[1/10, 9:57 PM] Billy Galadanci: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi   Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha.       *Wannan shafin nakine 'Yar uwata Hafsat Elham, Allah yabar mana zumuncinmu, Yakuma albarkaci rayuwarki Ameen*                          01 Hafsat!!  Malamin nasu ya daka mata tsawa,d'aukacin yaran class d'in sun tsorata da wannan tsawar amma Hafsat ko'a jikinta a zahiri ma ko d'ago kanta batayi ta Kalli malamin ba, zuwa yayi cikin azama ya daki teburin da take Kai yace cikin fusata "How dare you! Are u stupid? " a hankali ta miqe daga zaman datake sannan cikin ko inkula tace "No sir I'm not" cikin qaraji yace "what!!  Repeat what u just said now" cikeda kwanciyar hankali ba alamun tsoro tattare da ita tace " I just say I'm not sir" murmushin mugunta yayi dama yana jiranta a cike yake da ita fam "Hafsat look into my eyes and repeat after me OK? "batayi magana ba ya kuma cewa "oya say that you,you are stupid " wani shu'umin murmushi tayi sannan tace "You! You are stupid!!!! " zaro idonshi yayi sabida ba haka yake tsammanin zatace ba yace " How dare you, are u in ur senses? " ita d'inma cikeda raini tace tana Zare ido  Kamar yanda yayi tace  " How dare you? Are you in ur senses?? " cikin azama ya sanya qaton hannunshi irinna yarbawa ya zabga mata lafiyayyan Mari seda taga jiri dafe wurin tayi ta saka kuka aikam malamin se wani cicika yakeyi irin ya hasala, hanyar fita waje tayi Kai tsaye office na principal nasu ta nufa Tanata uban kuka irinna shagwab'abb'un yarannan marasa ta ido, PC na ganinta ya miqe tsaye ya sani idan ba'ayi sa'a ba lokacin korar wani malamin ne yazo "Hafsat lapiya me kikewa kuka haka?  Meya  sameki?" tana kukan ta kwashe qarya da gaskiya ta sanar masa, a haka aka tarar wa malamin sanda ya bata haquri sannan tace ta yadda bazata fad'awa daddyn tab'a, domin kuwa mahaifin nata shine mamallakin makarantar kuma itadin yar gatace gaba da baya ba Wanda ya isa ya taba Hafsat Poojah ya zauna lapiya mahaifinta be had'a kowa da itaba kasancewar ita k'adaice 'ya d'aya  tilo da Allah ya bashi se kuwa yayan ta shammaz......     Class dinsu ta koma,dashigarta mazan class d'in suka dauki ihu,pooja!pooja!pooja!....wani Yaro dan masu ji da naira nalura yana dai daga cikin taqadarun students d'in makarantar yace,    Poojah babe ina fatan kinsa an lallasa wannan malamin?, Abokinsa Wanda duk halinsu d'aya yace, Ni bama Sonai takaishi Kara ba,   Sonayi itama ta kifa masa Mari ya za'ayi tana yar me makaranta ya Mareta?, Haushi taji yadda yanuna rashin gamsuwarsa da abinda tayi, wato ma bata burgeshi ba harara ta kwadamai kafin tace, Banga damar ramawa bane,kaima kasan inkifa masa Marin yana dai daga cikin kananun ayyukana kamar yadda Kaima baka wuce in zabga MA Marin ba mtswww, Baki asake yake kallonta se Abokinsa wizkid Yasoma ihun kiran sunanta,poojah!poojah!kina burgeni wallahi, Cikin halinta na basarwa tace,    Dalla kuyi mana shiru ninagaji da wannan banzan hayaniyar naku, Sum sum mata da mazan dake a tsaye  suka Nemi mazaunin su batareda sunyi magana ba,  Wannan shine kadai aikin hafsat a makaranta taga damar submitting  plane sheet lokacin exam kuma duk teacher Dinda yai failing  dinta ze rasaa aikinsa ne bakuma Dan wai batasan mezata rubutaba sedan kawai ta nuna isa da tantagaryar shagwab ganin makarantar  ta mahaifinta ne kuma baya ganin laifin ta aduk shirmen dazatayi,  1:50pm aka Tashe su tun daga sama ta leqo bata hango motar driver dinta ba, tafiya take bata kallon gabanta hartagama saukowa daga stairs d'in be k'araso ba,tafiya take Tana tunanin hukuncin dazatayi wa Ayuba yau,tana isa gate segashi yazo dasauri yazo ya Karbijakarta ya sa bayan motar itama yabude mata tashiga Se cin magani take,  Wallahi tallahi tayarce tayi faci dan Allah kiyi hakuri karkisa narasa hanyar cin abinci na,ayuba yasoma bata hakuri bayan yashiga motar, Wannan shine babban kuskuren daka tafka banaso kadamu kunnuwana dawannan kalmar tahakuri Dan bawai zan yibane, Gumi yake ta ko'ina,shine gatan kannen sa da mahaifiyarsu,wannan aikin dayake ciyarda su dashi,      Dagudu ta k'arasa wurin daddy ta tana kuka,   Lafiya dai Hafsat waye yataba min ke?, Daddy wannan ayuban ne yabarni har Nazo gate dakafa, Subhuhanalillahi, Ayuba dama Kai ya akayi haka?,    Wallahi ranka yadade tayarce tayi faci kuyi hakuri,     Sautin kukanta Takara, Tsaya Hafsat  me kikeso ayi yanzu?   Daddy ni akoreshi banasonshi, Kudubi girman Allah kiyi hakuri insha Allah wannan shine nakarshe bazan kuma irin hakaba wannan aikin shine hanyar abincina, Furr taki saurarensa daddy  yace to za akawo miki sabo kaikuma Ayuba zaka ringa fita da hajiya dakumawanke motocin gidan, godiya yayi yajuya yana godewa uban giji daya sanya dukda kasancewar hafsat batada m mahaifanta nagartattun mutanene dasuka san girman dan adam matuka.... A tsakiyar parlor ta fara wurgi da jakarta da sannan tacire takalminta a hanyar dazata sadata da matattakalar benen gidan komai a inda ta samu take wurgi dashi gata da tsafta amma bata farin cikin ganin masu aikin gidan suna hutawa,mero me aiki ce ta sameta a daki tace bayan ta saka kayanta da tabi ta tsinto akasa cikin laundry basket ta ajiye school ba da sandal a ma'ajiyarsu " kulelen daddy yau me kike sha'awar ci??" ko kallonta batayi hakan ya tabbatar wa mero bawai kulatan zatayi ba sabida indai da sabo toko ta saba da rashin kunyar Hafsat,wannan ya sanya ta juya kawai taje ta hado mata snacks da apple and avocado smoothie ta kawo mata a saman table na coffee chairs dake a parlor dinta ta ajiye mata sannan ta kalleta tana zaune tana danna remote domin canja channel tace da ita " Hafsat ga favorite dinki nan na hado miki" a wulaknce ta kalli kayan tace "Grill fish and chips,plus sugarcaine and apple juice nakeso ni kenan kullum fulawa so kikeyi na zama bom bom adena yayi na" shiru mero tayi se can tace " ki daure ki dan rage yunwa da wannan sena hado miki wancan din" harara ta wurga mata "nace baran ciba ana dolene?" kwashe kayan mero tayi ta juya tana girgiza kai a hakan ma wai meron kadai ke shiri da ita acikin yan aikin,kuma itace abokiyar hiranta sabida tana mata gatana, itadin ta kasance abokiyar wasan mahaifiyanta ta wurin uwa auren wuri aka mata a qauye Allah yawa mjjin rasuwa itadin bazata wuce shekaru ashirin ba aduniya sedai akwai kaifin hankali,kusan shekararta goma agidan tun hafsat na yar shekaru hudu,sun shaqu sosai da ita. Koda ta dawo daga school mamakin mutanen data gani birjik a kofar gidan tasomayi mafiya hawa daga cikinsu 'yan gidena ma'ana y'an uwansune,bata wani kawo komai arantaba tazo zata wuce su,abba haris ta gani da gudu ta ruga ta fad'a jikinsa tace cikeda shagwab'a "Abba haris zanbika gun ummi" murmushi yayi yace "kulele ai bakui hutu ba,ina saura kwana bakwai kuyi hutu? Bazan ma turo driver ba da kaina zanzo na d'aukeki" murmushin itama tayi sannan tace "To abba zaka sauya mun waya? Anfa dena yayin tawa?" "Lele ai dole na sauya miki yanzu blackberry bold 4 zan siya miki,an dena yayi curve dinnan" tsalle ta kuma ta fada jikinnshi sannan tayi ciki aguje,tab'e baki shammaz dake tsaye yayi wanda akanshi akayi wannan taron murnar dawowanshi dayayi shekaru kusan 8 baya kasar yace aranshi "kaddai har yanzu su daddy basu dena shagwab'a hafsat ba,inko hakane da matsala a tarbiyar yarinyar,ko yanzu ya fahimci ba wanda ta gayar a duk yawan mutanen dake wurin.....A parlor ma ba wanda tawa magana se Aunty surayyah wacce ita kadaice take masifar tsoro indai har tana wuri tofa iskancin hafsat qasa qasa yakeyi,kallon ta surayya tayi tace " ke Hafsat ni kadai kika gani anan sauran fa? ,d'an turo baki tayi sannan ta juya ta kalli jama'ar parlor din a wahalce tamkar wacce zatayi kuka tace "Ina wuninku" amsawa sukayi daganan suma saka mata dariya ganin irin shirmen datakeyi mafiya akasarinsu kuwa sun dauki hakan datayi amatsayin kuruciya,wasunsu kuwa sunsani sarai iskancine sundai kama bakinsu ne sabida suna samun alkhairi a wurin uwarta Haj Nasara wacce bata had'a kowa da ita ba,tana sharar k'wallah tayi sama a hanya ta hadu da mairo kalllanta tayi tace "Kulele momy ya akai?? Waye ya tabamun babbar 'yata" wurgi tayi da jakar ta tace "Bayan Aunty surayyane tace wai dole sena gayar da mutane bayan kuma arayuwa ni natsani gayar da kowa ma wlhy" rungu mota tayi jikinta "Haba babyn dady kiyi hakuri kinji ba wanda ze kuma tilastaki gayar da mutane amma fa ki sani ita gaisuwar wajibice idan ba hakaba yanzu zakiji ana cewa bakida kirki" wucewa kurin tayi bayan ga qwace jikinta ba tare da tayi magana ba,bayan like an hour se gatanan tafito sanye da vest da gajeren wando iya gwiwa tana tsotsa alawar lollipop,mutane sund'an ragu se yan uwa na dole batare data kalli kowa ba tayi dining serving warmers tagani tuma tuma awurin tsayawa tayi daga inda take ta kwallah ihun kiran mero "mero!!" wanda ya mayarda hankalin akasarin mutanen dake parlor akanta,da sauri mero tazo tace "Lele ya akai?" zumburo baki tayi tace "Dayake kinfison mutanen nan dani shine kika barni da yunwa tun dawona nake jiran abincina,ni ki zubamun to" kallon ta mero tayi tace "Dady ne ya sakani aiki kiyi hakuri mezan saka miki?" duk abinnan dasuke a gaban idon shammaz ne, ko kallonta batayi ba ta saka alawar datakesha a baki ta hau tsotsa sannan ta hard'e hannayenta gu daya,ganin haka mero ta gano rigima takeji yasanya ta dauki plate ta saka mata snacks da papaer chicken ta juyo ta miqa mata, karb'a tayi sannan ta kifar da abincin a wurin cikeda raini da shagwaba tace "ni wannan nace dake ina so? Shreded chicken zanci" batayi auneba taji saukar lapiyayyen mari wanda ya kusan zautar da ita,dafe wurin tayi ta saka kuka kowa a parlor din ya taso ana baiwa Shammaz haquri ita kuwa mero tazo da sauri ta riqe hafsat tana rarrashinta,wani kallo shammaz ya wurgawa mero, cikin fada ya furta " Maryam zan mareki wlhy kema,maza ki saketa ta clearing wannan mess datayi" jikinta har rawa yakeyi ta duqa ta soma tattare wurin tana sharar k'wallah tana gamawa yace " se kinci wannan din yar rainin hankali da zaki wani zo tana tambayarki kina iya shege sannan yanzu an zuba miki ki kifar an gaya miki a qasa ake haqowa" juyawa tayi zata haura sama da plate a hannu tana kuka yace cikin daga murya "Maza zo nan zaki zauna ki cinyeshi a gabana" dawowa tayi ta janyo kujerar dining daya tana kuka tanaci harta cinye tatas,momy dai batace komai ba amma harga Allah bataji dadin abinda shammaz yayiwa Hafsat ba agaban mutane,kumama tsabar rashin tunani daga dawowarshi duk wanda yaga yayiwa qanwarshi wannan abin aiseyaga tamkar baya san tane.......... Mom Nuaiym ce [1/10, 9:57 PM] Billy Galadanci:         *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin.            wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                  02 Hawa saman tayi bayan ta kammalawa cinyewa taje rufe kofar d'akinta tasaka wani uban kuka tanata faman shura qafa,duk abinda ta samu seta fasa ita adole zuciya,su momy sunzo juyin duniya sunyi akan ta bude kofar d'akin amma fir taqi se dad'a sautin kukanta takeyi Aunty surayya ma datazo tayita fadan amma yau ko gezau,surayyace takira Yaa shammaz yazo bakin k'ofar yace cikin daga murya "Hafsat Allah idan har kika kuskura na sameki a d'akin batare da kin budeshiba ranki ne zeyi matukar b'aci anan" cikeda fargaba ta bude kofar d'akin ta qura masa ido jan hannunta yayi sukayi waje sannan yakaita b'angarensa,zaunar da ita yayi suna fuskantar juna yace "ke har yanzu Hafsat girma da hankali basu wadace kiba? Mero sa'an kice sannan yanzu wannan uban borin dakikeyi a daki ke kadai wa kikewa shi? Sarai kinsan halina tsaf zan zaneki karkiga kamar yanzu na dawo zaneki zanyi sosai,kuma idan na kuma ganin kina wannan kukan ko hawaye daya na gani a idonki sena zaneki yanzumma kece da kanki zaki gyara barnar dakikayi a dakinki,sakaryar yarinya kawa,kuma daga yau duk bayan kwana biyu kece zaki riqa zuwa kina gyaramun wannan bangaren nawa,ki share ki goge da komai kina jina?" da sauri ta daga masa kai a ranta tace "Ina kammala exam zan gudu gidan Abba wlhy bazan zauna wannan mugun ya kashe niba" a fili kuma godiya ta masa sannan ta fita daga dakin..... *Washe gari*          Yaa shaam na zaune a a daya daga cikin gujerun da aka qawata ht dake farfajiyan gidan dasu yana karatun news paper hannunsa daya na riqe da cup na hot meantleaf coffee yana kurba a hankali,ganin Hafsat ta fito ya sanya da sauri kuma cikeda mamaki ya mayarda dubanshi zuwaga wrist warch dake hannunshi,dagowa ya kumayi yaga driver yazo ya bude mata tashiga gidan baya ta zauna,driver din ya kwallawa kira yazo ya da sauri ya durqusa yana jiran cewar sa,kamar baya sanyin magana yace " Ina zakujene k'arfe tara da rabi na safe?" kanshi a qasa yace "Yallab'ai Haj qarama zankai makaranta?" Haj k'arama ya nanata a ransa sannan a sarari yace "yaushe yakamata ace kana fitowa kaita makaranta?" "yallab'ai dama da safene kullum k'arfe bakwai anan gidan yakemun,hajiyar ne bata fitowa se sanda taga dama" cikin mamaki yace "Ita hafsat ne setaga daman zuwa skul zataje? Maza jekamun kiranta" koda friver ya sanar mata tana fitowa mota kuka ta saka ta kwasa ciki aguje,miqewa shima yayi a fusace yabi bayanta,daddy da mommy na zaune  a dining taruga ta fada jikin dady,kan wani cikinsu yayi magana sega yaa shaam ya shigo a fusace,momy ce tayi saurin magana "shaam lapiyanka kuwa meya sameka kaida qanwarka haka taketa kuka" daddy ya kalla yace "Amma daddy sabida Allah kuna kallo se yanzu hafsat zataje makaranta qarfe goma saura fa?? Wannan wane irin tarbiya aka mata ba kwab'a ba komai ace yarinya se sanda taga dama zataje skul wannan ai ba soyayya aciki" shiru daddy yayi saboda yasan gaskia shaam ya fada momy ce tace cikin quluwa "Kaga shammaz nafa kula tun dawowarka jiyannan ka takura yarinyarnan,hafsat baccin safe ne da ita kamar me ya kakeso muyi? " kallon momy yayi rai a b'ace yace "wannan ai rashin sone idan naga zatayi rashin hankali na barta,wannan ba takura aciki tsantsar soyayya ce nake mata,kuma ita jakar inace bata ma tsoron duka irin wannan mugun lattin ai dole setasha duka kullum" "makarantar mahaifinku take zuwa,se abinda taga dama takeyi ba wanda yake takura ta wlhy"  tsaki yaja yace "wlhy ba wanda ya isa ya b'atamun qanwa ina numfashi haba mana daddy ni haka kayimun? Ni bansan wannan wane irinn qata kuke nunawa hafsat ba sekace a kanta kuka fara ganin 'ya'ya wlhy ni idan suka gama wannan jlce din sauya mata skul zanyi" momy zatayi magana daddy ya hanata "duk yanda kayi  daidai ne shammaz na tsame hannuna a lamuran hafsat tunda magajinta yazo haj kema naki idone lallai idan kina taka masa birki zakija masa raini a gunta kuma kinsan ya isa da ita sannan kuma ke karan kanki nasha sanar miki zaki ruguza rayuwar hafsat ne idan kina biye mata,yarinyar nan tanada kokari sosai zama mu iya cewa gifted idan bakya nuna mata muhimmancin karatun watsarwa zatayi" shiru momy tayi badan ranta yaso hakan ba  daganan daddy ya daga hafsat ya bar gidan gaba daya,a gaba shaam ya saka hafsat har wurin mota yayi kiran driver din yace "Daga yau ita zata riqa bude mota da kanta tashiga sannan karna kuma jin kace mata wata hajiya karama,kuma ita zata riqa gayar dakai ba wai ka gaidata ba,yarinya sa'ar y'arka zaka zauna kana wa biyayyah kuma kullum idan tawuce 7/30 batazo kun wuce skul d'in ba kazo ka sanarmu" tana kuka tawuce suka je....... *Bayan wata daya*      Tun bayan da yaa shaam ya dawo gaba daya rayuwar poojah ta sauya ko a makaranta sun fahimci hakan,sabida tazamo so quiet a rayuwarta ta tsani yaa shaam kuma masifar tsoransa takeji matuqa,zuwa yanzu duk wani abu dazesa yamata fad'a tofa gudunsa takeyi kuma idan tana parlor d'n k'asa ya shigo yanzu zata gudu shi kanshi ya kula da hakan kuma harga Allah baya san rashin walwalarta a kusa dashi danya kula momy ma ta sauya masa ba kamar daba gani takeyi tamkar yana cutar mata da yarinya......yauma kamar kullum hafsat na zaune a parlor tana kallon wani catoon series na barbie yaa shaam ya shigo ko kallonta beyiba ya zauna tana ganin haka ta miqe zata gudu yace yana danna wayar hannunshi " Hafsat zo" kawai seta soma hawaye dawowa tayi ta tsuguna a gabanshi tana sharar k'wallah,kan yayi magana phone nashi ya soma ringing d'agawa yayi ya kurawa hafsat data sadda kanta ido,mamaki yakeyi me aka mata take wannan hawayen ,cikin sanyin murya yace "Haleema na ya akayi?" a d'aya bangaren seji yayi tana kukan shagwab'a "Haba mana boo me kwana biyu kana cikin garinnan amma sam bakazo ka ganni ba Allah yau idan har bakazoba ni gobe da sassafe zan wuce wana sokoto kuma Allah bazan dawoba sekaje da kanka" k'arayin kasa da murya yayi "Haba leemah dear,zanzo yau dinnan inshaa Allah kuma ma yaune alqawarin new phone nakifa nama isa naqi zuwa,u expect me anything 7:pm inshaa Allah" daga nan sukayi sallama akan se yazo kallon hafsat yakumayi yace "Lele zoki zauna kusa dani" da mamaki ta d'ago ta kalleshi amma bata taso d'inba sanda yakuma cewa "zomana ki zauna anan,magana zamuyi" yafada yana nuna kusa dashi d'in, jiki a mace tazo ta zauna kusa dashi ya kalleta yace " haba lelen dady kukan kuma na menene eye? Ba abinda zan miki,nifa yayan kine uwa daya uba daya,me zaisa kina tsoro na har haka daga yauma mun zama best friends kinji" murmushi tayi tace "To na gode" a sanyaye "Dama zancen school ne,zakice premier kuma interview din gobe ne,ss1 zakiyi interview nasu" girgiza masa kai kurun tayi sannan tace "Zanje nayi sallah se goben" ta miqe " ki shirya zamuje dake wurin yayarki yawo,ko bazakiba?" fara'arta fa fadada tace "Zanje mana gun matar dazaka aura ko yaa shaam Aunty leemah?" murmushi yamata yace "ea can 6:45pm kina sallame magrib ki sameni mota,bana karbar uzurin african time?" juyawa tayi tana murmushi tana kuma mamakin sauyawar yayan nata lokaci daya,dukkuwa dayake ta hango sosai ba wasa a lamuransa musamman akan karatu"..... Mom nuaiym. [1/10, 9:57 PM] Billy Galadanci: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi Vote me on wattpadd@68billygaladanchi. *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 03 Hafsat kyakyawar yarinya ce fara qal me tsayin gashin kai,siririyace samb'al sedai fa ba gaba ba baya duk da yake bazamu yankewa surarta hukunciba kasancewarta yarinya y'ar shekaru goma sha hud'u wanda har yanzu bata gama hada girman jikinta ba,tana da dogon hanci me tsayin gaske da manya manyan dara daran fararen idanu masu wani d'igon zaiba zaiba aciki koda wane lokaci idanun zaka gansu a lumshe tana da d'an mitsitsin baki amma lips nata suna da dan kauri sedai ba cancanba,sosai takeda gashin gira dana girar ido baki wuluk,sannan kuma suman kanta yazo har k'asan goshinta kwance luf luf gwanin ban sha'awa...... Ilai kuwa lokacin daya fad'a lokacin ta isa jikin motarsa sanye da wando jeans blue da red top ta yane kanta da mayafi red tayi kyau matuqa,batare dayace komai ba yaja suka tafi sanda suka kama hanya sannan yace "Poojah" gabantane ya yanke yayi mugun fad'uwa jinya kirata da wannan sunan ta kasa cewa komai,hannunta ya kamo ya saka a nashi yace "kinaji ina kiranki zakimun banza,ina poojah shine sunan da friends naki suke kiranki kuma karki manta we r now friends arn't we?" murmushi tayi tace "sure mana we are" murmushin ya kuma yi "Wane kalan waya kikeso kinsanfa ban kawo miki tsara baba shine zan fanshe" itafa sam bata sakin jikinta dashi harga Allah tsoron shi takeyi murmushin takumayi "ko wanne ma inaso" yagano a tsorace take ya sanya be kuma cewa komaiba,dasuka isa k'ofar gidansu leemah seyace tashiga ta gaisa dasu umman leemah inyaso su fito tare,ba musu tashiga gidan,da sallama ta isa har kofar parlor din amma ba wanda ya ansata haka ta danna kai ta shiga dama hafsa ba manners,tana zuwa taga ashe kowama yana zazzaune a tsakiyar parlor din suna zazzaune abinsu suna hira,yan mata ne sunfi su shida se babbar mace a tsakiyansu, kallonta kowa keyi amma ba wanda yace da ita kanzil a kasale tace "Sannunku Aunty haleemah nake nema?" babbar macen ce tace "ke wacece yarinya baki iya gaisuwa bane?" kallon matar take ta qara lumshe lumsassun idanunta tace a wahalce "Namayi kokarin ce muku sannu ai ina tundazu nake ta rafka uwar sallama kukamun banza" da mamajin furucinta umman ta miqe tsaye tace "wacece ke yarinya meye kike nema awurin haleema?" cikeda takaici tace " yaa shaam ne yace nazo na gayarda umman matarsa daze aura haleemah, kuma yace nace ta fito su tafi inda zasun" ana haka sega haleemah tafito,kallon Hafsat tayi tace "ke meye haka lapiya?" kallonta kurun hafsat tayi tace "yaa shaam na jiranki a waje" tana kaiwa nan ta juya abinta bata ko kalletaba,da gudu taje tariqe rigar hafsa ta baya tasanya hannu ta dungure mata kai tare da kai mata ranqwashi tace "y'ar gidan uban waye me dazaki wa mutane iskanci haka ake fadar saqo" atake idon hafsat ya cicciko tace " Yar gidan uban yaa shaam ceni kuma nice qanwarsa dayake da ita hafsat,akwai wani magana ne??" da sauri leemah ta seseta kanta tace "Allah sarki hafsat kulele,ya kike wlhy ban ganekiba,nasha fitsararrun yaran unguwane ashe babbar sis ce,umma kinga qanwar shaam" tafada tana kallon umman tare da kashe mata ido daya alamar a saisaita zancen,murmushin yaqe umman ta somayi "Laa wai itace kinsan fani nafi ganewa ace shammaz sam datace shaam ban gane wa take nufi ba,kikace hafsat sunanta sannu kinji 'yata zonan kusa dani,kinga munata surutu wlhy bamuji sallamarkiba" ahaka dai suka rinqa zuba uban surutu wananna yace mata wannan wancan yace wannan,dazasu fita kuwa aka rinqa kwaso mata kyaututtuka,itadai shigowar farko dukda tanada kuruciya gidan be mataba wayannan yan matan masu zubin karuwai.....!!!! Amota kuwa leemah se janta takeyi da hira ita kuwa taqi ta saki jikinta gaba d'aya a tsure take hankalinta baya jikinta tunaninta daya yazatayi kar yaya ya auri wannan itafa lokaci daya taji ta tsaneta da yan gidansu gaba daya,haka sukaje siyan wayar yaa shaam ya siya mata iri daya dana leemah wanda atake ta fahimci cewar bataji dadi ba sabida kallonsa tayi tace "Boo me wannan qaramar yarinyar zaka siyawa danqareriyar waya irin wannan a gaskiya kunaso ku b'atata da yawa" a yanda kuma hafsat ta fahimta shima beji dadin yanda tayi ba domin kuwa be kula da zancenta ba,daganan ya siya musu ice cream da kaza ya mayarda leemah gida....tana shiga kuwa tacire mayafin ta fada tsakiyar parlon da sukecin kasuwa tace "Umma wlhy da matsala wannan shekiyar qanwar tasa itace matsalar tamu,baya shayin mata komai,kinga yawan kaza da ice cream d'aya ya siya mana abin haushin ma wai hatta waya iri d'aya ya siya mana yarinya sekace kishiyata,ina wannan yarinyar ina riqe babbar waya har haka wlhy rashin hankali ne tsantsa,kuma tsaf maganinta zamuyi domin idan ba haka ba ita zata takurawa rayuwarmu ta hanamu cimma burinmu" gyada umman tayi tace "Ai maganin shegiya zamuyi ku barni da ita gashi sam batada kunya ko kadan wlhy amma damu take zancen!!!! *Washe gari pooja a bisa rashin sani tashiga interview na wayanda ke neman shiga ss3 kuma abun mamaki tazo na daya acikin su kusan 32 koda suka je bincike aka tabbatar musu taci akan ta soma zuwa on monday,monday tana zuwa taga an kaita ss3 mamaki ya kamata tace dasu kuskure ne ita ss1 zataje su kuwa suka kafe akan ko exam datayi na ss3 ne kuma itace overall gaba daya,haka ta zauna ita kadai qaramar yarinya acikin manya kowa se tsokanarta yake dukta takura,tana dawowa gida kai tsaye part din yaa shaam ta nufa harda kukanta ta sanar masa "ke wace iriyar sakarai ce dazaki shige exam daba nakuba?" share kwallanta tayi tace "yaa shaam nifa na gaji dajirane inajin ankira badge 3 seniours sena shiga kawai ashe ss3 ne" shiru yayi yace taje se gobe,juyin duniya yayi dasu akan yarinyace amma sun dage akan bazasu mayarda overall student tasu abaya ba,seda aka qara bata exam din lapiya lau ta lashe komai dole haka ya hakura akan ta zauna din,data dawo gida yayi kiranta akan ya akayi ta iya abubuwan ss3 anan yakeji cewar a library na school dinsu har books na nursery take karantawa dana ss3 kuma abinda bata ganeba taje gun malaminsu ko principal idan besan amsaba ya hada ta da malamin dake subject din" gamsuwa yayi da bayanan yamata fatan alkhairi sannan ta juya ciki...... Mom Nua'iym [1/10, 9:57 PM] Billy Galadanci:       *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi Vote me on wattpadd@68billygaladanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                 04 Sam yaa shaam baya saurarawa Elham indai zancen karatune,har me extra lesson yanema bata dawowa gida se 5,kuma anayin isha  malamin islamiyyarsu zezo ita da mero sekuma 9,wannan ne ya sanya sam batada time,a haka har lokacin waec da neco yazo lapiya lau sukayi suka gama a wannan lokacin hafsat takeda shekaru sha biyar a duniya qawayenta dasuke school tare duk sun girmeta babbar qawarta me suna huda shekarunta sha takwas ma,sosai suka shaqu ba kadan ba tana d'aura hafsat akan hanyoyi masu kyau sabida tanada hankali kuma ba laifi tana ragewa dukda yake shagwab'a irinna hafsat bawai tana denawa bane kurun dai ta rage yiwa mutane rashin kunya......wannan kenan     Yaa shaam shine babban yaron da Alhaj muhammad gaya dakuma haj Nasara suka haifa wanda bayan haihuwarsa sun cire rai gaba daya da cewar zasu qara haihuwa kasancewar kafin samuwarshi ma ansha fama,sosai suke qaunar shammaz ba kad'an ba wanda bayan an haifi hafsat ma soyayyarshi ko kad'an be ragu ba a zukatansu,sedai fa sun d'auki soyayyar duniya sun d'aura akan hafsat basu bama har Abba haris wanda ya kasance qanine a wurin daddy uwa d'aya uba d'aya,a wurin mahaifansu su hudu ne kacal maza biyu mata biyu haj maryam dakuma autarsu haj Harira,Abba haris yanada yara bakwai,Surayya itace babba se yan biyu hassana da husaina,se khairiyya da Auwal sannan Abduljabbar da Abdurqadir...Maryam kuwa yaranta biyu rak Bunyameen da yusuf,harira keda biyar saratu,sa'adatu,shamsiyyah, sha'awanatu se autarta safiyyah.batada namiji ko d'aya gaba dayan wannan babban family din su a qaunar junansu baka tab'ajin wani munafurci ya taso a tsakaninsu ko rashin jituwa koya yana kokarin hakuri da d'an uwansa kazalika kuma dukkaninsu 'yan boko ne masu ji da kud'i muhammad shine  babban cikinsu sannan kuma gaba dayansu yafisu kud'i,mahaifiyarsu wacce sunanta hafsat taci tana nan daram ita da mijinta mlm Abubakar gaya,sune ma sukafi kowa shagwaba hafsat domin kuwa suna matukar kaunar yarinyar.......      Shaam tun yana secondry school yake soyayya da leemah lokacin yana ss3 ita kuwa tana jss3,sam leemah bawai yarinya ce,sabida yanzu tayi 27 yrs ko shaam shekarunshi 8 baya kasar be dawoba seda yazama cikakken likitan zuciya kuma ma kan yaje yayi kusan 2yrs da gama makaranta bejeba,duk sanda ya dawo hutu suna manne da juna,sam wlhy 'yan gidansu leemah basuda kunya ko kad'an akansu sannan kuma dukkansu basusan girman mahaifinsba yan matane su bakwai rasss se uwarsu mara kunya da hankali sun mayarda mahaifinsu wagili basa ganin girmansa sabida bashida karfi sune da kansu suke karuwanci suna cida kansu da uwarsu,sam ba dan Allah leemah ta nacewa shaam shikadai yake haukansa amma itakam ta da biyu takeyi......     