewa za'a siya jamb sai in cike tare da course ɗin da nake so, in naga ban iya ba sai in same shi ya koya man (kun ji ba Bigboo, ko ya manta da halin gidan nasu ne?) da to muka bishi da umman tawa, kuɗi ya ajiye kusa da umman tawa masu ɗan dama yana faɗin ko zata buƙaci wani abu, sannan ya ƙara jaddada mata kar taci Abunda likita ya hana, idan muna nuƙatar wani abu muyi mashi magana. Umman tawa ce ta shiga faɗin lallai ba zata amshi waɗannan kuɗi ba, cikin girmamawa ya shiga bata haƙuri da faɗin duk abin da yayi mana haƙƙinshi ne da yayi mana, wannan ba wani abun damuwa bane, duk ma in muna buƙatar wani abu mu tuntuɓe shi a shirye yake da ya taimaka mana. Godiya ta shiga ƙara jera mashi da yabanma dukkan in hidima da yayi damu ɗin "ba komai umma, Allah ya ƙara sauƙi" ya faɗa yana mai taka wa ya bar ɗakin riƙe da Takaddu na a hannun shi. Oh Allah🙏🏻 Ashe zanyi karatu a rayuwa ta? Ashe Ya Ameen na magana haka? Yanda naga ya zage suna ta fira da umma ta, kuma duk wata kalma da zai faɗa cikin taka tsantsan da girmamawa yake yin ta kaman yana magana da Hajiya kubra, murmushi na shiga saki akai akai, ina mai sauke ajiyar zuciya, mafarki a ya kusa tabbata, jikina na bani mun kusa fita daga cikin halin ƙuncin da muke ciki ni da umma ta, daga na gama karatu na samu aiki zan gina mana gida, na ɗauke umman tawa muje cen muyi Rayuwar mu, muma muci gashin kanku, mu rabu da takura da jaraba Hajiya kubra, Allah na gode maka, Allah ka saka ma wannan bawa da Alkhairi a rayuwar shi, ka haɗa ci da mata ta gari, da zata kula dashi, kuma tayi haƙuri da halin hajiya Kubran. "Tashi ki naɗe dadduman in kin gama murnar" u mata ta faɗa cikin murmusawa da ke nuna sallar jin daɗin ta, da farin cikin ta. Yunƙurawa nayi ina mai da rawa a fili na shiga faɗin "umma ai dole inyi murna kin gama man komai, Allah ya cika mana burin mu, ashe da rabon zan yi karatu nima in samu ilimi kaman yanda kowa ke samu?" Murmusawa tayi tana mai kishingiɗawa tare da faɗin "Ai wannan yaro ɗan albarka ne, Allah dai ya bamu ikon saka mashi da alkhairi kaman yanda yake mana shi da mahaifin shi, ki kauda kuɗin nan ki maida hankali ki ci abinci" da to na bita ina faɗin "ni wallahi ummana tsabar murna ma yasa naji na ƙoshi" "ki dai maida hankali" umman tawa ta bani amsa tana mai lumshe idanun ta murmushi fal a fuskar ta. Ta ɓangare guda kuwa Al'ameen ɗin na fita wayar Mom ɗin nashi na na shigowa, tare da umartar shi da cewa ko me yake ya tabbatas ya biyo jirgin yamma ya isa Katsina tana son ganin shi, shi kin mamaki ya shiga tambayar ta ko lafiya? "Lafiya lau" ta bashi amsa tana mai datse kiran, Layin Afnan ya nema gami da tambayar ta, ta faɗa mashi kawai dai taga an kira ta ne daga gidan Amman bata san ko wanene ba, kuma daga gani gulma aka kawo mata, "is OK" ya faɗa yana mai katse kiran ganin kiran babban Abokin nashi da zai kawo mashi ziyara yau ta shigo wayar shi. Amsawa yayi cikin son kauda zargin komai daga ranshi, bayan sun gaisa ne yake faɗa mashi ya iso gashi a airport, cewa yayi ya jira shi yana zuwa ɗaukar shi. Ko da ya isa ya tadda abokin nashi yana jiran shi, cikin son juna da tsantsar farin ciki suka rungume juna suna mai mararin juna da tsantsar ƙauna ga aminan guda biyu, basu bar airport ɗin ba sai da ya yanka masu ticket guda biyu tare da kallon Bilal ɗin ya shiga faɗin "yaro yau ƙauye zaka kwana, ka taddani tafiya ta gaugawa ta taso mani" cikin murmushi Bilal ɗin ya kai mashi ɗan ƙarami duka a damtsen hannu yana mai cewa "To ya zanyi Friend" ai ko ruga ka kai ni dole in kwanta, ya zanyi tinda na riga nazo?" Cikin walwala da jin daɗi suka bari airport ɗin direct gida ya wuce dashi domin yaje yayi wanka ya huta kafin lokacin sallar azahar ta ƙarasa. ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ _*Page ~13~*_ _To Readers_ --- *Abun da kuka ji da zai amfane ku ku ɗauka, wanda kuka ji akwai kuskure ciki, kuyi watsi dashi, mu ba muji wahalar zaunawa muyi amfani da idear ɗinmu ba mu rubuta maku labarin da zai amfane mu ba baki ɗaya ba, sai ku da zakuyi comment ƙarƙarinta layi biyu zuwa uku, shine zai ke maku wahala, Anya kuwa readers kuna kyautawa🤔? Muna maraba da gyara ko ƙorafi, Amman ba ta hanyar zagi, ko cin zarafi ba, kuskure kowa nayi indai kai ɗan adam ne, kuma ajizi, so saboda haka muna shawartar ku da ku dinga ƙarfafa mana guiwa, wadda kuma taga labarin baiyi mata ba, toh ta bar mana abunmu ba sai ta karanta ba, bamu sanya kowa dole ba, imfact ma babu dole sai rai yaso a rayuwa. fans muna godiya da irin supporting ɗin da kuke bamu 💓muna yinku over, Allah ya bar ƙauna, wannan saƙo ne daga ƴan ƙungiyar ~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Fira sosai suka shiga yi da aminin nashi da bashi da kamar shi, kaman ba Ya Ameen ɗin da kuka sani ba, har yana zaulayar abokin nashi, akan zancen bikin nashi da za'ayi watanni ƙalilan masu zuwa inda anan Abuja zai auri yarinyar ya tafi da ita cen. Sai da sukayi wanka suka shirya tsaf sannan suka wuce wani eatery mai bala'i kyau da tsada suka ci abinci sannan suka koma gida domin ƙara hutawa. Al'ameen ɗin ba mai yawan yawo bane indai yana ƙasa, yafi ganewa ya zauna a gida a part ɗin nashi yayi aiki. Yanzu ma hakan ce ta faru, yayin da ya jawo laptop ɗinshi ya shiga aiki, wannan ce ta sanya Bilal ɗin fahimtar cewa ƴan maganar sun bar kan aminin nashi, to ko wacce magana zai yi mashi fa zai yi mashi shiru ne, har sai lokacin da yaso tankawar kuma baya maido da zancen da ya riga ya wuce, wannan ɗabi'ar shi ce tin yana ƙarami, balle yanzu da ya girma. Kwanciya Bilal ɗin yayi domin yana jin baccin gajiya gashi ya ƙoshi har wani lumshe ido yake yi. Bilal ɗan gayu ne na ƙarshe, yana da hankali da tunani sosai duk da kasancewar shi cikin jajayen fata, hakan bai canza halin shi da mu'amala shi ba, wannan ce ta sanya abotar su da Al'ameen ɗin da take tin ta yarinta take daɗa ƙarko har kwanan zancen. Aikin shi yake yi cikin salo da kwarewa yake sarrafa kwamfuta, kaman dama cen shi ne ya ƙera ta, to ai dama karatun shi kenan kada ku manta. Kiran salla ne ya farkar da Bilal ɗin yayin da Al'ameen ɗin har ya ɗauro tashi alwalar, bayan Bilal yayo ne suka nufi masallacin da yake gefe ta jikin ɓari ɗaya na gidan nasu. Ƙarfe biyar daidai sukayi shirin barin garin, yayin da Al'ameen ɗin ya tara dukkanin ma'aikatan gidan domin bar masu jan kunne tinda za'a bar gidan ba kowa sai mu kaɗai. Ni da umma ta ce kawai bama wurin, ja masu kunne yayi sosai akan su kula da komai, Bilal ɗin na tsaye gefen shi yana ta murmusawa domin ya san abokin nashi kwarai da rashin son wargi, gashi dai ya iya mu'amala da ma'aikata dama cen, sai dai shi mutum ne mai son taka tsantsan da kula. Bayan ya gama dasu ne, ya nemi Bilal ɗin da ya raka shi ɗakin namu domin ƙara duba jikin umman tawa. Kwarai Bilal ɗin yayi mamakin ina yake nufa haka da yake ta ratsa sashen ma'aikata haka, sai dai bai ce mashi komai ba ya cigaba da bin shi a baya har zuwa bakin ƙofar ɗakin namu da yake tsaf a share tas, Sallama sukayi, yayin da umman tawa ta basu izinin shiga, kai tsaye suka cusa kansu cikin ɗakin namu da babu wadatar abubuwa. Miƙewa nayi ga barin karanta littafin *Jinnul Ashique* (na Harira ƴar fillo) domin littafin ya tafi da hankali na akwai tsantsar soyayya da abun al'ajabi da ban mamaki cikin shi, ina ma nima zan samu wanda zai gwada man irin wannan soyayya haka? (zaku iya neman shi ku karanta, zaku same shi online) Darduma mai ɗan girma na shimfiɗa masu lokacin da nake ficewa a ɗakin, Sam bazan lamunci zama na wuri ɗaya dashi ba, ƙamshin shi, idanun shi, ba ƙarami makami bane da kan taimaka wajen ruɗewa ta ba. Jikin umman tawa ya duba, Alhamdulillahi sauƙi ya samu sosai, faɗa mata yayi tafiya ta gaugawa ta taso mashi, da fatan dai babu abin da muke buƙata? Babu umman tawa ta bashi amsa sannan ta ɗora da godiya ta haɗa har da Bilal ɗin da tana ganin shi jefi jefi a gidan Amman sai ayi shekaru ma, in ba Al'ameen ɗin na gari ba. Harda Bilal ɗin a cewa babu komai Allah ya ƙaro sauƙi, kusan ma zamu iya cewa Bilal ɗin yafi gogan naku magana har ma da murmusawa, domin yau ƴan miskilancin na akai. Miƙewa sukayi suka baro ɗakin, tarin tambayi yi fal acikin ran Bilal ɗin, Amman ba lokacin yi su bane, matar ta burge shi, to wacece yarinyar da ta shimfiɗa masu darduma ta fita bayan ta gaishe su? Tsafta da ƙamshin ɗakin sun burge shi, abun ya ƙawatar dashi, matar kaman ya santa cikin ma'aikatan gidan fa, amman fuskar tata kaman ta ɓace mashi, any way🤷🏻‍♀ zai tambayi aminin nashi in sun natsu. Ta inda nake zaune jikin ɗan dandamalin flours suka zo suka gitta ni, tin daga nesa Naji tahowar su ta dalilin ƙamshin Ya Ameen ɗin da ya fara isowa hancina kafin ƙarasowar tasu, sadda kaina kawai nayi ƙasa har suka wuce, bansan barin garin zasu yi ba, wannan ce ta sanya ban masu adawo lafiya ba, kuma koda cen ma ba halina bane yawan tanka ma maza aduk al'amurran da basu shafe ni ba, sai dai ina ƙara ganin girman mutumin da ya kasance mana kaman uban gida ne a gare mu bama mu kaɗai ba, duk wani da ya kwana ya tashi ya amsa sunan ma'aikaci a gidan. Bilal ɗinne ma naga kaman zai tsaya sai kuma yaga abokin nashi bai tsaya ba, ya wuce kai tsaye zuwa ga motar tashi yana mai kwala ma Idi driver dake cen bisa kujeru dake wajen gate suna fira da mai gadi. Dagudu ya taso ya wuce ta inda nake zaune, hankalin shi ma bai kai kaina ba, ga motar ya isa yana mai russunawa tare da faɗin "gani yallaɓai" makullin motar ya miƙa mashi yana faɗin "airport zaka kai mu sai ka dawo da motar" "To" yace yayin da ya amshi makullin ya shiga mazauni driver ɗin, Bilal ɗinne ya shiga gidan gaba, yayin da Al'ameen ɗin ya shiga gidan baya, shiru ya ratsa motar in ka ɗauke ac dake yin aikin ta a hankali a hankali. Ban jira tashin motar tasu ba, na miƙe a hankali cikin salon tafiyar tawa na nufi sashen namu; ta gefen idanu ya bita da kallo yayin da suke ficewa daga cikin katafaren gidan nasu, shi kau Bilal juyawa yayi ya bita da kallo har suka fice yana ƙissima abubuwa da yawa a ranshi. Ƙarfe biyar da rabi jirgin nasu ya ɗaga zuwa Kaduna daga cen za'azo ɗaukar su domin ya ma mom ɗin tashi waya tin ƙarfe huɗu da ta turo driver ya ɗauke su. Shidda da wani abu suka isa, sun tadda driver na jiran su, basu wata wata ba suka nufo gidan nasu kai tsaye, da yake lafiyayyar mota ce sai gashi bayan isha'i da kaɗan sun isa state ɗin tasu ta hauhuwa, (Katsina ta Dikko kenan, garin tudu ɗan marna, ɗakin kara kunya gare mu ba dai tsoro ba) Mama zuwaira tayi murna da zuwan jikokin nata, masalan Al'ameen ɗin da Bilal dama ta kwana biyu bata ga Bilal ɗin ba, saboda ba yawan zuwa yake yi ba, family ɗinshi duka suna cen ƙasar, har ma da kakar tashi mace tinda namijin ya rasu. Aiko babu wata wata ta ta sanya masu aikin ta suka shirya masu teburin cin abinci, kala kala, duk da cewa da suke yi sai sunyi wanka sun huta hakan baisa ta kyale su ba, jikin tsufa ya kama ta dole su lallaɓa ta, haka suka ɗan yayyabiɗa sama sama, suka tashi, shi Al'ameen ɗin ma yafi shan coffe da salak ɗin da yaji ƙuli-ƙuli, 🤣kunsan gidan tsofaffi ko da me ƴaƴan su zasu zama, sun fi son abincin su na gargajiya da muhalli su na gado🤣 Da yake shi Al'ameen a nan gidan Alhaji Isuhun yake da part, wannan ce ta sanya basu haɗu da sauran ƴan uwan nashi da iyayen ba daidai zuwa safe. Bayan sun gama komai ne na al'adar kwanciya a ɗakin da yake mallaki Al'ameen ɗin suka kwanta domin gajiya ta baibayesu na zaman mota ga doguwar tafiya (a cewar su) Bilal ɗinne yayi gyaran murya yana daga kwance gefen gadon, hakan ce ta sanya Al'ameen ɗin miƙewa zaune yana mai fuskantar abokin nashi, da ya daɗe da Miƙewa zaune shima. Natsuwar da yaga yayi ce ta sanya shi gane cewa maganar mai muhimmanci ce, hakan ce ta sanya shi tattara dukkan Natsuwar shi shima a kan abokin nashi. "Bros ina so ne muyi wata magana da tin ɗazu nake so inyi maka ita, Amman na zaɓi nan ne saboda naga yafi da cewa muyi ta a natse" "Ehen ina jinka friend faɗa man minene kake son ji da baka san shi tattare dani ba" Al'ameen ɗin ya faɗa yana mai gyara zaman shi gami da jingina bayan shi da makarin gadon. Bilal ɗinne ya gyara zaman shi daga kan gadon sannan ya cigaba da faɗin "Ina so ne in san wacece matar nan da muka shiga ɗazu sashen ma'aikatan gidan ku muka dubo? Kuma wacece yarinyar da muka tada ɗakin? Menene alaƙarsu?" Da kallo Al'ameen ɗin ya bishi na tsawon mintina biyu, ganin abokin nashi na so ya ɗauko mashi dogon labari gashi shi kuma bacci yake ji. Ganin da yayi abokin nashi ya shiga koma ta tinani ne ya sanya shi sake faɗin" kayi haƙuri fa idan na shiga hurumin da ba nawa ba, Amman matar ta burge ni iya matuƙa, sannan bansan dalilin barin yarinyar ɗakin ba lokacin da muka shiga" "Huh" Al'ameen ɗinne ya gumtsi fuska ya fesar lokacin da yake zamewa ya kwanta akan bayan shi yana rigingine yana kallon pop ɗin dake liƙe sama ɗakin da aka ƙawata da fitili masu matuƙa kyau, sai dai a kashe suke saboda dare yayi bacci suke so suyi, hannun shi duka biyu yasa ya tallafo kanshi dasu yayi matashi, lokaci ɗaya yana mai lumshe ido cikin sanyi halin shi na miskilai, a hankali ya buɗe bakin shi ya shiga furta "Frnd bacci nake ji mu bar maganar nan zuwa safe, ni yanzu tinani na yafi karkata akan dalilin da ya sanya umma ta kiraye ni cikin gaugawa" Bilal ɗinne ya sauke dukkan ƙafafu nashi ƙasa daga kan gadon yana mai cewa "OK as you wish Bros, Amman ka sani na san halinka, baka komawa kan magana muddin aka yi ta ta wuce kenan, na lura baka son faɗa man ne, ina mai baka haƙuri akan shiga al'amurran ka da nayi, duk da na lura kana taka tsantsan" daga haka ya miƙe gami da shige wa toilet ɗin da yake ta cikin ɗakin. Tinani da tarabbabi ya sanya Al'ameen ɗin ciki, tabbas bai kyauta ma aminin nashi ba, ya so kanshi da yawa, babu abin da suke ɓoye ma juna, abokan shawarar juna ne, ko wanne hali ɗaya ya shiga suna taruwa ne su warware natsalar su a tare, me Bilal ɗin ke son sani?shima bai san ita ɗin ko wacece ba, bai san umman Suhan ɗin ba kaman yanda ita ma kanta ɗiyar bata san kanta da ko ita wacece ba. Bilal ɗinne ya fito yana tsane fuskar shi da ɗan ƙaramin towel, yayin da ya isa ga ƴar ƙaramar hangar kusa da mirror ɗin da ya mamaye kusan rabin bango ya maƙale shi cen, ya taka a hankali ya isa ga gadon gami da kwanciya yaja blanket ɗinshi mai taushi ya lulluɓe kusan rabin jikin shi "Suhan, Umma Maryama" Abunda Al'ameen ɗin ya faɗa kenan sound so husky, hakan ce ta sanya Bilal ɗin lamo yana sauraren shi, yayin da ya yi tsammani ma bacci ya kwashe shi, domin a yanda ya tafi ya bar shi a haka ya dawo ya iske shi, da alama ma ko matsin kirki baiyi ba, juyowa yayi yana mai fuskantar Al'ameen ɗin daga kwance. "Nima ban san su ɗin ko su wanene ba," Al'ameen ɗin ya cigaba da magana ba tare da ya jira cewar Bilal ɗin komai ba, to shi ɗin ma baiyi niyyar tankawar ba, saboda ya san halin aminin nashi sarai. "Shekarar su kusan sha bakwai a gidan namu, wannan baisa a san ko daga ina take ba tare da yarinyar dake hannun ta da take iƙirarin ita ce ta haife ta, sai dai sanin wanene mahaifi yarinyar, daga ina suke? Shine wannan sai ita umman, ciwon da Kaga mahaifiyar yarinya nayi Mom ɗita ce sanadi, wannan ce tasa Kaga ina basu kulawa daidai gwargwado" daga nan ya kwashe komai da ya sani ya faɗa ma Bilal ɗin na dangane da Rayuwar su Suhan ɗin, sannan ya ɗora da faɗin, "Bataso a taimaka masu ne ko alama, bansan minene matsala tata da hakan ba, na sha yunƙurin taimakon ta tana dakatar dani, Abunda na lura dashi ma, dukkan ma'aikatan gidan masalan matan, suna nuna masu wariya da ƙyarar su, Amman hali irin na Umman da take da haƙuri da tawakkali hakan bai nuna wata damuwa ko gazawa koda a fuskar ta ne kuwa, yanzun ma da ta amince da maganar karatun yarinya saida aka kai ruwa rana sannan, kuma ta gargaɗe ni da ɓoye duk wani taimako da zan masu dangane da karatun yarinya, ga dukkan alamu Mahaifiya ta ita ce babbar matsalar matar a gidan" Dakatar dashi Bilal ɗin yayi gami da tambayar shi "yarinyar fa? Naga kaman bata son mu'amalan tar kowa a gidan ayadda na lura ko mutane ma kaman bata shiga, ka duba tin daga gaisuwar da tayi mana bata ƙara tankwa ba duk da a gaban idon ta muka gitta ta inda take zaune, ƙarshe ma Miƙewa tayi ta koma cikin sashen nasu" Wannan karin, Al'ameen ɗin ne ya kalli Bilal ɗin ido cikin ido sannan ya shiga faɗin "Oho mata, ita wannan haka take, ban cika kula da al'amurran ta ba, Amman zan iya ce maka irin tarbiyyar da mahaifiyar tata ta bata kenan, bata saki jiki da kowa in ba mahaifiyar tata ba, hakan ya samo asali ne daga wariya da ƙyara daga sauran ƴan uwan nasu ma'aikata" ya faɗa yana mai ɗan taɓe bakin shi, sannan ya juya ya gyara kwanciyar shi gami da karanta addu'ar barci. Ganin haka da Bilal ɗin yayi, ya san ba zai ƙara tankawa ba kenan ya kuma wuce da maganar kenan. Shiru yayi shima yana mai hangen bayan kan Al'ameen ɗin da suma ta kwanta mashi luf abinshi, abun ka da farar fata sai yayi kaman wani ba'indiye, ta cikin haske dumlight ɗin da suka sanya mai ɗan duhu sosai kalar shuɗiya. Shiru ɗakin yayi in banda ac dake aikin ta a hankali a hankali, sai kuma Bilal ɗin dake ta saƙa da warwara, idanun shi ƙyam akan murɗaɗɗen abokin nashi, da tini bacci yayi awon gaba dashi, yana ta sauke numfashi a hankali, a hankali. Shima dai a haka baccin ya kwashe shi, washe gari duk suka haɗu a nan cikin gidan Alhaji Isuhun da duka nan suke karyawa da iyalan ƴaƴan nasu guda biyu watau Yaya Auwalu da Alhaji Mustapha Dambulan Sai da kowa ya gama karyawa, har da Bilal ɗin kuwa sannan aka koma babban falon domin sake sabuwar gaisuwa ga iyayen nasu guda biyu da kuma sanya lokacin da za'a zauna meeting da ƙarfe biyu rana, wannan karo harda ƴan uwan nasu mata,watau Gwaggo Aisha da kuma Gwaggo Fatima dake aure nan cikin kankiya da kuma kannen su mata watau Hassana da Hussaina suma duk an masu waya, saboda irin wannan taron babban taro ne da yake ƙara haɗin zumunci da ɗabbaƙa shi, hatta da yaran su matan an kikkira su a waya, tinda ƴan uwan nasu duk sun zo har da waɗanda ke ma'aura ya kamata kowa yazo a gana a kuma ƙara sanin juna. To sai mu ce Allah yasa ayi taro lafiya a kuma tashi lafiya Alhaji Isuhu family ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~14~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Zama ne da akan yi duk lokacin da ɗaukacin family ɗin suke nan, wannan ma karon kowa ya hallara, Alhaji Isuhu ne tare da ƴaƴan shi maza suka fara zama, sun tattauna abubuwa masu mihimmanci wanda mafi akasari Yaya Auwalun ne ke zartar da hukuncin, kasancewar shi babba namiji, sai da suka kammala tattauna war su sannan aka umurci kowa da ya hallara a babban falon sashen Alhaji Isuhun, kowa ya zazzauna Amman banda gogan naku, hakan ce ta sanya Alhaji mustapha ɗaukar wayar shi ya kirawo shi tare da umurtar shi da yazo sashen iyayen nasu. Taro ne da aka buɗe da addu'a bayan zuwan Yaya Ameen ɗin, inda aka gabatar da gaishe gaishe da kuma ƙara sani ga juna duk da dai kowa ya riga ya san kowa. Alhaji Auwalu ne ya fara da godiya ga Allah subhanahu wa ta'ala, sannan ya ɗora da faɗin, "Ba dan komai muka tara ku anan ba sai dan kuji maƙasudin tara ku anan da hukumci da tsarin da muka zartar, kasancewar kowa ya san ba shawara muke tambayar ku ba, amman dai hakan ba zai hana mu jin naku ra'ayin ba, idan mun gama sanar daku Abunda muka tattauna da shi Alhaji gashi nan" ya faɗa yana mai nuna farin tsohon da yake zaune bisa kujera irin ta alfarma yana ta faman murmusawa da kallon jikokin nashi har ma da surukkan nashi guda biyu watau Hajiya Kubra da Mama Zainab dake zaune ɓangare guda, duk da kasancewar Mama Zainab ɗin babba ga hajiya Kubran, Amman kai kace ita ce babba, saboda jin daɗin da gogewar kai harma da suturar ba ɗaya ba. "kai Aliyu, munsan buƙatar ka na anema maka auren Khadeeja, wanda mun yanke hukuncin nan ba da jimawa ba zamu je a nema maka auren" ya faɗa yana mai kallon babban ɗanɗan nashi namiji da ya sunkuyar da kai yana ɗan murmusawa, Yaya Auwalun ne ya cigaba da faɗin "sannan ku kuma Saudatu, da Nihal sai Hafsat (Ɗiya ga yaya Auwalun ta uku domin ta biyun mai suna Amina itama tayi aure har ma da ƴaƴan ta guda biyu, kuma itama tana zaune ne a wurin) kuma muna da buƙatar ku turo mana da manema aurenku zuwa gobe ko jibi domin mu tattauna dasu kuma mu basu izini" gabaki ɗaya sunkuyar da kai sukayi yayin da saudat ta zumɓuro baki ita fa bata shirya yin aure yanzu ba, dama Nihal ɗince mai saurayi, sannan ita hafsat dama tana da maneman ta masha Allah kasancewar ta nutsattsiyar yarinya ga kunya da girmama na gaba da ita, kyakkyawa ce masha Allah, domin su Nihal ɗin babu abin da zasu nuna mata. Dakatawa yayi yana murmusawa tare da cewa idan Alhaji mustapha yana da magana yayi yana sauraren shi, to shi ɗinma cewa yayi babu sauran wani abu sai dai ko a cikin yayyen nasu mata idan da mai magana. Goggo Aisha ce ta shigo da buƙatar tallafin karatun ƴaƴan nata maza da suka gama makarantar secondry yayin da Goggo Fatima tace ita kam babu abin da take buƙata, duk buƙatocin nata ƙannen nata sun gama mata komai sai Sam barka, tau suma ɗin dai haka Aunty Hassan a da hussainar babu abin da suka buƙata, sai godiya da suka shiga yi. Yayin da aka tambayi su Hajiya Kubran dake Zaune gefe, Hajiya Zainab dai cewa tayi babu komai, yayin da Hajiya Kubra ta buɗe baki cikin isa, ta shiga faɗin "Maganar Al'ameen fa? Banji kunce komai ba dangane dashi, shima ya kamata ya fiddo mata cikin wannan lokacin, in ba haka ba zan zaɓo mashi da kaina cikin family ɗin ƴan uwa na ko kuma cikin ƴaƴan ƙawaye na" Alhaji mustapha ne ya shiga kallon ta cikin ɗaure fuska yayin da Yaya Auwalun ya shiga girgiza kai a hankali yana ɗan murmushi, kasancewar duk sun san halin ta ne ya sanya abun bai basu mamaki ba. Shi kau Ya Ameen bazan iya fasalta yana yin da ya shiga ba, "wai me yasanya Mahaifiyar tashi take haka ne? Me yasanya idan zata yi abu bata tinani akai? Me yasanya, me ya sanya?" haka ya shiga furta wa cikin zuciyar shi da take ta kai komo, bugun zuciyar shi ya ƙaru, idan ko haka ne zai rufe bakin ta, zai bata mamaki, yana so ya cenza mata tinani, yana so ya cenza mata kallon da take yi ma kowa na bai isa ba sai ita kawai, yana son Mahaifiyar shi, ba zai so yana kallon ta tana tafiya bisa turbar da ba ita bace kuma ya sanya mata idanu ba. Hajiya zuwaira ce ta sanya baki a karo na farko, tin zaman da aka fara kusan awa guda kenan da suka shuɗe, ita ɗin ma murmusawa tayi, yayin da ta kalli Hajiya Kubran ta shiga faɗin "Ke kau Kubura me yasanya kika sanya ma wannan mijin nawa ido ne wai? Mai mata kaman ni har a ce ya fiddo da aboki yar rayuwa, ko ba haka ba ma ai shi Ameenun baki ga yanda yake ba, wannan ma mai tsoron matan? Ina ce ma ni ban taɓa ganin ya tsaya kula ƴan mata ba ko jin labari" kowa sai da ya murmusa banda Hajiya Kubran da take zaune hakim ce gefe guda yayin da Hajiya Zainab mata ga yaya Auwalun ta ɗora da faɗin " wannan gaskiya ne Mama, kamata yayi a bashi lokaci ya fiddo a tsanake, kaman yanda Aleeyu yayi, gashinan abokanan shi har da masu mata biyu Amman shi sai yanzu ya samu ya lalubo, zaɓen aboki yar rayuwa ai abune mai wahala sai an bincika sosai. Kowa yayi na'am da wannan maganar yayin da Hajiya Kubran ta Sake ɗaure fuska tana faɗin "Akwai ɗiyar Abokin wasa na Sen. Abubakar ɗan Malam, yarinya ce mai natsuwa, duk abin da ake buƙata mace da shi itama tana dashi, ta fito daga babban gida babban Family na yardar mashi yaje ya neme ta ni zan shige mashi gaba wajen aiwatar da komai" toh fa, Hajiya Kubra kenan, ita a ganin ta dukiyar ta arziƙin ta ya kai ta aiwatar da duk abin da take so, ta manta itama a ƙarƙashin wani take. Wannan karon cikin ɗan zafin rai Alhaji Mustapha ya shiga faɗin "Babu wanda zai sanya in ma yaro na auren haɗi, bamu taso munga ana yi mana shi ba anan gidan, kuma duk mu muka zaɓo ku, haka su Yaya Aisha duk su suka kawo mazajen aure, in ma haɗin ne ai muna da yaran da suka taso gaban mu a cikin family ɗin gasu nan duk sun isa aure, Meyasa bamu ce ya zaɓa a ciki ba?" Yaya Auwalu ne ya kamo hannun shi ganin abun na neman kwaɓewa, bai kamata a samu irin wannan saɓanin ba gaban yara, shi kau gogan naku, zaune yake kaman mutum mutumi, me yasa Mahaifiyar tashi take haka ne, mahaifan shi ke saɓani akan shi? Lallai babu wadda tayi mashi, baya kuma jin zai iya auren yarinyar da take nufi, kai shi Sam ma tarbiyyar ta bata yi mashi ba, dama ya kula da yanda take shisshige mashi idan yaje gidan, ashe da biyu ma Mahaifiyar tashi ke aikenshi gidan, itama yarinyar dalilin da yasa take mashi wasu abubuwan kenan? Sai yanzu ma zuciyar shi ta shiga hararo mashi wasu abubuwan, yayi nisa a cikin tunanin yayin da idanu wan shi suke rufe ya tsinkayo maganar wan Mahaifin nashi yana cewa "ya isa Mustapha, Ya isa su ai mata ne, tinanin su ragagge ne, kuma duk wannan abun dake faruwa shi yaron ai gashi gaban ku zaune, har yanzu bai tanka ba, bama mu sani ba shin ko akwai wadda tayi mashi cikin rai? Ko akwai wadda suke tare? A bari aji ta bakinshi tukunna" yayin da ya maida kallon shi ga Al'ameen ɗin sannan ya cigaba da faɗin "Shin Kai Al'ameen a cikin ranka akwai wadda kake so kuka yi maganar aure da ita? Ko akwai wadda ka yima Alƙawarin aure ne? Falon yayi tsit, baka jin komai sai ƙarar ac da take ta aikin ta ahankali ahankali, kowa ya maida hankalin shi da natsuwar tashi akan Yaya Al'ameen ɗin, yayin da kanshi yake ƙasa, da yawa daga cikin ƴan matan da suke falon suna so ace sune ya zaɓa a matsayin aboki yar Rayuwar shi, Al'ameen ɗin ɗaya ne tamkar da dubu, komai ya haɗa, kyau, natsuwa, ilimi, gayu, ga uwa uba naira, runtse idanu shi ya sake yi gam, yayin da yake jinjina girman maganar da zata fito daga bakin shi, ahankali ya buɗe idanun nashi ya fara ɗora wa akan kakan nashi, Alhaji Isuhu da shima kaf natsuwar shi na akan jikan nashi, kaka zuwaira ya kalla ta sakar mashi murmushi irin nasu na dattawan da suke cike da natsuwa da kuma dace da ƴaƴa nagari, sannan ya ɗauke kallon shi kacokam ya ɗora shi akan Mahaifiyar tashi da ta cika fam, uwa zata fashe, dan dai wayewa da kuma halin tarin rai irin nata, Sam bata kawo ma ranta cewa yaron nata zai bijire ma buƙata tata ba, na amsar tayin ƴar ɗan uwanta da tayi mashi ba gaban kowa, bata yi tinanin zai watsa mata ƙasa a ido ba. Kallon shi ya maida kan iyayen nashi maza biyu da suke zaman jiran cewa shi, sake ajiyar zuciya yayi ahankali, yayin da ya gyara zaman shi kan lallausan carpet ɗin da ya malale ilahirin falon, sannan ya nisa ya cigaba da faɗin " Eh ABBA, Akwai wadda muka yi Alƙawarin Aure, sai dai kuyi haƙuri jin ko wacece, Nidai ita nake so, kuma itama tana so na, kuma ina mai roƙon alfarmar da aura man ita, ita na zaɓa a matsayin abokiyar rayuwa ta, uwar ƴaƴa na, tarbiyyar ta tayi mun, komai nata yayi mun, kuma, kuma ina mai roƙon ta yi maku kaman yanda tayi mun" Ya faɗa cikin salon maganar shi mai kama da ta saraki, sannan ya ƙara she yana duƙar da kai alamar roƙo da girmamawa ga iyayen nashi har dama kakannin nashi da suke zaune a wajen. Murmushi Alhaji Isuhun ya sake cikin halin dattako ya shiga faɗin " Alhamdulillahi Faɗi kanka tsaye Ameenullah, nan kowa jiran yaji taka zaɓen yake yi, in da hali sai a haɗa da na shi Aleeyu baki ɗaya ma a wuce wurin. Toh fa! kan kowa da yake zaune a falon ya ƙulle, har da mahaifan shi Al'ameen ɗin watau Hajiya Kubran da Alhaji Mustaphan, Aunty Feena ce ta kalli ƙanen nata cikin wasiwasi da tarabbabi, kada ya janyo masu wani abun kuma, ita ta san bayada wata budurwa da yake so, kuma ta san babu wacce yayi ma Alƙawarin aure, toh fa! Kaman zata ce wani abu sai kuma tayi shiru, ganin Al'ameen ɗin ya fara magana "Abba Hauwa'u ce ta gidan mu watau Suhaann.. ɗiyar Ma.. Ma Maryama ta ɓangare masu aiki" Salati Hajiya Kubra ta sake tana mai miƙewa tsaye tana taɓa hannuwa kaman wata sakarai, jin maganar tayi kaman saukar aradu, sakin baki tayi, yayin da su kuma su Nihal suka ƙwalalo idanu, ba su ba har Aunty feenar ma ta shiga komar mamaki, Afnan kuwa murna da farin ciki ne suka mamaye ranta, Aunty Suhan fa! Ko dai kunnen ta ne ke gaya mata ba daidai ba? Nihal ce ta shiga zumɓuro baki tana faɗin wallahi yaya a'a mai aikin mu ce fa? Murmushi Alhaji Mustaphan yayi, ko babu komai ya san dalilin yaron nashi na yin hakan, tabbas ya jinjina ma yaron nashi, yayi na'am kuma da buƙatar tashi, sannan kuma ya bashi goyon baya ɗari bisa ɗari, jinjina kai ya shiga yi yana faɗin "Masha Allah, haka ake so Al'ameen yarinya tayi, kuma ina tare da kai, insha Allah zan shige maka gaba wajen ganin komai ya daidaita" yayin da Hajiya Kubran ta koma ta zauna bisa kujera inda ta tashi tana faɗin "kai shashasha ne Ameenu? Ashe baka da hankali? Me zaka ci da wannan yarinyar? To bari kaji ban yadda ba ka auri yarinyar da bata da asali koda kuwa ace mata sun ƙare ne a duniya, Ban yadda ba Sam, idan ba haka ba kuwa zaka gamu da fushi na, au ashe dama munafintata kake yi? Kana cen kana soyayya da wannan ƴar jariri yar abun? Sam ban lamunta ba, Alhaji har kana faɗin ka yarda, tau bari kuji ni Sam ban yarda Bako sama da ƙasa zasu haɗe bazan lamunci wannan auren ba" Alhaji Auwalu ne ya shiga kwantar mata da hankali yana faɗin "Kai Mustaphan bamu gane yarinyar da yake faɗi ba, kar dai ace yarinyar da aka zo da ita a goye gidan ka, ɗiyar wannan mai aikin?" Jinjina mashi kai Alhaji Mustaphan yayi cikin son bashi tabbaci, yaya Auwalun ne ya shiga faɗin ai ko hajiya ta yadda mu ba zamu yadda da wannan abun ba har sai an nemo asalin ita yarinyar, kai Ameenu ka bamu lokaci zamuyi ƙwaƙƙwaran bincike akai, kuma bamu ce ka cigaba da neman yarinyar ba har sai mun samu cikakke bayani akan ta, Alhaji Mustaphan ne ya shiga faɗin hakan yayi daidai, zamu bincika bayan wannan yarinyar bata da wani abun da za'a ce an kasa auren ta, kasancewar ta ɗiyar mai aiki, wannan ba hujja bace, ni na yarda da yarinyar da kuma tarbiyyar ta, Allah yayi maka albarka Al'ameen kayi Abunda ake so, ina alfahari da kai da wannan tausayi da jin ƙai da kake tare dashi, Allah ya ƙara ma Rayuwar ka Albarka duniya da lahira" Da ameen kowa ya amsa, yayin da Hajiya Kubra ta miƙe ta fice daga falon kaman zata fashe, da kallo kowa ya bita yayin da wasu suka shiga jinjina kai, shi kau Al'ameen ɗin duƙar da kanshi ya sake yi ya maida idanu shi ya kulle, me ya sanya shi yin hakan? Me ya janyo mashi? Yana so ne Mahaifiyar tashi ta canza halin ta akan masu aiki, yana so ne ta gane mecece duniya da Abunda ke cikin ta, Suhan ɗin alkhairi ce duk da kasancewar irin taƙaddamar dake cikin auren, ba soyayya tsakanin shi da yarinya Sam, bata ma san wainar da ake toyawa ba, kuma da wanne ido ma zai kalle ta yace mata ita ce ya zaɓa a matsayin wadda zai aura? Ta yaya zata kalli abun? Ta yaya ummanta zata fassara abun? Baya tinanin idan har umman bata yadda ba ko ta bada goyon baya ba abun idan zai yuwu. *Wacece Suhan ɗin???* Tambayar da ya shiga yi ma kanshi kenan Nisawa yayi yana mai sakin ajiyar zuciya ahankali ahankali, yayin da ya kai kallon shi kan sauran ƴan uwa nashi, tashin hankali da ƙyara ƙarara ya hango cikin idanu saudat da Nihal ɗin tau sai dai shi ba tasu yaje yi ba, yana hango Abunda zai faru ne nan gaba, da irin ƙalubalen da zai fuskanta nan gaba wajen Mahaifiyar tashi, gashi har ta fusata ma tabar falon, dama ya san hakan ce zata kasance, kuma shi baya jin idan zai iya janye maganar shi, hakan ma wata dama ce da yarinyar zata iya tantance wacece ita. Alhaji Auwalun ne ya shiga kwantar mashi da hankali, yana faɗin ba zamu ƙi amince maka ba, muddin muka ga babu abun ƙi tattare da asalin yarinyar, sannan muna mai baka shawara ka koma ku sasanta da Mahaifiyar ka, saboda abun yayi maka albarka, idan babu mai magana zamu rufe taro da addu'a da kuma sanya ran cewa manema auren saudat da Nihal ɗin zasu zo gobe idan Allah ya kai mu. Babu wanda yace komai, kowa da Abunda yake saƙawa acikin ran ta, abie ma ba zamu iya tantance halin da yake ciki ba, mutum ne mai zurfi ciki, kusan ma yaso yafi Al'ameen ɗin, tau sai dai shi ɗan ɓangare Hajiya Kubran ne, sai abin da tace, ko ta zartar, saɓanin Al'ameen ɗin da komin yake biyayya yaga za'a kauce ma gaskiya baya bin wannan ayarin. A haka aka kulle taro da addu'a yayin da iyayen nasu maza suka cigaba da zama wannan karon har da mama zuwaira ɗin domin su ƙara tattaunawa Kowa ɓangare shi ya wuce, wannan ce ta sanya suma su Nihal ɗin komawa cikin nasu sashen inda suka tarar da hajiya Kubran zaune tana ta faman cika, zaman jiran Alhaji ya shigo domin ita ba da Al'ameen ɗin zata yi ba da wanda ya ɗaure mashi gindin yin abun zata yi, zata ji dalili, kuma tabbas zaman munafukar matar cen ya ƙare a gidana tinda so ake a mallake man ɗanɗa na. Abunda take ta faɗa kenan yayin da ta miƙe ta shiga safa da marwa, su dai aunty Feena da afnan ɗaki suka shige yayin da su saudat suka zauna suna ta ƙara yi mata famfo da ingiza mai kantu akan al'amari, muddin aka ce yarinyar cen ta auri yayan nasu ai sun kaɗe, yarinyar da babu irin wulaƙanci da tozarcin da basu yi mata ba, Amman ace wai zata zama aunty su, tabɗijam "lallai Mom baki ga ta zama ba" cewar Saudat ɗin °°°°°°°°°°°°°°°°°° Kai tsaye ɗaki shi ya wuce, kayan shi kawai ya cire ya faɗa toilet ɗin ya sakar ma kanshi shower, ko sauraren Bilal ɗin baiyi ba, da yake ta mashi magana, shi ɗin ma ya san halin ƴan kayanshi, ba zai samu amsa ba, balle ma ya lura da condition ɗin abokin nashi, anya kuwa wani abu bai faru ba a zaman taron na family ɗin? Yana cikin tinani Al'ameen ɗin ya fito daga toilet, ƙugunshi ɗaure da fari ƙar ɗin towel, yana ɗauke da ɗan ƙarami yana tsane kanshi, jikin shi ko ina gargasa ce kwance luf, baƙa siɗik, abun ka da farar fata, sai tayi mashii gwanin kyau, ko kaya bai tsay Sanyawa ba, balle ya cire towel ɗin ya faɗa kan gadon yayi rigingine fuskar shi na kallon cilling. Kafaɗarshi Bilal ɗin ya dafa yana daga kwance "Man me ya faru ne? Ka gaya man na lura baka cikin natsuwa" kaman yana jiran cewar Bilal ɗin ya shiga faɗin "Friend na yanke ɗanye hukunci, ba tare da nayi tinani ba, Friend why? Me yasa nayi haka? Anya kuwa ban sha wani abu ba? Friend gaya man" ya faɗa yana mai tashi zaune ya juyo sosai busa gadon yana fuskantar abokin nashi, idanu shi sun kaɗa sunyi jajur dasu "Yarinyar tausayin su kawai nake yi, babu soyayyar ta ko ɗigo cikin raina game da ita, me yasa haka? Na jawo ma kaina raini, duk dan in faɗa kar da mahaifiya ta akan illar tsanar mutum haka kawai, yaya Mahaifiyar ta zata kalli abun, miƙewa yayi yana mai gyara zaman to wel ɗin a jikin shi, ya shiga taka wa a hankali cikin ɗakin, kai komo ya shiga yi cikin ɗakin kaman yana neman wani abu. Miƙewa Bilal ɗin shima yayi yana mai kamo hannun abokin nashi, tabbas ya san duk lokacin da yaga abokin nashi cikin irin wannan halin yana buƙata neman taimako ne. Zaunar dashi yayi bisa sofar dake ɗakin mai zaman mutum biyu, "Cool down Friend, ka natsu ka gaya man meke faruwa ne?" kaman yana jiran shi ya ɗan zabura ya zamo daga bisa kujerar kaman zai zauna ƙasa, yayin da ya kama hannun Bilal ɗin ya runtse shi sosai, kaman zai tsinke hannun "Friend ni na zaɓe ta da kaina, ni na amince ma auren ta da kaina, yarinyar da ka gani jiya a gidanmu, na amince zan aure ta, Friend ka bani shawara, how am i going to do? Wannan ƴar yarinyar Friend, ko aure zanyi Ai tayi man kaɗan, Amman nine da bakina nace su Abba su nema man auren ta Friend ya zanyi? Bata san meke faruwa ba, bata san zan iya yanke wannan ɗanyen hukunci a kanmu ba, zata so ni? Zata yarda dani? Mahaifiyarta zata amince mani? Ya faɗa yana miƙewa tsaye, shima ɗin dai Bilal ɗin a kiɗime ya miƙe jin abin da abokin nashi yake faɗa mai kama da almara, mai kama da tatsuniya. *"WHAT"* *Al'ameen Are U In Your Sense?