Hafsat zaune asaman stairs dake sadaka da saman gidan tana latsa wayarta,sam hankalinta baya kan wayar ta rasa dalilin daya sanya zuciyarta take azalzalarta akan yayanta shaam,sam idan bata ganshiba a wuni wani zazzafan zazzabi takeji yana rufeta,ganin har shabiyun rana ya gota be shigoba ya sanya tamiqe ta nufi part d'inshi,knocking tasomayi a hankali shikuwa ya taso ya bud'e,kallon mamaki yamata yace "poojah yadai" d'an murmushi ta msa tace "Dama nayi tunanin baka karyaba bane kuma banga ka shigo cikiba,shine nace barinzo in duba inga ko lapiya" mamaki yarinyar ta bashi sosai sabida shidai wannan yarinyar har yanzu be gama gamsuwa da nutsuwartaba gyaran murya yayi yace "Tunda aka fara zancen aurennan senakeji ko yunwar ma banaji mantawa ma nakeyi da abinci abubuwa sunmin yawa gashi im all alone" murmishin yaqe tayi haka kawai taji gabanta na faduwa jin yayi zancen aurennan,kuma ta rasa dalilin jin hakan dukkuwa dayake sam ita bata damu da wannan shegiyar matar da yayan nata ze aura ba "Aikam yaya daka dena zama da yunwa,baka ganin zaka kasa hidimomin idan ulcer ya damk'eka mezan dafa maka ne??" murmushi yayi yace "ke me kika iya lelen daddy?" shagwab'e fuska tayi tace "yaya bayan tunda ka dawo gaba daya ka sauyamun rayuwa,tare dani fa ake girki a gida,nifa yanzu koma meye zan iya girka maka tumba snacks ba" shi mamakin wani shagwaba da take masa ma yakeyi,san yan kwanakinnan ya kasa gane kan kanwar tasa se kallonta yayi yace "jeki ki kawo mun koma meye da aka gika kuma kizo ki tayani zaben kalan decoration da zamuyi gun dinner" batayi magana ta juya tanajin wani zafi a ranta,abincinma kasa dawowa kawo masa tayi shikuwa dama hankalinshi na online yana neman decor na bugawa a jarida sabida yaci burin wannan auren.....koda taje daki ta kwanta kasa yin komai tayi a haka huda ta kirata "Huda yadai?" "lapiya lau lil friend,zanzo gidanku da mijina da zan saura zuwa 4 na yamma seku gaisa,jiya jiyannan ya dawo daga uk ya matsamun yanaso yaga wannan poojah din danafi santa dashi" murmushi kurun tayi tace "toh" har yamma bata fitoba gashi mommy tana abuja, a haka har Huda tazo gidan,kallonta tayi bayan ta shigo bedroom din ta ganta a zaune tace "Poojah lapiyanki kuwa?? Tunda na kiraki naji muryanki wani iri" dan guntun tsaki taja tace "Huda wlhy na tsani inji ana zancen aurennan na yaa shaam gaba daya dena riqa ji jikina yana mutuwa,kuma banajin dadin rayuwata" kallon nutsuwa huda ta mata sannan tace " Hafsat lapiyanki kuwa?? Meye hadinki da auren yayanki keda ya dace ace kina masa murna ma kinmaga yanda kika dawo kuwa,waini yau dinnan ma kinci abinci?" lumshe idonta tayi sannan ta bude su a hankali zuwa yanzu har sun cicciko tace "Huda wlhy banida lapiya wataqila aljanaine suka shafeni,bana iyacin abinci tun bikinnan saura wata d'aya sannan kuma bana iya zama banga yaa shaam daga zaran na wuni ban ganshiba sena ringa jin zazzabi na damuna kuma idan muna tare banaso mu rabu,huda anya kuwa ba aljanai bane suka shafeni??" sosai huda ke nazarin kalaman hafsat,secan ta nisa tace "Poojah da gaske uwarku d'aya kuma ubanku d'aya da yaa shaam?" d'an tab'e fuska tayi sannan tace "wannan wane irin tambaya ne huda,wlhy uwarmu daya ubanmu d'aya dashi wannan bako tantama,bayan haihuwarshi kuwa ancire rai za'a kara samun haihuwa Allah ya kawoni" jinjina kai huda tayi jikinta duk yayi sanyi,tabbas hafsat abin tausayice domin kuwa wannan ba tantama san yayan nata takeyi kuma ta sani sarai koma menene akwai wata a qasa,ubangiji baya taba jarabtar bawansa da abinda baze iya d'aukaba,tayaya ma kanwa zata so yayanta har haka,amma a sarari se wayancewa tayi tace "Hafsat kiyayyar dakikewa matar da yayanki ze aura tayi yawa hadda kasa cin abinci har haka"murmushi kurun tayi domin kuwa ita kanta batasan cewar soyayya bace aranta!!!!!!!!! [1/10, 9:57 PM] Billy Galadanci: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi Vote me on whattpad@chi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                 05 Da dare bayan isha malaminsu na islamiyyah yazo,sam hankalinta baya jikinta haka tafito tafiya takeyi tamkar wacce k'wai ya fashewa a ciki gaba d'aya hankalinta baya jikinta,motsi d'aya idan tayi da tunanin yayan nata take yinshi, A farfajiyar gidan ta hangoshi yana waya se raha yakeyi kallo d'aya zaka masa ka tabbatar cewar yana cikin farin ciki,haka kawai lokaci d'aya ta tsinci kanta dajin wani haushi mara misaltuwa ta tabbatar da Aunty leemah yake waya,kan tayi aune hawaye ya fara sintiri akan fuskarta,juyawa tayi sam bazata iya zuwa makarantar ba,karo tayi da mero tana kukan,kallon mamaki mero ta mata tace " kulele lapiya dai?? Meyake damunki?" batace komai ba tayi sama abinta rufe kofar tayi tana rusar uban kuka tarasa meke damunta...Allah sarki hafsat ga quruciya yarinya yar shekaru goma sha biyar na neman shiga damuwa akan abinda ta kasa gane meye shi,haka hafsa ta dawo sukuku dukta rame tayi baqi sam bakace ita bace,a haka har lokacin bikin yayan nata yazo..... A parlo zaune ta tarar da Daddy da momy suna hira,zuwa tayi ta zauna kusa da momy batace komai ba,kallonta baban yayi yace "Hafsatu kulele na meyake damunki ne wai kwana biyu?" murmushi tayi kurin batace komai ba momy tace "Girmane fa yatasowa Hafsat ai Alhj baka ganin wani sabuwar nutsuwa daya tasowa kulelen taka" dariya yayi yace "yar daddy gashi kinyi qanqanta da zuwa jami'a wane skul zaki je ko computer school zan sakaki?" murmushi takumayi sannan tace "Daddy naci jamb fa,kusan 240 kumama ai yanzu na girma banwa jami'a qanqantaba dan Allah idan na samu admtn ka barni naje" "ba damuwa yar daddy Allah ya sa ki samu admtn din,wane couse kikeso?" "Education English nacika dakuma pure Elhglish duk wanda na samu zanyi ne" adua ya mata kanwani yayi magana sega yaa Shaam ya shigo durkusawa yayi ya miqawa daddynshi envelope,wasu invitation cards ne masu kyau aka ciro daga ciki,daddy se washe baki yakeyi yana ya kalli yaronshi yace "Allah ya sanya Alkhairi my son,ranar da akayi reception ranar zamuyi tarin bude clinic dinka,sabida yafi" haka kawai hafsat ta kasa controling kanta ganin invitation card na d'aurin auren ta saka kuka wiwi,kowa hankalinshi ya dawo kanta se tambayarta suke lapiya? Amma i a da gudunta ta ruga dakinta,ta fad'a kan gado se kuka me karfi ya subuce mata hannu ta saka ta dafe inda takejin wani azababben radad'i a haka Shammaz ya shigo ya sameta hannu yasaka ya d'agota ya d'aurata a jikinshi yana mejin tausayinta a hankali ya furta "Little sister meya sameki har haka? Waye ya tab'aki kike wannan uban kukan haka?" acikin kuka tace "nima ban sani ba yaa shaam ko wane lokaci idan akayi zancen aurenka sena riqa ji tamkar zan mutu nabar duniya gaba daya,idan na wuni ban gankaba banajin dadin Rayuwata idan naga kana murna kana farin ciki indai akan zancen aurenkane sena riqajin zuciya na yana tafarfasa yaa shaam wlhy banasan kayi aurennan kaga nan? Ta nuna zuciyar ta da hannunta "zafi yakemun zogi nakeji tamkar zan mutu,tun saura wata daya aurenka na rasa nutsuwata duk sanda na tuna ko abinci bana iya ci bansan meyake damuna ba anya yaa shaam baka ganin aljanaine suka shafeni?? Mesa ada ba ruwana dakai? Mesa ban damu da rashinka ba akusa dani? Mesa ada bana leqen shige da ficenka ta window? Meyasa ko maima yaa shaam,a yanda nakeji gameda zancen aurennan idn akayishi mutuwa zanyi" k'ura mata ido kurin yayi harta kai aya,mamakin kalamanta ne yake shirin birkita masa k'walwa sam yakasa saisaita tunanin shi idan har abinda zuciyar ke sanar masa gaskiya ne lallai kuwa da babbar matsala a gaba,sabida sam shi wannan yarinyar kallon qanwa yake mata uwa daya uba daya,kai koda ba haka ba shisam idan ba leeman shiba se rijiya,gaba daya hankalinshi ya tashi cikeda dabara ya kalleta yace mata "Lallai kam hafsat se aljanai sabida kin taba ganin inda qanwar mutum uwa daya uba daya tayi kishi kotaji haushi akan zeyi aure,ki sani su e sukeso su shiga a tsakaninmu sam basa san suga muna qaunar junanmu,kuma ta Allah ba tasu ba sabida haka kiyi hakuri ki dinga adua kinji,inshaa Allah zasu rabu dake,kuma karki sake ki fadawa kowa wannan maganar" kai kurun ta gyad'a masa yayi da mero dake jikin k'ofa a lab'e ta dafe qirji tana salallami domin kuwa tun ba yauba ta fahimci sarai hafsat san shaam takeyi,inkuwa hakane iska tana wahalar dame kayan kara domin kodajin wannan zancen dayaa shaam yayi ta kula baya ma buqa tar ta sanarwa wani atilastashi aurenta yafi san son nashi ya kasheta kenan,aranta ta kudirta gayawa momy gaskiya sedai ya kashe ta...... Bayan isha mero taje ta samu momy a d'aki bayan ta gaidata ta zauna ta fuskanceta sannan tace "Momy wata muhimmiyar magana nakeso muyi dangane da hafsat domin kuwa akwai matsala akasa" kallonta momy tayi batare da bawa maganar muhimmanciba tace "Ina jinki" "Momy na sani bani kadaiba dukkan nin mutanen gidannan sun kula cewar Kulele bata cikin nutsuwarta da walwala sam,sa'annan ko abinci bataci gashi batama koda kallon data sabayi" gyada kai kurun mony tayi taci gaba "To wannan kukan dakikaga tanayi a d'azu ba komai bane illah kishin zancen auren yaa shaam datakeyi domin kuwa da bakinta naji tana sanar masa,take ta kwashe komai ta sanar mata har sanda taji tana baiwa qawarta labari da abinda qawar tace mata har tambayar data mata akan zancen yayanta ne kuwa uwa daya uba daya?" shiru momy tayi tana nazarin kalaman mero tabbas idan basanshi takeyiba ba abunda ze sanya taji hakan,inko hakane to wlhy da sake domin kuwa so sone amma sankai yafi komai,da wannan tamiqe zuwa b'angaren daddy......ita kuwa Hafsat a daidai wannan lokacin ta shirya zuwa roqar daddy akan ya barta taje gidan abba haris batasan yan biki su cika gidan ana hayaniya,zama momy tayi ta zayyanewa daddy komai shi kuwa cikin fada yace "Haba Nasara!!! Ina nidake muka zauna muka roqi dangi akan su rufe zancen cewa shaamaz da Hafsat ba uwarsu daya ubansu daya ba har abada,tayaya ma yarinya zata so yayanta inama hafsat ina sanin meye so?? Meta tauna vare ta had'a arayuwa?? " cikin fusata momyn tace "Haba Alhj mesanya agaban duniya ka nuna kanasan gmhafsat amma a bad'ini ba haka bane,karfa ma manta tsakaninta da shaam waka haifa da cikinka?? Itace 'ya daya tilo da Allah ya baka,tayaya akan abunda bekai ya kawo ba seka dau zafi haka,tunda har tana sanshi mezai hana a hadasu susu biyu a aura masa kowa ya huta" hara daddy ya wurga mata yace "wlhy kinji na rantse kobada shaam ba bazan wa hafsat aure yanzu ba,tsabar mata bakuda hankali,ke kinga karma ki nuna mata kinsan tana sanshi ki barta tayita haukanta,amma ba zancen auren a tsakaninsu yana da wacce yakeso ita kuwa taji dashi karna kuma jin wannan maganar wlhy" hafsat dake a waje kuma taji komai dafe qirjinta tayi tace "Ba daddynmu daya dakai ba yaa shaam to waye babanka?? Menene ma dangar takarmj dakai?? SO SO kuma tayaya meye mashi? Wannan shine abunda nakejin friend kullum tana mun magana akanshi game da saurayinta da gaske san yaa shaam nakeyi? Anya ban dakkowa kaina wahala ba kuwa? Lallai kuwa da babban aiki jaaa ma agabana. Mom Nua'iym              [1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi Wattpad@galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                   06 Jiki ba k'wari ta juya zuwa d'akinta,sam hankalin hafsat beyi yawan dazatayi zurfin tunaniba ta kasa tariyo komai,wayarta ta ciro daga k'asan filo ta kira huda,d'agawar farko tace "Huda dan Allah kina ina yanzu??" da mamaki hudan tace "Ina kan hanyar zuwa gun Ashraf tela" to yayi nima ganinan zuwa da maganar danike so muyi" kan huda tayi magana ta katse wayan,da sauri ta zari hijab tayi k'asa a hanya tayi karo da yaa shaam ko kallonshi batayiba sabida hankalinta sam baya jikinta,driver din momy ta gani tayi kiranshi da hannu,ta fada mota sukayi gaba....a shagon janyo hannun huda tayi suka dawo mota ta kalleta bayan tayiwa driver din umarni daya fita waje tace "Huda wai da gaske sosai ni Hafsat ina san yaa shammaz??" kallon ta huda tayi cikeda nutsuwa tace "Ban fahimce kiba?" kwashe komai tayi dataji su momy na fada ta gayawa huda ta qara da cewan "ke kadaine zaki iya fadamun gaskia dan Allah waida gaske wannan abun danaketaji gameda yaa shaam shine so? Kuma shi din suwaye iyayenshi??" sosai huda ta gano hafsat kuruciya ya mata yawa, banda haka ina zatasan su waye iyayen shaam,ni sawa tayi tace "poojah ki nutsu mana,zancen gaskiya ko shakka banayi kina san yayanki kuma sosai bawai kadanba,amma abunda nakeso dake shine kibi komai a hankali sabida kinga already an kusa aurenshi kuma tunda su momy basusan kinji maganar suba karki fadawa kowa karkuma ki nuna musu,wannan abun dakikeji idan yana waya da wacce ze aura da kuma idan ana zancen aurenshi shi ake kira kishi,kuma kishin ya miki yawa ina tausaya miki sabida tunkan kisan meye so da kishi kika fara kinsan kuwa illan kishi a tattare dake? Kishi masifane kamar yanda yake halittane na Allah ajikin d'an adam sedai da yake na wani yafi na wani zafin,dan Allah hafsat ki daure ki yakice sanshi a ranki,a yanda na fahimta da kika masa bayanin abinda kikeji game dashi sarai ya gano sanshi kike sabida baya muradin ki yasanya yace karki sanar wa kowa,ki manta dashi kici gaba da kallonshi a matsayin yayanki uwa d'aya uba d'aya" hawayen daketa faman tarewane suka gangaro mata tace "Huda lallai so masifa ne kuma kishi fitinane,indai haka so yake to a gaskiya da matsala,ni bansan sanda na fara sanshiba tayaya zakice in cire sanshi a raina? Nida bansan yanda ya shiga ba ya zansan yanda zan cire?? Wlhy bazan iyaba" tausayinta huda taji ta janyota ta rungume tana bubbuga bayanta a hankali,a haka suka rabu jiki ba k'wari..... *Bayan sati biyu* Sosai aka cashe wurin bikin yaa shaam kuma acikin part d'inshi dake gidan anan aka kawo amarya Haleematu,yau sati daya kenan da tariyarta,kullum hafsat ke zuwa tayata aiki,kasancewar ba abinda takeyi agidan,ta d'auki shawarar qawarta ta dena nuna komai a idon mutane harma momy ta soma qaryata zancen cewar hafsat tana san yayan nata....yauma kamar kullum tana kitchen din Aunty haleema tana tayata aiki,suna d'an tab'a hira yaa shaam ya shigo,ba kunya suka rungume juna har tana manna masa sumba a wuya " Baby yadai? Bana hanaki yawan aikinnan ba? Kije ki huta mana tunda ga Hafsat ta iya komai" kallon shi tai cikeda kissa tace "Haba honey yaya daga zuwan yarinya tayani aiki seka wani ce na barta tayi,nooo ni banasan small oga ta tasha wahala" hancinta ya danja ta saka qara yace "Kinga Baby da gaske ki rage yawan aikinnan ita wannan sakaryar yarinyar shagwab'abb'iyan yarinyane yanzu take koyan aiki ki barta ta koya kekuwa semu huta abunmu" wani langwabe kai tayi tace "Haba shaam meye hakannan wai,nika tafi idan muka gama zanzo" hannu biyu ya saka dukda zaman ta katuwa ya dauketa yabar kitchen din da ita,ita kuwa dama gulmane haka takeso ya sanya bata wani musa masa ba, hannu hafsat ta sanya ta share k'wallan daya kwaranyo mata "Yaa Allah ka yayemun wannan masifar,Allah ka rabani da k'aunar yaa shaam,Allah ka ciremun kishinsa,Allah ka kawomun agaji" wannan itace adu'ar datakeyi a sarari cikin kuka,tafi mintuna biyar a haka,kanta barwa Allah taci gaba da aikinta.....haka rayuwa taci gaba wa hafsat kullum itace da bauta agidan yaa shaam sekace wata yar aiki,shi kuwa kullum kwanan duniya qara tsanarta yakeyi yakuma rasa dalilin tsanar dayake wa kanwar tashi wanda a sanda tana qarama bashida wacce takeso sama da ita,amma yanzu tun sanda yagano sanshi takeyi seya dauki hakan a matsayin raini ya d'auki karan tsana ya d'aura mata kullum acikin bautawa gidanshi take ita kuwa yi hawai takeyi domin ta faranta masa,momy kuwa komai akan idonta take tafiya yanda ake takurawa yarta ba karamun damunta yakeba,duk kuma sanda tayi magana sekaga fuskar daddy ta sauya akan hakan. Hafsat da huda sun samu admsn a Usman d'an fodiyo university dake sokoto,inda dukkansu suke karantar English,dabadan hafsat tanada kokari ba dabazata gane komai ba a makaranta kasancewar gaba daya hankalinta yana kan yaa shaam kullum kwanann duniya da begensa take kwana kuma take tashi,shekarunta goma sha shida yanzu yakamata ace ta qara girma irinna tashen balagan nan amma sam damuwa ya hana ta,tanaso ta yakice wa kanta soyayyar yaa shaam amma ta kasa,ganin rayuwar gidan yamata k'unci ya sanya tabar sama road gaba daya ta tattare kayanta tace gidan Abba haris zataje gun khairiyyah dayake itace tsarar haihuwarta,momy bata hanataba kasancewar tasani sarai 'yar tata tana cikin damuwa,gwara ma tane candin kota samu sassaucin abinda yayan nata kemata wannan kenan. Tunda hafsat takoma gidan Abba haris se kewar shaam ya taso mata,shaam seyayi sati biyu bezo wurinsu abba haris ba,dukkuwa dayake sune iyayensa na ainahi,sabida kawaici,lokacin da yayan abban haris yayi aure wato mahaifin hafsat yajima be haihuba kai har haris yayi aure suka haifi shaam,shine fa suka baiwa yayanshi shi na har abada ganin yana matukar san y'ay'a amma Allah be kawo masa ba shiya sanya hafsat datazo sanda ba'a zataba bata gane cewar ba mahaifansu daya ba na haihuwa se daga bisani,domin kuwa an cire rai kamar daga sama Allah ya kawowa haj nasara cikinta samun hafsat be sauya komai ba na dangane dankaunar dasu momy da daddy kewa shaam ba......duk tabi ta qara yamutsewa batada kiza kiza,har Abba haris ya fahimci haka,kuma yayi juyin duniyarnan amma sam tace ita ba abunda ike damunta,da wannan yayi kiran khairiyya yace lallai tabi yar uwarta taji meke damunta cikin hikima domin ya kula ko wannan dawowan da tayi da dalili. Da dare hafsat ta tashi kukan data sama na rashin yayanta,wayanta ta dauko ta qurawa hotonsa ido a sarari kuwa tana kuka tace "yaa Allah ina rokonka,ya ubangijin sammai da kassai,ya Allah ka ceceni Allah ka cire mun san yaa shaam a zuciyana,Allah ka rabani da kaunarshi,Allah ka ceci rayuwata karna mutu"" kuka me tsanani ya kwace mata khairiyya da ke kwance tana kallonta tana kuma saurarenta da mamaki tazo ta dafa tace "Hafsat yaa shaam kuma? So? So naji kina ambata,shine zaki bari san dan uwanki ya hallakaki har haka? Kinga kuwa yanda kika dawo sekace ba poojah kulelen daddy ba? Meyasa zakiyi shiru kibar abu aranki bayan kuma kinada gatan da za'a miki abinda kikeso?" tana kuka ta kasa magana dakyar khairrii ta rarrasheta tayi shiru sannan ta kalleta tace "Anya khairiyyah yaa shaam ze tab'a sona kuwa? Baze taba sona ba shekaru biyu kenan da yasan i a sanshi amma banda tsana ba abunda yake qara nunamun kullum,ina kyautata zaton a duk fadin duniyarnan a zuciyar yaa shaam wanda ya tsana ni kebin shedan,nikuwa bansan mesaba nayi rashin sa'an zuwana duniya wlhy inaga san yaa shaam ne zeyi ajalina amma dan Allah karki sanarwa kowa kinji?" hannunta ta kama tace "Wlhy bazan barki cikin azaba bayan inada maganinta,wlhy sena gayawa Abba gobe da safe tayaya poojah?? Tayaya san dan uwanki ze illataki bayan kinada gatanki? Ni gaskiya sena fad'a" kwanciya tayi ajikin khairiyya tama kasa magana......washe gari khairii ko breakfast batayiba taje ta kwashe komai ta sanarwa Abba,aikam ya hau bambami yace "Amma shine kulelen tayi shiru,shekaru biyu tun lokacin aurenshi fa kenan,lallai wannan yarinyar tasha wahala wlhy bazata sab'uba dole dan ubanshi seya aureta shi kuwa kodan halaccin ubanta akanshi,maza tashi kije anjima zan nemeku" tana barin wurin ya daga waya ya kira yayanshi da shaam akan zezo gidan ya samesu akwai magana,da khairii da Hafsat dakuma umman su khairri aka je.....bayan an gaggaisa ya kalki yayan nashi yace "Yaya wannan ramar da damuwar da hafsat ke kici duk akan tanasan yayanta ne shaam aurenshi take sanyi ni kuwa na yanke hukuncin ayi auren tunda yanada halin yin hakan" tamkar saukar aradu haka yaa shaam yaji wani maganar da sauri ya d'ago ya kalli abba haris,daddy ne yace "Haris ai ita kace tana sanshi shifa bamuji ta bakinsa ba,kai shammaz menene ra'ayinka?" k'asa yayi da kanshi kan yace "Daddy ni bawai bana san hafsat bane ba amma dama tun farko ita na fara aura amma sam ni ba tsarin mata biyu a ra'ayina tayi hakuri kawai ta nemi wani" umma ce ta yanka masa wani mari dabesan da zuwansa ba "Kai mara hankalin inane dazaka taramu anan ka gaya mana wani tsari to bari kaji wallahil azeem ko yanzu na mutu indai ba hafsat ce tace bata sankaba bazata aure kaba kaine kaqi wlhy Allah ya isa ban yafe maka ba indai kaine ka kuma cewa bazaka auretaba" se huci take abba haris ma yace "Lallai wannan anyi dan banzan yaro,toka sani ninan na yanke hukunci kuma wlhy koda wasa kakuma furta bakaso na sallamawa duniya kai aure kuma nanda sati biyu masu zuwa zan daura idan muka kaima ita ka dawo mana da gawarta washe gari tsabar rashin san rugura tsari" shidai bece komai ba yayinda hafsat se kuka takeyi daddy yace "haris ina darai zaka yankewa shaam hukunci? Ina nine ubansa? To baza ai masa auren dole ba indai ina numfashi" ran abba haris ya baci ya kalli yayanshi yace "yaya iya tsawon zamana dakai ban taba maka musu ba amma wlhy wannan karon bazan lamunta a cutar mun da 'ya ba,wlhy indai har ina numfashi nanda sati biyu zan daura aurensu sannan kuma idan yace yafasa Allah ya isa tsakanina dashi" jikin daddy ne yayi sanyi kuma harga Allah shima yanasan auren,momy ma dadi fal aranta sabida tasani hafsat nasan shaam sosai......bayan sun watse hafsat na d'akinta yayinda kahirri ke toilet shaam ya shigo tamkar wani mayunwacin zaki,tana ganin ta mike a tsorace,Da baya da baya take tafiya har suka isa bango,ya sanya hannunshi ya matse hannunta sosai yace "Kika zab'i aurena bayan kinsan na tsaneki ko? Kika zab'i aurena bayan kinsan zakisha uquba a hannuna? Kika zab'i had'ani da iyayena sabida tsabar san zuciya ko?? Wlhy ki sani se kin gwammace kid'a da karatu indai muddin kika yarda kika shigo hannuna,sekin gwammace da bakizo duniyaba sekin kasa tantance nine kuwa kobani bane,shawara nake baki ki janye inba haka ba ko hmmm wlhy senci qaniyarki da mai da yaji,k'aramar yarinya se iskanci banza tambad'addi'ya....yana kaiwa nan ya saketa ya juya,ita yauma ta kasa koda kukanne sabida bakin ciki,gashi sam bazata fasa aurenshiba koda ze yanakatane gida biyu idan anyi auren......hmmm hafsat kenan anya baki daukowa kanki masifa ba kuwa??.... Mon Nua'iym [1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* Wannan shafin nakine kyauta Aunty me jiddah musa,Allahu ya wadata ki da hasken rayuwa ya sanyaki a aljannarsa madaukakiya 08 Mamakine ya kama hafsat sanda ta farka taga har qarfe tara ta gota sauqinta daya tana fashin sallah,jiki ba kwari ta tashi ta shige toilet tayi wanka ta sanya rigarta mara nauyi pink color doguwace har qasa ta sanya kula bayan ta tufke kanta a tsakiya sannan ta fito zuwa ktchn indomie da kwai ta dafa ta dawo parlor tad'an tsakura kad'an ita har yanzu ta kasa gane meyene yake damunta wasu lokutan tanaso tayi kuka amma fir se hawayen suqi zuwa tama kasa tunanin komai gaba d'aya,ta kunna uban fankacecen tvn dake cikin parlor din amma takasa fahimtar me akeyi abinda yafi bata mamaki shine batasan tunanin me takeyiba idan za'a yankata batasn me take tunaniba abu daya ta sani shine wani zafi na musamman zuciyarta ke azabtar da ita dashi wanda kuruciyarta ta sanya ta kasa gane dalilin zugin....a haka yaa shaam ya shigo ya sameta bayan yayi amfani da key dinshi yashigo gidan kasancewar yayita faman knocking bata bude ba,kallon tsana ya wurga mata sannan yace " ke hafsat dama tsabar rainin hankaline ya sanya kina jina ina knocking kikamun banza?" gani ko motsi batayiba ya sanya ya matsa kusa da ita ya doddoki kafad'arta firgigit ta dawo daga duniyar tunanin dataje,da sauri ta miqe tsaye tace cikin tsoro "Na'am yaa shaam" harara da kallo me nuna tsananin tsana ya rabita dashi "kina nufin duk wannan knocking dana jima inayi bakijiba,tsabar zamanki sokuwa,kinzo kin tasa tv a gaba kina kallo,Dabadan gidanmu daya ba kuma nasan acikin daula kika taso danace ke dinnan anyi daqiqiyar yar qauye,zuwa nayi inji meyene ya hanaki zuwa ki taya haleemah ku hada breakfast kokuma harkin fara tunanin cewar kishiyar kice kin fara kishi da ita?? Sadda kanta tayi kasa tanaso tayi hawaye koda wannan gululun bakin cikin datakejin ya tasomata ze kwanta amma ina sam ta kasa takuma rasa dalili,abin se yawo yakeyi yana mata sintiri tsakanin maqoshinta zuwa cikin yayan hanjinta dakyar ta iya furta kalmar "kayi hakuri na makarane" tsaki yaja "ki tabbatar kinje yanzu kun daura girkin rana da ita sabida ba baiwar gidan uban kowa bace dazata girka abinci agidan,kuma ni bazanci abuncin yar aiki ba" Batace komai ba ta juya da siririyar halittarta zuwa ciki domin dauko hijabi,wani tsakin taji yaja a sarari ya furta " Sabida ansan ba wanda ze daukeki da wannan bushashen kunkurun tamkar na marainiyar kaza shine za'a cinnamun,mace se kace allo samb'al haka" sarai ta jiyoshi wani azababben baqin cikine ya dunqule ya sake taso mata mara misaltuwa fatanta daya tasamu tayi hawaye koda ta samu salama amma sam abun yaci tura ta kasa,da wannan ta dauko hijab dinta tafito,bayanshi tabi har sashen haleema ba wani nisa a tsakaninsu kofa kawaice part din kofofinsu suna kallon juna,suna shiga parlor din haleemah ta taso ta rungume shaam,shi kuwa ya manna mata sumba a goshi bayan ya sauke hannayenshi a saman faffad'an kuib'inta ya sauke yana me shafar manya manyan mazaunanta,wani shagwab'ewa tayi tace " Boo mie banfa karyaba" hannunshi ya kuma saqalawa a kugunta " Bazaki iya girka komai bane da kanki sweetest?" gyad'a masa kanta tayi cikeda shagwab'ar da sam bata karb'eta ba tace " Ni kasanfa jiya baka wani barni bacci ba na gaji kuma chips nake sanci with liver sauce" kallonsa ya maida kan Hafsat "kulele kije ki hada mata breakfast dinnan datakeso sannan bayan kin kammala ki daura lunch kinsan kuma banaso ya wuce 1:00" murmushin yaqe tayi batare datayi magana ba ta wuce su zuwa inda take saaran nanne kitchen din sabida kula da tayi komai na tsarin gidan irine dayane da nata kayane dai ta kula kowannensu da irin nashi,taje ta had'o breakfast din ta kawo dinig ta ajiye sannan ta juya zuwa daura na rana,zuciyarta tana mata suya sosai a daddafe ta kammala girka musu chinese rice da veg pepper chicken and mock champagne drink,a dining ta jere su bayan ta kammala had'a colslow sannan batare data d'ibi komai aciki ba,ta juya zuwa part d'inta,wanka tayi ta sauya kaya sannan tayi kiran umman yaa shaam ta asali akan a aiko mata abinci,da wannan umman ta kira shaam akan yazo ya karb'a wa hafsat abinci,da mamaki yafito parkor din gidanshi ganin kayan abinci a jere ya sanyashi mamaki amma batare da wani dogon nazariba yafita yaje ya karbo ya dawo, da iya karfinsa ya banko kofar gidan ya shigo a parlor ya sameta kwance ta daura wayarta asamn flat tommy d'inta tana tunanin data saba wannan shigowar da yayi a haka be sanya tako motsa ba sabida ta shiryawa kanta tarb'ar duk wani bakin ciki dazezo mata bama yanzu ba har nan gaba,a kanta ya tsaya "Wane munafuncinne ya sanya dakika girka abunci baki ebi naki ba sekika kira sabida ke ba Allah aranki burinki kawai kiga kin had'ani da mahaifiyata,shegiyar yarinya me munafuncin tsiya wlhy kika kuma mun haka sena illata miki fatar jikinki kuma inji zancen nan gidan agidan daddy ko gidan Abba ko hmmm rahbb wlhy nida kene,kuma zanyi baqi da dare kiyi girki a nan part d'in" Harya gama fadan shi ko motsi batayiba a haka ya juya be jima da fitaba sega su huda lokacin kuwa har 3 ta gota ba karamun sanyi tajiba atake huda ta tayata suka hada girki me yawan gaske basu suka zauna ba se 6, wanka hafsat ta sakeyi sukayi sallah sannan suka kule d'akin hafsat kallon ta huda tayi tace "Qawata nasani kina cikin damuwa me tsananin yawa kuma na fahimci hakan tun zuwana,nasani bakyaso ki tattauna matsalolinki da kowa amma ki sani hafsat kin burgeni matuka lallai kinyi hankalin da ban zata kuma inaso naja hankalinki akan abu d'aya,karki kuskura ki sanar wa iyayenki irin zaman da kike acikin gidannan,ke bama suba kowa harni,duk sanda kikeda wani matsala kimun matsal ki gayamun sabida yawan barin abu a zuci yana sanya ciwon zuciya,karki yadda da kowa se kanki,kuma bawai rashin fad'a ba hadda nuna wa dan Allah yar uwata kina daure wa kuma kina jure duk wani wulaknci da shammaz ze miki,kiyi zaman aure me kyau kindaiga ke qaramar yarinyace idan kika biyewa waccen tsohuwar matar wlhy wahala zakiyi sosai sabida nisam ban yarda da ita sabida haka ki kiyaye kinji" se a sannan taji wani kuka ya qwace mata rungume huda tayi ta dinga kuka seda ya isheta sannan ta sake huda ta mata suka yi sallama akan washe gari zasu dawo....... Mom Nu'aiym [1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 09 Da darema haka ta zauna zaman jiran yaa shaam amma shiru kakeji tamkar an aiki bawa garinsu,haka ta kwana ranar kam tana rusar uban kuka,tana idarda sallan asuba wayanta ya soma ringing tana dubawa tagan sunanshi gabanta ya fadi, jiki ba kwari ta d'aga kiran,yace da ita "Karfe 9 zanyi baqi saga abuja zasu sauka a lodge su uku ne ki hada break fast before 8 sabida nafiso su taradda shi suna zuwa" to kawai tace ta ajiye wayan tana sharar kwallah,ga ciwon kai sabida kuka da rashin bacci ga azabar aiki sekace jaka,a daddafe ta hada musu finger sandwitches da sultan chips fried chicken and jello,se 8:15 ta kammala,tana shirin fitowa kitchen d'in ya shigo da sauri taja baya ta durqusa har qasa "yaa shaam barka da kwana" harara ya wurga mata "ke jakar gidan uban waye wai? Bance dake before 8 ki kammala ba yanzu karfe nawa?" sadda kanta tayi kasa wani qututun bakin ciki ya tasoma mata ta kuma rasa dalilin daya sanya sam bata iya kuka idan yaci zarafinta sedai zuciyarta ta dinga wata suya me azababben rad'ad'i,da k'yar ta lalubo kalmar "kayi hakuri" tsaki yaja "Dama mana kullum kece ayi hakuri,idan kin isa gobema na sakaki aiki na baki lokaci ki wuce time d'in wlhy zaki d'and'ana kud'arki a hannu" batace kanzil ba taje ta dauko warmers d'in data zuba abinci aciki ta sakosu acikin wasu cute baskets guda biyu ta ajiye a gabanshi ta juya zuwa d'akinta cikeda qunci,tana zuwa tayi kiran umma akan zancen yarinyar dasukace zasu kawo mata me tayata aiki,sabida a yanda ta gaji yanzu bataji zata iya girka lunch and dinner kuma taga har haleemah tafara fita aiki tun jiya,bayani umman ta mata akan an kawo yar aikin khairiyya zatazo ta kawota anjima kadan...... *Bayan wata biyu* Rayuwa a haka taci gaba wa hafsat cikeda qunci da wahala,gashi duk k'wak'war mutum be isa yasan abunda ke damunta sabida dama batada jiki balanta na kace tayi rama,sannan kuma bazaka gane a fuskarta,tana zuwa school yanzu 200l suke kullum huda cikin bata shawarwari na kwarai take akan tayi hakuri kasancewar itace kadai aduniya tasan meyake damun hafsat,kuma har wannan lokacin shammaz baya kwana gidan hafsat indai abubuwan more rayuwane da kudade sedai ta baiwa wani amma sam ba magana me dadi a tsakaninsu wasu lokutan sam ko gayar dashi tayi baya amsawa,yau agajiye ta dawo daga skul tana fitowa wanka wayanta ya soma ringing,d'agawa tayi ganin sunanshi yace " Yanzunnan ki kawomun abinci yunwa nakeji" cikin takaici tamkar zatayi kuka tace "yaya yau ba abunda naci wlhy yanzunnan na dawo daga skul ko sallah banyiba dan Allah kace Aunty haleemah ta baka mana" wani mirmurshin mugunta yayi da har tana jiyo sautinsa yace " Ita d'inma yunwa takeji kuma yauma agajiye ta dawo ke muke jira ki bamu abinci kuma 1 hour kawai na baki" yana kaiwa nan ya ajiye wayar,cikeda takaici taje kitchen ta dafa musu sphagetty bolognese da orange juice tafita kaimu su haushi tamkar ta had'iye zuciya ta mutu,da sallama tashiga parlor din amma abun mamaki se numfarfashi take jiyowa juyawan dazatayi tagansu akwance suna kissing junansu shaam se shashafa leemah yakeyi yana mamatsa breast dinta kai abubuwan data gani sam bazasu fad'uba,wani takaicine ya taso ya tarnaqeta a wannan lokacin ji hafsat keyi tamkar ga kashe kanta har lahira,da kyar tayi karfin halin zuwa dininga tabajiye kayan ta juya,abunda yafi bqanta ranta shine yanda sukayi tammar basu ganta ba kuma sarai ta sani dukkaninsu ba wanda be sanda zuwanta ba wani abin ma har da gayya suke yinshi,wanda sosai ta kula Aunty haleema wannan surutun datakeyi danta gantane,a wannan ranar kuka hafsat ta kwanayi ko abunci bata iyaci,Allah sarki qaramar yarinya akace ana wata ga wata domin kuwa tun daga sanda hafsat ta gansu a haka se wani azababben sha'awa yake taso mata gashi wannan lokacin ne tashen balagarta seta rasa yanda zatayi a haka take danne zuciyarta tana adu'a Allah ya kawo mata d'auki... Ranar wata juma'a bayan sallan isha tashiga part din haleemah sabida tanasan ganin yaa shaam akan zancen bikin huda dayake wani satin za'ayi tana zuwa kofar d'kin tajuyosu suna iskancin nasu dasuke ihu sekace wasu maguna,juyowa tayi cikeda takaici anan taci karo da abinda tangamemen tv n dake parlor din ke haskawa wato BF,gabanta ne ya fad'i ganin me akeyi take taja baya se kuma wata zuciyar tace kindaiji ana labari amma yaune ganinki na farko,jeki ki kalla...da wannan ta tsaya ta kurawa tvn idon tana kalon masha'an da ake tafkawa rashin kunya iri iri,dakyar ta dakatar ta juya zuwa part d'inta jikinta har rawa yakeyi wasu abubuwa takeji suna mata yawo kasa haqura tayi da tambayoyin da zuciyar ta ta gaya mata ta zari key na motarta zuwa gidansu huda......kallon huda tayi bayan sun zauna a d'akinta tace bayan ta tattare nutsuwarta zuwaga hudan " friend mene ne sha'awa? Yaya kakeji idan kanajin sha'awa?" kallon mamaki hudan ta mata tace "Ban fahimcekiba?" sosa kanta tayi ta labarto mata tun farkon ganinta dasu shaam dakuma abu da ta gani ayau,ta qara da cewar "Huda wasu lokutan sena kasa bacci kinga har kuka nakeyi sena ringajin ina matukar sanjin abinda Aunty leemah keji tana sambatu idan yaa shaam yana mata wannan abun,kuma kinga yau danaga turawannan suna wannan abun sena ringa jin dadi sosai nima inaso kuma naji na rage yawan sha'awa shine nakesan siya nakuma ana yawan cewa haramun ne kallon wayannan abubuwan kuma yana saurin kashe ido?" cikeda tsoro huda tace "kinga hafsat wlhy ki kama kanki,inake ina kallon wannan abun?? Masu siyarwa ma karuwai kad'ai suka san inda suke masu browsing a waya kuma wlhy duniya tana kallonsu sosai da sosai,sa'annan na kula kinada karfin sha'awa sabida haka wlhy kine ki samu mijinki kice dashi kina buqatarsa inba haka ba wahala tana ganinji,kuma wlhy idan nakuma jin wai zaki siya wayannan mugayen films senaje na fadawa momy,ki barsu yaa shaam matarshi batada maraba da karuwa wlhy ni sunaso su b'atamun ke,wainikam ma tukunna tsaya sanar dani kina yawan adu'a da tsayuwar dare?? Kuma kina azkhar?" dan sosa kanta tayi tace "Gaskia bana,wani yi ina dai adu'a" "Toki riqayi akan mijinki da duk wata damuwarki kinji huda,adua yana da kyau da kyautata ibadu yawan yin azumin nafila da sallar nafila dakuma azkhar,kina yiwa qananan yara sadaka tunda baki rasa ba kinji,ki cire ranki da wannan mugun kallon indai ba wuta tsundum kikeso kije ba,kuma masu san kalllon wannan ma idan suka saba basa iya denawa,sekiga idan ba namiji a tare dasu suna yiwa kansu abubuwa da hannu kuma wlhy masifa ne Allah ma yayi alkawari. Azabtar da masu irin wannan mugun aikin,seki kiyaye kinji qawata" gyada kanta tayi alamar gamsuwa sannan tamata sallama tabar gidan,huda se tausayinta takeji matuka.......hafsat se tunanin rayuwarta takeyi da abubuwan ban mamaki datake ta faman gani arayuwa,a haka ta isa gidan cikeda damuwa,a harabar ajiye motocin gidan taci karo da yaa shaam tamkar bashiba,bashida niyyan koda kallonta ne balantana yamata magana,da sauri ta qarasa gunshi "yaa shaam ina wuni?" "Lapiya" ya amsa a taqaice yana shirin shigewa motarsa takuma kallonshi tace " yaa shaam magana nakeso muyi" batare daya kalletaba yace "Enhmm" "Dama nikam wai yaya banida wani haqqi a gidannan ne koda na kwana a part dinane yanzu kusan watannina biyar agidannan amma koso daya baka taba kwana bangarena ba atare dani" wani kallo ya wurgo mata ya murtuke fuska sannan yace "Idan tunanin kike kinada wani haqqi a kaina to kuwa kinyi babban kuskure domin nidai,ni shaam wlhy nafi kardinki sam *Bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane* bakida wani abu ajikinki ko a fuska daze gayyaceni kwana sashen ki,sa annan kuma bakida wani diri na ya mace dage gayyaceni zuwa shimfidarki,wlhy Hafsat bakida banbanci da namiji awurina,iyayenki sun cuceki domin nidai bazan taba iya furta kalmar saki agarekiba kamar yanda bazan taba iya makwanci dakeba sabida haka idan ma mafarki toki farka samni kam bana san mace sekace tsinken stintsiya se dare kamar wani daren yunwa,kuma me harma kinyi girman dazaki tareni da wani haqqinki wlhy kika kuma mun irin wannan maganar sena tattaki mara kunya fitsararriya haqqin uban wahe dake a hannuna sekace da yunwa take kwana a gidan" batare datace komai ba tayi ciki aranta tace "Nice ma bankai mace ba,nice ma ban isa yasoni ba,nice banida banbanci da tsinken tsintsiya" ko wannan daren hafsat kasa bacci tayi kuma se zazzab'i me zafi ya rufeta Allah ya taimaketa ta kammala exams nata gaba d'aya........washe gari yayi kiranta wai tasan haleemah nada juna biyu bata iyacin abinda ta girka ta kawo mata abunci,tace dashi "yaa shaam nima a kwance nake ko bacci banyiba wlhy banida lapiya" tsaki yaja yace wai mintuna talatin yabata ta kawo kalacin.... Mom Nu'aiym [1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*     *Wannan shafin nakine maryam Abdullahi gumel,nagode da qaunarki agareni* 10 Tunda hafsat tashiga gida take rusar uban kuka daganan tayi alqawarin ficewa sha'anin yaa shaam koda kuwa soyayyar sa zata hallakar da ita har abada.....da wannan ta mayarda hankalinta akan karatunta matsalar fa d'aya tsananin sha'awar dake damunta kullum ba dare ba rana,ta rasa yanda zatayi da kanta kuma tayi alqawarin koda huda bazata sake sanarwa da duk wata matsala tata ba zata qalubalanci rayuwarta ita daya, amma fa sam bata acikin walwala.....yau dai shirin zuwa gidan momy tayi sabida sunday ne ba school,harta shiga mota yaa shaam ya tsaidata "Kije ki dafa mana abinci sabida Babyn shaam bata da lapiya kin kuma sani sarai tanada juna biyu bata iya cin abinda ta girka" tamkar zata yi kuka haka ta ji amma seta daure batace komai ba tafito zuwa cikin gidan,a bangarenta ta girka komai sannan ta shirya ta dauka takai bangaren haleemah,tana zuwa ta ajiye a dining ta sanar musu,seda haleemah ta kalleta sannan tace,cikeda sigar rarrashi "Dan Allah hafsat kiyi hakuri wlhy bazan iya cin komai ba se indomie,ki daure ki taimaka ki girkamun" kallon mamaki tabita dashi sannan batare datace komai ba ta juya zuwa ktchn din a gurguje gani karfe uku ta gota momy se waya take mata akan bata zoba ta dafa ta kawo mata,har takai kofar barin parlor din tajiyo karar daya bata mamaki "Nashiga ukuna ni haleemah,wlhy boo me baran iya ciba yaji ne aciki sosai ga kuma magi yamun yawa" wani mugun kallo shaam ya wurgawa hafsat "muguwar yarinya dawo nan ai kinsan muguntar da kika kullah me baqar zuciya,dan ubanki da dakikasan bazaki iyaba meya hanaki kanki tsaye kice bazakiyiba,wato wannan cikin na jikinta shi kikeso ki kashe ko? Muguwar banza muguwar wofi wlhy yau bama inda zaki,kin dinga girka mata indomie kenan se sanda kika girka mata kalan wanda tace ya mata" kan tayi magana kuka ya kwace mata se kuma wayanta ya soma ringing,dagawa tayi tana me hadiye kukan lokaci daya ta qaqalo murmushin daya baiwa shaam mamaki takuma saisaita muryanta "Momy dan Allah kiyi hakuri,wlhy Aunty Haleema ne batada lapiya inaga kamar bazan samu damar shigowa ba yau,kinga ita kadaice bazan barta haka ba" murmushi momyn tayi tace "Eyyah Allah sarki Allah ya bata lapiya ki gaida ta kinji,yanzu se yaushe??" "gobe sha biyu nake qare lectures inshaa Allah daga school se gidanki momy karki damu" "To Allah ya kaimu hafsat Allah ya miki albarka kinji" Ameen kawai tace ta ajiye wayan sannan ta juya zuwa kitchn din,dafa wani tayi bata saka yaji ba ta kawo,ai loman farko ta zubar aqasa ta kalli yaa shaam fuskar nan harta soma kawo ruwa "Yaa shaam kaci kaji wlhy ba taste yanzu fa ko d'an green pepper ta saka man amma haka tayishi,Allah ni bazan ciba kuma" Tsaki hafsat taja bada shirinta,dama fa hafsat gwanar rashin kunya ce kurin tsoron yaa shaam ne ke durqusar da ita,yau kam ta cika fam "Gaskiya Aunty haleema bansan ya kikeso na miki ba na dafa wancan kince bazakiciba na dafa wannan indomie kince yaji,na kuma dafa wani kince ba yaji ni kije ki dafa da kanki,ko aikin bauta nazo na muku wlhy ko zaku kasheni bazan dafa muku wani ba" kallon mamaki shaam ya mata domin shi har tasoma bashi tausayi ya matso kusa da ita yace "Jeki kitchen ki dafa mata me abunda takeso" tsayuwa tayi a wurin taqi koda motsi,saukar wani kyakyawan mari taji seda ta ga wasu taurari na musamman,yace "ina wasa dakene? Nace kije ki dafa mata wani" kamar yanda batayi magana ba haka bata koda motsa ba da wannan ya shaam ya soma dukanta tamkar wani mahaukaci baji ba gani seda haleemah taga tayi lilis sannan ta saka kukan muna furci tazo tana qwatar hafsat "shaam dan Allah kayi hak'uri,idan ka illatar da qanwarka ni za'aga laifina kuma kaga ai tama gaji ni dama ba ina nufin ta dafa wani bane,nama ji na qoshi tea ma ya isheni,miqewa tayi tsaye ita kuwa tayi hanyar waje har wannan lokacin bakinta be mutuba tana kaiwa kofa tace "kuma wlhy ko zaku kasheni na dena muku girki kenan har abada" bebi ta kanta ba ya dawo wurin haleemh da rarrashi...... Bayan magrib tana d'akinta tana rusar uban kuka abinta shaam ya shigo,zama yayi kusa da ita da yace "Hafsat ni kikewa baqar magana??" bata kulashiba yace "Kinaso na ci gaba da lallasaki kenan?" budar bakinta se cewa tayi "ka lallasanin ai akwai Allah,kuma wlhy duk wanda yaci zalina Allah ya isa" mamakin kalamanta yakeyi "waye yake koyar dake rashin kunya hafsat?" nurguda bakinta tayi sannan tace "Wanda suke cin zalina kullum kuma Allah ya isa" miqewa yayi yace "hafsat kin janyowa kanki zaman bakar uquba a gidannan sabida kinga ina miki wasa shine kikemun wulaknci san ranki ko? Wato ke kin isa lallai kuwa zakisha baqar wuya a hannuna" bata kulashiba taci gaba da kukanta yayi ficewarshi yana mejin tsananin tsanar hafsat,tundaga wannan ranar kuwa shaam komai qanqantar laifi idan hafsat ta masa se duka har yakasance daga dazan ya sanyata abu jikinta ze soma rawa,kuma da sauri takeyi,sedai kwanakinnan batada lapiya ko kadan, da wannan ta sameshi tace dashi "Yaa shaam kwanakinnan da zazzab'i sosai nake kwana ko zakaje dani clinic dinka a dubani" kallon ta yayi ya rufe jaridar dake hannunshi " A matsayinki nawa zakijemun clinic? Kinga nawa clinic ma na masu matsalar zuciyane,sabida haka kije wani asibitin kawai" batace masa komai ba taje gun huda daganan suka wuce wurin mijin ta dayake shima likitane,binciken farko ya fito da tambarin heart problem ajiki,sosai sadeeq ya shiga cikin shock,huda ya fara kira a gefe yace "Baby wai anya qawarki ba kashe kanta takeso tayi akarin banza ba @kan soyayya kinsan kuwa ciwon zuciyane da ita,fisa bilillah @her age gaskiya bance ba'a samun irin wayannan cases dinba sabida yanzu irin wayannan cutukan sun yi yawa a wurin yarama harda hawan jini,amma ni tausayi take bani gaskiya me take sakawa a zuci har haka,jininta mafa hawa yakeyi" dafe kai huda tayi tace dashi "Hubby kasanme har fa dukanta yakeyi sannan ko kwanciyar aure bayayi da ita,ga school ga problem dinshi girki mafa ita kewa matarshi ko sau daya betaba kwana a bangarentaba,ga hafsat da zurfin ciki tacika barwa kanta abubuwa ni wlhy har naji kaina yana ciwo ma,yanzu meye solution?" dafe kanshi yayi yace "Amma gaskiya shaam ya bani kunya wane irin sakarai ne qanwarka guda daya matar da iyayenta suka nuna maka so tamkar sune suka haifeka shine tsabar mugunta yarinya ko 17 bata hada ba zaka hadata da ciwon zuciya mugun banza" wurin hafsa suka koma dakyar sadiq ya tattaro nutsuwarsa ya shaidawa hafsat komai cikeda rarrashi da nuna mata hanyoyin dazatabi tunda abin beyi nisaba,sosai hafsat tayi kuka sannan ta nuna musu su rufa mata asiri karsu sanar wa kowa,hakan dai aka bata magunguna ta koma gida da damuwa me dinbin yawa wacce ta ninka tada,tundaga wannan lokacin hafsat ta dawo sukuku sam bata walwala gashi batada lapiya a haka har Haleemah ta haifi yaro namiji,wanda bataje wankan gidan ba kuma tanayin 40 days aka maidashi kwana wurin hafsat,komai wahalar khaleefa hafsat keyi baji ba gani, harma ya saba sedai yasha madara wasu lokutan idan ya tashi a bacci da dare ya saka kuka setayi ta rarshinsa idan yaqi itabdinma seta saka mar kuka suyitayi se me aikinta tazo ta karb'eshi.......a haka har khaleefa yayi wata hudu a duniya,san suniya shaam ya dauka ya daura akan yaronnan bama a san ranshi yake barinshi kwana acan ba,danma bayason bacin ran haleema na...... Ranar wata juma'a Cikin dare khaleefa ya tashi da wani irin ciwon da hafsat ta kasa gane na menene,kuka yake tayi tamkar me yana zabure zabure,hankalin hafsat ya tashi ta dauki wayarta tayita kiran shaam baya dagawa,takira haleemah akayi rejectin call din sannan kuma aka kashe ma wayar gaba daya,shaam yaga ta kuma kiranshi yace "Haleemah lafiya kuwa? Kodai in daga inji menene dalilin kiran naga bata taba yin hakan ba?" wani narkewa haleemah tayi tace "Boo me dan Allah manta da ita,nasan kuka khaleefa ke mata shiya sanya kaga ina ce maka akaishi acan kar ya hanamu walawa" biyeta yayi sukayita har kofar gidan tazo ta bubbuga suka mata banza,koda ta koma yaron baya motsi lokacin ma karfe biyar na asuba,da kukanta takira shi again be daga ba,ta aika masa message "Yaa shaam nayita kiranka inaga fa Khaleefa ya rasu" yana fitowa daga gun alwala yaji aran message yaje ya duba a rude ya gayawa haleema da salla be dameta ba tana baccinta aibhar ture juna sukeyi sabida tsabar gidi mewa,banka kofar sukayi suka sameta rungume da gawar tana uban kuka, "yaa shaam kunga illan rashin daga waya ko? Shine inata kiranku yaron nan se zabura yakeyi amma kuka qi dagawa wlhy kungani ya mutu" ta sake fashewa da kuka,ai shaam na dubawa yaga da gaske ya mutu ya soma jibgar hafsat "yanzu tsabar bakida mutunci shine kika kashemun yaro,dama wannan qiyayyar taki akanshi ta wuce tunani wlhy kema sena kasheki,jibgarta ya hauyi baji ba gani haleema se kuka takeyi ta dauki gawar se jijigawa takeyi,dakyar yadena dukanta yace dan ubanki kije na sakeki saki d'aya ki barmun gidana........yana kaiwa nan yabar dakin yana me karbar gawar yana kuka,wayanta ta janyo da kyar ta kira Abba haris,yana dagwa dak'yar tace "Abba kazo ka daukeni yaa shammaz ya sakeni kuma so yakeyi ya kasheni da duka,banama iya tashi"............. To jama'a kunjifa yanda ta kasance,anya kuwa shammaz yanada hankali? Anya kuwa wannan halin nashi asirine kawai kodai har da qiyayya da wulaknci? Yaya rayuwa zata juya masa? Mom Nu'aiym *Don't forget to vote and comment,ur votes and comments are more important to me than anything plsss do vote for me*      [1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* Wattpad@ 68billygaladanchi 11 Sosai ran Abba haris yake a b'ace sanda yazo gidan,kai tsaye part d'in hafsat ya wuce ya tarar sabuwar yar aikinta dasuka saba sarai ta tasata agaba tanata kuka ko motsi batayi,da hancinta da bakinta duk jini,sosai ya tsorata bema wani damu shaam sabida bashida abun ce masa ya sakata a mota itada sarai suka nufi asibiti.....waya yayiwa matarshi da dama ya barota hankali a tashe tana salallami akan driver yazo dasu Uduth suna can,Dr. Sayyeed hamid Ali shine dr d'in da ya duba Hafsat sunkai kusan awanni hud'u akanta kafin ta farfad'o,zuwa yayi ya kira Abba haris a office d'inshi ya kalleshi sosai sannan yace "Sir wannan yarinyar shekarunta nawa ne?" dubanshi abban yayi yace cikin damuwa "shekarunta sha shida inaga nanda watanni biyar zata cike sha bakwai" jinjina kanshi yayi sannan yace "Amma yallab'ai kuna zaune da qanqanuwar yarinyabhar ciwon zuciyata da hawan jini su mata yawa haka,ni fa a gaskiya nasan is very rare kagan yara masu qananun shekaru irin nata suna fama da wannan cutar,sa'annan wannan uban dukan da kuka ce mijinta ya mata kyautuwa ma yayi ku kaishi gun hukuma sabida kuwa ya tab'a wa yarinyar kai, yanzu haka idan ta farfad'o gaba daya bamusan a wanne halin zata tashiba,sabida jini ya taru mata a k'walwarta,rayuwar yarinyar abar tausayi" dafe kai abba haris yayi tare da zare ido waje cikeda kad'uwa yace "wane irin ciwon zuciya da hawan jini kuma likita? Anya hafsat tamu kake magana kuwa?" nisawa Dr. Sayyeed yayi cikeda tausayawa yace 'Alhj wlhy itan kuwa,kana nufi kenan bakusan tana fama da wayannan cututtukan ba? Bincike ya nunar mana cewa har magungunan take sha" A zuciye ya miqe yace "wannan azzalumin mijin nata ya sani sabida kuwa shikeda asibitin zuciya sukutum wacce itace k'wallin k'wal agarinnan,kuma shine babban likitan zuciya" kallonshi sayyeed yayi cikeda mamaki yace "Alhj Karkace dani Dr. Shammaz kake nufi sabida a iya sanina shikad'aine ya mallaki asibitin zuciya me zaman kanta,bazan amince ba idan har kace dani wai shine da kanshi yayiwa matarshi irin wannan dukan" kallonshi Abba yayi cikeda takaici sannan cikin d'acin zuciya ya furta "Amma zaka iya yadda cewar nine mahaifinsa na asali na haihuwa,yayinda mahaifin wannan yarinyar da yayiwa wannan dukan shine mariqinshi shine ya zamto gata agareshi harya kai wannan matsayin dayake kai a yanzu,amma shine tsabar yana butulu ya aikata wa yarshi wannan mummunan ta'adin" sosai wannan maganar ta girgiza Dr.sayyeed ya zare madubin idonshi ya dawo kujerar dake kusa data Abba ya zauna sannan yayi abba nuni da daya kujerar akan shima ya zauna ya ce "Amma nayi mamakin jin wannan maganar,sabida da badan kai bane mahaifinshi wlhy da bazan yarda ace wai Dr. Shaam ne yayi wannan aikin ba,sabida sanin dana masa mutumin Kirkine kuma kamili,Allah yamana tsari da sharri shaidan,yanzu dai bazamu sanar daku komaiba se yanda bincike ya nuna mana,sabida haka ku bamu nanda yamma seka dawo nan muji koma meye" Godiya Abba haris ya masa sannan ya fice kai tsaye gidan Daddy ya wuce ya tarar ana jajen mutuwar khaleefa,a fusace ya kalli jama'ar dake parlor kasancewar duk yan gidane se daddy da shaam,idonshi yayi jajir tamkar gaushin wuta "waye acikinku ya nemi sanin inda Hafsat take da baku ganta ba" mero ce tayi saurin cewa "Abba mun tambayeta amma yaa shaam ya sanar mana wai tana makaranta" wani kukan kura Abba haris yayi ya shaqi wuyan shaam ya miqar dashi tsaye ya surfafa masa lapiyayyen mari har guda uku a jere a jere,cikin mamaki d'aukacin mutanen dake parlor din suka miqe daddyy ne ya riqeshi "Harisu lapiyan ka kuwa meya faru?,yaro yana cikin zillar rashin yaronshi zakazo kana surfafa masa marika haka,meya maka" cikin huci yace "Sabida yaronshi ya mutu seya nemi kashe yar mutane,wai har shammaz dan bashida imani ba Allah a ranshi ze riqa baiwa hafsat renon yaro cikin dare yashige da tsohuwar matar daya ajiye suna holewa,kuma sabida Allah ya karbi ranshi rana daya ya ce wai hafsat ce ta kasheshi kuma ya mata dan banzan duka harta suma,bayan sakinta dayayi duk wannan be isaba se sanin ya dasa mata ciwon zuciya ba wanda ya sani harma da hawan jini,yanda ga wayannan kuma gashi likita ya tabbatar mun cewar wai hafsat kanta ya tabu sabida dukan daya mata aka,wlhy Yaya Abu bazan tab'a yafewa Shammaz ba,na yafewa duniya shi kuma bazance masa komai ba yaje duniya ce,daga rana me kama da ta yau kar naji kona qara ganin yace nine nan na haifeshi ko mutuwa nayi wlhy banda shammaz a gadona kuma ko'a lahira se an mana hisabi dashi,yaci mutuncina yaci mutuncin dan uwana,yaci mutuncin matarshi yaci mutuncin aure,kuma be ragawa Allah ba,na kuma tabbatar Alkah bazenraga masa ba" Da sauri Daddy ya rufewa Haris baki tare da zaunar dashi dukkuwa danyake yaji maganganun tamkar saukar aradu,wai kan kulelen sa ya tab'u kuma a dalilin dukan da shaam ya mata,sa'annan kuma wai tanada ciwon zuciya adalilin mene wannan? Dakyar ya saisaita kansa ya kalli shaam "shammaz kaji abubuwan da harisu ya fada hakane??" sadda kanshi yayi qasa sannan yace "Daddy niba abunda nake mata,kuma wlhy bansan da zancen ciwon zuciyaba,da ina mata wani abin aidanta fada tuni,zancen khaleefa kuma itace da kanta taroqi Haleemah akan yana kwana gunta kuma jiyan ma wlhy banso ya kwana candin ba,dukan dana mata kuma ba'a san raina bane harma sakin dana mata duk acikin b'acin raine da gigicewar rasuwa khaleefan" Shiru daddy ya kasa magana kowama yayi shiru se momy dake kuka lokaci lokaci tana jan hanci kasancewar kukan nata bame sauti bane,yafi mintuna biyar kafin yace " Harisu dan Allah markayiwa d'anka baki,ka janye wayannan kalaman daka masa kuma ka nutsu wannan maganarbta gida ce ba abun tashin hankali bane" miqewa Abba yayi "wato yaya ba kadan ba ka ke sakarwa shammaz dama yana durun uwarsa san ransa,ni za'a gayawa wai harkar gida wlhy tallahi sena maka wannan yaron kotu senaji dalilin wannan ha'incin kuma koban masa bakiba haqqin yata seya kamashi rasa kunya kawai b'eran tanka,dana sani shine babban amininka koba yanzu sekun kulla babbar abota dashi wlhy" yana kaiwa nan yayi waje,yayinda momy tayi kiran mero suka nufi asibitin uduth daddy ma da shaam din suka bi bayansu kasancewar haleemah tana gidansu..... Acikin d'akin kowa yayi zugum zugum an qurawa hafsat dake wance ido, A hankali ta bud'e manya manyan dara daran idonta,sunanan dai a lumshe tamkar mejin bacci a kowane lokaci,d'aya bayan d'aya take bin kowa da kallo,har shaam wanda taqurawa ido bata ko k'iftawa,a hankali kuma ta rufe idon tamkar me bacci can kuma bayan yan mintuna tamkar wacce aka tsira kuma seta fara fizge fizge kan kace me wannan ta soma zabga sambatu "Dan Allah karka dakeni wlhy ba abunda nawa khaleefa,yaa shaam ka dena dukana zaka kasheni,wayyo Allah daddy kazo ze kasheni,Abba yaa shaam ze kasheni" dak'yar suka rirriqeta shaam yaje yayi kiran nurse dake kusa akan ya akira doctor sannan ya koma kanta, koda dortor yazo seta fara kuka sekuma ta saka dariya kowa a d'akin kuka yakeyi yayinda lokaci d'aya kunya,danasani,nadama da bak'in ciki suka qara taruwa suka lullub'e shaam yama rasa me yake ciki a yanzu,Dr.sayyeed ne yazo dubatan ya kalli shaam ya miqa masa hannu suka gaisa sannan yane kai tsaye wurin hafsat,cewa yayi kowa ya saketa sannan ya sauke mata lallausan murmushi bayan ya riqe hannunta na dama,qura masa ido tayi dukda acikin rashin lapiya take amma setake masa kallon rashin sani yace yana ci gaba da fad'ad'a murmushinsa "Hafsat sannu kinji meye ne yake damunki? Cikeda wowta tamkar wata yar shekaru biyar tace "Bayan yaa shaam kullum yake dukana na ganeshi so yakeyi ya kasheni,ni ku fita dashi a d'akinnan inba haka duka na zeyi kuma banasan ganinshi" K'ara riqe hannunta yayi yace "Ai indai ni Uncle sayyeed ina nan wancan shaam din baze dakeki ba idan ma yazo dukanki nine zan mar d'an banzan duka yanzu sanar dani ina ne yake miki ciwo?" amaimakon ta bashi amsa se kawai ta matso ta qamqameshi tana kuka da sambatu alamun ba hankali atattare da ita "Uncle sayyeed karka bari yazo kusa dani dan Allah,daddy idan bazakuce ya wuce ba ni bana sanku"k'wallah Abba ya share cikin hikima yayi waje a haka a haka kowa ya watse ya kama gabanshi cikin k'unan rai,Dr.sayyeed be ajiyetaba seda tayi bacci shida kanshi yarinyar ta bashi tausayi over,be tab'a ganin case maka mancin wannan ba awurin yara dai...... Shaam na fitowa yakira Haleemah suka gaisa se kukan munafurci takeyi dak'yar ya rarrasheta ya sanar mata halin da ake ciki,cikeda kirsa tace "Amma ai yaa shaam na sanar maka karka daketa ba laifin ta bane ba inaga kaddara ne kawai" sallama dai ya mata ta ajiye wayar ashe sam shi be ajiyeba yana jiran yaji tace I love you boo me,yanda suka saba se kawai yaji an tafa hannu ana sowa "Wlhy umma gabad'aya jin wannan labarin senaji gwarama da khaleefa din ya mace,dama kinsan ance seka haifi wanda zeyi silar arziqinka to zuwan khaleefa kenan a duniya,nifa da farko dakikace boka yace rayuwar khaleefa fansa har naji bakya sona,ashe kinfini kaifin hankali tunda ko yanzu nakeso zan iya qara haihuwa,amma fa wannan aikin da tsauri yake umma ji nayi kince bokan yace sena kwana biyar a gidanshi yana saduwa dani kuma kince wai idan har mijina yasan zanje konan dacan aikin bazeyiba sannan kuma idan har yayi koda tunanin muna masa asiri bare ma ya gane to aikin ya karye,ni kuwa ai bazanso hakan ba yanzu ya kenan??" "Kinga hali dubu yar mama,barni da shegen yaronnan maganinsa zamuyi ai,yanzu ki hau bori zaki tsaya anan,kinga gobe seki je,duk ya kira akan zezo ki hanashi harse mungama aikinmu,kuma kinji boka yace daga zaran kin sadu dashi na karshe karki bari awuce awa ashirin da hudu ba tare da kin sadu da mijinki ba,kina yin hakan gaba daya ze kwashe mana dukiyar sa ya bamu,daga nan idan munso mu kasheshi ko kuma mubar masa gidansa inyaso mu koma lalubo wani me kudin,karfa ki manta khaleefa kika bayar akan kinasan yin arziki gudan jininki sabida ki nutsu kar a samu kuskure kuma ki tabbatar yaji wannan ganyen a abinci sabida shine ze gusar mas d hankali yakwashe mana dukiya a arha" dariya tayi suka tafa wanda shaam yaji komai zufa se keto masa takeyi ya kasa sauke wayar a kunnenshi yana saurarensu sunata shirya makirci,shi gaba daya ma ya rikice musamman jinda yayi suna zancen sun dasa masa qiyayyar hafsat,lokaci daya ma yaji ya tsani kansa kuma soyayyar dayake mata ta yaya da kanwa kai tsaye ta dawo da gudun fanfalaqi,amma fa har yau bawai yaji yana santa na soyayyaba......... Dr. Sayyeed ne ya kalli shaam bayan sun zauna,yace raunin na kanta ya taba mata kwalwa harma yana neman zautar da ita,sannan kuma ga zuciyarta ta tsananta abinda na fuskanta duk sanda kazo wurinta se hawan jininta ya tashi ga bugun zuciyarta dake qaruwa,sabida haka kadan daga mata qafa,zancen gaskiya kuma aikin manta bame wahala bane sedai zeci kudi,abu mafi muhimmanci danakeso ka sani matsayinka na likita shine,lallai wannan jijiyar tata me aika jini me makon saqonnin fahimta akanta aikinta ze janyo wani matsalar,kodai lalacewar ido,kokuma ta kunne sabida haka sekun saka haquri a lamuranku" kuka shaam ya saka tamkar wani qaramun yaro sabida shi gabadaya tunaninsa ya tsaya cak,tayaya ze kalli su abbba da daddy da wannan zancen? Ina courage din? Menene ma mafita agareshi?" A yanda ran Abba haris ya baci idan wani abun ya samu hafsa agarin aikinnan ai tsaf ze tsine masa wlhy kowa ya huta,dak'yar Dr.sayyed ya rarrasheshi yabar asibitin.... *Ur vote is important also ur comment fan's,inasanjin ra'ayoyinku,i hope ur enjoying this story* Mom Nu'aiym[1/21, 9:43 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 12 Dr.sayyed tunda yaje gida yake tunanin yanda zasu b'ullowa lamarin hafsat,haka kawai ya tsinci kansa da tsananin tausayin yarinyar,indai har acikin halin hauka bata manta muguntar da yake mata tokuwa lallai abun ba qaramun abu bane yana cutar da ita over,sam bayaso wani abu ya tab'u a jikinta kuma yasani sarai chancess na rashin samun hakan ba qaramun abu bane, yanaso ayi aikin as soon as possible amma fa sam bayaso ayi garaje a samu matsala....... Shaam kuwa koda yaje gida masa bacci yayi,bangaren zuciyar sa na masa zafi akan abinda yaji da kunnensa haleemah na fad'a itada uwarta,yayinda dayan bangaren na zuciyarsa ke masa rad'ad'i akan abunda abbansa yace dashi akan hafsat,wani dogon tsaki yaja yace a asarari "Gaba d'aya wannan hafsat d'in ta jamun masifa wlhy,dabadan ta maqale akan seta aureniba wlhy daban shiga wannan mugun yanayinba,ita kuma haleema yaya zatamun haka?? Ina sanki sosai haleema ko baki sani bane" a haka ya dinga sambatu shi kadai harna shirme....... Dr. Sayyeed da kanshi yayiwa su Abba bayanin rashin lapiyan hafsat da kuma da kuma abinda yake hange idan har aka mata wannan aiki,fatanshi d'aya ayi aikin lapiya kuma adu'arsu itace abun nema" Babu yanda suka iya dole su yarda da akan ayi aikin dukkuwa dayake Abba haris yaso a fita da ita waje daddy ne yace duk inda akayi aikin nasara a wurin Allah take,da wannan aka tsaida ranar aikin nan da sati d'aya...... Hafsat dai tana nan jiya iyau,ba abinda ya ragu har yau ba hankali akanta,yaa shaam tunda suka yaji wannan zancen nasu haleema seya kirata yace ta zauna gidansu se bayan sati biyu zuwa lokacin hankalinta ya kwanta dama kuma hakan takeso ya sanya ta kwantar da hankalinta tayi gidan bokan ta.... Sati ya zago Aka shirya shiga da hafsat