* Bilal ɗin ya shiga faɗi a kiɗime cikin ɗaga murya, yana fatan kunnen shi basu ji mashi daidai ba, yana fatan ace mafarki yake yi, ina Al'ameen ɗin ina ƴar aiki, marar galihu, jiya jiya nan fa da daddare Al'ameen ɗin ke ce mashi ba'a san asalin yarinyar ba, inko haka ne me ya ja ma abokin nashi? Me ya shiga kanshi, saɓanin abin da yake son yaji ne ya shiga faruwa, lallai Al'ameen ɗinne ya shiga gƴaɗa mashi kai cikin tabbatas wa, da kuma neman mafita. ~Oum-Deedat ce~ [8/5, 8:25 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~* *Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat) *Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat) *Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare. *Page ~15~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° "Hajiya Laila kina jina ko? Ki bani way out please ƙawata, ɗan cikina ne zai auri ƴar talaka? Talakan na ma'aikaciyar gida na? Wadda bata da komai, bata da asalin kirki ma? Kai ina ba zai taɓa yiwuwa ba sam wallahi" Hajiya kubra ce riƙe da waya a hannun ta da alama waya take yi tin bayan shigar ta sashen nasu, ko zama t akasa yi sai kai kawo take yi a tsakanin tanƙamemen falon nasu da yaji kayan alatu kaman ba za'a mutu ba "ina jin ki Hajiya Kubra" daga ɗaya ɓangaren aka bata amsa cikin isa da izza ga dukkan alamu dai ƙawarta ce. "Ba kina jina zaki ce ba Hajiya Laila, mafita nake nema, kin dai sanni, kinsan buri na, kin kuma san yanda nake ƙaunar Al'ameen a duk cikin ƴaƴa na" Ta tari numfashin Hajiya Laila cikin sauri "Gaskiya ne Hajiya ta, ai wannan maganar ba ta waya bace, anya ma kuwa ba asiri sukayi mashi ba? Kin san fa tin lokacin da kika kula da shisshige masun da yake yi ya kamata ace kin taka ma abun burki, Amman son da kike mashi ya hana" "Hajiya Laila wallahi nayi ƙoƙarin hakan tin lokacin, Amman ɗan banzan yaron nan yaƙi bani haɗin kai, kin dai sanshi da shegen zurfi ciki, da kuma miskilanci, ni kaina rasa gane kanshi nake yi" Hajiya Laila ce ta tari numfashin hajiya kubran da cewa, "ba kince su keyi maku girki ba?". "Eh kwarai kuwa hajiya, in ba girkin su ba baya cin na kowa wlh" humm, Hajiya laila ta numfasa gami da sakin wani ɗan guntun murmushi ta cen ɓangaren, sannan ta ɗora da faɗin "To wallahi ina mai tabbatar maki a nan suka samu, suka samu abin da suka barbaɗa mashi yaci, yanzu abin da nake so dake ki kwantar da hankalin ki, abun zai zo mana da sauƙi, kedai kiyi ƙoƙarin dawowa akan lokaci" Nisawa Hajiya Kubra tayi cikin ƙunar zuciya da tsanani ɓacin rai, kaman zata haɗiyi zuciya ta mutu, sannan ta cigaba da cewa "Shikenan Hajiya Laila, ina so please kiyi tinanin neman mafita, saboda ni duka ma kaina ya ƙulle wallahi, gabaki ɗaya yaron nan so yake ya birki ta mani lissafi, na yarda dake ne, insha Allahu kuma zanyi ƙoƙarin ganin na dawo akan lokaci, yanzu ma zuwan maneman su suhan ne kawai zai tsaida ni" "Is OK Hajiya Kubra, baki da damuwa ki kwantas da hankalin ki, ina mai tabbatar maki da maganar nan zata sha ruwa, ko shi Alhajin da ya goya mashi baya, ba zai ma ƙara tada maganar ba, balle wani Alhaji Auwalu cen, da zaki ɗaga hankalin ki aka shi;To ko Isuhun ma bai isa ba balle ƴaƴanshi"😒 Hajiya Kubran ce ta murmusa mai cike da yaƙe, "Humm Hajiya Laila kenan, baki da dama, haka nake so, Shiyasa nake son ki nafi yadda dake akan kowa cikin ƙawaye na, na mayar dake aminiyata ta hannun dama ta, wuƙa da nama na hannun ki, a fara komai kafin in dawo, zan tura maki duk abin da za'a buƙata" "Ba damuwa Hajiya Laila, ke dai sai kin dawo dai, ƙibar komai a hannuna, sai mun yi magana" "OK shikenan a huta lafiya Hajiya Laila, sai Naji daga gare ki" ta faɗa tana mai datse kiran gami da zama cikin ɗan samun sassauci, saboda sanin halin hatsabibancin ƙawar tata, komai take so mai sauƙi samu ne, indai tabi ta hannun amini yar tata. ************** "Look Friend kayi gaggawar yanke hukunci, aure ba abu bane da akeyi mashi hawan ƙawara, yarinya r zaka iya taimako ta, ba sai ka aure ta ba, ina so ka sani aure babu soyayya ba abu ne da ke ɗorewa ba, masalan yanda zaka yi manage na zama da ita, a yanda na san ka yarinyar bata yi daidai da ra'ayin ka ba, beside ma mahaifiyar ka...... " Dakatar dashi Al'ameen ɗin yayi, ta hanyar ɗaga mashi hannu," Bilal! Please mubar maganar haka, kayi man addu'a kawai" abin da ya faɗa kenan, ya miƙe a hankali ya zura kayanshi, gami da zarar keys ɗinshi na mota ya fice daga gidan ma baki ɗaya. Da kallo abokin nashi ya bishi dashi, "Hooo Al'ameen kenan, ko sai yaushe zai cenza? Kaman bashi bane yanzu yake neman way out, yaro kaman mai bira'izai? Wannan ko auren yayi wahalar da yarinyar kawai zai yi, bai iya wata soyayya ba, balle ya tsaya bata kulawar da ta dace, kullum kai kenan a murɗe? A baibai? Humm" ya faɗa a fili yana mai miƙewa shima ya fice daga ɗakin zuwa cikin lambu. *********** Da sallama ya shiga sashen nasu, fuskar shi a matuƙar ɗaure, ko babu komai ya san bata kyauta mashi ba, a gaban kowa ciki har da iyayen shi ma, Amman taso tayi jayayya dashi, har tana ɗaga murya akan kowa da ficewa ma baki ɗaya daga perlour ɗin, dole ya nuna mata ɓacin ran shi, alwashi ne ya sha shi aure sai anyi, zai ga wanda yake gaba, cikin shi da ita; ko ɓangaren da take bai kalla ba, ya wuce kai tsaye zuwa bedroom ɗinshi domin wanka da shirya ma zuwa sallar magariba da ta gabato. Haka yazo ya sake wuce ta, tana zaune tana kumburin ta da kaɗa ƙafa ɗaya dake kan ɗayar, Hajiya Kubra kenan, ai shi duk abin da Allah ya tsara baki da kuɗin da zaki cenza ikon shi akan komai Itama tana kallon shi, Amman yanzu kam duk son da take ma Alhajin, zata danne shi ne, ba zata taɓa bari da girman ta, da ajinta ba, ta tozarta, to ai ajinta ma ya zube in har ta bari ƙawayenta suka ga wadda ɗanɗan nata yake son auro mata a matsayin suruka, yarinyar ƴar ƙauye da babu abin da ta iya sai bauta, sam Suhan ɗin ba ajin *Moh'd Al'ameen Al-Mustapha Dambulan* ɗin nata bace. Wannan ce tasa har ya kuma fitowa ya fice baki ɗaya daga gidan bata kula shi ba, tasha Alwashin yi ma abun tufkar hanci, ba Alhajin ne yake taƙama dashi ba? To wannan karon har shi ba zata ƙyale shi ba. ----------- Haka kuwa aka yi, washe gari da wuri maneman auren su Nihal ɗin suka iso, masha Allah yara ne ƴan gayu, ƴaƴan masu faɗa aji, kaman yanda hafsat ɗin take kamila da sanyin hali haka shima saurayi nata yake, kowa yayi mamakin shi duk da, da alama naira ta jiƙa shi sosai, Amman baya da jin kai irin na sauran masalan saurayi Nihal ɗin, ahaf, ai kowa yana samun daidai dashi ne, basu jima ba sosai bayan sun gabatar da kansu, iyayen na su saudat suka ga, ai iyayen nasu ba baƙi ma bane a wajen su, umurtar su sukayi da su turo su domin tsaida lokacin aure, Abun Alkhairi sosai suka ba yaran su Goggo Aisha, sukayi ta Sam barka da sanya alkhairi, basu tafi ba sai da Kaka zuwaira ta zo ta zazzaulaye su, cikin wasa irin na kaka da jika, hakan ya ƙara faranta ran su, domin su ɗin dama sangartattun ƴan gata ne, sun saba zaulayar granny ɗinsu at any moment. Atare suka koma zuwa Abuja gabaki ɗaya, bayan kammala zumuncin irin na wannan lokacin, da yazo da saɓani da abubuwan farin ciki da dama. Ta ɓangaren Hajiya Kubran kuwa, har yanzu sama sama suke da Alhajin, domin ya sha Alwashin gargaɗar ta da kuma yi mashi katsalandan acikin Al'amari auren yaron nashi. Kowa da Abunda yake saƙawa cikin zuciyar shi har ƙarasowar su zuwa cikin gidan, wannan ce ta sanya bamu san da labarin dawowar tasu ba, kowa part ɗinshi ya wuce kai tsaye, duk da suna farin cikin gabatar da masoya nasu ga iyayen su, Amman ta ɓangaren guda, ƙudirin yayan nasu ya kasa barin zuciyar su, haƙiƙa wannan labari ne mai muni, labari ne mafi ƙona zuciya da suka taɓa ji tin bayan mallakar hankalin kansu. Al'ameen kuwa, Daurewa kawai yake yi wajen amsa ma abokin nashi duk maganar da yayi mashi, ziyara ya kawo mashi, baya so yaga kaman yana wulaƙanta shi ne, ta ɓangaren Bilal ɗin kuwa yayi mashi uziri, ya san damuwar abokin nashi, ya sani sarai, ya yanke hukunci ne cikin fushi, gashi abun yazo daga baya yana damun shi, kuma shi ba irin mutanen da suke amai su lashe bane, ya sani, koda za'a dinga yankar naman jikin shi, ba zai koma yace ya fasa ba, ba zai warware nuƙatar tashi ta auren Suhan ɗin wajen iyayen shi ba,koda kuwa hakan na nufin faruwar mummuna abu ne a gareshi. ***** Tura ƙofar aka yi, gami da shiga cikin ɗaki kai tsaye, wucewa tayi i zuwa ga bakin gadon ta samu ta zauna, sanye take cikin kayan bacci irin masu mugun tashin nan, sai walƙiya take, Hajiya kubra kenan, ikon Allah, "Alhaji nazo ne muyi magana da kai" Shiru yayi mata kaman ma baya cikin ɗakin Bata saurare shi ba, ta cigaba da faɗar Abunda ke cikin zuciyar ta. "Alhaji ina so ne fa ka sani, ina nan kan baka na, lamarin auren Al'ameen da yarinyar cen ta sashen masu aiki, ban yarda dashi ba har yanzu, bana kuma tinanin zan yarda har abada, ni ce na haife shi, baya da ikon yin abun da ban yarda mashi yayi ba, mu ne gaba dashi, ba shine gaba damu ba, mune muka haife shi, ba shine ya haife mu ba, ina so ka sani muddin ya sake ya auri yarinyar nan, zan mugun saɓa mashi, bana so ka bashi goyon bayan auren baiwar mu..... " " Ya isa Kubra, ya isa hakanan nace" ya katse ta cikin tsanani ɓacin rai, da tsawar da ta gigita ta, har ta miƙe tsaye bata sani ba, to ita ai bata ma san lokacin da ya miƙe zaune ba. "Idan baki son in saɓa maki ƙibar maganar nan, ina so ki sani muddin baki bashi damar auren yarinyar ba, to fa lallai ne ki bashi dama ya zaɓi wadda tayi mashi, namiji ne, mata ma bamuyi masu dole ba balle maza, namijin ma kaman Moh'd Al'ameen, Kubra me yasa baki tinani ne wai in zakiyi abu?kin gama tozarta ni gaban ƴan uwan nawa da ƴaƴan nawa, shine kika biyo ni nan ki sake ƙarawa? Yaushe har abun naki ya kai haka ban sani ba? Toh ina so ki sani, duk hukunci da na yanke nan gidan akan ƴa] a na ya yanku, ni ne sama dake acikin gidan nan, kuma dole kema kibi abin da nake so, ina so ki sani, maganar sake yin aikin Maryama da yarinyar ta acikin gidan nan na haramta shi, kaman yanda na faɗa maki acen baya, ban barsu sunyi aiki ba, ada cen saboda lafiya su, balle yanzu da suka zama *Surukkai na"* A razane ta kalle shi, "Alhaji Surukkai fa kace? Yaushe har suka zama surukkan ka?" "Ah to nadau faɗa maki, kuma abin da nace kenan, na gama magana, zaki iya cigaba da faɗar dukkan Abunda ke ran ki, ruwan ki ne ki ƙyale yaro yayi Abunda yaga ya fiye mashi, ko kuma ki sanya ya fara bijire ma umarnin ki, da biyayyar da yake maki" yana gama faɗar haka ya koma ya kwanta, gami da jan bargo ya lulluɓe jikin shi, sannan ya sanya hannu ya kashe dumlight ɗin ma gaba ɗaya, ɗakin ya gauraye da duhu. Ƙutawa tayi, gami da tashi ta fice daga ɗakin zuwa nata, tana mai ƙudurce abubuwa da dama acikin ranta. ********* "Son" Alhajin ya kira sunan yaron nashi da yake zaune bisa kujera mai cin mutum ɗaya, hakan ce ta sanya shi ɗago kyawawan udanun nashi ya ɗora su akan dad ɗin nashi, shigowa shi kenan part ɗin mahaifi nashi domin har yanzu ya kasa tun ƙarar mahaifiyar tashi, "Ina so ka ƙara tabbatar mani da maganar da ka faɗa a cen kankiya kan yarinyar nan, shin da gaske kana so ta?" Alhajin ya jefa mashi da tambayar bazata da ta ƙara ruɗa shi, ƙasa yayi da kanshi yana mai murza yatsun hannun shi, ya ma rasa me zai faɗa ma dad ɗin nashi. " Eh Abba, da gaske nake, ina so ta, kuma a shirye nake da in taimaka mata. " Ya faɗa ciki-ciki, sai dai duk da haka Alhajin ya ji shi, "OK Son, Abunda nake so da kai, kabar maganar nan for now, saboda hajiya ta huro wuta, hakan zai sanya ta matsa ma zaman su acikin gidan nan, akwai abubuwa da dama gabanmu, na san mahaifiyar ka ko wacece, hakan zai sa tayi tinanin mun bar maganar ne, to sai dai zamu shirya dukkan Abunda zai yuwu ne bayan mun gano asalin ita yarinyar, talauci ko rashin mahaifi ba zai sanya in kasa barin ka ka aure ta ba, ina so ka sani, ni ba kaman mahaifiyarka nake ba, kuma itama ina mata addu'ar Allah ubangiji ya shirya ta, ta gane gaskiya" da ameen ya amsa iya maƙoshi, sannan Alhajin ya ɗora da faɗin "Maganar karatun yarinyar, ina so kayi dukkan mai yuwuwa ta tafi makaranta, hakan zai bamu damar bincike na haƙiƙa, dole kuma sai da haɗin kan mahaifiyar yarinyar, sannan kaje ku daidaita da mahaifiyar ka, ga nemi gafarar ɓata mata da kayi, hakan ba yana nufin ka janye maganar auren naka ba, ina so kuma ka cire dukkan wata damuwa da ke cikin ranka, komai Kaga ya yuwu yi ne na Allah, na san dalilin ka na son auren yarinyar, nima na bada goyon baya ɗari bisa ɗari, Allah ya tabbatar mana da Alkahirinsa. Nan ma da ameen ya amsa cikin zuciya, Alhajin ne ya wayance ya shiga janshi da firar kasuwanci, da shirin buɗe sabon estate ɗin su mai suna *Dambulan estate* da za'ayi zuwa ƙarshen shekara, wadda take mallaki Al'ameen ɗin. Da haka ne ya samu ya saki jiki dashi, nan suka karya su uku, har da Bilal ɗin da ya shigo daga baya gaishe da Alhajin, bayan sun gama ne suka fice atare da Alhajin kaman wasu abokan shi. Jikin Ummantawa yayi sauƙi sai Sam barka, hankalinmu a kwance, saboda ƴannkuɗaɗen da ya Ameen ɗin ya bamu, su ne muke riritawa da siyan abubuwan da likita ya gindaya ma umman tawa cinsu, tin bayan tafiyar su hajiya da kwana ɗaya bamu sake jin ɗuriyar shi ya Ameen ɗin ba, sai bayan dawowa su ne, saƙo ya iske mu, na dakatar damu daga aikin gidan gabaki ɗaya da aka yi daga bakin mama talatin, a cewar ta wai saboda jikin umman tawa, to mu dai duk da haka jikinmu yayi sanyi kwarai matuƙa, sai dai gudun sanya zargi wani abu, ko damuwa ya sanya muka kauda dukkan wani shakku a cikin ranmu game da hakan. Hankalinmu bai ƙara tashi ba saida aka dena bamu abinci gabaki ɗaya, mun gane hakan ne ta yau da safe da na kai cooler ɗinmu kitchen a zuba mana abinci, sai mama sauden (mai girkin ma'aikata) tace man ya ƙare, abun ya bani mamaki sosai, sai na share na koma ɗaki na haɗa tea cikin kayan da ya ameen ɗin ya siyo mana kafin ya tafi na sha. Da rana ma hakan ce ta kasance, wannan karon free ta fito ta faɗi man cewa an dakatar da bamu abinci a cikin gidan, saboda yanzu mu ba ma'aikata bane, abun ya bamu matuƙar mamaki, me hakan ke nufi ne? Ko dai wani ne ya ja mana wani sharri kuma? Umma ta ce ta bani haƙuri, da unurtata kada in sake komawa amso abinci, har saida suka mula, suka sha iska dan kansu suka bamu. Ɗan Abunda ke gare mu a ɗaki, shi muka dinga ci ni da ni da umma ta, sai gashi nima na koma cin abunda masu ciwon zuciya suke ci; amman ya zamuyi? Dole mu haƙura, babu, ce da zama ƙarƙashin wani ya ja mana. Amman ace a gida irin wannan ya wuce ace ana irin haka ga masu aiki, sai dai in da wani abu a ƙasa. **************** Da sallama ya shiga cikin ƙayataccen sashen nata, tana zaune bisa kujera tana waya da ƙawarta Hajiya Laila, cewa tayi ta bata minti biyu zata sake kiran ta, kashe wayar tayi tana mai amsa mashi gaisuwar da yake mata ciki ciki tayi, sannan ta ɗora da faɗin "ya aka yi ne Al'ameen?" "Mom kiyi haƙuri please, babu kyau iyaye na fushi da ƴaƴansu nazo ne in baki haƙuri" ya faɗa a taƙaice idanun shi na bisa fuskar ta don ganin yanda zatayi Ɗan guntun murmushi ta saki, cikin duniya ci tace "haba son menene haka? Ai ya riga da ya wuce, na san ba zaka yi Abunda zai ɓata man rai ba, Allah yayi maka Albarka" ina so kaje ka yankar ma su Afnan ticket saboda zuwa anjima zasu wuce, hutun nasu ya ƙare kada su rasa flight" "OK ya faɗa yana mai miƙewa cikin salon tafiyar shi ya taka ya fice daga part ɗin na mahaifiyar shi, da tin dawowar su bai shige shi ba sai yau, saboda bai san abin da zai je ya tada ba, zuciyar shi cike da wasu wasu, me mahaifiyar tashi take ƙullawa ne? Shi fa yayi mamakin sauri saukowa ta, Amman koma minene zai bita ta ƙarƙashin ƙasa in ta san wata ai bata san wata ba. Ita kuwa a ɓangaren ta, da murmushi ta bishi tana faɗin "yaro yaro ne, koda kuw ɗan giwa ne, kaman yanda ka bari cikin cikina, Al'ameen ka bar maryam da ɗiyar ta har Abadan abada, hhhhh" ta kyalƙyale da dariya shu'umanci, domin kuwa hajiya Lailan ta bata tabbacin hakan, ita kuma ta yarda da hajiya Lailan ɗari bisa ɗari, in tace zata yi, to fa zata yin ne, koda kuwa sama ce zata haɗe da ƙasan. ~Toh fa! Anya kuwa Hajiya Kubra Alkhairi take ƙullawa kuwa 🤔~ ~Ya makoma Suhan da Umman ta a Rayuwar da ake ciki na hana su abincin da zasu ci ma?~ ~Al'ameen kuwa ya bar maganar auren suhan ɗin? Ko dai irin abun nan yayi mata na yaro bari murna...~ ~Oum-Deedat cee~ [9/15, 7:36 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *_Page ~16~_* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Komawar Bilal ɗinne ya sanya abubuwa suka ƙara yi mashi yawa, ginin shi da kuma kayayyakin su da suka iso, wannan ce ta sanya hankalin shi ɗauke wa daga kan su suhan ɗin, to dama dai taimako ne kawai tsakanin shi dasu acikin ranshi, ba kaman yanda yayi iƙirarin soyayyar ba gaban mahaifan nashi. Ta ɓangaren mu kuwa, komai yayi tsanani, rashin abinci ai ba ƙaramar barazana bace ga ɗan adam. Idan hankalina yaso ya tashi umman tawa ce ke taɓo ni, da nasiha da wa'azoji da dama, dole ne in daure in maida komai ba komai ba, gudun ɓacin ran nata. Bamu da wani aiki a yanzu sai sallah, wanka da kuma bacci, mu kan share tsawon yini biyu bamu ci komai ba, saidai ruwa da kuma ɗan farau farau ɗin da muke kaɗawa mu sha, saboda rashin kuɗi a hannun mu, sai umma ta ce ta bani ƴan abunda suka rage a hannun ta na siyo mana fura cen cikin gari, muka dama muka ajiye in munji yunwa mu ɗiba mu tsiyaya ruwa mu kwankwaɗe, da haka har muka kwashe tsawon yini biyu Idan ma fita muka yi tsakar gida haka zamu dinga fuskantar ƙananan maganganu da habaice habaice daga sauran ƴan uwan namu ma'aikata, hakan ce ta sanya umma ta hanani fita, idan ba aike ba to fa mun gwammace muyi zaman mu a ɗaki umma tayi ta ƙara man karatu in mun gaji mu kwanta Ko wanki a banɗakin ɗakin namu nake yi mana, iyaka shanya ce zanyi a tsakar gida, sai sharar ɗakin namu da ƙofar ɗakin. Mun zama bare na ƙarfi da yaji a cikin gidan, gashi shi wanda ke ɗan tausaya mana ɗin ma ya ɗauke ƙafar shi ɗaf daga gare mu, afnan kuma sun riga sun koma tini, saidai kafin tafiyar tata, tayi dabara zuwa sashen mu, duk da ba kuɗi ta kawo mana ba, abubuwa ne masu yawa nata ta tattara ta bani, irin su kaya da kayan kwalliya. Ta ɓangaren su hajiya Kubra kuwa, komai ya mata yanda take so, magana ta mutu murus, su ɗin da ta tsana ko jin ɗuriyar su yanzu bata yi, lallai Hajiya Laila ƙawar tata hatsabibiya ce, gashi ko Alhajin ma ta dena jin zancen auren Al'Ameen ɗin a bakin shi, gashi ya sake mata sun koma kaman da cen yanda suke To dama dai ita ɗin wannan ne kawai burin ta, tini Al'Ameen ɗin ya samo masu kuku har biyu suna masu aikin abinci, Wannan ce ta sanya ta ci gaba da harkokinta cikin kwanciyar hankali, ta ci gaba da zuba mulki da isa da ikon ta kaman yanda take so Likafa ta ci gaba, yanzu bata ko zama sosai a gidan, tanƙamemen shagon kayan ƙyale-ƙyale da make-up ta buɗe, irin na manyan mata da riƙaƙƙun yara masu tashe da watayawa a faɗin Nigeria. Yara ta ɗiba kyawawa ta zuba suke aikin, wannan ce ta sanya wurin haɓaka, duk wata mace da ta amsa sunan ta a faɗin garin na Abuja shagon take zuwa ayi mata gyaran jiki, da kuma siyan kayan ƙyale-ƙyale da take yo order ɗinsu daga ƙasashe mabanbanta To shima Alhajin baiyi yunƙurin hana ta ba, asali ma, shi ma ɗin ba mazauni bane, gara ma Al'Ameen ɗin, yafi zama a gida Nigeria, yana kula da sauran ma'aikatan nasu da suke ma'aikata da kamfanoni daban daban. Duk da cewa ya fara jan Abie yana koya mashi abubuwan da suka danganci kasuwancin, shi kaɗai ba zai iya ba, ina zai kasu? Gashi yanzu amana tayi ƙaranci a wajen jama'a. ********* Duk wannan abubuwan dake faruwa, Al'Ameen ɗin bai san dasu ba, tsarin da aka ɓullo dashi a gidan na hana mu abinci, Yana iyakar ƙoƙarin shi ganin cewa babu wani ma'aikaci acikin gidan dake fuskantar matsala, Wannan ce ta sanya ya shafa'a Sam damu da al'amarin namu, gashi yanzu ko a hanya bama haɗuwa dashi, saboda babu inda nake zuwa, haka umman tawa, kullum tana ɗaki tana karatun ta, kuma tana iya bakin ƙoƙarin ta, wajen kauda tinanin komai, gudun sake tashin ciwon ta. Tafe yake cikin takunshi mai ɗaukar hankali, sanye yake cikin fari ƙal ɗin wandon jeans da riga ƙirar polo mai ruwan makuba. Cikin sauri ya kwala ma mudi driver kira, da ɗan gudun shi ya iso wurin, yana mai russunawa cikin girmamawa ga uban ɗakin nasu yake faɗin "Gani Alhaji" "Mudi gashi" ya miƙa mashi ƴan makullayen motar, "yau bana jin daɗi sosai, so bazan iya driving ba, ina so ne ka kai ni office, aikin gaggawa ya taso mani, da bazan ma iya fita ba" mudin ne yayi saurin amsar makullin, yana mai ƙara russunawa yake faɗin "Angama ranka ya daɗe" Buɗe mashi ƙofa yayi, ta mai zaman banza ya zauna sannan ya sake zagaya wa ya shiga yayi ma mota key, tare da danna horn ga mai gadi, cikin daƙiƙa da basu Gaza biyu ba ya wangale masu gate, yayin da mudi ya harba motar bisa titi, yana mai sake danne ma mai gadi horn alamar sai sun dawo, shi kuma ya shiga ɗaga masu hannu yana mai washe haƙora. Mudi ne ya shiga kallon ubangidan nashi ta gefen ido, dafe yake da kanshi dake sara mashi, kaman zai faɗo, gyaran murya yayi sannan ya shiga faɗin "ranka ya daɗe ko dai asibiti zamu fara zuwa ne?" Girgiza mashi kai Al'Ameen ɗin ya shiga yi cikin rashin son Magana irin tashi, sannan ya buɗe baki daƙyar yana faɗin "Naje jiya mudi, na sha magani ma ai" ɗan guntun murmushi mudin yayi kasancewar ya san ubangidan nashi yanda yake tsoron asibiti da Allura tin ba yanzu ba, idan akwai Abunda ya tsana baifi ace za'ayi mashi Allura ba Sake nisawa yayi cikin san gulma, "ummmmm yallaɓai nace, dama...... Uhm" ya faɗa yana mai ɗan haɗiye miyau cikin in-ina, "Ina jinka" ya tsinkayi muryar Al'Ameen ɗin yana faɗa a hankali. "Yallaɓai ka gafarce ni, na san in bani ba, babu mai zarafin gaya maka wannan maganar, dama ina ta son samun dama, ayyuka ne da naga sun yi maka yawa ne yasa ban tinkare ka ba" Ya isa mudi, kawai ka gaya man meke faruwa ne? " ya faɗa har yanzu idanun shi na a lumshe, hannun shi har yanzu yana a bisa kanshi, ya to kare shi da murfin motar " Maganar su Suhana ce Yallaɓai, yarinyar nan da suke zaune ita da mahaifiyar ta, da aka dakatar dasu daga aikin gidan..... " Cikin hanzari ya buɗe idanun shi, da suka kaɗa sukayi ɗan ja, hakan ce ta sanya suka ƙara shanye wa. Kallon muɗi ɗin yake yi cikin alama ta son jin meke faruwa dasu ne kuma? Baice ƙala ba, hakan ce taba mudi tabbacin yana sauraren shi kenan "Yanzu fa ba'a basu abinci a gidan nan, bama asan halin da suke ciki ba, gashi har yanzu lokacin albashi baiyi ba, nima a bakin saude mai dafa abincin naji, kasan su da ƙananan maganganu, kuma wai........ " Ya salam" ya furta cikin tsananin firgita, sauke hannun shi yayi bisa cinyoyin shi, hakan yayi daidai da ƙarasawar tasu bakin gate ɗin tanƙamemen company ɗin, mudi na shirin danna kan motar cikin gate ɗin da tini an riga an buɗe masu "Mudi" "Na'am Yallaɓai" "Mu koma gida, muyi gaggawar komawa gida, me ya sanya baka faɗa man ba tini? Wanene ya bada wannan damar ta hana a basu abinci?" Ya jefa ma mudi tambaya cikin ɓacin rai, "Magana nake yi maka mudi" Cikin sanyin jiki, da nadamar gaya mashi zancen da yayi muɗi ya duƙar da kanshi ƙasa yana faɗin "Allah ya huci zuciyar ka yallaɓai, Amman Hajiya Babba ce ta hana tin waccen tafiyar da kuka yi, mu kuma muna tsoron gaya maka a samu matsala, hajiya ta gane daga bakin mu maganar ta fito" Ya faɗa a sanyaye yana mai juya akalar motar zuwa inda suka fito. "Haƙiƙanin gaskiya raina ya ɓaci mudi, menene laifin yarinyar da mahaifiyar ta? Aikin ai basu ne suka ce basa yi ba, wannan ɗaukar alhakin yayi yawa mudi, ya kamata ka dinga sanar dani abubuwan dake faruwa a gidan, saboda na kula munafunci yayi yawa a tsakanin mata ma'aikatan gidan nan" Mudi ne ya sauke ƙaramar ajiyar zuciya, yana faɗin "haka ne yallaɓai, Allah ya kyauta gaba, kayi haƙuri idan irin hakan ta ƙara faruwa, za'ayi gaggawar sanar da kai" Shiru ne ya biyo baya cikin motar har zuwa lokacin da suka isa zuwa ga gidan, ko daidaita tsayuwar motar mudin baiyi ba, Al'Ameen ɗin ya ɓalle murfin motar, cikin sauri da azama ya isa zuwa ga sashen na masu aiki. Cikin sallama yake ratsa sashen namu har zuwa bakin ƙofar ɗakin namu Kwance nake nayi matashi da cinyar ummata da take zaune gefen katifa tana ƙara man karatun umdatul ahkam, Nikam har ga Allah bana gane karatun Sam, yunwa ce kawai ke cina, ko motsin kirki na kasa yi, sauraren ta kawai nake ba tare da gane abunda take faɗi nake ba Ita ɗin ma ƙarfin hali take, rabon da mu sanya abinci acikin cikin mu anfi sati, kullum saidai farau farau wanda tin jiya ma furar tamu ta ƙare Sallamar shi ce ta dakatar damu daga karatun da mukeyi, banyi yunƙurin tashi ba, haka ma umman tawa bata matsa man ba, saboda ta san halin da nake ciki, ita ce ta yunƙura dakyal ta miƙe, bayan ta zame kaina daga saman tata cinyar. Ɗakin da yake sakaye ta buɗe, da ɗan murmushi a kan fuskar ta, sannan ta shiga faɗin " a'ah Muhammad ne? Shigo mana, ka tsaya daga bakin ƙofa?" Jiki a sanyaye ya sanya kai cikin ɗakin yayin da ummata ke shimfiɗa mashi yalwata ciyar dadduma a gefen ta katifar daga ƙasan tiles ɗin Zama yayi yana mai gaida umman tawa, cikin natsuwa da girmamawa, haka itama umman tawa ta shiga amsawa da ɗan murmushi a kan fuskanta, kai daga gani ka san na yaƙe ne. Nikau dakyal na ɗaga na zauna gami da ja na jingina jikin bangon ɗakin "Ina kwana?" na faɗa a hankali, murya ta har bata fita sosai, kallona yayi cikin ido sosai yana mai amsawa, ya ɗauke kanshi zuwa ga umman tawa. "umma nazo ne in baki haƙuri, a bisa Abunda yake faruwa acikin gidan nan" ya nisa sannan ya ɗora da faɗin "Sam bansan me ke wakana ba, sai yanzu ne mudi driver ke faɗa mani, umma menene ya sanya in irin haka ta faru ba kwa sanar dani da gaggawa? Idan an dakatar daku aiki, ai ba hakan yana nufin ba kwa cikin gidan bane, kuna nan kaman yanda kuke a da" Ya tsagaita yana kallon umman tawa da kanta yake ɗan duƙe tana murmushi, dame zata saka ma Al'Ameen ɗin? Lallai yaro ne ɗan albarka da bai biyo halin mahaifiyar tashi ba Sam, murmusawa tayi ta shiga faɗin "kai haba babu komai ai Al'Ameen, Hajiya bata yi komai ba, ni ban ma so muɗi ya faɗa maka maganar ba, bana so hakan ya kawo saɓani tsakanin ka da mahaifiyar ka Muhammad, don Allah ina so ka bar zancen nan, Mungode da alkhairi ka gare mu, Allah yasa ka gama da iyayen ka Lafiya, ka cigaba da yi masu biyayya, insha Allah zaka ga haske a rayuwarka" Cikin jin daɗin addu'ar da umman tawa tayi mashi ya murmusa yana faɗin "Ameen Umma, nagode kwarai da addu'ar ki, ina mai ƙara baku haƙuri insha Allah komai yazo ƙarshe, ina so komai ya tsaya iya mu ne dake nan, ku siyo abubuwan buƙata da Abunda zakuyi girki iyakar naku, ku dinga cin abinci, duk abinda kuke buƙata kuma insha Allah ku tuntuɓeni kai tsaye ina tare daku. Kuyi haƙuri da halin mahaifiya ta, ina mata Addu'a Allah yasa ta gane gaskiya" Miƙewa yayi tsaye gami da ajiye mana kuɗi masu yawa sosai, gami da complement card ɗinshi da yake ɗauke d suna da number tashi ta waya, sai kuma matsayi shi na MD Dambulan And CEO Dambulan Estate and More, sai Address ɗin Office ɗin nashi. Murmushi umman tawa tayi tana mai Cewa "a'a Muhammad ba zamu karɓa ba gaskiya, abun yayi yawa, ai ana hidima damu, kwarai da gaske, Allah ya ƙara buɗi" Ameen ya amsa yana daga tsaye, yake faɗin "Umma ki amsa Alkhairin da nayi maku, ba kowa ya sanya ni ba, ni na sanya kaina, ba roƙona kuma kuka yi ba, ni ne naga dacewar hakan, indai kin ɗauke ni ɗanɗan ki da kika haifa, ki amsa ki sanya man Albarka umma" yana gama faɗar haka ya juya ya fice cikin azama, har yanzu kan nashi na sara mashi matuƙa gaya Da kallo nabi bayan shi har ya idasa ficewa gaba ɗaya daga ɗakin namu, ajiyar zuciya na sauke a hankali ina mai zamewa na kwanta lamo abubuwa da dama na man kai kawo cikin ƙwaƙwalwa game da wannan cukurkuɗaɗɗiyar rayuwa da muke yi. Watau ni na ma rasa gane kan wannan mutum wallahi, Ya Ameen daban yake cikin mutane, kallona na maida kan uban damin kuɗin da ya ajiye, in ba gizo idanuna keyi man ba, raper ce ta ƴan dubu ɗaya har guda biyu, sai katinshi da ke bisa kuɗin ajiye, Ba ɓala lokaci na mirgina ina mai wawurar kuɗin, na sanya hannu na zaro masu ɗan yawa ina Miƙewa kaman zan faɗi Mun daɗe bamu da ko sisi a daƙin, me zamu tsaya jira tinda ga dama tazo ta iske mu har inda muke? Ban bi ta kan ummata ba, na zari hijab ɗina ina mai ɗaura wa bisa kayan dake jikina na atamfa ɗinkin doguwa riga bubu dake jikina "Umma me zan fara siyo mana muci kafin mu nemi mafita?" na furta daga tsaye ga dukkan alamu ma ba sauraren cewa da take yi "ke suhan menene haka?" nake yi ba Ɗan murmushi tayi cikin tausaya war mahaifiya ga yaron ta ta shiga faɗin "Ko me kika nemo mana suhan zanci" "To umma" Na faɗa ina mai ficewa a daƙin, da zallan kallon tausayi ta bini dashi hawaye na biyo kuncin ta suna silalowa, "Allah yayi maki Albarka Hauwa'u ya ƙara shirya man ke, ya baki miji nagari, mai tausaya ma maraici ki, Allah ya ƙwato maki haƙƙin ki, ya kuma saka ma zalumcin da aka yi maki Ameen. Ta daɗe zaune tana kuka tana share wa, gami da jera ma gudar tilon ɗiyar tata adduo'i na alkhairi da take fatan su bita ko bayan babu Rayuwar ta, sannan ta miƙe gami da kauda sauran ragowar kuɗin da kantin kada ƴan bani na iya su leƙo su gani, ɓalli ya tashi, Abundant bata sani ba, tin bayan shigar Al'Ameen ɗin sashen ma'aikatan, mama uwani, da mama Talatu sun gashi, suna laɓe bayan ƙofar ɗakin su suna hangensu, saidai basa iya jiyo me yake faɗa ko kuma me yake wakana acikin ɗakin, fitowarshi, da kuma fitowar suhan ɗin ba jimawa da fitar Al'Ameen ɗin duk sun gani, Cikin sauri mama uwani ta fito ta bi bayan Suhan ɗin, saidai cikin rashin sa'a ta tadda Al'Ameen ɗin ya fice cikin motar shi, da matsananci gudu yayin da ita kuma suhan ɗin tabi ta gefen titi tna tafiya alamar ma tafiyar tasu bata zo ɗaya ba, tinda su a tinanin su ko Al'Ameen ɗinne zai ɗauki suhan ɗin su tafi tare da ita. Abinda duk basu sani ba shine, Al'Ameen ɗin dukan su tara su yake yi, lokaci yake jira yazo da dukkan su zai shayar dasu Madarar mamaki. _Masu karatu kada fa ku manta har yanzu fa a cikin ma'aikatan gidan, babu wanda ya san da maganar auren Suhan ɗin da Al'Ameen ya bijiro da ita, har ita kanta suhan ɗin da umman ta_ ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:36 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~17~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Tini rahoto ya isa kunnen Hajiya kubra, wannan ne ya sanya ta wakilta mama talatun da ta kai mata tsogumin zuwa ɗakin namu ta duba mata me ke wakana, domin dai ita dakanta ba zata iya taka sashen masu aikin ba. Cikin sa'a kuwa, ko da ta isa ta tadda umman tawa zaune bakin katifa tana jan carbinta a hankali yayin da idon ta yake kulle haka ta jingina bayan ta da jikin bangon ɗakin, bata yi sallama ba har saida ta isa tsakiyar ɗakin tana mai ƙare ma dukkanin lungu da saƙo dake cikin ɗakin kallo, cikin matuƙar mamaki umman tawa ta buɗe idanun ta tana mai bin mama talatun da kallo wadda har ta samu gefen katifa ta zauna, Amman duk da haka bata bar bin loko loko na ɗakin da kallo ba, ko zata hango wata leda ko wani abu. "A'a Talatu ce yau a ɗakin namu? Sannu da zuwa" umman tawa ta faɗa cikin ɗan murmushi haka kaɗan a fuskar ta, domin dai ta san me ya kawo mama talatun ɗakin namu "Eh wallahi kuwa Maryama, nazo duba jikin naki ne, ya ƙarfin jiki?" ta faɗa cikin ɗan ruɗewa kaɗan kama ta da umman tawa tayi tana mata kalle kalle a ɗaki. "Aikuwa Naji sauƙi sosai Alhamdulillah wallahi Talatu, kinga kaman ba ni ba Naji ƙarfin jiki na, Allah dai ya saka da Alkhairin sa" Umman tawa ta faɗa tana mai komawa ta jingina da bangon, daga haka ta ja bakin ta ta tsuke, hakan da mama talatun ta fahimta ne ya sanya ta cewa "Madalla Madalla, Allah ya ƙaro afuwa" ta miƙe cikin hanzari zata fice yayin da umman tawa ta bita da ameen tana mai kallon bayan ta, gami da girgiza kai a hankali a hankali Daidai bakin ƙofa muka haɗu da ita, gaida ta nake yi ma, Amman Sam hankalin ta na ga ƙatuwar ledar da na ciko mana ita taf da siyayyar abinci da zamu ci kafin muyi tinanin mafita. Har na gitta ta na shige ɗakin tana tsaye tana bin ledar da kallo, domin sanin menene ciki, niko ba ta ita nake yi ba, sanin halin ta da nayi, sai ma na tsinci kaina da baƙin cikin shiga ɗakin namu da tayi, koda yake ba zuwan kanta bane turo ta aka yi. Jiki a matuƙar sanyaye ta wuce direct zuwa sashen hajiya Kubran ta zauna zaman jiran ta fito, domin taji ba'asin aiken da tayi mata. Ta ɓangaren mu kuwa ba ma ta ita mukeyi ba, abincin mu muka ci cikin jin daɗi, da sanya ma Ya Ameen albarka, ko babu komai ya zo mana a lokacin da muke buƙatar shi, mu bamu damu da halin mahaifiyar shi ba, ko ma me zata yi ai yunwa bata da hankali. Ƙarya da gaskiya ta shiga zayyane ma Hajiya Kubran, yayin da ita kuma take zaune hakimce tana sauraren ta, take gyaɗa kai a hankali, lokaci guda ta sallami talatun da take faɗa mata ƙarya da gaskiya gami da kiran hajiya Laila aminiyar ta, kuma maganin kukan ta. **************** Washegari tin da sassafe sai ga mudi driver ya mana sallama, gami da miƙo man fararen takaddu ƙal dasu, yake shaida man Alhaji ƙarami yace in cike zai aiko shi ya amsa anjima Amsa nayi gami da mashi godiya, na koma cikin ɗaki fuska ta fal da annashuwa, farin ciki nake yi sosai matuƙa, domin dai ko ba komai na fahimci ya danganci karatu na ne, umma ta na shiga nuna mawa, itama tayi murna sosai, gami da ƙara gode ma Al'ameen ɗin da ya tsaya ma Al'amarin mu kai da fata. Bamu kaɗai yake ma haka ba, kowa a cikin gidan yana taimaka mashi, muddin abun ya sha kai, domin kwanaki ma sai da ya biya maƙudan kuɗi aka yi ma yarinyar mama saude mai girki aiki, muma cikin gida ne muke ta jin raɗe raɗi, da irin taimakon da yake ma ma'aikatan baya ga albashin su. Cikewa na shiga yi, da gani dai kaman Jarabawa ce zan rubuta watau Jamb, inda naga ban gane ba sai in tsallake, a haka har na gama na maida cikin folder ɗin na ajiye jiran mudi yazo ya amsa. Wannan ce ta bani damar yin aikace aikace na cikin jin daɗi, lallai ina dab da cika buri na, abun ya matuƙar ƙarfafa man guiwa, saidai na nazo wajen zaɓen choice na Abunda zan karanta tsallakewa nayi, na bar mashi ya zaɓa man, duk abinda ya zaɓa man daidai ne. Zuwa azahar na gama komai, har list ɗin abinda zanje in sissiyo mana na buƙata nayi, wanka nayi cikin shiri na simple ba mai ɗaukar lokaci ba, doguwa riga ta material ce jiki na, Afnan ce ta bani ita cikin kayan da ta kawo mani kafin ta koma, da gani ma bata taɓa sanya ta ba, ta amshe ni matuƙa, gyale na ɗauko zan yafa, umma tayi man wani irin kallo, ba arziƙi na ajiye ina ƙumshe dariya a ciki na, oh umma bata so taga nayi gayu, ita har kullum gani take yi ba'a matsayin kowa muke ba, in ana ganin ka ƙwas-ƙwas ma sai ayi ta gulmar ka acikin gidan, dama ga shi ga irin zaman da mukeyi acikin gidan. Sallamar mudi ce ta katse man dariya da nake yi a zuciya, ɗauko takaddun nayi na miƙa mashi ina ƙara mashi godiya, amsa yayi yana dariya tare da ƙara ma umma ta ya jiki, saboda ɗazu da yazo basu gaisa ba. Sai da na gama kitsawa sosai, sannan na ɗauki ƴar jikka ta gami da takadda ta list ɗin abubuwan buƙatar, sallama nayi ma umma gami da ficewa daga ɗakin namu kai tsaye zuwa ga barin gidan cikin salon tafiyata da lokutta da dama umma ta kace Allah yayi mani nawar tafiya, su kuma sauran ma'aikatan kance ya ga ce, kai ba kowa kowa ba Galadima kashi🤣 Tin daga nesa na hango shi tsaye jingine jikin motar shi, mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, baƙa ce wuluk sosai, saidai gilassan ta masu sauƙi duhu ne, ni ban ma taɓa ganin shi a cikin wannan motar ba, da gani dai sabuwar siye ce, to abu da masu abunsu Sanye yake cikin riga ƴar shara, da wando dogo har ƙasa, kanshi babu hula saidai baƙin gashin shi da akoda yaushe yake kwance luf bisa fatar kanshi, hannun shi na riƙe da makullan mota da takaddun nawa a hannun shi yana dubawa, Baƙin sun glass ɗin da ya sanya ma idanun shi, su ke katange ka daga kallon cikin ƙwayar idanun shi, kaman kullum dai yana tsaye cikin kwarjini shi, da kamalar shi, Al'ameen mutum ne da idan ka kalle shi sai ka ƙara kallon shi Duk da ba ni yake kallo ba hakan saida ya jaza mani harharɗewa, cikin son gyara tafiyar tawa na isa daidai saitin inda suke tsaye shi da mudi driver "Ahaf, yallaɓai ai gama ta nan tafe" mudi ya shiga faɗa mashi, ga dukkan alamu magana suke yi ko kuma aika mudin yayi ya kirawo ni. "OK ce mata tazo ina kiran ta" Abunda ya faɗa kenan, har yanzu idanun shi na kan takaddun ko sau ɗaya bai ɗago ya kalle ni ba, Kwala man kira mudin yayi "Ke Suhana, kizo yallaɓai na kiran ki" chak naja na tsaya, da ɗan ɓacin rai a fuskanta, in ma kiran ne ai sai ya isa inda nake ba ya kwala man kira ba haka gatsau kowa na saurare. A hankali na juya akalar tafiyar tawa daga nhfar gate ɗin zuwa wurin su inda suke tsaye, da sallama a bakina na isa lokaci guda ina mai gaida shi "Yaya ina wuni?" bai ɗago ba har yanzu idanun shi na kan takaddun yana nazari su ya amsa mani da "Lafiya" a gajarce Gyara tsayuwa ta nayi duk a takure nake wallahi, kwarjini shi kan ƙara ruɗani, ɗan guntun murmushi naga ya saki, yana mai juyawa kai tsaye zuwa ga bakin motar tashi ya sanya makullan da suke hannun shi ya buɗe tare da ɗauko wasu biruka guda biyu ya dawo inda nake tsaye Still bai kalle ni ba, ya shiga man tambayoyi wasu ina bashi amsa, wasu ina yin shiru dan ban sani ba. Choice ɗina ya tambaya na Abunda zan karanta, nan ma shiru nayi mashi, murya ta har rawa take idan zan bashi amsa da ya kula, inda Allah ya taimake ni mudi da yake tsaye ta gefen mu yana sauraren mu. Maimaita man tambayar yayi, cikin san kauda shirun da nayi na duƙar da kaina sannan na shiga faɗin "Yaya na bar maka zaɓi, duk abinda ka zaɓa man, ni bani da wani zaɓi, ko wane course ne dai insha Allah zan iya kuma zanyi" Ɗan shiru yayi jin ta kai aya, ɗagowa yayi a hankali ya zare glashin dake manne a idanun nashi yayi, kafe ni yyai da idanun shi, aikau na ƙara sadda kaina ƙasa, ko alama bana iya ɗago fuskata balle in kalli cikin ƙwayar idanun nashi da har wani zaiba zaiba suke yi "OK zaki iya tafiya" Abunda yace kenan ya maida idanun shi kan paper ɗin, alamar ya sallame ni kenan Cikin ƴar sassarfa na bar wurin ina mai hamdala da tambayoyi ba suyi tsawo ba, ba zai iya fahimtar yanda nake ji da aduk lokacin da magana ko tsayuwa ta haɗa mu wuri ɗaya dashi ba. Cikin san kauda tinanin na tare abun hawa na hau, ina mai faɗa mashi inda zai kai ni, saidai duk yanda naso inbar tinanin ya kasa bari na, ko wanne course ne zai zaɓa man ni suhan? Koma dai minene kuma koma dai wanene zanyi insha Allah, da haka har na isa inda zani,na gama abinda nake yi na juyo gida da tarin siyayya ta *************** Abubuwa sunyi mana matuƙar sauƙi, yanzu kam Alhamdulillahi, kwana biyar kenan ban kuma jin ɗuriyar hajiya ba, balle ƴan baran dan ta, hidimar bikin su aunty Saudat aka shiga yi ga dan gadan, abun ka da masu dashi, bikin dududu sati huɗu aka sanya shi, bayan iyaye sun shiga al'amarin, matuƙa Hajiya Kubra taso Al'ameen ɗin ya fidda matar aure, Amman fir ya nace shi fa indai bata kyale shi ba, tau ya riga ya zaɓi mata, kuma a shirye yake a ɗaura auren shi ko ma yaushe ne, in ma dasu Nihal ɗin za'a haɗa duk ɗaya ne Hakan ya tada hankalin hajiya, ta ƙara kafa mana karan zuƙa, gashi yanzu ta fiye ta fiye suke ta yi, yin oder ɗin kayan ɗakin su Nihal ɗin, nima na samu ɗan sauƙi, domin yanzu na rabu da wahalhalun su, bama kullum muke haɗuwa ba, duk da duk lokacin da zamu haɗu ɗin saƙon harara ne kawai za'ayi ta aike mun har sai na wuce sannan a bini da daigon tsaki wani lokacin harda tofar da miyau, sannan ace Allah shi kyauta mu haɗa iri da waɗannan mugayen talakawan ƙasƙantattu. Duk da bana jin me suke faɗa, hakan na mani ciwo, na dai san magana ce marar ɗaɗi suke faɗa a kaina da umman tawa, wannan ce ta sanya bana ma rawar ƙafa ko ɗokin zuwan bikin nasu, duk da wani lokaci ina jin sanyi na zasu bar gidan zan ɗan samu sauƙi, saidai nima ɗin ai ba zamana kenan ba a gidan Ƴar ƙaramar waya ta ce ta ɗauki ringin, ajiye gugar da nake yi nayi, cikin mamaki na ɗauki wayar ina duba number ɗin da ta kira ni, na kasa ɗagawa har ta katse, ɗan taɓe baki nayi na ajiye, cikin zuciya ta ina mai faɗin koma waye in ya masu ya kira, Nidai bana da kati a waya, kuma bana da wannan number ɗin a waya ta, dama in Naji kira, ko dai Afnan, ko Aunty Saudat, ko Aunty Nihal, sai kuma ita uwar gayyar Hajiya Kubra, ko cikin ma'aikatan banda number kowa sai ta Mama Talatu, itama dan ita ce shugabar mu. Cikin ko in kula na cigaba da Abunda nake yi, ina kallon umma ta na bina da ido har wayar tawa ta sake ɗaukar tsuwwa, cikin natsuwa na danna madannin amsawa da sallama a baki na "Assalamu Alaikum wa Rahmatullah" Abunda nace kenan naja baki na na kulle, shiru ne ya biyo baya na tsawon daƙiƙa biyar, cikin mamaki na ɗaga na kalli fuskar wayar, Still dai wayar na tafiya alamar ba'a datse kiran ba, har zan danna da niyyar kashewa ganin