tiyata yaa shaam har kuka yayi abubuwa sun taru sun masa yawa yanzu ya tabbatar wa kansa cewar abinda yaji gaskiyane,coz kwana kusan uku baya samun number wayan haleema kuma koyaje gidansu se a ce masa wai batanan sunfita da momy........Aiki dai anyishi cikeda nutsuwa da kuma na sara an samu damar kwashe duk wani jini daya taruwa hafsat a kai, yanzu jira kawai akeyi ta farfad'o, a ga yanda zata tashi...... Umma da momy sunyi jigum jigum suna adu'ar farfado war hafsat lapiya,se suka jiyo maganarta sama sama "Saro kunna mun fitilar d'akin nan kuma ki bani ruwa" kallon juna su umma sukayi sabida su sam basusan da wani zancen wai za'a iya samun matsala ba,da sauri suka miqe atare sukayi kanta,umma ta riqe hannunta tace "Sannu hafsat ai ranane aikin da'aka mikine akai,inaga lallai alluran nan ne be sakeki ba shiyasanya kike ganin duhu,sannu kinji" Shiru tayi tafara tunano abubuwan da suka faru da ita ita dai bata jin wani jiri gashi ta tabbatar wa kanta cewar idonta abude yake yama za'ayi ace wai allurace,amma seta kama bakinta tayi shiru kawai tana me mamakin har meyake damunta daza'ace wai ammata aiki akai,wasa wasa hafsat haka ta wuni ta kwana bata gani zuwa wannan lokacin har su momy sunsan halinda ake ciki kowa ya sakata agaba har Shaam tana bacci tana farkawa tace "momy zansha ruwa?" ruwan momy ta bata tasha sannan ta kwantar da ita gyaran kwanciya tayi tace "Momy dan Allah wai se yaushe gari ze waye ne,ni nagaji da ganin duhu idan ma garin be waye ba ku kunna mun fitila" D'aukacin mutanen d'akin suka saka kuka sabida tsabar tausayi daddy ne ya qarasa gunta yace "Hafsat nasani maganar dazan fad'a miki zaki jita wani iri kuma tabbas zata tayar miki da hankali,amma inaso kiyi hakuri ki yarda da khaddarar Allah ya d'aura miki,khaddarace ta sameki sakamakon dukan da yayanki yayi miki wannan ne ya sanya kanki ya samu matsala na tab'in hankali, to agarin yi miki aikine kuma wata khaddarar ta sake samuwa gashi dai munyi nasara hankalinki ya dawo jikinki amma an tab'a miki wata jijiya aka wacce tayi sana diyar lalacewar idonki yasanya kika dawo makauniya bakya gani" shiru tayi kamar yanda kowa yayi shiru tamkar bataji meyace ba secan hawaye ya fara gangara daga cikin idonta da suke abude bazaka taba cewa basuda lapiyaba ,batayi magana ba wannan ya sanya kowa ya sanya bakinshi ana bata baki seda taji kowa yayi shiru sannan ta sanya daya hannunta dabashida ruwa ta dafe qirjinta tace cikin d'aga murya "meya sanya a rayuwa nayi rashin sa'an zuwana aduniya? Meya sanya wannan baqar zuciyar tawa takesan mutumin da yafi qaunar mutuwarsa akan ya d'aura idonshi koda akan me ita,meya sanya a rayuwa sam na zab'i bak'in cikina akan farin cikina,meya sanya zuciyata keson wanda bashida buri illah yaga qarshenta,lallai ina cikin tashin hankali ba adadi,lallai yaa shaam da inada ikon raba wannan wahalalliyar zuciyar tawa da k'aunarka wlhy da nayi a yanzu,inama ace inada ikon raba raba rayuwata da ruhina ko zan huta da wannan baqar soyayyar da batada ci gaba ko kad'an seci baya,ina ma ace zan iya sanya hannu in lalubo inda rad'ad'in sanka yake inyi wurgi dashi,kaico na dana zab'i abu mafi muni arayuwata,kaicona dana zab'i mummunan k'haddara da hannuna khaicona dana siyo makancewar idona da hannuna kaicona ni hafsatu,kaicona ni lelen daddy da Abba" wani razanannen kuka ta saka me tsuma zuciya wanda baya misaltuwa duk kuwa cikin d'akin aka rasa me rrrashinta.......Dr.sayyeed ya tabbatar musu da cewar matsalar bame yawa bace idonta ze iya bud'ewa yanzu,ko gobe ko anjima ko wata ran ko wata shekara kokuma har abada,Allah shine yabarwa kansa sani,haka hafsat tayi wata daya a asibiti gashi sam ya kasa yiwa halima komai sabida san dayake mata kurin dai ya qaurace mata kuma sannan be nuna mata komai ba,har aka sallami hafsat ta koma gidan Abba haris. A gida Abba haris yayi kiran shammaz agabdan daddy da momy ya kalleshi cikeda nutsuwa yace "shammaz abinda yasanya nayi kiranka ba komai bane illah zancen komawan hafsat d'akinka wato gidan auren ta" Da sauri ya d'ago ya kalli abba yace dashi "Abba nifa na rigada na saki hafsat kuma bance zan maida ita ba wane komawa kuma zatayi,kurin dai Allah ya bata wani mijin ta aura" cikeda mamaki kowa ya kalleshi wannan karon har daddy abba yayi karfin halin cewa " Ai wlhy tunda ka nakasa ta seka zauna da ita,so kakeyi ka gama lahanta mata rayuwa" cikin bacin rai yace " Haba abba nifa ba qaramun yaro bane,sa annan kuma zakuce zakumun dole,yarinyar ban sota tanada lafiyaba se yanzu,dan Allah na rokeku karkuce zakumun dole kalar na farko kundai ga ba aci nasara ba,ba alkhairi a tare da wannan auren,inshaa Allah zataji sauqi ku aura mata wani,kuma ni ba qinta nakeyiba kurun dai ina gudun gurbacewar zumuncine sabida kunga bawai san aure nake mata ba,kuma ma koba itaba banasan auren zumunci" Sosai da sosai maganganun shi suka girgiza rayukan ilahirin mutanen wurin,lallai shaam baze rasa yin shaye shaye ba,Abba haris miqewa yayi yace " Bazan maka baki ba Shammaz amma kaje duniyace,inshaa Allah kana darai hafsat zataci gaba kaikuwa kana bayan yan baya" yana kaiwa nan yayi waje,daddy ma waje yayi batare da yayi magana ranshi a b'ace momy ce tace "kaima danane shaam amma dan Allah inaso ka dubi girman zumunci ka taimaki qanwarka,waye ze aureta tana makauniya yarinya ga qarancin shekaru ko haihuwa batayiba" budar nakinshi se cewa yayi "momy dan Allah kiyi hakuri wlhy bazan iyaba" aikam momy kuka ta saka cikeda takaici shikuwa ko a jikinshi yayi waje abunshi.... Mom Nu'aiym [1/22, 7:56 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                      13 Yaukam rayuwar daddy tayi matuqar b'aci da wulakncin shaam akan hafsat,lallai wannan yaron yazo da salo na raini iri iri,banda haka tayaya ma agaban su kaikoma ba agabansuba zece wai baze auri hafsat ba haryana iqirarin be sota tana da lapiyaba se yanzu data zama nakashashiya,ba abunda zece dashi koya nuna masa zega iya gudun ruwanshi tare da jiran matakin da Haris ze dauka.......    Hafsat zaune tanaso taci abuncin dake gabanta amma bata saka cokalin wurin daya kamata,har ranta takejin wani tuquqi,wannan ya sanya ta ajiye cokalin ta laluba ta gincira,duk wannan abun datakeyi khairri na kallonta tana hawayen tsananin tausayinta,zuwa tayi ta zauna kusa da ita ta kamo hannunta tace "Sister ya bakici abuncin da yawa ba kaddai harkin koshi?" Murmushin yake tayi tace " Na qoshi ne wlhy" "Nasani baki koshiba hafsat,kawai sabida bakya saka spoon din inda ya dace ne,kiyi hakuri na baki kanki saba kuma inshaa Allah zaki warke ai haka doctor yace zakiji sauqi kinji" hawayen da dukkaninsu ke qoqarin tarewa ya silalo musu hafsat tace "Khairiyya haryaufa yaa shaam bezo ya duba niba,da gaske manufarshi kenan ya rabu dani har abada?" kukane ya kwace mata ta toshe bakinta,khairiyya tama rasa me zatace mata "kiyi hakuri hafsat,amma barin kira miki shi awaya" batace komai ba wannan ya sanya khairiyya taje waje tayi kiran shammaz akan dan Allah yazo hafsat ta damu da rashin zuwansa,beyi musu ba yace yana nan zuwa da dare.....     A parlor zaune hafsat take a kujera me mazaunin mutum biyu,se shaam dake zaune a me mazaunin mutum d'aya,dak'yar ya iya bud'e bakinshi yace "Hafsat ya jikinki" "Naji sauqi Alhamdulillah" "Akace kina nemana?" sadda kanta tayi qasa "Yaya dama zancen komawa nane gidanka,dan Allah kayi hakuri abubuwan dasuka faru wlhy ko mutuwan khaleefa ba laifina bane lokacin sa ne yayi" murmushi yayi yace "Haba hafsat,kewai bakya fahimtar abubuwane? Ban soki nakuma zauna dakeba sanda kike mutum me lapiya,se yanzu dakika zama nakashashiya,na dade da fad'a miki sam bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane saura miki yaushe ki gama iddah,idan ma banyi kuskure ba aiba idda a kanki,saboda haka kiyi hakuri ki kalli dahir ni bazan taba dawo dake gidana ba,ina miki ao irinna yan uwantaka matsayinki na kanwata amma bawai zancen aure ba" dukda bata gani amma hakan be hanata duban inda take jiyo sautin muryanshiba tace tana kuka "Yanzu yaa shaam idan kai dakake dan uwana ka gujeni akan inada matsala waye aduniya ze aureni? Kaine sanadin lalacewar rayuwata,ka b'atamun duk wani abu danake taqama dashi,bani ga karatuna babu labarin future na,banida d'a ko d'aya a duniya da wanne kakeso inji?" murmushi ya kuma yi "Hafsat wlhy kinji na rantse bazan tab'a iya zaman aure dakeba,ke ni idan ma kinamun wannan maganar haushi kike bani wlhy,kimun magana kanki tsaye indai zaki bani matsayin yayanki to zakiga gata na haduwa,amma zancen aurennan yarabu kenan har abada,idn bakida wani abun fada zan wuce"......sanda ta d'anyi shiru sannan tace " Nayi dana sanin saninka arayuwa,nayi danasanin kasancewarka d'an uwa na jini agareni,nayi danasanin aurenka,nakuma yi danasanin aurenka,nayi danasanin kasantuwar zuciyata tawa ina ma ace canje aka mun bisa kuskure dana roqa a sauyamun da tawan sabida na kaucewa wannan wahalalliyar soyayyar,daga rana me kama da yau inaso ka nemo biro da takarda kakuma rubuta ka ajiye cewar ni hafsat nakashashiya nafita arayuwarka na har abada,na yanke duk wata alaqa dake tsakanina dakai, harta zamanka d'an uwana,ko a hanya ka ganni karka nuna sanayya tsakanina dake,bana buqatarka arayuwata ka sani ayau d'innan wlhy na tsaneka tsana mafi munin tunani,bazan hana zuciyana haukanta na sanka ba amma zan iya haramtawa rayuwata koda gaisawa dakai koda hakan yana nufin zan rasa ilahirin rayuwata kuwa tunda ai ka gama nak'asani meya ragemun,nice nan yaa shaam zan tabbatar maka da cewar bakin rijiya sam ba wurin wasan makaho bane" Yad'anyi mintuna biyu bece komai ba secan ya nisa yace "Hafsat me kuma ya kawo maganar tsana anan nifa d'an uwankine" miqewa tayi ta soma doddogara sandarta tana neman hanyar waje,kasancrwar tasan tsarin gida. Yasanya tayi amfani da basirar ta ta nufi cikin gidan zuwa dakinsu.....duk wannan zantutuukan nasu akan kunnen abba haris tausayinta me tsananin gaske ya rufe shi,daganan ya qudiri niyyar nemawa hafsat lapiya kota halin qaqa koda kuwa dukkanin abinda ya mallaka ze qare.....     Hafsat tama kasa kuka,gaba d'aya wani mummunan yanayi takeji a zuciyarta game da shaam,tabbas yau tafara jin yana fice mata arai cikin qanqanin lokaci,wayantane ya soma ringing tashiga lalubarta tana kamowa dama wurin sazata amsa kira baze mata wuyaba ya sanya ta d'aga ta kara a kunne "Assalamu Alaikum" shine tajiyo am fad'a a d'ayan b'angaren tun kafin tayi magana,cikin sanyin murya tace "Amun wa Alaikassalam,barka da wuni" "Hafsat ya gida ya kuma jikinki?" "Da sauqi Alhamdulillah" ta bashi amsa "Sunana Dr.sayyeed Hameed Ali uncle d'inki" Murmushitayi tamkar yana gabanta sannan tace "Ayya Uncle say ya aiki yakuma kwana biyu?" "Alhamdulillah hafsat,dama Number din abban ki damuke da afile nayi tankira baya zuwa gashi kuma emagency case ne ya taso,shiya sanya nace barin nemeki ko zaki had'ani dashi" "Babu damuwa uncle say barin je ingaya mishi seya duba last call nawa ya kiraka,amma sekayi hakuri ni kadaice adakin khairii batanan,idan tashigo seta rakani gun abban" sosai ta bashi tausayi yace "Babu damuwa hafsat,nagode sosai" "nima nagode sosau uncle say Allah ya saka ma da alkhairi" har ranshi yaji dadin adu'arta lokaci d'aya ya tuna da matarsa margayiya data tafi ta barshi da tsananin kewa,itace take yawan masa adu'a irin wannan tun bayan mutuwar mahaifiyarsa......       Office Abba yaje ya sameshi,bayan sunyi magana awaya,da suka gaisa Dr.sayyeed ya tattara nutsuwarsa gun Abba sannan ya gyara zaman gilashin idonsa yace da Abba "yallab'ai Allah shine ya dasamun tsananin tausayin hafsat wanda tunda nake ban taba jin tausayin patient kwatankwacin yanda naji akan hafsat ba,musamman yanda na kula da karacin shekarunta, da farko dai ni haifaffen qasar India ne amma kuma d'an asalin Nigeria,mahaifina likitane kwararre wanda gaba d'aya acn yake aiki acanne ya had'u da mahaifiyata datake Ba'indiya kasancewarta musulma gaba da baya ya sanya basusha wahala iyayensu suka aminta dasuyi aurensu, acan aka haifeni kuma acan nayi karatu na gaba daya,bayan mahaifiyata ta rasune mahaifina ya dawo ainahin qasarsa wato nan Nigeria a kuma birnin sokoto,inada qanne na mata guda biyu suna gidansu mahaifiyata dake Babban birnin indiya wato Goa acan suke karatunsu,ni kadaine nabiyo mahaifina nayi aurena anan har Allah ya karb'i ran matata a wurin haihuwa......Dalilin daya sanya na baka tarihin rayuwata shine sabida inaso kaje kayi bincike kaji koda zaka da abinda zan fad'a maka yanzu,dukda yake dakai nakesan muyi tafiyar idan ma hakan ta kama" Dukda yake Dr.say yayi magana me harshe damo amma abba be katse shiba yace "Ina jinka sayyeed" "Mahaifina ya mallaki qatotuwar asibiti tashi ta kanshi a k'asar india inda kusan garuruwa hudu a fadin qasar zaka tarar akwai branches nata,zan baka komai sekayi browsing ka gani,akwai wani qwararren likita dake aiki a asibitin na mahaifina wanda shararre ne a b'angaren k'walwa shine nayi waya dashi sabida al'amarin hafsat yana damuna a bakin shi naji cewa inshaa Allah indai tanada rabon gani a duniya Allah ze bashi ikon mata aiki kuma fitowar farko ta warke sabida badashi aka haifeta ba, dama nikuma zanje india gun yan uwana dakuma kula da asibitin ta mahaifina shine nake sha'awar zuwa tare dakai da hafsat idan bakuda damuwa,nidai ayanda nake tausayin hafsat bana san ko sisin ku har jirgi ma nine nan zan dauki nauyi amincewarku kawai nake buqata dakuma uwa uba adu'arku" sosai Abba haris yaji dad'in wannan zancen yace "wannan ai babban ci gaba ne sayyeed,kuma zancen yadda tun yaushe aina yarda zancen kuma wai kyauta duk bata taso ba nine nan zan biya komai har zancen tafiyar ma,kuma wlhy na gode nagode maka sayyeed Allah ubangiji ya albarkaci rayuwarka ya sanya haske acikinta yakuma d'aukaka,Allah ya jib'anci lamuranka ya baka wata matar ta gari ya ilmantar da bayanka yakuma tallafi bayanka sayyewd" godiya sayyeed din tun kafin abba yabar asibitin yafara processing visa batare da sanin kowaba.......      Ranar wata juma'a hafsat na kwance ta rufe idonta acewarta ba amfanin bud'asu wayanta ya soma ringing janyowa tayi ta kara a kunenta bayan ta d'aga,jin muryanshi kad'ai ya sanar mata waye me kiran cikin shagwaban dabata masan tana dashiba tace "Uncle say se yanzu,ni baran ma kula kaba Allah kuwan" murmushi yayi tamkar tana gabanshi " Beauty kefa rigimanki baya qarewa,wlhy Aikine yasha kaina matuqa kiyi hak'uri yanzu ya jikinki ina fatar kinji sauqi?" turo baki tayi "Ni bazan kulakaba" dariya sosai tabashi amma sabida bayasan ya b'ata ranta yace "Kiyi hakuri mana Beauty,aina sanar miki uzurina kuma fa yau zan siya miki pop corn da ice cream plus frozen coffee amor" murmushi tayi "Ni bazaka siye ni da wannan ba bazan ma shaba,nidai kawai ka kawomun qawata dan Allah itane take d'ebemunnkewa" "Naji zan kawo tan indai suhaila ce amma dai gaskiya se gobe,yau ina riqe sosai" murmushi tayi tace "Babu damuwa uncle say Allah ya kaimu goben" sallama sukayi sannan suka ajiye wayoyin su, hafsat se murmushi takeyi tun zuwan suhaila arayuwarta take jin sanyi abubuwa da dama suna canja mata ko yanzu tanata faman tunanin yanda zatayi idan tabar qasar,shiya sanya taso ayi auren uncle say da suhaila kafin tafiyarsu india dase su tafi tare da qawar tata me yawan d'ebe mata kewa...... Yauce ranar tafiyar su hafsat india,kowa se adu'a fatar samun nasara suke musu, tafiyar har da umma aciki, da abba......nima ina musu fatan alkhairi.. Don't forget to vote and comments...... [1/23, 9:57 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 13 *FLASH BACK* A ranar da yaa shaam yaji komai a ranar Haleemah taje wurin bokanta,kallonsu yayi itada uwarta yace "Kunyi sakaci dukkannin aikinku ya lalace,kuma mijin yarinyarnan yaji komai ciki kuwa hadda kashe masa gudan jininsa,kunsan cewar wannan abun ba qaramun b'ata ran shi yayi ba,sabida haka wannan aikin dazakuyi bashida wani amfani,idan kuwa kunaso amasa sabon aiki daze rufe masa baki tokuwa ke Haleemah sekin baiwa Aljani kyautar mahaifarki sukutum,tareda sha'awar mijinki ma'ana zamu cire dukkanin wata sha'awa dayake da ita a 'ya mace" zabura haleemah tayi tace "Nashiga uku boka,shikenan ni bazan qara haihuwaba? Kuma shi mijin nawa baze qara samun wata sha'awa akaina ba to meye amfanin auren??" Tsawa ya daka mata "ke!!!! Karki kawowa mutane raini kinji ko,kune da kanku kuka fada masa kuma yaji,aljani meramo yaso taimakonki ne idan bakyaso kije can,amma kin san na sanar miki asirin ze karye kuma ke zaki haukace,idan kin fisan haukar kije da mahaifar keda hankali sedai ki gani ga wari" zaro ido tayi tace "Kayi hakuri boka ba haka nake nufi,abunda ya kadar dani zancen qwace masa sha'awa" zbura yayi " K'wace masa sha'awa tare yake tafiya da sanya ya manta daduk wani abun da ya faru kuma yana ji yana gani yankasa magana koda be samu mantawar duka ba,shida sha'awar wata mace bama keba har gaban abada,kuma kece da kanki kikace dukiyarsa kadai zaki kwashe kiyi gaba to meye naki da sha'awarsa" haka dai dole suka yarda atake awurin aka hanawa zuciyar shammaz daukar wani mataki yaji a rayuwa baze iya mata koda tsawa ba,mahaifiyar haleemah ta kalli bokan tace "Aiki yayi kyau ya saki kishiyarta sedai yan gidansu nasan zasuce ya dawo da ita bama san hakan shifa ya za'ayi?" "Dama kin dena wahalar da kanki,sabida wannan yaron basan yarinyar yakeba,bana tunanin ze maidata kudinku da jikinku su huta hakanan" Godiya sukayi sannan suka wuce masaukinsu inda zasu qarashe tambad'ewa Allah ya shiryar damu ya kare muna imaninmu..... Hafsat Ajikin umma tayi baccinta jirgi,gaba d'aya Dr. Sayyeed duk wani motsi da zatayi idonshi na kanta masifar tausayinta yake ji, gashi yarasa dalilin daya sanya a wuni idan dai har ko kiranta beyiba seyaji wani uban zazzab'i na shirin rufeshi gaba daya,yakuma kasa fahimtar meyake damunshi arayuwa...... *INDIA* Kwanan su biyu a can agidan su maman Dr.sayyed suka sauka dukansu kasancewar gidan babban gidane ga kuma family d'in sananne ne a mumbai, Abba haris shikad'aine ya sauka a masauki sabida ganin rashin dacewar tarewarsa gidansu alhalin shi namijine....Ranar da aka shiga tiyata da hafsat har Dr.sayyeed dashi aka shiga tunkan amata allurar da za'a shemar dabita take kuka,sosai Dr.sayyeed yaji tausayinta ya kama ta ajikinsa shi dinma sanda yayi kuka da adu'a d'auke a bakinshi aka soma aikin.......... *Bayan kwanaki biyu* Cikeda fad'uwar gaba ake jiran sakamakon idon hafsat,wanda tsabar fad'uwan gaba ya sany Dr.sayyeed gaba daya ya kasa cin komai ranar,Kasa shiga yayi wurinta sedai a waje ya zauna wurin su Abba haris, sunfi 3 hours zaune zugum zugum kafin fitowar Dr . Din yana zuwa ya miqawa Dr. Say hannu da murmushi d'auke a fuskarsa sannan yace "Congratulations brother, we've succeeded" Miqewa yayi lokaci d'aya " Are you sure my Dr.?" murmushi ya kuma sakar masa "Sure bros" Rungumeshi yayi sannan yaja hannunshi zuwa d'akin da hafsat take a kwance,takasa banbance tsakanin farin ciki da bak'in ciki wanne takeji,Matsawa yayi kusa da ita yace "Sannu Hafsat,Alhamdulillah komai yayi normal yanzu" kallonshi tayi ta gane muryanshi amma bata taba zata haka kyawunsa yake ba sekace wani haihuwar larabawa,lokacin datake ganinsa bata cikin hankalinta batama iya tuno waye a kanta bare ta tantance fuskoki,ganin batayi magana ba ta qura masa ido ya sanya yayi gyaran tsayuwa yace "Beauty sannu kinji?" murmushi ta sakar masa sannan hawayenta ya silalo da gudunshi tace " Thank you,thank you so very much uncle say,may Allah bless and reward u abundantly" hannunta ya riqe sannan yace yana fad'ad'a fara'arsa " Beauty nafiso inji kina fad'an Alhamdulillah shine ya baki lapiya Allah,soni nawa taimako yazone ta hanyarshi" murmushi tayi amma ta kasa tsaida hawayenta,hannu ya sanya ya share mata hawayen sannan yace "Beauty kiji sauqi gaba d'aya da sauri so nakeyi na kaiki yawo,watannin da kikayi bakya gani duk sekin rama wannan kallon" murmushinta ta fad'ad'a har fararen haqoranta suka bayyana,sannan tace "Uncle say i so much like you,apart from my parents ur d only person nasan yana kulawa dani tamkar blood d'aya yake yawo ajikinmu,bana fatan abunda ze raba zumuncin mu har abada" murmushi kurun yayi haka kawai ya tsinci kanshi da matukar jin dad'in kalamanta "Ameen ya rab" ita kad'ace kalmar daya tsinci harshensa da furtawa,kan wani ya kuma yin magana har su Abba sun afko d'akin.. Da sauri Abba ya rungume hafsat jin ta kira sunan sa,suka yita kukan murna sam barka abinsu. *Bayan sati biyu* Hafsat gaba d'aya jikinta yayi saiqi har yawo sun zaga garin ba laifi,sabida har shirin komawa sukeyi,gaba daya qannen say mata suna matukar qaunar hafsat sun shaqu da ita itada khairii ba kadan ba,har roqa sukeyi wai su zauna dasu india suma suyi karatu dayake dukkansu sunajin hausa sabida babansu dabhausar yake musu magana mamansu kadai ke musu yaren india kan tarasu kuma itama tanajin hausar,koda Hafsat ta roqi Abba haris akan abarta anan tanasan tayi karatun low mmbe hana suba har khairii yace su zauna atake aka nema musu gurbin karatu inda dukkansu suke karatu a jami'a d'aya se dai hafsat low take karatu yayinda kharii ke karantar business admn..... *NIGERIA* Zaune ake a babban parlor ana hirar dawowar yan india daddy ba qaramun dad'i yakejiba ganin cewar hafsatunsa harta fara sabon karatu,sabida anan niger tamayi missing semester d'aya kowa se murna yake shi sam yaa shaam hankalinsa baya wurinsu sabida damuwarsa ma ta isheshi sam baya iya tab'uka komai a shinfid'ar matarsa sannnan kumanya kasa gane dalilin daya sanya komai zatayi baze iya yi mata magana ba,tazo tayita karb'ar kudade hannunsa amma baya iya cewa da ita kanzil,daddy ne yace " Shaammaz kaji qanwarka ta samu gurbin karatu a india,tana can mumbai tana sha'ani abinta banji ka sanya albarka ba" Dan tab'e baki yayi sannan yace "ni anawa tsarin banason banso yarinya taje wani qasar karatu,kawai dai ina mata fatan alkhairi,banza kowa ya masa aka ci gaba da hira,shi dama abba baya amsa koda gaisuwarsa ne...... Kwance hafsat take tana karatu Dr.say ya kirata, "Uncle say ina wuni" kwaikwayar maganarta yayi sannan yace "Duk wannan ladabun baze hanani zazzanekiba,an gayamun bakyashan magani mesa haka?" shagwab'ewa tayi "Allah ni uncle say ka yarda dani ina shan magani,sameera fa qarya takemun" "Naji amma mesa bakya shansa akan tsari,Allah idan kukayi hutu punishment dinki shine bazakizo Nigeria ba" kukan shagwaba ta saka masa dakyar ya hakura sannan sukayi sallama.... Mom Nu'aiym [1/25, 8:54 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                   *wannan shafin nakine kyauta Ta ma'aiki,inajin dadin comment naki Allah yabar zumunci* 15 Tun bayanda su hafsat sukaji labarin auren uncle say sataji gaba d'aya duniyar ta mata qunci tayaya ma uncle say ze hanata zuwa hutu,ace bikinshi sukutum wai bada ita za'ayi yishiba,gaskia abu beyi ba kam wannan ya sanya taketa fushi dashi,shi kuwa ya kafe akan bazata zoba wanda wannan umarni ne na abba haris,bayaso ya hanata da kanshi amma sam bayaso tazo ta sake tada hankalinta akan shammaz gashi ance su kula sabida matsalar ta na heart,haka akayi bikin tanata qunci batazo ba,gashi su sumayya da suhaila duk sun tafi itada da khairii ne kawai shekara d'aya kenan rabonsu da gidan....... *Bayan shekara Biyu* *Takun saqa* Ba kad'an ba hafsat kejin dad'i zatazo hutu Nigeria bayan shekaru biyu cur datayi harma da yan watanni bata Nigeria,tsakanin itada khairii bazakace wa yafi wani zumud'i ba,koda jirginsu ya sauka hafsat ji takeyi tamkar ta bangaje dukkanin mutanen dake tafiyar yangarnan ta sauko,sabida ba qaramun missing gida tayiba, A yangace yangar dabata san sanda ta koyeshiba take tafiya,ba shakka wanda yasan waccen siririyar hafsat kamar ka busata ta fadi baze yarda cewar wannan data tara mula mulan abun zama da iyayen heeps tare da doka dokan breast cewa itace hafsat d'in daba,sanye take da straight skirt na roba light blue da top red wacce ta d'ameta takuma bayya no ainahin surar da Allah ya mata,ga wani tsukakken flat tommy da bazaka tab'a yadda cewar mamallakiyar wannan booties ne dashiba,tamkar arayuwa ba'a saka masa komai aciki,sanye a idonta dan qareren qaton shade ne me kyau,a saman kanta sirirn fayafine ta yane kanta dashi,tun daga kan goshinta har girar idonta gargasa ne baqae wuluk se sheqi sukeyi,lallai hafsat tayi kyau, takuma qara girma side bag ce me kyau kalar ja rataye a kafad'arta yayinda a k'afarta take sanye da wages blue masu kayu matuqa, khairii ma irin shiga d'aya sukayi kalace kawai ta banbata domin kuwa ita pink and white tayi,sunyi kyau matuka,Abba haris suka fara hangowa inda basuyi qasa a gwiba suka zarce wurinsu suka rungume shi suna murna, "Abba kai kad'ai kazo ina su momy?" hafsat ta tambaya cikeda k'osawa,murmushi yayi yace "Nine nace kowa ya zauna ba wanda zw biyoni duk suna gidana ku kadai ake jira yau daddy ma na gayyata can sabida yara nema zasu dawo" murmushi tayi sukayi gaba abunsu zuwa mota.......murna sosai akayi domin zuwansu anyi girke girke na masifa masu matukar qayatarwa da dai hafsat nak tayi kasancewar ta jima rabon dataci abuncin gida,su momy suka wuce ita kuwa tace bazata ba se gobe,da dare bayan sun huta wayanta ya soma ya ringing tana dubawa taga sunan uncle say,qin d'agawa tayi gaba d'aya ta turo baki tamkar zatayi kuka kuma kamar yana ganinta,kallonta khaiirii tayi "Uncle say nefa ki d'aga mana" harara ta wurgo mata sannannta tsiyayar da hawayen datake ta faman tarewa "Bazan d'agaba ai cewa yayi dani shine ze dakkomu daga airport shine be zoba kuma na kirasa yama kashe wayan" murmushi kawai khairi tayi indai fad'ane dama tasaba ganin sunayi batanan sanda suke shiryawa abunsu.... Washe gari yamma liqis hafsat tace da driver ya ajiyeta gunsu momynta,haka ta shirya ta wuce yauma kalar dressing na jiya tayi sedai wannan karon lemon green and orange tayi ga alama wannan dressing shine d'abi'ar ta yanzu,a baking katafaren gate d'in gidan tace driver ya ajiyeta yayi tafiyarsa,ba komai a hannunta se wayarta kirar iphone 7 da side bag lemon green dake rataye a kafad'arta,koda ta shigo gate d'in gidan wayarta take dannawa,acikin qatoton madubin idon dake idonta,murmushi takeyi har fararen haqoranta suka bayyana ganin khairii na mata iya shege kan whatssapp akan tafiyanta gida, jitayi ance "Hafsat ce" D'agowa tayi fuska a had'e jin muryar me mata magana tana taunar cingam dake bakinta,batace dashi kanzil ba ta wuce taci gaba da tafiya abunta,mamakinta ne ya kama shaam ganin abunda ta masa,se wani yanga takeyi yayinda duk taku d'aya se yalwataccen qugunta yayi magana,ko kallon inda yake bata qara yiba tayi gaba,sosai tabashi mamaki ya had'iye wani yawu me d'aci a rayuwarshi yace "Lallai idan kika zomun da raini sekin gane kuskurenki" ... A parlor ta tsaya suna gaggai sawa dasu momy da daddy,daddy kallonta yayi "Lallai kulelen daddy girma yazo miki kinga yanda kika dawo kuwa,kuma yanzu naga ba rigima" murmushi kawai tayi batace komai ba, shine ya kuma cewa "Banga jakar kayankiba na zata zakizo gidane ai" sosai kanta tayi tace "Daddy nan gidan ba kowa ni gobe zan koma Allah kuwan" "Ni bazan takurakiba kulele so karki damu kinji" Miqewa da zummar zuwa kitchen ta hadaw onion samosa da ta zame mata jiki,kullum setaci ko a can dama abuncin suce,kan taje ko ina sega yaa shaam ya shigo ko kallonshi batayi kuma kowa ya kula da hakan shi kuwa ya qurawa yalwataccen gashinta ido harta b'acewa ganinsa,zama yayi kusa da daddy cikeda fusata yace "Daddy kagan kuwa hafsat wulakancin datamun ko gaisawa mafa batayi daniba ko kallona ma batayiba" murmushi daddy yayi yace "kayi hakuri zan mata magana,wataqil fushi takeyi dakai har yanzu" bece kanzil ba harta dawo d'auke da plate dinta na onions samasas ta zauna kusa da momy "Mommy zakiji samosar albasa zallah,da dad'i wlhy" kallonta momy tayi ta d'an b'ata fuska "Hafsat mesa baki gaida yayan kiba,ko baki ganshi bane?" cikeda rashin kulawa tace "A a momy waye kuma yayan nawa naban gaidaba,nina gaisa da duk wani jinina dama wanda ba jinina ba a gidannan kumafa kina kallo" "yayanki shammaz nake magana,hafsat" d'an tab'e baki tayi ta yamutsa fuska "Hmmm lallai ma mommy,bakin rijiya fa ba wurin wasan makaho bane,ina nayi matsayin dazan gayarda d'anku,kuma ni wlhy Allah ya kiyaye ya zama yayana" mamakin kalamanta kowa keyi daddy yace cikin fushi "Hafsat kinad hankali kuwa,a gabanmu kike fad'ar wai shammaz ba yayanki bane" turo baki tayi ta soma hawaye sannan ta miqe ta tattare mayafinta ta yane kanta ta wurga wayarta ajaka ta shuri takalminta,wlhy indai kukace zakuna takurani akan gaida wannan wlhy bazan qara zuwa muku ba,ku tambayeshi mana yaya mukayi dashi,ai mun raba duk wata alaqa tsakanina dashi to meye kuwa ruwansa dani" tana kaiwa nan tafito daga main parlor d'n tana kuka, Ganin Uncle say a tsaye jikin motarshi ya sanya ta qara turo baki takuma qara sautin kukan datake har tana doka kafarta a qasa,da sauri yazo kusa da ita "subhanallah Beaty,.eya sameki kike kuka?" sauke hannunta tayi tace "Bayan su daddy da mommy ne wai sena gayar da shammaz,ni kuwa alqawarin nayi har abada bazan kuma masa magana ba,ni Allah bazanma kwana musu ba" hannunta ya janyo "Hafsat ur 19 fa,why are u still behaving so childish? Gaskia banaso kuma zamuyi fad'a,meye idan kin gayar da yayanki?" turo baki tayi tace "Uncle say bazaka ganeba banaso ina tunaninshi kuma banso ina ganinshi,tsanar kaina nakeyi kuma wlhy zuciyana yanamun zafi ko tunasa nayi,uncle say plss karkace na gaidashi kaji" tausayinta yaji ya sani sarai har gobe hafsat tanasan shammaz,kuma yasani zuciyarta a cunkushe yake da tsanar abubuwan da ya mata,kan yace wani abin daddy da shammaz sun fito,gaisawa yayi dasu yayinda hafsat tayi kici kicin,bayani daddy ya masa akan fushi zata gida,lokaci daya ya hade fuska yace "Hafsat kinsan shiyasanya na hanaki zuwa hutunnan Allah idan baki nutsuba nida kene,kina girma amma bakya wayau maza ki koma ciki" turo baki tayi tana hawaye "Uncle say bamu mafa gaisa kuma its been long,dama ba wurina kazo ba?" "Gunki nazo amma yanzu ammun waya yayarki tana labor so zanje gunta" matsowa tayi kusa dashi ta soma doddoka k'afa "Allah ni Uncle say sena bika dama tunda nazo banga Aunty ba" girgiza kanshi yayi a gefe d'aya kuma yana jinjina girman da hafsat tayi da kyau,se d'an karen wawta data qaro,kuka kuwa ya saba kullum ne ko a waya se an masashi akan zuwa gida..... Mom Nu'aiym *Babu tabbacin cewar gobe zaku samu,se yanda Allah yayi ina busy ne sosai kwanakinnan* [1/28, 8:22 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*   * A shafin daya gabata,munyi kuskuren number,amaimakon 14 se muka saka 15,idan muka ce zamu dawo baya da matsala wasu zasu rikice sabida haka zamu ci gaba da 16 inshaa Allah,nagode.