nayi sallama ba'a amsa ba, kuma ga dukkan alama koma wanene yana jinya yayi man shiru Muryar shi ce ta karaɗe illahirin kunne na, cikin salon maganar shi dake tafiya da hankalin mai sauraren shi ya amsa man sallama cikakkiya kaman yanda addini ya koyar. A ɗan zabure na ɗaga wayar ina mai ƙara kallon number, kaman mai son gano ainahin kamannun shi a fuskar wayar, natsuwa na nema na sanya ma kaina, gudun kada ya gane mamakin da nake yi, ko ba'a faɗa ba shine, ina ya samu number na? Zuciya ta ta shiga saƙa man, "Afnan" wani ɓangare na zuciyar ya bani amsa, ganin ba zai ce komai ba, na kauda shirun ta hanyar gaida shi "Yaya ina kwana?" "Lafiya" ya bani amsa a gajarce, ga dukkan alamun shi ne yin magana a gajarce, ya kauda man tinanin da nake yi ta hanyar faɗin "Ki shirya Gobe kuke rubuta Jarabawa, zan aiko mudi ya kawo maki abun buƙata, ƙarfe takwas na safe, in kin shirya ki kira ni da wannan Layin" yana gama faɗar haka ya datse kiran. Da kallo nabi wayar, kaman mai son gano wani abu, a sanyaye na ajiye wayar daga kunne na, ina mai kallon umma ta d take bina da kallon tana buƙatar ƙarin bayani, "Eh umma, yaya ne, yace gobe zan rubuta jarawaba, muɗi zai kawo man abubuwan da zan buƙata" na ɓata amsa, ina mai sanya hannu na kashe Iron ɗin da nake gugar gami da silalewa na kwanta bisa tantagaryar tiles ɗin dake manne da ƙasan ɗakin, nayi matashi da hannuwa na. Umman bata ce man komai ba, ta miƙe tsam gami da shige wa toilet ɗin dake cikin ɗakin tana mai mani addu'ar nasara acikin zuciyar ta. Na daɗe ina muɗiɗɗika a tsakiyar ɗakin, nama rasa tinanin da zanyi, mudi yayi sallama a bakin ƙofar ɗakin, tsam na miƙe gami da buɗe ƙofar ina mai gaida shi, ya miƙo mani leda irin ta botique gami da cewa "gashi inji Oga" Amsa nayi gami da gaida shi, ya man sallama ya wuce, yana mai cewa in gaida umma ta, da kallo na ishi, ko babu komai mudin yana daga cikin mutanen da nake ganin girma da daraja shi a idanu na, ganin cewa ban taɓa samun shi da koda alamun munafirci ba, irin na sauran drebobin gidan da zaka ga suna ƴan ƙusƙus da su mama mama Talatu da mama uwani. Zaune nake ina ta juya ledar na gagara buɗewa, har u mata ta fito daga cikin banɗakin ga dukkan alamu dai wanka ta gama, "Menene haka? Kin Gaza buɗewa ki duba, ko kin fasa karatun ne?" umma ta jefo man tambaya tana mai zama gami da janyo kwandon kayan shafan ta tana mutsittsika mai a jikin ta. Ban amsa mata ba, na shiga buɗe ledar bina fiddo kayan dake ciki, uniform ne ma su masifar kyau, da sandal da socks farare ƙal, sai ƴar ƙaramar jikka ta goyo Amman irin ta zamani an yi mata ado da flowers masu ƙyau da ƙyalƙyali, sai litattafai tili guda na karatu, da suka danganci physics, chemistry, biology, english mathematics ds. A hankali na shiga warware kayan da suke a goge tas, da gani sababbi ne, skirt ne iyakar guiwa, sai riga longslip da belt da gani tok-in akeyi sai ƴar ƙaramar hijab, da zamu iya kiran ta kai tsaye da himar, cikin kwalalo idanu na kai duba na kan ummata da ta dakata da shafa man tana mai bina da idanu, baki na a buɗe na shiga girgiza kai, "bazan iya sanya waɗannan kayan ba, da gani ma wannan makarantar ba ta musulmai bace" Umma ce ta wurga man wani irin kallo sannan ta shiga faɗin "kar ki sanya ɗin, sai ki canza wasu ai, tinda tsarin ki zasu bi, ko ba ta musulmai bace, ai rana ɗaya ne sai ki sanya dogon hijab, in kinje can kya cire, kada kiyi wasa da damar ki suhan" Linke kayan na shiga yi ina mai jinjina yanda zan sanya kayan nan in rasa mutane, kaman wata ƙaura, Amman ba zance ba zan sanya ba, ko don gudun wasa da dama guda da Allah ya bani. Haka na kwana karatu, lallai na yarda in ka bar karatu da yini guda zai barka da shekara ne, haka na dage nayi ta cusawa ina criming da joting har na samu na samu iya abinda zan iya ɗauka, san nan na duƙufa salla da addu'ar neman nasara, da da cewa duniya da lahira ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:37 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~18~* *Kyautar Page gare ki _Fatima Batula_ marubuciyar BUGUN ZUCIYA TA Nagode da ƙauna da kuna sadaukar da Page da kika yi mani, ina sonki tsakani da Allah kaman yanda kike so na, haka nagode da Alkhairin ki gare ni, Page ɗinnan naki ne, in kinga dama ki hana kowa karantawa* 🤣 ~Masu karantawa Bakwa comment, kuna yi ma kanku, in mu marubuta mun yi maku yajin rubutu, naga me zaku karanta kuma har ku share?, in kunyi mana comment kun ƙara ƙarfafa mana guiwa dame kuka ragu? Ai ka nuna kaji daɗin Abunda akeyi maka ma wani ɓangare ne na godiya, haba jama'a, ai ko Allah da ya halicce mu yana son godiya balle mu da ya halitta ya sanya mani hali irin na ɗan adam, da kuma son a gode mana, da nuna Abunda mukeyi kuna amfanuwa dashi, please ku gyara ba don mu ba~ °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Shawarar umma na bi, bayan na gama shiryawa, ni kaina kunyar kaina sai ta kama ni, ina kallon umma tana satar kallo na tana girgiza kai. Riƙe nake da wayar tawa sai jujjuya ta nake yi ina daga tsaye, na kasa kiran shi, gashi lokaci yana daɗa ƙurewa, har takwas saura, shahada nayi na danna ma Layin nashi kira, wannan ne karon farko da hannu na zai soma kiran wani ɗa namiji a rayuwa ta, shi ɗin daban ne, abubuwa da dama shine mai buɗe man ƙofofin yin su. Na zurfafa a tinani har wayar ta katse ban sani ba, sai dubawa nayi naga ashe ma bai ɗaga ba, ban ƙasa a guiwa ba na sake gwada kira, still dai bai ɗauka ba, haƙura nayi na koma gefen katifa na zauna, ina mai gyara safar dake ƙafa ta da take fara ƙar, sai ɗaukar idanu take yi. Ci gaba nayi da craming ina mai gyara zaman jikkata a saman kafaɗa ta, idan ka kalle ni kai zaka rantse da Allah ba ɗiyar Hausawa bace, kayan sun matuƙar fidda man shape, skirt ɗin da yabi lafiya ƙuguna ya zauna ɗas kaman a wajen aka ɗinka shi, nayi matuƙar mamakin yanda aka yi har ya gane size ɗin kayan da zasu iya yi mani Miƙewa nayi ina gyara zaman belt ɗin a saman ƙhgu na da yabi shafaffen cikina, kai kace bana cin abinci, duk da ni ba siririya bace hakan ce ta sanya kayan suka cika ni nayi ɗas ɗas dani. Waya ta ce ta ɗauki tsuwwa alamar ana kira na, cikin hanzari na ɗaga kasancewar naga har takwas saura minti sha biyar tayi, gashi yace ƙarfe takwas ne ake shiga Jarabawar, sallama kawai nayi ko amsa mani baiyi ba, cikin hanzari yace "Fito" Abunda ya faɗa kenan ya datse kiran Sallama nayi ma umma, ta shiga bina da addu'a kuwa, gami da gargaɗa ta da in kama kaina, in tsare mutumci na, kasancewar makarantar wadda take haɗe maza da mata, da murmushi na bita, ina jaddada irin ƙaunar da umman tawa take mani, da son kasancewa ta ta gari a duk inda na shiga. Hannu na sanya na ɗauki gogaggiyar zumbuleliyar hijab ɗita da take ajiye gefen katifa nayi, na warware ta na sanya, ba ɓata lokaci na fice daga ɗakin namu addu'a ɗauke a bakina. Kasancewar safiya ce, babu kowa a harabar gidan, balle ƴan tsurku su samu na rahoto, ko ba haka ba ma kuma ɗaukacin mutanen gidan basa nan, wai sun tafi turkey siyayya, cikin hanzari na isa ga motar da take fake tsakiyar harabar gidan, da gani a cikin ta ne za'a kai ni makarantar. Baya na buɗe zan shiga, har ga Allah na ɗauka muɗi driver ne zai kai ni, "dawo gaba" muryar shi ta doki dodon kunne na, ba gardama na maida murfin na rufe gami da buɗe gidan gaba na shiga. Ko zama ban daidaita ba ya fizgi motar gami da ficewa daga harabar gidan da tuni mai gadi ya wangale mashi gate. "Kina cen kina shiririta har kin so ki makara" Abunda ya faɗa kenan ya maida bakin shi ya rufe kaman ba shine ya mani magana ba, ɗan ɗagowa nayi gami da ɗan waiwayawa ta gefen da yake zaune yana tuƙi na ɗan kalle shi haka, tuƙin shi yake cikin kwanciyar hankali da kwarewa, sharara gudu yake yi kaman waɗanda zasu bar gari, yayi kyau abun shi, cikin manyan kaya, da dukkan alamu yana son manyan kaya kaman ya san suna matuƙar da cewa dashi, ɗinkin dakakkiyar shadda ce mai masifar kyau da ɗaukar idanu, zamu iya kiran ta da royal blue, hakan ce ta sanya fatar shi haskawa sosai, fatar nan tashi kaman bata shan rana, lumui ga gashi da yake kwance saman ta, hannun shi na ɗauke da zoben azurfa mai kyau da ɗaukar idanu, yayin da agogon shi ƙirar iphone take ta walƙiya cikin hasken ranar da ya riga ya gama hudowa. Maimakon in bashi ansa, sai na kauda zancen da cewa "Yaya Ina kwana?" Bai bani amsa ba, sai ma ɗagawa da yake yi yana kallon agogon dake maƙale a hannun nashi, yana sarkin ɗan siririn tsaki. Daidai bakin gaye ɗin makarantar yayi parking, yana mai waiwayo wa ta inda nake zaune yake faɗin "Ki tabbatar kin cire wannan hijabin kafin ki shiga makarantar nan, doka ne gashi nan rutuce a jikin gate"da" to" na bashi amsa ina mai ficewa Tsayawa nayi tinanin ta ina ma zan fara cire wannan hijab ɗin ni na ma rasa ta yanda zan ratsa tsakiyar mazan dake ta wucewa zuwa cikin makarantar ga dukkan alamu dai mun soma makara. Ban aune ba Naji muryar shi ta baya na yana cewa "ba zaki hanzarta ba sai sun rufe shiga? Bani hijab ɗin nan, ba zasu bari ki wuce da ita haka ba, zasu ga kaman exam malpractics zakiyi da ita, bana son ƙauyanci" ya faɗa yana mai ƙara sowa ta inda nake tsaye Ɗan waiwaya wa nayi ina mai kallon shi cikin ɗan marairaice fuskar da babu komai samanta, daga hoda sai kwallo da lip balm, Miƙoman hannu yayi alamar in cire na bashi. Soma kiciniyar cire wa nake yi Naji yana faɗin "ai bake kaɗai bace a haka, haka dokar makarantar take, su a kamarantar su ake rubuta jamb ɗin, student ɗinsu basa zuwa ko ina, kiyi maza ki shiga bana so a samu wata matsala" Miƙa mashi na yi, gami da juyawa na fara taka wa a hankali zuwa ga shiga makarantar da duk na tsargu, gani nake kaman kowa ni yake kallo, Amman a zahiri ba haka bane, wasu ɗaliban ma harda ɗan gudun su, zuwa cikin makarantar hankalin su duk baya jikin su, tafiya nake yi ina ɗan ƙara jan skirt ɗina ƙasa har ga Allah a takure nake. Daf da zan shiga makarantar ne na ɗan juyo haka, yana nan dai tsaye inda na bar shi, ni yake bi da kallo duk wani taku na ɗaya akan idanun shi suke, wuf na faɗa cikin gate ɗin gami da ƙara ɗaga ƙafa cikin sauri na doshi babban hal ɗin makarantar da naga kowa na nufa. Ɗan jingina bayan shi yayi da jikin motar yana mai sauke ajiyar zuciya, tabbas sai yanzu ne yake na damar menene ya zaɓa mata wannan makarantar da uniform ɗinta suke haka? Kayan sun matse ta da yawa, yanzu a haka kowa zai ta kallon ta? Amman baya da yanda zai yi, makarantar ita ce makaranta mafi girma da kyau da ƙayatuwa a duk faɗin garin na Abuja, makaranta ce da aka yi recomending akan irin ƙoƙarin ta da hazaƙarta, ɗaliban makarantar basa faɗuwa exam duk wahalar ta, saboda suna follow-up da kuma jajircewa wajen ganin ɗaliban nasu sun kai ga gaci. A hankali ya shiga taka wa har zuwa ga motar murfin motar ya buɗe gami da zama, tada motar yayi yana mai ajiye hijab ɗin kujerar da shan ɗin ta tashi. Ya rasa dalilin shi na damuwa da halin da yaga suhan ɗin ta shiga na tsarguwa da kanta, ya san tarbiyyar ta ce haka, shi in ba yau ba ma zai iya cewa bai taɓa ganin ta da ko gyale ba ma balle kayan da suka matse ta haka ba, ɗan runtse idanun shi yayi yana buɗewa gami da ɗan bugun sitiyarin motar, ji yake kaman yaje ya maida mata hijabin ta ta ɗora saman waccen da ita da babu duk ɗaya ne. A haka har ya isa office ɗin nashi tinanin bai bar shi ba, yaji duk ya rasa sukuni, bai san menene haka ya tsaya ya to kare mashi zuciya da maƙoshi haka ba. To ko bayan ya shiga office ɗin kasa taɓuka komai yayi, sai jujjuya kujera yake yi idanun shi a rufe ya ɗaga kanshi sama, duk da ya rasa tinanin da zai yi, ƴar ƙaramar ajiyar zuciya yayi yana mai jawo wayar shi ya latsa kiran lambar Bilal domin yaji ya shirye shirye nashi bikin ke tafiya. *************** Cikin ikon Allah, ba zance banji wahalar exam ɗin ba, saidai zan iya cewa ta zo man Da sauƙi ba kaman yanda na zata ba, karatun da nayi ya matuƙar taimaka mani, inda na ɗan samu matsala kaɗai cumputer ɗin da ban san yanda ake amfani da ita ba, inda Allah ya taimake ni an nunnuna mana yanda duk zamuyi, sai gashi kafin lokaci ya cika ma na gama duka, ina dai ta addu'a cikin zuciya, saboda Jarabawa dace ce, ba ƙoƙarin ka ko hazaƙarka ke baka ba, iko ne kawai na Allah. Bayan mun futo ne, ina jingine jikin bangon hall ɗin tsaye rataye da ƴar jikka ta, wayata tayi tsuwwa. Ina ɗauko wa naga Afnan ce, cikin hanzari na amsa, gaisa wa muka yi cikin mutu ta juna da ƙaunar juna ta shiga zaulaya ta, tana ceman ya exam ta kira yayan ta yace mata ina cikin exam, kuma ga lokacin da zan fito shine tace bari ta kira taji ya wasa kwalwa, cikin dariya nace mata "haba ai wlh ba wani wasa kwalwa, komai masha Allah, sai fatan fitowar ta lafiya" itama dariya tayi ta ɗaya ɓangaren tana mai cewa "kai aunty na, ko dai yayan nawa ya samo maki satar amsa ne? Baya so ki wahalar mashi da kanki? Ɗan sororo nayi ina mai sauraren ta, to me hakan ke nufi? Me maganar tata take nufi ne? Ɗan murmushi nayi ina cewa" Haba afnan wace irin magana kike haka? Kaman ya in wahalar mashi da kaina? Wai tsaya ma yaushe ne na zama auntyn taki? Cikin kwalalo idanu afnan ɗin tace "wai sorry" ɗif ta datse kiran tana mai maida numfashi da ajiyar zuciya ta maida kallon ta ga aunty feena dake zaune tana tsefe ma Nasreem kai, murmushi aunty feenar tayi nata cewa "Ah to uwar surutu, ina tinanin fa yarinyar da mahaifiyar ta basu san menene ke faruwa ba a gidan nan, gashi ke kin kira zaki gwangwaɗa mata, ke da Al'ameen ai, indai yaji katoɓarar da kika aikata mashi" cikin ƴar shagwaba irin wacce suka saba ta shiga diddire ƙafafu, Allah kuwa aunty ba zai ji ba, saidai in kece kika faɗa mashi, kinga ita suhan ba surutu ke gareta ba, hasali ma ban taɓa ganin suna magana da yaya ba, wallahi shaf na manta ance a bar maganar na ɗauka Mom ta amince ne" "Ah to kedai kika sani da shegen surutun ki" Aunty Feenar ta faɗa tana mai sake murmusawa alamar zolaya. Ta ɓangaren na kuwa sototo nayi da waya a hannuna, bayan na fahimci Afnan ɗin ta riga ta datse kiran daga ɓangaren ta, ɗan taɓe baki nayi ina mai sauke kafaɗa ƙasa, afnan da shegiyar shiririta take, bari Ya Ameen yaji mai take faɗa zata gane kuren ta ne, ni ce zata ding haɗawa da yayan? Abunda ta san wutsiyar raƙumi tayi wa ƙasa nisa, haka kuma sama tayi wa yaro nisa har a badan abada, ci gaba nayi da taka wa har zuwa bakin gate ɗin, naja na tsaya ina shawarar tarar abun hawa da zan koma gida. Ta bayana Naji sallama, ɗan juyawa nayi, su uku ne tsaye sai faman murmushi suke irin nasu na ƴan gayu sakatattu alamar son suke suyi magana dani. Kayan uniform da na gani jikin su irin nawa ne ya sanya ni amsa masu sallama tawa ina mai kauda kai gefe, ganin bani da Case dasu ne ya sanya ni fara taka wa da niyyar basu waje, ga dukkan alamu irin ƴan makarantar nan ne marasa kunya da duk yarinyar da suka gani sai sunyi mata magana. Gaba na suka sha, suna mai faɗin "Haba beb, ya zamuyi maki magana kiyi banza damu ki kyale mu, har kina shirin gudu wa?" ɗaya daga cikin su ya faɗa yana mai ɗan girgiza kai da jiki haka, alamar ya daɗe cikin iskanci irin nasu na ƴaƴan masu kuɗi. Bance mashi ƙala ba, na kuma zagaye su da niyyar wucewa, ɗaya daga cikin su ne ya sanya hannu gami da janyo hijab ɗina, dole naja na tsaya ina mai wulla masu manyan idanun a, alamar su kyale ni, basu ma kula da Abunda nake nufi ba, su a tinanin su ma fari nayi masu da idanu, Abunda ya ƙara burge su kenan. "Haba beby, tin shigowa ki hall muka ji kinyi mana, kin kwanta mana, duk faɗin makarantar babu yarinyar da ta kaiki kyau da sura, ki kalle ki fa sama har ƙasa" ya faɗa yana nuna ni da hannu sama zuwa ƙasa Gudan ya amshe da cewa "Ni sunana Adnan, wannan kuma Mujaheed, sai wannan Umar ana kiran shi U-Boy, in kinji ana cewa triples to mune, makarantar nan babu wata mace d zamu kalla muce muna so ta ƙi amsa mana balle ke da kike sabuwa zuwa makarantar" Tsoki naja ba tare da na ce masu komai ba, na kuma zagaye su na wuce ina mai Allah wadarai da irin tarbiyyar su, ga kansu duk askin banza, hatta da wandon su duk sun saɓulo shi ƙasa ass down, to ni ko maza sun ƙare zan tsaya sauraren waɗannan ƴan tautsin yaran ne? Ƙila ma duk in ka bincika na girme su.. Basu haƙura ba suka sake biyo ni suna janyo mani jikka, cikin rashin sa'a kuwa har hannun jikkar ya katse, dama ɗan sirri ne, littattafan da waya ta ne suka watse ƙasa, cikin hasala na zuƙunna na shiga tattara wa, bana so in masu magana ne abun ya yi ƙamari, ina so mu rabu lafiya ne, tinda na san da wuya idan zan kuma komawa makarantar a rayuwa ta, dariya Naji sun kece da ita suna mai cewa "kanburauba, baba Kaga wata iphone waya nan? Ɗaya daga cikin su da bazan iya tina sunan da aka faɗa mashi ba ya shiga faɗa yana mai nuna waya ta da hannu yana tin tsira dariya harda buga ƙafa ƙasa. Hannu ne kawai naga ya shiga tattara mani sauran takaddun da littattafan ya niƙo mani, cikin ɗan firgici na ɗago ina mai kallon shi, kwalla da nake ɓoyewa ta wulaƙanci da suke mani ce ta shiga silalowa, wata na bin wata, hannu ya sanya yana ɗauke mani hawayen cikin isa da kwarjini irin nashi ya miƙe yana mai zaro sabon hanky daga aljihun shi yana mai miƙo mani, amsa nayi ina Miƙewa gami da share kwalla tawa da ta fara yawa a fuska ta. Sake zuƙunnawa yayi ya ɗauki wayar tawa da take gefe, ga dukkan alamu dukkan abubuwan da suke faɗa akan kunnen shi ne, da bansan yaushe ya iso wajen ba, saboda ban kawo ma raina zai dawo ɗauka ta ba. Hannuwa na kawai Naji an shiga ja a hankali har zuwa bakin mota, ya buɗe man gidan gaba na shiga na zauna, ya zagaya ya buɗe ya shiga gami da yima motar key, saida muka hau saman babban titi sana ya sanya hannu ya jawo hijab ɗina da ya maida gidan baya, ya ɗora mani bisa cinya, alamar in sanya kenan. Su ko yaran da kallo suka bishi, su kansu basu san lokacin da ya iso wajen ba, daidai suka gan shi zuƙunne, hankalin su na gare ni da suke ta yi man shaƙiyyanci. Ɗaya ne daga cikin su ne yace shi kuma wannan waye? Ko dai ƙanwar sa ce? Ko kuma budurwar shi? Wanda aka kira da U-Boy ne yace "kai baba yanzu baka gane wannan gayen ba? Dambulan ne fa, shine babban ɗanɗan Alhaji mustapha, ai ni ta bayan layinsu muke, bansan wannan acikin ƙanen shi ba, ai su basa karatu Nija ma, ba dai san menene haɗin shi da ita ba, Mujaheed ɗin ne ya riƙe baki," kai haba U-Boy, ashe da mun ci ubanmu, yanda na san gayen cen baya da wasa ko alama, yana iya Sanyawa a kulle mu fa wallahi, baya son rashin kunya" "Muje Baba, Allah ya so mu ba gaban sauran guys ɗin aka yi ba, ai da mun sha kunya" Adnan ɗin ya faɗa yana mai jan hannun su suka cigaba da tafiya domin barin makarantar *************** Muna isa gidan ya sauke ni baƙin gate, bai ceman ƙala ba, haka nima ban tanka mashi ba, na Miƙa mashi hanky ɗinshi, ɗaga man hannu kawai yayi alamar in bar shi, fita nayi na kulle motar, gami da ɗan ja baya, ina jiran ya miƙo mani wayar, motar shi ya ja ya wuce ba tare da ya ko kalle ni ba, jiki a saɓuke na shige gidan zuciya ta a cunkushe, har saida umma ta fahimta Aiko ta shiga tambaya ta lafiya? Ko Jarabawar ce tayi wahala? Girgiza mata kai nayi, ina mai ƙaƙalo murmushi dole nace "a'a umma, Jarabawa Alhamdulillah, kawai gajiya nayi, gashi kaina yana ɗan ciwo, kinsan na kwana karatu jiya ban samu isasshen barci ba" cikin tausaya wa ta shiga ɗan ɗaga man kai alamar eh, sannan ta shiga cewa "to maza kiyi wanka da sallah, kici abinci ki kwanta ki huta, ai an daɗe ba'a gamu da karatun ba, dama sai a hankali" da to na bita ina mai kwaɓe kayan na shiga ban ɗaki domin yin wanka. Sai da na kammala komai, sannan na shiga cin kafiyayyen abincin da umma ta girka mana, duk da zuciya ta babu daɗi akwai tinanin da nake son yi nafi so sai na natsu, gashi waya ta dake hannun Ya Ameen ɗin, naso in kira Afnan domin jin me take nifi da kalama ta na ɗazu? Saidai wata zuciyar tana mai ƙwaɓa ta, gami da tunatas da dani shirme da shiriritar afnan ɗin lokutta da dama. Da haka bacci ya kwashe ni, bayan gama yabiɗar abincin, dama da tarin gajiya fal acikin a jikina. ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:37 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~19~* *Gaisuwa da ɗaukacin marubutan Golden Pen Writer s Association, Ina matuƙar yinku a ko ina kuke, kuci gaba da rubuta mana litattafai masu ma'ana, mu kuma muna suburbuɗa karatu Insha Allah, Allah ya ƙara maku ɗaukaka da zaƙin hannu. _Love u All_* *kyautar Page gareki _Khadeeja s. Dogarai (Lipton Girl)_ shafinki ne wannan kiyi kaca-kaca da ɗan Albarka, abu naka maganin a kwaɓe ka* 🤷🏻‍♀ °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Bacci yayi daɗi, nice ban tashi ba sai da kiran sallar la'asar ya tada ni. A gurguje na sake watsa ruwa domin in ƙara jin daɗin jiki na, na maida komai na adana daya danganci karatu na. Mamaki nake yanda umma tayi mana girki a cikin ɗaki nake, kasancewar umma ta mace mai tsafta da kula, ya sanya bama a gane anyi girki a wajen har ta kauda ɗan ƙaramin gas cylinder ɗin da na siyo mana, aka ciko ta da gas, saboda stove akwai ɓata wuri, ga warin kerosine. Wuraren ƙarfe biyar na yamma ne, abun duniya ya isheni, ina son waya ta a kusa dani, gashi abinda yaran nan suka mani ɗazu a makaranta ya tsaya mani a rai, ai duk shi ya ja mani da ya bar mani hijab ɗita a mutumce ba ɗan iskan yaron da yaso ma tunkara ta. Naji mutum da ƙarfin hali, wai har cewa yake ina cen ina shiririta na kusa makara, ko sau nawa ma na kira shi bai ɗaga ba? 😡😏 Shashantar da zancen nayi, gami da miƙewa na janyo kayan guga ta da ban ƙarasa ba jiya na hau idasa wa. ******************* Ya daɗe office zaune yana jujjuya wayar a hannu, ƙare mata kallo yake tsaf, shi dariya ma abun yake bashi, lallai mace sai dai a barta, bai ga abun kuka ba anan, ita bata san ma kukan da take masu zai ƙara masu ƙaimi wajen Abunda suke shirin aikata mata ba? Tin farkon biyo ta da sukayi yake kallon su ta cikin mota, har kawo inda ɗaya ya janyo mata ƴar hijab ɗin dake saman kanta, baiyi niyyar fita ba, Amman kasancewar hangowa da yayi abun nasu na neman wuce makaɗi har ta kai ga sun janyo mata jikka ta katse, shi ya tunzura shi ya fito a sukwane zuwa gare su, yayi niyyar hukunta su, sai kuma ya fasa ganin cewa zai iya ja mata, wata rana ko a hanya suka haɗu da ita su so su rama abinda ta sanya aka yi masu, hakan ce ta sanya bai ko tanka masu ba lokacin da ya isa wurin. Hannun shi ya ɗaga gami da kallo, cen ƙasa zuciyar shi na raya mashi, me yasa ya kama mata hannu? Har da goge mata kwallar dake zirara saman fuskar ta? Me hakan ke nufi? Shi dai ya san in afnan ce ba zai iya bari yana kallo a so aci mata mutumci ba, ba zai iya jura ba, ita kuwa suhan ɗin yana mata kallon kamar afnan ne, ko don saboda tsananin ƙaunar afnan ɗin ga suhan ɗin. "Sai dai kada ka manta, ita ɗin ba afnan bace, ba muharrama ka bace" Abunda wani sashe na zuciyar shi yake tinano mashi kenan, ɗan murmushi ya saki yana mai girgiza kanshi irin na gamsuwa. Murmushi ya sake saki har saida kuma tun shi gabaɗaya suka loɓa, tinowa da yayi da hajiyar shi ƴar drammer, da yanda ya rufe mata baki d damun shi da zancen aure da take yi, nisa wa yayi gami da jawo wayar shi, ya kamata ma ace sun dawo hakanan, gidan baya mashi daɗi ya kasance babu kowa daga shi, sai masu aiki, Alhaji nasu ma baya ƙasar duk da shima gaf yake da dawowa ko don hidimar bikin su Nihal ɗin. Kira biyu yayi Alhajin ya ɗauka yana dariya "Yaya dai Son? Kwana biyu kajini shiru ko?" Murmushi ya saki yana mai cewa "Nothing Dad, good afternoon, Ya aiki?" "Aiki Alhamdulillahi Ameenullah, ya fama da jama'a? Fatan dai komai yana tafiya normal?" Amsa mashi yayi suka ɗan taɓa fira haka mafi yawanci da ya danganci aiki ne, yana kuma sanar dashi shirye shiryen kammala ginin gidajen nashi, da yanda za'a shirya ƙaddamar dashi, Alhajin ne yace su bari tukunna su gama da hidimar bikin su Saudat ɗin, saboda kada ayyuka su rincaɓe masu, ba haka yaso ba, yaso ya cigaba da shirye shiryen shi, hidimar biki ai ba tashi bace shi da yake namiji, kuma ba bikin shi ba ko na abokin shi Bilal, da to ya amsa ma Dad ɗin nashi, sannan ya sa yo buƙatar shi ta son Alhajin yayi ma Hajiyar tashi magana su dawo gida hakanan, duk abinda basu gama siya ba, akwai a gida nigeria, shi bai ga dalilin da za'a ce siyayyar kayan gida ba, sai an kwasa zuwa wata uwa duniya, murmushi Alhaji Mustaphan yayi, ko ba komai ya san yaron nashi wajen kishin ƙasar tashi ta nigeria, amsa mashi yayi da zai kira su ya sanar dasu, sallama sukayi suna mai marmari da begen juna, ƙauna ce mura ran mai tsafta Alhajin yake ma yaron nashi, ko dan kafin hankali da zurfi tinani irin na ɗanɗan nashi, duk ayyukan dake gaban shi, baya taɓa gajiyawa, ko ya nuna ya sare, balle ya gaza, addu'a yaci gaba da bin yaron nashi, Allah ya cigaba da taimaka mashi da haskaka mashi a dukkan al'amurran da ya sanya a gaba. *********************** Ko da Alhajin ya kira su akan su koma gidan, a cen ƙasa ran Hajiya Kubran ba haka taso ba, saidai isa da izza ba zasu bari ta bari ta nuna ba har ma waɗanda suke tare su gane, watau su Hajiya Laila, da kuma wata ƙawar ta makusanciya watau Hajiya sa'a, dama su shidda ne sukayi tafiyar sai sabuwa ƴar aikin da suka samu itama yarinya ce duk da zata ɗara ma Saudat kanta a shekaru, idanun ta a buɗe yake, dama bata aiki sai gidan masu hali, ga iya tuggu da munafunci, wannan ce ta sanya ta ƙara shisshigi ma hajiyar, duk da tana jin haushin mulki irin na hajiyar, su bakwai kenan, Hajiya Kubra, Hajiya Laila, Hajiya sa'a sai Nihal da Saudat sai hafsat ɗiyar Alhaji Awwalu da za'a haɗa bikin nata da su Nihal ɗin sai kuma sabuwar ƴar aikin tasu mai suna Maria, ana ce mata Maree. Ko da Hajiyar ta faɗa masu batun komawa tasu, basu ji daɗi ba matuƙa, kumburi suka shiga yi, harda cewa zasu kira Dad ɗin nasu su roƙeshi ya ƙara masu sati, Hajiya Kubran ce ta hana su, saboda mulki da taƙama na kai kawo acikin jinin jikin ta, kuma bata isa saɓa ma Alhajin ba, saboda shi ɗin namiji ne tsayayye a gidan shi, baya ɗaukar wargi ko saɓa dokar da ya gindaya akan kowa dake zaune a gidan. Ta ɓangaren Hafsat kuwa abun yafi kowa faranta mata rai, cikin zuciyar ta dama ta ƙagara su koma ƙasar tata ta haihuwa, ta samu ta koma gidan su cen Katsina, dama abban ta ne ya tilasta mata zuwa, ko mahaifiya ta ba don taso ba, saboda ta san yanda family ɗin na ƙanen mijin nata suke da bala'i jin kai da sangarta, uwa uba kuma mahaifiya su da dama ba wani shirin arziƙi suke ba, domin ita ba zata iya binta ba, a matsayi ta na wadda take gaba da ita, ko ba komai daga ita har mijin nata basa jiran komai daga garesu, don dai ma kawai ƴan uwantaka, da kuma shi Alhaji Mustaphan da ba halin shi ɗaya ba Sam da matar tashi. Ware ta suke yi, komai za'a siya ko za'a zaɓa ra'ayin su ake ɗauka, ba kuma komai bane in an siya masu ake siya mata ba, to don dai itama mahaifiya tata tayi ƙoƙari wajen ganin ta haɗo ta da ƴan kuɗaɗe daidai ƙarfin ta, gudun faruwa hakan, Hafsat yarinya ce mai natsuwa da kawaici, hakan ce ta sanya ko sunyi waya da mahaifiyar tata bata faɗa mata komai da halin da take ciki, ta riga da ta san Allah ya bata miji da gari, mai natsuwa na nuna ma sa'a, ita ba wannan abun duniyar ne yake gabanta ba, fatan ta dai kawai ɗaya ta koma ƙasar tata ta haihuwa, ko zata ga mahaifiyar ta mai share mata ku kanta, tana kewarta sosai, dan wanda zata aura bata jin shi, saboda kullum suna tare a waya ko kuma we-chat. Saboda haka yanda suke ware ta ko kuma suke nuna mata halin ko in kula bai dameta ba, duk da abun na mata ciwo, wai ace waɗannan ƴan uwanka ne, Amman babu wata alaƙar arziƙi da zata haɗa ka dasu, kai su dai waɗannan ba suyi da cen hali ba, nazajen su sun kwasar ma kansu, yara babu abinda suka sani daga sangarta sai jin kai? Ta lura ita kanta ƴar aikin tasu Maree munafuka ce, bata cen bata cen, wannan ce tasa ta ja jikin ta bata sake masu sosai su kansu, balle su wulaƙanta ta, duk da ta san maƙudan kuɗi Alhajin ya haɗo su dasu, kuma Yayansu Al'ameen na sake turo masu wasu akai akai, hakan bai sanya mata kwaɗayin abun su ba Sam, kuma shi Alhajin da sunan siyayyar yara uku yake bada komai, har shi Al'ameen ɗin yana sake haddada masu duk da Abunda suka siya su siyawa Hafsat itama, Amman basa ji daga su har mahaifiyar tasu, da ta kwaso ƴan barandanta saboda kankan a suka wani taho siyayyar aure. ************ Cikin kwana na biyun da basu umarni sai gasu sun tarkato sun dawo dukan su da tarin siyayya raga raga, tare suka taho da kayansu, hayaniya ƴan taron su ne ya alamta mana da dawowar tasu, ba zance bamuji daɗi ba, saidai lallai gabanmu ya faɗi, daga ni har umman tawa. Jiki ba kwari muka fito taron su muma, gefe mukaja muka tsaya gami da gaishe su, cikin su ba wadda ta amsa mana, sai a tsaki da Saudat tayi ta shige war ta cikin gida, Hajiya Laila ce naga tana mani wani irin kallo da na Gaza gane ma'anar shi, ita kau Hajiya Kubran ko kallo bamu isheta ba, Hafsat ce kawai ta matso inda muke tsaye cikin girmamawa ta gaida umma ta, cikin fara'a ta amsa tana mai tambayar ta Mamanta, Lafiyarsu lau ta tabbatar mata, sannan ta janyo hannuna da nake tsaye gefe guda cikin zaulaya tace "Ƴan mata ya ake ciki?" murmushi nayi ina jan hannun ta zuwa gefe, na shiga cewa "ke Hafsat zakiyi laifi fa, ki bari zamuyi magana anjima" da to ta bini, tana mai matsawa gefe, hakan ce ta sanya ta ƙara basu haushi, bata ko kula su ba ta shige cikin gidan. Bamu bar wajen ba muna tsaye har saida suka shige cikin gidan, sauran ma'aikatan duk suka watse suka barnu nan tsaye, umma ta ce ta matso inda nake tsaye ta shiga kallo na cikin gargaɗi, "Ki kula suhan, kar ki ja mana wani abu daban, kinga dai yadda suka dawo, tin anan ya alamta maki yanda abun yake, ki kiyaye" gyaɗa mata kai na shiga yi cikin gamsuwa da maganar ta, wucewa tayi gaba Ina binta laƙwai-laƙwai har zuwa sashe namu. *************** Al'ameen da yake tsaye ta jikin window ɗinshi, yana kallon duk abubuwan dake faruwa, tin daga shigowar shi gidan har watsewar su, ya sauke ajiyar zuciya, lallai Abunda yake gudun afkuwar shi ne yake faruwa, tsanar mutanen guda biyu ce yake hange cikin kayar idanun mahaifiyar da ƴan uwa nashi. Tabbas ya san shine ya jaza masu, ba tare da sanin su ba, ta yaya zai bi ya warware wannan tsanar da suke fuskanta? Laifin shi ne, ina ma ace da wata yayi wannan trap ɗin ba suhana ɗin ba, "Huh" ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin jiki ya ja ƙafafu shi daƙyal ya isa ga bakin gadon ya zauna yana mai dafe kanshi cikin matsananci yar damuwa, menene ya sanya yanzu yake yawan kula da al'amarin yarinya ne? Menene ya sanya yanzu tinanin ta baya fita a ranshi? Hannu ya sanya gami da jawo wata farar leda, fiddo Abunda yake ciki yayi ya shiga juyawa a hannun shi, waya ce mai masifar kyau, sabuwa dal a kwalin ta, ƙirar Samsung galaxy. Tunani yake ta yanda wayar zata isar mata ba tare da kowa ya fahimta ba yanzu, tinda ƴan gidan sun dawo, su kansu munafuka masu aikin yanzu zasu dinga kai komo acikin gidan, wani tinani ne ya faɗo mashi arai, maida wayar yayi cikin ledar ya miƙe gami da aza ta bisa mirror ɗin da yake ɗakin ya fice domin zuwa yi ma Mom ɗin tashi barka da zuw. A babban falo dukan su ya tada su, sun baje gajiya tayi masu ligif, Hajiya Kubra ce kawai bata wajen ita da aminan nata, suna cen sun ƙule a sashe na Hajiyar suna tattauna wa, gaida shi suka shiga yi, ya amsa masu babu yabo babu fallasa, sannan ya maida hankalin shi akan Hafsat ɗin da take jingine da kujera saman carpet, cikin ɗan dakin fuska yace "Hafsat ya gajiyar tafiya, fatan kun dawo lafiya?" ɗan murmushi tayi tana mai cewa "lafiya ƙalau yaya, ya muka same ku?" Lafiya lau ya bata amsa, yana mai nufar upstair domin zuwa ga Mom ɗin tashi. Ƙwanƙwasa ƙofar ya shiga yi, daga cen ciki aka bashi umarni ya shiga, cikin takun shi na ingarma namiji ya taka ya shiga bakin shi ɗauke da siririya sallama, da kallon ƙauna mahaifiyar tashi ta bishi, ɗan nesa dasu ne ya samu kujera gami da zama, ya shiga gaida su harda ƙawayen mahaifiyar tashi, cikin fara'a suka gaida shi suna tambayar shi wajen aiki, ya amsa masu da lafiya, yana mai tambayar su hanya, duka lafiya suka shaida mashi, miƙewa yayi gami da cewa "Mom zan ɗan fita kafin ki gama dasu, ina dawowa anjima" Bai jira cewar ta ba, ya fice daga falon, cen ƙasan ranshi, haushi fal na abokan mahaifiyar tashi, domin shi fa in ba zuga ta ba, da ƙara kambama mata kai baiga abinda suke yi ba, baiga dalilin ta ba ma na kwasar su su wani tafi siyayyar aure ba, Abunda ko daga nan gida nigeria zaka iya Kyi order ɗin duk abinda kake so, ya iso maka kuma har gida, salon ɓarnatar da kuɗi kawai, da son neman suna😒 Da kallo suka bishi dukan shi, har ya idasa ficewa a falon, ajiyar zuciya suka shiga sauke wa, sa'ilinbda Hajiya sa'a ta kalli Hajiya Kubra, "Lallai Hajiya ta, Al'ameen ne ya ƙara girma haka? Kina me da har yake neman jawo maki magana da raini, ta hanyar auren waccen koɗaɗɗar? Kiyo iya yin ki duk yanda zakiyi kiga kin daƙile wannan maganar wallahi, yaro mai jini a jiƙa kaman wannan ga naira ga kyau ga gayu? Tabɗi gaskiya kinyi sake, ni ba ma ga amfanin zaman da suke yi a cikin gidan ba, har ma zai dinga iya ganin ta kullum, kiyi amfani da damar ki, tin kafin kina kallon ruwa kwaɗo yazo yayi maki ƙafa, kina dai gani irin waɗannan yaran su ne yaran masu kuɗi da faɗa aji a faɗin duniya suke so su samu, ba ma nigeria ba, yo wannan ko a India yaga wata yace yana so ai wallahi ba zata yi mashi musu ba, balle waɗancen talakawan" Hajiya Kubra ce ta nisa gami da cewa " Humm bari dai Sa'a, wallahi kina ganin shi haka shegen tarin kai ne dashi kaman mahaifin shi, ba yanda banyi ba Amman abun yafi ƙarfi na, dama da dukiya nake taƙama, tau duk kansu daga shi har mahaifin nashi babu wanda bai fini ba a halin yanzu, nayi ƙoƙarin nuna ƙarfin uwa akan shi, Alhaji yana man ba razana da aure na, ni kau kjnga ba zanyi sake in rasa alhaji ba, samun kaman Alhaji a yanzu zai yi mani wahala... " Hajiya Laila ce ta katse ta da cewa ki bar mana komai a hannun mu Kubra, ba zai gagara ba, me aka yi a kayi Maryama balle wata ɗiyar ta cen, bari a gama hidimar nan zamu san abun yi, in ance ya ƙara kallon su ma ba zai kalla ba ko da kuɗi, kuma beside ma ni bana tinanin son ta yake yi, kinsan fa waɗannan miskilan yanda suke, nafi tinanin dai yana so ya kulle maki baki ne akan zancen aure da kike mashi" duk kansu sun gamsh Sa da hakan sun kuma sha alwashi ɗaukar mataki bayan kammala bikin Saudat da Nihal ɗin da yake saura sati biyu ayi. Kai tsaye sashen shi ya koma, baya jin ma mararin fitar, idan ma ya fita ba inda za shi, shi ba mutum bane mai yawo, Shiyasa ma ko abokan kirki baya dasu, sau tari yafi buƙatar ya zauna gida yana aiwatar da dukkan muhimman abubuwa a cumputer ɗinshi akan ya fita ya ɓata lokacin shi ga banza wajen abokai, duk kuwa da yanda samari da dama ke fatan ace shi ɗin abokin su ne, koda kuwa na wucin gadi ne. Bilal ya kira suka sha firar su, yake sanar dashi shigowar shi satin sama, domin su fara tsara yanda tashi hidimar zata kasance, "Abokina kayi ƙoƙari kaima ka fidda matar aure, duk da na san kai mata basa ga anka, Amman ai ba zaka ci gaba da zama haka ba, ko so kake yi ne sai mun haɗa ka da abie ne sannan zaka yi auren, ka kuwa san lokacin ka tsufa babu wadda zata gani ta ƙyasa" Murmushi yayi irin wanda ke ƙara ƙawata mashi kyakkyawa fuskar shi, sannan ya shiga maida mashi da amsa "Ai sai kazo kayi mani malan, na lura kaima team ɗin Mom kake, Kaga mubar maganar nan sai kazo zamu tattauna, bari in tashi in fita wajen mata san cen da na sanya a tattara mani zamuyi meeting dasu da ƙarfe biyar na yammaci kasan yanda abubuwan suke yanzu wallahi, ina tinanin zan basu hutu ne har agama hidimar nan ta bikin yaran nan, kada kwalwa ta ta buga hakanan" "Is ok Friend sai kunyi magana" Bilal ɗin ya amsa mashi ta ɗaya ɓangaren, sallama sukayi yayin da ya tashi ya fice hannun shi ɗauke da ledar wayar nan. Muɗi driver ya ba, ya umarce shi da ya kawo mani, shi zai fita ne sai ya dawo mmanka kula. Cikin hanzari kuwa ya russuna ya amsa yana mai cewa "To yallaɓai" kai tsaye motar shi ya nufa, yayin da mudinya nufi sashen namu ba tare da ya damu da ya san menene acikin ledar ba. Sallamar mudin ce ta katse ni daga shirya mana kaya da nake ta faman yi a wardrop, amsawa nayi gami da zura hijabina na leƙa ina mai gaida shi, amsawa yayi yana mai miƙo manledar dake hannun shi, "Gashi inji Alhaji ƙarami yace in kawo maki" amsa nayi ina mai cewa tou Mudi an gode, juyawa yayi ya bar wajen tin kafin wani ya gashi, yayin da na koma cikin ɗaki ina mai nuna ma umma ta dake zaune bisa darduma tana karatu. "Wai Ya Ameen ne yace ya kawo mani" na faɗa ina dire ledar gabanta, ba tare da na damu da sanin menene ciki ba, duk a zato na Abunda ya danganci karatu na ne. "Ki buɗe mana kiga menene a ciki" cewar umman tawa, tana mai ɗan ɗaure fuska haka kaɗan bansan menene dalili ba. Kwalin dake cikin ledar na fiddo, gaba na ne ya faɗi, na ɗan ɗago na saci kallon umma ta da ta tura mani idanu taga yanda zanyi, hannu na kuma Sanyawa na zaro ƴar mitsitsiya waya ta da Naji tana vibrating a cikin ledar. Saƙo ne ya shigo, number ce ban damu da in buɗe ba balle inga Abunda aka rubuta, durkushe nake gaban umman tawa kawai ina so inji hukuncin da zata yanke a kaina game da amsar kyautar waya daga hannun yaya Al'ameen ɗin. ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~20~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Sai faman zare idanu nake yi, kaman wadda tayi ma sarki ƙarya, hukuncin umman tawa kawai nake jira inji me zata yanke akai. Shiru tayi na tsawon minti biyar, nazari ɗiyar tata take yi, fatan take ace ba ita ce ta roƙeshi ba. Nisawa tayi kaɗan a hankali ta muskuta, tana mai ajiye littafin dake hannun ta, har yanzu bata ɗauke idanun ta akai na ba. " Suhan! Ina fatan dai ace ba kece kika roƙeshi waya ba, ba zaki iya haƙuri da wadda Allah ya baki ba" na tsinkayo muryar ta kwatsam cikin kunne na. Girgiza mata kai na cigaba da yi, ina cewa "a'a umma wallahi ban roƙeshi ba" kwashe yanda muka yi da yaran nan nayi a makaranta kwana biyu da suka wuce, har zuwa kan inda ya ɗauki wayar bai bani ba, Amman ban gaya mata ya goge man ƙwalla ba, balle ince ya kama man hannu, don na san tashin hankalin da zan fuskanta. Shiru ta sake yi sannan tace "Allah shi kyauta, an gode, Amman ina so ki riƙe talaucin ki, ki dinga juya ma abun duniya baya, wannan ƴar ƙaramar ta isheki, sai dai bazan hana ki amfani da wannan ba, saboda zamani ne yazo da ita" Cikin ɗan murmushi nace "to umma nagode" sake kallo na tayi da wani irin yanayi, sannan ta shiga cewa "sai ki kira shi kiyi mashi godiya ko? Sannan ki kula ba zan gaji da cewa ki kula ba, kindai san zaman da mukeyi a gidan nan" "Eh umma haka ne, to zanyi mashi godiya insha Allah" na faɗa murya ta fal farin ciki, sai dai cen ƙasa zuciya ta, wani irin tsoro ne da fargaba, me zai faru idan aka ce maganan Afnan ce ta fara tabbata?, me ne ya sanya shi share man hawaye Wancen lokacin? Me hakan ke nufi?" Jikina ne yayi sanyi ƙalau, komawa nayi na zauna, ina mai zaro wayar daga cikin kwalin ta, waya ce mai matuƙar kyau da tsada, ko a cikin ƴaƴan masu dashi ɗin ba kowa ne ke riƙe irin ta ba. Gashi tana da girma, har ina jin tayi ma hannuna mugun girma wajen riƙewa, saidai ko babu komai nayi farin ciki, ɗan chatting ɗin nan da kowa keyi nima zan fara, zan ga me duniya ke ciki, lokaci ne nima da zan fita daga cikin wannan duhun kan zama waje ɗayan. Ban mantawa, lokacin da nake secondry school, dukka kusan ƴan ajinmu na da waya, kasancewar ta makaranta da ƴaƴan manya, wasu ma biyu ne suke da ita. Ɗan murmusawa nayi, tinowa da nayi yanzu fa har afnan zamu dinga magana da ita kullum, ga wata ƙawata tin ta makaranta mai suna khairat, ta soni sosai, tana tausaya mani, ita gidan su masu hali ne, har wayar taso bani, nice dai na ƙiya don na san halin umma ta, yanzu gashi da nayi haƙuri na samu irin wadda ban zata ba ban tsammani ba. Kunna ta nayi, aiko ta ɗauka kaman jira take yi, nayi mamakin da layi ciki guda ɗaya, saidai babu komai a kanta sai Numbers guda biyu an masu saving da AMD bansan me hakan ke nufi ba. Niyyar goge su nayi, sai kuma wani tinani ya ɗarsu a zuciya ta, in shi ya ajiye su da? In suna da muhimmanci fa? Share wa nayi ban ko taɓa mashi abun shi ba, na jawo waya ta ina maida numbobi na ciki, har da ta khairat ƙawa ta da na janye mawa kusan shekara nawa? Itama ganin hakan sai ta haƙura ta ƙyale ni, kada ta jaza man matsala, fahimta da tayi umman tawa bata son tarayya ta da ita. Ko tana ina ma yanzu haka? Dukkan motsi na umma ta na kula dashi, tausayi na ne fal acikin ranta, tana addu'a Allah ya kawo lokacin da nima zan zama wata abu, lokacin da zamu fita a halin ƙuncin da muke ciki, lokacin da muma zamu zama mutane masu cikakken ƴanci kaman kowa. Sallamar Hafsat ɗince ta katse mana zaman shirun da muke, niko ina ta faman jujjuya waya a hannu, mamaki ya cika ni, ta yadda naga kuɗi tsababa cikin wayar, yanzu ko na tabbata wayar tashi ce, ƙila siyan ta yayi yana amfani da ita ya bani, bata san shine ya siya domin ita ba, ya zuba kuɗi domin ita, saboda harga Allah cin mutumcin da aka yi mata yayi mashi ciwo, ace kaman wanda yake gidan su ace ana ci mashi mutumci saboda wani abu wai waya, menene amfanin arziƙi nasu in har ba zai kare mutumcin mutanen dake rayuwa cikin shi ba? Da murmushi na bita ina mai cewa "A'a Hafsy ce? Shigo mana" na faɗa ina nuna mata gefen katifa inda nake zaune, alamar ta zauna, murmushi tayi ta ƙara so ta zauna tana gaida umman tawa, itama cikin dakin fuska ta amsa tana mai sake tambayar ta maman su, duk suna lafiya tace, a hankali suka shiga fira da umman tawa, yayin da ni kuma hankali na na kan waya, har umman tawa ta miƙe ta shiga ban ɗaki, sai a sannan ne ta maido hankalin ta kaina. Hannu ta sanya ta amshi wayar, tana murmushi take faɗin "Ya Suhan, wannan mai zafin fa? Yaushe kika shiga yayi ban sani ba? Domin dai ina da number ɗinki, Amman naga ko WhatsApp bakyayi kuma kina da irin wannan babbar waya haka, ko ni fa bana iya riƙe irin ta" ta faɗa fuska cike da murmushi, ta ƙara she da zaulaya. Hafsat ɗin dai kaman yanda kuka sani ɗiya ce ta yayan Alhaji mustapha Dambulan, watau Alhaji Auwalu da yaje zaune cen Katsina, tana zuwa gidan akai akai, in suna ƙasar, saboda iyayen su masu zumunci ne akai akai, suna yawan tura ƴaƴan su gidajen nasu, hatta su saudat ɗin ana tura su Katsina, duk da dai basa so, suna cewa takura suke yi wai basa walawa a gidan yayi masu ƙarami, duk da kuwa irin girman gidan nan da kayan more rayuwa dake cikin shi shima, domin yanzu Alhaji Auwalun ya kai matsayi director a ma'aikata tasu,ya samu rufin asiri daidai gwargwado, duk da kuwa bai ko kama ƙafar Alhaji Mustaphan ba. Bana hafsat kaɗai ba, dukkan in ƴaƴan Alhaji Auwalun da hajiya zainab, yara ne masu sanyin hali, girmama naga a dasu, da kuma kawaici, basa da girman kai Sam, wannan ce ta sanya tamu tazo ɗaya da Hafsat ɗin da ko zata girme mani tau fa da kaɗan ne. Ita dai ba'a isa a hana ta zuwa sashe namu ba, hasali a In tazo ba wani damuwa da al'amarin ta suke ba, ba ta ita suke yi ba, lokutta d adama ma haushin ta suke ji, suna cewa duhun kai yayi mata yawa, itama ta gama karatun ta tsaf a makarantar ummaru Musa ƴar adu'a dake jihar Katsina dabon. Sai gashi kuma Allah ya bata miji nagari, na nuna ma sa'a, hasali ma dukka mazajen daga na Saudat, har Nihal ɗin babu Abunda zasu nuna ma nata, sai ma shi ya nuna masu tarbiyya da kuma dattako. Murmushi na ɗanyi ina cewa "Uhm Hafsy kenan, nima yanzu wayar ta iso mani wlh" kasancewar ta mutum da ta san halin da muke ciki, da irin zaman da mukeyi, ya sanya na kwashe labarin yanda aka yi na samu wayar na faɗa mata. Aiko murna ta fara yi, tana ce an "kinga kada ki damu, rabon ki ne ya rantse, ai Ya Ameen ɗin mutumin kirki ne, Sam shi ba halin su ɗaya dashi ba, yana taimakon na ƙasa dashi, ko bayan dawowar mu Naji ana cewa ya raba ma dukkan in ma'aikatan kamfanoninshi kayan abinci da tufa fi masu kyau da tsada, a bakin su Hajiya Naji da tana waya da wasu ɗazu. Amsar wayar tayi ta shiga buɗe man abubuwa irin su WhatsApp, Facebook, da wani chat wai shi duo, nice nace ta bar shi hakanan, har sai na iya waɗannan tukunna. Fira muka shiga yi sosai, har take cewa zata dawo ɗakinmu da zama kafin lokacin tafiyar tata yayi, nake ce mata tayi haƙuri ta rufa mana asiri, kwanciyar ta tayi tana cewa "uhmm, kanki kuma akeji Suhan, KEDAI Allah yayi maki tsoro kaman farar kura" Koda ta sanar da umman tawa da ta fito daga banɗaki, murmushi kawai tayi, ai kaso mai sonka ka kuma girmama duk wanda yace yana sonka. "Umma wata Alfarma nake so in roƙe ki don Allah, ki ara man suhana ta taya ni zuwa wajen gyaran jikin, da ƙarashe siyayya har zuwa lokacin da zan koma gida, kinga dai su Saudat ware ni suke yi, bana da aboki ko ɗan uwan da zan tun kara, Suhan ɗin dai ita ce" Hafsat ɗin ta faɗa tana marairaicewa, kaman wadda zata yi kuka, lokaci guda tana kallon umman tawa. Ba matsala umma ta tabbatar mata, saidai taja hankalin u akan mu kula da me mukeyi, idan mun fita mu san ina zamu, kuma kada mu sake mukai magariba a waje waɗannan sune sharuɗɗan ta. Da to muka bita, hafsat ɗin kuwa taji daɗi, dama ko ba komai bata kawo ma ranta umman tawa zata hana, saidai ta san halin umman tawa, wani lokaci kaman mai aljannu take, zata iya hanawa a lokacin da ba'a tsammata ba. Faɗa mata nayi ina son in kira yayan in mashi godiya Amman ina jin kunya, harara ta tayi cikin wasa tana cewa "menene na kunya Suhan? Ai ya yanki ne yanzu an riga an zama ɗaya, ki kira shi kawai wlh, ko kuma ki tura mashi text ai zai gani godiya daɗi gareta, balle yayan namu da yake miskili yana iya dakin fara godiya ya katse wayar" Amincewa nayi da gara in mashi text, in mun haɗu a zahiri na ƙara gode mashi, sai dai fa inda gizo ke saƙar, bansan me zan rubuta ba, sai jujjuya wayar nake a hannu. Hakan da ta fahimta ne ta fizge wayar a hannu na tana cewa "Dallah kawo nan, kai a tukunya, ai gara ma kizo kije makarantar ko kin ƙara wayewa, godiya ma kin gagara yanda zakiyi ta, wannan duk lokacin da kika yi saurayi naga yanda zakiyi dashi" ta faɗa cikin zaulaya da dariya, Nidai bance mata komai ba, sai a kishingiɗawa da nayi ina mai ɗan murmusawa a hankali. Ban san me ta rubuta ba, na dai ga kawai ta jawo wayar ta ta ɗauki number ɗinshi ta tura, sannan ta miƙa man wayar tana faɗin "Done, saƙo ya isa" Firar mu muka cigaba da yi, tana faɗ man yanda tsare tsaren bikin nata zai gudana, duk da ba wani pherty zata yi ba illa iyaka traditional day da za'a gudanar lambun gidan, wanda su kau su saudat sun haɗa pherty ya kai kala biyar wata rana ma sau biyu za'ayi. Ita dai tace ba zata shiga ba, cikin hidimar su, bata da ra'ayi, duk da mijin nata yaso ayi ko kala biyu ne saboda abokan shi, Amman ta kafe kawai tace kowa ya sanyo kayan gargajiya, yazo yaci goruba ya sha rake🤣🤣 Nan ne na ƙara fahimtar sauƙi hali irin na hafsat ɗin, lallai duniya da Abunda ke ciki ta basa gabanta, tana tausaya ma mijin nata, tace wannan kuɗin da zai kashe sun isa yayi hidima da baƙin shi har su tafi. ******************** Shigar shi kenan part ɗin nashi, a matuƙar gajiye yake, waya kawai yayi ma Nihal ta kawo mashi snacs yunwa yake ji, kai tsaye ɗakin shi ya faɗa ya shiga kwaɓe kayanshi, wanka yake son yi ko zaiji sauƙi gajiyar dake nuƙurƙusar shi, gashi part ɗin nashi yayi matuƙar dauɗa, rabon da ya samu kyakkyawa n gyara tin wanda Suhan ɗin tayi mashi. Bayan ya gama wankan ne, ya shirya cikin pajmas na maza, saboda sauƙin nauyin su, gashi yana so ya kwanta ya ɗan huta, sallama yaji ta baƙuwa murya daga cen falin nashi, a hankali ya miƙe gami da fita domin ganin wake sallama, kaman muryar mace yake iya jiyowa. Maree ce tsaye, hannun ta ɗauke da farar roba mai garai garai, kana iya hango Abunda ke ciki, a tsakiyar falin ya iske ta tsaye tana ƙare ma sashe nashi kallo, ita asali ma bata taɓa shigowa cikin shi ba, saidai kawai ta hango shi daga nesa, duk da a zahiri kasan zubin nashi dama zai yi kyau, saidai ya zarta yanda take tunani. Ƙamshin turare ne, ya alamta mata lallai akwai wani tsaye kusa da ita, ɗan zabura tayi kaɗan tana cewa "Yallaɓai barka da hutawa, gashi inji Aunty Nihal tace in kawo maka" ta faɗa tana miƙa mashi robar cikin ƴar rissinawa tana wani far-far da idanu, ko kallon ta baiyi ba, ya nuna mata stool dake gefen kujera ajiye, alamar ta ajiye bisa, gami da juyawa da niyyar komawa cikin ɗakin yana cewa "Ki turo mun Nihal ɗin" Da kallo ta bishi ta baya har ya shige ɗakin nashi, ajiyar zuciya ta sauke, dama haka Al'ameen ɗin yake? Lallai dole ne ta sake taku, wannan ai kalar nasu ne, ko ba zai aure ta ba, lallai dole ne ta ɗanɗana zumar shi, zata san yanda tayi ta jawo hankalin shi gareta, saidai ita kanta ta san da wuya, da wahala, domin a yanda ta ganshi ba zai yi wasa ba ko ya ɗauki wargi, ƙafafunta ta ja gami da barin sashe tana ta saƙa mugun nufi da mugu nƙuduri akan bawan Allah Al'ameen. Har ɗaki Nihal ɗin ta tadda shi, kwance yake ba bacci yake ba Amman idanun shi a kulle suke, ƙare mata kallo yayi daga sama har ƙasa, sannan ya shiga balbake ta da faɗan, ya sanya tayi mashi abu, ta sanya wata ƙazama cen ta kawo mashi Abunda zai ci, mamakin shi take yi, ai ita a sanin ta yana cin abun hannun ƴan aiki, tinda yana cin na Suhan da mama Maryamar. Katseta yayi daga tinanin da take yi, "dole ki amshi hukuncin, gobe in Allah ya kai mu ki tabbatas kin gyara mani sashe na tsab, kaman yanda kika ga Suhan nayi mashi, bana son ƙazanta, baƙi zanyi cikin satin nan zaki iya tafiya" Juyawa tayi tana kumbura baki, har ga Allah in har Yayan nasu na ƙasa yana takura masu, ya sanya sun dawo ƙasar kuma yana neman ya sanya su wahala? Aikin gyaran wannan sashen ai ba ƙaramar wahala bane, ita da ko toiket ɗinta bata iya wankewa, yanzu saidai ta sanya Maree tayi mata, duk da bawai ta gansu da tsaftar mareen ba kaman suhana, zuciyar ta na raya mata ta sanya Maree ta gyara mashi, wani sashe na zuciyar nan kwabar ta, tabbas zai iya ganewa ba ita tayi ba, inko hakan ta faru ta kaɗe har buzunta, ba zasu rabu ta daɗi ba, ɗan guntun murmushi tayi, mafita da ta samo, ai yace irin yanda Suhan keyi ko? To ba matsala, ai Suhan ɗin ce ma zata yi maka yaya sha kuruminka, tinda aikin nata kake so. Da haka har ta isa sashen nasu, tana labarta ma Saudat ɗin yanda sukayi da yayan nasu, murmushi kawai saudat ɗin tayi gami da cewa "gara ki sanya ta tayi shegiyar, kinga yanzu daga dawowar mu har ta janye Hafsy, ai wannan yarinya wallahi akwai mayya". (😝😝 kunji fa readers ashe sun damu hda hafsat ɗin🤔) ******************** Bacci yake son yi, saidai yunwa ta ishe shi, gashi bai jin zai iya cin abinda yarinya ta kawo mashi, miƙewa yayi a hankali ya isa kitchen ɗin da yake mallakin shi, kaman wata macen, fridge ya buɗe ya ɗauko lemo kwali da ceramic cups ya fito, kai tsaye bedroom ɗin ya koma gefen gado ya zauna, gami da tsiyaya lemon ya sha, kaman wanda aka yi ma dole. Wayar shi ce tayi tsuwwa, alamar saƙo ya shigo, share ta yayi ya cigaba da shan lemon shi har ya gama, gami da miƙewa ya maida kitchen, ya dawo daƙin gami da saisaita ƙarfin Ac ɗin dake aiki cikin ɗakin. Gadon nashi ya haye, tare da jan lallausan bargon nashi ya rufe ƙafafun nashi ruf, wayar shi ya jawo gami da maida ta sylent, har zai ajiye sai kuma ya lura da ɗan akwatin saƙo da yake cen sama wayar a maƙale. Cikin kasala ya buɗe, yayi mamakin ganin sunan ta ɓaro ɓaro a wayar, bai ƙara shan mamaki ba har saida ya karanta Abunda saƙon ya ƙunsa, karantawa yayi ya sake maimaitawa, ita ɗin ce kuwa? Zaune ya miƙe bisa gadon, gami da jan bayan shi ya jingina shi jikin lallausan tissue foam ɗin dake jikin wood ɗin gadon. Sake dai maimaitawa yayi, lallai ita ce ta turo idanun shi ba gizo suke yi mashi ba. Hannu ya sanya gami da ɗan yin typing a hankali ya maida mata reply, unlight ɗin wayar yayi, gami da tura ta ƙarƙashin fillow. Zamewa yayi ya kwanta idanun shi a lumshe, zuciyar shi na ta kai komon karanta saƙon nata, su kansu idanun nashi sun gaza dena nuno mashi hoton Rubutun, tiryan tiryan yake karanta shi cikin idanun shi, kaman yana kallon scream ɗin wayar ne, a hankali bacci mai nauyi ya kwashe shi. Niko da muke cen ɗakin mu mun bararraje muna ta fira da Hafsy, ko ba komai dai Naji sauƙin kaɗai ci yau, na samu aboki yar fira, tana ta bani labarin tafiyar su, ina ji daman nice ace yau na ganni a ƙasashe ƙetare, mu biyu ne cikin ɗaki, domin umma ta ta fice ƙofar ɗaki gami da shimfiɗa tabarma ta zauna tana yanke farce. Sabuwar waya ta ce ta ɗauki tsuwwa, alamar shigowar saƙo, hannu na sanya gmi da jawo wayar, na buɗa. Cikin ƙwalalo idanu nake kallon wayar, hakan ce ta jawo hankalin hafsat ta tashi zaune tana tambaya ta ko lafiya? "ina fa lafiya Hafsy?" na faɗa bayan na gama karanta Abunda ta ta tura da shi kuma wanda ya turo. "To menene a ciki Suhan? Naga ai godiya kawai nayi ba wani abu ba, menene na damuwa, shima ko kinji yace wani abu ne?" ta faɗa bayan ta amshi wayar ta karanta reply ɗin da yayo. "A'a Amman ni kin sa har na fara jin kunya, waɗannan kalama ai irin naku ne na masoya hafsat, kada fa ki sanya yayi tsammnin wani abu" na faɗa hankali na aɗan tashe, har ga Allah kunya duk tabi ta baibaye ni, kaman ina gaban shi, sai yanzu nayi na damar barin ta ta tura Abunda ta rubuta ba tare da na amsa na karanta ba. "kinga karki wani damu kanki Suhanan umma, ki kwantar da hankalin ki Yayan namu wayayye ne ba zai kawo ma ranshi komai ba akasin Abunda aka rubuta" Ta faɗa cikin son ƙarfafa man guiwa, Nidai lafewa nayi jikin bango ina sauke ƴar ƙaramar ajiyar zuciya, gami da ce mata "To Hafsat Allah ya sanya" ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~21~* *Ina ma ɗaukacin Al'ummar musulmi barka da shigowa sabuwar shekara a musulunci, Albarka dake ciki Allah ya sada mu da ita, sharri da tsautsayin da yake ciki, Allah yayi mana tsari dashi Albarkacin fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° _Assalamu Alaikum, Yaya ina yini, ya gida da aiki? Ya fama da jama'a? Ina fatan komai lafiya, na rubuto in maka godiya da abun arziƙi da alkhairi da kaman, bani da bakin godiya a gareka, irin kyakkyawar kulawa da kake bani, i do appreciate Yaya, Allah ya ƙara arziƙi da wadata_ Ya kai sau biyu kenan ina ƙara maimaita karanta saƙon da Hafsat ɗin ta rubuta ta tura mashi, ina hango rashin dacewar kalaman, idanun a kaman zasu faɗo ƙasa saboda yanda na ƙura ma scream ɗin idanu, kunya tana baibaye dani, gashi dai tini hafsat ɗin ta fice taje ta kwaso kayan ta, Amman duk kina nake yi wani iri, a hankali idanun a suka kai ƙasa kan nashi saƙon da ya maido tin bayan tura saƙon da mintoci kaɗan _OK ba damuwa, Ameen_ Iya abunda ya rubuta kenan, sai nake ƙara ganin rashin dacewar hakan, fata na dai ace baiyi mani wata fahimta daban da. Tare da Hafsat ɗin muka kwana a ɗakin mu, wanda saidai umma ta shimfiɗa tabarma gefe cen ƙasa tiles ta kwanta, ta bar mana katifar. Yau mun hutar da umman tawa, ni da hafsat muka yi komai muka kammala har abun kari, sannan muka yi wanke wanke a cen gefen ƙofar ɗakin namu, kallo ake ta binmu dashi sauran ma'aikatan wasu na zunɗen mu da baki, mu dai bamu damu ba, harkar gabanmu kawai mukeyi. Hafsat ɗin na kula dasu, shaye da mamaki ta kalle ni lokacin da muka gama wanka muka zauna zaman shafa, "Suhan wai dama haka ma'aikatan gidan nan suke yi maku ke da umma?" ta faɗa mamaki fal a fuskar ta. "Eh nace, ina mai basar da zancen, saboda umma ta bata so ake zancen su. Girgiza kai kawai tayi gami da cewa" Allah shi kyauta" daga haka itama ta ja bakin ta ta kulle lura da tayi Suhan bata son maganar tasu. Muna cikin shafar ne Naji waya ta tayi ƙara a hankali na jawo gami da dubawa, saƙon nihal ne take sanar dani wai inje in gyara ma yaya ameen ɗakin shi, in turo hafsat ta amsar mani makulli. Cikin tsantsar mamaki na kai kallo na kan umma ta, aiko ta ƙure ni da idanu alamar tana neman ƙarin bayani. Sanar da ita nayi saƙon, sannan na ƙara da cewa, umma ina ce an dakatar damu aikin gidan, me zai sanya ba zata sanya maree taje tayi mashi ba?" kuma umma........, shiiiit🤫 ta dakatar dani, gami da cewa" Suhan bana son Abunda zai kawo tashin hankali, Hafsat je ki amso makullin ki kawo mata, kije ki taya ta ku gyara mashi ɗakin, ai ba wani abu bane don kin gyara mashi, yaron da yake mana alkhairi ai ba zamu ji kyashin kyautata mashi ba" "Haka ne umma" cewar Hafsat da ta miƙe tana ficewa zuwa Amso makullin. Umman tawa ce ta maida kallon ta gareni, sadda kaina nayi ƙasa, ni fa har ga Allah bana son Abunda zai ke haɗa ni dashi, masalan ma yanzu da afnan ta rubuta mashi wannan text ɗin, umman ce ta katse man tinanin da nake yi gami da cewa "Suhan ki kula fa, kinga Hafsat ƴar'uwarsu ce ba zata ji daɗi ba idan taga kaman bama son kyautata masu, ita ba lallai ta fahimci komai ba, ki saki ranki, kije ki gyara mashi, yafi gaban nan a wajen mu, shine ya zame mana kaman uba yanzu, ni na san Alfarmar shi ce ko zaman da mukeyi a gidan nan" Jikina yayi sanyi ƙalau, lallai gaskiyar umma ta kuma, dole zan ajiye kunyar in gyara mashi ɗakin nashi, wannan ne kawai Abunda zanyi in faranta ranshi ko dan in biya kaɗan daga cikin Abunda yake yi mana. Shigowar Hafsat ce ta katse mana maganar da muke, miƙewa nayi gami da zira hijabina. Tare muka ɗunguma zuwa sashen Ya Ameen ɗin muna tafe muna firar mu gwanin sha'awa kaman wasu ƴan uwa ko ƙawaye. Santin sashen Hafsat ta shiga yi, lallai ya ameen ɗin daban yake, watau sashen ma ko datti baiyi ba sosai, ba don ma shi ɗin mai tsafta bane, kaman yanda sauran maza suke, ai da ba sai ma an tsaya ɓata lokacin gyaran ɗakin ba, komai tsaf yake a ajiye a muhalli shi, kaman Wancen gyaran da na taɓa yi mashi, da alama dai ya kula da mazaunin komai ne ya sanya yanzu yake kula wajen misplacement ɗinshi. Hafsat na bari ta gyara falon, yayin da ni kuma na shige bedroom na shiga gyara, hai bathroom duk saida na gyara, na kwal kwale komai tsaf, ko kafin in fito har ta gyaro har kitchen komai tsaf, room freshner na fesa, gami da sakin Ac a hankali a hankali. Jawo ɗakin muka yi, har yanzu Hafsat bata dena santi ba, ga dukkan alamu Ya ameen ɗin mutumenta ne, sai yaba kirki da halin kwarae nashi take yi, anan ne take faɗa man irin taimakon da yake yi masu cen gidan nasu, dama duka mutanen garin kankiya, duk mai buƙata shi yake nema kai tsaye, kuma baya gazawa wajen taimaka masu bil haƙƙi da gaskiya. ************* Tsaye yake tsakiyar ɗakin hannuwa shi duka biyu soke a aljihun farin yadin da yake jikin shi an yi mashi ɗinkin osimbanjo, yayi matuƙar kyau, masalan yau da ya kafa hular dara a bisa kanshi, saboda ja ce sai ta ƙara ƙawata fuskar tashi, ko ina na sashen yake bi a hankali, a hankali. Tabbas wannan gyaran ya san ba na Nihal bane. "Suhan" zuciyar shi ta raya mashi, Amman As How? Ya tambayi kanshi cikin zuciya, "Huh, any way" ya faɗa a fili, yana sauke ajiyar zuciya, gami da kaɗa kai a hankali ya nufi bedroom ɗin. Mamaki ya kama shi, kanshi ya kulle, a hankali ya isa ga gadon da yaji bedsheet yayi limui, zama yayi gefen gadon yana mai mamakin irin gyaran da yarinyar ta iya, kaman inji, Alwala yake son yi, hakan ce ta sanya shi miƙewa gami da isa toilet ɗin. Alwala ya ɗaura, ji yake kaman kada ya fita a toilet ɗin, ɗan ƙaramin showel ya ɗauko yana mai tsane fuskar shi hannuwa shi da suke lulluɓe da gashi luf luf dasu. Idanun shi ne suka kai kan wani abu dake cen gefe yade yana ta ɗaukar idanu. Hannu ya sanya gami da ɗauko wa, ɗan kunne ne mai matuƙar kyau da tsada, tsohon abun kunne ne, da ko wajen siyar dashi yake da daraja, mai ruwan gold, sai sheƙi yake yi, ɗan murmushi yayi na gefen baki, kallo ɗaya yayi mashi ya gane ba gold bane, saboda yana da katafaren shagon siyar da gold da changin kuɗaɗen ƙetare. "Nata ne" yaji wani ɓari na zuciyar shi yana sanar dashi, saidai tayaya zai bata ɗan kunnen ta? Fitowa yayi dashi a hannun shi riƙe yana mai jujjuya shi, a aljihun wandon shi ya saka shi, da niyyar idan ya fito ya haɗu da ita a harabar gidan ya bata ko ya tura mudi ya kai mata, sallar da yaji an tada ce ta sanya shi hanzari ficewa daga gidan baki ɗaya zuwa masallacin f Ban tashi gane ɗan kunnen baya kunne na ba, har saida naje cire wa zanyi wankan rana, sake laluba wa nayi, still dai baya kunnen, bayan na fito ne a wankan na dudduba ɗakin baya nan, sai lokacin na tambayi Hafsat da take zaune tana cin abinci, Abunda ke bani mamaki har kawo yanzu babu wanda ya damu da zaman hafsat ɗin sashen namu kaman yanda aka yi ma afnan lokacin da tazo. "Ban ganshi ba kuwa Suhan gsky, Amman tin lokacin da kika cire hijab ɗinki naga ba ɗan kunnen a kunnen ki, anya kuwa kin sanya shi kafin mu fita?" Hafsat ɗin ta bani amsa, ta ƙara she da jefo man tambaya, "Aikuwa tabbas na sanya shi a kunne na, Allah dai ya sanya ba cen sashen na yaddo shi ba, kinsan kuwa wannan ɗan kunnen ya daɗe, umma ta tace tin irin na da ɗin nan ne, itama gadon shi tayi. Shiyasa ma bana fidda shi a kunne na, sai in zanyi bacci kawai" na ƙara she ina mai dafe ƙirji alamar ƙirjina ya faɗi. Shigowar umma ce ta sanya na wayance tare da yima Hafsat alama da tayi shiru, aiko ta ja bakin ta ta tsuke, saidai da umman tawa ta kula zata gane alamun rashin gaskiya a tare damu. Tinani na shiga yi ta yanda zan bi in samu ɗan kunnen ya dawo gareni ba tare da umma ta kula ba, gashi an mayar ma Nihal ɗin da makullin, kenan ba damar in koma ba tare da kowa ya kula ba in ɗauka, kuma ko ba haka ba ma ina zullumi zuwa ya kasance yana sashen nashi. Hafsat ce take sanar dani in shirya zan raka ta siyayya anjima idan anyi sallar la'asar, da to na bita a zahiri, cen kau cikin zuciya ina ta laluben hanyar da zan bi abun kunne na umma ya dawo gareni. Daga masallaci bai dawo gidan ba wuce wa yayi wajen harkokin shi, ya manta da bai kulle ɗakin ba shaf, abu ne mai muhimmanci ya taso mashi. Ganin ana ta salla a masallacin gidan namu, ya sanya ni tinanin zuwa ɗakin nashi, da yanzu nake tunanin ma mallakin ɗakin baya ciki in ma har yana gidan to lallai yana masallaci. Fakaitar idanun kowa nayi, da hafsat muka shirya ko zata kula da umma kada ta gane bana nan, zata ɗauke hankalin ta. Cikin sa'a kuwa na tadda part ɗin a buɗe ɗan murɗawa nayi a hankali na tura na shiga ina ɗan waige waige. Fara dubawa nayi ko ina ban gan shi ba, dama na san bani ce nayi aikin falon ba, ya sanya kaɗan kaɗan na duba falon na wuce kai tsaye zuwa bedroom ɗin. Sai dai me duka ko ina na duba bangani ba, har toilet, bashi ba alamar shi, hankali na in yayi dubu ya tashi, Sam duk na firgice ko ganin kirki bana yi nice leƙa hada ƙarƙashin gado. Gadon na haye baki ɗaya, gami da yaye zanen gadon🤣🤣 duk cikin nema ne, ina tinanin ko ya faɗa ta bayan gadon, nan ma ban ganshi ba, jawo gadon na shiga yi, da yake gado ne irin mai tayoyin nan, aiko ba wahala na jawo shi, katifar na shiga ɗagawa cikin hanzari, gudu nake mai ɗakin ya dawo ya iske ni. Al'ameen da yake bakin ƙofa tsaye tin bayan shigar ta ɗakin nata ya shigo, da mamaki sama fuskar shi lokacin da ya jiyo motsi a ta bedroom ɗin nashi, a hankali ya shiga takawa har zuwa buɗe ƙofar. Da yake bata da ƙara ya sanya Sam bata ji ba, duk ta haɗa zufa sai aikin janyo gado take yi, ɗakin nan fa tayi mashi watsa watsa, hatta da bedsheet ɗin bisa side drower ta ɗora shi, filaluwan kuwa da katifar duk ta jingina su jikin wardroop ɗin tana ta faman leƙawa cen ƙasa gadon ko zata hango shi, da yake da zata gyara har gadon ta ɗaga ta sharo, sai tayi tinanin ko cen ya faɗa. Gyaran murya yayi a hankali, cak na ja na tsay, in ba kunne na bane yake man gizo, kaman gyaran muryar Yaya Al'ameen ɗin nake iya jiyowa. Kasa juyowa nayi, kurkusa nake jin shi, kaman ma ya shigo ɗakin, a slow na juyo, aiko idanuna suka faɗa cikin nashi, kasa ɗauke idanuna nayi akan shi, aiko kafe ni yayi da mayatattun idanun shi, wani irin kallo ya shiga bina dashi a hankali ya shiga takowa zuwa inda nake tsaye. Ja na shiga yi da baya ina yarfe hannu, na shiga uku kada fa ya ɗauka sata na shigo yi mashi, buɗe baki na shiga yi da niyyar kare kaina. Hannu ya ɗaga man alamar inyi shiru baya son jin komai, kuma har yanzu bai daina matsowa ta inda nake tsaye ba....... ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~22~* *Wannan Page ɗin sadaukar wa ne ga ɗaukacin WRITERS ɗin Golden Pen, Allah ya ƙara mana ɗauka ka, basira, da zaƙin hannu, Allah kuma ya bamu ikon rubuta Abunda zai amfani Al'umma baki ɗaya. AMEEN* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Ban dena ja da baya ba ina yarfe hannu, haka shima bai dena matsowa inda nake ba, har saida na dangane da bangon ɗakin, ba arziƙi na ja tsaya ina ta ƙwalalo idanuwa kaman uwar da yaranta suka ɓata. Daf dani ya ja ya tsaya, har ina iya shaƙo ƙamshi turaren da ke jikin shi, saurin sadda kaina ƙasa nayi, yanda ƙjrji na ke bugawa, har ina jin kaman zuciya ta zata tsago ƙirjina ta fito tsabar yanda take bugawa. Bai ce man ƙala ba, nima bance mashi ba, sai ma nake ganin dukkan abunda zan faɗa don kare kaina ba yarda zai yi ba, tinda tin farko ya nuna man baya buƙatar hakan. Hannun shi ya sanya a aljihu wandon nashi gami da ɗauko waren ɗan kunnen nawa da yake ta walwali cikin hasken farin ƙwan dake ɗakin yana ta sheƙi da walwali. Miƙo man yayi, kaman wadda ƙwai ya fashe mawa a ciki na sanya hannu gami da amsa, duk da yanda zuciya ta ke bugawa, hakan bai sanya murna da farin cikin da nake ciki sun ɓoyu ba daga fuska ta, murmushi na saki, har saida siririyar wushirya ta ta bayyana, fararen haƙora na da suke jere reras ya bi da kallo, lokaci guda yana mai ɗauke idanun shi gami da juyawa yana nufar ƙofar fita cikin salon takun tafiyar shi. Kaman ance ya tsaya, ya kuwa ja ya tsaya, gami da juyowa, Allah sarki, ta kuwa ƙure warin ɗan kunnen wanda yake cikin tafin hannun ta da idanu, ga dukkan alamu dai taji daɗin ganin abun kunnen, kuma ko babu komai ya ameen ya gane dalilin bincika mashi ɗaki da ya tadda ta take yi. "Sai ki gyara man ɗaki na tsaf, kaman yanda kika tadda shi" Abunda ya faɗa kenan gami da juyawa ya idasa ficewa zuwa falon. Da kallo na bishi, zuciya ta na raya man, wai in gyara mashi kaman yanda na tadda, kaman ba nice na gyara ɗin ba😠 Cikin sanɗa ma shiga bin shi a baya, bayan na maƙala ɗan kunnen nawa a mazaunin shi watau kunne na. Leƙawa nayi falon a hankali, hango shi nayi zaune bisa kujera mai cin mutum biyu, gaban shi da laptop yana ƙoƙarin kunna wa, ga dukkan alamu aiki zai yi cikin ta. Rufe ɗakin nayi, gami da murza mashi key, a hankali ya ɗago jin ƙarar sanya key a ƙofar, ɗan murmushi ya saki na gefen baki, yana girgiza kai bayan ya kauda idanun shi daga ƙofar ɗakin zuwa laptop ɗin. Nikau dalili na nayin hakan, ba zan juri in gyara mashi ɗaki harda gado ba, alhali yana cikin sashen kuma mu biyu da gani sai shi, ina ai ba zai yuwu ba. Gyaran da nayi ma yafi na farko wanda nayi, saboda wannan karon ɗakin ya samu canje canje da nayi, hatta gadon na canza mashi mazauni, da ba a saitin taga yake ba, gashi muna yanayi na zafi, wannan ce ta sanya na maida kan gadon saitin taga, yanda fresh air zata ringa shigowa, zai samu sauƙi kunna ac ɗin da yake yi, wanda kowa ya sani tana da illa ga lafiya ɗan adam. Ina gamawa, ban jira komai ba, na fito da niyyar ficewa, yanzun ma ban tanka mashi ba, shima bai ko ɗago ya kalle ni ba, duk da yaga gittawa ta, Amman ƴan maganar basa kusa, koma suna kusa me zai ce mata? Yarinyar da ƙiri ƙiri ya nuna bata yadda da shi ba a zahiri. Ina daf da ficewa na tsinkayi muryar shi yana cewa "Ki kira man Hafsat in kin fita" & an waiwayowa nayi ina cewa to gami da idasa ficewa gabaki ɗaya a part ɗin. Fita ta ne yayi daidai da fitowar maree daga babban sashen gidan, direct ɗakin Ya Ameen ɗin ta nufa, Nikau da idanu na shiga binta, wasu irin kaya ne ta sanya matsattsu, dinkin ya kama ta sosai, bayan nan kau an wawashe kusan rabi, haka ma gaban rigar, kai abun dai babu kyaun gani, ɗan gyale ne ta yafa wanda dashi gara babu, takalman ta masu tsinci ne, wannan tasanya duk takon da tayi sai ya bada sauti "ƙwas" Itama bata yi sanya ba ta bini da kallo, mamaki fal a cikin ranta, me naje yowa sashen Yayan ne? Gashi kuma ni kaɗai ta gani, wani wulaƙantaccen kallo ta shiga jefo man, tanayi tana tauna chewin gum tana ƙas ƙas dashi tana farfara idanu tana wata yatsina, ni wallahi sai ma ta bani dariya. Wucewa nayi ina mai waiwaye ta, lallai kuwa ɗakin ta ke da niyyar shiga, Amman taja ta tsaya tana ƙara gyara zaman riga da skirt ɗin a jikin ta, ikon Allah, yau ina kallon abu, to me zata je yowa sashen nashi a haka? Har ga Allah dai na san duk da ba'a shedar ɗan mutun, na san shi ya Ameen ɗin bai da wannan ɗabi'ar, kuma ma dai na san ko neman matan zai yi, ba zai tsaya ma wannan ballagazar ba, wanda ko jirin kirki da kyaun kirki bata da. Ban aune ba naga har na isa ɗakin namu, sallama nayi na shiga, naki yi sa'a umman tawa bata nan ta fita, Hafsat kawai na tadda a zaune tana ta faman yin waya da wanda zata aura, murmushi tayi gami da cewa "Laa gata nan ma muna maganar ta" miƙoman wayar tayi tana faɗin "gata ku gaisa ma" Amsa nayi ina mai ɗan harararta cikin wasa, alamar ban shirya ba haka kawai ta dunguno man wayar tana dariya shaƙiyyanci. Ba laifi mun gaisa cikin raha, harda ɗan wasa haka, yana tambaya ta "ya shirye shirye biki, tace yau zaku fara ko?" da eah na bishi don bansan ta kan zancen ba, muka yi sallama yake faɗa man ya kusa shigowa ƙasar zai zo mu ƙara tattauna wa. Itama ɗin sallama tayi dashi, bayan na miƙa mata, ta ƙagara taji ina na samo ɗan kunnen da ta hanga a kunne na bayan na cire hijab ɗin dake wuya na. Aikau na kwashe komai na faɗa mata, na ƙara she da faɗa mata saƙon na yayan namu. Me ko zata yi in ba dariya ba, nan ta shiga zaulaya ta, ta miƙe tana cewa bari inje inji kiran da yayan namu yake yi mani, in kaji kiran shi ai samu ne wallahi, kiyi maza ki shirya lokacin fitar tamu ya ƙarato. Sallama tayi cikin shaƙaƙƙiyar murya, ga dukkan alamu ba ƙaramin ƙoƙari tayi ba wajen siranta muryar tata, bai ko ɗago ya kalle ta ba, shi duk a zaton shi hafsat ce, gashi kuma yaga ana nufo inda yake zaune ba tare da ɗar ko wani shayi ba, tin daga ƙafafun nata yake bi da kallo, sun kuwa sha mai sunyi da bare da bare abun su🤣🤣 sai sheƙi suke yi cikin man da ta shafa. Aiko cikin hanzari ya ɗago yana bin sauran jikin nata da kallo, har zuwa kan fuskar ta, runtse idanu yayi gami da juyar da kanshi, ko babu komai dai yayi mugun gani, domin kuwa kusan rabin nonuwan ta a waje suke, show me your breast kenan🤔 "Keeee" ya miƙe a fusace yana mai daka mata tsawa, sannan ya ɗora da faɗin "me ya kawo ki nan? Wani abu kike buƙata? Ko wani ne ya kira ki? Ya faɗa cikin fushi da matuƙar ɓacin rai. Rau-rau da idanu tayi alamar tausayi, wanda hakan da tayi ne ya ƙara ƙular dashi ma, sannan ta shiga faɗin" Suhan ce ta ce inzo wai kana nema na" ta faɗa cikin yanko ƙarya tana mai lailaya mashi. "Get out from here" ya faɗa yana nuna mata ƙofar fita, ba ke nace ta kira mani ba, Hafsat nace, ke me zan maki in nace ta kira mani ke? Ko ni kike ma aiki ne?" ya faɗa yana mai jefo mata tambaya kaman zai make ta. Girgiza mashi kai ta shiga yi, har ga Allah jikin ta yayi sanyi, domin ko kafin tazo nan saida ta shisshirya, hatta wankan da tayi da ruwan magani tayi shi, tayi matse matse da dama, domin tana tinanin Al'ameen ɗin kanwan lasa ne, da har zata jawo hankali shi ta ruwan sanyi haka. "A'a yaya, kayi haƙuri" ta faɗa kaman wata baiwar Allah, sannan ta juya tana wata irin karairaya har zuwa ficewa ta a ɗakin. Da kallo ya raka ta yana mai jan wani irin tsoki, baya son wulaƙanta mutum masalan ma wanda yake ƙarƙashin shi, Amman wannan dole ce ta sanya, in banda tana sakarya ma ya za'ayi ta yi irin wannan shigar sannan tazo gaban shi tana karairaya kaman zata faɗo mashi? Sallamar Hafsat ɗin ce ta katse mashi dogon tinanin da ya shiga, zama yayi yana mai amsawa a hankali, rufe laptop ɗin yayi yana mai kurɓar ruwan tatattun ƴaƴan itatuwa masu sanyi da suke gaban shi yayi. Ɗan nesa da shi kaɗan ta samu ta zauna tana mai cewa "yaya gani Suhan tace kana nema na" Da idanu ya bita yana mai ƙirƙiro murmushi dole cikin son kauda ɓacin rai da yake ciki, kenan waccen Yarinyar da ta fita yanzu ƙarya take ma Suhan da tace ita ce tace tazo yana neman ta? Sake kauda tinanin yayi cikin ranshi, yana mai gyara zama ya fuskanci hafsat ɗin sosai, tambayar ta ya shiga yi shirye shirye da sauran abubuwan da take buƙata wanda bata idasa ba, yana gargaɗar ta da kiran nasu gidan domin neman wani abu, duk Abunda take so yana iya yi mata, ta tunkare shi kai tsaye kawai. Da yake akwai fahimta sosai tsakanin su da ƴar shaƙuwa, yana son hafsat ɗin, ko don sanyin halin ta da kuma girmama na gaba da ita, ba kaman sangartattun ƙannen nashi ba, ta shiga zayyane mashi dukkan abubuwan da take buƙata, take yayi mata trnsfer na kuɗaɗen duk da zasu isheta ta kammala hidima ta har ma tayi saura, sannan ya shiga sanar da ita hukuncin Alhaji na cewa ba zata koma gida ba, har sai an ɗaura auren nata, suma duka sauran mutanen nan ba da daɗewa ba zasu tarkato su taho Abuja acen za'ayi duk wasu shirye shirye da hidima bikin, hatta da su kaka zuwaira duk nan za'a taho dasu domin suma su ɗan shaƙata, zaman wuri ɗayan ya isa hakanan. Ƴar fira sukayi kaɗan kaɗan, abun ka da wanda bai damu da magana ba, hakan ce ta sanya ta yi mashi godiya gami da miƙewa ta fice harda tukuicin ja mashi ƙofar, wani ɓari na zuciyar ta na tambayar ta me maree taje yi sashen yayan nasu? ************* Maree da take zaune ɗakin mama talatun da ta kasance ita ce mahaifiya ta, Amman ba kowa ya sani ba, ƙwalla take share wa, cikin ƙunan rai ta shiga zayyane mata Abunda ya Ameen ɗin yayi mata, aiko ashar ta lailayo ta zunduma tana faɗar baƙaken maganganu, "kika ce har Suhan kin gani a sashen nashi?" ta jefa mata tambaya, tana daga tsaye riƙe da ƙugu. "Eah mama, na ganta lokacin da ta fito, har ma harara ta ta dinga yi.... " ta faɗa cikin ƙunar zuciya, uwar tata ce ta katse mata maganar da take yi "ke dallah ja cen ki ba mutane wuri, ki tabbata duk yanda zakiyi kiyi, ki jawo hankalin yaron nan a gareku, ki tsaya kallon ruwa kwaɗo yayi maki ƙafafu, ki dai san a nan gidan babu wanda ya san nice na haife ki, ko shiga hidimarki kika ga bana yi, bana so kwabar mu tayi ruwa, Amma billahillazee duk yanda zamuyi sai mun mallaki ƙaramin yaron nan attajiri, sai mun mulka da juya gidan nan fiyee ma da yanda Kubra keyi" ta faɗa tana huci da hurtai. "Kyalesu, na san abun yi, ba dai ke ya wulaƙanta ba,? Zai dawo ne yana neman soyayya ki da roƙon ki, a yayin da zamu juya shi kaman waina a cikin tanada, goge hawayen ki, ki koma bakin aikin ki kada su dawo su tadda baki kammala Abunda suka sanya ki ba, ina so ne ki shiga jiki su, kaman yanda jini yake gudana a jikin nasu, kuma ki tabbatas duk magungunan da na baki kina zuba masu a abincin da suke ci, ki kula fa, kinsan kukun nan basu da mutumci, kinsan ƴan kudun nan, shegu ranakun banza" ta ƙara she tana gyara zaman za in ta da har ya warware tsabar bala'i gab yake da faɗuwa, har ɗan kaman ta kana iya hange. Da too mareen ta bita, tana mai tashi ta fice daga ɗakin, ko da zata gifta ta inda ɗakin nasu Suhan yake saida ta wurga mashi harara kaman Suhan ɗin ce a ciki. ******* Kammala shiryawa tawa, yayi daidai da shigowar Hafsat ɗin ɗakin namu tana mai cike da farin ciki, rungume ni tayi tana faɗin "kin gani ko Suhan, kingani dama nace maki kiran yayan Alkhairi ne a gare mu" kuɗin soyayya ya bamu wadda zamuyi har sai mun gaji da kashewa" cikin murmushi na zame jikina daga nata, domin tana niyyar kadan ne, na bita da kallo ina cewa "aiko kin gode wallahi hafsat, don Allah to karki kira gida a ƙara maki wasu tinda waɗannan sun isheki, ko shi Abdul ɗin (sunan saurayi hafsat ɗin wanda zata aura) kar ki amshi masu yawa a wurin shi." da to ta bini, tana mai ƙara gyara fuskar ta, sallama muka yi ma umma da take zaune tsakar gida tana sauraren radio sallama, addu'a tayi mana da sake faɗa mana kar mu kai magribawaje mu dawo da wuri. Ranshi har yanzu a matuƙar ɓace yake, me Yarinyar ke nufi dashi ne? A cikin gidan nan ma zata dinga yin irin wannan shigar tana matsayi mai aikin gidan da yake wadace da ƴan aiki maza, kama daga masu gadi, drebobin da masu gyaran lambu da ba flowers ruwa da share gida?, miƙewa yayi gami da shigewa ciki domin canja kaya, so yake ya fita ko zai shaƙo iskar da zata sanyaya mashi rai. Bai ko kula da yanda ta canja ma ɗakin tsari ba, har ya canja kayan ya fice, da yake wardrooo ɗin ta cikin bango ce, mai azabar kyau da ƙayatuwa. Keys kawai ya zara, gami da kwasar wayoyin shi na hannu, ya fice daga sashen nashi, gami da murza mashi makulli ya rufe😅 Tin daga nesa ya hango su, ya sheda hafsat, Amman gudar ce bai gane ba, har saida ya matsa daf dasu, inda suke tsaye suna jiran driver yazo ya kaisu, saboda yau ba ita kaɗai bace, ita da hafsat ce ya sanya ta yadda zata shiga motar gidan, shima saida suka kai ruwa rana sannan. Ƙala bai ce masu ba har ya isa ga motar tashi da take gefe tana ta ɗaukar idanu, horn ya danna masu, hafsat ɗin ce ta kula dasu yake kira, ƙara sawa tayi wurin shi, tambayar ta ya shiga yi tsayuwar me suke wurin, sheda mashi tayi driver suke jira ya ƙara so, yace ya kusa isowa gidan. (da yake muɗi sun fita da su Hajiya Kubra da amare) "Ku shiga in ajiye ku, idan ya ƙaraso sai yaje ya ɗauko ku in kun gama" Abunda ya faɗa kenan yana mai bin agogon hannun nashi da kallo don sanin ko ƙarfe nawa. Juyawa tayi gami da ya fito ni da hannu, a hankali na shiga taka wa gami da ƙara sawa inda take tsaye bakin motar Hannu ta sanya gami da buɗe man gidan baya, "ki shiga, yaya ne yace zai kai mu, in mun gama mun kira driver ɗin ya maidamu" Ba a son raina ba na shiga, "ya salam" na furta cikin raina, sanyi da ƙamshi motar sun tafi da imani na, ɗan lumshe idanu nayi, lokacin da Naji motar ta daidaita a saman kwalta. Ta baya nake satar kallon shi, tuƙin ma a natse yake yin shi, yayi kyau cikin riga marar nauyi kamfanin Adidas da baƙin wandon jeans a jikin shi, kai shi duk yadda ya sanya kaya ma kyau suke yi mashi. Duk yanda naso in hana idanu na kaiwa gare shi, basa jin magana, saidai in samu kaina dumu dumu ina mai ƙare mashi kallo tas, har baƙi siɗik ɗin kwantaccen gashin kanshi. Wani irin sanyin ni'ima ne gami da gaurayayyen ƙamshi turaren shi ne yake busowa, hakan ce ta sanya ni lafewa daga baya, ina tsura ma kyakkyawar fuskar shi idanu ta cikin madubi, tunanin nika ne masu yawa suke kai komo a zuciya ta, inda na taɓa faɗa mashi a ƙirji, inda na taɓa cakumo shi da umma ta bata lafiya, da kuma a makaranta kwanaki kaɗan da suka wuce. Ban aune ba na tsinkayo muryar shi daga cen gaba yana cewa " *kallon fa?