*                               16 A asibiti kuwa uncle say gaba daya hankalinsa ya tashi jin za'a shiga da suhail cs sabida ta kasa haihuwa,sosai hankalinsa yaqi kwanciya,yakasa zaune ya kasa tsaye shi kuma ba b'angarnsa bane gefen haihuwa,Ganin Dr. Hafiz ya fito daga thereter room ranshi a b'ace ya sanya qirjin say ya doka da k'arfin gaske,yana fatar ba abunda ya faru kenan ba, Gwiwa a sace Dr. Hafiz yazo kusa dashi kallanshi yayi sannan ya d'ora hannunshi a kafad'arshi ya kura masa ido,hannun nashi Dr. Say yabi da kallo sannan a hankali ya mayarda dubansa zuwaga Dr. Hafiz amma beyi magana,cikin dakiya hafiZ yace dashi "Im so sorry to say we lost both the mother and the child,tunka mufara thereter d'in Allah yayi ikonsa akansu kayi hakuri abokinaHaka Allah ya tsara"Kasa koda motsi yayi idonshi sun qeqeshe sunyi jajir amma ba alamun ruwa acikinsu,ihun da hafsat ta kwallah ne ya dawo dashi duniyar tunanin dayaje,da sauri sukayi kanta se gunjin kuka take wayyo ita Allah Aunty suhaila, bata taba ganinta ba se a hoto kasancewar wancen lokacin dasukayi shiri sosai ita bata gani kuma tunda ta warke bata zoba amma sunyi wata irin shaquwa mara misaltuwa kullum se sunyi waya yafi a irga,ko jiya sanda sukayi waya,yauma da safe haka, sosai hafsat ta gigice dajin zancen Dr.Hafi,say shi yama rasa me zeyi Dr.bafiz ne ya lallashinta azatansa qanwar marigayiyar ce, A haka ya lallaba yayiwa mahaifinshi waya da kuma nata mahaifin kasancewar dama basusan ankawota asibiti ba,mutuwar suhaila ta rikitar da Dr. Say sabida yana matukar qaunar matar tasa,sannan be tab'a kawo mata mutuwa ba ko kan yafita da safe lapiya lau ya barta kuka yake tayi tamkar wani qaramun yaro har akayi sadakar uku,hafsat ma gaba d'aya ji take duniyar ta mata duhu,batajin dad'in komai,haka dai dole kowa ya haqura wanda ya fisu san baiwarsa ya dauke abarsa gaba daya....... *Bayan sati uku* Yaa shaam zaune a parlor din gidansa kusa dashi haleema ce take ta faman taunar cingam sekace abun dole, shi kuwa gaba daki daya hankalinsa baya kan kallon dasukeyi yana gun wannan hafsat da gaba d'aya tun zuwanta ta sauya masa tunani,be tab'a zata akwai ranar da tunanin hafsat ze hanashi sakat ba,anya kuwa bazece da abba yayi nadama ze maida itaba,kai idan yaje gun abba baze saurareshiba wataqil gwara ma yaje gun daddy,da wannan tunanin yaje ya kwanta.... Niko nace hmm ubanka zakaci d'anye wlhy.. "Mero ni kuwa wai in tambayeki?" kallon hafsat meron tayi "Ina jinki mana Allah yasa na sani" gyaran zamanta tayi ta tattare nutsuwarta gun mero tace "meyake damun yaa shaam? Naga duk yabi yayi baqi ya rame,kuma ya rage kiza kiza" kura mata ido mero tayi na yan dak'k'u kan daga nisani bayan ta gama nazarinta ta nisa tace " kaidin mace ke d'awainiya da shaam hafsat,wlhy haleema tagama da yaa shaam ta shanyeshi tas,danma su momy sun tashi tsaye da adu'a,danma bazaki fahimta bane amma da kunnena naji tana magana da qanwarta harira akan naqasashin dasukayi,ko kad'an fa baya sha'awar mace wai sabida karya tuna abunda suka aikata,in taqaice miki dai kud'ad'e take karba a hannunshi da kadarorinsa baji ba gani nan da kika ganshi yanzu bashi da komai se asibitinsa shi d'inma sabida daddy yana tsaye ne akan asibitinsa da takardun wurin gaba d'aya,sedai tayita yawon banza nabin maza,ni a ranar danaji suna zancen aunmai asiri a ranar na sanarwa momy nanne fa aka d'an samu sauqi domin adu'o i da magungunan tsari sukayita nemar masa,gashi baya kula da ibadunsa da addininsa seda daddy ya tashi tsaye yanzu dai yaji sauqin rashin jin sha'awa duk nice yar rahoto akwai lokuta da dama da idan naje gidan nikan tadfasu suna wasaninsu wasu time ma har kwanciyar aure nake fahimtar sunayi dukda ni ban yarda da matar ba,yanzu abu daya ya gagaremu shine rabashi da matar sabida tsananin santa yakeyi fa,gashi ita kuwa komai ya samo seta qwace shi tatas ni na rasa wane irin kaine sa yaa shaam,gashi kumansu daddy sun saka yana adu'o i kema dai ki tayashi gaskia,yana cikin wahalar mace" nisawa tayi sannan tace "Allah ya kyauta musu,Allah ya shiga tsakaninsa da ita" kallon tausayi mero ta mata ganin tana kwallah tace " Nasani hafsat har yanzu kina san shaammaz ina rokon Allah ya daidaita tsakaninku" kallonta takumayi tana me sharar kwallan daya zubo mata tace " Mero bana fatan sake zaman aure da shaam,ko a mafatki naganni matsayin matarshi lallai senayi adu'ar tsari daga mugun mafarki had'eda yin sadaka, har kwanan gobe ina san yaa shaam sedai a yanda na fahimta sam wannan bashi bane mafita agareni,so tari zakiga abubuwan damu y'an adam muke so basu suke zamtowa mafakar alkhairi agaremu,yaa shaam ko banda asiri ba sona yakeyiba kuma tsana ta zahiri,nidai wlhy kinji na rantse miki nidashi har gaban abada,ina dai masa fatan alkhairi" jinjina kai mero tayi "To Allah ya kawo miki muji na gari me qaunarki" "Ameen" ta fad'a ataqaice sannan ta kwanta ta runtse idonta...... *Bayan sati biyu* Shaam durqushe agaban daddy da abba haris dasu momy harma hafsat wacce dominta aka tara zaman,kasancewar wai shaam yace ze aureta kuma ze barta harseta qarasa karatunta a india,kowa yayi shiru yana kallon ta tsuniyar daddy domin kuwa ilahirin jama'ar wurin kallon me bada tatsuniya suke masa harya idar,hafsat dai batace qala ba kazalika bata koda girgiza da zancen ba tunda taga yana mata bata dagawa be dena kiranba ta tabbatar cewar lallai da wata aqasa..... Kallon su Abba yayi yayi wani malalacin murmushi sannan ya kalli hafsat yace "y'ata nasan bazaki tab'a watsan qasa a idoba,ina sauraronki menene naki ra'ayin ni duk abunda kikeso shi zan miki" kallon shi ta dago tayi ido cikin ido suna had'a ido abba ya gano ta shaqa,ta nisa sannan tace idonta a qanqance " Bazan sake fad'ar abunda zan fad'a a yanzu ba,abu d'aya nake san kusani shine,dukkanin abinda kukaji zan ambata yanzu babu wasa kokuma wani abu makamancin raini aciki,kuskurewa qa'idata d'aya ka iya janyo lalacewar komai musamman idan na aikata abinda zan aikata idan aka kuskuremun qa idar" shiru ta danyi kowama yayi tsit taci gab "Ni bazawarace ba budurwaba kuma a tsari na addinin musulunci nice dakaina nake da haqqin zab'awa kaina mijin aure a yanzu,bazan lamuncewa zab'in kowa ba tsarin addinina zanbi, kuma wlhy summa tallahi bazan tab'a komawa auren shammaz ba,ko gawata akayi kuskuren daurawa aure da shaam ban yafewa wanda yayi ba koda mahaifinane kuwa, idan aka qarabtayarmun da zancennan wlhy na sanya qafa nashiga duniya nida gida har abada,idan dame tantama kuma ya gwada tada zancen kuga ikon Allah, ku tambayeshi kuji dalilansa naqin zama dani idan dai basankai kuke sanyi ba ai bazaku qara cutar saba kamar yanda kukayi abaya,da bakinsabyace dani ya tsaneni!! An cuceshi da aka had'ashi aure dani,da bakinsa gashinan zaune ya kalli tsabar idona yace dani Babu tabinda ze zauna da mace bushashiya ni menakedashi,mena ajiye ajikina ina fama da qasusuwa,da bakinsa ya kalli tsabar idona yace dani na dena mafarki ze tab'a had'a shimfud'a da banza irina bushashiya,ashe nidin nan icce ce a idonku,ashe bajini a jikina,ashe qarfeceni bansan dadin mijiba,idan har baku sani ba toku sani yau nasha baqar wahala rayuwa da miji fanko,ina da aure an kawar dani sabida gudun wannan yaso ya cillani gayinta banda a litttafan hausa da fina finai ina kuka tab'ajin anyi aure shekara daya amma namiji be taba koda riqe hannun matarsa ba duk sanda kuka ga jikina da nashi ya hadu tofa duka ne,kuma da bakin sa ya sanar mun cewar bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane,shine ina makauniya zan dauki kaina inkai daidai bakin rijiya,sabida bana tsoron afkawa aciki,toku sani ina tsoro!! Na rantse da Allah kona rasa mujin aure bazan auri yaa shaam,ninan ni kadaice na san baqar wahalar danash a hannunsa,a ranar dana samu matsala dakaina na roqeshi akan waze aureni idan yasaken ya taimaka ya maidani gidansa,bud'ar bakinsa se cewa yayi dani be soni sanda nake da lapiya ba se yanzu dana dawo nakashashiya,bayan shine silar lalacewar rayuwata da quruciyana kowa namun kallon bazawara!! Kullum zancensa d'aya ya tsananeni yana tunasar dani bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane,shine yanzu ze bazamo kome ya gani ajikina oho!!! Ko kuwa dai yanzu zan iya wasa a bakin rijiyar tunda naqasa ta tafi oho!!! D'aukacin mutanen parlor dinnan ku shaideni ranar dazaku qara zuwamun da zancen komawa gidan shaam kun rasani kenan har abada!!!!"" Jikin kowa yayi sanyi yayinda abba haris ya zabgeta da albarka,shaam kuwa ya saka kuka wiwi wai ta taimaka masa....to phaaaa.. Zaune suke idata Uncle say a babban parlor na gidan daddy se shagwab'a takeyi wai bazata koma india ba,shi biyeta yakeyi ya saba haka sukeyi da qannenshi sesu sakashi gaba abu beje yazo ba su saka masa kuka "Haba dan Allah uncle say,idan kuma na tafi bazan qara ganin kaba fa" murmushi yayi yace "Dan Allah hafsat ki dena rigimarnan,bakya ganin khairi batayi haka ba? Ke komai se kace jin jira,komai rigima komai kuka,na sanar miki akwai wani coirse dazanyi a india na shekara daya kuma nxt montj zanzo,tunda kunfara school seki koma kafin nazo" turo bakinta tayi waje " Ni dai jiranka zanyi bazan iya juran rashin ganin kaba na tsawon wata ni yanzu im used to you over,i just cnt imagine my self with out you around" Murmushi ya sakar mata "Nima haka beauty amma ya zamuyi yanzu idan namiki aure ya zakiyi? Sekice dani zaki tafi" B'ata fuska tayi "Ni nace dakai zanyi wani aurene,ni bazan taba aureba aje ana dukana,maza basuda kirki wlhy" janyo hannunta yayi shi yarigada ya saba da al'adar indiyawa yace "Beauty banasan wannan mummunan tunanin dakika sakawa kanki,sam be dace kina cewa bazaki qara aure ba,adu'a zakinayi Allah ya kawo miki muji na gari me qaunarki tsakani da Allah" kallonshi tayi ido cikin ido tace "Ni koba wannan ba bazanyi aureba,idan nayi aure mijin baze bari ina ganinka kullum ba,nikuwa that will be d worst thing that will happen to me ever,i just cnt imagine my self living a day with out u" murmushi ya sakar mata yana nazarin kalamanta sannan yace "yanzu dai naji,amma ki daure ki koma school Allah zan siya miki sabon waya da sabon laptop da sabon ipad kuma zan siya miki sabon kaya ma,na zuwa school madam gayu" tana murmushi tace "Thank you for that,buh bana buqatar komai daka lissafa i just need u beside me,idan wannan baze samu ba,zan haqura nace haka Allah ya tsara" sakin hannun mata yayi yace yana miqewa "Thats very good of u gold,zancen waya kuma i already bought one for you, samsung s8 your favorite product,yana mota muje nabaki " miqewa tayi tana ihu tamkar ta rungumeshi,say akwai principles seyaga dama suke riqe babbar waya fa!! A hanyar fita suka had'u da yaa shaam,uncle say ya miqa masa hannu su gaisa,dakyar ya bashi hannu sannan yace " ke hafsat wai an sanar miki kowane mutum kika dakko secikin gida ake kaishi haka akeyi?? Ga guest parlor can kuje amma se ciki,ba wani privacy kuma bare ma" kallon mamaki say ya masa ita kuwa taja hannun say batare data koda kalle shiba domin kuwa ita alqawari tayi idan yayi sallama zata amsa,ita kuma tashigo koda shi kadaine a wuri zata masa sallama amma bazata taba yi masa magana ba,koda ze mata bazata kulashi ba, gabansu yasha sekace wani dolo yace "ke badake nake magana ba?" say ne yace "kayi hakuri Dr. Shammaz inshaa Allah bazan qara zuwa muku gidan bama gaba daya bare kayi fadan bare ya shiga ciki" kawai se hafsa ta saka masa kuka " look uncle say,lemme just go n pack my things im going back to my Abba's house,im tired of this mesa daga zuwa hutu,Allah bazan kuma dawowa Niger ba sena gama school" hannu ya sanya ya dauko mata mayafin daya fadi ya rufe mata kanta sannan yace " Ina sauri ne gold,muje na baki wayanki" wani kishine ya tasowa shaam yace kai din dan iskan inane dazaka taba ta?? Dama iskancin dakuke kenan ko?" sosai rayuwar say ta baci ya wuce su zuwa mota,ya shige ita kuwa hafsat bakin ciki ya hanata koda motsi daga inda take se kallon say takeyi kunyarsa dukta rufe ta,hannun ta shaam yaja ya mannata da kofar parlor din yace " Ke wlhy ko zaki mutu sekin koma gidana wlhy ki sani wannan kayan dakika tara sena mora,bazan bari banza ta wuce niba" kallonshi kawai takeyi harya gama ya saketa batace dashi ci kanka ba,rayuwarata intayi dubu tota baci,haka ta zauna ta dinga kuka tana kiran uncle say yamma yaqi dagawa gaba daya ta damu da fushin sa,tsinuwa kuwa shaam yashata cikin kwando dubu.... Koyaya zata kaya a wannan bada qalar,gamu gani dai..... Mom Nu'aiym ce🔨 [1/30, 8:18 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                    17 Yaa shaam juyawa yayi zuwa gidansa,ransa a b'ace  yarasa dalilin sha'awar hafsat da Allah ya jarabeshi da ita,gashi sam shi har yanzu beji yana santaba,amma dai tunanin ta kullum dashi yake kwana yake kuma tashi.......hafsat har washe gari idan takira wayar uncle  say baya d'agawa duk hankalinta ya tashi, se messages take sending mai na ban hakuri sekace ita ta masa laifi,ganin dukta damu mero ta kalleta tace " kulele lapiya dai?? Naga tun jiya kamar kina cikin damuwa?" lumshe idonta tayi sannan tace a wahalce "Uncle say ne yake fushi dani mero,sam yaqi ya saurareni" kallon nutsuwa ta mata take hankalin mero ya tashi,kaddai ace hafsat san wannan sayyeed d'in takeyi? Inko hakane wannan yarinyar taga rayuwa ita gaba daya kullum san maso wani takeyi,kuma a yanda ta kula koda tana san say din batamasan tana yiba,ta yiyu wannan karon da sabon salon daya zo mata "Menene ya faru yake fushi dake har haka?" dafe kanta tayi sannan ta zayyane mata komai da ya faru ta qara da cewar "Amma mero kinga ya dace ace wai ya d'auki zafi dani har haka? Bafa nice namar laifi ba,taya ma za'ayi laifin  wani can ya shafan?" nisawa tayi sannan tace "Tooh hafsat kinsan wani be iya fushi ba ta yiyu bawai fushin yake dakeba ranshi ne kurin a b'ace idan ya huce ze kiraki" kan wani yayi magana wayan ta ya soma qara,jikinta har rawa yakeyi ganin uncle say ne,da sauri ta d'aga ta kara a kunne,kasa magana tayi kurin ta sanya masa kuka me tsuma zuciya a hankali yace "Rose menene kuma na kukan,ke komai bakida wani uzuri,kizo ina parlorn qasa a gidan daddy" zabura tayi ta suri mayafinta ta sauke da sauri,taje kusa dashi ta zauna tace tana sharar kwallah " Uncle say im so sorry" kallonta yayi yace "meye na bani hakuri kuma me kika mun,naga cols dinki ne,inata fama attending patients jiya goda naje gida it was late i coul'nt col u back,yau kuma tun asuba aka mun waya muna emergency thereter,i had to go there wlhy kina raina,shiyasa da sauri ina gamawa da office nazo na ganki kiyi hakuri"  share k'wallan daya gangaro mata ta saka hannu ta share sannan ta kalleshi tace "Ni na damu na zata fushi kakeyi dani,rabon danaci abinci tun jiya ma" zaro ido yayi yana kallonta "Wlhy ina ganin mutane masu wawta na dad'e sosai banga irinkiba hafsat,tayaya bakimun laifin komai ba zan soma fushi dake,maza tashi muje na siya miki abun dadi a season 7" murmushi ta masa tace "Karka damu zanyi samosa a gida" B'ata fuska yayi "Lallai ki tashi mu tafi,banasan shashanci" ahaka taje ta sako hijab tazo suka fita,suna fita yaa shaam na danno kan motarsa acikin gidan,qwafa yayi yace aranshi lallai dani kuke zancen sena qulla maka sharrin dabakasan akwai irinsa a duniya ba !!!!!..... *Bayan wata d'aya* Tun bayan da su poojah suka koma school yaa shaan yake cikin damuwa,da kanshi ya fahimci cewar lallai ko bayan sha'awa san poojah ya masa mummunan kamu ba kad'an ba, gaba d'aya mantawa ma yakeyi da wata haleemah a rayuwar sa kuma sam yadena bata kud'i hasalima baya kwanciya wuri d'aya da ita sun raba jaha ita kuwa dama ba sanshi takeba wannan ya sanya bata damu ba neman mazan datake kawai tasaka agaba tana samun kudad'e dama abu d'aya ya tsayar da ita shine asibitinsa daya saura ta k'wace masa,ganin kuma baya zuwa wurinta azatonta aikin da boka yace ze koma yine na ganin sun kwace asibitin daya kuma cewa lallai ne seya hanashi jin sha'awarta,wannan ya sanya hankalinta yake a kwance,yau shiri na musamman yayiwa zuwa gidan daddy akan maganar auren sa da hafsat wanda yake wannan kadaice mafita agareshi,koda yaje ga mamakinsa daddy haquri ya bashi akan lallai se idan hafsat dince da kanta ta amincewa komawa gidan sa amma muddin ba ita kesan koma masa ba toko lallai ya zame masa dole ya haqura,da wannan b'acin ran ya koma gidan sa. *INDIA* Tun bayan rasuwar matar Dr. Say yake cikin tsananin damuwa,shidai sosai ba kadan ba yake santa over,yaji zafin mutuwar ta fiyeda tunanin me hankali,zaune yake a babban parlor ya rufe fuskarsa da littafin dayake nazari,tunani ne fal a ranshi na suhaila wanda sam bemasan cewar hawaye sun fara gangaro masa ba,poojah kuwa tajima tsaye akanshi tana nazarinsa wanda shigowarta gidan kenan daga makaranta,a hankalibta sanya hannu ta janye littafin dake saman fuskar tasa ganin hawaye ya sanya ta danja baya a d'an tsorace,k'ura mata ido yayi itama din shi take kallo,zama tayi kusa dashi ta kalleshi cikin kulawa tace cinkin mutuwar jiki "Uncle me kuka kuma? Meya sameka haka?" d'an juyar da kanshi yayi yace "Hafsat suhaila na,suhaila na nake tunawa,yaushe zan samu macen da zata mayemun gurbinta arayuwa?? Wlhy ina matukar kewarta" tausayin sa ne ya kamata tace jikinta a mace "Uncle say dan Allah ka rage damuwar nan,idan kana wannan kukan mu kuma muce me? Batun yauba na kula dakai sosai kake damuwa da rashin ta koka manta cewar Allah wanda yafi kowa santa mahaliccin ta shine ya karb'e abarsa,kuma arayuwa ba'a tab'a barin wani dan wani kuma Allah shi yasan dalilinsa na dauke rayuwarta alokacin daka fi buqatarta,dan Allah kayi hakuri" kallon ta yayi yace "Na sani hafsat wlhy na sani narasa dalilin daya sanya na kasa cireta araina,kuma kullum tunanina a duniya waye zata mayemun gurbin suhaila? Waye ze soni kamar yanda suhaila take sona,wa zata kula dani kamar yanda suhaila take kula dani?" riqo hannunsa tayi sannan tace tana zubar kwalla "Nice nan zan maka dukkanin abubuwan nan daka rasa uncle say,meyasa bakasan kawa kanka adalci ne,had'uwana dakai had'in Allah ne sabida haka tun farkon had'uwa na dakai nakeji ajikina i meant for u and u alone,Ban tab'aji araina ina sanka ba ko kadan bantaba jin soyayyarka araina ba,amma kullum ina tambayar kaina menene k'auna? Banida mutumin danike matukar kewa sama dakai aduk fad'in duniyar nan,banida mutumin danike matukar tausayi aduk fadin duniyar nan sama dakai,banida wanda nakejin damuwar sa tawace har raina se kai kad'ai uncle say,banida wanda arayuwa nakejin tamkar zan rasa farin cikina idan yana fushi dani sama dakai,banida wanda arayuwa banida burin daya wuce naganni kusa dashi sama dakai,banida wanda nakejin zan iya sadaukar da dukkanin farin cikina akansa se kai kad'ai uncle say,banida burin daya wuce farin cikinka arayuwa,babu abinda yake qayatar dani se inganka cikin walwala,babu abu mafi soyuwa agareni se ganin farin cikinka inga kana dariya yafi komai saukarmun da nishad'i,a iya tunani wayannan abubuwan ba soyayya bace,k'aunace me zafin gaske,ada nayi tunanin so shine komai se yanzu danake rayuwa dakai na tabbatar wa kaina cewan so shirmene zallah,ada nayi tsammanin cewa akan soyayyar shammaz na shige halin da nashiga na ciwon zuciya se daga baya na fahimci cewar zallar mugunta,cin amana,cin zarafi dakuma wulakantanin dayakene ya sakamun ciwon zuciya,sabida soyayya ruwan shayi ce yana zubewa a qasa kuma sedai kanemi madarar ka rasa shimfidar ruwan banza kawai zaka gani a kasa,kauna kuwa kakkauran kindirmo ce sabida zubewar sa a qasa baze tab'a zama sanadiyar b'acewa kalarsa ba,itace nake maka zallarta,dan Allah uncle say ka k'aunaceni,dukkaninmu muna tsananin buqatar kulawar junanmu" sosai yake kallonta harya kasance ko qiftawa bayayi ya rasa dalilin sa najin komai tamkar a mafarki jikinsa gaba d'aya yayi sanyi,har yanzu hafsat yarinya ce bazata tab'a fahimtar saba idan yace mata kuma bashida hanyar daze bar zuciyarsa ta k'aunace ta sabida wasu manya manyan dalilai,batare dayace mata qala ba ya miqe yabar parlor d'in fuska kici kicin zuciyarnan sam babu dadi a jagule...... *kome hakan yake nufi,da Alama hafsat batada farin jinin masoya a duniya,ba wanda yatab'a cewa yana santa,sannan kuma ita sedai taso wannan taso wancan amma babu wata nasara,Allah ya temaketa dai,muje zuwa kuci gaba da bin alqalamin mom Nu'aiym.....            [2/1, 8:32 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 18 Dafe kanshi yayi bayan ya kwanta yace cikin kukan dabesan sanda ya kwace masa ba "Meya sanya arayuwa Hafsat take shan wahala har haka,ina tsananin sanki hafsat amma bazanyi ganganci nuna miki hakan ba,kamar yanda bazan tab'a bari soyayya ta tayi tasiri azuciyarki ba,gwaramun haqura dake a matsayin mata akan narasa rayuwarki har abada.." kukan yashigayi kaikace qaramun yarone,ganin wannan bazata fiddashi ba ya sanya ya shirya zuwa gun amininsa kamal khan domin sanar masa matsalarsa...... "Kamal akwai damuwa fa babba wlhy,duk sanda na kwanta senati mugwayen mafarkai akan lallai idan har na kuskura na auri yarinyar nan se an kasheta har lahira,ni bazasu iyamun komai ba sabida riqon addini haka sukace amma wai itad'in alqawarine duk mesan tan daya aureta lallai se sun ga bayanshi babu ita ba tarawa da wani d'a namiji harta bar duniya ni sosai take ban tausayi wlhy,wama yasan ko wancan yayan nata hakance ta faru dashi,ni ina matukar san hafsat son daban taba yiwa wata 'ya mace irin saba a duniya,rashin adalci d'aya zuciyarta tamun na sanya ta qaunaceni,Bansan yanda zatayi da ciwon zuciya ba idan har naguje mata,kuma ni bazan iya cewa da ita ga abunda yake faruwa ba harga Allah" nisawa khan yayi cikin yaren india yace " Sam karka gjjeta,karkuma ka nuna mata baka santa,wannan ba abinda zeyi illah ya wargaza mata zuciya gaba daya,sanan ni ina abu d'aya ne cikin biyu,kodai iskokaine da ita kokuma asiri aka mata,danni bantab'a jin hakan ba se'a irin harkar iskan nan,nifa a nawa tunanin kabata lokaci,ka kula da ita ka nuna mata soyayyar dakake mata inyaso a hankali kana koyar da ita girman adu'a da tsare azkhar safe rana da dare dakuma yawaita yin azumun litinin da alhamis,kana ana yawaita yin salatin annabi ba adadi,idan ma iskane zasu bayyana kansu idan kuma asirine lallai Allah ze taimaka kaga abun ya karye" murmushi yayi ya daura hannunshi akan kafadar khan "Inajin dadin shawar warinka abokina,Allah bar zumunci hakan zamuyi ai dole ma". Tunda hafsat taga yananyin Uncle say se jikinta ya mata sanyi,dak'yar ta iya jan jikinta zuwa bedroom nasu,har akayi magrib da ish bata fito ba,har akazo cin dinner koda aka aika kiranta se cewa khairii tayi ta qoshi tasha fresh milk,ganin haka Uncle say ya gano damuwa tashi ga wannan yasanya ya janyo wayarsa ya rubuta mata txt kamar haka "My love i swer idan bakizo munci abinci ba bazan ciba nima,kuma na tabbatar bazaki so Uncle say naki ya zauna da yunwa,plss kizo I LOVE YOU". Kasa dauke idanta tayi daga message din tana mamakin kalamansa har ya kuma turo wani jinta shiru "Baby na dagaske fushi kike sabida namiki shiru dazu,tsabar jin dadin kalamanki ne yake shirin sakani kuka a dazun,kuma inajin kunyar nayi kuka a gabanki amma trust me i love you more than words can tell,plss com and hav dinner together with ur fam" Tana murmushin jin dadi tazo dining d'in ta zauna amma me tarasa dalilin daya sanya matukar kunya ya hanata had'ata ido dashi har abincinma ta gagara ci se wasa takeyi da cokalin hannunta,wayarsa ya dauka ya rubuta mata "Meye hakan kunyan wa kike kuma? Yauba shagwab'a kenan" karayin k'asa tayi da kanta bayan ta karanta message d'in amma batayi replyin nashi ba,murmushi yankumayi yace cikin message "u go and get set,we r going for a date" murmushin dake qarawa fuskarta kyau ta d'ago tana masa cikeda qauna sannan a hankali bayan sun had'a ido ta sadda nata idon k'asa lokaci daya taji tana masifar jin nauyinsa kuma ya mata kwarjini,miqewa yayi kakarsa ta kallesa tace "Bakaci komaiba?" murmushi ya sakar mata "Nida hafsat zamuje yawo ne,bamasan mu qoshi danyawa a gida,murmushin tayi itama bata tankaba,tun dazu ta kula da yananyinsu ai yau taga sauyi sosai awurin dukkansu musamman Sayyeed dabaya iya d'auke idanshi akanta duk wani zumud'i yake ji...... A hanya yau hafsat gaba d'aya ta kasa sakin jikinta dashi,hannunta ya janyo yace "'Yan matan uncle say yadai niyau tsiwar nakesanji sa shagwab'ar" batayi magana kurun dai ta juyar da kanta d'ayan gefen tana murmushi,hannunta dake had'e da nasa ya matse sosai da sauri tashiga janye hannun ta saka wata qaramar qara,tace cikin shagwab'a "Nashiga uku Uncle say dazafi wlhy" sake hannun yayi yace yana dariya "gobe ma kya kuma mun banza idan ina miki magana" batace komai ba,shima shirun ya d'anyi,se can taje bayan ya wuce wani samosa joint "Uncle say onions samosa zanci" kallonta yayi yace "sekin cemun baby tukunna" zaro ido tayi tace "Haba mana Uncle sayyeed" murmushi ya sakar mata yace yana kallon dayan gefen alokacin dayake shan kwanar barin layin "Kinwa kanki sekince Baby say zan siya miki komai ma" Turo baki sannan ta sadda kanta kasa a hankali tace "Baby" dariyar mugunta ya saki sannan yakuma cewa "Cewa zakiyi,Baby say zanci onions samosa" Kara turo baki tayi batai magana na yace "Bazaki fada ba na qara gudu kinwa kanki kenan??" cikin muryan kuka tace "Baby say zanci onion samosa" parking yayi ya mayarda hankalinshi akanta,sannan yace "kinsan Allah hafsat ba wasa a zancena akan wannan yawan koke koken wlhy semunyi fad'a ke ko wasa aka miki se kinyi kuka,bazan ma qara miki wasa ba" D'agowa tayi tace tana share kwallan " Im so sorry Uncle say,bazan kara ba" cikin kuka tayi maganan ko yanzu,shi wlhy dariya ma ta basa,itafa komai qarantar abu kukane,kannewa yayi yace "Oya call me Baby say again" tana kukan tace "Baby say" yace "Noo cewa zakiyi I love u baby say" kallonshi takumayi sannan tace "I love you Baby say" ta fashe da kuka" jiyayy kamar ya rungumota amma ba hali,ya tabbatar cewar lallai jitai kamar yace ta maresa dayace setace masa baby,yasani tanajin nauyinsa amma wannan ita kadaice damar dazeyi amfani da ita ta saki jikinta dashi mastayin saurayi seya ganar da ita amfanin suturta jiki dakuma yawaita ibadar mahaliccii.... Da wannan yace "kiyi hakuri dear,bazan kuma sakaki kuka ba kinji?" daga masa kai tayi tace "Tokimun matashin murmushi mana,dariya tayi gaba daya hawaye shabe shabe a fuskarta tace " Uncle say a murmushin ma akwai matashine?" dariya ya saki shima "Ea mana bagashi kinyi ba?" suka saka dukkansu...... Mom Nu'aiym [2/4, 9:26 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                   19 Shammaz zaune a office d'insa duniyar habaki d'ayanta baqi take masa yarasa yazeyi akan zancen hafsat,sam mahaifinsa yaqi ya basa fuska,gaisuwar sa ma dak'yar yake amsawa,gashi gaba d'aya Haleemah ta gama rainashi zaman auren kawai sukeyi amma sam bajin dad'i har qasar take bari bada izininsa ba,yama rasa tayaya zeyi gashi dai hafsat yanzu kusan shekaru hudu da barinta qasar acewar Mommy ma takusa dawowa domin tace qasarta zata bautawa,amma duk inda yaje da zancenta ba sauqi har wurin hajiyar su wato kakarsa......     