*" Ɗan duburcewa nayi, ina mai faɗa a zuciya ta cewa na shiga uku ni Hauwa'u, Ya ameen ya kama ni dumu dumu ina kallon shi, Sam bansan idanuna na kan madubi ba, ban Kuma kawo ma raina cewa zai iya hango ni ba ta baya, da yake motar na da ɗan duhu haka. Tsaf ya tsare ni da idanu ta cikin madubi yana ɗan cije bakin shi da haƙoran shi kaɗannkaɗan. Hafsat ce da hankalin ta ya kai kanmu, kuma taji abinda ya tambaya, ɗan juyowa tayi kaɗan tana waywaye na, hakan ce ta sanya ni ɗauke kaina na maida idanuwa na kan glass ɗin da yake gefe na, gami da ƙure titi da idanu, ba tare da ko alamun bayar da amsa ba. *indai kunya ce, tau nidai yau na riga na shata ni Suhan* _Share_ _like_ _Comment_ ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page~23~* *Page ɗinki ne maman sadeeq, kiyi yanda kike so dashi, asha karatu lfy* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Fuska ta a ɗaure, ko da muka haɗa idanu da hafsat, harara na sakar mata, ita kau juyawa tayi tana ƙunshe dariya a ciki, harda rufe baki, saboda ta fahimci Abunda duk ya faru. Har yayi parking ƙofar katafaren supermarket ɗin ban ƙara yadda mun haɗa idanu dashi ba, ina ƙoƙarin sauka ne idanun A suka kai kanshi ta madubi, ya ƙureni da kallo ko motsi baya yi, hannun shi duka akan stiyarin motar ya jingina jikin shi da marfin motar ta ɓangaren shi, yayi kyau kaman saraki, saurin ficewa nayi har ina harɗewa da zumbulelen hijab ɗina Allah ma yaso ban kifa ba. Lumshe idanu yayi, ya sake buɗewa lokacin da yaji duk sun fice hafsat na jero mashi godiya, da kallo ya raka su, a zahiri gaskiya ba ita yake kallo ba, tinanin abinda maree tayi mashi kawai yake yi, ita kau mutuniyar tawa sai ta ɗauka still ita yake kallo. Jan motar yayi a matuƙar fusace ya bar wajen, dole ne ya ɗauki mataki, ba zai lamunci ƙaramin iskanci a cikin gidan nasu ba. Mun sha soyayya, abinda ke bani mamaki yanda hafsat ta ragargazo mani siyayya sosai da sosai, kayan fitar biki ne masu tsada ta siya man, harda kayan Fulani da za'a sanya ranar tradutional day da za'a gudanar a lambun gidan nasu. Kwanan mu biyar muna fita siyayya, har ɗinkunan mu duk mun amso, saboda kuɗin shap-Shap Hafsat ɗin ta biya aka yi mana. Gyaran jiki Hafsat ɗin ta tursasani saida na biye mata aka yi tayi mana tare, wanda a zahirin gaskiya ma gyaran jikin yafi karɓa ta tinda na fita haske sosai. Ban sake jin ɗuriyar Ya Ameen ba, haka suma mutanen cikin gida bama jin ɗuriyar su, hidimar biki ta sanya su gaba, ko ta kanmu ma basa bi. Tini gida ya ɗauki harama, dukkan kayan dake cikin gidan nan saida aka fidda shi aka cenza wasu, hatta fentin gidan baki ɗaya saida aka cenza. Kullum da kalar baƙin da za'ayi a cikin gidan, muma ta ɓangaren mu ba baya ba, muna shirya daidai ƙarfin mu. Gida ya fara tara jama'a, wanda hatta mutanen kankiya sun iso, da family ɗin Alhaji awwalun, da aka buɗe ma babban sashe guda, dole hafsat ta tattara ta koma sashen da aka basu, inda aka mallaka mata babban ɗaki guda ɗaya da komai da komai a ciki. Ba yanda bata yi ba don inzo muje tare nace aa, umma ta ma da ta tambaya cewa tayi a'a, indai tana buƙatar wani abu daga safiya zuwa dare tazo ina nan Amman banda kwana,dole ta haƙura ba don taso ba, muka cigaba dayin shirye shirye yanda ya kamata, daga safiya har dare kaman yanda umman tawa ta faɗa muna tare, domin nice na zame mata babbar ƙawa kaman yanda ta faɗa. Su kau sauran amaren ma ba ganin su mukeyi ba, suna sashen da aka buɗe masu su da ƙawayen su kawai, Shiyasa in ficewa zasu yi har sun fita ta ƙaramar ƙofa ma babu wanda ya gansu.to dama dai mu bamu damu da al'amarin su ba, babu abinda zai haɗa sai tradutional day da Hafsat ɗin tace shi kaɗai zata yi. Hajiya Kubra tare da manyan aminan ta da ƙawayenta sai shige da afice akeyi, bikin fa na manya ne, mata kake gani manya jugunannu daga kowanne ɓangare suna fitowa, zo Kaga ruwan ƙaryar gudunmuwa, har saida ta wakilta ƙawata Hajiya Laila ta dinga karɓa domin ita ta gaji da hayaniya. Ana saura kwana bakwai biki su Aunty Feena da Afnan suka iso, karkaso kaga murna, ba ma kaman yanda suka tadda gidan ya cika da ta kowanne fanni ƴan uwa da abokan arziƙi, dangin Hajiya lailan ma sun iso suna babban sashen ta aka sauke su, yo ai su nata ne ko, su kuwa ƴan kankiya ɓangaren kusa da na Hajiya zainab maman Hafsat aka basu, to dama dai sun fi shiri da jituwa da ita, saboda tafi Kubra sauƙi da girmama dangin mazajen nasu. Afnan ce ta rungume ni ta baya, tana "oyoyo Aunty na, wow kinga yanda kika yi kyau kika haska kuwa? Allah kaman ba ke ba, minene Sirrin?" ta faɗa tana kashe man ido ɗaya. Murmushi nayi na sanya hannu na jawo ta gabana, "Afnan yaushe zaki bar ce an auntyn nan? So kike a jiki ki jaman?" na ƙara she alamar tambaya. Murmushi tayi, sannan ta buɗe baki da niyyar magana, dakatar da ita nayi ina mai cewa "to yanzu dai ya hanya? Ya shirye shiryen biki?" "Shirye shirye ai sai ku, ko aunty Hafsat?" ta maida tambayar tata akan hafsat, bata jira cewar hafsat ɗin a ta zauna tana mai cewa "tau yanzu dai minene shirin ku? Ya ban ganku a sashen amare ba ku? Shiru muka yi mata ni da hafsat ɗin, ɗan nazarinmu tayi na tsawon second biyu, sannan ta ɗaga hannu alamar dakata-dakata " Bama wannan ba, gara da kukayi zaman ku nan ɗakin umma ta, (Tana nufin umman suhan) ku ƙyale su cen da ƙawayensu ƴan fafa, mu cigaba da hidimarmu anan kawai mu share su". Dukkanmu murmushi muka yi, umma ta dai tana gefe zaune, ƙala bata ce mana ba, da yake mun samu sauƙi tsangwama yanzu hidimar biki tasha kan kowa, sai ba'a damu da shigar afnan ɗin cikin mu ba mu kayi ta shirye shiryenmu daidai gwargwado. Afnan ɗin fa ta shige cikin mu, kaman ma ba ƴar gidan ba, ko wajen yayyen nata bata zuwa, komai mun kammala, hatta da kayan da amarya zata sanya tsawon kwana biyar da za' a fara hidimar bikin zuwa bayan kai ta gidan mijin nata, muma haka ta taya mu muka shirya su mu duka muka adana abunmu. Yau ne za'a kawo lefe, hakan ce ta sanya muka shirya zuwa wurin ƙunshi a yau, tau suma ɗin sauran amaren dai duk yau za'ayi masu, Amman su har gida za'a zo ayi masu, saboda a gobe ne za'a fara program ɗinsu tinda mu tradutional day ne kawai, saura kwana biyu biki ne za'ayi shi shi. Afnan ce ta jamu zuwa wani shago inda aka ƙware da zanen lalle, ɓaki da ja, aka yi ma amarya, masha Allah, gaskiya yayi kyau sai ɗaukar idanu yake, duk da hafsat ɗin ba fara bace, Amman kunsan amarya yanda take, kuma ƙunshi yayi daidai da kalar fatar jikin ta, sai aka yi ma afnan, ita fara ce tas, su tace baƙi take so duka, haka aka yi mata, masha Allah kaman ka sace ƙafar da hannuwan nan. Nice ƙarshe, hakan ce ta sanya nace ni ja nake so duka, ɗan kaɗan, cikin hannuwa da yatsu sai tafin ƙafa ya ɗan hau kaɗan, haka aka yi man shi, sunce yayi kyau sosai, nima na san yayi kyau ɗin, dama ba don wani nayi ba don kaina nayi. Haka muka dawo da yamma lis, mun tadda an kawo lefe, a bakin umma ta muka ji, wanka muka yi muka sake kaya sai ɓangaren maman Hafsat, mun gaishe ta da duk wanda ke sashen, da yake sashen ba hayaniya, bikin da za'ayi ba a gidan ta ba, Shiyasa batayo gayya ba sosai, duk da itama ƴaƴa biyu zata auras da Hafsat ɗin da yayan ta. Sashen su kaka zuwaira muka shiga, abun ka da wasu daga ƙauye suka zo, an fa yi ma sashen diƙi diƙi, abun ka da farin tiles da fenti sai dattin ya fito fili, tin kaka zuwa Iran na magana har ta haƙura ta gaji, shima saida Giggo Aisha, yayar su Alhaji mustaphan tayi mata magana, tace ta ƙyale su don Allah duka kwana nawa za'ayi kowa ya tattara ya koma? Jawo Hafsat ɗin kaka zuwaira tayi, tana mai cewa "Zonan ja'ira, ina kika samo miji malaniya haka? (Wai millioneire take sabon cewa🤣), kin kau ga kayan da aka kawo maki? Akwati ashirin da huɗu? Ko su iyayen kankambar ba'a kawo masu haka ba, sunkuyar da kai hafsat ɗin tayi tana mai ɗan murmushi, Giggo Fatima ce ta ce "Haba Hajiya, ya isa hakanan ki ƙyale ta, kowa ba da goshin shi yake zuwa ba?" Duk da haka saida ta danƙwashe kanta tana ƙara zaulayar ta, ita kuwa da taga haka sai ta sulale ta kwanta bisa cinyar tsohuwar tana mai cewa bari inyi hawan ƙarshe 🤭 Dukansu dariya suka sanya suna cewa ta ɗaga masu tsohuwa kar ta karya masu ita, da yake amarya farin jini gareta, sai kowa ya dawo nan aka yi ta fira da ita, to ko babu komai ai hakan yafi, dama su saran sarakan basu ko leƙa sashen ba tin bayan da suka je suka gaida su ranar da suka zo, saɓaninnhafsat ɗin da kullum sai taje, ko in raka ta ko ta tafi ita kaɗai. Nayi nisa cikin gyaran sashen da ya kusa komawa kwalta tsabar datti, cen an zubda tea, cen abinci, cen an jiƙa bredi an zubda, gida ne ba wanda ƙuda ya saba zama ba, Amman zuwan ƴan kankiya saida sashen ya koma matattarar zaman ƙudan, duk da wasu na kiyaye wa, Amman wasu kau sai a hankali, yo an kwaso ƴaƴa an taho dasu cin duniya 🤣 Saida na gyara ko ina tsaf, harda falon da suke zaune saida suka ɗaga na gyara, sannan muka bar sashen zuwa namu domin magariba ta kawo jiki. Goggo Aisha ce ta kalli Goggo Fatima tana cewa "wai ni kau Fatima, wannan ba yarinya nan bace da Muhammadu na wajen Mustapha yace yana so ba?" "ita ce kuwa, nima da farko ban gane ta b, sai da uwar tata ta shigo gaidamu ne sannan na gane ta, ai kinsan ita ce ta rako ta" kaka zuwaira da take zaune gefen su bata sanya masu baki ba, sai yanzu ta tanka tana mai cewa "haba, ni kau da har zan tambaya ina Hafsatu ta samo wannan yarinya haka mai natsuwa da son aiki, yarinya tana da tarbiyya wallahi, ku duba duk lokacin da tazo sashen nan sai tayi mana aiki, ko gazawa batayi" Goggo Aisha ce ta shiga jinjina kai alamar gaskiya ne zancen mahaifiya tasu sannan ta shiga cewa "aiko in haka ne, ni banga abun ƙi ba a tattare da yarinyar, yarinya kyakkyawa da ita masha Allah, ga hankali da natsuwa, ai irin ta ce kowa ke burin samu a matsayi suruka, in banda hauka irin na kubura" "kema kinnfaɗa Yaya, Allah shi kyauta yasa ya ta gane gaskiya" Ameen kowa ya amsa. nan suka bar zancen suka kama wata tashar kuma, yayin da cikin zuciyar hajiya zuwaira ta yaba da natsuwar Suhan ɗin sannan ta ƙhdurce abubuwa da dama akan lamarin. Washegari da wuri muka farka, domin yau ne ƙawayen Hafsat ɗin zasu fara zuwa, duk da ba wani event zata yi ba, Amman sunyi mata kara sosai sun zo da yawa kuwa. Bamu san wanene ya tsegunta zaman hafsat ɗin sashen su ba, ba cikin amaren ba, sai ga mama Talatu an aiko ta, cewa Hafsat ta koma sashen da aka ware ma amaren, ita da gayyar ta, ba don son ranta ba ta tattara ta koma cen, aka ware mata ɗaki ɗaya babba dazai isheta har zuwa ɗaurin auren nata. Komawa sukayi ita da Afnan roƙon ummata akan ta barni in tafi tare dasu, da farko ta hana, sai kuma ta barni tare da shara ɗin duk Abunda za'ayi mani kar in kula, in yi haƙuri in share, da haka muka ɗunguma zuwa sashen amaren Amman a ɗakin u nake komawa inyi wanka in shirya. Umma ta ta kan leƙa sashen Mama zainab ɗin, kama mata wasu ƴan ayyukan, da haka har suka saba, in ma bata ga tazo ba ta kan aika a kira ta. Mun shiga cikin hidimar bikin dumu dumu Dukkanmu, albarkacin Hafsat da mahaifiyar ta, Abunda banyi zaton umman tawa zata lamunta ba, sai gashi ita dakanta ke ƙara gaya man irin halin kirki da karamci irin ma Hajiya zainab ɗin, da gani dai Hafsat ɗin ita ta biyo. Abunda na kula dashi shine, duk lokacin da zan gifta ko zan wuce ta falon shine shewa da ƴar guɗa da ake Sanyawa haka ana zunɗe na sai kuma ayi tafi a kashe, manyan yara ne masu ji da kansu, ban ma yi tinanin zasu tsaya kula ko zunɗena ba, tinda Nidai bansan me suke mawa ba, bansan me na aikata masu ba da har suke yi man haka. Share su nake yi kaman yanda umman tawa ta umurceni. "Hahaha, Wannan? Yo me haɗaɗɗen saurayi kaman wannan zai ci da wannan? Haba Nihla, kisan me kike faɗa mana, dubeta fa, kaman alhaja, har koɗa take yi, ni anya ma ba sadaukar yalla bace, irin waɗannan masu muna bara muna karuwanci bace? Ni wallahi na tsani yarinyar bansan dalilin da ya sanya Dad ya sanya suka dawo nan ba, kishin ta nake ji sosai har cikin raina, bansan dalilin shi na son auren ta ba, bayan gani." Ɗaya daga cikin ƙawayen su Saudat ɗince ke cewa haka, ban ko kalli inda suke ba nayi saurin wucewa, fatana dai ace ba dani suke ba, yo me ma zai sa inyi tinanin dani suke? Bayan banji sun kama suna ba, kuma ni na san babu wanda yace zai aure ni balle har wata tayi kishina a banza. Share zancen nayi, ina mai shige wa ɗakin amaren da suke ta shirye shiryen zuwa bridal shiwer ɗin da aka shirya za'a gabatar a yau, duk da ita amaryar tasu tana kwance, tace ba da ita ba, bai hana su cewa wallahi sai sun je ba sun kashe ƙwarƙwatar idanun su. Harda Afnan aka shirya sunyi shiga ta jar riga da straigh skirt Black, sai hula itama baƙa an ɗaura wani abu mai kyalkyali a hannu shima ja, sunyi kyau ba laifi, Amman a haka wai ƴaƴan musulmai zasu fita, Allah shi kyauta. Motoci aka kawo aka shiga ɗaukar amaren, dama even ne na mata, wani ƙerarren gida dake ta bayan Layin su aka shirya ma abun, shima ya sha decoration Red and Black, sai amaren da sukayi complet White, ba ƙaramin daɗi suka ji ba da hafsat tace bata yin even ɗin, dama wai suna gudun a cika masu wuri da ƴan ƙauye, Shiyasa suka bata getpass guda biyar kacal. To ita cewa ma tayi bata zuwa, sai ƙawayenta ne su huɗu suka shirya aka tafi tare dasu, suka saje cikin ƙawayen amaren, saura getpass guda kuwa ajiye shi aka yi baya da wani amfani, gidan fa yayi tsit, duk masu rawar kan an da ƴan ƙaryar na sun kwashe sun tafi, sai Naji dama gidan ya cigaba da zama a haka Ohh🤔🤔 su suhan da ƙarfin hali ake. Washegari sukayi arebian night, hall aka kama mai kyau da tsada, acen aka gabatar da shirin, wannan haɗe yake maza da mata, sunyi yadda suke so, da yake ba ya ameen babu mai kwatsa masu, abie ƙanen su ne y bai isa yace gyadda za'ayi ba duk da Aunt Feena na wajen, to itama bata ce ga yadda za'ayi ba, tinda Rayuwar turawa ta shiga kansu da yawa. Mothers eve, aka shirya washegari, zo Kaga yadda aka ƙawata gidan da yake a haraba gidan za'ayi, anyi ɓarin kuɗi kaman da gayya, makaɗa da mawaƙa sun sha daloli, dole ne asan da bikin ƴaƴan Hajiya kubra Dambulan akeyi, rawa dai da juyi sunyi shi, manyan mata ko kunya basa ji haka suke juyi suna watsi da kuɗi, babu Abunda kake hangowa illa, gwala-gwalai, da ɗanyun lesussuka malam, masu video coverage nayi, masu hotuna nayi. Duk abun nan da akeyi Ya ameen ɗin na tsaye ta window ɗin falon nashi yana hango su, hannuwan shi duka soke cikin aljihu wandon bugaggiyar shadda tashi, fuskar nan tashi murtuk, bai san me ke damun mahaifiyar tashi ba, bidi'a da alfahari kawai ne acikin ranta, in banda haka duk wannan watsi da kuɗin da akeyi duk na menene? Wa za'a burge? Wa ke bai san suna da kuɗin ba? To indai haka ne shi a ganin shi wannan almubazzaranci ne. Makullan motar shi ya zara gami da ficewa ta ƙofar baya, jin kiɗan dake tashi a cikin gidan zai fasa mashi dodon kunne duk kuwa da girma da faɗin gidan. Zaune nake kunnuwa na toshe da headphone, ƙira'ar Sheik abdurrahman sudais ce nake saurare. Ina jin daɗin muryar bawan Allahn, a hankali nake bi shi cikin suratul baƙara, nayi nisa cikin bin shi karatun, ɓangaren ɗaya kuma tinani ne barkatai cikin ƙwaƙwalwar ta, a hankali Naji wani abu na bimanta cikin ƙafa, saurara wa nayi, lallai wani abu ne ki bi man jiki dagudu, a zabure na tashi ina kwalla ƙara gami da fara dire dire da ƴan tsale tsale. Bai aune ba yaji an kai mashi cakuma, zuwan shi kenan ta wurin yaji ihun mace, ni kau da dai Naji na samu wanda zan kama sai na kuma ƙwaƙume shi ina ta kurma ihu da tsalle tsalle, duk na cukuikuye hijabi na da fuska ta, wayata datayi tsallen baɗake gefe ta faɗi har headphone ɗin ya zare, karatun ta take ci gaba da rerawa a hankali a hankali. Ƙoƙarin raba ni yake da jikinshi, ni kau sai ƙara ƙwaƙumeshi nake yi cikin murya ta mai cike da tsoro nake faɗin "wani abu na bina, ƙila kunama ce, a taimakeni" "Ke ke wai meye haka ne, ya isa babu abinda ke binki, ba kunama bace, gidan nan babu kunama, ana yin feshi ki natsu" Ban ko saurare shi ba, har saida na cire hijabi na wurgar da ita ta gefe, kama zanin nayi da niyyar kwance wa ya daka man wata irin tsawa, ba azziƙi na dawo cikin hankali na. Sai sannan ne wata irin kunya ta kama ni, ganin Abunda nake shirin aikatawa, gani tsaye ko hula babu a kaina balle ɗan kwali, duk nayi wurgi dasu harda hijab ɗin. Kaina kuwa kaman wata sabuwar mahaukaciya, dama ɗazu muka je akayo mana saloon, babu wanda baiyi santin kyawon da kaina yayi ba da tsawon da yayi har kusan tsakiyar baya, dama ban taɓa yi ba wannan ne yina na farko, duk da cika da yawan da gashin nawa yake dashi haɗi da tsawo. Tattara gashin nawa na fara yi, na maida baya, sannan na wawuro hijab ɗita na sanya gami da ɗaukar wayar tawa da har yanzu sautin ƙira'ar malamin ke tashi. Juyawa nayi da niyyar barin gurin ina mai cewa "Yi haƙuri yaya" dakatar dani yayi fuskar na tashi murtuk "Ko kin koma cikin gidan basu gama kaɗe kaɗen nasu ba, zo muje" Yana gama faɗar haka ya juya ya cigaba da tafiya, zuwa ga ƙofar da zata sadaka da bayan gidan, wanda sai kayi doguwar tafiya kafin ka shawo kwana zuwa bakin Gates. Mamaki ne cike da raina, in bishi muje ina cikin wannan daren, ko ba ma haka ba, in ummata ta ganni ince mata me? Ko idan wani ya ganni yaje ya faɗa mata fa? Ganin yaja ya tsaya ne gami da ɗan waigowa ya sanya ni ɗaga ƙafa cikin sauri na shiga binshi, juyawa yayi gami da cigaba da tafiya, duk da ɗan hasken farin wata da fitilu jefi jefi dake bayan gidan, da naga zai yi man nisa na kan ɗaga ƙafa a sukwane in bishi, har muka ɓulla ta fuskar gidan. Hamdala nayi ganin mutane jefi jefi a ƙofar gidan da alama ma wasu zance sukeyi, bugun zuciya ta ne ya ƙaru, ganin ya nufi motar shi dake fake gefe guda ya kunna ya shiga, alama yayi man da in zagaya in shiga nima. Ba musu, dole na buɗe gidan gaba na shiga shiga na zauna, ɗan kwali na a hannu, sai raba idanu nake yi. Tada motar yayi gami da ficewa daga Layin, bai tanka mani ba haka nima ban ce mashi ƙala ba, kowa na fama da ƴan miskilancin shi a kai, ni gani ma nake yi ya cika ƙarfin hali, haka kawai sai yasa ni in shiga motar shi ya ɗauki hanya dani alhali bansan inda zai kai ni ba? "Sai daki zanyi" Abunda yace kenan ya ja bakinshi yayi shiru, ɗan zaro idanu nayi, bansan zancen zuci ya fito fili ba, ɗan waiwaya wa nayi na kalle shi, ina mai sadda kaina ƙasa, "kayi haƙuri, ummata bata san na fito ba Kaga dare yayi, Shiyasa nake jin tsoro" Maimakon ya bani amsa, sai shiru da yayi yana mai maida hankali shi kan tuƙin da yake yi, shiru ne ya biyo baya acikin motar kaman ma ba zai tanka ba, sai kuma cen Naji yace *"Kallon me kike yi mani rannan??? "* ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~24~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Shiru nayi mashi ban tanka mashi ba, har yanzu fa ni a tsorace nake, yo naga muna ta sharara uban gudu hanyar ba kowa, bansan ina muka nufa ba, sai aikin murza yatsu nake, ganin ban bashi amsa ba na ɗauka ya bar zancen kenan. *"Kallon me kike man rannan?* Tambayar ta ƙara zo man a bazata, bayan duk tsawon lokacin da muka ɗauka ban tanka ba. Shahada nayi wajen cewa" kayi haƙuri" "Ba haƙuri na tambaye ki ba, so nak insan dalilin kallon, ko nayi maki kama da wanda kika sani?" Ya jefo man maganar da banyi tinanin zata iya fitowa a bakin shi ba. Shiru na sake yi mashi ina sun ne kaina, ni sai ma ya bani ƴar dariya, bansan sautin dariyar tawa ya fito ba sai ji nai yana cewa" Dariya ma na baki ko?" Ɗan juyawa nayi ina mai sake kallon shi, shi ɗin dai ne, Ya Ameen ne yake ta tuƙin shi hankali kwance yake zaroman magana kaman ba shi ba, ashe dama yana magana haka? Tinani nake ta faman yi, yayin da shi kuma ya sake maida hankalinshi a kan tuƙin shi, ban tashi farfaɗowa daga kogin tinanin da na shiga ba saida naji tsayawar mota alamar dai mun iso inda zamu. Ɗaga idanuna nayi ina mai ƙare ma wajen kallo, yayin da shi kuma har ya fita gami da kullo ƙofar. Airport ne muka zo, lallai wajen ya ƙayatar dani, ba ƙaramin ƙaramin kyau wajen yayi mani ba, na saki jiki ina ta more kalle kalle na, tinda na san baya cikin motar, Naji maganan shi kaman daga sama. "Malama sai ki fito" Ɗan zabura nayi, kunya duk ta dabaibayeni, domin Sam bansan yana tsaye yana kallo na ba, ashe glass ɗin motar ƙasa yake kaɗan. Fitowa nayi, zullumi da fargaba duk sun cika man zuciya, na san yanzu umma ta suna cen suna nemana, wayyo Allah na, na san kuma Hafsat zata ce mata bata san inda na tafi ba. Gaba yayi ina bin shi a baya, sai harɗewa nake ta cikin hijab, yana kallo na kuma bai ce man komai ba, sai nayi kaman zan faɗi, sai ya juyo ya ɗan kalle ni Amman ba zai ce an komai ba. Mutane ne ke ta hada hadarsu, ga wajen tar da hasken ƙwan fitilu mashi masifar haske kaman rana. Wasu da ƴan alluna, an rubuta su aye, ga mutane suna ta fitowa daga wani ɗan ɗaki na glass, tin daga nesa ya hango shi, da ƴar sassarfa ya ƙara so inda muke gefe tsaye Ya Ameen yana ta gabana haka. Tafasa sukayi lokaci guda suna sakar ma kansu murmushi na tsabar ƙauna irin ta aminai "Ya dai Friend? Ai ban ɗauka zakazo haka da wuri ba, na Ɗauka sai ka shanya ni kaman yanda ka saba" Ɗan murmushi na gefen baki ya sake yi, sannan ya shiga cewa "wallahi ai kasan gidan mutane sun yi yawa, duk an cika gidan da Bidi'o'i sun dameni, suna neman fasa man kunne Shiyasa ma na fito haka da wuri" Juyawa sukayi suka shiga tafiya suna riƙe da hannayen juna. Da alama ma ƙila ya manta da wata abu wai ita Suhan a bayan shi tsaye. Ganin haka nima sai na shiga binsu, mu yi tafiya mai ɗan nisa, sannan muka isa ga motar tashi. Sai sannan ya tina da ita, juyawa yayi a hankali yana kalle kalle alamar yana neman wani abu. Da yake ina ta gudan ɓarin mota bayan Bilal ɗin sai bai lura dani ba, ganin ya juya alamar zai koma ta inda muka fito ne ya sanya ni cewa "gani nan yaya" Tsayawa yayi, gami da juyowa, ya sanya key ya buɗe motar, Bilal ɗinne ya juyo a ɗan razabe jin wata irin siririyar muryar mace ta bayan shi. Kallon tuhuma ya shiga yi ma Al'ameen, yayin da shi kuma ya basar yana mai shige wa motar, bayada zaɓi illa shima ya shiga, zamana cikin motar ne yayi daidai da tashin motar yayi revos ya halba ta bisa titi. Ba wanda yace uffan har muka yi nisa, ganin shirun tayi yawa ne kowa da Abunda yake saƙawa cikin rai, ya sanya Bilal kauda shirun ta hanyar cewa "Mutumena ya hidimar biki" "Suna cen suna yi" ya bashi amsa a taƙaice, shiru Bilal ɗin yayi don ya san halin Al'ameen ɗin, tinda ya ji ya fara amsa mashi a gajarce ya san ƴan maganar basa kanshi. Har muka isa gidan ba wanda ya kuma tankawa, an tashi daga mothers eve ɗin da ya tashi daga evening ya koma night, sai aje ayi ta faman ƙara'in salloli kuma. Da kwai sauran mutane, Amman jefi jefi, har cikin gidan ya shiga gami dayin parking, dama abunda nake jira kenan, nayi saurin ɓalle murfin motar gami da ficewa, kai tsaye sashen amaren na nufa da yanzu cen ɗakinsu Hafsat nake kwana. Duk agaji anyi tuɓus, wasu ma duk sun kwakkwanta, hakan ce ta sanya ba kowa ne ya lura dani ba, Hafsat ce kawai zaune tana waya da angonta, ita kau Afnan ta shiga watsa ruwa toilet. Lallaɓawa nayi gami da kwanciya kafin Hafsat da take tsaye bakin window ta ganni. "Tashi Tashi na ganki wallahi, gaya man daga ina kuke?" Abunda Naji hafsat ɗin ta faɗa kenan, bansan ma lokacin da ta katse wayar ba, sai ganin ta nayi har ta ƙara so inda nake kwance bisa katifa. Tashi nayi duk borin kunya ya kama ni, cire hijab ɗin na shiga yi, ina cewa" uhmm wai daga ina muke? Ko dai daga ina nake, ko kin ganni da wani ne da zaki ce daga ina muke?" " Eh" ta bani amsa kai tsaye, sannan ta ɗora da cewa "ke da Yaya Al'ameen da Yaya Bilal da ganku kun dawo yanzun nan" Ɗan zaro idanu nayi, kaman ƙasa ta tsage in shige nake ji uwa wadda tayi wa sarki ƙarya. "Kinga fa wallahi shine ya......" fitowa afnan ce daga toilet ɗin ɗaure da towel ya katse man maganar da nayi niyyar faɗa ma hafsat ɗin. "Humm" kawai afnan ɗin tace tana ɗan murmusawa, da alama duk taji zancen da mukeyi, saidai ƙala bata ce ba. Lura da ita ne da Hafsat ɗin tayi ya sanya ta basar da zancen itama, tana mai miƙewa zuwa toilet ɗin. Duk ina zaune ina saƙawa da warwarewa, har afnan ɗin ta gama shirin kwanciya, lokacin ne Hafsat ta fito da alama itama wanka tayo, "Ki tashi ki bar tinanin hakanan Aunty Suhan kije kiyo wankan kema" Abunda afnan ɗin tace man kenan, ta sake gyara kwanciyar ta gami da juyawa tana murmushi. Duk fa na bi na tsargu kaina, kaman wadda kwai ya fashemawa haka na miƙe ina jan ƙafafun nawa har na shige toilet ɗin. Da murmushi itama Hafsat ɗin ta bini, tana fatan Abunda take zargi ya tabbata, da tafi kowa jin ɗaɗi, kuma taga ƙarshen Hajiya Kubra da ta ɗauki son duniya da burin duniya ta aza shi akan yaron nata. Makullin sashen kawai ya miƙa mashi, yana mai cewa "bari in nemo mana Abunda zamu ci" Amsa Bilal ɗin yayi gami da juyawa ya nufi sashen aminin nashi, yayin da shi kuma Al'ameen ɗin ya kaɗa kan motar gami da sake ficewa daga cikin gidan. A bisa kujera 3seater ya zube, gajiya fal a cikin jikin shi, Amman ba ita ce tafi damun shi ba, ganin aminin nashi da yayi da yarinyar da yake iƙirarin auren ta, kar dai ace da gaske abokin nashi yake akan zancen yarinyar, saidai lura da yayi da yanda ya gansu, da kuma irin zaman da aka yi cikin motar har kawo dawowar su gidan babu wata alama dake nuna maka cewa su ɗin soyayya suke, Amman in ko haka ne, menene dalilin Al'ameen ɗin na yawo da ita cikin mota da daddare haka? Ya daɗe nan kwance yana saƙawa da warwarewa har Al'ameen ɗin ya dawo, nan ya tada shi kwance yayi zurfi a tinani, ɗan dukan shi yayi a cinya yana "tashi yallaɓai, ba dai bacci kake yi ba haka, ko wanka ba kayi ba balle kaci abinci" Tashi yayi yana murje ido, yayin da Al'ameen ɗin ya wuce kitchen ɗauko spoons da plate da lemo da ruwan sha, a haka ya dawo ya tada abokin nashi zaune yana narai narai da idanu. Zuba masu abincin yayi, yayin da ya jawo stool ya ɗora masu akai, Al'ameen ya san darajar baƙo, duk da kasancewar Bilal ɗin ɗan gida kuma aminin shi, haka yake in yaso har ruwan wanka yana haɗa mashi in ya kawo mashi ziyara. Har suka gama cin abincin, Bilal na ma Al'ameennɗin kallon tuhuma, to abunka da aminai, tini Al'ameen ɗin ya ɗago shi, murmushi yayi yana mai goge baki da tissue "Bari in gaya maka Abunda kake son tambaya ta tin kafin ka tambaya, yarinyar da ka ganni ɗazu ya ita, na san dai ka santa kasan komai a kanta, kuma har yanzu ina kan baka na a kanta, saidai ita bana tsammani ntasan komai, dalilin da ya sanya kuma ka ganni tare da ita, shine....... " nan ya kwashe komai ya faɗa mashi a gajarce. Murmushi yayi yana faɗin" Mugu, watau har kasan Abunda nake son tambayar ka ko? To ai shikenan Allah ya zaɓa mafi alkhairi a cikin Al'amarin, Amman dai ka kula gudun ja ma yarinyar matsala ko a wajen mahaifiyarka, kadai ga yanda take iya ƙoƙari wajen bata tarbiyya" yana faɗin haka shima ya ajiye spoon ɗin dake hannun shi ya tashi gami da shige wa bedroom domin yin wanka da rama salloli dake kanshi, sannan ya kwanta, shi kau oga Al'ameen, maida komai yayi kitchen, gami da wanke na wankewa, ya gyara komai tsaf, dama haka yake, baya son ƙazanta ko kaɗan, duk wani abu da ya san zai yi na tsabta baya jira ayi mashi shi keyi da kanshi, saidai Abunda ya san zai ɓata masa lokaci ne. Hatta da girki ba Abunda bai iya dafawa ba, saboda shi ba abincin kowa yake iya ci ba, ko zaman da yayi ƙasashe waje shi keyi a kanshi abinci, matuƙar bai yadda da wanda aka kawo mashi daga cikin hotel ɗin ba. Sun daɗe suna fira kafin su kwanta, yayin da ni kuma har bayan na kwanta ɗin juye juye kawai nake yi, hafsat ɗin na kula dani, har yanzu bata gaji da wayar ba haka, tinani nake yi na abubuwa da dama, Amman tinanin nawa yafi karkata ma ga Jarabawa da na rubuta kusan kwanaki da dama baya. Sai daga baya ne tinanin Al'ameen ɗin ya faɗo mani, lallai ni bansan ma me zan kira Abunda yayi mani dashi ba Gashi in akula har yaja hafsat ta fara mana wata fassara ta daban, ɗan guntun tsaki naja ina mai sake gyara kwanciya ta gami da karanto addu'oin barci, banga dalilin ma ɓata lokaci yin tinanin abun ban haushi ba, ko in kalle shi inji me? Ko ya ɗauka nima ina cikin ƴan matan da suke rububinshin ne oha? 🤷🏻‍♀ Washegari ansha bacci, yayin da maree da mahaifiyarka mama talatun baccin su ragagge ne, suna ta saƙa yanda zasu yi su mallaki Al'ameen ɗin, domin suna hango ma kansu rayuwa ta jin daɗi da zasu iya fuskanta nan gaba kaɗan ba da jimawa ba, saidai Abunda ya ƙara ɗugunzuma hankalinau shine ganin da mareen tayi ma Suhan ɗin a motar Al'ameen lokacin da suka dawo, haka ta koma fa tayi ta rusa kuka, da gaske son Al'ameen ɗin ya kamata, yayinda ita kuma mama talatun ba ta wannan take ba, abun duniyar kawai take hange, haka kawai ta shiga ce ma mariyar zauna nan abun duniy ya kashe ki, akan waccen kucakar da na san ko kyauta aka bashi ita ba amsa zai yi ba, kawai dai ita ce da uwar ta ke shisshigi mashi, Amman zanyi ma abun tufkar hanci. Kowa hidima yake yi fafa, gida fa ya kacame, wasu irin garƙama garƙaman tuƙwane ake ɗorawa, bayan abincin da ake yo order ɗinshi daga manyan restourent. Ƴan kankiya sunyi bajinta ta nan fannin, domin duk wata sanwa da za'ayi suna kamawa, yayinda ƴan uwan Hajiya kubra kejin sun wuce nan, kaman su ba zasu iya fitowa yin girkin hidima ba, rarraba ake da abinci kaman ba'a so. Kowa sai shirin yin ƙauyawa yake yi yau, da yake duka amaren yau zasu yi, ko wanne ɓangare shiri akeyi, sai shigowa akeyi da dami damin kara, da su goruba, magarya ɗinta, nan cikin gida kuma an sanya ayi lafiyayyen dambu, da zogala ɗanya, ga lafiyayyar fura da amma da taji lafiyayyen nono da yoghurt da madarar ruwa, abun dai gwanin ban sha'awa. Hajiya Kubra taji haushi wannan event ɗin, saida taga cewa kowa na murna dashi ne sannan ta sake, to muma ta ɓangare namu mun yi murna, saboda yau ne za'a zama ɗaya, da mai ji da kanshi da mara ji da kanshi duk za'a zama ɗaya, matan sunyi shiga irin ta Fulanin usul, musamman suka ɗauko wasu Fulani suka zo sukayi masu kwalliya irin tasu ta filani, an zane masu fuksokinsu ram da kalli baƙi da ɗige ɗige, sai suka ba kansu dariya, kuma suka burge kansu, masalan da suka ji angunan na cewa sunyi kyau. Banso banso nake cewa, Amman a haka saida Hafsat da afnan suka matsa aka yi man saisa saisa, nima kayan Fulanin na sanya sun matuƙar amsa ta, sun yi man cif cif, dama saida Hafsat ɗin ta zaɓo mana saƙi mai kyau harda jikkarsu ta Fulani. A haka kowa ya hallara aka fara event, kasancewar da marece ne, da sauran Haske kuma ga maza a tattare guri guda, ya sanya ni takura, gefe na koma gami da zama bisa wani kututture ƙarƙashin bishiyar gwaba, ina ta kallon su ina dariya, hannuna riƙe da ƴar sandarsu ta Fulani ina wasa da ita. Kwallon su nake tayi, ina tafaman murmusawa, yanda maza ke gatsar rake suna sha suna santi, gefe mata masu ji da kansu su wasu ne, sun dage suna ta gwaguyar goruba duk don su faranta ma amaren rai, gefe wasu gunsu ne suna ta faman afa tambu baka, ga wasu dandalin gefe suna ta faman shan fura cikin ƙorai masu matuƙar kyau da suka sha zanen wuta. Wasu kuma suna zaune gefe wasu kuma a tsaye suna zance da samarin su, kai abun dai kaman a ƙauye, sai abun ya burgeni, hannuna riƙe da taura guda ɗaya ina ta faman jujjuya ta, ina so inci ina jin kunyar ɗimbin maza, abokan anguna da suke ta wajen. "Allah kuwa Friend ina son leƙa wa wurin cen fa, Naji kiɗan mu na gargajiya na tashi fa a wajen, har ma na ƙagara inje," Bilal ne da yake tsaye bisa kan Ya ameen ɗin, shi kuma yana kishingiɗe yana latsa waya yake bashi amsa "To kaje mana, ai ni dama ban hana ka ba, Nidai na gaya maka, hidimar yara ce ba zan shiga ba." Ɗan murmushi yayi, son zuwa wajen na ƙara tsuma shi, "Pls Pls Al'ameen Dont do that to me please i beg u Friend" Ɗan tsaki yaja a hankali yana mai miƙewa "Muje na lura kai in maye ne ya kama mutum sai ya lashe mashi kurwa tas wallahi" "Eah Naji ba komai shege, tinda fa ba kai kayi niyya ba, ai komai ma zaka iya faɗa" Je rawa sukayi suna ci gaba da tafiya, har zuwa tafkeken lambun nasu da ya wadatu da mutane da ɓawon rake da wasu suke gefe suna ta fama n fere bayan suna rage mashi baƙi. Da ƙafar dama Bilal ɗin ya shiga wurin, domin yana saka ƙafa ya hango one of his colique a cikin abokan ango, ya ja area cen gefe yana ta zuƙar zaƙin rake, hannun Al'ameen ɗin yaja suka isa har inda yake zaune bisa wani dutsi shida abokan shi. Ji yai an taɓo shi ta baya, ai waigawar da zai yi sai suka haɗa ido da Bilal ɗin, a sukwabe ya tashi yana ihu, "Wow wa nake gani nan kaman Bilal Musaddiƙ ja?" ya faɗa cikin murna, yanayi yana murza ido da gudan hannun da bai riƙe karan ba. "Nine son Ubanka Mubin, long time not see, ka ɓace ɓat fa baba, ya rayuwa?" y a faɗa yana mai kamo hannun Bilal ɗin. "bikin wa kazo nan?" Wanda aka kira da Mubin ɗinne ke tambayar Bilal, dariya Bilal ɗin yayi gami da cewa "Kai zan tambaya Mubin ai ni nan gidan mu ne, duka amaren ƙannai ma ne, wannan shine Abokina Moh'd Almustapha Dambulan da kuke jin labarin shi" ya faɗa yana mai juyawa gami da nuna Al'ameen ɗin da yake tsaye yana ta faman doka murmushi. Su kansu miƙewa sukayi gami da miƙa ma Al'ameen ɗin hannu suna mai girmamawa, "Nyc to meet you our gallant Yaya" suka faɗa cikin barkwanci, har yanzu basu bar shan ka ransu ba. "Bikin fa Sadeeq Mufti akeyi angon Hafsat, ai mu so mu gayyace ka shi sadeeq ɗin ya hana a cewarshi ayyuka sunyi maka yawa, da wahala ka shigo Nija withing this Period of time" Mubeen ɗin ya faɗa cikin jin daɗin ganin abokin nashi. "Braboo, ai banga ta zama ba, muje ka nuna man shegen surukin namu" ya faɗa yana kamo hannun Al'ameen. Sun gaggaisa sosai, nan suka shiga firar yaushe rabo, shi dai Al'ameen ɗin sai faman murmushi yake, mutane sai zuwa suke gaida shi, da waɗanda suka sanshi a zahiri da waɗanda ma sunanshi kaɗai suke ji, nan da nan fa aka shiga kallon Moh'd Al'ameen ɗin gami da nuna shi, waɗanda ma basu san shi ba yau duk sun sanshi kuma sun ganshi. Duk abubuwan dake faruwa ina zaune gefe ina kallo, nayi mamakin yanda sunan Al'ameen ɗin ya buɗe wajen cikin ɗannƙanƙanin lokaci, koda yake shi ɗin mai yi ne, na matsa ne, domin kafin ka samu matashi kaman shi da yake da kishin matsa da samar masu da ayyukan yi sai ka tona. Wani ƙadangare ne da bansan da tahowa shi ba, ga dukkan alamu ma faɗa suke yi, irin manyan nan ne masu jan kai da bindi. *Jiffff* Ƙarar fadowar ƙadangare ne bisa kaina ya zabura dani daga faman murmushi da nake yi, ƙara na ƙwalla gami da daka tsalle, bai sauka ba ma, sai ƙara maƙalƙaleni a yayi yana neman shige wa cikin riga ta. Wata razananniyar ƙara na kuma saki da saida ta karaɗe illahirin lambun nan baki ɗaya, lokaci guda na saki ajiyar zuciya ina mai sulale wa ƙasa sumammiya. Rige rigen isa inda nake yaushe suka shiga yi, Al'ameen ne, da Bilal sai Hafsat da afnan, tini suka ƙaraso inda nake kwance a sume, Afnan ce ta tallafi kaina tana sakin wani tsumammen kuka, lokacin da ƙadangaren ya sauka daga bisa jikina ya sulale abin shi yanayi yana gyaɗa kai. "ta suma Yaya ta suma ka taimaka mata" Abunda afnan ɗin ke faɗi kenan, daidai lokacin da su Saudat da Nihal suka iso wurin su da tawagar ƙawayen nasu, da sauran angunan nasu. Baiyi wata wata ba ya sun kuce ta, hankalinshi a tashe ya nufi cikin gidan da ita, har yanzu bata ko motsi bata san inda kanta yake ba. Sakin baki sukayi gami da bin shi da kallo, tini ƴan maganganu suka baibaye wurin, wasu na cewa ƙanwar shi ce, wasu na cewa budurwar shi ce. *To koma dai miye ku biyo alƙalamin ~Oum-Deedat~ domin jin yanda zata kaya* ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~25~* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Rasa inda zai nufa yayi da ita, daya kalle ta yaga yanda take sake a hannun shi, sai ya ƙara ɗaga ƙafa, sashen shi da yafi kusa da lambun ya nufa da ita kai tsaye. Bai ajiye ta a ko'ina ba sai bisa gadon shi, Bilal Sadeeq Afnan da Hafsat amarya da suke biye dashi, cikin su babu wanda baiyi mamakin shi ba, to saidai shi ɗin ba tasu yake yi ba. Ruwa yace Afnan ta ɗauko masu sanyi, miƙewa yayi daga bisa gadon yace Afnan ɗin ta shafa mata a fuska. Ajiyar zuciya na sauke, jin saukar ruwan a fuska ta, har saida ƙirjina ya ɗaga sosai, ƙoƙarin miƙewa nake yi afnan ɗin ta sanya hannu ta maidani kwance. Lamo nayi ina sauke ajiye zuciya a hankali a hankali, har yanzu jikina rawa yajeyi, tsoro gami da firgici har yanzu bai sake ni ba. A hankali zazzaɓi mai zafi ya lulluɓeni, ganin ina rawar sanyi ne ya sanya ta jawo bargo ta lulluɓeni ruf, ga tashin bargo ga laushi katifa, uwa