Sosai hafsat ta tara abubuwan burgewa ajikinta,yanzu batada wata damuwa ita da uncle say sambarka,duk da yabar qasar ya koma Niger amma koda wane lokaci suna maqale da juna awaya,sunyi wani sabo mara misaltuwa,kwance take acikin dakinsu tana karatun wani English novel me suna she's with me,khairii ce tashigo ta kalleta taja tsaki "Allah hafsa kin shiga ukunki kekam,wannan wane irin karatun jarabane kikeyi haka? Kinfasa tafiyarmu nanda kwana ukune, amma meye naki na tsayawa karatun wani banzan novel,kofa kayanki baki had'a ba wannan zumud'in na uncle say duk gulmane abaki kawai ya tsaya bekai zuciba" bata kula taba,kuma sarai tasani bawai kulatan zatayiba wannan ne ya sanya taja wani tsakin ta shiga had'a musu kayan har hafsat,se zumud'in ta takeyi ita kadai tana mitar san banza irin na hafsat.... *NIGERIA*       Gaba d'aya hafsat gani takeyi tamkar mutanen dake yanga akan jirgin basu san ciwon kansu ba,sakkowa ajirki sekace wanda ya tasa tray na samosa agaba,se yanga sukeyi tamkar basa taka qasa,tun a airport na sultan muhammadu maccido dake garin sokoto ta fahimci sauye sauye da dama da aka samu a garin,idon tane ya sauka akan masoyinta uncle say,shekara d'aya kenan rabon data ganshi,takowa tayi a hankali taje har gabansa ta tsaya ta sakar masa lallau san murmushi,kankace meye wannan kuma idonta ya cicciko ta soma kwallan murnar ganinsa,a hankali ta furta "i so much miss u Baby say" murmushin shima ya sakar mata sannan ya ja hannunta ya riqa cikeda kulawa yace "Rose kukan kuma na menene,daga had'uwarmu zaki fara ko Baby?" murmushinta ta fad'ad'a batare data dena zubar wahayen ba tace "Uncle say bakada labarin akwai hawayen dadi? sune nake zubarwa tsabar murnar ganinka" Janta yayi suka juya se mota,dama shi kadai yazo tarar su suka shiga suka wuce gidan abba haris kai tsaye,se labarin soyayya sukeyi cikeda qauna da tsananin murnar ganin junansu......    Satinsu daya agarin aka tsayarda ranar auren say da hafsat nanda watanni hudu masu zuwa,dama can tun tana india akayi tambayar auren kowa ma yasan da zancen auren. *Bayan kwana biyar*     Tun da hafsat ta dawo basu hadu da yaa shaam ba har yau,gwara ma matarsa sun had'u a gidan daddy,shi kuwa yana sani yake gujewa ganinta sabida gudun karya tayarwa kanshi cutar so da ta jima tana addabar zuciyarsa,yau dai seda ya kira qaninsa da safe ya sanar masa cewa suna gida sannan ya shirya zuwa gidan na daddy,bashida lamarin hafsat ta dauki al'adar waje bata fiya fitaba seda yamma,wannannya sanya ta zuro doguwar rigar jallabiya ja har qasa tasha shape da bakin mayafi da uban qaton madubin ido,lips dinnan sunsha red lipstick,a hankali take taunar cingam dake bakinta tana yamutsa fuska,yau sam setakeji tamkar batada lapiya driver din na parka wa tafito a yangace zuwa cikin gidan daddy cikeda yanga, A hot na gidan ta hango yaa shaam lokaci d'aya qirjin ta ya mugun dokawa,adu'a taci gaba da karantowa ta dauke kanta tamkar bata ganshi ba,murya ya d'aga yace "Hafsa zo zan" qirjin ne yaci gaba da mugun dokawa amma bata ko waigo ba, yi tayi tamkar bata jishiba, shikuwa ganin haka kuma yasan sarai tana jinsa ya sanya yayi saurin tasowa yafara takowa zuwa inda take,ita d'inma sauri ta qara amma ina kan ta isa kofar dazata sadata da cikin gidan ya rigata,tsayawa tayi cak ta runtse idonta ta sauke wata nannauyan ajiyan zuciya,a hankali cikin sanyin murya yace "Hafsat ya kwana biyu" bud'e idonta tayi a hankali batare da tayi magana ba,tana kallonshi ta cikin gilashin idonta,ya kuma cewa "Bazak gayarda yayan naki ba?" hannu ta saka ta zare madubin idonta sannan ta lumshe manya manyan ida nuwanta tace "Yaa shaam ina wuni,ya kwana biyu?" murmushi yayi shima hade da daura hannunsa saman qirjinsa yace "Lapiya qalau hafsat yaushe agarin?" murmushin itama tayi tace "Au baka masan zanzo ba aikuwan na cika tara,seka biya" wani dad'i ne ya xiyar cesa ganin ta sakko,besan kuwa nan umarnin yaa say kawai take bi ba abun beyi wani damuntaba,dak'yar ma take masa murmushin,shikuwa se dadi yake ji ya kalleta sosai "poojan dady an girma fa sosai yanzu" murmushin takumayi tace "yaa shaam d'in daddy kuwa ya zama tsoho tunda qanwarsa ta girma" Murmushi yayi ya shafi gefen fuskarsa "Ki shiga ciki yan matan Yaa shaam" wata dariya tayi me cikeda ka raina kanka ta wuce ciki kawai.... Tunda yaa shaam yaga hafsat na sakar masa fuska se kawai ya qudurta aranshi shine ze angwance da ita,da wannan har tunaninsa ya kaishi ga zuwa ya ziyarci Innah wato kakarsu ta wurin iyayensu maza.... Zama yayi ya saka mata uban kuka,akan wai ai asiri aka masa ada,yanzu kowa yasan yana san matarsa Amma abba haris dasu daddy sun hanashi sun baiwa wani har an saka rana nanda watanni hud'u,Innah kuwa tacika fam ta fusata,i da take shiga batanan take fita ba akan za'a hanawa magaji mata,aikam tana da rai basu isaba,da wannan tayi kiran kowa da kowa a gidan ta!!!! Kallonsu tayi bayan kowa ga natsa yana saurarenta tace dasu "Dama akan zancen hafsat ne da Magaji,tayaya dukkaninku kunsan airine yayi tasiri akan shi a wancan lokacin yanzu zece yanaso amayar masa da matarsa hankalinsa ya dawo jikinsa amma tsabar bakusan muhimmancin zumunci ba zaku rufe ido ku baiwa wani inada rai banma sani ba,to wlhy kunyi kadan kunji na gaya muku,na baiwa shaam auren hafsat tunda dama saku d'ayane a tsakaninsu,kuma na dawo ma da bikin wata me fita" kallonta Abba haris yayi cikin rudu yace "Innah dan Allah karki taso da wannan maganar yarinyar nan yanzu ta samu wanda takeso,kuma bazamu zamo qananun mutane ba munyi magana kuma mu dawo muce dasu wai amfasa,dan Allah ki rufa mana asiri maganar nan tunkan ta tashi daga nan mu barta" kanwar haris me binsa ma tasa baki kowa dai yayi magana tana jinsu seda duk suka gama sannan ta kallesu tace "Dukkaninku nan baku isa kun sauyan ra'ayi ba,sannan idan qaranta kuke gudu ni nan bana gudunta,ku sani wlhy ko yau na mutu duk wanda ya sauya wannan maganar tsakanina dashi Allah ya isa ban yafe ba" zaro ido sukayi dukkansu suka shiga lallami da ban baki,amma qememe tace dasu acikinsu ma wanda ya kuma tada zancen bata yafe ba,indai ba akan zancen bikin bane,kar wanda yazo mata dashi kuma kartaji sun sanar wa Alhj wato mahaifinsu" ai gaba d'aya mamaki ne ya damqe ilahirin su,suka silale d'aya bayan d'aya..... Mom Nu'aiym ce [2/6, 9:16 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 20 Zirga zirga abba haris keyi tamkar me ynqurin naquda,sam ya kasa gayawa hafsat meke tafiya gata durqushe a gabansa amma se gumi yake had'awa,kar yarunyar nan tayi tunanin cewar san kai yake mata akan d'ansa,ganin yayi shiru beyi magana ba ya sanya takuma cewa "Abbana gani" jikinsa ne yayi mugun mutuwa jin takirasa da abbanta, yasani hafsat duk gatan da mahaifinta keyi mata gani takeyi tamkar shine ya haifeta kuma yafi santa,hannu ya sanya ya rage zufar data tsatsafo masa a goshi sannan yace, "jeki ki dakko mayafinki kizo mu je wani wuri" dubanshi tayi haka kurun taji qirjinta na dokawa kuma kanta ya soma sara mata,jiki a mace ta miqe zuwa part nasu ta sako hijab a saman doguwan rigar atamfar dake jikinta tafito...... *A parlor daddy* Tunda hafsat ta ga kowa zaune har yaa shaam jikinta ya mata sanyi,gaba ki d'aya setaji wani iri,zama tayi yaukam ma akasan carpet ta gayar da kowa,kallonta daddy yayi yace "Hafsat ina fatan kin san cewar mu iyayenki ne kuma mun isa mu sakaki komai a yanda muke so muke kuma ganin ya dace?" kallon su tayi d'aya bayan d'aya sannan ta sauke idanta akan yaa shaam dayake ta faman murmurshi a hankali hawayenda suka taru mata tun farko suka silalo,ta gyad'a mar kai alamar gamsuwa da jawabinsa sannan yaci gaba "kuma kinsan cewar dukda muke iyaye a wurinku muma muna da iyayen dasuke sakamu abu adole koda bamaso se munyi shi?" nanma d'aga masa kai kurun tayi wannan lokacin kam tana kuka sosai,ganin yaa shaam na murmushi ta gano da babbar matsala,daddy yaci gaba "Innah ce da kanta tayi mana umarni akan lallai mu d'aura aurenki da shammaz nanda wata d'aya me zuwa,kuma idan d'ayanmu ya sauya wannan maganar ko bayan ranta bata yafe masa ba" qirjinta ya dad'a dokawa fiye da da,ta d'ago cikeda razani ta kalleshi,idonta ya kada yayi jajir yanzu kam tama kasa kukan se quna da zuciyarta keyi,miqewa tayi ranta a b'ace ta qarewa kowa kallo sannan ta kalli Abba haris tace cikin wata murya me d'aci wacce basu santa da ita ba "Abba na da gaske wai Innanku ne ta fad'a haka ba shiri bane wannan,na tabbatar kai kadaine zaka sanarmun zallar gaskiya" wasu yawu ya had'aya dak'yar masu d'acin gaske sannan yace dak'yar "Inna ce ta bada umarnin nan jiya hafsat" hijabinta ta gyarawa zama sannan tace " To yayi" Ta juya da gudu zuwa waje batare da tasan me yake damunta ba ko ina zataje ba,daddy da Abba haris ne suka bi bayanta,da gudunta suma haka a haka tafito daga gate d'in gidan tana kawowa kuwa wata motar na dannowa da gudun fanfalaqi atake tayi mata ebar karan mahaukaciya.......dafe kai sukayi dukkansu bame abunyi haka aka cillata acikin drainage dake gefen titin,abbah haris na kuka kamar wani yaro yaje ya fada ya cirota,sam babu alamun numfashi a tattare ita,ta sume mamallakin motar ma daya kasance matashin saurayi dan gayu fitowa yayi ya taya abba haris daukarta suka saka ta mota suka fada atare yaja da karfin gaske sukayi gaba,anan suka bar abba a tsaya ya kasa koda motsi sabida rudu,dakyar ya iya komawa ciki ya kallesu yace "Bana tunanin hafsat , Zata tashi,koda kuwa ta tashin bana tsammanin mata ingantacciyar rayuwa a yanda mota tayi mata wannan eban karan mahaukaciya ta cillata a gota" momy ce ta riga kowa miqewa jin kalamansa ta dage qirji "A ina wannan ya faru Alhj?" kallonta yayi da rinannun idanunsa yace "A kofar gida yanzu data fita da gudu,ina jiye mata idan ba ajali bane ya fitar da ita" zarewa momy tayi tayi waje da gudu shi kuma ya bita, dak'yar ya samu kanta tazo aka dunguma mota bayan sun kira abba ya sanar musu suna asibitin uduth wurin dr. Say....... Say yana zaune a office abba haris ya shigo masaa birkice,dakyar ya iya sanar masa mota ta kad'e hafsa tana waje,ai banke abban yayi ya fito da gudu,Trauma suka wuce kai tsaye da ita,babban tashin hankalin say be wuce ganin pause nata yayi qasa ba sosai,sannan gashi bata numfashi daidai abu mafi ban tsoro shine jininta dakeyin qasa sosai amaimakon ya hau,yaukam kasa yin komai yayi ya janyewa wasu likitocin suyi,har yamma suna kanta sedai ba sa'a,Dr. Shuraim ne yafito ya sameshi har iffice shida abba haris da daddy,suna ganin ya shigo suka tashi tsaye,kai tsaye wurin sayyed ya nufa ya dafa kafad'arshi,hannun nashi say yafara kallo sannan ya kalleshi da kyau,yace kafin shuraim yace wani abun "Dr. Shuraim karkace dani abunda nake tsammani?" kallonshi shuraim yayi cikeda tausaya wa,duk sunsan hafsat itace xe aura kuma yana matukar santa yace "To zaka ja da ikon Allah ne sayyeed?" kafin wani yace wani abun say ya sulale wurin a sume.... Mom Nua'iym [2/7, 9:14 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 21 Taimakon gaggawa suka bashi atake ya farfad'o,kallonshi Dr. D'in yayi yace "Haba sayyeed da kanka en uwanta kuma suce mana me?" kallon mamaki yake masa sannan yace "Allah yasanya mafarki nakeyi" murmushi Dr. d'in yayi yace "Ya zakayi da ikon Allah akanta to? Arziqinmu d'aya ma karayar iya hannu ne,se buguwa datayi aka,wanda wannan shine yake san bamu matsala sabida dama akwai wannan matsalar damuwa na d'aya idanta" sauke ajiyar zuciya yayi sannan yace "Indai da ranta komai yazo mana da sauqi ai,indai inada rai da yardar Allah da izininsa seta samu lapiya" ahaka suka dunguma dunkansu dakin da take.......tunda hafsat taji likita awa su daddy bayanin cewar idantane suke tunani adawo baya kuma idan ya samu matsala lallai wannan karon gyaruwanshi se Allah,amma dai bazasukai karshen maganar ba seta farfad'o idan har bata gani da matsala idan kuma tana ganin komai to wannan daidaine,hankalinta ne ya tashi amna bata nuna ta farka ba hasalima ko motsin kirki batayi ba daga kwanciyar datake,har suka fita aka barta ita kadai,da sauri ta bud'e idon nata tana ganin hasken fitila da komai sannan ta sauke ajiyar zuciya had'e da tunano abinda ya faru,dukda tanajin azabar d'aurin da aka yiwa hannunta seta samu kanta da murmushi,ita kadai tasan ma'anar sa kuwa........ Washe gari hafsa ta farka amma qememe tanuna bata gani,wannan abun ya tashi hankalin sayyeed musamman dayake ya sani yanzu kam da matsala tunda shine na biyu,agaban su daddy sanda yayi kuka sosai yana me mata adu'a,shaam kuwa koda Dr. Shuraim yamasa bayani kasa cewa komai yayi gaba ki daya jikinsa ya masa sanyi,dana sanin abubuwa da dama ya farayi ciki kuwa hadda zuwa ya ziyarci Innah,yana ganin dayabi abun a hankali da duk haka bata zo ta faru ba,jan jikinsa yayi zuwa kofar dakin da hafsa take ciki,a hankali ya tura ya shiga ganin ba kowa ita kuma tamkar me bacci ya sanya ya matsa kusa da ita ya kurawa fuskarta ido dayake da tabbacin lallai dabeyi yunkurin tarwatsa farin cikinta ba da duk hakan bata faru ba,da fuskarta bata kumbura har haka ba,da yanzu tana gani yanda kowa ke gani da yanzu hannunta be karye ba lapiyanshi qalau,da yanzu bata kwance a wannan asibitin, dafe kanshi yayi ya furta a sarati cikin muryar kuka "Mesa arayuwa ni shammaz na cika san kaina da yawa? Mesa zan wulaqanta jinina kuma yarinyar data zab'i zama dani ta sadaukar da farin cikinta akaina? Mesa zan sakaki a had'ari hafsat? Mesa tunda kika fara girma kika san meye so kika fara dani nake kuma kan wulaqanta miki rayuwa? Tunda kikace kina sona nake qasaki ta hanyoyi daban daban,Allah kuwan Allah ze barni kuwa? Zan iya jin dadin rayuwa bayan haqqinki na saman kaina?" fashewa yayi da kuka awurin cikeda ban tausayi sam sam bayasan abunda ze tashi hankalin hafsat yanzu,ita kuwa duk wani abinda yaje fada a kunnenta yake fad'a sedai tana d'aukar kalamanshi cikeda yaudara mara misaltuwa,sam bata yarda dashi musamman a wannan gab'ar data nemi san datake msa ta rasa gaba d'aya........ Uncle sayyeed ne yazo dakinta da dare ba kowa se ita kad'ai,ta rufe idonta ruf tamkar me bacci zama yayi a kusa da ita ya kura mata ido ba tare da yayi magana ba,taji kamshin turarensa wannan ya sanya ta bud'e idanta a hankali,tabbatarwa kanta tayi da cewar shi kadaine ya sanya ta sauke masa su,cikeda tsoro yankalleta dakyau murmushi ta sakar masa tace "Uncle baby,wannan ita kad'aice hanyar dazanbi in raba kaina da shammaz,na tabbatar a yanda nake nakasasshiya baze aureni ba,nakuma sn bakada labarin cewar Innah ta sokoto ta rantse sena auri shammaz kota tsinewa sundaddy, banje mota ya kadeni da gangan ba,amma jin cewar idona idan na farfado yana a rufe baze taba budewa ba ya sanya naji gaba daya na samu mafita,karka sanar da kowa se bayan aure na dakai" murmushi yayi yace a sarari "Alhamdulillah,amma hafsat kya baiwa kanki wahala duk akaina? , Zama a matsayin makauniya anya ba wahalar da kanki bane" murmushi ta masa "Uncle sayyeed banida burin daya wuce na ganni a tare dakai,babu abu mafi soyuwa agarareni daya wuce na zamto mata agareka,babu abu mafi bani kwanciyar hankali illah in ganni kusa dakai kusanci mafi dad'i acikin kusance kusance,dan Allah ka tayani cimma wannan burin nawa" murmushi ya sakar mata yace "Babu damuwa Babyn ubcle say,Allah ya baki lapiya amma kin kware a pretending" dariya tayi sannan tace "Kaina yana masifar yimun ciwo,da kuma hannun nan,ni samosa zanci" dariya ya kwashe dashi jin excuse nata nasan cin samosa yace "Madam ina zan samo miki samosa yanzu?" turo bakin tayi "Ni koma a inane" To naji barinje season seven su dama 24hrs service sukeyi" bata ce dashi komai ba ya miqe yayi waje..... Shammaz kuwa ya kasa bacci,ga haleema zaune a kusa dashi amma sam yama manta danita,ita kuwa se hotuna take faman dauka tana sakawa a snap gashi batada maraba da tsirarara,kallonshi ta d'anyi a kaikaice tace dashi "Shaam lapiya nka kuwa ?" dan waigowa yayi ta gefenta ya marairaice "Hafsat ne tayi accident shekarnjiya fa,kuma idonta ya kuma rufewa gashi babu chance yanzu sabida shine na biyu,ya kamata kije ki duba ta" tsaki taja "Yo sabida nakasasshiya ta qara naqashewa shine kwana biyu duk ka canja,Allah ma yasanya ta zama gurguwa a had'a mata double" kallon mamaki ya mata sannan kamar ya maketa yace "Tsabar ba Allah a ranki zakiwa yar uwata kuma jinina mugun fata har haka?" "mtsww aikin banza,ai inada labarin accident din biris dai na maka wai kare ya taka sisi,in banda rainin wayau akan kanaso ka auri wannan karuwar zataje ta kara mota ya kadeta,kaji na rantse ba inda zani,kuma ka sani wlhu idan kace zakamun kishiya sena yanka tsuliyar uban kowa ma ya huta" tana kaiwa nan tayi waje,dama ya zama mujin hajiya se shiru yayi,shi yanzu damuwarsa lapiyar hafsat...... Muhammad Jalalludden Auwal,shine mutumin daya kade hafsat shekarnjiya,yaune kuma yake shirin zuwa lapiyarta domin tunda ya baro asibiti be koma ba sabida ayyuka sun sha kanshi,sanye yake da babbar rigar farar shadda dinkin sufani yasha kyau,gabaki dayanshi komai na jikinsa fari ne kaikace shirin zuwa qabari yakeyi, hatta hanky daya tiqe fari ne,agogon hannunsa ma haka haka ya taka yace asibiti,hadaddiyar mercedese benz dinsa ya parka a harabar asibitin ya fito yana tafiya irin ta manyan mutane dududu shekarunsa bazasu wuce 37 ba aduniya amma gabaki daya manyance ya masa yawa,ga uban kwarjini daya keda koda ya fito acikin motar kowa qura masa ido yayi,a yangace ya isa kofar dakin dayake tabbacin nanne,a hankali ya tura kofar ya shiga da sallamar sa,momy ce zaune kusa da ita tana ganinsa ta miqe suka gaisa sedai bata shaidasa ba,sabidanita basu hadu ba ranar,murmushi yayi yace "Mama nine wanda na kade hafsa,nazone in duba lapiyarta sabida gobe zan bar qasar,kuyi hakuri banzoba kwana biyu ayyukane suka sha kaina" kallonsa hafsat tayi da qasan idonta ta dauke kanta lokaci daya,gaisawa sukayi da mama sannan ta masa godiya sosai "Mama yanzu menene matsalar hafsat?" sadda kanta tayi tashiga rero masa tundaga matsalar farko data samu har zuwa wannan akan rashin ido,taqarashe sanar dashi cikin kuka sosai, girgiza kanshi yayi cikeda damuwa yace bayan ya zare madubin dake fuskarsa ya shafi idonsa "Bazan yadda cewar idon baze bude ba sedai idan basu san kan aikinsu ba,akwai likitana dake a china,a can zamu da ita,idan mahaifanta zasu yarda zan dauki nauyin komai na aikin da tafiyar" shiru momy tayi hafsa ce tace "Niba inda zani,ku barni anan kawai Allah ze bani lapiya" kallonta yayi yace cikin fada "Hafsat idan kika kuma saka bakinki amaganar manya sena sassa b'a miki wlhy" tsoronsa ne ya darsu aranta lokaci daya,tanajin tsoron ayi tafiyar aje garin gyara ayi barna,tunda lapiya ta qalau,amma dai bata kuma cewa komai ba" sallama ya musu akan zece wurin su daddy da kanshi,yana fito wa ya hadu da shammaz,kallon kallo suka tsaya yiwa juna sannan ba tare da sunwa juna magana ba suka raba kowa ya wuce Hmmmmm toophaa ga oga muhammad ya iso Mom Nu'aiym [2/8, 8:47 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 22 Tunda hafsat taji zancen zuwa china se tafara tsoron tafiyar,lallai idan har ta kuskura akayi tafiyar nan tofa se an ce za'a yi mata aikin,kuma lallai garin neman gira rashin idone ze biyo baya,tana kwance tayi shiru uncle say ya turo kofar dakin ya shigo da sallamar sa,yunkurawa tayi ta tashi zaune sabida yanayin hannunta da har yanzu da sauransa ta tashi zaune,kura mata ido yayi yana murmushi sun dad'e sosai suna hirar su ta masoya kan ya mata sallama harya kai kofa ya juyo ya kalleta,murmushi ta sakar masa tace "Uncle say yau nakula ka nacewa kallona lafiya dai?" girgiza mata kanshi yayi "Ai dama can kinsan ni sam bana gajiyawa da kallon kyakyawar fuskar nan taki" lumshe idanta tayi cikin sanyin murya tace "Nima haka baby say" batare dayayi magana ba ya juya sanye da murmushi a fuskarsa, gabaki d'aya wani tsoro ne yakeji da yawaitar fad'uwar gaba yarasa dalili seyakeji gabaki daya duniyar tana juya masa.... Shaam zaune yana dannan wayanshi a farfajiyar shan iska dake cikin gidansa haleemah tazo ta sameshi,cikeda rashin mutunci tace dashi "Wai kaikam me kake nufi dani tunda qanwar ka ta qara zama naqashashiya kake wani shamun mur sekace nice nan na nakasata?" dagowa yayi ya kalleta yace "Me kuma ya kawo maganar hafsat anan?kuma ban sanar miki cewar kidena ce mata naqasashiya ba?" tsaki taja "Meye laifina danna kirata da sunan dayafi dacewa da ita? Wlhy akan hafsat zan baka mamaki" "Kya daiji dashi,amma ki sani wlhy sena aureta a nakashen,ni tazo ma ta haifamun yara tunda kin zama juya,narasa me kika dauki duniya dabazaki haihu ba hakanan,shasha kawai me bakin hali" a fusace ta furta "Kafi kowa sanin cewar niba juya bace tunda na haifa maka ya qanwarka ta kashe,kuma ka sani wlhy koba hafsa ba indai banice zan haifa maka yara ba kaida haihuwa har gaban abada kuwa" tsaki yaja ya miqe yabarta gun a tsaye...... Tunda haleema taji zancen auren hafsat da say zeyi seta tashi hankalinta ta sani sarai boka ya sanar mata ba ita ba haihuwa har abada sannan kuma gashi yanzu sam asiri ya dena tasiri akan sa,bokansu ya sanar musu sun sanar mata cewar lallai ya riqe addininsa yafi karfinsu ko kusantar sa ma gaba daya bazasu iyaba, wurin ummansu taje ta zayyane mata komai atake kuwa aka shirya cewan ayi airin akan hafsat gaba daya tunda itace banza.....hmmmmm Say yana zaune tare da hafsat suna hira muhammad ya shigo cikeda taqama yaud'inma acikin shigarsa ta shadda fara amma ba babbar riga bace, yau dinkine dai na zamani me kyau komai nasa fari,hannu ya miqa masa suka gaisa sannan ya mayarda dubansa akan hafsat da alokaci daya qirjinta ya soma dokawa "Hafsat ya jikin ki?" kallon sa tayi tace "Naji sauqi Alhamdulillah" shiru sukayi dukansu su uku can muhammad yace "Ke baki iya gaisuwa bane,ko bakisan girman manya bane?" idon tane ya ciciko sannan tace "Kayi hakuri yaa muhammad" dan guntun tsaki yaja sannan yace "Mesa zakiyi karyan bakya gani kuma bayan sarai idanki lapiyanshi qalau,bayan yanzu gashinan kina kallo na kuma kallo daya na miki na tabbatar kina gani kema kuma kina kallo na ido cikin ido duk sanda nayi magana" shiru tayi yayinda say ya miqe tsaye yace "Amma yallabai anya bakayi shishigi da yawa ba kuwa,baka ganin cewar mu doctors mune mukeda haqqin komai nata bawai kaiba,kuma mun tabbatar cewar idan nata bashida lapiya kai miye naka aciki? Kuma idan taimakonta zakayi mu bawai mun kasa bane ka barshi kawai mune family nata zamu mata komai ma har fita wajen" shiru ne ya ratsa wurin dukkansu sun bata dakiku suna kallon juna kafin muhammad yace "mesa arayuwa zaka kalli girma na kace zaka kirb'a mun k'arya,zanyi magana a d'aga licence dinka na zama likita idan dai har tsabar hauka wannan idan ne zaka ce baya gani" jin ankira hauka ya sanya say ya dago da fuskarsa gaba daya cikeda fusata "Kai waye? Mekake taqama dashi? Me kuma kakejin ka isa kayi da zaka kalli tsabar idona kace dani mahaukaci,dakake iqirarin cewar zaka sanya akarbe license dina mesa kai bazaka qwace ba idan ka isa,tunda nake ganin mahaukata bantaba ganin mara hankali irin kaba,tayaya zaka kalli idan mutum kace masa mahaukaci beside waye ma ya baka damar yi mana iko anan?" wani murmushin qasaita yayi sannan ya shafi gemunsa yace "Ba license d'inka ba har abu mafi muhimmanci arayuwarka zan iya kwace wa shine rayuwarka,kuma wlhy kaf fadin Nigeria ba wanda ya isa yamun komai,kuma zaka gani wlhy,ke kuma karna dawo asibitin baki gayawa doctors masu hankali kina gani dakyau ba" yana gama fad'ar hakan ya juya ya fita hafsat ta kasa koda motsi dakyar ta hadiye wasu yawu sannan ta furta "kayi hakuri uncle say ka rabu dashi,wannan mutumin na tsaneshi wlhy" matsowa yayi kusa da ita yace "Mesa nakejin matukar tsoro da yawaitar fad'uwar gaba hafsat? Gabaki daya banjin dadin tawa rayuwar sekace nine nake ciwo,wlhy hafsat hankalina baya kwance,bawai wannan muhammad dinba da kalamansa aa, komai ma senake ga kamar mutuwa zanyi ayanda nakejin duniyar tanamun qunci" zare idanta tayi waje "Haba Uncle sayyeed? Ya kake magana haka? Inshaa Allah atare zamu rayu babu abunda ze sameka,kuma inshaa Allah atare zamu mutu" murmushi ya sakar mata yace "Zanje gida na dawo nanba jimawa inshaa Allah" batayi magana ba haka yaja kofar ya fita, ita dinma dai haka kawai takejin tsananin faduwar gaba me tsanani,hankalinta sam baya jikinta,koda momy tazo bayan isha abinci kurin tabata sukayi sallah seta kwanta,say yazo sun dan taba hira,wuraren karfe tara yamata sallama akan seda safe ze dawo,har kuma ze fita ya dawo ya kalketa yace "Hafsat idan har Allah yasanya wani abun yafaru dani kimin adu'a ita kadaice nake buqata agareki" kura masa ido tayi dukta rude murya na rawa ta furta " mesa kake irin wannan tunanin wai? Sabida kawai wannan muhammad din yayi wannan furucin seka damu,inshaa Allah ba abunda ze iya yi maka" murmushi ya sakar mata "Hafsa nafasan waye muhammad,sam yayi furucin dayayi ne sabida kawai ransa ya b'aci amma mutum ne me nagarta sosai,matsalar sa d'aya kafirar zuciya da rashin human relation amma hes a nice person" shiru ta masa kawai amma bawai danta yarda ba,tanaso ta tsani muhammad dinnan amma zuciyarta taqi aminta da tsanar tasan...... Wuraren sha dayan dare unle say ya dawo wurin hafsat,zama yayi kusa da ita yamata a dua lokacin tamayi bacci sannan ya kashe fitilar dakin ya fito ganin ko momy bacci ya kwashe ta batare data kashe fitilar ba,yana barin dakin ya kula da mutumin daya wuce part din fuskarsa a rufe da mask se suaune kansa yakeyi,harya wuce kuma seyakasa nutsuwa ya dawo baya gaba daya,binsa yayi yaga lallai dakin ya dosa,ya murda sad'af sad'af ya shige aikam say da sauri ya biyo bayansa shima yafada dakin,ganin yayi mutumin ya dauki filo ya danne fuskar hafsa se shura kafa takeyi acikin duhun dakin,kuka kura yayi yayi kanshi aikam fada ya kaure har suka tashi momy,da sauri ta haska torch light dinta tana ganin haka ta kunna fitilar dakin kokawa suke sosai da sauri ta kwallah kara,amma kan wani ya farga kasancewar darene har mutuminnan ya daga wuqa ya cakawa uncle say a qahon zuci har wurare biyu......ko kafin mutane su zo wancan mutumin ya gudu,hafsat ma ta farka tuni sakkowa tayi tama manta zancen karaya,sayyeed kuwa tuni rayuwa tayi halinta,se kuka takeyi tamkar ranta ze fita a haka doctors dake nan sukaxo,kowa se hawaye yakeyi ana fadar mutuwarsa .... Mom nuaiym [2/9, 8:55 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 23 Ba shakka hafsat ta gama haukacewa da mutuwar uncle say,tsakani da Allah tanki tana gani aka fita da gawarsa wanda ko ba'a gaya mata ba ta tabbatar wlhy ya mutu,ko dan ganin jinin daya zuba ajikinsa, kasa zama tayi asibiti dole aka wuce da ita gidansu.......tunda hafsa taje gida take kuka ba qaqqautawa shi kanshi shaam din ya girgiza da mutuwar sayyeed,musamman da yake ko a dakin da hafsat take aka kashe shi,kuma ita bata gane wanda ya danne mata fuska ba da filo,kasancewar acikin dubu ne farkawar momy ne ta ga sayyeed..... Da yamma yan sanda sukazo gunsu da tambayoyi kallon ta sukayi bayan ta momy ta gama fadar iya abunda ta sani suka ce da hafsat "Hafsat dukda yake munsha mamakin ance kinada matsalar ido,amma se gashi faruwar abinnan idon naki ya bude,muna san sanin shin sanda abun ya faru kina ganine? Ko kuma aa bayan faruwar abun kika soma gani" kallon dan sandan tayi gaba daya gani tayi ya gama raina mata idan dai har karatun datayi na lauya harta zama qwararriya ba shirme bane a yanda ta fahimci kalamansa zarkin nasa akanta ya fara shi "Tun ranar danayi a hatsari na farfado komai ina ganinsa lapiya lau" gyaran zamansa yayi ya kalleta sannan yace "To meyasanya likitoci sukace bakya gani,kema kuma kike ta faman pretending?" kallonshi tayi shima sanda ya razana da kallon sannan tace.."Banasan auren yaa shaam,shikuwa so yake na aureshi sabida wata manufa tashi da ban santa ba,nakuma san ba dan Allah bane da wannan yaje ya sanya kakanmu tace dole sena aureshi,ranar dana samu accident ranar naji doctor yana wa su daddy bayanin cewar idan har na farfado idona ya sake tabuwa baze gyaruba,kasancewar shine na biyu,daganan dabara tazomun ta nunawa duniya cewar bana gani sabida nasan yaa shammaz baze aureniba ina naqasashiya,uncle say da abokinsa Dr.shuraim sunsan ina gani tangaram dama shirine se bayan na auri zabina sannan kowa yasan ina gani clear" nisawa kowa dake wurin yayi ganin tana fad'ar gaskiar ta kai tsaye,police din ya sake cewa "Menene zaki iya tuna ya faru a daren jiya?" hawayen daya gangaro mata ta saka hannunta ta share sannan tace " Kawai dai nasan munyi sallama da uncle say tun karfe tara na dare akan se washe gari,daganan yana fita na kwanta nayi bacci,acikin baccin ne naji an sakamun pillow a danne mun fuska sosai bana iya numfashi,can kuma sena ji an sakeni na sanya hannuna da ke lapiya na janye pillow din amma sabida yanayin dakin ba wadatar haske banga komai ba seda momy ta farka ta haska torchlight jin hayaniya,ananne naga uncle say da wannan mutumin me mask a fuska suna kokawa,harya caka masa wukar,kuma kan momy tayi wani yunkuri mutumin ya fita da gudu,amma fa ni naga face d'insa asanda uncle yaji azabar ya caka masa wuqa ya da damko face mask din wacce ina saran tana hannunku" nisawa police din yayi yace "mungode da amsoshinki kai tsaye,dakuma hadin kai,muna fatar idan muka dawo zamu samu hadin kanki idan buqatar hakan ya taso" a fusace ta miqe tace "Sabida yana da kudi? Ko sabida yana taqama da isa dacewar shidin wanine ze kashe mun muji ya zauna lapiya,ku sani akwai sadakin sayyees akaina wanda yake nuni ya kuma isa hujjar kasancewata matarsa sabida haka wlhy sena ga karshen shari'ar nan,matsayi