uba wani daɗaɗɗen ƙamshi da nake shaƙa suka taru suka sanya nayi luf abuna. Juyawa Ya Ameen ɗin yayi gami da fita daga ɗakin, ganin haka ne Sadeeq ɗin da Bilal suka mara mashi baya wajen ficewa su bamu wuri. Afnan ce ta kalli Hafsat gami da cewa "Aunty Hafsat ya kamata ki koma wajen baƙi, kinga ke amarya ce, ba kin baro mutane kizo ki zauna nan ba, gashi ba'a tashi daga event ɗin ba, ga kuma angonki da baƙin shi" Miƙewa hafsat ɗin tayi gami da cewa "bari inje in sallama kowa, ni na tashi hakanan" girgiza mata kai Afnan ɗin tayi, kiyi haƙuri, Aunty Suhan ta samu lafiya, kinga ma bacci take yi, kar kiyi haka, kije nima gani nan zuwa" Hafsat ɗince ta shiga gyaɗa kai, sannan ta juya gami da fita itama, a falo ta taddasu zazzaune ba mai ce a ɗan uwanshi kanzil, gara ma Bilal da yake ta fama latsa waya, ganin fitowar ta ne ya sanya Sadeeq ɗin shima miƙewa yana cewa "ya jikin ta ne?" "Ta samu bacci ne, kasan Suhan da mugun tsoro, ita fa abu kaɗan ma kan firgita ta balle wannan ƙaton ƙadangaren" "Haka ne kam, gaskiya dole ta firgita, Allah ya bata lafiya" binta yayi suka fice tare gami da komawa wajen baƙin nasu. Sun tadda an cigaba da hidima kaman ba Abunda ya faru, baƙin nasu dai ne sai a hankali, ganin yanda amaryar tasu ta firgita ya nuna masu cewa lallai itama ƴar gidan ce, hakan ce ta sanya jikin su yayi sanyi, saida suka ga dawowar su sana suka saki jiki aka yi ta kwasar gara da nishaɗi, su kau dama su Saudat ɗin taɓe baki sukayi, gnai da cewa Allah ya bata lafiya, suka koma wajen ƙawayen su aka cigaba da shagali, domin Suhan ɗin bata kai wadda zasu tashi hankalin su a kanta ba, ko mutuwa tayi balle ta ruguza masu farin cikin da suke ciki. Har aka tashi Afnan bata dawo ba, ita kau Hafsat dama tinda ta koma bata saki jiki ba, ƙawayenta sai bata haƙuri suke yi gami da ban bakin ƙawar tata zata samu lafiya. Cikin hanzari ta nufi sashen na Yayan nasu bayan duk ta sallama baƙi masu komawa, na cikin gidan kuma ta raka su sashen nasu na amare, gami da ɗaukar excuse ɗin cewa zata je ta dawo. Miƙa nayi, salati ɗauke a bakina, sannan na karanto addu'ar tashi daga bacci, wara idanu nayi, gami da saurin yaye bargon da aka lulluɓeni dashi. Nazarin ɗakin na shiga yi, ba ɗakin umma ta bane, ba kuma ɗakin Hafsat bane, ba kuma asibiti bane, to ina ne nan aka kawo ni, har bisa gado harda kuma lulluɓeni? Zumbur nayi na tashi, ina mai ƙoƙarin sauka daga kan gadon, dafe da kaina dake saramun alamun ciwo. Afnan ce ta shigo ɗakin da saurin ta jin alamun motsi, kamfani tayi gami da taimaka man na zauna, ƙafafu a a ƙasa. Bin ɗakin na shiga yi da kallo, ɗakin Ya ameen😳 bisa gadon shi🤭 ni Suhan??? Aikau a sukwane na miƙe har ina harɗewa da zanin gadon da ya maƙale man a ƙafa. "Yi a hankali Aunty Suhan" Abunda afnan ɗin ke cewa kenan "Afnan nan kaman ɗakin Ya Ameen? Wa ya kawo ni nan? Me yasa?" na shiga jero mata tambayoyi a firgice ina mai jiran amsar ta. Ɗan murmushi tayi gami da jan numfashi, "to miye? Ai ya ameen ɗin ne ma da kansa ya ɗauko ki ya kawo ki nan kuma......." Katse mata hanzari nayi daga amso shin da take bani, " me? Ya ɗauko ni fa kika ce? Au shine ma ya ɗauko ni ya kawo ni nan?" na faɗa ina ɗan jinjina kai gaba jiran ƙarin bayani. " To miye ne? Kaji aunty Suhan da wani zance, ke ba ƙanwar sa bace? Kuma ai nan yafi kusa akan cen cikin gida, hankalin mu fa duk ya tashi wallahi, masalan ma shi, mu ai mun ɗauka abun yafi haka, ashe razana ce kawai" Gaba nayi ina mai cewa "ai na warke, wajen umma ta zanje ni" jawo hannuwana ta shiga yi, ki bari su dawo yaje siyo maki maganin zazzaɓi, kar yazo ya tadda baƙya nan inda ya ajiyeki" Girgiza mata kai na shiga yi, kayan kunya iri iri ina shan shi ƴan kwanaki nan, kaji fa wai shine ma ya ɗauko ni da kansa, kaman wata baby, kuma wai kar yazo ya tadda bana nan inda ya ajiye ni, kaman wata kayansa😗 "ya baki ki kawo mani, ina sashen mu" Abunda nace kenan ina mai ficewa daga sashen, kai tsaye ɗakin namu na tura na shiga, umma ta da bata nan kuma bata kulle ɗakin ba, hakan ce ta sanya ni kwanciya dafe da kaina da yake ta sara man kaman zai faɗo. Ɗan murmushi Afnan ɗin tayi, gami da gyara gadon, ta nayi tana zancen zuci, "lallai ya Ameen da gaske yake, kaji fa yanda ya ruɗe, ko mune dai bama lafiya ai iyakar ruɗewa da zai yi kenan" 😉☺ Bilal ne da yake zaune kujerar mai zaman banza, ya kalli abokin nashi gami da muskutawa ya gyara zama. "Abokina it seems fa labari yana neman ya cenza, naga fa ka damu da lamarin yarinyar nan over, wai whats going on ne? Yayi maganar in a serious tone. Ɗan kallon shi Al'ameen yayi yana mai maida hankalin shi kan tuƙi, baya da Abunda zai ce ma Bilal ɗin, ba zai fahimta ba, shi ba zai gane tsabar tausayin da yarinya take bashi ba, halin da suke ciki ita da mahaifiyarta kaɗai abun dubawa ne. "Oh ba ma da amsa ko" ya faɗa cikin son kauda shirun da Al'ameen ɗin yayi mashi. Ya fara ƙule shi da waɗan nan maganganu nashi, ashe shi ba mai bashi goyon baya ne ba kan taimakon da yake son yi. "Idan Kaga kare na shinshinar takalmi...." "ɗauka zai yi" Bilal ɗin ya ƙara sa mashi yana ɗan murmushi. Gefen damtse hannun shi ya kaima bugu, "watau shege tini ka fito kayi man bayanin Abunda ke faruwa ka tsaya sai kwana kwana kake yi, nima ai na fara gundura da zaman naka hakan a babu mashinshiniya, saidai fa kasan ka ɗauko dala ba gammo, ka ɗebo ruwan dafa kanka mutumena, ina tsoron Allah ina tsoron Hajiya, bana son Abunda zai baka matsala, kuma hakan ba yana nuna bana tare da kai bane, aa am 100% with you abokina" Ɗan guntun murmushi na gefen baki Al'ameen ɗin yaja, ga dukkan alamu ya zama al'ada shi. "Tinda haka kake so kaji, na faɗa hankalinka sai ya kwanta, banza magulmaci" Dariya Bilal ɗin ya saki, saida yayi mai isar shi sannan ya tsagaita. "Kana nufin don inji daɗi kenan ka faɗa ba gaskiya bane" "Duk yanda ka ɗauka, naga babu haramci a ciki inma cewa nayi ina so" "ai ba cewa aka yi haramun bane Alhaji, ana so ne dai a nuna maka matsayi ka yafi gaban ace wannan yarinya kake so da aure, shi fa aure ba abun wasa bane, abu ne for life, zama ne na dindindin" "Naji malam bilalu, ai sai ka faɗa man yanda yake tinda kayi kaji yanda yake" ya faɗa cikin ɗaure fuska da gundura da zancen. "Oho dai, ai ko banyi ba ina kan hanya, kuma na fika tinda ina da gurin yi" "Nima ai ina da burin yi ɗin, tinda gashi na samo" Tsoki Bilal ɗin yaja cikinbƙuluwabyake cewa "kai dai Kwallon ɗan iska ne wallahi, ana cewa ga ruwa kana ga wuta" "Eh Naji a barni in faɗa wutar in ƙone ba shikenan ba, kowa ya huta, tsuntsu dayaja ruwa ai shi ruwa kan doka" ya faɗa yana mai ficewa daga motar da tini ya isa gidan. Afnan ya shiga kira a wayar shi, tazo ta amsar mata maganin, tinda shi tinanin shi har yanzu suna sashe nashi, Shiyasa bai shiga ba. Bayan ta amsa ne ma take faɗa mashi cewa ai ta koma ɗaki su, wai ba zata iya zama ba kunya take ji. Bajce komai ba ya nufi sashen nashi Bilal ɗin na biye dashi, "Kudai tabbatar tasha maganin, kinga dare yayi, ciwon daren ake gudu" da to ta amsa mashi tana mai nufar sashen su Suhan ɗin. Umman tawa ma a haka ta tadda ni, ban gaya mata me ya faru ba, illa dai iyaka nace mata kaina ne yake ɗan man ciwo. Sannu tayi man tana cewa hayaniya ce. Saida na sha maganin da Afnan ɗin ta kawo man sannan na kwanta, dama ina fashin sallah ne. Sannu Afnan ɗin tayi man, bayan tayi tayi dani muje cen ɗakin nasu na ƙiya, a haka ta fice tana ƙara man sannu, gami da cewa Hafsat ɗin na gaida ni, baƙi ne sukayi mata yawa. Duk yanda mama talatin taso ta danne gulmar tata abun yaci tura, gani take yi abun na ƙara gaba, ga maree sai tazo ta sanya ta gaba tana ta mata koke koke, idan har taga Al'ameen ɗin da Suhan ɗin, masalan ma yau da kan idon ta Al'ameen ɗin ya sunkuci Suhan ɗin kaman matarshi ko kuma wata ƴar baby, ai ko daƙin nasu bata gama shiga ba ta fasa kuka, ba yanda mama talatun bata yi ba akan tayi shiru ta kasa. Hakan ce ta sanya ta miƙewa ta doshi sashen hajiyar da yake cike da baƙi, a haka ta kutsa har zuwa ɗakin hajiyar. Taci sa'a ba kowa, domin tin isha'i ta shiga ta huta, duk ƴan baran dan nata suna ɗakunan su, balle da yanzu kusan ƙarfe goman dare ne. Ƙwanƙwasawa tayi, daga ciki hajiyar ta buɗe, tana mai cewa "a'a Talatu, kece cikin daren nan, ba mu gama magana ba, ta shirye shirye da za'ayi gobe" "Eah hajiya, ba wannan ce tafe dani ba, labari na kawo maki" dakin ƙofar hajiya tayi gami da juyawa ta isa ga tanƙamemen gadon nata ta zauna. Maida ƙofar mama talatun tayi ta rufe, tana mai bin bayan hajiyar har gaban gadon zan nan ta zube ƙasa, gami da tanƙwashe ƙafafun ta cikin salon koro gulma da munafurci. Ƙarya da gaskiya ta shiga koro ma hajiyar, harda cewa yanzu ma Suhan ɗin har tallar kanta take kaima Al'ameen ɗin har ɗaki shi, ko ɗazu ma da kanshi ya ɗauke ta cikin bainar jama'a ya shiga da ita sashen nashi ya kullo, alamar sun fara cin galaba kenan a kanshi. Salati Hajiya Kubra ta rafka, tana mai miƙewa ta shiga tafa hannuwa, ɗanta? Ɗanta ne ya lalace haka? Yaro ma kaman Al'ameen? Baya san lokacin da ta zari hijabi ba, ta tsallake mama talatun da take durƙushe tana ta fama hakin ƙaryar da ta shirga, ita kanta ta san da gaskiya zata bayyana, babu Abunda zai hana ta barin gidan, don idan kowa ya barta ta sani Al'ameen ba barin ta zai yi ba. Sashen Alhaji ta nufa kai tsaye, yayi mamaki da ya buɗe yaga ita ce, tin kafin yace komai ta fasa kuka, salati ya sanya cikin ruɗewa yake tambayar ta menene? Kuka take fafa, ta ma ƙi ta tsaya ta bashi bayani, waya ya ɗauka gami da kiran Al'ameen ɗin yace ya same shi sashen shi, ga Hajiya na ta kuka taƙi magana. A firgice ya zabura, gami da zura jallabiyar shi, Bilal ɗin na tambayar shi bai tsaya bashi amsa ba, kawai dai yace Alhaji ne ke kiran shi. Ko da ya isa, ya tadda tana kuka, haƙuri shima ya shiga bata, yana cewa tayi masu bayanin me ke faruwa. Ko da ta shiga koro bayani, irin wanda mama talatun ta kai mata gulma, shiru Al'ameen ɗin yayi yana ta faman kallonta, Alhaji ne ya shiga jifan shi da wani irin kallo na tuhuma, shi ya ma kasa buɗe baki balle ya kare kanshi. "Ka bamu kunya Moh'd, ina tarbiyyar da muka baka? Abunda zaka yi mana kenan ka lalata ma ƴar yarinya tarbiyya, me ka nema ka rasa? Mene baka mallaka ba? In ma mata huɗu kace kana so a aura maka, wallahi ina mai tabbatar maka zamu aura maka su, kuma zaka iya riƙe su, me kake nema wajen waccen ƴar tatsitsiyar yarinya? Kucaka ƴar aiki, marar galihu? Wallahi *kafi ƙarfinta* nayi matuƙar baƙin ciki, nayi nadamar sanina dasu a rayuwa, yau ba zasu kwantar mani a gida ba, zasu bar gidan nan koma wace duniya zasu bana da damuwa, domin cece ɗana, domin in ceceka daga halin da kake ƙoƙarin jefa kanka, babu abinda ba zan iya yi ba. Alhaji mustapha da yake tsaye, ya gaza gazgata gaskiya ko akasinta, domin dai ga moh'd ameen zaune Amman ya kasa musantawa ko ƙaryata Abunda mahaifiyar tashi take faɗa da bakin ta, illa iyaka ma dai miƙewa da suka ga yayi ya nufi ƙofar domin fita daga ɗakin. "ka gani ko Alhaji, ka gani ko? Yana aikatawa, ya gama bada kanshi gareta, sunci galaba kanshi, ashirin da suke yayi tasiri kan yaro na, ina gab da rasa shi, Alhaji kayi wani abu" Daf da bakin ƙofa ne suka ga y a yanke jiki ya faɗi, babu alamun rai a tare dashi. Da gudu suka zabura inda yake kwance, rige rigen taɓa shi suka shiga yi, Alhaji ne yayi da dabarar kiran Bilal da abie yace su fidda mota Al'ameen ba lafiya, ita ko mom kuka ta ƙara ruahewa dashi, ba zata juri rasa ɗan nata ba akan wata banza yarinya, saidai ayi ɗaya cikin biyu. Bilal ybatashi a firgice, yaga fa lafiya lau abokin nashi ya bar ɗakin, kuma Alhaji ne ya kira shi, gashi kuma ya sake kira yace baya lafiya, baiyi wata wata ba ya tashi a hanzarce ya zura kayanshi, gami da ɗaukar ma ƙullin mota babba da suke zube kanbstool ɗin falo, ko tsaya kulle sashen baiyi ba ya fice gami da juya mota. Daidai nan Alhaji da Abie suka fito ɗauke dashi babu fa alamun rai a jikin shi, babu ɓata lokaci suka saka shi cikin motar gami da shiga, mai gadi ya wangale gate suka fice cikin matsananci Gud. Shima hankalin shi a tashe ya kulle gidan yana fatan dai lafiya uban ɗakin nasu yake. Wata private hospital da tafi kusa suka kai shi, da gudu nurses suka zo suka tura shi bisa gadon ɗaukar marasa lafiya, har yanzu Hajiya Kuba kwalla take mataewa, shi kau ABBA sai binta da kallo yake yi, duk laifin na kanta ya ɗora shi, baima yadda da Abunda tazo mashi dashi ba tin asali, da ya san wannan shashashar maganar zata kawo mashi da bayyi ma gigin kiran Al'ameen ɗinba. Tin a hanya suka maƙala mashi oxygen, Abunda ya ƙara firgita su kenan, suka sare da Al'amarin, su kau Bilal da abie tambayoyi ne fal a ransu Amman babu wanda zasu yi mawa, basu sare ba saida suka ga ana goga wani abu kaman dutse guda ana man nawa a ƙirjin Al'ameen ɗin, shi kau sai ya yunƙuro kaman zai tashi sai ya koma, duk cikin son samo numfashinshi ne, dukan su ba wanda idanun shi ba suyi ja ba, Abie da har ya fara kuka, Bilal ɗin ya shiga bashi baki, duk da shima zuciyar shi kaman zata fito saboda tsabar ƙuna. Kukan da Hajiya Kubra keyi ne, ya sanya nurses ɗin zagyowa suka ce don Allah a janye ta, suna kan aikin su ne, dole tasanya suka janye ta gami da komawa reception suka zauna Kusan ƙarfe goman dare na farka a firgice, umma ta dake gefe na kwance ce tayi azamar tashi gami da kamo ni, har nayi hanyar fita daga ɗakin, lafiya, ta shiga tambaya ta, ba zance komai ba, mafarki nayi mai ban tsoro, saidai ba zance ga Abunda na gani ba a mafarki, saidai naga fuskar Ya Ameen a ciki, addu'a tayi man gami da maidani ta kwanta. Lamo nayi ina mai sauraren ta tana ta tofa an adduo'i, abun ya dameni, menene nawa na mafarki shi? Kuma fa kaman yana cikin wani hali ne, Allahu a'alamu. Runtse idanun a nayi, Amman fa har yanzu shi nake gani cikin mawuyancin hali ya na miƙo mani hannu alamar in fiddo shi, miƙewa nayi gami da shiga tiolet na ɗauro alwala, gami da zuwa na kabbara sallah, ina addu'ar Allah ya sanya dai lafiya, domin ban taɓa yin irin haka ba Itama umman tawa ganin sallah na tada sai ta rabu dani ta koma ta kwanta, Amman ta kasa runtsawa, tinani take yi me ya samu ɗiyar tata da tin ɗazu ta ganta wani iri, Amman taƙi bayyana mata halin da take ciki. *koma dai miye tana fatan ya kasance lafiya ko kuma yazo da sauƙi* _To sai mu ce dai Ameen Mama Maryam_ ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~26~* Kyautar Page gareki Safiyya, na cika Alƙawari, na baki shi halak malak, ina sonki fiye da yanda kike son littafin nan, Allah ya bar mu tare. 🤝🏻😍 °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Wata irin nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, lokaci guda yana mai ƙoƙarin buɗe idanun shi, likita da nurses ɗin dake kanshi duka suka maida dubansu a kanshi, tini fara'a ta bayyana a fuskokin su suka fara cema juna congratulation, sanin shi ɗin wanene da sukayi, da ceto Rayuwar shi da sukayi, taimaka mashi suka cigaba da yi, har numfashinshi ya daidaita, sannan suka ɗan ƙara mashi allurar barci, lamo yayi yana sauraren su har dai nannauyan barci yayi awon gaba dashi. Hajiya Kubra da tini tabar kuka, saidai ajiyar zuciya da take sauke wa, to dama dai Bilal da Abie ɗinne masu lallashi ta, shi kau Alhaji tsabar ɓacin rai da Abunda taja masu ya sanya ko kallon ta ma ya dena yi, ba yanda likitocin ba suyi ba akan su shiga office ɗinsu su zauna, Amman hakan ya gagara. Bilal da yake ta safa da marwa hannuwan shi goye a bayan shi, fuskar nan tashi ba annuri Sam, ya san ba ƙaramar matsala bace yin hakan ga Al'ameen, ya sani duk lokacin da aka faɗa mashi wata magana ne ta ɓacin rai ko mummunan abu ne yakanyi haka tin yarintar su, likitocin cen ƙasar sun sha gargaɗin a dena ɓata mashi rai irin haka, amman dai hajiyar bata ji, tinda zai iya cewa ya lura kaman ita ce sanadi a yanda yaji Alhaji na cewa "hankalin ki ya kwanta, ke har abada ba zaki dena ɗaukar jita jita ba, ba bincike ba komai kin laƙaba ma ɗanki ƙazafin da aka yi mashi, to inaso ki sani, ni ban yadda da Abunda kika zo dashi ba, ba kuma zan yarda ba har abada, ko daga baya kika ƙara tada zancen nan, ko su Maryamar kika yi mawa ban yafe maki ba, kuma wallahi kika yi sanadin da yarona ya mutu sai nayi shari'a dake, tinda Nidai tini nace ƙibar maganar, da yake bakya jin magana kika yi kunnen uwar shegu, su masu kawo maki gulmar ai gashi sun zura ki zaki kashe ɗanki da kanki, in ke kin lamunta ni Sam ba zan iya lamunta ba, dole ne in aka gama bikin nan in yi bincike da kaina, duk wanda na samu da hannu cikin Al'amarin nan zai sha mamaki na wallahi, ashe ni ina cen ina ta yadda zamu samu rufin asiri, ke kina nan kina fama da magulmata munafukai a cikin gida da ma wajen gidan, kin kasa riƙe gida kina cen kina ta zuba mulki da isa, in ma hakan ta faru wanene keda sila? Ai kece tinda saida yace a aura mashi ita, atafau ke kika ce ba haka ba, kin manta ƴaƴan yanzu duk yanda suke maka biyayya, zasu iya bari akan Abunda suke so, kuma hukuncin Allah rubutacce ne" Yana gama faɗar haka ya koma gefe ya zauna, hannayen shi harɗe cikin na juna, sai karkaɗa ƙafa yake yi ƙasa, ita zata iya cewa tinda take duniya ma bata taɓa ganin ɓacin ran Alhaji haka ba, shi mutum ne mai sauƙi, duk da yadda yake tsaye akan al'amarin gidan shi, dawowar Al'ameen ɗinne ma ya samu sauƙi ya janye ya bar mashi wasu al'amurran. Ba tace ƙala ba a lokacin sai faman share kwalla take yi da gefen gyalenta, to me zata ce? Ai kuma yanzu ta lafiyar shi akeyi, amman fa ita tasha alwashin ɗaukar ma abun mataki, ta san mama talatun ba zata yi mata ƙarya ba, gudun kada Alhaji yace bata ji maganar shi ba, zata yi nata binciken itama ta ƙarƙashin ƙasa, ba zata taɓa lamunta yaron nata mai ji da kyau, ilimi, kwarjini, da wadata ya ɓige ga auren maƙasƙanciyar mai aikinsu ba, ɗiyar mai aiki, kai ina ba zata yuwu ba, tasha Alwashin ko dukkan Abunda ta mallaka zai ƙare sai ta raba yaron nata da waccen shegiyar yarinyar, yo shegiya mana, in banda haka duk duniya wanene ya isa ya nuna wani yace ga ubanta? Yarinyar da ko asali bata dashi balle ma uba. Cikin dare misalin uku saura ya farka, lokacin duk an bar su sun shiga ɗakin, shi dai alhajin kujera ya nema ta gefe mai cin mutum ukku ya zauna shi da Abie, ita kau Hajiya kubran kujera taja irin ta silver mai soso da mugun taushi, gefen gadon ta ajiye ta gami da zama ta tura ma yaron nata idanu, ita kanta ta yarda yaron nata ya rame fara ɗaya, a hankali yake sauke numfashi, ya sake yin fari ƙwal kaman ba jini, Amman fuskar tayi jawur kaman an gaggaura mashi maruka, Bilal ma kasa zama yayi ya koma ta gefe guda kusa da kan Al'ameen ɗin yaja ya tsaya, abokin nashi yake kallo da duk ya fita hayyacinshi lokaci guda, kuma ya san duk akan yarinyar nan ne, a yanda ya fahimta Alhajin na ma hajiya magana, in ko haka ne, Soyayya na ɗawainiya da abokin nashi, ba zai yadda bane kawai, ai in har taimako ne ba zaka yarda ka dinga shiga irin waɗan nan haɗarurrukan ba, ba tare da ka sallama wannan taimakon ba. Ganin da sukayi ya farka ne yana neman tashi lokaci guda gami da ƙoƙarin buɗe ido ya sanya Abie rugawa office ɗin likitocin domin ya kira su, ita kau Hajiya miƙewa tayi gami da kamo hannun Ameen ɗin ɗaya mai ɗauke da canula ta riƙe gam tana "Son buɗe idanun ka mune nan wurin da Alhajinka da Abokin ka Bilal🤣, don Allah ka tashi Son karka mutu ka barni". A hankali ya shig buɗe idanun nashi ya wara su akan mahaifiyar tashi, saurin maida idon yayi ya kulle, sai da Bilal ɗin yayi mashi magana ne ya sake buɗe idanun ya ɗora su kan Bilal ɗin da ya zagayo ta ɗaya ɓarin shima gami da ranƙwafowa sosai kusa da Al'ameen ɗin, hannu ya miƙa ma Bilal ɗin a hankali, shima ya kama gami da sakar mashi murmushin ƙarfafa guiwa, Soyayyar abokan guda biyu, abun burgewa ce da ban sha'awa, hakan ba ƙaramin ƙona ran hajiya kubra yayi ba, duk yanda tayi akan yaron nata ya kalle ta yaƙi kallon ta. Alhaji Mustapha da yake gefe cen zaune, yana kallon duk Abunda ke faruwa, hamdala yayi ga Allah, domin ya san dole ne ta fuskanci hakan ga ɗanɗan nata, tinda har zata iya yarda da ƙazafin neman mata da aka laƙaba mashi kuma ta hau ta zauna akai, hakan ce ta sanya sai bai taso ba bai kuma tanka ba, har saida yaga shigowar likita cikin ɗakin. Dudduba shi yayi gami da yi mashi ƴan aune aune, sannan ya ɗaura mashi ruwa gami da tsira Allura cikin ruwan, a hankali baccin ya sake ɗauke shi, to dama dai ya kulle idanun nashi gam, duk da sun san cewa ba bacci yake ba, Amman akwai Abunda ke kai kawo a zuciyar shi da har yake sa baya son kallon su. Jikin Hajiya kubra yayi sanyi matuƙa, gashi da ta kai kallon ta kan Alhaji ya kan auna mata harara har sai ta ji ba daɗi ta janye idon nata, Abie fa har yanzu kanshi a kulle yake saidai da yake shi ɗinma halin shi daban, baya shiga Abunda babu ruwa shi duk da sangartar shi, bakin shi yaja ya kulle gami da kishinhiɗawa kusa da alhajin tinda ance ya samu lafiya daya farfaɗo za'a basu sallama,tini bacci ya kwashe shi shima, tau an sha ƙauyawa day an gaji matuƙa, ga rashin barci, shi kau har yanzu Bilal ya kasa koda zama ne, duk da ƙafafun shi da sukayi matuƙar sanyi, baya jin zai iya zama har sai yaga farkawa Al'ameen ɗin. Har aka yi kiran salla suna nan zugum, ganin za'a tada sallah ne ya sanya Bilal tashin Abie suka nufi masallacin dake cikin asibitin, a daidai lokacin kuma Al'ameen ɗin ya sake farkawa, ganin mahaifiyar tashi a kusa dashi ne ya sashi saurin maida ido ya kulle, magiya ta shiga yi mashi akan ya buɗe idanun koda sau ɗaya ne ya kalle ta, hakan ce ta sanya shi buɗe idanun da suka koma ƴan ƙanana ya shiga kallon ta. Ba zai iya jure kallon nata ba ya maida ya kulle, ganin tinani zai dame shi ne ya sanya shi sake buɗewa gami da tashi zaune sosai, ya zare robar ƙarin ruwan da daf yake da ƙarewa, ya jingina bayanshi jikin bango, gami da jawo ƙafafun shi ya soke kanshi ciki. A haka suka tada su zaune ba mai cewa ƙala, da sauri Bilal ɗin ya isa bisa gadon gami da zama ya kamo hannuwan Al'ameen ɗin duka, shi kau Abie ganin haka sai ya koma zarce wa kiran likita yayin da Alhajin ya ƙara so yana faɗin "son ya ƙarfin jikin? Akwai inda ke maka ciwo?" Ɗago wa yayi yabi Alhajin nashi da kallo, gami da ɗan murmushin ƙarfin hali a fuskar shi, Amman bai ce kanzil ba, likitan ne ya shigo ya sake duddubawa gami da rubuta magunguna ya sallame su, da gargaɗin abar shi ya sake hutawa, kuma a guji tada mashi zancen da aka yi mashi har ya faɗi. Da to suka bishi, inda Abie da Bilal suka kama shi har zuwa cikin mota, a haka suka isa gidan babu mai tankawa kowa da Abunda yake saƙawa cikin ranshi. Har suka isa gidan babu wanda ya fito illa mai gadi da mudi driver, harda muɗi naka kama shi suka isa dashi sashe nashi gami da kwantar dashi suka ja mashi bargo, duk da ba barci yake ji ba, ya sha barci a asibiti hakan baisa ya Musa ba, illa iyaka kwance da yayi yananshaƙar ƙamshin humrar ta da ta bari ɗazu a sama gadon, abubuwa da dama na kai komo a ranshi, shi da yake ɗanɗanta tayi mashi haka ina ga ita baiwar Allah? Ganin ya juya masu baya ne, ya sanya su ficewa, jiki a sanyaye itama Hajiyar ta fita zuwa sashe nata, gami da yin sallah, kwanciya tayi bata so a dameta ne ya sanya ta kashe wayoyinta gami da kulle ɗakin baki ɗaya, shima Abie sashe shi ya koma haka Alhajin ma kwanciya yayi domin ya ɗan samu yayi bacci tin kafin abokan shi su fara isowa. Shima Bilal ɗin raɓawa yayi ya kwanta ta bayan Ameen ɗin gami da jan bargo, bacci yake so yayi, ya sha Alwashin ba zai taɓa tada mashi maganar ba in har ba shine yayi mashi ita ba, tinda likita yace a guji yin hakan, da haka har bacci Ɓarawo ya sace shi. Tin da safe aka fara shigowa ya shanye, da raguna sai kaji da aka kawo mota guda, to dama dai an sallama komai har masu gyara na nan gefe, masu suya kuma basa wahala tinda yau ne daren biki gida ko ina a cike yake, aiki aka hau yi fafa, bayan anyi break fast, dama yau babu wani event da zasu gabatar sai gobe idan an ɗaura aure ne zasuyi dinner, wannan kuma harda iyaye, ko da aka yi ƙoƙarin neman hajiya mama Talatu da Hajiya Laila ne suka hana suka ce tana bacci, su sukayi tsaye wajen komai har Hajiya sa'a ta iso itama suka cigaba da bada command, ita dai Hajiya Zainab da ƴan sashe ta saidai kallo da taimakawa, suma su Goggo Aisha duk sun fito a cewarsu ma ai sune masu tsayawa ayi komai kan idonsu tinda gidan ƙanen su ne, hatta su Goggo Hassana da Hussaina ba'a bar su a baya ba, kowa ta ɗebo zuri'arta kaf zuwa gidan bikin domin Alhaji Mustapha mutum ne na jama'a ba ruwan shi da nuna halin ƙyamar talaka ko mara shi, hakan ce ta sanya kowa ke matuƙar jin daɗin raɓarshi. Umma ta da domin Hajiya Zainab take yi, ganin itama taja baya sai itama bata je wajen aikin naman ba, duk da ba yanda zasuyi da wannan naman don ma dai akwai ma'aikata da aka ɗauko na musamman aka ƙara dasu mama sauden. Tin da nayi salla na koma na kwanta, jikina duk a mace yake na rasa dalili, da safe sai ga Afnan da Hafsat sun zo dubani, Naji sauƙi, na kuma ji daɗi sosai, sune ma suka sanya ni tashi har ma na karya gami da yin wanka, a haka suka janki dole ba don naso ba na bisu sashe nasu na amare, itama dai ummata taji daɗin hakan, domin bata son kwanciyar da nake yawan yi, gashi ta kula jikina a sanyaye, in nazauna nan kuma ba abokin fira saidai inta tinani. Itama wanka tayi ta fice zuwa sashe nasu Hafsat domin ta gani ko da Abunda zata kama. Wata ƴar matashiya yarinya ce tayi sallama ɗakin namu, amsawa mukayi mu duka da muke zazzaune ana ta fama fira da bada labarin event ɗin da aka yi jiya, "Wacece Suhana a cikin ku?" ta faɗa cike da yatsina, nuna ni Hafsat tayi gami da cewa "gata nan lafiya dai ko?" "eh lafiyar kenan, Saudat ce ke kiran ta" tana gama faɗar haka ta juya gami da ficewa. Afnan ce ta miƙe gudun kada a wulaƙanta ni bayan naje, "muje in raka ki" jerawa mukayi har ɗakin nasu gami da sallama, mun taddasu zazzaune bisa gado wasu a sama carpet, sun yi break oast ko ina gaja gaja, wasu ma duk babu kaya jikin su illa na barci ƴan yalolo. "Ɗakin nan zaki gyara mana ki wanke mana toilet yayi datti gashi muna son yin wanka" Saudat ɗin ta faɗa cikin gadara da nuna isa, binsu nashigayi da kallo, su su ɓata don son neman magana Amman nice za'a kira in gyara bayan an dakatar damu daga aikin da mukeyi a cikin gidan? Afnan ce tayi saurin cewa "Amman fa Aunty Saudat an hana suhan aiki a cikin gidan nan, ko dai maree za'a kira maki?" "Ke" ta daka mata muguwar tsawa da har saida na razana, su kau sauran ƙawayen nasu ƙyalƙyalewa sukayi da dariya, wasu na latsa waya wasu ma system ce a gaban su ba Abunda ya sha masu kai. "Je na kira da zaki biyo wa? Ko kin biyo ta ne ki gani in aiki zan sanya ta ki hana ta? Zaman me suke yi mana a cikin gida? In banda son su mallake mana yaya su mallake Abunda ya mallaka? To dole ne ayi mana aiki wallahi ko a tattara a ƙara gaba" ta faɗa cikin matuƙar ɗagawa da karara zance yanda zai shiga har cikin ƙwalwa ta, ya kuwa shiga a sanyaye na kalli afnan ina mai cewa "Afnan bashi kawai zanyi, ki koma ɗaki don Allah" Afnan ɗince ta ƙuta gami da ficewa a hasale ta koma ɗakin nasu, ni kuwa tattare hijab nayi na shiga aiki, wata daga cikin ƙawayen nasu, wadda na kula tana yawan zubda mannhabaicinlomuta da dama in suna falo zaune ce tayi ƴar dariya cikin salo na son cin mutumci ta shiga faɗin "Haba Saudat bari wannan maganar mana, ai yayan namu ya wuce ajin wannan yo in banda ma ke da abunki me zai ci da ƴar aiki irin wannan? Dubeta fa ai in ba don Allah ya sanya tana da ɗaske ba da ba ƙaramar mummuna aka yi nan ba, duk tarin matan da suke sonshi a faɗin garin na Abuja da kewaye ya rasa wadda zai kula sai wannan? " ta ƙarshe tana mai nuna ni da hannu. Shewa suka sany gami da tafawa, ni kuwa zuciya ta zo man iya wuya, saidai bana son tashin hankali ummata ba lafiya ce gareta ba, inko har na tanka abun kanta zai koma, gara a lallaɓa a rabu lafiya duka saura kwana nawa ne a rabun? Girgiza kaina nayi gami da cigaba da aiki, raina na matuƙar ƙuna, Allah sarki Ya Ameen a kammu fa zai gamu da ƙalubale da dama tinda yace yana so ya taimake mu. A haka na kammala masu gami da ficewa daga ɗakin a matuƙar sanyaye, maganganu marasa daɗi dai yau na sha su, a hakan ma wani abun baya faɗuwa, har kwalla saida nayi ta baƙin ciki, Amman Allah ya san damu bai manta damu ba. Ina komawa sashe namu Hafsat ta balbaleni da faɗa wai akan me nayi aikin ban ce mata banayi, ni kau ce mata nayi nayi aikin ne saboda ummata kada abun ya shafe ta, tana jin haka taja baki tayi shiru Amman fa ranta ya gama ɓaci, ita kuwa afnan haƙuri ta bani tana cewa sai ta gaya ma ya Ameen ɗin, nice na hana ta ina mai cewa haba ai ko ba komai su ɗin yayye na ne ba Abunda ba zan iya masu ba, saidai in har basu buƙata ba. Muna cikin haka ne wayata ta ɗauki tsuwwa alamar an mani saƙo, dubawa nayi mamaki fal a fuska ta, Ya Ameen ne ya turo mani saƙo kaman haka _Ya ƙarfin jiki, kin dai sha magani ko?_ Ɗan murmushi na sauke, raina yyai fari ko ba komai dai idan wani ya ƙi ka wani zai soka, duk da su ɗin sun nuna man halin ƙiyayya ga ƴaƴan su nan yana nuna man halin kula. Ban maida mashi da reply ba na share, muka cigaba da fira, wani saƙon ne ya shigo _"kina dai lafiya ko?"_ Wannan karon nima maida mashi nayi da cewa _" Eh yaya ina lafiya, nagode da kulawa"_ Shigowar saƙon nata ne ya sanya shi tashi zaune, dama dai yana son yaji halin da take ciki ne, kada ace mahaifiyar tashi ta koma ta sake yin wani abun kuma. Bilal ɗin dai na kallon shi kanzil bai ce mashi ba, sai faman ɓoye murmushi da yake yi, ajiye wayar tashi yayi gami da shige wa toilet domin yin wanka saboda yanzun kusan ƙarfe sha biyu da rabi lokacin sallar juma'a ya ƙara to. Saida Bilal ɗin yaji alamar ya fara watsa ruwa sannan ne ya ɗauki wayar tashi ya shiga duba saƙonni. Tiryan Tiryan ya shiga bin saƙonnin da suka aike wa juna, saidai shi baicin karo da wani saƙo dake nuna soyayya ba, illa iyaka kulawa da kuma saƙon godiya da ta taɓa aike mashi da daɗewa bayan ya bata waya. Jin alamar fitowa ya sanya shi saurin kashewa ya ajiye, shi dama ya riga ya shirya Al'ameen ɗin yake jira, miskilancin na na na a kai, ya sanya bai tanka ma Bilal ɗin ba har ya gama shiryawa, saidai yana kula da Bilal ɗin da irin kallon da yake bin shi, basarwa yayi yana faɗin zaka ci ubanka ne ai. Daidai parking lot muka haɗu dasu, tin daga nesa na hango su, hakan ce ta sanya ni ƙara ɗaga ƙafa, afnan ce taja ta tsaya tana cewa Laa ga yaya bari yazo mu gaisa tin jiya rabona dashi, Ganin Hafsat ɗinma ta tsaya dole nima naja na tsaya. Cikin tafiyar shi ta ingarma namiji suka ƙaraso gare mu, afnan bata yi wata wata ba ta rungume shi tana faɗin oyoyo yaya, shima rungume ta yayi kaɗan yana mai janye ta daga jikin shi ya shafi gefen fuskar ta "Ya kike sweet Heart? Ya faɗa cikin kulawa hannuwan shi cikin nata," Lafiya Lau Bro love" Mu kau ganin hankalin shi na ga Afnan ɗin sai muka shiga gaida Bilal, Bilal ɗin da ya kafe ni da ido ne ya amsa mana, duk hankalin shi na a kaina, har saida na tsargu na duƙar da kaina, Hafsat ce na ji tana gaida Ya Ameen ɗin shi kuma ya amsa mata cikin kulawa, ɗago kaina nayi da niyyar gaida shi idanun mu suka sarƙe cikin na juna, wani irin shirk ne Naji ya jani kaman an jona man wutar lantarki, yayi kyau cikin dakakkiyar shadda shi ruwan sarari samaniya, hula da takalmin dake kanshi duk kalar shadda ne, saidai hannun shi dake ɗaure da haɗaddiyar agogo ƙirar kamfani gucci riƙe yake da makullan mota, fuskar nan tayi fayau da ita, sai ƙasumbar da take kwance a haɓarshi ce ta ba fuskar damar ƙara haske idanun shi manne ikin fari tar ɗin glass da ya ƙara fiddo da kyaun fuskar tashi. Saurin sadda kaina nayin ƙasa ina mai matse ƴan yatsu na, domin wani abu Naji ya tsira mani tin daga kai har tafin ƙafa ta, "Ba gaisuwa?" Naji ya faɗa, saurin ɗaga kaina nayi gami da kallon shi ina addu'ar dai ace ba dani yake ba. Idanuwan shi kuwa fes a kaina, "Ina yini" na faɗa ina mai son kauda kaina ga barin kallon shi, ji nake yi duk ya cika gidan, irin Abunda nake fuskanta kenan a duk lokacin da zan ɗora idona a kanshi. "Ba zan amsa ba, tinda saida na roƙa" ya faɗa yana mai zagaye mu ya wuce zuwa ga motar shi, da tini Bilal ya isa yana jiran shi, da kallo na bishi har ya wuce, lallai ya Ameen ya haɗu ta ko ina, cikakken namiji ne mai tarin kwarjini.... Ɗan ɓangazata Afnan tayi da kafaɗa ganin yanda nabi yayan nata da kallo tana murmushi cikin zaulaya take cewa "Lallai Aunty Suhan yayan nawa yana yin ki, ga dukkan alamu kema kina yin shi na gani" Ɗan firgigit na dawo hayyaci na daga da tinanin da na tafi na wucin gadi, buɗe baki nayi da da niyyar cewa wani abu muka ji cikin kakkausar murya daga bayan mu ance *Al'ameen* Dukanmu juyawa mukayi gami da maida hankalin mu wurin Hajiya Kubra da take tsaye tin ɗazu tana nazarin mu ta fara tako wa a hankali cikin isa da taƙama fuskar ta tam babu fara'a ko alama a fuskar Sanye take cikin wata haɗaɗɗiyar atamfa anyi mata ɗinkin nan mai A shape marar breast cup, sai ɗan kunne da sarƙar gold gami da abun hannun su danƙara danƙara sai walwali takeyi. Tini jikina ya fara ɓari naja baya a sukwane, ni da Al' ameen kawai na lura take kallo, Al'ameen wanda har ya sanya key zai buɗe mota ya fasa gami da dawowa inda taja burki ta tsaya gami da cewa "Gani mom Lafiya dai ko?" Ya faɗa yana mai kafe ta da idanu, cikin fushi ta buɗe baki gami da cewa........ 😛😝😜🤪😜🤪😛😝🤪😜😛😝 ~ku tara a Page na gaba~ ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~27~* *Page ɗinki ne Aishatu Babayo, muna matuƙar yinki, kuma muna jin daɗin comment ɗinki matuƙa, ɗaukacin ƴan golden pen suna gaisheki* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° "Kasha maganin ka ne da kake ƙoƙarin fita?" Mom ɗin tashi ta faɗa, har yanzu fuskar ta a matuƙar ɗaure take. Gyaɗa mata kai kawai yayi, ba tare da ya tanka mata ba, kallon ta ta maida kan Bilal da yake tsaye ta bayan Al'ameen kaɗan haka, yana gaida ta. Amsawa tayi gami da cewa" Bilal ka kula fa da abokin ka sosai, kada ka bari ya wahala Kaga dai Abunda Dr. Yace". Ɗaga mata kai Bilal ɗin ya shiga yi yana cewa "consider it done Mom" Hafsat na tsinkayi muryar ta tana gaida ta, hakan ce tasa nima na gaishe ta, gaisuwar Hafsat ɗin kawai ta amsa, itama a daƙile, hakan ce ta sanya na ƙara shan jinin jikina gami da ƙara ɗan matsawa baya. Afnan ce ta ruga kusa da yayan nata, daidai lokacin da Mom ɗin ta juya da niyyar barin wurin, maganar Afnan ɗince ta dakatar da ita da barin wurin da take niyyar yi. "Yaya me ya same ka? Baka lafiya ne? Yaushe kaje hospital bamu sani ba? Duk ta jero mashi tambayoyi tana mai kamo hannuwan shi gami da dudduba jikin shi da idanu. Ɗan zare hannun shi yayi yana mai shafo gefen fuskar ta kaɗan," Am OK Dear Love, ba Abunda ke damuna" ya faɗa yana mai juyawa ya nufi jikin motar tashi, domin ya kula sosai da rashin amsa gaisuwar da mahaifiyarshi tayi ma Suhan ɗin. Bai jira komai ba ya buɗe motar gami da shiga, shima Bilal ɗin shiga yayi, ganin haka ne Hafsat ɗin ta shiga jan hannuna tana cewa "zo muje Suhan, Afnan ɗin zata tadda mu" Binta na shiga yi, muka shiga tafiya, daidai lokacin da Mom ɗin ta bimu da kallon tsana da jin haushi ƙarara a fuskar ta. Afnan ce ta bita da kallo daidai lokacin da ta juya da niyyar wucewa sashe kaka zuwaira, girgiza kanta ta shiga yi tana mai ɗaga ma yayan nata hannu har ya fice daga gidan. Bayan an sauko masallacin ne kiran Alhaji Mustapha ya shiga wayar tashi, umurtar shi yayi da yazo gidan gonarshi yana son ganinshi yanzu shi da Bilal ɗin. Sai da ya ɗauki hanyar gidan gonar ne, yake sheda ma Bilal ɗin kiran da dad ɗin nashi keyi masu. Har suka isa babu mai tanka ma wani. Sun tadda falon cike da manyan mutane, sai firar su suke cikin nishaɗi, ga sanyin Ac na ratsa su, wucewa sukayi cen gefe gami da zama ƙasa domin girmamawa ga iyayen nasu. Miƙa mashi wata kyakkyawar emvelop mai ado da ruwan gold dad ɗin yayi yana mai cewa duba nan ka gani. Amsa yayi cikin girmamawa ya shiga dubawa, bayan ya gama karantawa ne ya miƙa ma Bilal ɗin, ya maida duban shi kan mahaifin nashi yana mai neman ƙarin bayani. Dad ya gyara zama gami da duban yaron nashi cikin soyayya, farin ciki fal a kan fuskar shi, sannan ya cigaba da cewa"Daga sarkin Katsina ne, haɗin guiwa da sauran sarakunan yankin namu na arewa, saboda yanda kake taimakon matasa ƴan uwanka da basu ayyukan yi, da taimaka masu da jari, da koya masu sana'oi, suka ga ya dace su girmama ka domin suma sauran matasan masu hannu da shuni suyi koyi da kai, sun yanke shawarar naɗa ka sarautar *yariman matasan arewa* kuma suna buƙatar daga yau zuwa gobe ka shirya komai domin a goben ne zasuyi maka naɗin bayan kammala ɗaurin aure, sannan kuma akwai hawan daba bayan kammala lunching ƙarfe biyar na yamma, da fatan zaku je ku shisshirya komai da ake da buƙata, sannan inaso ka aika manyan motoci guda biyu Katsina da zasu kwaso iyayen matar Aleeyu tin da safe su juyo dasu ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~27~* *Page ɗinki ne Aishatu Babayo, muna matuƙar yinki, kuma muna jin daɗin comment ɗinki matuƙa, ɗaukacin ƴan golden pen suna gaisheki* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° "Kasha maganin ka ne da kake ƙoƙarin fita?" Mom ɗin tashi ta faɗa, har yanzu fuskar ta a matuƙar ɗaure take. Gyaɗa mata kai kawai yayi, ba tare da ya tanka mata ba, kallon ta ta maida kan Bilal da yake tsaye ta bayan Al'ameen kaɗan haka, yana gaida ta. Amsawa tayi gami da cewa" Bilal ka kula fa da abokin ka sosai, kada ka bari ya wahala Kaga dai Abunda Dr. Yace". Ɗaga mata kai Bilal ɗin ya shiga yi yana cewa "consider it done Mom" Hafsat na tsinkayi muryar ta tana gaida ta, hakan ce tasa nima na gaishe ta, gaisuwar Hafsat ɗin kawai ta amsa, itama a daƙile, hakan ce ta sanya na ƙara shan jinin jikina gami da ƙara ɗan matsawa baya. Afnan ce ta ruga kusa da yayan nata, daidai lokacin da Mom ɗin ta juya da niyyar barin wurin, maganar Afnan ɗince ta dakatar da ita da barin wurin da take niyyar yi. "Yaya me ya same ka? Baka lafiya ne? Yaushe kaje hospital bamu sani ba? Duk ta jero mashi tambayoyi tana mai kamo hannuwan shi gami da dudduba jikin shi da idanu. Ɗan zare hannun shi yayi yana mai shafo gefen fuskar ta kaɗan," Am OK Dear Love, ba Abunda ke damuna" ya faɗa yana mai juyawa ya nufi jikin motar tashi, domin ya kula sosai da rashin amsa gaisuwar da mahaifiyarshi tayi ma Suhan ɗin. Bai jira komai ba ya buɗe motar gami da shiga, shima Bilal ɗin shiga yayi, ganin haka ne Hafsat ɗin ta shiga jan hannuna tana cewa "zo muje Suhan, Afnan ɗin zata tadda mu" Binta na shiga yi, muka shiga tafiya, daidai lokacin da Mom ɗin ta bimu da kallon tsana da jin haushi ƙarara a fuskar ta. Afnan ce ta bita da kallo daidai lokacin da ta juya da niyyar wucewa sashe kaka zuwaira, girgiza kanta ta shiga yi tana mai ɗaga ma yayan nata hannu har ya fice daga gidan. Bayan an sauko masallacin ne kiran Alhaji Mustapha ya shiga wayar tashi, umurtar shi yayi da yazo gidan gonarshi yana son ganinshi yanzu shi da Bilal ɗin. Sai da ya ɗauki hanyar gidan gonar ne, yake sheda ma Bilal ɗin kiran da dad ɗin nashi keyi masu. Har suka isa babu mai tanka ma wani. Sun tadda falon cike da manyan mutane, sai firar su suke cikin nishaɗi, ga sanyin Ac na ratsa su, wucewa sukayi cen gefe gami da zama ƙasa domin girmamawa ga iyayen nasu. Miƙa mashi wata kyakkyawar emvelop mai ado da ruwan gold dad ɗin yayi yana mai cewa duba nan ka gani. Amsa yayi cikin girmamawa ya shiga dubawa, bayan ya gama karantawa ne ya miƙa ma Bilal ɗin, ya maida duban shi kan mahaifin nashi yana mai neman ƙarin bayani. Dad ya gyara zama gami da duban yaron nashi cikin soyayya, farin ciki fal a kan fuskar shi, "Daga sarkin Katsina ne, haɗin guiwa da sauran sarakunan yankin namu na arewa ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~27~* *Page ɗinki ne Aishatu Babayo, muna matuƙar yinki, kuma muna jin daɗin comment ɗinki matuƙa, ɗaukacin ƴan golden pen suna gaisheki* °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° "Kasha maganin ka ne da kake ƙoƙarin fita?" Mom ɗin tashi ta faɗa, har yanzu fuskar ta a matuƙar ɗaure take. Gyaɗa mata kai kawai yayi, ba tare da ya tanka mata ba, kallon ta ta maida kan Bilal da yake tsaye ta bayan Al'ameen kaɗan haka, yana gaida ta. Amsawa tayi gami da cewa" Bilal ka kula fa da abokin ka sosai, kada ka bari ya wahala Kaga dai Abunda Dr. Yace". Ɗaga mata kai Bilal ɗin ya shiga yi yana cewa "consider it done Mom" Hafsat na tsinkayi muryar ta tana gaida ta, hakan ce tasa nima na gaishe ta, gaisuwar Hafsat ɗin kawai ta amsa, itama a daƙile, hakan ce ta sanya na ƙara shan jinin jikina gami da ƙara ɗan matsawa baya. Afnan ce ta ruga kusa da yayan nata, daidai lokacin da Mom ɗin ta juya da niyyar barin wurin, maganar Afnan ɗince ta dakatar da ita da barin wurin da take niyyar yi. "Yaya me ya same ka? Baka lafiya ne? Yaushe kaje hospital bamu sani ba? Duk ta jero mashi tambayoyi tana mai kamo hannuwan shi gami da dudduba jikin shi da idanu. Ɗan zare hannun shi yayi yana mai shafo gefen fuskar ta kaɗan," Am OK Dear Love, ba Abunda ke damuna" ya faɗa yana mai juyawa ya nufi jikin motar tashi, domin ya kula sosai da rashin amsa gaisuwar da mahaifiyarshi tayi ma Suhan ɗin. Bai jira komai ba ya buɗe motar gami da shiga, shima Bilal ɗin shiga yayi, ganin haka ne Hafsat ɗin ta shiga jan hannuna tana cewa "zo muje Suhan, Afnan ɗin zata tadda mu" Binta na shiga yi, muka shiga tafiya, daidai lokacin da Mom ɗin ta bimu da kallon tsana da jin haushi ƙarara a fuskar ta. Afnan ce ta bita da kallo daidai lokacin da ta juya da niyyar wucewa sashe kaka zuwaira, girgiza kanta ta shiga yi tana mai ɗaga ma yayan nata hannu har ya fice daga gidan. Bayan an sauko masallacin ne kiran Alhaji Mustapha ya shiga wayar tashi, umurtar shi yayi da yazo gidan gonarshi yana son ganinshi yanzu shi da Bilal ɗin. Sai da ya ɗauki hanyar gidan gonar ne, yake sheda ma Bilal ɗin kiran da dad ɗin nashi keyi masu. Har suka isa babu mai tanka ma wani. Sun tadda falon cike da manyan mutane, sai firar su suke cikin nishaɗi, ga sanyin Ac na ratsa su, wucewa sukayi cen gefe gami da zama ƙasa domin girmamawa ga iyayen nasu. Miƙa mashi wata kyakkyawar emvelop mai ado da ruwan gold dad ɗin yayi yana mai cewa duba nan ka gani. Amsa yayi cikin girmamawa ya shiga dubawa, bayan ya gama karantawa ne ya miƙa ma Bilal ɗin, ya maida duban shi kan mahaifin nashi yana mai neman ƙarin bayani. Dad ya gyara zama gami da duban yaron nashi cikin soyayya, farin ciki fal a kan fuskar shi, sannan ya cigaba da cewa"Daga sarkin Katsina ne, haɗin guiwa da sauran sarakunan yankin namu na arewa, saboda yanda kake taimakon matasa ƴan uwanka da basu ayyukan yi, da taimaka masu da jari, da koya masu sana'oi, suka ga ya dace su girmama ka domin suma sauran matasan masu hannu da shuni suyi koyi da kai, sun yanke shawarar naɗa ka sarautar *yariman matasan arewa* kuma suna buƙatar daga yau zuwa gobe ka shirya komai domin a goben ne zasuyi maka naɗin bayan kammala ɗaurin aure, sannan kuma akwai hawan daba bayan kammala lunching ƙarfe biyar na yamma, da fatan zaku je ku shisshirya komai da ake da buƙata, sannan inaso ka aika manyan motoci guda biyu Katsina da zasu kwaso iyayen matar Aleeyu tin da safe idan Allah ya kai mana ranmu sai su juyo dasu, sannan ina so ka tabbatar da cewa an gama tsara komai na wurin da za'ayi lunching ɗin, akwai manyan mutane da zasu halarta harda shugaban ƙasa da sarkin musulmai, sannan muna da baƙi da zasu fara isowa a yau ɗinnan muna so a kama hotel mai kyau da zasu ji daɗin zama saboda mutanen waje ne" Ya faɗa yana nazarin yaran nashi guda biyu da suke durƙushe gaban shi. Fara'ar dake fuskar Bilal zamu iya cewa ma tafi ta kan fuskar Ya Ameen ɗin, wannan ai wata ɗauka ka ce da Allah yayi ma abokin nashi, ko ba komai dai ya san ayyukan Alkhairin da abokin nashi keyi ya zaga dukkan sassan nigeria ba ma arewa kaɗai ba. Cikin matuƙar jin daɗi suka shiga yin godiya basu fita ba saida dad ɗin nasu ya sallame su, shi fa Al'ameen mamaki kawai yake yi, a ina manyan ƙasar nasu suka san da duk abubuwan da yake yi, bai ƙara sarewa ba saida yaji ana sanarwar naɗin nashi da za'ayi a gobe idan Allah ya kai mu, a hanyar su ta komawa gida. Sun isa gidan ne, sannan suka kira mudi driver gami da bashi makullin gare jin nasu dake cen gefen gidan gami da umurtar shi da ya fiddo manyan mitocin nan ƙirar homa bomber ya bada a wanke su ɗauki hanyar Katsinan a yanzu nan. Ficewa suka sake yi daga gidan, saboda gidan ya ƙara ɗinkewa da jama'a ta ko'ina duk mata ne ga wasu manya manyan canofee da ake ta kakkafawa a harabar gidan gefe guda kuma wasu manyan speakers ne aka kakkafa kaman za'a tashi gidan. "yanzu ina muka dosa ne? Ni fa wallahi duk ma na rasa ta ina zamu fara, kayan da nayi niyyar Sanyawa yanzu dole in cenza su in nemi masu babbar riga, duk yanda kuwa nake gudun ta saboda zafin nan da akeyi" Al'ameen ya faɗa yana mai kallon Bilal ɗin da hankalin shi yake kan tuƙin da yake yi. "Ni na san ta ina zamu fara, kai dai kayi kallo kawai" ya faɗa da ƴar Fara'ar shi, mamakin abun har yanzu bai gama sakinsu ba. Da kallo ya shiga binnhanyar da suke bi har kawo lokacin da sukayi parking daidai wani tanƙamemen shago an rubuta *Your Choice* a jiki. Je rawa sukayi har cikin shagon da aka ƙawata shi da farin glassai suna ta ɗaukar idanu. Kaya ne maƙilbiya kallon ka, shaddoji ne ƴan ubansu an masu ɗinku a irin na manya, sun sha aiki matuƙa, kowacce tare da hula tangaras kalar zaren aikin shaddar, gefe guda kuma ƙananan kaya ne iya kallon ka da hange ka, yayin da sashe guda na shagon kuma bugaggun takalma ne kalar na sarakai da manyan masu kuɗi. Miƙewa mai shagon yayi gami da tarar su cikin farin ciki, domin ya daɗe da sanin Al'ameen ɗin tin ba yanzu ba, hasali ma Al'ameen ɗin shine ya fara bashi jari a rayuwar shi, bayan ya gama makarantar design da Al'ameen ɗin ya buɗe tin yana ƙasar america. Gaishesu ya shiga yi cikin girmamawa, basu ɓata lokaci ba Bilal ɗin ya faɗa mashi me yake tafe dasu, da taimakon shi suka zaɓi kayan da suke so. Shaddoji ne farare ƙal suka ɗ auka, duk da cewa ta Al'ameen tafi haɗuwa, sai ƙamshi take yi da walwali, anyi mata aiki da riyal blue ɗin zare, yayin da hular ma take kalar royal blue ɗin, sai takalmin shi irin na sarauta mai half cover da lanƙwasa ya sha adon farare duwatsu sai ɗaukar idanu yake yi. Shima Bilal ɗin ya zaɓi masu kyau, saidai shi kuma kalar nashi farar shadda ce da aikin Brown, hakan ne ya sanya shi ɗaukar takalmi Brown masu matuƙar kyau da tsari, sai Abie da suka ɗaukar ma kalar sararin samaniya da aikin bula mai ruwan omo. Sashen masu haɗewa aka miƙa kayan, daidai jikin su aka auna sannan aka haɗe, Al'ameen ɗinne mai cewa a maida mashi babbar rigar fitted yayin da Bilal ɗin ke cewa a ƙyale shi ayi mashi yanda zata yi kyau. Su sha mamaki matuƙa lokacin da suka zo biyan kuɗin yace ba zai amsa ba, ba yanda ba suyi ba yace Sam Allah ya sauwaƙe ya amshi kuɗin su, ganin ba zasu yarda ba ya sanya shi faɗin bari ya gaya masu dalilin shi na ƙin amsar kuɗin nasu. Tiryan Tiryan ya basu labarin Alkhairin da Al'ameen ɗin yayi mashi, sannan ya ƙara da faɗin "Haba yallaɓai, ni wane irin butulu ne kuwa da har zan iya amsar kuɗin kaya a hannun ka? Bayan dukkan shagon nan da yanda na zama a rayuwa kai ne sila, yanzu haka ƙanena yana aiki a kamfanin ka na sarrafa hatsi a Lagos, dama ban daɗe da gama sauraren radio ba, Naji irin gagarumin naɗin da za'ayi maka a goben idan Allah ya kai mu, bansan zaka zo ba i da har gida zan kawo maka da kaina, Amman ko yanzu bata ɓaci ba, insha Allah kuwa zan halarta harda iyali na baki ɗaya, Mungode Mungode Allah ya shirya maka zuri'abyasa ka gama da iyayen ka lafiya" Ko ba komai wannan kaɗai ya isa ya ƙara sanya shi farin ciki, ashe dai shi alkhairi ko ya yake baya da kaɗan kuma daɗi ke gareshi, gashi Alkhairin da yayi ma mata san a lokacin da aka yaye su, har shi ya girbi abinda ya shuka. Sun mashi godiya matuƙa, yayin da Al'ameen ɗin ya bashi ƙaton shi, gami da cewa bayan hidima ta kwaranye ya neme shi su sake gaisa wa sosai, har bakin motar su ya raka su, yana mai ɗaga masu hannu har suka fice daga plazar, sannan ya juya da maɗaukakin farin ciki, dama tini ya daɗe yana addu' ar Allah ya haɗa shi da Al'ameen ɗin ko a hanya ne ya ƙara mashi godiya, domin ya san ba lallai bane in ya neme shi ya same shi. Daganan suka zarce kasuwa, inda suka shiga neman kayan kwalliyar doki, da ƙyar suka samu, domin har Al'ameen ya gaji har ya fara faɗin su koma gida hakanan shi fa ya fara gajiya da wannan wahalar sannan suna da sauran ayyukan da zasu aiwatar da yawa kafin zuwan daren. Kalar kayansu kowa ya ɗauka, sun kwaso kayan kwalliya doki sosai, bayan da Bilal ɗin ya tambayi abokin nashi dokin da zai hau, "Farar Goɗiyar" ya bashi amsa a taƙaice cikin gajiyawa. Ɗan murmushi yayi shi kuma yana faɗin "sai in hau gwaska ni, shi kuma Abie ya hau kule" Bai tanka mashi ba har suka iso gidan, Barde mai tsaron barar suka kira gami da bashi kayan dokin suna faɗin ya shirya su goben bayan gama cin abincin ɗaurin auren, sannan suka faɗa mashi dawaman da zasuyi amfani dasu a cikin dawakan dake gidan. Saida suka ajiye kayan sannan suka watsa ruwa gami da cenza kayan jikin su zuwa ƙananan kaya sannan suka fice daga cikin gidan bayan sun ajiye motar suka cenza wata. Ganin yau bamu da aikin komai, ya sanya mu kwanciya muka huta bayan mun ware duk Abunda muka san zamuyi amfani dashi gobe, to bamu da yawa dama, mu bakwai ne harda amaryar sai mai kwalliyar mu da suka taho ta ita tinda ga Katsinan yasa muka kama mu takwas, ɗaki ne tanƙameme da toilet, bamu takura ba sosai komai namu tsaf yake, kaka zuwaira kaɗai muka fita muka gaida yau sai hafsat ɗin da taje Sashen mamanta, cen ta tadda ummata har take tambayar ta ina ina? Take ce mata ina ɗaki lafiya ta lau. Washegari tin da asubar fari aka farka kusan ince dukka gidan, bayan gama sallah ne aka shiga ɗora Abunda za'a karya, tinda dugu-dugu aka yi break fast, sai kuma aka shiga hidima wanka, masu girka abinci nayi masu sake shirya harabar gida inda za'ayi zaman cin abinci nayi. Mu dai bamu tashi ba sai wajen ƙarfe takwas na safe, mun tadda an kawo mana kayan karin mu, hakan yasa saida muka gama wanka duka sannan muka zauna zaman karyawa, amarya aka fara shirya mawa, mai kwalliya ta hau aikin ta na cakare amaryar, yayi da muku a muka hau gyara ɗakin namu tsaf. Tin da aka fara hidimar biki banga afnan ɗin taje sashen nasu ba, Sam ta fita harkar su kaman ba ƴan uwanta ba, koda yake hali ya bambanta Shiyasa basa shiri, Amman da yake halin na Saudat da Nihal ɗin ɗaya ne gashi nan kansu a haɗe yake kaman ƴan biyu, saidai wani lokacin aunty Feena kan aiko mata da Nasreem da Ayan masalan ma in tana wata hidimar da yake ita a ɗaki ta ta sauka da yake cikin babban sashen gidan inda aka sauki ƴan uwa Hajiya Kubran. Dama tini ta maido kayan ta kaf da ta san zata yi amfani dasu cikin hidimar bikin. Mun gama gyaran kenan muna hutawa wata ƴar matashiya budurwa tayi sallama, yaran dangin hajiya kubran ne, da suke cike da jiji da kai da tinƙahon su ɗin wasu ne, babu wanda ta gaida ta shiga faɗin "wacece suhan wai? To taje Aunty Saudat na kiranta a ɗakin nasu" tana gama faɗar haka ta fice daga ɗakin ba tare da ta tsaya jin me za'a faɗa ba. Tinawa da wulaƙanci da sukayi mani shekaranjiya ne ya sanya ni zamana ba tare da na raya ma raina zuwa ba, har aka gama ma Hafsat ɗin kwalliyarta aka fara ma Afnan da tace lallai sai an fara yi mani ai ina gaba da ita, kuma nice babbar ƙawa, daƙyal dai ta haƙura aka fara mata, ganin yanda nakafe sai an gama mata sannan za'ayi mani. Ba sallama saidai muka ganta tsulum cikin ɗakin. Da matuƙar fushi ta maida kallon ta a kaina, bayan tabo kowa dake cikin ɗakin da kallon baku isa ba. "Dame kike taƙama ne da har zamu sanya a kira ki kiƙi zuwa? Ta jefo man tambaya, Afnan ce riƙe da ƙugu ba'i na cin ta cikin zuciya, ko kallon inda take banyi ba, haka in bangon dake ɗakin ya tanka mata tau nima na tanka mata. Hakan yayi bala'i ƙona mata rai kuwa, cikin hasala tace "Aikin mu anan gidan shine aikin ki, kuma a ƙarƙashin Alfarmar Ya Ameen kuke zaune acikin gidan nan, sannan ina so ne in faɗa maki cewa ke baki kai matsayi da har mu zamu ce ga Abunda mukeso kiyi mana ba ki ƙiya, kuma ba zaki taɓa kai matsayi ba, kwaɗayayyun banza da wofi, ke da waccen sululu kasa ɗin uwar taki..... " *" Aunty Nihal ya isa"* *"Ya Isa Hakanan, in ba haka ba wallahi zanje na faɗa ma Ya Ameen ɗin"* Afnan ce take dakatar da ita cikin ƴar tsawa, ranta in ya kai dubu tau ya ɓaci, bata ma san ta ƙwace fuskar taba daga kwalliyar da akeyi mata, ni kau tini fuska ta ta jiƙe da ruwan hawaye, ji nake kaman ƙjrji na zai tsage zuciya ta ta fito. Wannan cin fuska yayi yawa, gaban ƙawayen Hafsat da basu san ko ni ɗin wacece ba ta biyo ni nan tana ƙasƙantar dani, tini na ruahe da kuka mai sauti, domin ina jin in har banyi ba zuciya ta zata iya bugawa, Hafsat ɗince ta ƙara so wajen da nake zaune bisa gado bansan lokacin da na tashi zaunen ba. Bubbuga baya na ta shiga yi, ganin haka ne ya sanya ni rungume ta, Allah ma yaso bata kai ga sanya kaya ta ba, da tini zan cukuikuye su, iri. Daƙumar da nayi mata. Ita kau Nihal jin hakan da tayi ya sanya ta ficewa tana mai saukin maganganu masu zafi a kaina da umma ta, Afnan ɗince ta miƙe gami da ƙarasowa inda nake ta shiga bani haƙuri, gami da cewa "Bari inzo, ai sai na faɗa ma Yayan tinda su dai basa son zaman lafiya" Nice na riƙo hannun ta ina mai girgiza mata kai cikin kuka, fasawa tayi gami da shiga lallashi na, daƙyar suka samu nayi shiru, babu wanda bai tausaya man ba a cikin ɗakin Allah wadai suka shiga yi ma Nihal ɗin Afnan na jinsu ƙala bata ce ba, to me zata ce ai halinka shi ake faɗi ko bayan ba ranka kuwa. Manyan kuloli ne aka shiga shigowa dasu cikin gidan, rumfa guda aka ware da aka jejjera abinciccikan, sai ma'aikata masu serving da aka zube saidai Abunda mutum yake da buƙata a kai mashi, babu kalar nau'ikan abincin da babu acikin gidan nan, har ma da na gargajiya ga masu buƙata, kama daga su Alkubua, fankaso, waina, dambun shinkafa lafiyayye da ya sha zkgala da kayan lambu, to dama dai kowa ya san Katsina wa da wannan cimaka kuma bikin nasu ne, wannan ce ta sanya basu yada al'adar tasu ba. Kaman yanda aka jejjera abinci cika da lemuka kala kala, haka ma acen tanƙameme hall ɗin da yake mallakin Alhaji Mustapha inda za'ayi walimar cin abincin aka har haɗa komai da taimakon su Al'ameen ɗin da Bilal, basu bar wurin ba hr saida suka ga komai ya kammala, kuma an ware ma manya iyayen ƙasa nasu ɓangaren ta inda babu ma mai ganin su, sannan suka wuce gidan domin shiryawa Ƙarfe ɗaya ƴan Katsinan suk iso iyayen khadeejar Yaya Aleeyun da yake ma harda shi aka je ɗauko suruka nashi, ya sanya shima saidai abokanan shi ne suka taimaka mashi har haɗa komai. Har zuwa ƙarfe ɗayan ban yadda anyi mani kwalliya ba, yo ni kwalliyar ma me zanyi? Saida Afnan da Hafsat ɗin suka matsa ne gami da tsoratar dani zasu gaya ma Ya Ameen ɗin Abunda ya faru to, sannan na yarda aka yi mani ƴar Light ba mai yawa ba, duk da haka nayi kyau ba laifi kam. Kowa na ɗakin namu ya haɗe cikin ƴar ubansun ashoben yinin da ta kasance ƴar ubansu atamfa, fara ce tas sai ƴan pattern na dark blue da Orange, atamfar bata da hayaniya, hakan ce ta sanya tayi matuƙar kyau da haskawa gashi zanenta ba mai irin yawan nan bane jefi jefi ne. Haka muka shirya cikin atamfar, Nidai kasa tashi ma nayi saboda Hafsat ce ta bada mana ɗinkin da aka yi mana, kasancewa ƴar ƙibar dake gareni ya sanya skirt ɗin kama ni tsam, duk nabi na tsargu kaina, yayin da su kuma sauran suka ruɗe da ganin ƙirar da Allah yayi mni suna cewa dama su. Gyalena da takalma na masu tsinci duk blue ne, yayin da siririyar sarƙar dake wuya na ta kasance fari tar ɗin duwatsu da kar ta Orange, lallai munyi kyau, kaman yanda vail ɗina yake blue haka na kowa dake ɗakin namu ya kasance, banda Hafsat da ita kalar golden ne gabaɗaya jikin ta hatta sarƙar gold ɗin dake wuyan ta da Sadeeq ɗin ya zubo mata su cikin lefe kaman ba kuɗi ne ya siya ba. Masu aiki ne suka leƙo sashen namu gami da faɗa mana mu fito za'a fara cin abincin kaman yanda aka tsara. Tin daga nesa ake kallonmu, domin dai yau duk hassadar ka ba zaka kushe mu ba haka ma amaryar tamu, runfuna ne guda bakwai kaman yanda aka tanada, Hajiya Kubra, Hajiya Zainab, Kaka Zuwaira da tawagarta, sai ta Saudat, Nihal Da Hafsat ɗin. Kowa da tawagar shi yake zaune. Hajiya Kubra ce na fara hangowa, saboda wani irin kwarjini da cika idanu da take yi, ta kame ɗaya daga cikin kujerun Alfarmar dake ƙarƙashin haɗaɗɗiyar rumfar tata da taji ado da silkin yadi da balam balam. Sanye take cikin wani ɗanyen pink ɗin lace anyi mata ɗinkin bubu, wuyan nan nata babu Abunda yake yi in banda walƙiya, haka ma kunnuwan ta da hannayen ta da suke cike taf da zobuna da abun hannuwa na gold Yau ko gyalen ma babu a wuyan ta, sai ƴan fadan ta da suke zaune kujerun da suke gefen nata, sauran kuma duk kansu kujerun ƙarfe ne anyi masu ado da fararen ƙyalle in ka cire na kaka zuwaira da na Hajiya zainab, sai na amare da suke royal chairs kaman na kamu haka. Rumfar da babu kowa sai kujeru muka nufa gami da zama idanun kowaa kammu masalan ma ni da bani da alama da ƴar aiki ayau, ba wata wata ma'aikata suka fara serving ɗin mutane, baka jin komai sai ƙarar chokulla, ni kau na kasa cin ma abincin sai juya cokali nake ta faman yi. Da na ɗaga idanu na kuwa sai su faɗa cikin na Hajiya Kubra, data ƙure ni da kallo tana so ta gano Abunda yaja hankalin yaron nata a jikina, saidai duk iya kallon nata bata gano komai ba, domin in hasken fata ne ko hanci babu kalar wanda yaron nata bai gani ba har cen ƙasashen ƙetaren Da mun haɗa idanu kuwa zan saurin sadda kaina ƙasa saboda irin kallon tsanar da take bina dashi, sa'a ta ɗaya ummata bata wurin domin dukka ƴan aiki acen sashen nasu suke in abincin, hakan ce ta sanya su zama sashen namu, ita kau ummata ma ɗaki ta shiga gami da kwanciya saboda ta gaji gashi har juwa take ji.. Ƙarfe biyu daidai dubban mutane suka shaida ɗaurin auren Saudat Almustapha da Kamal jamu, akan sadaki naira dubu Hamsin, sai Zuwaira (Nihal) da Nuradden Baffa itama akan sadaki naira dubu hamsin, sannan Hafsat Auwalu da Abubakar Sadeeq Muftee itama akan sadaki naira dubu Hamsin ɗin Sannan na Aleeyj Auwalu da Khadeeja Ibrahim akan sadaki Naira dubu ɗari domin su ne suke da alhakin sanya ma ɗiyar tasu sadaki ba Alhaji Auwalu ba, tinda su cewa sukayi ba kuɗin ke gaban su ba albarka auren da ɗorewa shi suke so. Bayan kammala ɗaurin auren ne, haka dubban jama'ar suka shaida naɗin ya Ameen ɗin a matsayi *Yariman Matasan Arewa* Bayan kammala naɗa mashi rawani ne da miƙa mashi sanar girma sai aka lulluɓa mashi alkyabba fara ƙal da surkin royal blue Tini fa Yariman namu ya Faso, cikin salon tafiyar shi ta ƙasaita, yau kam tafiya ta tabbata, shi ba gadon sarauta ba Allah ya ci dashi, bayan ya kai gaisuwa ne ga dukkanin sarakunan dake wajen mai girma shugaban ƙasa ya mallaka mashi makullin dunƙulalliyar mota ƙirar royce - royce 2019 da lambogini 2019 collection a matsayi kyautar shi shi kuma, nan fa aka yi ta mashi kyaututtuka, fadawan da aka mallaka mashi suna mashi godiya, a haka ya nufo cikin gidan Bilal ɗin na take mashi baya domin zuwa kaima tashi mahaifiyar gaisuwa. Matasa kuwa ya gansu kowa so yake ya gaida shi, don ma fadawan na buɗe mashi hanya, a haka ya ratso dimbin mutanen nan har zuwa cikin gidan nasu. Tin daga nesa mahaifiyar tashi ta hango shi, Miƙewa tayi gami da isa wajen shi, baiyi wata wata ba kuwa ya sunkuya ya kai gaisuwa gareta, itama bata yi wata wata ba ta sunkuya gami da rungumo shi cikin ƙirjinta ta miƙe tsaye dashi, sowa aka ɗauka da tafi kowa sun burge shi, yanyameshi aka shiga yi ana ta kai gaisuwa, abokan wasa na yankar shi, hatta da kaka zuwairan da take tafiya daƙyar saida ta taso ta iso gareshi. Sa hannu yayi ya rungumo ta gami da ɗora mata peck a tsakiyar kai, dungureshi tayi tana mai cewa "ja'iri girma ya hau kanka yanzu saura mata" Haka yabi yana rungume ƙannen nashi amare da suka kai gareshi Hafsat ce kawai bai runguma ba, saidai ya kamo mata hannu yana mai cewa "Congrat ƙanwa ta" da murmushi ta bishi tana mai cewa " Same Yaya" Duk yanda dogarawan nan suke kaffa kaffa da daƙunar da ake kai mashi, dole suka haƙura, domin sabon babin ɗaukar hotuna ne aka buɗe kowa so yake ya shiga ayi dashi, masalan dangin Hajiya Kubran da suke ji su wasu isassu ne. Nikau da nake zaune sai sarkin murmushi nake yi akai akai, domin sun matuƙar burgeni, sarauta yayan namu tayi mashi kyau matuƙa, sai naga har girma kaman ya ƙara da cika ido, sai faman murmushi yake yi, shi kau Bilal bakin nan nashi kaman gonar auduga. Maida kaka zuwaira aka yi aka zaunar da ita, domin ta gaji sosai gashi shi kin rana suke sosai, domin duk sun baro wurin zaman nasu. Binshi kowa ya shiga yi da idanu ganin ya sulale ya fara tafiya, ƴar razana nayi ganin ya nufo inda nake zaune, waigawa na shiga yi domin ganin ko akwai wani kusa dani da yake nufo inda nake zaune. Ganin da gaske yake yi ni yake tunkaro wa ya sanya ni sauke kaina ƙasa ina wasa da yatsun hannuwa na duka biyu, bansan ma me zanyi ba, wane kalar tinani zanyi, gashi dai kowa mu yake kallo. Hannuwan nawa Naji an kama, bansan lokacin da na miƙe tsaye ba, jana ya shiga yi zuwa wajen mai ɗaukar hoton, saboda tsabar ruɗewa ni kuwa har gyale na yana sumɓulewa, daidai cikin taron jama'a yaja burki ya tsaya, hakan ce nima ta sanya ni tsayawa don dole, uwa ƙasa ta tsage in shige nake ji, gashi kowa ya zuba mana idanu, Hajiya Kubra kuwa kaman idanun ta zasu faɗi ƙasa saboda tsabar yanda ta ƙwalalo idanu tana kallonmu. *Ke ba zaki zo ki ɗauki hoton bane da mijinki?* Maganar da ya raɗa mani a kunne kenan daidai lokacin da ya zuƙunna yana mai ɗauko Gyalena daya sumɓule ya shiga yafa mani. Ai bansan lokacin da na ƙwalalo idanu ina mai Binshi da idanu ba na shiga rufe bakina da hannuwa na ina girgiza kai na. Ɗaga murya yayi sosai yanda kowa zai iya ji ya shiga faɗin *Alƙasim ga mata ta ina son ka ɗauke mu ni da ita kaɗai bana son kowa ya shiga in banda amini na Bilal* Ya faɗa da wani killer smile a saman fuskar shi yana yi yana cije leɓon shi guda ɗaya gami da kafa ma Mahaifiyar tashi idanu..... 🤣🤣🤣🤣🤣 ~Oum-Deedat ce~ [9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ *Page ~28~* *A madadin ƴan Banfi ƙarfin ta ba Fans* Gaisuwa da saƙon ta'aziyya zuwa ga ƙawarmu kuma ƴar uwarmu mai bada goyon baya da ƙoƙarin comment, (Salamatu Muhammad) a bisa rasuwar mahaifinta da tayi, Allah ubangiji ya jiƙanshi ya sanya ya huta y baku haƙurin rashin shi, ya sanya kwanciya hutu ce, ya bashi ikon amsa tambayoyin kabari,ya raya Abunda ya bari yayi masu Albarka Ameen. 🤲🏻 °^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^° Hajiya kubra wadda ta zabura da niyyar isa wurin da yake tsaye riƙe da hannuwan Suhan ɗin, da sauri Hajiya Sa'a ta riƙo hannun ta, domin ta kula sarai da niyyar hajiyar yanda take fitar da huci kaɗai ya isa ya shaida maka Allah ne kaɗai zai kare Al'ameen ɗin daga marukan da taso zazzagba mashi. Ganin za'ayi abun kunya ne a wurin Hajiya sa'ar ta shiga jan hannuwan ta zuwa cikin gidan ba tare da kowa ya ankare ba, domin kuwa kowa hankalin shi na kan Al'ameen ɗin da dogarawanshi suka zage suna ta gyara mashi malum malum da take suɓulewa. Rasa inda zan tsoma rain inji daɗi nayi, lallai wannan maganar tayi man tsauri, ƙwaƙwalwa ta har bana jin zata iya ɗauka, tini naga duniyar na juya mani, duk da hasknn flasher ta ko ina da take ta haske mu, ƙoƙarin zare hannuwa na nake yi domin in samu in ruga, na kula ma saboda tsabar yanda na tsorata numfashina har wani ɗauke wa yake yi. Gabaki ɗaya hankalin ƴan matan dake wurin ya tashi, waɗanda ma basu kula da ko waceceni ba, son sanin ba'asi suke yi. Ran kaka zuwaira kwal, lallai yau kowa ya shaida Al'ameen ɗin akwai wacce yake so, mutane da dama zasu dena yi mashi kallon mai ɗaga ma ƴan mata kai, saidai ita ɗin wannan wacece? Daga baƙin ƙofar gate, makaɗa da mawaƙa ne da masu kirari suna ta wasa Al'ameen ɗin da mahaian shi, Abie ne ke ta masu ruwan kuɗi fuskar nan taf da fara'a, duk wainar da ake toyawa a harabr gidan ma bai sani ba. Bilal ne ya zare jiki daga wurin da yake tsaye zuwa sashn Al'ameen ɗin, sannan ya ɗauko waya ya latso lambar Al'ameen ɗin. Daga cikin Aljihu yaji wayar tashi na vibrating, hannuna ya saki da niyyar ɗauko wayar, ni kau ganin wannan damar ta samu na zare hannuwan nawa gami da nufar sashnn namu kai tsaye harda haɗawa da ƴar sassarfa. Ganin Bilal ɗinne ya sanya shi ɗan juyawa bai hango shi ba, domin shi dai ya san tare suka shigo gidan, to ina kuma ya nufa? Bai ɗaga ba har ta katse, yana ƙoƙarin bin kiran wani ya sake shigowa ɗagawa yayi sannan ya kara akunne "Malam wai me kake yi ne haka? Menene dalili ka nayin hakan? Baka gudun kaja ma yarinyar wata matsala kuma? Ka saki yarinyar mutane hakanan, kuma ka shirya amsar hukunci daga wajen Mom domin ba don Allah ya tsare ka ba an janye ta da kasha maruka a gaban bainar jama'a" Bilal ɗin ya faɗa ta ɓangare ɗaya, shi kau gogan kasaƙe yayi da wayar har bai a san Bilal ɗin ya kashe ba, ƴar dariya yayi mai cike da yaƙe lokacin da yaji "ƴaƴan Goggo Fatima na yankar shi wai dole sai sun ɗauki hoto dashi tinda amaryar tashi mai kunya ce ta gudu, shi kau da baya da kunya dole ya tsaya. Ganin da yayi zai ɓata ma kanshi lokaci ne wajen ɗaukar hoton ya sanya shi juyawa kai tsayezuwa ga sashen nashi, baya ma jin yunwa, ko da yana ji kuma baya tinanin ma in zai iya kai wani abu bakin shi. Daga bakin ƙofa dogaransuka ja suka dogare, kai tsaye ya kutsa kanshi har cikin bedroom ɗin nashi inda ya tada Bilal ɗin nata faman kaiwa da komowa. Da ƴar sassarfa ya isa inda Al'ameen ɗin ke tsaye, cikin ɗan ɗaga murya ya shiga faɗin "me kayi haka ne? Hakan da kayi kana ganin daidai ne? Kana nufin zaka ja da mahaifiyarka ne? Ta wanna sigar ya kamata ka ɓullo ma Al'amarin?" ya ƙarshe yana mai zagaye Al'ameen ɗin ya nufi jikin window ya tsaya ba tare ma da ya san ya isa wurin ba. Yana tausaya ma abokin nashi, Abunda zai je ya komo baya hasashen idan zai zo ma abokin nashi da sauƙi, amsar shi kawai yake jira, saidai jin Al'ameen ɗin bai tanka bane ya sanya shi juyawa domin yaga halin da abokin nashi yake ciki. Shi kau ta ɓangaren shi, duk da kalamnn abokin nashi sun Dakar mashi zuciya kuma ya jisu har cikin ƙwaƙwalwar shi hakan bai sanya yaji ko ɗar a cikin zuciyar shi ba, karaya da wuri ba nashi bane ba, wannan karon dole ne ya nuna ma magulmata cewa hassadr su da baƙin cikin su babu inda zasu kai su sai fagen nadama. Takawa ya shiga yi har zuwa gaban gadon nashi, har yanzu bai ko tanka ma abokin nashi ba,baya so ne ya kai shi ga faɗin dukkan Abunda ke cikin zuciyar shi a fili, shi yafi so saidai kawai aga yana aikatawa. "Kanajina malam kayi mani banza, wato baka ma da lokaci na ko? To inaso ka sani dukkan Abunda ya taso kar a ƙasa ran zaka tunkaro ni ka samu mafita, maganin kar ayi to fa kar a soma" Bilal ɗin ya faɗa sannan ya juya da niyyar barin ɗakin. Al'ameen ɗin da yake ta ƙoƙarin cire kayan nashi domin ya watsa ruwa, barin cire kayan nashi yayi sannan ya juyo a hankali yana faɗin "Dakata Malam" Dakatawa bilal ɗin yayi ga barin ɗakin da yayi niyya. A hankali Al'ameen ya shiga ta kowa kaman mai jin tausayin ƙasa, har zuwa inda bilal ɗin yake tsaye, a hankali ya sanya dukkan hannuwan shi ya dafa ka faɗar bilal ɗin, sannan ya shiga faɗin "Ni Moh'd Al'ameen nine mazinaci, fasiƙi mai neman yarinya da lalata har cikin ɗaki na, ni take tallata ma kanta ni kuma nake biye mata alhali ina cikin hankali na...." Bilal ɗinne ya dakatar dashi ta hanyar sauke dukkanin hannuwan da yayi amfani dasu wajen dafa kafaɗar bilal ɗin " Dakata Friend, kana cikin hankalina kuwa? Kasan me kake faɗa? Ya zaka dinga jifar kanka da waɗannan mugayen kalaman? Ko dai ka fara shaye shaye ne ban sani ba?" Bilal ɗin ya faɗa cikin ɗaga murya, ga dukkan alamu kalaman abokin nashi sun ɓata mashi rayuwa gabaɗaya. " Na sani Bilal, na san me nake faɗa, kuma waɗannan magangannn ba daga bakina suka fito ba, daga bakin mahaifiya ta suka fito, and kuma bansan wanene ya faɗa ba, shine naga tinda har neman yarinyar akeso inyi to zan fa nema ɗin Amman ba ta hanyar da su suke nemana da ita ba, ta hanyar da shari'a tazo mana da ita, watauta hanyar *Aure*" Ya faɗa shima cikin ɗan ɗaga murya kaɗan, saidai Sam na bakin ƙofa ko na cikin falon ba lallai ne ya iya jiyo Abunda yake faɗa ba. " Huh" Bilal ɗin ya sauke ajiyar zuciya mai matuƙar ƙarfi, a hankali shima ya shiga takawa har zuwa gaban gadon, daɓas ya zauna yana mai dafe kanshi da yake sara mashi uwa zai rabe gida biyu, wannan shine dalilin rashin lafiyrr abokin nashi? To indai haka ne munafukan na acikin gidan, lallai tausayin abokin nashi da na yarinyar da ake neman a laƙaba ma sharri bata ji ba bata gani b ya tsira mashi har cikin zuciya. Sake miƙewa yayi gami da isa ta inda abokin nashi ke tsaye ya haɗe kai da bango yana ta faman maida numfashi yayi, da dukkanin alamu ɓacin ran nashi ya sake komawa sabo fil a cikin zuciyar shi. Da dukkanin hannuwan shi yayi amfani wajen kamo abokin nashi har zuwa lokacin da ya zaunar dashi bisa gadon nasu, shima zaunawa yayi a hankali, shi ya ma rasa tinanin me zai yi a ranshi, llai abokin nashi na buƙatar wanda zai taya shi wannan yaƙin da ya tunkaro ka, ace wai a wurin aiki baka samu matsala ba sai a cikin gida. Ummata da take kishigiɗe bisa darduma, gama sallar ta kenan ta jawo cesbaha tana ja idanun ta a lumshe, tsulum na faɗa ɗakin namu ina ta faman haki, ni ban ma san umman tawa na cikin ɗakin ba, ai da bari nayi sai na saisaita kaina sannan in shiga. Da hanzarin ta ta tashi tana mai cewa "ke lafiyar ki kuwa? Ko wani abu ne ya same ki? " Ganin ban bata amsa ba ya sanya ta ficewa da niyyar zuwa taga menene yake faruwa, saidai bata fahimci komai ba, saboda ko da ta isa wurin mutanen ta tadda wasu suna ta faman cin abinci yayin da wasu ke ta faman ɗaukar hoto da Al'ameen ɗin. Hakan ce ta sanya ta dawowa zuwa ɗakin gami da share ni ta cigaba da laziminta, in na matsu na faɗa mata Abunda ya tashi hankalin nawa. Ban gama warwarewa ba sai ga Hafsat da Afnan sun shigo cikin ɗakin, cewa sukayi in biyo su muje ko suyi mani tonon silili wurin umman tawa. Ba arziƙi na miƙe gami da yafa mayafi na na bi bayan su, ina kula da Afnan wacce take Ƙunshe dariya a cikinta. Da kallo umman tawa ta bimu tana kaɗa kai, koma miye in tayi wari taji. Masifa da bala'i ba kalar wanda Hajiya Kubran bata sha ba cikin ɗaki, haƙuri suka dinga ɓata, kada ta ɓata taron bikin nan DON Allah, da ita cewa ma tayi aje a sallami kowa tinda an gama cin abincin. Shawarwari ba kalar wanda ba'a bata ba, daƙyal suka samu tayi haƙurin zuwa dare ayi wacce za'ayi, cikin gidan zata ga mai zaman wani a cikin su ko ita ko su, lallai wannan aikin asiri ne tsab, kenan ma Abunda aka faɗa ɗin ya tabbata gaskiya ne, inko hakane wallahi Sam ba zata saɓu ba bindiga a ruwa. Abunda ya faru ɗin sai ya sanya ƴan ƙanannn maganganu suka shiga yawo a cikin gidan bikin, duk inda Kaga gungu an haɗa kai maganar akeyi, lallai Hajiya Kubra ta faɗi ƙasa babu nauyi inko har ta bari ɗanɗanta da aka yi ittifaƙin tafi son shi akan dukkanin sauran ƴaƴan nata ya auri talakrr ƴar aikin su. To dama itama dai Abunda take gudu kenan, kuma tini labarin gulmammakin da akeyi cikin gidan ya isa kunnen ta, domin duk inda ka zaga maganar akeyi. Hakan ce ta sanya bata ƙara fitowa harabrr gidan ba, duk wanda yazo saidai a shiga dashi sashen nata, shima ɗin saidai in manya ne, inko jigari jigari ne iyakar su babban falo a basu abinci suci ba ta gudunmuwar da suka kawo take yi ba, Alla Alla take yi dare yayi domin ayi wacce za'ayi. Kusan ma zamu iya cewa bikin sai ya koma sashen hajiya zainab da kaka zuwaira, dama su ta fannin su abun yayi masu 100% sun yaba da yarinyar da kuma tarbiyyar ta, alwashi dai sun sha shi indai da gaske Al'ameen ɗin yake yi yana son yarinyar itama tana son shi to fa babu makawa da izinin Allah sai abun ya tabbata, tinda sun san yaron nasu ba irin raggwayen mazan nan bane. Haka har suka sake shiryawa suka fice dogarawanshi na biye dasu a baya suna mashi kirari da wasa shi wannan karon harda ce mashi Angon Hauwa'u sai dubu ta taru. Domin duk akan idon su Abunda ya faru ya faru. Ɗaki suka sanya ni gami da titsiyeni suna tambaya ta wai in faɗa masu lokacin da muka fara soyewa da yayan nasu basu sani ba. Ba kalar rantsuwrr da banyi masu ba, Amman fir suka ƙi yarda, dole naka bakina nayi masu gum, ina jinsu suka cigaba da zaulaya ta. Afnan ɗince mai cewa "Ni fa tin lokacin da yaya yazo da maganar auren aunty suhan ɗin na yarda dashi, dama na daɗe ina addu'ar hakan a zuciya ta..." Hafsat ta amshe da cewa "Kedai bari Afnan, kuma ke fa don ma baki nan, baki ga yanda yake kulawa da al'amarin ta ba ke dakin gani ma kinsan ba banza ba wlh" "Welcoee to our Family Aunty Suhan" Afnan ɗin ta faɗa tana mai rungumi ni zuwa jikin ta. Nan suka shantake suna ta zaro fira, ni wani abun ma in sun faɗa saidai in kwalalo idanu, gani nake yi kaman sharrinsu ne kawai Al'ameen ɗin ba zai iya yin hakan ba. Sauran ƙawayen Hafsat ɗin duk sun dawo ɗaki, nan fa aka buɗe sabuwar fira, cikin su ma har akwai wadda tayi man congrat gami da faɗin "Lallai kunyi matuƙar da cewa, ku duka kun iya zaɓen abokin rayuwa" dariya kawai aka sanya maganar gaskiya zukatn Afnan ɗin da hafsat ɗin cike suke taf da farin ciki marar misaltuwa, yayin da ni kuma ta ɓangareaa na ma rasa kalar tinanin da zanyi, har yanzu ba wai na gaskata bane, gani nake yi kaman mafarki nake yi ko kuma yaudara ce irin ta ɗa namiji akwai Abunda yake son cimma wa. " ba zata taɓa saɓuwa ba wallahi, ashe yaya bai bar zancen nan ba har yanzu, gaskiya ya zubda mana aji at All wallahi, duk da yau ta kasance ranar farin ciki a gare mu ta wani ɓangaren ranar tazo da akasi" Nihal ɗin ta faɗa tana mai faɗa wa kan jibgegen gadon nasu inda Saudat da sauran ƙawayen nasu suke ana ta maida yanda akayi "menene ba zai faru ba? Ai ya riga ya faru saidai Allah ya kyauta gaba kawai, Amman ke kina kallon cikin idanun yaya wallahi kinsan har cikin zuciyar shi ne sonta yake da gaske" Wata daga cikin ƙawayen nasu ce da ta kasance ƴar uwarsu ta fannin Hajiya Kubra ke faɗin haka, ta bala'n so shi itama a da, ganin ba kula ta yake yi ba, hasali ma ba ta ita yake yi ba, duk iya yin da take dashi da fi'ili lokutta da dama gwasale ta yake yi ko kuma yayi ma kaman bai san ta nayi ba, ya sanya ta dole ta watsrr da makaman soyayyrr nata rabi wani sarkin. Wata daga cikin ƙawayen ce ta sake amshe zancen da cewa "dalla bari wannan maganar khairi, ai ke kinsan wallahi Ya Ameen ya wuce da ajin wannan ƴar aikin, ni ina gani ko dai asiri sukayi mashi ya aikata a cikin jama'a ba tare da ya san ya aikata ba" "Confirm cewrr Saudat da take kishigiɗe sai lokacin ta tashi zaune, gaskiya Yaya bai kyauta mana ba Sam, haba ina shi ina wannan kucakar? Duk tarin ƴan matan da suke rububinshi ace bai hango kowa ba sai wannan ruɓusar, ke kiga jikin ta ma fa ko ina a sake take ko irin slimming ɗinnan ma ita bata iyawa saboda duhun kai anfj so a zauna tuɓs ko ina tsoka" Shewa suka sanya suna faɗin Amman fa Saudat baki da dama wallahi, "Amman fa ni kinsan ina tsoron irin wannan jikin, komai fa suka sanya zama yake das yayi masu kyau daidai jikin su" Cewar ɗaya daga cikin ƙawayen nasu da suka zo masu hidimar bikin tin daga ƙasar ta ta America. Nan fa aka buɗe sabon babin yin zancen suhan ɗin duk kusan rabin firar aibantawa yafi yawa a ciki (Hmmm Allah shi kyauta, Hassada ga mai rabo taki) Ana gama sallar la'asar aka fara shirin hawan dabar, bayan an ci an sha, anyi hani'an. Sarakunan jihohin namu na arewa suna nan sai washegari zasu koma gruruwan nasu, inda aka yi masu masauki a fadar shugaban ƙasar namu ta nigeria. Hawan daba fa ya ƙayatar, tashohin gidan talabijin suna ta ɗauka live, matsa dai an gansu a wurin, kowa yayi mamakin irin yanda dawakai suka yalwata a wurin kaman dama an san da naɗin sarautar. Ƙarfe shida suka gama zagaya duk inda zasu zagaya, manyan namu suka samu suka koma masaukin nasu domin su huta, yayin da cikin gidan yake ɗinke da jama'a gefe guda ga masu kiɗin ƙwarya suna ta chashewa ana masu ɓarin kuɗi, abinci kuwa har kawo yanzu shigowa akeyi da sababbi, duk Abunda kayi sha'awrr ci akwai shi. Gudun sake tada gulmammaki ya sanya Hajiya Kubran ta dage ta cije, Amman fa har kawo yanzu da magariba ta kawo jiki bata saki jikinta ba, walwalarta har yanzu ragaggiya ce, don ma su Hajiy Lailan na bata baki da shawarwari akan yanda za'a ɓullo ma 'amarin. Hajiya sa' ar ce tayi mata alwashin ta bar komai a hannun ta nan da kwana uku zata ga Abunda zai faru a cikin gidan. To da haka ne fa ta samu ta lalubo walwala ta yafa a kan fuskar ta Amman ba don har cikin zuciyar ta haka yake ba. Wannan karon sashen na Al'ameen cike yake da baƙi, abokanan shi da suka zo mashi ɗaurin aure da naɗin sarautar tashi, da yawa ma daga cikin abokan yanzu sunan shi ya tashi daga Ameen ko Dambulan da suke kiran shi dashi ya Koma Yariman Matasa, duk da baya so Amman a haka yake amsawa, saidai kowa ya kula da rashin walwalar tashi, Amman sun mashi uzuri akan cewa hayaniya da jama'a ne. Gida yayi tsit tin bayan da aka tashi sallar isha'in Yo kowa ya gaji wasu ma har sun fara bacci, har yanzu zuciya ta a cunkushe take na kasa gane kaina, Alfarmar su Hafsat ɗin na roƙa akan su barni inje in kwana tare da ummata ko Naji sauƙi. Basu hanani ba, saidai sunce su ba zasu rakani ba, a haka na ratso tsakiyar gidan zuwa sahen namu, ummata har ta kwanta na kwankwasa mata ta buɗe na shiga. Da kallon ke lafiya kuwa ta bini, yi nayi kaman ban kula da ita ba, kai tsaye na haye katifar na kwanta, yayin da itama ƙalau bata ce mani ba ta hawo itama tare da kwanciya. Saidai me? Bacci Sam yayi mani ƙaura, idanun a kaman an soya, saboda rashin baccin har wani raɗaɗi suke yi mani. Saidai in juya in sake juyawa, idan na tinank kaɗan sai in ɗan ja tsoki kaɗan in sake juyawa. Ƙwaƙwalwa ta fa har yanzu a cunkushe take, ina buƙatar wanda zai yi mani fashi baƙi dalla dalla fa, saidai wanene shi? Wayata ce ta ɗauki haske alamar saƙo ya shigo, da hanzari na jawo ta gami da buɗewa, banyi mamakin sunan shi da nagani ɓaro ɓaro kan screan ɗin a, saidai Abunda saƙon ya ƙunsa shi ne ya bani mamaki. Ummata wadda bansan da ta tashi zaune ba, kwatsam saidai Naji muryar ta tana mai ceman "Mamana na kula dake fa tin da rana, ga dukkan alamu akwai Abunda yake damunki, Amman in kinga ɓkyemun shine Abunda yafi ɗin, sai ince Allah ya sanya hakan ne, domin bana so kizo kiyi danasani akan dukkan Al'amurranki, idan kuma kin yanke shawarar faɗa mani tau ina saurarenki" Cikin ƴar razana bakina na rawa na tura wayar tawa ƙarƙashin follow, bansan lokacin da na shiga ce mata "umma fa ba komai, kawai na gaji ne, kuma gashi kaman ba ɗan jin daɗi ne..." Na ƙarashe cikin in ina wadda take alamta ba gaskiya a cikin maganar tawa, wanda ni kaina bansan dalilin nawa na ɓoyema umman tawa ba, da duk duniya bani da abokiyar shawarar da ta wuce man ita. Gyaɗa kai kawai tayi, bata sake ce mani komai ba ta koma ta kwanta, tana fatan Abunda na faɗa ɗin ya kasance gaskiya, duk da bata taɓa kamani da laifin yi mata ƙarya ba. *_"ki dena yawo cikin dare, sannan ki shirya fuskantar duk wani ƙalubale da ka iya tunkaro mu"_* Abunda ya rubuta mani kenan, ban iya bashi amsa ba, duk kuwa da karanta saƙon da nayi sau ba adadi. Ni ya ma ƙara sanya ni cikin wani duhun wallahi, wai ni shin me yake nufi dani ne? So yake ne ya tarwatsa mani ƙwaƙwalwa ne ko kuma me? ~Oum-Deedat ce~ https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/ 🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹 🌺🌺🌺🌺🌺 *~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~* *~We are bearer's of so golden pen🖊~* *~we write assidiously perceive no pain~.