na na cikakkiyar lauya nice zanyi bincike me ma'ana idan har ku bazakuyi ba" cikeda rashin fahimta suka kalli juna sannan dayan yace "Ban gmfahim ceki ba?" atake ta zayyane musu abubuwan dasuka faru tsakanin muhammad da sayyeed da kuma furucin muhammad ta qara da cewar "A shari'ance muhammad ya aikata babban kuskura furta wannan kalamin kawai balanta na yakai ga aikatawa,nice zan sameshi da nawa tuhumar nice zan bincikeshi dan kaina ina ikon tsayawa kaina nima din cikakkiyar lauya ce meji da kanta" kallonta mutumin yakumayi yacewa "haj amma ina ganin kamar Barrister muhammad kike magana ko?,a iya sanina dai shine mutumin da akace ya kade ki,kuma babban lauya ne da ake fafatawa dashi a fadin kasar nan gaba daya" tsaki taja ta sanya hannunta me lapiya ta bubbuga kirjinta "Sabida yana taqamar shi babban lauyane seya kashe mutum? To nima babbat lauyace ta kaina,kuma wlhy senabi jinin mijina" shiru sukayi ganin yarinyar nacikin zafin mutuwar.... *Bayan kwana uku* Shirin ta tayi tsaf kasancewar mahaifinta yamata komai na lauya me zaman kanta bata gwamnati ba,domin kare haqqin sayyeed daya mutu akanta,kai tsaye gidan Barrister muhammad jalalludeen Auwal yana zaune a harabar gidansa yana kurbar lemo a hankali cikeda yanga,dama kuma yasan da zuwanta kuma police ma sunzo sunyi nasu har sun wuce,har a news paper an sanya tuhimarsa da yake wanda wannan ko kadan be daga masa hankali ba sam sabida yasan meya taka hmmmm.....A yangace ta fito daga cikin motar zuwa inda yake zaune shi kuwa tun daga nesa yake kallonta yana wani murmushin kin rainawa kanki hankali,Tana zuwa ya miqe tsaye sinfi mintuna biyu suna kallon juna,hannu ya miqa mata,sanda tabi hannun nashi da kallo sannan a wulaknace ta miqa masa nata yace cikin muryarsa me tarwatsa littafinta "Bar.muhammad j Auwal AkA j.A" murmushi tasaki me ban haushi ta furta a yangace "Bar. Hafsat muhammad gaya AKA Miss poojah" murmushi ya sake meban dariya "Nice meeting u young barrister" "Nice meeting u too the oldest one" murmushin ya sakeyi tace "ina fatan kasamu labarin suing naka damuka yi a court,ina kuma fatan ka nemi qwararren lauya macecinka" juice ya dauko ya kurba sannan ya zauna ya kalleta ya nuna mata da hannu kujera "Have a sit miss poojah" zama tayi ta dauki cup na juice da hannunta me lapiya ta kurba sannan ta kai dubanta zuwa gareshi tace "Bakace komai ba" sanda yaja numfashi sannan yace "Hafsat lallai kin dakkowa kanki abunda bazaki iya karasawa ina so ki sani bakin rijiya fa ba wurin wasan makaho bane,ni dinnan nafi karfin tunanin ki wlhy"Murmushi tayi har haqwaranta suka bayyana sannan tace "Tabbas zancenka dutse ne Br. J.A,Amma ina san ka sani wlhy bazan saurara maka ba harse naga bayanka" cup dinshi ya dire akan table yace cikin nutsuwa batare daya kalli inda take ba "Miss poojah courage dinki yana burgeni sosai,abinda nakeso dake shine wannan fafatwar tamu ta zama deal" kallonshi tayi ta kauda kanta gefe batayi magana ba yace "Idan har kikayi wining case dinnan zan karbi hukuncin kisa kuma zan mallakamiki daukacin dukiyar dana mallaka fiye da rabinta zan baki,dukkanin abubuwan dana gada awurin mahaifina kuwa kashi uku zan masa in baki kashi biyu in yarona daya tilo dayan kashin,idan kuwa har nine nayi wining wannan case to kuwa ko kina so ko bakyaso sekin aureni" da sauri ta dago ta kalleshi taga shidin ba ita yake kallo ba,sai saita kanta tayi ganin deal din ba wani babba bane kasancewar tanada yaqinin shi yayi kisan kuma zata diddigo abun,tace "Na amince da wannan kuma zanyi" ta miqe kallonta yayi yace "Bakida wayo,shiyasanya nace dake bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane ai,an tab'a deal ba'a rubuceba idan na cuceki fa? Zama zakiyi mu rubuta muyi sighning inada photocophy machine se nabaki copy daya nima na ajiye dayan kuma ke zan baiwa orijinal ma" yafada yana murmushi kauda kanta gefe tayi sannan ta zauna amma sam bata karayaba,sanda suka gama komai sannan ya miqa mata hannu yace "Deal?" murmushin yaqe ta masa tace "Deal" daganan ta karba ta juya yace "Semun hadu a court poor poojah" juyowa tayi ta washe masa baki sannan tayi gaba abunta ta shige mota sukayi gaba,ya koma ya zauna yace "Smart poojah". Toophaaa jama'a wasa farin girki yanzu ake book kam,yanzu race ya fara. Idan kaji dadin wannan page dan Allah comment and vote..... [2/10, 10:05 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                       24 Tunda hafsat ta koma gida take nazarin abubuwan da suka shiga tsakaninta da J.A sam bata ankare da wautar data aikata ba se yanzu,idan ya kasance shi yayi wining na case din fa? Ko kuma ya kasance ba shi bane yayi kisan fa?" wani tsoro ne ya shigeta lokaci d'aya qirjinta ya soma wani irin dokawa,dafe kanta tayi ta shiga rero adu'o i kala kala na tsari.....    Brr. J.A kuwa  bayan fitar hafsat a fusace shima ya fita,be tsaya ko ina ba se asibitin uduth kai tsaye wurin masu bada katin shiga wurin ya nufa bayan sun gaisa ya nuna musu ID card d'insa sannan yace "Nazo bincike ne akan wani case na murder da aka samu anan asibitin kwanakin baya,ina matukar buqatar had'in kanku domin tallafawa family d'in wannan babban rashin ba bisa haqqi ba,nima kuma da ake zargi ku taimakamun matsayin na na baban lauya me matsayi ace ana zargina da kisan kai" sosai suka fahimce shi dama mutane da dama sun dad'e da qaryata zancen zargin da ake masa kasancewar mutane da dama sunsan halinsa na nagarta, babban cikinsu yace "Wane taimakao kakeso mu maka yallab'ai?" gyaran zaman madubinsa yayi sannan yace "Record nakeso na dukkanin motocin dasuka shigo asibitin nan aranar 11/11/2016 tunda shabiyun daren shigar ranar har zuwa shabiyun daren wucewar ranar,na kuma san kunada cctv camera anan so idan ba damuwa ina buqatar video d'in" gyaran zama ogan nasu yayi sannan yace dashi "Dama plate number ne muke d'auka mubaka card na shiga,se kuma sunan motar da color dinta da model number na motar,cctv kuwa yana daukar shiga da fice na kowa a asibitin nan,sabida haka yallab'ai komai daya dace zamu baka inshaa Allah" godiya ya masa sannan yashiga tattare muhimman informations da aka lokaci daya ya harbo bakin zaren......... Shammaz kuwa tunda abun yafaru yakejin wani tausayin hafsat,a qasan zuciyarsa kuwa yanajin wani iri tamkar laifin sane komai,zuwa yayi ya samu haj Innah ya sanar mata yafasa auren hafsat baya santa kuma ta janye qudirinta,dama ita tunda taji cewar sabida auren sa da aka ambata hafsat ta gigice harta samu hatsari ta kudurta aranta bazata qara wannan furucinba kuma idan ma hafsat taji sauqi zatace abata zab'inta,shi kenan kuwa ta amince wa shaam akan ya gayawa iyayensu...... *Court*         Hafsat ce a zaune tare da lauyan me kare J.A se wasu lauyoyin guda biyu,acikin babban court dake jihar sokoto,Justice d'inne ya rero bayanin zargin da akewa Brr. J.A tare da baiwa masu qara damar bayyana hujjojinsu daya sanya suke zarkin sa da kashe likitan,batare da bata lokaci ba hafsat ta zayyane komai daya faru agabanta ta qara da cewar "Furucin sa kad'ai ya isa ya nuna mana cewar shine yayi kisannan" dayan lauya din me kare wanda ake qara ne ya miqe yace "Objection my load" kallon sa justice din yayi shikuwa yaci gaba "my load be kamata lauyan wanda suke qara ya riqa alaqanta laifin kisan kai kacokam ga wanda ake zargi ba,tunda ai zargin sa ake bawai an tabbatar ba" justice ya kalli hafsat yace "A kiyaye" ya sake kallon Brr. Khaleed yace " yallab'ai zamu so akara mana lokaci kadan domin gabatar da shedunmu kuma zasu so a gayyato mana babban Abokin marigayin anan wato Dr. Shuraim" dama aka basu daganan aka d'age zaman sena da sati d'aya. *Bayan sati d'aya*      Lauyan wanda ake qara ne yace fara magana kamar haka "My load wannan gabaki d'aya record ne na motocin dasuka shiga asibitin ranar da abun ya faru,acikin mun samu mota iri daya kirar honda civic kalar ja wacce aranar tashiga asibitin kusan 7 times a wannan ranar cctv camera ta main gate data ward din da akayi kisan duk sun tabbatar mana da shigar mamalakin motar so bakwai a wunin ranar, kuma duk shigar sa kai tsaye ward d'in yake nufa wato inda sin din ya faru kuma mayannin dayayi duka ba face mask a fuskarsa se ziyartarsa ta karshe inda har yayi nasarar hallakar da sayyeed,sannan kuma a binciken da muka gabatar,makashin yaje kashe hafsat ne ita kadai bawai da sayyeed,sabida sayyeed ba asibiti bane gidansa,kuma idan ma kasheshi zeyi sedai yaje gidansa ya kashesa acan,abinda muka sani shine sayyeed taimako yaje a yanda muka gani a camera shine harya fito ya ganshi ya shiga seya bisa a baya,abinda camera ta kasa nuna mana shine menene ya soma faruwa acikin dakin kasancewar babu wadatuwar haske ya sanya se bayan yayi kisan ya juya ze fita haske ya wadata kuma har fuskarsa mun gani,abunda masu qara sukace wanda yaje kisan hafsat itace wacce yafara dosawa pillow a fuska kafin sayyeed ya cece ta,idan ko har hakane furucin da muhammad yayi sam bashida alaqa da wannan kisan na sayyeed" shiru yayi hafsat gaba daya kanta ya daure sabida batayi wannan tunanin ba shi kuwa yaci gaba "Munyi nasarar cafke wanda yayi kisan,kuma munaso yazo nan da bakin sa yayi bayanin wanda ya sakashi kisan idan har kotu ta bamu damar yin hakan" izini. Aka basu akan su gabatar da mutumin......koda alqali ya tambayi mutumin seya fara bayani kamar haka "Da farko dai sunana kamilu,kuma ni dan area boy ne ina zamane a unguwar iraqi dake cikin garin sokoto,ina zama wani likita me suna shuraim yazo ya sameni akan yanaso in masa aiki akan wata mara lapiya me suna hafsat,ni kuwa dama ba ruwana aiki ko wane irine indai na kudine to kuwa zan yishi yabani details na komai da komai na dakin datake da time da babu yawaitar mutane awurin yakuma ce na danneta da pillow sabida gudun zargi ganin zan samu kudi ya sanya na amsa tayinsa naje nagama monitoring na wurin da komai,nashirya rana daya naje,shine qaddara ya fadowa wanda yazo tare fadan na kasheshi da wuqa ta,shine wayannan suka bi ta hanyar kotar danake hawa suka kamoni" jinjina kai kowa keyi yayinda hafsat ta rikice tabbas wannan shine mutumin data gani kuwa,dama sun buqaci ganin shuraim shi kuwa be karaji daga wurin wannan mutuminba so bezata hakan zata faru ba,koda aka buqaci yazo beyi gaddama yazo a rude ,tambayar sa akayi dalilin san kashe hafsat baiwar Allah yafara magana kamar haka "Na kasance ina matukar san yarinyar tun tana secondry schoool amma ta wulakantani,har kuka nake mata amma bata damu dani ba,ganin nayi nayi taqi kulani yasanya nashiga malamai na sanya duk wani namiji idan ya kalleta zeji yana matukar tsanarta idan kuwa me riqon addinine yafara santa semu saka masa mafarkai na tsoro akan zamu kashe duka su biyun harse yagaji ya kyaleta,kwatsam mukazo asirinmu damuke mata ya dena tasiri bincike ya nuna mata an mata magani kuma turarukan datake using ba wani aljanin daze iya rab'ar inda take ma, da wannan naji zuciyata tanamun zafi a yanda nakesan hafsat lallai na qudurta araina idan har ban sameta ba to kuwa bazan taba bari ta mori wata rayuwa da wani namiji ba,a wannan karon kuwa naga bazan iya kashe abokina ba kuma asirin yaqi cinsu shine nayi amfani da damar kwanciyar ta asibiti na aikata hakan,amma wlhy nayi nadama musamman rashi aminina na sosai sosai" shiru aka danyi kan mutane su fara mamakin dan wannan guntun laifin ze saka tsabar rashin imani ka kashe mace har lahira,hukuncin daya dace dashi aka yanka mai aka tarwatse karar aka kuma gargadi muhammad akan furucinsa daya janyo masa cin zarafi....... *Washe gari* Tsaf J.A ya shirya yaje gidan su hafsat a parlor akai masa masauki,sannan akaje kiran hafsat,jiki a mace ta sakko yana ganin ta ya miqe tsaye yazo suna fuskantar juna yace "Bakin rijiya poor barrister,the youngest one,nazone in sanar miki ki gayawa iyayen ki one week kawai na saka d'aurin auren mu,lokaci yakusa zuwa dazaki san waye muhammad,menene kuma matsayin wanda ya tozartar dashi yakuma bata masa suna a idan duniya" wasu miyau ta hadiya masu dacin gaske ta runtse idonta sosai ta bude su a hankali sannan tace "Kayi hakuri muhammad" bece komai ba ya miko mata waya kirar iphone 6 yace zan miki waya,idan buqatar hakan ya taso,yana gama fadar hakan ya juya a nan ta durqushe ta saka kuka me tsuma zuciya..... Mom nuaiym      [2/11, 8:52 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 25 Da k'yar ta iya lallasr kanta tayi ciki,tarasa wazata tunkara da wannan maganar a duniya,ganin shirun baze amfaneta da komai ba ya sanya for the first time tun bayan rabuwarta da yaa shaam ta d'aga waya ta kirasa,mamakin ganin sunan ta yayi amma seya dauka da sauri ya kara a kunne tare da cewa "Hafst ya jikinki" amaimakon ta ansa shi se kawai ta saka masa kuka,mamakin jin kukan tane ya kamashi yace cikin rud'u "Subhanallah hafsat meya faru? Bakida lapiyane ko kuma shari'an ne be miki ba mu d'aukaka qara?" cikin sheshekar kuka tace "Dan Allah idan baka komai mu hadu a season 7 park,inaso muyi wata magana dakai ne" batare da bata lokaci ba yace "Babu damuwa in the nxt 25 mnts zan isa wurin" "To yaa shaam nima a haka" da kanta tayi tuqi tana isa wurin ta tarar ya rigata aranta ta ayyana wata qila yana kusa da gun dama,motarshi ta nufa kai tsaye ta bud'e gidan gaba ta zauna,gaidashi tayi sannan ta miqa masa takarda,cikeda mamakin takardar meye ya karb'a ya bud'e zare ido yayi bayan kammala karatun takardar sannan yace yana kallonta "Hafsat se yaushe zakiyi hankali ne wai e? Mesa komai naki bakya san ki saka tunanin mezeje ya dawo aranki? Yanzu gashi kin janyowa kanki sabida babu wani wanda ya isa ya watse wannan maganar yanzu,kuma sanin kanki ne j.A babban lauya ne wanda ya shahara a fannin iya shari'a,ni bawai auren sa bane banso kiyi sabi kowa ya masa shaidar halayya ta kwarai kuma sosai reputation dinsa ya girgiza da faruwar wannan abun waya sani koda wata manufar ze aureki ta cutar wa? Babban burina shine ki samu nutsuwa a gidan mijinki wannan shine dalilin daya sanya sam kikaga na janye zancen aurenki da zanyi sabida na tabbatar wa kaina bazaki tab'a samun nutsuwa dani ba musamman akan halima,yanzu sanar dani yaya kikeso muyi kuma yazo miki da wata maganar ne?" Kallonshi tayi tama kasa kukan yanzu kam tace "Yazo da yamman nan,yake cewa dani wai nagaya wa su daddy aure nan da sati daya yakeso kuma zan fahimci ba'a cin zarafinsa a zauna lapiya,har ya bani wannan wayar akan zemun waya idan buqatar hakan ya taso" nisawa yayi yace "Hafsat gaskia kinyi kuskure da kika aikata wannan shirmen,babu abinda zakiyi illah kije ki gayawansu daddy ayi masa yanda yakeso kije kiyita hakuri,danni nan matsalolin dakike fuskanta suna daukarmun hankali bamu sani ba ko wannan auren dazakuyi dashi ya zamo sanadiyar jin dadin na har abada ta yiyu ma adu'ar iyayen mu ne Allah ya karba zakiji dadi" kallonshi tayi qirjinta na dokawa tace "Baka tunanin cewar wani zargi ze iya shiga tsakani na da mutane? Baka ganin wasu ma zasu iya cewa hadin bakine kisan da aka yiwa sayyeed nida muhammad? Baka ganin kuma idan sun fada haka basuyi karya ba,muhammad so yake ya batan suna nima so yakeyi gaba daya nima duniya ta zageni,idan har na yadda da zancen aurennan tofa wlhy kowa zega tamkar ban damu da mutuwar sayyeed bane musamman lokacin nan daya diba kadan,dama ace nanda watanni hudu yace ko biyar" "Hafsat kije ki lallab'asa da dabarunku na mata cikeda hikima sabida ya yarda abar auren har nan da koda watanni uku ne,kuma kije gidansu sayyeed na nan garin ki nunawa mahaifinsa wannan takardar ta yar jejeniya ,shima mahaifin na say kizo masa da hikima ta hanyar rokarsa akan ya nema miki alfarmar muhammad ya janye wannan agrement din ya hakura da auren ki,ta wannan hanyar kadai zaki tsira da mutuncin ki a wurin iyayen sayyeed koda kuwa an daura auren nanda sati daya" jinjina kanta tayi cikeda gamsuwa da bayaninsa "Yaa shaam dan Allah mana muje gida na ajiye motana muyi sallan magrib in yaso ka rakani gun baban sayyeed ni tsoron wannan muhammad din nakeyi wataqil idan ya aureni ma mutuwa kawai zanyi" murmushi yayi yace "Kece mutuwan ai,sekace wani dodo"....... Bayan ta gama yiwa mahaifin sayyeed bayani yakuma ga takardar murmushi ya sake yace "'yata wannan muhammad din yana sani ya miki haka,sabida yasan bashi bane yayi kisan so kekuma bakida wani hujjan dazaki iya cewa aa bayan an gama shari'ar,shawarata anan shine kije ki lallab'ashi" kallon dattijon tayi tace "Daddy dan Allah ka bashi hakuri akan ya janye wannan zancen nidai bana sansa,kuma idan su daddy sukaji nayi wannan shirmen bazanji da dad'i ba" kallon ta yayi shima yace "To hafat kije gobe zan sameshi da kaina,suna kokarin barin wurin kanwar sayyeed datazo hutu daga india ta shigo,se kallon shammaz takeyi,suna fita ta biyo bayansu da suruun ganin hafsat,a can tace da hafsat "T loojah waye wannan?" hafsa tayi sannan tace "Bros shaam my big bros kenan"murmushi tayi "hes handsome ina sansa kuwa?" zare ido hafsat tayi "Da gaske Baby?" "Ea mana da gaske wlhy" murmushi tamata tace "Idan zaki auresa shikenan sena gaya masa" dariya tayi tace "Zan aure sa mana ai yafiki kyau" haka dai suka rabu baby se matsawa take da zancen shaam,koda sukaje mota hafsat ta gaya masa dariya yayi yace "Ina ni ina ba indiya rufamun asiri" cike da zolaya tace "Kai yaa shaam banda boye boye fa,Allah ina ganinka se wani kallonta kake kana murmushi" dariya yayi yace "Ina wasa dake zan mareki wlhy" seda sukaje gidan sannan ya karbi numer din baby haka kawai yakejin yarinyar ta masa wannan zankadediyar yarinyar lolxx. Qememe muhammad ya kafe akan lallai baze janye qudirin saba kuma nanda sati daya zeyi auren danita,su daddy hankinsu ya tashi kowa gani yakeyi auren manufa ne na rama sunansa da aka nemi batawa zeyi. Waya kawai ya kira hafsat bayan magaribar ranar yace da ita ta sameshi a mota,tana zuwa ta shiga gefen me zaman banza ta gaidashi,fitilar motar ya kunna fiskarsa ba yabo ba fallasa yakai hannunshi ya daga hannunta dake ciwo,dan kara ta saki ya juyo ya kalleta itama d'in shi take kallo harta soma kwallah,dauke kanshi yayi sannan yace da ita "Har yanzu hannun nan be gama dawowa daidai bako?" batace dashi komai ba se hawaye,tausayin kanta takeji sabida sosai take tsoron muhammad,hannu ya saka ya share mata hawayen daya gangaro mata yace bayan ya dauke kanshi "Mesa kike kuka hafsa? Banasan ganin saukar tsadadden hawayenki yana zuba a banza kinji" sauke kwayar idonta tayi kasa batayi magana ba,ya sake cewa "Yanzu sanar dani me dame kike buqata,bazakiyi shagalin biki ba,ni zanyi dinner da reception sabida yanzu ne zanyi auren soyayya na kuma zab'ina" kallon shi tayi tana kuka tace "yaa muhammad dan Allah kayi hakuri" dagowa yayi a karo na farko "Hakurin me kike bani" kukan ta ne ya tsananta ta dukar da kanta taci gaba da yi,tafi minti talatin tana kuka amma bece da ita komai ba seda dan kanta tayi shiru,kanta ne ya soma sara mata ta bud'e mitar da nufin wucewa cikin gida yace cikin izzah "Nine nace dake na gaji dajin wannan zazzaqar waqar da kika sakani agaba kina reramun? Maza dawo kici gaba dayi harse ya isheni" kallonshi tayi cikeda mamaki idanta ya kad'a yayi jajir,yakuma cewa "Dawo mana nace ki rufe murfin" a hankali ta sako kafafunta ciki batare da tayi magana ba "Kalli idanki hafsat,duk yayi ja sabida bakyajin magana,nace dake kukan na menene amma kinki ji,kin zauna kina kuka sekace wacce ke rero waqa,idan ba so kike na sassab'a miki ba karna kuma ganin hawayenki wlhy,sanar dani yanzu tsakanin ki da Allah menene kikewa kukan?" sadda kanta tayi kasa tace "Auren ne bana so" kallonta yayi ya sakar mata murmushi "Banida maganin wannan gaskia,so kiyita kukan,shika d'aine damuwar kodai da wata bayan wannan?" sadda kanta tai a qasa tace "So nakeyi ka tausayawa rayuwa ta ka agazamun ka bar aurennan har nan da wata biyu na roqe ka yaa muhammad dan Allah" kura mata ido yayi na yan dakiku kan yace "sekin mun alqawari guda biyu,tsakaninki da Allah" kallonshi tayi amma batace dashi komai ba yace "Na farko sekinmun alqawarin bazaki taba kawo matsala me kamada kin fasa auren ba idan na qara miki lokaci,na biyu kuma sekin mun alqawarin bazaki sakeyin kukannan agaba naba sabida gaskia banaso yana batan rai" yawu ta had'iya tace "Abba haris ya sanar dani muhimmancin Alqwari sabida haka bazan taba fasa auren kaba,sedai idan kaine kace ka fasa,kukan ma zan kwatanta" gyada kanshi yayi yace "Nima ai alqawarin auren ki nayi,idan ko bazaki karya ba ni mezesa na karya, nasan muhimmancin alqawari ai,kije na yadda nanda watanni uku idan munada rayuwa se ayi auren" godiya ta masa ya tsare ta akan setayi dariya seda tayi dariyar kuwa sannan suka rabu,se dadi takeji...... Shaam ba kad'an ba yake jin yana san baby,sedai be sanar da kowa zancen ba se daddy kasance war shi abba haris har wannan lokacin fushi yake dashi,sedama hafsa ta saka baki yake dan sake masa kadan,cikin sirri kuwa aka shirya auren sa da baby tare da nasu hafsa,sam haleemah batasan wainar da ake toyawa ba,tunda taji hafsa zata auri wani shikenan hankalinta ya kwanta...... Hafsa gabaki daya ta rame tayi baqi,sam wani jarababben tsoron muhammad takeyi gashi abu mafi ban mamaki shine tunda ya tafi akan ya dage zancen aurensu be qara zuwa wurin taba kuma gabki daya ya dena kiranta,ita kuma duk sanda tayi yunqurin kiransa se gabanta ya fad'i, huda ce ta fad'o mata arai ta d'auki wayar ta kirata,komai da ake ciki ta sanar mata,hudan kuwa ta bata shawaran akan lallai ta kirasa,kuma ta basa kulawa as if tana matukar sanshi,wasan da yake so su buga idan ba ta wannan hanyarr ta biyo masa ba lallai akwai matsala,sabida ya shirya daukar fan sane,sosai tayi wa huda godiya koda sun dade basu hadu ba amma sosai suke hurda,huda yanzu tana germany itada mijinta. Cikin sanyin jiki kuwa tayi kiransa a waya,kamar baze daga bama,se can taji muryarsa me saukar mata da fad'uwar gaba yace "Hello" sanda ta d'anyi jimm sannan tace "Yaa muhammad Barka da yamma" gyaran murya yayi yace "Barka dai" a ta k'aice,jikinta ne ya qarayin sanyi tace "Dafatar kana lafiya" "Ina lafiya" itace amsar daya bata,runtse idonta tayi sannan ta kara budewa tace "Yaa muhammad ka gane me magana kuwa" kamar baze amsata ba yace "Na gane mana ba hafsa bace?" "Ea nice ya kwana biyu?" tafad'a cikeda jin zafin wulakancin data janyowa kanta "Lafiya lau,ya akayi ne?" dafe kanta tayi dayake barazanar rabe wa gida biyu tace "Dama naga kusan watanni biyu ban jika ba,shine nace Allah ya sanya lafiya" "Lafiya lau mana,me zan miki to? Ina auren Agreement ne zamuyi,sekace wata soyayya ke tsakaninmu dazanta damunki,kokuma daze kasance komai nawa sekin sani?" kasa hakuri tayi tace "Koda na kirak bakaji na ambaci soyayya ba ai,danni a wannan zamanin banajin ma akwai soyayya,kurin dai kamata ya sanya nayi kiranka sabida ni nasanta" sarai ya sani magana ta gaya masa,amma seya dake yace "Ni ai tun farko na sanar dake yanzu ne zanyi auren soyayah, kuma zab'ina bakijiba ne,kece bakya sona so meye zesanya na nanuqe miki?" jan dogon numfashi tayi sannan ta furzar da wani iska me zafi tace cikin wata rikitacciyar murya "Yaa muhammad" shiru ya mata tace "Why?" cikin dakakkiyar murya yace "Hafsatu manga yar sarki wacce maza ke rarrashi,koba haka taken yake ba?" ganin ze raina mata hankali ya sanya tankashe wayar ta ajiye,be kuma kiraba se qarar shigowar message taji a wayarta kamar haka "This should the very first and last time dazaki ajiye mun waya,koda mun gama magana kuwa lallai nine zan zama na farko da zan ajiye" jikintane ya qara macewa jin kalamansa ta daga waya takuma kiransa yana d'agaba tace dashi "Yaa muhammad kayi hakuri" cikin sanyin murya yace "wuyarta ka bani hakuri kai tsaye za'a wuce wurin,dama gobe zanzo zancen kayan lefenki ki shirya zuwa dubai" "To Allah ya kara girma na gode sosai" "Se anjima" shine abunda ya fada a zatonta ya ajiye wayar ashe be kashe ba,ajiye tata wayar tayi ta sanya hannunta a kirjinta ta shiga rero kuka tana sambatu ta shiga uku,ita dai batayi sa'an zuwanta duniya yazatyi da masifan yaa muhammad,tunda tasan hankalinta take kwasar bakin cikin d'a miji,da karfi ta furta "Allah na tuba ka yafeni,Allah idan na aikata wani laifin ake jarabtana da wannan masifun Allah na tuba ka yafeni,kuma ka bani ikon cinye jarawar nan daka dauramun" kuka take sosai,muhammad dake saurarenta ma dafe kanshi yayi,ba abunda ke hanashi zuwa gun hafsa illah wannan kukan nata,ya tsani kukan ta masifaffen tausayinta yakeji,shidai bazece yana santa ba kuma bawai wata manufa ta cutar da ita yake da itaba kurun dai tausayinta yakeji yana gani kamar lallai idan ta auri wani zatasha wuya ne,tunda kuwa ya binciki tarihin rayuwar ta kaf,ya sani sarai dabe biyo mata ta wannan hanyar ba,shaam zata komawa kuma matar sa ma masiface a wurinta,kwanciya yayi ya runtse idansa yana mejin zafin zubar hawayenta..... Menen ra'ayoyinku game da auren hafsat da muhammad? Ina tsumayin jin comments naku. Vote plss Mom Nu'aiym ca [2/12, 8:21 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 26 Washe gari da yamma hafsat tana kwance mero ta shigo tace da ita "Kulele kije guest parlor muhammad yana jiranki yace wai baya samun wayanki" k'irjinta ne ya dan doka ta dago ta kalli meron "Ke kika ganshi da kanki?" kallon ta mero tayi,batun yauba ta fahimci ko zancen muhammad akayi hafsat tsorata takeyi tausayin tane ya kamata tace tana dafa kafad'arta "Inshaa Allah babu abinda ze sameki,kuma inaji ajikina tarayyarki da wannan muhammad d'in alkhairi ne mutum ne me nagarta sosai na kula da hakan tun a yanayin gaisawar da yakeyi da mutane,dan Allah ki saisaita nutsuwarki gu d'aya" batace komai ba ta sanya hijab dinta ta sauka zuwa qasan......Da sallama ta shiga parlor d'in kanta a kasa,ansawa yayi batare daya kalli inda take ba,karasowa tayi ta zauna kusa a kujerar dake fuskantar tasa tace "Ina wuni yaa muhammad?" Amaimakon ya amsa ta seya wurgo mata tambaya "Mesa kika kashe wayanki,bayan na sanr dake tun jiya yau zanzo?" kanta a kasa yayinda qirjinta keci gaba da uban dokawa tace "Banida caji ne" "Bakuda wutane?" ya wurgo mata wannan tambayar cikin tane ya juya ta dago da sauri suka had'a ido saurin janye nata idan tayi sannan tace "Da Akwai wuta caja nane ya lala ce" D'an kishin gida yayi sannan yace "Mesa baki saka layinki a wayan dana baki ba,kumama mesa bakya amfani da ita tunda na kawo miki ita da layine a ciki" "Kayi hakuri" shine abunda ta furta,ya tsani wannan ban haqurin na hafsat wlhy ita komai se ban hakuri qara tubire fuskar sa yayi yace "Zancen zuwa dubai ne had'o kayan lefe,idan ina irqawa daidai yau saura 27 day's daurin aure,so inasan sanin keda wa kuke da intl pasport wacce ayau zaku iya tashi zuwa dubai ko gobe a misali?" kanta a qasa tace "Nida khairiyya ne,amma inaga anan ma za'a iya siya ai base anje dubai ba" kallonta yayi na yan daqiqu sannan yace "Ba zuwa nayi ki bani shawara ba umarnin tafiyar nake baki hafsat,abu d'ayane zaki riqe mu zauna lafiya shine rashin yimun gaddama,nine da kaina zan sanarwa da Abba haris zancen tafiyar nanda kwana biyu zakuyi tafiyar,yanzu zamuje gidan Abba haris mu karbi pasport din nata,kema ki bani naki daga can zan masa bayanin tafiyar,akwai kayan dana saka aka kawo daga saudi wasu daga dubai,suma zamuje ki duba ,kayan gidane abinda be miki ba ki fada a sauya wani" kallonshi tayi taso tace dashi ai su daddy zasu siya mata kayan daki,amma tunawa da tayi yace bayasan gaddama ya sanya taja bakinta ta guntse.... Abba haris bayan ya gama jin bayanin muhammad tare dajin cewar wannan tsarin sane kana yanaso ma aqara sati biyu akan ranar daurin auren kasancewar bayaso a samo matsala tunda tafiya na Allah ne,be masa gaddama ba sedai yace sedai suyi tafiyar tare da babbar Aunty d'insu Aunty surayya,sabida zamanto warsu mata qananun yara,zuwan na surayya kuwa shine ze dauki nauyin sa,idan har mijinta ya Aminta,kara kallon abban yayi yace "Abba zancen kaya gida kuma,dan Allah karkuga kamar na raina iyawar ku kawai dai tsarinane nine nake siyan kayan gidana da komai,matana ta farko ma nina mata, sabida haka hafsat ma na riga na siya komai,kayan kitchen ne kawai bana siya,amma komai nine nakeyi" nisawa Abba yayi "Bazamu hanaka yiwa matarka alkhairi ba,sedai muma haqqin mune muyiwa hafsat, gyaran daki sabida haka zamu bata kud'inta tsaba,shawarar yanda zatayi dasu kuwa ze shiga tsakanin kai da ita ne,sabida kaine mijinta" Godiya yayi sosai sannan yamasa sallama,waya yawa hafsat tafito suka kama hanyar zuwa ganin kaya,kallonta yayi sosai ya furta "Hafsat karki qara yimun karya daga yau,a ina kika samu cajin yanzu? Kuma naga wayar kusan full ma? Bakida labarin karya ba kyau,kuma batada kad'an?" sosai taji kunya wannan ya sanya ta sauke kanta qasa tace "Insha Allah bazan kara ba kayi hakuri" murmushi yayi "Mesa kika kashe wayar ki?" murya a kasa tace "Nima dai yau sena tashi banso a kirani,shiyasa kawai amma ba komai" be kara cewa komai ba ita mad'in shiru tayi sanda suka isa wani qayataccen gida me kyawun gaske,tun a gaban gidan zakaga had'uwarsa da qayatuwarsa ba karya...Gate din automatic ne wannan ya sanya ya bud'e kanshi yana ganin dosowar motar, a wani farfajiyar ajiye motoci ya ajiye motarsa wanda had'uwars ba'a ma maganarta, kallon