* *~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~* *~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~* >>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>> *Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_ *Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_ *Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._ A haka dai na kwana juye juye, zan mabiya cewa ko baccin kirki ban samu nayi ba, umman tawa duk tana kula da dukkan motsi na Amman ƙala bata ce mani ba. Washegari kuwa tin dasafe aka tashi aka hau shirye shiryen walima da za'a gabatar itama dai a farfajiyar gidan, wannan karon harda dangin anguna duk zasu halarta, daganan ne za'ayi buɗar kai, bayan an gama sai a basu amaryar su su tafi da ita. Tin da safen kuwa sai ga su Afnan wai sun zo ƙara tafiya dani, aikuwa fir naƙi binsu, ba irin magiyar da basu yi mani ba, Amman na ƙiya, bana so in koma wurin ne a sake samun matsala gashi naga ga dukkan alamu ummata tana shirin zuwa wurin ne. Kwanciya ta nayi ko bayan fitar su, har itama umman tawa ta kammala shirin ta ta fice, gyara kwanciya ta nayi gami da jan abun lulluɓa domin baccin da ban samu nayi ba a daren jiyan. An ƙawata wurin fiye da na jiya, tini dangin angunan sun iso tin wajen ƙarfe goma na safiya. A sashen Hajiya kubran aka yi masu masauki, saidai dangin sadeeq ɗinne suka ce a nuna masu wajen surukar yaron nasu acen ne zasu zauna. Ba musu aka nuna masu, ganin su manyan mutane kowacce cikin shiga ta alfarma. Hajiya Zainab ɗin bata yi tinanin haka ba, Shiyasa ba'a shirya masu tarba ba dukkanin kayan tarbar suna cen sashen Hajiya Kubra. Nan fa ta shiga ina taka saka su. Lura da sukayi ne ya sanya suka ce karta damu kanta, ba wannan ce ta kawo su ba, su yarinya kawai suke so a basu. Rumfuna bakwai aka kafa ayau, sunsha deciration kuwa, rumfa ta farko ta hajiya kubra ce, sai ta kaka zuwaira, sai ta Hajiya Zainab, sai ta dangin anguna guda uku, gefe kuma ta anguna ce da abokaninsu maza An zagaye farfajiyar gabaki ɗaya illa iyaka hanyar da za'a bi a wuce. Ƙatuwar darduma aka shimfiɗa tsakiya inda gefe aka jera amaren kowacce tasha lulluɓi da kalar nata kayan da sukayi masu matuƙar kyau, gefe guda kuma aka jera ƙawayen amaren a yau babu bambanci duk kansu wuri guda suke zaune, cikin atamfar su english, kalar ta yarbawa yellow ne da ɗige ɗigen ja a jikin ta. anyi masu ɗinkin buba duk kansu, hakan ce suka sanya jan gyale da sarƙar murjani a wuyan su ɗaurin zanen ma bisa riga aka yi shi, hannuwan su riƙe da ɗan mafici mai ƴar bazar gashi gashi haka. Kowa ya hallara, nan fa aka fara gabatar da jawabai da kuma gabatar da kai. Kowa ka kalla yana cikin farin ciki, banda hajiya kubra da fuskar nan take ba yabo ba fallasa masalan ma data kula dangin iyayen mijin Hafsat ɗin sun zarce na yaran ta gabaki ɗaya a komai kuma. An kira kowanne ango yazo ya nuna amaryar shi, gami da kama hannun ta zuwa gaban dangin shi ta kai gaisuwa, sannan sauran mutanen, haka suma angunan amaren suka kama su har gaban nasu iyayen suka gaida su. Kaka zuwaira ce duk wanda yaje kusa da ita sai ta zaulayeshi tace ita ba sadaki take so ba na goro take so, haka suka babbata kuɗi gami da komawa suka zauna. Bayan ƴan abubuwa da aka gabatar aka buƙaci iyayen anguna da su kawo kayan aure. Nan fa idanun mutane ya shiga buɗewa ganin iyayen kaya na ƙarya da kuma kuɗi da ake ɓari kaman wanda ba'a so. Ba'a sha mamaki ba saida iyayen mijin na Hafsat suka taso, nan fa wuri ya hau tafi da sowa, ganin irin iyayen kuɗin da suka ajiye gabanta, daloli ne iya kallon ka, tare da sarƙar gwal da abun hannunta da zobunan ta wasu irin manya ne ko daga ina kake zaka iya hango su, tare da makullan mota guda biyu, ita ɗaya mahaifiyarta ɗaya, sai makullin tanƙamemen gida da yake nan cikin abujar da suka mallaka ma mahaifin Hafsat ɗin. Nan fa ƙaryar iyayen su Nihal ta ƙare masalan dangin Hajiya Kubran, saidai ita ce tayi ƙarfin hali ita kuma taba dangin mijin ƴaƴan nata motoci da kujerar Makka a matsaynn tukuicin kayan auren da aka kawo masu. Hajiya zainab bata san da wannan al'adar ba, hakan ce ta sanya bata tanaji komai ba, gashi kuma mijin nata baya kusa. Shiru aka yi, kowa naso yaga me su Hajiya Zainab ɗin zasu bada tukuicin wannan babbar kyauta da aka yi masu. Takawa ya shiga yi har gaban iyayen mijin Hafsat ɗin ya ajiye check gami da wata takadda ya koma ya zauna, Ya ameen ne da yake zaune cikin rumfar abokan angunan, tini kuwa kallo ya koma kanshi, Hajiya Kubra tsabar ƙuluwa kaman idanun ta zasu sauka kan Al'ameen ɗin. Mai jawabi ne ya taka har gaban iyayen mijin Hafsat ɗin ya sanya hannu gami da ɗaukar check ɗin da kuma farar takardar da take ƙar babu komai akai sai Rubutun Al'ameen ɗin jiki da ya gaji da ƙayatuwa. "Masha Allah, Alhaji Moh'd Al'ameen Almustapha Dambulan ya bada tukuicin Zunzurutun kuɗi Naira Million Biyar tare da kujerar hajji ta kimanin mutane biyar da kuma upper ta ɗaukar matasa aiki a cikin Zuriyar angon Hafsat ɗin ƙarƙashin jagorancin kamfanin, suma kimanin mutane Ashirin" Tafi aka saki, gefe guda wata zabiya ta saki guɗa, babu Abunda kake ji a wurin illa iyaka hayaniyar mutane data kauraye wurin kowa na faɗin Albarkacin bakin shi. Ajiyar zuciya mai ƙarfi Hajiya Zainab ɗin ta sauke, ganin cewa yaron nasu ya fidda su kunya, duk da ta san cewa ba da son ran hajiya kubran da take zaune cen cikin mutanen ta tana ta sakin yaƙen dole bane, Amman ko ba komai ta san Al'ameen ɗin mutum ne mai alkhairi da zai yi ma daman shi ba tare da hagun shi ta sani ba. Mutum ne mai hangen nesa da kuma kakkaifan tunani, baya buƙatar in zai fidda family ɗin nashi kunya sai ya jira shawara da wani. Ta ɓangaren Al'ameen ɗin kuwa idanu sukayi mashi yawa, ilahirin ɗaukacin mazan dake rumfar nan ya matuƙar burge su harda mazajen ƙannan nashi kuwa, wannan ta sanya suka ƙara gane B ƙaramin gida sukayi aure ba. Bayan kammala wasu Al'adun ne aka yi addu'a tare da ƙarin godiya, sai kuma aka fara shirye shiryen miƙa amaren ga dangin mazajen nasu bayan yi masu huɗuba mai ratsa jiki da Alhaji Auwalun da Alhaji Mustaphan sukayi. Hafsat tasha kuka, da kyar aka ɓanɓareta jikin mahaifiyr tata, babu wanda bata ba tausayi ba, yayin da su kau sauran ƙemadagas iyayen su ne ma suka sanya su mota babu wacce take kuka cikin su. To a ganin su dai auren so ne, kuma na wayayyu, auren ma sunan anyi ne, Amman suna da ƴancin da zasuyi komai a sadda suka so, kuma a lokacin da suka so. Kkwacce cikin su an mallaka mata jibgegiyar mota harda Hafsat ɗin kuwa, wannan kuma kyauta ce daga hannun Alhaji Mustaphan bayan gama masu huɗuba da sukayi. Har aka tafi kaisu kuma basu ma da alamar kukan saɓanin Hafsat da take ta kuka kuma tana laluben ina zata ga Suhan ɗin Amman ko alama bata hango mai kama da ita ba ma. Abun ya ɓata mata rai matuƙa, har saida tayi ma Afnan magana, wadda ita Hafsat tace zata bi Alabasshi daga baya zata je gidan ƴan uwan nata. Motoci ne aka zube bayan wadda su mazajen nasu suka kawo, kowacce amarya kake so kabi akwai mota free da zata kaika ta maido ka, duk da dai galibi wasu acen zasu kwana masalan ƙawayen amaren gashi kuma magariba ta doso ta kawo jiki. Hatta Hajiya kubran saida taji wani iri rabuwa da yaran nata da zata yi duk da ta san cewa koda yaushe zata iya ganin su matuƙar suna ƙasar. Bayan kammala komai ne da tafiyar dangin angunan da amaren su, aka hau gyaran gidan Gidan ya rage ƴan tsiraru sai masu aiki kaɗai ya rage don sashen Al'ameen ma babu kowa duk an kammala hidimar biki sun wuce masu jirgin gobe kuma sun koma hotel ɗin da suka sauka sai a goben zasu wuce. Kafin isha'i fa tas an gyara ko ina an wanke ko ina, wannan karon harda umman tawa da Hajiya Zainab da wasu daga cikin DANGIN alhaji Mustaphan ne suka sanya hannu aka yi dasu. Nikau ta ɓangare na, Naji matuƙar daɗin yau, kuma ina cikin farin ciki sosai duk da hayaniyar cen cikin gidan dan loud sleaker da ta dameni kusan ma ince hanani bacci tayi. Ƴan latse latse na na cigaba da yi ni kaɗai a ɗaki, salla kawai ke ta dani. Ko abinci saidai na sha complax da yake ni ba mai yawan ciye ciye bace ba. Ina cikin latse latse na a Internet naga alamar kaman an saki Jarabawar mu ta jamb da muka zana kwanaki. Aikuwa cikin sa'a na tabbatas da gaskiyar Al'amari, wata yarinya da muka zauna kusa da kusa mai suna Samira, ita na kira gami da tambayar ta, cikin farin ciki take sanar dani cin Jarabawar tata, wai ashe ma tin numu'a aka saki ban sani ba. Roƙonta nayi ko zata je ta dubo mani Alabasshi sai in bata kuɗin scratche card idan na fito, ba gardama ta amsa mani da zata duba mani ma yanzu ba sai na ɓata komai ba, saboda na taimake ta sau ba adadi a yayin zaman namu da ita, nan ne take faɗa man numb ta ce tayi loosing tin bayan canza wayar tata, waccen ta faɗi ne, jajanta mata nayi gami da cewa ina jiran ta sai na jita. Ko awa uku cikakka ba'a yi ba ta kira ni, tin daga muryar ta na gane kan zancen, ko saurarena ma bata yi ba ta shiga yi mani murna, muryar ta cike take taf da farin ciki ga dukkan alamu har cikin zuciyar ta ne. "Ƙawata kina da sa'a wallahi, zamana kusa dake ya taimake ni kwarai da gaske, ina alfahari da sanin ki a rayuwa ta, dad da mom duk sunce in miƙa saƙon godiyr su gareki takanas zasu zo har gida suyi ma su mom ɗinki godiya, kuma ina farin cikin sanar dake cewa duk school ɗinmu babu mai highest Mark kamarki insha Allah damun gama zan turo maki score ɗinki ki gani, zan kira ki insha Allah in mun tashi zuwa" Ko jiran godiyar da zanyi mata batayi ba ta kashe wayar, mamaki na shiga yi wannan wace irin yarinya ce, dama ko da muka zauna kusa da Juna duk da lura da nayi ita ɗin ɗiyar wani ƙusan gwamnati ce, Sam hakan baisa ta ɗauki kanta wani abu ba, tana da yawan dariya ga sauƙin kai don itace ta fara yiman magana ma da roƙon in taimake ta don Allah, wannan ce ta sanya na taimaka mata da iya gaskiya ta tinda ita ta karya kanta ta roƙeni. Ina hawa WhatsApp kuwa sai ga saƙon ta ya shigo wayar tawa, tayi screanshoot ta turo mani. Ai bansan lokacin da na miƙe ina sujada ga Mahalicci na ba, Sam ƙarar loudspeaker ɗin bata damuna ta murna ta kawai nake yi, ni kaɗai ace naci 280 Abunda ma wasu 180 suke nema? Lallai Allah buwayi gagara misali ne, kana taka Allah na tashi, Amman ni kaina in an faɗa man naci hakan zan iya musantawa ba don na gani ba. Saidai ada kam nayi mamaki da tace duk nafi kowa maki a duk faɗin makarantar da take cike taf da ƴaƴan manya wanda su za'a ma iya bi masu kadin abun, ni kuma da bani da kowa sai Allah gashi ya kwato mani ba don na isa ba. Kaman in tura mashi saƙo, sai kuma naga ai gani da kai yafi aike, nima tur a mashi nayi kaman yanda ta turo mani, naga ma kaman baya online, kusan ma ince rabon shi da hawa tin kwana biyu da suka wuce, to Allah yasa ma zai gani, gashi banda mail ɗinshi da sai in tura mashi ta cen na san zai fi saurin gani. Na mashi uziri ne tinda na san yana Cikin hidima da jama'a gashi kuma Naji kaman ance bayada lafiya rannan a bakin Hajiya Kubra duk da Nidai banga alamun hakan ba a jiya da ya bani kunya a gaban mutane, har yanzu saƙon shi na jiya yana kai kawo acikin ƙwaƙwalwa ta, saidai na Gaza gano mai yake nufi duk kuwa da kwana laluben da nayi. Umman tawa bata shigo sashen namu ba sai bayan isha'i bayan sun kammala gyara ko ina, a bakin ta ne naji tana cewa su Hajiya Zainab ɗin gobe zasu wuce, tace wallahi gidan ta zata koma, saboda gidan duk ya isheta dan ma ƴan kankiyar na nan ko ba komai tana jin ɗuriyar waɗanda ta sani. Sannan ta shiga yiman faɗan rakiyar Hafsat ɗin da banje nayi ba, tace tana jin Hafsat ɗin ta kira maman tasu tana mata tsogumi, kuma da gaskiyar ta "lallai kinyi laifi mamanta, ai kin san dai ba zan hana ki raka Hafsat ɗakin miji ba, yarinyar da ta fifita ki akan kowa na gidan nan har su ƴan uwan nata, to maza idan Allah ya kai mu kiyi sammakon shiryawa ki kira ta tayi maki kwatance kije mata ki gano ɗaki, Naji ance wucewa zasuyi ita da mijin cen ƙasar da yake aiki" To nace mata, ni yau fa zuciya ta fes, duk da umman tawa ta lura, ita fa harma ta fara zargn anya yarinyar tata lafiya take kuwa, yau farin ciki gobe akasinshi? Kaman ba ita ce ba jiya ta kasa barci, yau kuma ta kasa shiga jama'a, koma dai miye zata zuba ido ta gani. Ita Abunda ma yafi ɗaure mata kai, wasu ƴan maganganu da taji suna tashi daga bakin ƴan bikin masalan dangin Alhaji Mustaphan, har kaka zuwaira na cewa ita ce wannan? Lokacin da taje gaida ta dayi mata saida safe, sai gashi har tana bata saƙon gaisuwa zuwa wajen Suhan ɗin da tace mata yau bata ga giccinta ba, Allah dai yasa lafiya. Dariya tayi, zuciyar ta cike da wasi-wasin Abunda taji ɗin, harda wata taji tana cewa "ance fa ƴar aikin gidan ce, amman sun naniƙe ma Al'ameen ɗin" gabanta ya tsananta faɗuwa kaddai tinanin ta ya kasance gaskiya, domin maganganun sunyi yawa kuma ta fahimci duk akan ƴar tata ce, tinda ba kowa ya san ita ɗin wacece ba a wurin suhan ɗin, Shiyasa wasu ma a gabanta suke gulmar. Sheda mata nayi naci Jarabawa gami da nuna mata sakamakon a cikin wayata, tayi murna matuƙa Amman fa jikin ta yayi laƙwas, to ko shine dalilin da nima na kasa bacci jiya, kuma dai gashi taji ban tunkareta da maganar ba, saidai bata kyautata zaton haka ne, ƙila dai ƴan maganganu ne da gulmace gulmace irin na gidan biki da kuma jama'a Hakan ce ta sanya ta share wa da batun, sai a take tambaya ta ko na tura ma Yayan namu? Amsa mata nayi da cewa na tura mashi saidai ƙila bai gani ba, tinda har yanzu bai ce komai ba. A haka muka kwanta tinani fal zuciyar ummata yayin da ni kuma yau nasha bacci na harda saleɓa. A sashen Hajiya kubran kuwa dangin ta kawai suka rage sai ita kanta, duk da wasu suna cen gidan yaran nata, suma kusan duk gobe zasu wuce, su Hajiya Sa'a ɗinne dai sai bayan isha'i suka tafi suna mai kwantar mata da hankalin cewa tasha kurumin ta, zata ga me zai faru bada jimawa ba, ta yarda da hakan tinda ta san hatsabibancin ƙawayen nata, wannan ce ma ta sanya suke juya akalar mazajen nasu, sun zama hotiho a cikin gidan, tini itama suka so su rinjayeta Amman ita tana tsoron shirka, kuma ko ba haka ba in Alhajin nata yaji zai yi mata bore ne sosai kuma ta san halin shi. Bayan kammala shiryawarta ce da daddare ta doshi ɗakin mai gidan nata, so take taje ayi wacce za'ayi, tana so ayi ta ta ƙare su tattara su bar mata gidan ta, lallai tabbas ta yarda da maganar ta mama talatun cewa sun saba taɓa juna, in ba haka ba harma wani yafa mata gyale yake yi a bainar jama'a kuma yake kuranta matarshi, ko a gidan ubanwa ta zama matar tashi,? Ita zata ga yanda wannan al'amarin zai kaya, ko da kuwa zatabar duniyar ne ta kwammace indai ba zata haɗa jini da waɗancen maƙasƙantan Talakawan ba. Saidai Takawa take yi zuwa sashen zuciyar ta taf da wasu wasin ko zai amshi maganar tata, bata ma ko tadda shi a sashen nashi ba, yana cen suna fira dasu kaka zuwaira da Alhaji Auwalu ya sauran ƴan uwansu matan, suna jin damuwoyinsu, saidai Abunda hajiya Kubran bata sani ba kaka zuwaira tazo da maganar Al'ameen da Suhan ɗin kuma duk kansu sunyi na'am da zancen, shi kuma shi da yaya Auwalun sunce abar lamarin a hannun su tukunna har sai sun kammala bincike. A haka firar ta tashi kowa ya nufi sashen nashi, shima yaya Auwalun ya nufi wajen Hajiya Zainab ɗin domin dukkanin ƴan uwanta sun wuce yau bayan kammala tafiya da amaren, jirgi suka hau tinda ana fama da matsalar hanya masalan ma ta Abuja. (Allah ka kawo mana ɗauki, ka bamu zaman lafiya mai ɗorewa a ƙasar tamu) Baiyi mamakin taddata a sashen nashi ba,ya san hakan ce zata faru dama, kuma yana kyautata zaton maganar yaron nata ce ta kawo ta. Bai nuna mata ba Sam, sai a wayan cewa da yayi ya shiga zaulayar ta, bata biye mashi ba tinda ita ba wannan ne gabanta ba. Koda ta fara mashi mitar bai dakatar da ita ba har saida ta gama, shi mamakin ta ma yake yi wallahi, ace mace kaman Hajiya Kubra ta tsaya tana tada jijiyrr wuya akan mutanen da ko abincin da zasu ci basu da, mutanen da suke aiki ƙarƙashin ta abun a tausaya mawa, ita ko ta tara dukiyar da ko mutane dubu zata dinga iya ciyarwa a kulli yaumin har tsawon wasu shekaru ba tare da ta durƙushe ba, saidai da ita Abunda bai sani ba, jinin talakan ne ta tsana, Sam bata so ta haɗa iri dasu kar su goga mata talauci. Tinda yayi hargagin yayi kuma barazanar bataji ba, ya san kuma aikin abokan shawara ne koma ince mazuga, tau ya san ta inda zai ɓullo ma Al'amarin nata. Lallashinta ya shiga yi gami da nuna mata cewa yana sane fa da zancen kuma zai ɗauki matakin da ya dace Amman ba abu bane ba gaggawa, karfa ta manta duka gidan akwai baƙi, tayi haƙurin zuwa goben idan sun bar gidan sai ayi mai yuwuwa, da haka ya lallaɓa ta, ta fice daga ɗakin tana mita, ita lallai atafau ba zata taɓa lamunta ba. "mama fa wallahi ya kamata kiyi wani abu, kina gani fa jiya Abunda yayi ma waccen shegiyar yarinyar a cikin jama'a har yana kiran ta matarshi, kuma naji ƴan uwan Alhajin sunce sun yadda da al'amarin ɗazu da ina gyara masu sashen nasu, gaskiya na fara sarewa da dukkan alamu ba zamu samu nasara ba.... " Mama talatun ce ta buge ma mareen baki, cikin ɓacin rai ta shiga cewa" Kiji ja'irar yarinya ke har baki ma kike mana? Kinsan sharrin da na ja mata kuwa? Ai dolenta ma su bar gidan daga ita har shegiyar uwarta, kuma wallahi ba zata taɓa wankuwa ba a wurin hajiya, Abunda yayi ɗazun ɗin ni ai burgeni ma yayi, bansan ina da sa'a ba sai ɗazu ɗin da ya kamo yarinyar gaban hajiya, wannan shi ke nuna cewa lallai suna aikata baɗalar kenan... " Mareen ce ta katse mahaifiyar tata cikin zaro idanu " umma ba dai sharri kika ja masu ba? Kada fa abun ya shafi masoyin nawa kuma mama, gaskiya ki sake dai, kije kice ba haka aka yi ba, yarinyar kawai ke da laifi.. " " Ke jiman shegiya ƴal banza.. Kina nufin in koma in ƙaryata kaina kenan? Ke wace irin shashasha ce ne? Kinfi son shi a kaina kenan? Tinda gashi har kina neman ki ja mani kora a cikin gidan nan, duk fa Abunda nake yi don ke ne... " " a'a mama kedai faɗi gaskiya, naira kike so dai kici, Amman ni wallahi banji daɗin Abunda kika yi ba har ga Allah, ai ba zan so ace ya taɓa kusantarta ba wallahi, Allah ma ya kiyaye, insha Allah nice nan zan ɓare Abunda dal a leda" Rankwashi mama talatun ta sakar mata a tsakiyar kai, ta kuwa dafe da ƙarfi tana cewa "wash, karki kashe ni mama ai gaskiya na faɗa, gaskiya ki canza wani tsarin dai" bata ce mata ƙala ba sai ma juyawa da tayi ta kwanta, sai kuma cen abun ya ɗaɗimo ta ta juyo tana ba ƴar tata amsa. "Tinda kince haka shikenan na ƙyale ki, kiyi da kanki, ai ina ce ko kuɗin muka samu tare dake za'a ci.." "A'a mama, ni da zan aure shi ai saidai ke ince maki za'a ci tare dake, saidai Abunda na wawuro inzo in ɗan lasa maki a baki don ki ƙara ƙaimin nemo magani" ta faɗa hankalin ta a kwance kaman ba mahaifiyarta take faɗa ma haka ba. (Hmmm Allah shi kyauta, inda akuyar gaba tasha ruwa....) Zaune yake yana ƴan latse latsen shi cikin computer, kaman ance ya kunna datar, ya kuwa kunna gami da shiga WhatsApp ɗin, sai kuma ya ajiye domin massages ɗin su gama shigowa ya gani in da waɗanda zai ma reply, domin da yawa wasu abokanan kasuwancin nashi ta online suke magana. Bilal kuwa yana zaune daga ƙasa bisa carpet ya tankwashe ƙafar shi ɗaya ya miƙe gudar, mug ne a hannun shi yana sipping cofee, ɗan sanyi sanyin Ac ɗin dake aiki ya sanya shi yake jin daɗin cofee ɗin, hannun shi riƙe da remote yana kallon wrestling a tashar MBC Action ɗin, lokaci lokaci yana ma Al'ameen ɗin magana da hankalin shi ya ɗauku ga aikin da yake yi, shima lokaci lokaci yana bashi amsa, duk da sai a daɗe bai tanka mashi ba. Rufe computer ɗin yayi gami da ɗaukar wayar, sannan ya ɗan zama bisa kujerar ya kishingiɗa, daki daki yakebin saƙon in da aka turo mashi, wasu yana basu amsa daidai da saƙon wasu kuma yana wucewa ko ma karantawa ba yayi masalan ma waɗanda ya san ba masu matuƙar amfani bane. Har ya wuce number ɗinta, sai kuma ya dawo ganin kaman ya san number ɗin, domin a wayar da numb ɗin tata take ba'a ita yake chat ba. Buɗewa yayi gami da dubawa Abunda yaga an rubuta kawai shine _*Yaya Result ɗinmu ya fito*_ Sai kuma wani hoto da yagani daga ƙasan Rubutun, buɗewa yayi gami da dubawa a tsanake. A hankali ya shiga faɗin "very good Suhan, Allah yasa ma abun albarka" Bilal ɗinne ya ɗago gami da kallon shi alamar magana kake yi. Baice mashi komai ba sai miƙa mashi wayar da yayi. Amsa yayi gami da dubawa " Wow, wacece wannan?" "Suhaaan.." ya bashi amsa, saidai shi kanshi bai san dalilin nashi na jan sunan haka ba. Da kallo Bilal ɗin ya bishi yana cewa "congrat" sannan ya miƙa mashi wayar yana sake faɗin "Gaskiya tayi ƙoƙari, zata iya samun duk course ɗin da take so" Jinjina mashi kai Al'ameen ɗin yayi yana mai yin typing wani abu ya tura mata, fuskar nan tashi ba alamun dariya fa, duk da yaga cewa tayi ƙoƙari kuma ya jinjina mata, gaskiya za'aje da ita, ga dukkan alamu tanada matuƙar ƙoƙari sosai. "Friend inaso muyi wata magana Pls, Amman inaso ka fahimce ni nima in fahimce ka" Bilal ɗin ya faɗa bayan ya koma ya jingina bayan shi jikin kujerar da Al'ameen ɗin yake kai. "gyara zama yayi alamar ina jinka, domin ya san duk lokacin da Bilal ɗin yayi mashi haka tau fa magana ce mai amfani. Ganin bai tanka ba kuma ya tattara dukkanin natsuwarshi a kanshi ya sanya bai damu ba da rashin tankawar tinda ya san hali, ya fara magana. "Bro bawai nace ka sauka akan bakanka ba ko kuma niyyar auren yarinyar cen don ka fidda su a halin da suke ciki ba, a'a na san kai mai biyayya ne ga iyayen ka, ka sani sarai mom ɗinka tana matuƙar sonka kuma tana ji da kai fiye da dukkanin sauran ƴaƴan ta, kuma tana son dukkanin Abunda kai kake so koda bata nuna maka ba, sai nake ganin wannan al'amarin tinda ta nuna bata so kuma bata goyon baya, mai zai hana ka dakata kagani har zuwa lokacin da zata yarda don kanta ta amince maka? Babba babba ne kuma yaro yaro ne koda kuwa ɗan giwa ne, bamu san Abunda ta hango ba, ba kuma kusan Abunda take hararo maka ba zuwa nan gaba, kuma inaso ka sani yarinyar nan dai ahe's innocent bata san komai ba, dukkanin Abunda ke faruwa ma in ka kalli fuskar ta zaka gane ba wai ta fahimta bane, in banda jiya da kayi Abunda kayi, yau kaga koda giccinta ne? Na tabbata wannan saƙon ma da tayo maka, bata da yanda zata yi ne, baka tinanin zata yi maka kallon mugun mai son raba su da inda suke cin abinci? Me mahaifiyarta zata ɗauka, wanne irin kallo kake so tayi maka? Baka tinanin zasuyi maka kallon kafi ƙarfin su ƙila dai kana da wani buri ne a kansu? Ka taɓa zama kayi tinanin haka? Yeah for sure na san kaman yanda mahaifiyarka ɗin take faɗa, lallai fa kafi ƙarfin wannan yarinyar, kafi ƙarfin aure ta ita ba sa'ar auren ka bace. Kasan baka buƙatar sai na tina maka kalar ƴan matan dake rubibi a kanka, Nidai shawara ta anan ka dakata da dukkanin yaƙin nan daka ɗauko ka saurari mahaifiyarka, lallai zaka ga nasara, Amman ba wai nace karka aure ta bane, saidai inaso tin wuri tin kana wasa, kada abun yazo ya kasance ya zama da gaske ka fara son yarinyar nan a ranka, abun sai yafi rashin daɗi" ya ƙarashe yana waiwaya wa ya kalli cikin ƙwayar idanun abokin nashi. Lallai ko Bilal ɗin bai faɗa ba zantukan nashi sun ratsa zuciyar abokin kuma aminin nashi, shiru yayi yana sauraren maganar da zata fito daga bakin shi. Nisawa Ya Ameen ɗin yayi yana Sauke wata gagarumar ajiyar zuciya, saidai ya kasa buɗe bakin shi balle yace wani abu. Lumshe idanu yayi a karo na biyu yana sake sauke ajiyar zuciyar sannan ya sauko ƙasa ya zauna yana fuskantar abokin nashi cikin ɗaki ya irin ta maza ya fara magana kaman baya so "Na fahimce ka abokina kuma nima na daɗe ina nazarn hakan, saidai zuciya ta ba zata iya jure ganin su cikin wani hali ba, su ɗin mutane ne masu tawakkali Amman inaso kayi mani wata Alfarma guda ɗaya" ya ƙarashe yana kamo hannuwan abokin nashi duka. Sannan ya ɗora da faɗin "bana so ina raɓarta nima, bana so ina jiɓintar al'amarin su sosai, gudun ja masu matsala, saidai ba zan iya jure ganin su a mawuyancin hali ba, inaso zamuyi masanyar aiki ne, zan je in cigaba daga inda ka tsaya, ni kuma inaso ka cigaba daga inda na tsaya, inaso in nisanci gidan nan gabaki ɗaya, inaso ka ɗauki alƙawalin kula dasu da karatun Suhan har zuwa gamawarta, ka riƙe mani alƙawali da amana" Cikin ɗan zaro idanu bilal ɗinmke cewa "Wat? Me kake nufi ne Friend? Kana nufin a kanta zaka bar ƙasar taka da mahaifn naka? Kasan ne kake faɗa kuwa? Jinjina mashi kai yayi alamar tabbatas da Abunda yake faɗa ɗin sannan ya ɗora da faɗin " Zuciya ta, ta fara saba wa da bauta mata, ta fara saba wa dajin ɗuriyar ta a kullum, ba zan iya jure zama a muhalli ɗaya da ita ba, ba tare da na kusanci inda suke ba, Nidai kawai inaso ka amince, gobe goben nan nake son barin ƙasar da asuba zan faɗa ma abba zanje yin wani abu, kai ne zaka cigaba da kula da komai, tini na daɗe ina wannan nazarn, wannan tasa na gama shirya komai yanda zaka fahimta" Ya faɗa yana jawo laptop ɗin tashi, gami da kunna ta ya shiga nuna ma bilal ɗin schedule ɗin aikin, duk da ya ɗan san wasu, saidai ayyukan da aka ƙirƙiro daga baya, "zaka gane abokina, kuma mu cigaba da waya duk Abunda baka gane ba, bayan auren yarinyar na maka alƙawari zan dawo kai kuma ka koma bakin aiki ka" Ɗan jim bilal ɗin yayi, sai kuma ya nisa yana cewa "Ba damuwa Al'ameen zanyi maka yanda kake so, nima na fuskanci gara tafiyar taka, akan ka zauna matsaloli su taru suyi yawa, gara ka tafi, ita kuma insha Allah ba zan taɓa bari tayi kewar rashin ka ba, zan kula da ita kaman yanda kake yi, harma da mahaifiyar tata. Ɗan murmushi yayi da iyakar shi leɓo, yana jin wani ƙuna daga cen cikin ɓargonshi, gani yake yi kaman yayi sallama da ita ne. Ya ƙudurta a ranshi cewa zai warware matsalar da ya sanya yarinyar da mahaifiyarta kafin barin shi ƙasar a gobe. Cikin daren yaba Bilal ɗin number ɗinta gami da goge ta a cikin wayar shi baki ɗaya yayi blocking ta yanda koda ta kira shi ma ko ta neme shi ba zata samu ba. A haka suka kwanta kowa jigum babu mai tanka ma wani. Duk da kafin su kwanta ɗin saida ya haɗa traveling bag ɗinshi, da duk abubuwan da zai iya buƙata. To dama dai ƙasar ba baƙuwarshi bace a, hasalima kamfanin da bilal ɗin yake running na Alhaji Mustapha ɗinne, wannan ne ta sanya komai zai zo da sauƙi baya buƙatar amincewar kowa. Bayan an taso sallar asuba ɗinne ya biyo mahaifin nashi har sashen shi, ganin hakan ne Alhajin ya san cewa da magana, sauraren shi yayi tsab, gami da fahimtar yaron nashi, Allah sarki ashe ma babu wata maganar soyayya ko makamancin ta a tsakanin shi da yarinyar, gamsuwa yayi da bayanin Al'ameen ɗin yayi da yace idan Allah ya bata miji kafin ya dawo kawai a aurar da ita ga wanda take so, kuma yana buƙatar ya gaya ma hajiya kubran cewa ya janye sukda daga nan sashen Alhajin wajen Hajiya kubran zai wuce. Addu'a da fatan nasara ya bishi da ita, yana mai faɗa mashi lallai kafin ya wuce yaje yayi ma kaka zuwaira sallama kuma duk ya jejje gidajen ƙannan nashi domin yaga muhallin nasu. Hajiyar ba wai ta yarda da maganar da yazo mata da ita bace, saida taga fa lallai shi da gaske yake yi, ba kunya ta rungume shi tana sanya mashi albarka gami da nuna mashi zallar farin cikin ta, harda irin abun nan na Munafurci take cewa "Allah sarki yarinya da har na ƙullace ta, to ai ba komai zasu iya komawa ma bakin aikin su in Alhajin ya amince" To shi dama burin shi kenan ya warware ƙullin da ya san duk kanshi ne ake ta wannan dambarwr, ko ba komai daga baya idan suhan ɗin ta gane dalilin tafiyar tashi zata sanya mashi albarka da gode ma bakin nasu da ba zai rasa abinci ta dalilin shi ba. Sashen nashi ya koma yana ba bilal labarin yanda sukayi da hajiya, sunyi mamaki kwarai matuƙa, oh shi kenan ashe shi talaka ba mutum baneba? Sai da ya kira yayi booking flight kafin gari ya idasa wayewa, aka sanar mashi sai ƙarfe biyar na yamma jirgin zai tashi, hakan ce ta sanya ya gane cewa yana da sauran time da zai gama aiwatar da dukkanin abubuwan da zai yi ɗin. Bayan na tashi ne na share ko ina na gyara, umman tawa ce tayi mani tuni da zuwa gidan Hafsat ɗin, hakan ce ta sanya ni kiranta domin tayi mani kwatance, ta shaida mani zata turo sadeeq ɗin ya ɗaukeni, ita da har ma tayi fushi, gashi afnan yanzu zata tafi gidan Aunty Saudat, za'a barni ni ɗaya, ƙawayen nata sakkon tafiya sukayi ha yar bata da kyau. Ƙarfe sha biyu kuwa sai ga sadeeq ɗin, umman tawa ce tayi mani a dawo lafiya gami da cewa in kula kada in kai marece, da to na amsa mata ina mai ficewa daga gidan. Daga nesa ya hango fitowarta har zuwa shiga motar tata, kauda kai yayi, baya so ya sake shiga Al'amarin ta tinda anyi Wancen ta kwaranye, bilal ɗin na kula dashi, dama tare zasu fita zuwa office ɗin tare suke da dogarawan da aka bashi, wanda yace duk kansu suit zasu sanya ɗaya daya iya mota ya dingabjannbilal ɗin ɗaya kuma ya zama massinger ɗin office ɗinshi kowanne zai biya shi albashin shi mai tsoka, aikuwa sunyi murna, kuma sun yaba da karamcin ubangidan nasu da kullum suke jin labarin tarin alkhairanshi ga mutane Office ɗin suka isa ya nunnuna mashi komai, sannan yayi mashi maganar ɗaukar matasa ƴan family ɗin sadeeq mijin hafsat ɗin, sannan suka wuce ya nunnuna mashi building ɗinshi na estate da aka kammala komai sai lounching da za'ayi, sannan ya kikkira manajojin shi na sauran kamfanonin da suke sauran jihohnn ya haɗasu da bilal ɗin ta yadda komai zasu tunkari bilal ɗin kai tsaye. Daganan suka wuce gidan Aunty Saudat bayan sunyi sallar azahar, sun matuƙar yabawa da tsarin gidan, gida ne tanƙamemen babu Abunda babu na kayan more rayuwa, cen suka tadda Afnan har yanzu akwai sauran mutane ƙawayen Saudat ɗin a gidan, daganan suka wuce tare harda Afnan zuwa gidan Aunty Nihal ɗin, Afnan kuwa tin a gidan Saudat take rigimar barin ƙasar da zai yi, sukda zai koma kusa dasu ne, kuma zasu fi saurin ganin shi anan, saidai bata so yayi ma suhan ɗin nisa, gani take yi idan suhan ɗin ta kucce mashi da wuya ya iya samun wata mai nagartarta, ita kau Saudat ɗin a take tayi murna, ko ba komai sun san waccen maganar ta wuce. Itama Nihal gidan ta yayi matuƙar kyau, kowa da kalar kaya ta wanda su suka zaɓosu da kansu, basu wani jima ba, saboda suna sauri ne, kuma itama akwai dangin mijin ta sosai a gidan kusan ma cike yake sosai da yake ita dangin shi suna zaune ne Abuja. Gidan hafsat ne na ƙarshe don haka daga cen zasu koma gidan yayi ma iyayen nashi sallama. Bamusan da zuwan su ba, da yake abokan sadeeq ɗin na gari yau zasu wuce suma, ya sanya na kama mata mukayi masu special girki ko ƙarasowa ba suyi ba sai ga su Ya ameen ɗin. Ko ba komai taji daɗin zuwan su, dama tana so ta ƙara yi masu godiya akan irin hidimar da suka sha da su da dangin mijin nata. Ceman tayi in shirya masu abinci, nace mata ban iyaka kunya nake ji, tace ai dole inji kunya na san Abunda muka tafka rannan, sai dole kowa ya gane kuna soyayya. Ƙyaleta nayi ban tanka mata ba, har ta gama shirya masu abincin, da sunce ba zasu ci ba, Amman jin ƙamshin girkin yasa bilal cewa ta zuba masu kaɗan, har yake tambayar ta ita kaɗai a gidan? Cemashi tayi mu biyu ne, baƙi zata yi ne ma Shiyasa Suhan ɗin tayi masu girki, don da ita cewa tayi sunsha lemo, Amman suhan ɗin tace masu akwai fa masu barin ƙasar ke kin yarda azo maku kara kubar mutum ya tafi da yunwa. Duk zubar da take yi Ya ameen ɗin na jin ta bai tanka ba, ya dai ɗan ci abincin, duk da test ɗin abincin ya mashi daɗi, saidai kuma bai san Abunda ya to kare mashi maƙoshi ba da ya hana shi walwala ayau. Hafsat ɗin ce take ta kawaici ganin bai nemeni ba duk kuwa da ta sanar dashi cewa ina gidan, ni kuma na kasa fitowa daga kitchen tin da ɗazu naga text ɗinshi yana tambaya ta wai ne ya hanani fitowa ɗazu? To ban dai bashi amsa ba tinda banda abun cewa ɗin. "Yaya ko in turo maka Suhan ɗin?" ta tambaye shi daidai lokacin da yake goge baki da ƴar tissue. "Ɗan kallon bilal ɗin yayi sannan yace" Ƙyaleta kawai Hafsatu Sauri mukeyi tafiya zanyi n.... "." Kirawo ta" cewr bilal ɗin da ya tari numfashi abokin nashi. "To tace gami da miƙewa ta shiga kitchen ɗin da nake tsaye zafi duk yabi ya isheni. " Kije inji Ya Ameen da Abokinshi" haka kawai ta faɗa tana mai juyawa zata fice Saurin jawo hannunta nayi ta dawo baya, cikin ɗan waro idanu waje na shiga cewa "Ke... Kina nufin a haka zan fita babu ko gyale jikina? Kalli fa skirt ɗina ya kama ni sosai... " To miye? Ba yayyenki baneba?" ta faɗa tana janye hannuwan ta gami da idasa ficewa ta ƙyaleni tsaye ina ta rarraba idanu. Ganin ba mafita kuma na kusan share minti biyar ya sanya ni shahadar fitowa Daidai lokacin da Al'ameen ɗin ya kai duban shi ga agogon da yake ɗaure a wutsiyar hannun shi na hagu "Kaga fa Malam idan ba zata fito ba mu wuce kawai kasan fa...." Maganar ta maƙale daidai lokacin da na fito ina ta matse matsen jiki da dukkan alamu ni kaina kunyar kayan nawa nake ji. Idanunmu suka sarƙe cikin na juna, ya kai kusan second biyar yana kallon a, lokaci guda ya janye idanun nashi ga barin kallon nawa, daidai lokacin ni kuma na kai zaune bisa kujera ina gaida su. A gaggauce suka amsa gami da tambaya ta lafiyar mu lau dai ko? Lafiya na amsa mashi, bilal ɗinne ke ƙara mani congrat na Jarabawa lokacin da Al'ameen ɗin ya kai kallon shi kaina yana mai cewa "Tafiya ta kama ni, ga Bilal nan ko me kenan sai ki tuntuɓe shi, zai gama maki komai insha Allah" yana gama faɗar haka ya miƙe yana shirin ficewa. Hafsat ɗince ta fito riƙe da wata jikkar kwali mai kyau a hannuwan ta, ta ƙara sa ga Al'ameen ɗin gami da miƙa mashi tana mashi fatan Allah ya tsare ya kiyaye hanya. Bilal ne ya maida kallon shi kaina shima yana mai miƙewa gami da ce mani "Ya bani number ɗinki insha Allah zan kira ki" ya ƙara sa shima yana mai juyawa ya fice. Har gaban danƙareriyar motar tashi da his excelency ya bashi ta raka su tana mai waving ɗinsu har suka fita a harabrr gidan da mai gadi ta wangale masu gate. Domin gidan na Hafsat duk yace ma na sauran ban wuri a kyau da haɗuwa. Hatta kayan da aka yi ma hafsat ɗin saida sadeeq ɗin ya cire su ya cenza mata wasu sabbi dal masu masifar kyau ba tare kuma da dangin shi kun sani ba gudun ƴan tsogunguma. A falin ta iskeni zaune jikina sanyi ƙalau, to me ke shirin faruwa ne? Nidai na san Al'ameen ɗin ba haka yake yi mani ba, na kula ma ko kallon a baya son yi a yau, ko na bashi haushi ne rannan dana ruga ɗaki? Ko dai banyi ƙoƙari bane...... "Ke Suhan lafiyarki ƙlau kuwa? Naga jikin ki yayi sanyi, da ɗina dake wallahi wani lokaci ke baƙauya ce, ko irin ƴar rakiyar nan ma baki Iya ba" Firgigit nayi ina mai binta da ido bansan lokacin da na samu kaina da tambayar ta ba "wai da gaske Ya Ameen tafiya zai yi?" "eah mana Suhan, waike da kina nufin baki sani ba? Bai gaya maki ba?" "Huh..." Na sauke ajiyar zuciya lokaci guda ina mai ce mata "wallahi ban sani ba Hafsat" Mamaki ta shiga yi, har tana zaulayar ta wai wannan wace irin soyayya ce?banza nayi mata ban tanka mata ba, Amman fa gaskiya zan faɗa jikina ya mutu murus wallahi. Su kansu ƴan kankiyan sunyi mamakin tafiyar, Amman da yake sun san yana yin aikin nashi sai sukayi mashi fatan alkhairi, sun ɗauka zuwan na aje a dawo ne. Ƙarfe biyar bilal ɗin ya kai shi airport ɗin, ba ɓata lokaci jirgin nasu ya ɗaga zuwa america..... #cying Wash gaskiya na gaji fans gashi nan nayi maku na kwana uku. ~Oum-Deedat ce~