ta yayi yace "Bismillah muje ciki" Batayi musu ba kawai ta bishi suka wuce,ta bayanshi take se kallon cikar halittarsa takeyi yanayin halinsa yanayin maganarsa da uban ikon sa,wata kofa taga ya sakawa wani card lokaci d'aya ta wangale,kai tsaye ciki suka shiga tun a parlor ta raina dukiyar datake taqamar wai suna da ita,gabaki dayan parlor din komai na ciki gold ne se daukar ido yakeyi,dakuna guda biyar ne acikin gidan kuma flate ne me masifar kyau se paluka guda uku da fankacecen ktchn wanda ya gama hadewa da tsadaddiyar carbinet,gas cooker ne kawai aciki se freezer ta kwance da double door,a bed rooms din kuwa duka english bed's ne aciki,dayan dakin red and white,dayan blue wanda shi kuma akwai parlor aciki da lubby me kyau ga coffee chairs a walk way na zuwa barin,kuma komai light blue ne da white,dayan dakin purple dayan kuma pink $ white se thee green wanda aciki duk shine yafi burgeta,ko wane daki da toilet nashi,wanda a iya Bathrooms din idan aka barka zaka kwana kana kallon abubuwan ban mamaki,gidan ya hadu over bayan sun dawo parlor ne ya kalleta yace "Hafsatu manga,sanar dani tsakani da Allah ina kike buqatar a sauya miki?inda bakyso,ma'ana abun be miki ba?" kallon shi ta d'anyi sannan tace "Ni ko ina ma yamun ko ince yamun yawa ma,wancen corridor dinne kawai za'a saka mun console,se dining shelf dababu awurin dining,shima kuma zanwa daddy magana,nagode sosai Allah ya qara girma yakuma kara budi,Allah jikan iyaye kuma ya biya bukatocinka na alkhairi" har cikin ranshi yaji dad'in adu'arta tunawa yayi da Zainab wacce sam bata taba cewa dashi ci kanka ba duk girman alkhairin daze mata kuwa,murmushi ya sakar mata yace "Kinsan ni kwangila na bayar bansan wai ya kamata su zauna awurin ba,yanzu kawai muje shops asiya choice naki,ba wani su daddy" kallonshi tayi "To ai yaa muham......shhhhhh yafada hade da daura hannunsa asaman lips nashi,tunawa tayi da gargad'insa na rashin son gaddama ya sanya tayi gum da bakin nata,koda suka fito kasa hakura tayi dama hafsa akwai surutu tace dashi "Yaa muhammad gidannan yayi kyau sosai wlhy" Bece da ita komai ba kurun murmushi ya mata...... *Bayan kwana uku* Hakan kuwa Akayi,da hafsat da khairii da Aunty surayya suka dauki hanyar dubai a ranar wata wednesday,har suka isa suka kwana suna mamakin hali irin na muhammad,be basu ko sisin siyayyar lefenba,illah kawai tunkan su isa ya sanar dasu akwai driver daze kaisu masauki daga airport,kuma suna cin abincin wurin wanda menu kawai ake kawo wa su selecting,haushi duk ya gama kama hafsat kusamman ya da Aunty surayyah ke faman masifa akan ya rainawa mutane hankali,ko cewa akayi dashi basuda aikin yi,Wayan hafsa ne tayi qara tana dubawa taga number dinshi,a dake ta daga wayar sabida ba shakka ta shaqa yau kam,yace da ita "Hafsat ki fito idan kina masauki ina reception na hotel din" da mamaki ta kalli Aunty surayya dake gefenta tana uban mita,sannan tace dashi "A dubai din?" tsaki yaja yace "Noo a india,danla malama kizo ina reception ma wurin nace dake ko mun fara wasan banza ne haka?" cikin jin zafin gwasaletan da yayi tace "Kayi hakuri ganinan zuwa" kallonta surayya ta "Keda waye kuma Ina zakije?" "Muhammad ne wai yana wajen reception ashe yazo,kuma shi da number shi yake amfani niban sani ba" kallon ta tayi "Au dama shima zezo kika barni ina surfa mar ashar?" "wlhy Aunty bansan zezo ba,ni kawai zancen dan rakiya yamun" jinjina kai Aunty tayi "Wannan shegen muhammad din anyi miskilin masifa,ko wa yakewa iya shegen oho,jeki kiji" batace komai ba ta zari dan mitsitin mayafi tafito ga rigar irin straight gown din nan ne na roba ya kameta over, tun daga nesa tana ganin fuskarsa tasan akwai magana a d'an tsorace ta karaso wurin da yake,zama tayi kusa dashi a kujerar da yake tace "Sannu da zuwa yaa muhammad ya hanya?" kallonta yayi fuskarnan a daure yace "Banasan ya hanyar ki sabida jirgi daya muka zo daku ai,sannan wlhy mintuna goma na baki ki sako sutura dan wannan bakida banbanci tsirara,idan kuma na kuma ganinki da makaman ciyar wannan shigan wlhy sena sassab'a miki,sekace ba 'yar musulmi ba" kallonshi tayi se a lokacin ta tuna yanayinta,waifa ita tayi shigar ne a zuwan tazo garin farar fata kartayi qauyanci, jiki a mace ta miqe,zuwa tayi ta cire kayan ta sako abaya baqa har qasa tayi talha ta fito,surayya na ganin yanayinta tasan shigarta yayiwa masifa amma dai vata dameta da tambaya ba,koda tazo baya nan,wayarta ta daga takirashi amma be dauka ba,anan ta zauna tafi 30 mnt be dawo ba ta qara wayar tashi gaba daya ma tajita a kashe,gwiwa a sace ta koma dakin tace da Aunty surayya wai yace gobe zasuyi magana,kallo daya surayya ta mata kuwa ta fahimci da babbar matsala....... Washe gari tun asuba ta koma parlor tayi kiransa a waya,yana kallonta harta tsinke be daga ba, kusan 3 msd col,kawai seta fara hawaye tama rasa dalilin daya sanya take damuwa dashi zuciyarta sam batayi adalciba,data saka masa wannan tsoron na muhammad,tana cikin wannan tunanin taji qarar shigowar message "Room no 10,2nd floor" shine abinda ya aiko mata sarai tabgane nufinsa ta sameshi acan,miqewa tayi ta saka hijab dinta tayi hanyar daze sadata da wurin....knockin tayi yazo ya bude fuskarsa a hade,gaidashi tayi sannan ya janye mata ta shige a daya daga cikin kujerun parlor din ta zauna,ta qura masa ido,shima din ita yake kallo,yaukam seda tagaji da kallon nashi ido cikin ido sannan tace "Kayi hakuri bazan qaraba inshaa Allah" amaimakon ya baiwa maganarta muhimmanci se cewa yayi da ita "Meya faru kike kirana daga yin sallan asuba?" tama rasa mezata ce masa,se kawai ta miqe "zan koma bacci zanyi" tazaci ze dakatar da ita amma bece mata komai ba harta fice,a ranta kuwa taji zafin sa sosai.... *Nigeria* Sun dawo lapiya dauke da lefe da ban mamaki, har masifa su daddy sukayi,amma surayya tace dasu tamasa magana yace hafsa matar sace,babu kuwa wanda ze qayyade masa yawan suturun dayake buqatar wadata su da ita,kuma ya jibgo dogwayen riguna da qananun kaya over.......Aikam rana daya akayi daurin auren muhammad da hafsat,se kuma Shammaz da maryam,kuma aranar aka kai amaren biyu,wanda sam koda ma akayi auren hajia halima batada labari tana wurin gantalen ta dubai,acewarta taje saro kaya shikuwa da gayya ya ganta,yan uwanta kuwa dasuka ga pictures na ebar hankali da ba indiya se hankalinsu ya mugun tashi,amma sam basu sanar mata wai shaam yayi sabuwar amarya ba....... Hafsat kuwa tunda yan kai Amarya suka watse wuraren karfe goma na dare seta soma jin tsoron zaman gidan ita kadai, shi kuwa be leqo bama se sha daya da rabi, Abinci ya kawo mata sannan ya sanya hannu ya yane mayafin dake jikinta ya ajiye gefe ya kalleta, "Kina bazawara wani kunya zakiji,zaki wani lullub'e fuska" sosai maganar sa ya doki qirjinta amma bata nuna masa komai ba kurun dai murmushi tayi masa,ganin haka ya sanya yace "Kici abinci kazane da drinks ga youghurt da ice cream idan zaki sha" kallon su tayi tace "Gaskia Alhamdulillah na koshi,sedai zuwa safiya" miqewa yayi be wani damuba,kizo ki kulle kofofin gidan ni zan tafi seda safe" ko motsawa batayi ba daga inda take sabida mamakin daya bata,to gidan uban wa ze kwana?" ta tambayi kanta,ganin fa tsorone ze hallakata ya sanya harya kai parlor ta rugo ta riqe masa hannu,da mamaki ya kalleta tace dashi "Yaa muhammad zan bika dan Allah" juyowa yayi yabfuskance ta gaba daya "Ina zaki bini hafsat?" "Inda zakaje mana" "Ba inda zani fa, gidan zainab zanje na kwana,kishiyarki" tafi minti uku tana kallanshi, juyawa yayi ze fita ta riqe masa hannu again "Bazan iya kwana anan ni kadai ba,tsoro nakeji" murmushi yayi "Ni ban aureki danna tayaki kwana ba hajiya,ko mun rubuta haka acikin agreement namu?" gaba ki daya tsoro ne ya taso mata ta kalleshi sosai tace cikin dakiya idanta yayi ja sosai amma batasan tayi kuka "Na tuna kuwa babu wannan acikin rubutaccen auren mu,na manta bayan signing takardar yarjejeniya da mukayi ta aure,wurin daurin auren ma mun rubuta cewar kalar auren namu na dabanne ba wanda musulunci ya tsara ba,Kaje amma karka qara kawomun komai daya shafi rayuwar aure,idan bazamu kwana a tare ba babu wani abu dazakamun na aure,na yarda haka tsarin namu auren yake,kaje plss" tafad'a tana me d'addage hannayenta duka biyu alamar naci ka fam, matsowa yayi daf da ita ya sanya hannunsa asaman waist nata yamatse ta sosai da jikinsa yace "Ni kike gayawa magana hafsa? Sabida kin samu sake ko? Yanzu ma idanta ta dago sukayi kaura dana juna tace cikin jin haushin sa "So nake muyi sighning wani yarjejeniya kanka tafi" sakinta yayi yace yana murmushi muje gayamun wane iri ne?" zama sukayi a kujerun parlor tace "Sona ke mu kwana a roof daya,muci abinci atare,mu sake wa juna soyayya,mu aminta mudin masoya ne,idan har akayi watanni shida kaci cewar baka buqatar tarawa dani,kuma bakaji sona ko daya a ranka ba,to ka rabu dani,kuma tsakani da Allah zamuyi" kallonta yayi ya kwashe da dariya ya sani yanajin tausayinta amma sam baya santa wlhy, yakuma san baze taba san taba,da wannan ya aminta suka rubuta suka ajiye..... Hafsat ta kuma yin wauta a karo na biyu,yaya kuke zanin wannan zaman? Ze dore kuwa?" anya hafsat bata kirawa kanta zawarci na biyu ba bayan shaam ya aure fara me gashi abinshi? Muje zuwa dai..... Votes pls [2/13, 9:28 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 27 Muhammad a d'akinsa ya kwana yayinda hafsa ta kwana a nata d'akin,wata hatsabibiyar rigar bacci ta saka iya cinya,da saninta ta cire bra,pant kawai ne ajikinta se wannan rigar,sumar kanta datasha gyara ta gama barbajewa har saman goshinta daga bed room nata tafito zuwa kitchen,a parlor ta hangoshi zaune duk da zuciyarta takad'a qirjinta se dokawa yakeyi amma haka ta daure,tasani idan bata koyawa kanta rashin tsoron shiba akwai matsala,kallon ta yayi sosai ya raya aranshi so take taja ra'ayinshi wanda baze tab'a faruwa ba har gaban abada, bata ko kalli inda yake ba tayi gaba abinta zuwa kitchen,d'an guntun tsaki yaja ya mayarda dubanshi zuwaga film dayake kalla, Ha d'adden break fast tabshirya musu,finger sandwichs da chocolate sandwich,se kuma coffee amor da vegetable potatoe, tun yana daure wa har qamshin yasoma jan hankalinsa,ogar bata baro ktchn ba sanda ta hada samosa, jere komai tayi a fankacecen dining table,ta bude dining shelf ta baje komai da komai da ake buqata,bata wani kalleshiba sabida sam ma yi tayi tamkar bata kula dashi ba,dakinta ta wuce tasha wanka da wata doguwar rigar dress maroon color ta tufke gashin kanta da farin ribon,se flat shoe data saka shima fari qal, har tsakiyar falon ta sameshi kusa dashi sosai ta zauna ta kalleshi dauke da fara'a sosai a fuskarta,tana bude bakinta qamshi alawar datakesha ya daki hancin sa dauke kanshi yayi gefe d'aya "Barka da safiya yaa muhammad da fatar ka tashi lapiya?" dan juyar da kanshi yayi gefe daya sannan yace "Barka dai,kin tashi lapiya" Murmushi tayi "Breakfast kai kadai yake jira oga muhammad kose kayi wanka ne?" dagowa yayi dukda beso ba kasancewar tunda yayi aure da zainab,be taba tashi tabgayar dashi ba kuma yauce rana ta farko da mace ta gabatar masa da abinci,sedai kuku ne yake dafa masa,miqewa yayi yace muje dining d'in" kai tsaye tayi kokarin shiga gabanshi dauke da tafiya me daukar hankali gabaki daya gogan seya shagala da kallon mazaunan ta,susucewa yayi ya wani zama tamkar wani soko,sanda tace dashi "ka zauna plss" zama yayi yaga irin abubuwan data girka acikin lokaci qanqanin,yakuma san be rigada ya kawo cook a gidan ba dama niyyanshi yau da rana ze gabatar mata dashi "Mezan saka maka?" ta katse masa tunani da wannan tambayar "finger sandwich and veg potatoe zansha wancan abun kuma" batayi musu ba ta zuba masa komai da yace ta matso kusa dashi sosai wai bashi zatayi,kallon ta yayi ya d'an had'e fuska "Meye hakan hafsat?" kafe shi tayi da idanta "Yaa muhammad da kaina zan baka mana" a yanayin yanda tayi magana seya ganta kamar wata yar sha biyu kasa cewa komai yayi se bude bakin dayayi ta aika masa sanwch din ya gutsura,sosai yaji dadin abuncin yama manta inda yake har samosa seda yaci yasha coffee Amor dinshi sosai sannan ya daga mata hannu a lamar ya qoshi,kallon shagwab'a ta masa "Saura ni ka bani" dan mur ya qara sha "Na baki kuma me kenan?" Take ta hado shagwababbiyar fuska "Abuncin mana" tsaki yaja ya miqe kawai tashi tayi ta bi ta gabanshi tana doddoka kafa wanda ilahirin jikinta motsi yake tana kuma qunquni akan bazata maci abuncin ba yau gaba daya...bin bayanta yayi da kallo harta wuce ned room nata,girgiza kanshi yayi ya dawo parlor ya zauna ganin tafi 1 hour bata fito ba ya sanya ya bita ciki da kanshi, a kwance ya taddata rubda ciki takalmin kafarta kurin ta cire da zata kwanta amma komai najikinta nanan,mazaunan ta sun qara bajewa a yananyin kwanciyar datayi ji yayi tamkar ya sanya hannun sa ya taba wata zuciyar ta haneshi gyaran murya yayi yace "Hafsa mesa bazakiyi breakfast ba?" tana daga kwancen bata juyo ba tace "Bakai bane kace wai baraka feeding na da kanka ba,ni Allah bazan ciba idan baraka bani ba" shiru ya danyi kanyace "Naji muje zan baki" mirginowa tayi ta kiqa masa hannun ta waiya dagata,badan yaso ba ya miqa nasa hannun ya dagota,laushin hannunta kawai ya sanyashi runtse idansa cikeda kasala,a parlor kuwa seda ta koshi sannan tace dashi wai ita atabau seya dagata zuwa cikin parlor cikinta ya mata nauyi bazata iya tafiya ba, kallonta yayi yanaso yace kin cika rigima amma ya kasa,dagatan yayi ta wani lafe jikinsa har sukaje parlo ya direta ya zauna saman 3 siter zuwa tayi ta kwanta ta daura kanta saman cinyar sa tace dashi "Ka sosamun kaina zanyi bacci" bece da ita komai ba,aka soma knockin na gidan,dagata yayi yaje ya bude,kukun da yake jirane,koda aka nuna wa hafsat shi masifa ta saka akan itace da kanta zatana girka abunci,dole kuwa ya kyaleta ya sallami kukun, kallon ta yayi bayan fitar kukin yace da ita "Hafsat mesa kin cika rigima ne? Idan ma bakya buqatar sa mesa zakimun haka a gabansa? Seki bari idan ya tafi ko? Karki qara mun haka nan kina jina ko?" dan kallonshi tayi sekuma ta dake "Idan kayi hakuri kome zanyi ai na 6 month ne ka jira idan matar daba ta yarjejeniya ba tazo ka murza mata iko" sororo yayi yana kallonta ita harta wuce part dinsa, gyara masa dakin tayi ta kwashe kayansa ta wurga a loundry basket sannan ta yaye boxers nashi da singlet data ga ya cire ta wanke su ta shanya a toilet nasa, towel dinsa ta daura tayi wanka,tana fito wa ta ganshi asaman gadon dauke kanta tayi daga dubansa,tazo tana rawar sanyi, kusa dashi ta zauna ta rungumoshi gaba d'aya ta gabanshi "Yaa muhammad ka rufeni da jikinka akwai sanyi wlhy" gabaki daya ta gama da matsalar malam muhammadu,kasa ko motsin kirki yayi sanda taji daidai sannan ta miqe bayanta ya qurawa ido,taje mirror ta dakko wani mai tazo ta zauna,shidai yau ta gama rufe masa baki,shafa manta ta zauna tayi kamar kuma wacce aka tsikara ta laquto man ta janyo hannunshi ta saka aciki,juyawa tayi ta rage towel nata zuwa tsarar ta tace "Hannuna baze kaiba nika shafamun" shiru yayi dole ya murza man ya shiga shafe bayanta dashi,se wani lumshe ido yakeyi soft skin nata na daukar masa hankali sosai..... Da yamma yace da ita tazo su shiga bangaren zainab,ba musu ta caba ado suka wuce part din na zainab, suna zuwa parlor ya kalli wata yarinyar yace "Ki mata iso wurin zeezee" ya juya abinshi wani bangaren.....A zaune suka taddata ana mata gyaran kai,da alama wasune daga salon sukazo mata aiki a gida,har kafafuwanta ake wanke mata,kallo daya hafsat ta mta taji ta tsaneta,matar ma kallon sheqeqe tawa hafsat "Sannu" shine abunda tace dasu babu wanda ya koda kalleta acikinsu har masu aikin, duban su tayi tace Aunty zainab sannu" dagowa matar tayi cikeda isa tace "Kan mijin naki yakawoki gaidani be sanar dake ba'a gaidani a tsaye ba? Kuma ba'a saka ido acikin nawa sannan kuma ba'a kiran sunana hajiya zakice" kallonta hafsa tayi ta baki,ta juya abinta kawai aranta tace "qanin uwarki zanci ni kam wlhy,kajimun masifafgiyar mata,kinjawa kanki dani kuwa rashin mutun cine,gidan kika tarar... Kumun uzuri kaina ke ciwo [2/14, 9:00 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 28 A babban parlor na gidan hafsat ta had'u da muh'd kallanta yayi sosai ganin ranta duk a b'ace "Kaddai harkun gama gaisawar?" kallansa itama tayi "Ta dai gama wulakanta ni,Allah bazan qara zuwa wannan part d'in ba" tana gama fadar haka ta banki kofar tayi gaba abunta,binta yayi da kallo da kallo harta kurewa ganinsa,a ranshi yace lallai wannan yarinyar dama wai haka takeda fitina?....zuwa yayi kai tsaye d'akin da zainab take,Kallo daya yayiwa ma aikatan suka saketa suka watse,mutuqe fuskarnan yayi "Me kikawa hafsat ne?" kallon raini ta masa "Wacece hafsat kuma?" batare daya ce kala ba ya juya da nufin fita,ya gano raini zata kawo masa "Idan wannan shegiyar fitsararriyar yarinyar kakemun wannan kallon gwara ma ka dena,sanin kanka ne nan d'in gidanane kuma kowa dole ya girmama ni sabida nice babba" cak ya tsaya jin kalamanta sannan a hankali ya juyo ya kalleta "Gidan tane itama,ai auren mu aka daura bawai yar aiki na kawo miki ba,bakuma wai zama dadiro mukeyi da itaba,sannan da kike zancen girma aini ne me gidan idan baki girmama niba babu wanda ze girma maki wlhy,zaman lafiya nakeso kuyi da juna bawai shirmen kishi ba" miqewa tayi tazo har inda yake "J.A ni kake kallo kace dani wai kishi? Akanwa zanyi kishin kai? Danake sanka kokuma da aka gaya maka zaman jin dadi nake a gidan naka? Kaga wlhy idan ma mafarki kake ka farka,bazan tab'a kishin kaba sabida kasani sarai ba so araina" murmushi yayi dukda yaji zafin kalamanta sannan yace "Kamar yanda kikasan ni d'inma hakan take a wurina,nakuma auro matar so idan kin isa kem ki auro mujin so" Kallon mamaki ta masa sabida be taba cewa da ita baya santa ba se yau,qirjin tane ya doka lokaci d'aya taji ranta ya b'aci,kan tasamu bakin magana kuwa yayi gaba abinshi.... Koda ya dawo b'angaren hafsa kuwa a walk way ya sameta tanasham coffee,kallon shi tayi sosai "Mezaka ci dinner inaso zanyi girki?" kallonta yayi sosai "Bana cin abinda keda nauyi,so u think of something light" "Same here" tafad'a had'e da miqewa,sanda zuka parlor ya kalleta "Zan fita akwai wani abu?" matsowa tayi sosai kusa dashi ta hada jikinta da nasa,a kumatu tayi tsalle kadan ta manna masa kiss tace tana murmurshi cikeda rashin damuwa da abinda tayi "Ina maka fatan alkhairi,Allah ya sanya aje lafiya kuma a dawo lafiya" tana kaiwa nan ta juya abunta zuwa kitchn, yafi 3 mnts tsaye yana tunanin hafsat,tunda yake zeezee bata tab'a gwada yi masa adu'a ba akan wai ze fita ko wani abu daya shafi nasarar sa,wani sanyi yaji yana ratsa shi tamkar ruwan sanyi ayayin daka kwaso rana kake tsananin jin qishirwa, juyawa yayi ya fita amma sam bayan ya fitan seya kasa zama waje,duk motsin dazeyi kuwa zuciyar sa azalzalar sa takeyi akan ya dawo gida haka nan..... Shaam kuwa da maryam tun daren jiya suka angwance,ya samu nutsuwa me tsananin yawa a tattare da aurenta,yarinya ga tsananin riqon addini,domin kuwa ganin lokacin sallan asuba yayi shaam na bacci koda ta tasheshi sanda tayita mai wa'azi akan hakan,haleema kuwa batada labarin miyan da ake sha a niger da mujinta lolx..... Waffles sandwich ta musu da pizza ,se creamy la bees,sosai gidan ke tashin kanshi,wanka ta tsala tayi sallan ta na isha,daci ado cikin wasu riga da wando qanana pink and white masu matukar kyau,zokaga yanda heeps nata suka kwanta sosai gwanin sha'awa,kunce gashinta tayi ta taje shi zuwa baya yasha gyara se sheqi yakeyi haka ta zuboshi tamkar wata india,light makeup tayi tana fitowa sukaci karo a parlor,sanda ya lumshe ido ganinta kawai yaja numfashi, kamshin dayaji gidan nayi kawai ya wadatar balantana qamshin dayaji na ratsashi sanda ta fito, da sauri taje ta rungumeshi sosai ta kwantar da kanta a saman faffad'an qirjinsa ta furta a hankali "Sannu da zuwa yaa muhammad,ina fatan ka dawo lafiya" qamshin sumar kanta ne ya ebe shi besan sanda ya daura hannunsa yashafi gashin kan nata ba,yama kasa magana dama gashi ba ma'aboci son magana ba se kace ba lauya ba,dagowa da kanta tayi jin tayi lamo itama tanaso ta manta da muhammad ne fa,a shagwab'e tace "Yaa muhammad sekuma ka barni ni kadai,tun yamma fa ka fita" murmushi ya sakar mata me sanyi yama rasa me zece seya tsinci kansa da furta mata "Kiyi hakuri hafsat,wani abune ya tsaidani nima banso hakan ba,amma na kawo miki chocolate" wara ido tayi "Allah yaa muhammad? Thank you so much" ta qara rungumeshi sannan ta sakeshi ta juya,kallon duwawunta yake harta shige da jakar hannunsa da leda data karba,shi yaushe ma yataba samun arziqin a wani riqe masa jaka? Hmm lallai wannan auren yana ganin shine ake kira auren gaske kuwa.....A bed room nashi ma koda yashiga kamshin turaren wutan da aka saka dana freshner gaba daya ya banbanta,be taba kamshin daya kwanta masa araiba irin wannan,kallonshi tayi sosai,zuciyarta na dokawa sabida abinda huda tace tayi ya mata nauyi,haka ta daure sabida yanzu kam ta shirya yin wining wannan,taje kusa dashi botiran shirt nashi ta soma b'alle masa sororo yayi kuwa ita kam se murmushi take "Wanka ne ya dace dakai,a baho na had'a maka ruwan wanka da turaren wanka me tsananin kamshi,bayan kayi wanka se dinner kuma ko?" kallonshi tayi dasanjin amsar tambayarsa "murmushi ya sakar mata ya gyad'a kai alamar e,haka ta cire masa har wandon cikeda dauriya,ya dawo iya boxers de singlet ne a jikinshi, towel ta miqa masa tace "To zan jira kafito semu tafi tare" harta juya ya riqo hannunta yace "Sauran kayan fa hafsat? Su bazaki tayani ragewa ba?" murmushi tayi tace bayan ta kawar da kanta gefe d'aya "Yaa muhammad wannan ma aiya isa,dan Allah ka barni haka?" juyawa yayi zuwa toilet ba tare dayayi magana sarai ya gano nauyin sa takeji,wannan auren yana ganin shine mutu ka raba,shibesan ana wa maza gata ba har haka ai,a gurguje yayi wankan yana mamakin wannan kamshin da ruwan wankan keyi,haka yafito dagashi se towel halittarsa ta faffadan kirji ta kala,gaba daya jikinta ya mace sanda ta lumshe ido tana mafarkin ganin kanta a cikin wannan kirjin nasa,haka ya janyo man shafawa ze shafa,ita ta karb'i karamun towel ta goge masa jikinshi sannan ta shafa masa mai d'in,kayan baccin data ciro masa ta bashi ya karba yana murmushin da sam,yakasa daukewa a fuskarsa,da sauri ta bashi wuri tayi waje,a parlor ya taddata koda yaga pizza kallonta yayi "Daga ina kikayi ordering pizza,na season 7n kawai nakeci" kallonshi tayi ordering kuma sekace banida kayan had'in pizza d'in? Ni na hadashi ba dadewa fa" kallon mamaki ya mata "A ina kika koyi girki?" ya wurgo mata tambayar "A wurin mama na,kuma a india naje ctring classes yafi a irga,wasu zubin idan muna hutu ban dawo ba senayi joining,i so much like cooking ai" jinjina kanshi yayi yana me jin dadin yanda yake cin girkin matar daya ajiye a matsayin tashi,tunda yake so daya tak zainab ta dafa masa spag ita dinma san beci ba sabida ba taste kowa abincin cook yake ci,a parlor suka zauna kallo bayan sin ida,matashin kai tayi da cinyarsa anan bacci ya dauketa, se wuraren 11 ya dagata cak zuwa bed room nashi, sosai ya rungumeta ya kwanta shima....... Haleemah kuwa kwana bakwai da auren shaam ta dira niger,kuma a gidansu tafara sauka anan takejin mugin labari,aikam qungiya guda sukayi zuwa gidan amarya domin ciwo kan ubanta danye lolxxxz. Yau satin hafsa daya kenan a gidan muhammad sukan ci atare susha atare kuma a haka zasu kwana wuri daya,amma fa sam ba wani mu'amalar aure dake shiga tsakaninsu,sedai kullim kwanan duniya tana qara samun wani babban matsayi a zuciyar muhammad har yakeji baya iya daukar a wanni biyar batre daya ganta ba,yauta shirya zataje gidan shaam da gidan Abba haris,izini yamata akan ta karbo key na motarsa Avensus wurin zeezee sabida duka keys suna bangarenta taje da kanta tunda tace tare dasu momy zasuje gidan shaam din harsu khairii ma,koda ta aika wai bazata badaba,kai tsaye taje da kanta ,a zaune ta tadda ana matsa mata kafafu ta kalle ta sama da kasa tace ."Zainab key na Avensus fara zaki bani zanje unguwa" "shi me gidan naki be sanar miki cewar ni ce nakeda ikon komai da kowa ba agidannan,kice hajiya kuma ki durqusa ki rokeni key sannan zan baki" wata dariya hafsat tayi ta juya abinta zuwa waje,kallon driver na gidan tayi tace dashi "A waccen benz da key ke hannunka akwai mai ne?" kallonta yayi ya gyada kai,miqa masa hannu tayi kawai ta karba tayi gaba,tana tashin motar ta saisaita kanta sega zee tafito tana masifa ko kallonta batayi ba,tazo tasha gabanta aikam hafsa tayi cikin ta seda ta fadi sannan ta kauce tayi gaba abunta....... Topha koya zata kaya,su haleema sunyi qungiyar zuwa gidan shaam gakuma su hafsat zasuje koya zata kaya ohoo Vote and comment [2/16, 9:28 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*              29 Bayan ta d'auki su momy kai tsaye gidan shaam suka wuce,mota biyu sukayi kuwa,mamakin ganin motar gidansu haleema sukayi,kallo d'aya momy ta musu ta tabbatarwa kanta cewar ba lafiya,umartar kowa tayi dasu fito da sauri aikam a take suka fad'a gidan, mamakin ganin da sukayi su haleema sun saka maryam a gaba ta zuqa zuqan durina da kuma sanduna wannan ya mareta tanan wannan kuma ya mareta tacan,ita kuwa bakinta be mutu ba,se tambaya take su waye,da sauri momy tashige tsakiyar parlor d'in ta d'agata,mahaifiyar haleema ce ta wanke momy da mari kai tsaye,cikin fusata ta furta "Tsohuwar banza la'ananniya banda iskanci tayaya danki ze qara aure matarsa ta farko bata sani ba sannan ku baku nuna masa kuskuren saba? Aikam hafsa kukan kurciya tayi ta yanke uwar haleema da mari,daganan kuwa dambe ya kaure mahaifiyar shaam ta asali dayake tare ake da ita tashiga rabawa amma uwar haleema ta sharara mata marin gaske itama me kyau kuwa,aikam su khairi ma suka shiga damben,karamar su ce yar Aunty dinsu sumayya tayi wayon fita ta kira yaa shamm,dama yana hanya ya kusa karasowa,koda yazo kuwa se dukan iyayenshi akeyi agaban idanshi haleema batare data ganshi ba ta yanke momy da mari,babu yanda beyiba amma dangin haleema se dukansu suke da itace da dorina,kai tsaye dpo yayiwa waya akazo da motar police gida uku, kai tsaye aka wuce masa police station dasu haleemah da mamansu, su hafsa kuwa ansha duka jiki duk yayi tsami,dama mana dambe da yan tasha kai kuwa bawai saba wa kayi ba lolxxx... A station kuwa mamaki Shammaz ya baiwa halima domin bayaninsa cewa yayi wai sata take masa not knowing that takardunsa gaba daya na kadarorinsa original ones din suna bank,wayanda ke gida kuwa dukta sace tayi garkuwa da su,azatanta wai sune manyan sannan sunje har gidansa domin su kashe masa mata da iyayan sa,inta qaice muku qememe yace kotu zasu shiga..... Hafsat kuwa koda ta dawo gida a gaban gidan ta, ta tarar da Zainab ana mata matsar k'afa,sosai ta tamke fuskarnan tamau sannan tazo ta rab'a ta gefensu zata wuce,janyo hannunta zeezee tayi ta dawo gabanta "Ke baki iya gaisuwa bane? Ko bakya ganin mutane?" dan murmushi hafsat tayi sannan tace cikeda kasala "Zainab dan Allah kinga nifa bawai a makarantar karnuka aka haife niba,bakya gajiya da backing ne wai kekam? Irin wannan haushin dakike karnuka ne suke yinshi,kuma idan kin kula da kyau zakiga cewar su d'in dabbobine bawai mutane ba ni kuma mutum ce,sedai banida tabbacin koke kinada maraba dasu at all" miqewa zainab tayi ta d'aga hannunta da niyyar sharara mata lafiyayyen mari,se kawai hafsat ta riqe hannun nata ita ta wanka mara marin sannan ta cillar da hannun "Idan agidanku ba'a koyar dake gir mama d'an adam ba ni agidanmu an koyar dani,idan ke a gidanku ba'a koya miki zaman lapiya ni anamun bansan ma meye tashin hankali ba,wlhy zainab zanci uwar me garinku idan kikayi gigin taba'ani and karna kuma ganinki a k'ofar gidannan sabida bawai gidan ki bane nan din kinaji ko" shaqo rigar ta zainab tayi "ke dan ubanki ni zaki mara?wlhy yau sena hallakar dake shegiya me mugun bakin hali sati daya da aure anje gantale banza karuwa me aure aure kin kashe wanda zaki aura kinzo cin dukiyar dan tsohon gwamna,adaidai wannan lokacin muhammad yashigo gidan ya dawo daga masallacin sallar isha,da sauri ya karaso ya b'anb'are hannun zainab,yace yana kallon ta "Zainab karna kuma ganin ana shirin dambe agidan nan,kuma mesa zakizo nan part d'in banda neman fitina,wato dama jira kike ta shigo ki mata rashin m ko?" a kufule ta kalleshi "Yarinyar tayi niyyan kashe ni,hawa ta kaina taso yi da mota fa,wannan ai raini ne ma wlhy" kallonta yayi sosai ya kalli hafsat,ba agaban mutane yaso ya nuna mata kuskuren taba amma seya kalleta "Mesa kikayi niyyan hawa kanta da mota,cewa akayi dani seda ta kauce dagudu sannan tasha,atemted murder kenan fa,kuma kin sani" kallonshi tayi "Idan dai kasan ma'anar atemted murder ya kamata ace matsayin ka na babban lauya kasan ma'anar suicide,wanda suka gaya maka basu sanar maka mota na tafiya tasha gabanta da gangan ba? Ni ai hanya tace kuma tana sani ta kara tome zan mata" shiru yayi sabida yasan halin zeezee zata aika,sannan ya juya a hankali batare da yayi magana ba,ata bayanshi zeezee ta ciyo kwalarshi tayi dragging nashi gabanta ya juyo da mamaki takuma damqe mai kwalai agaban masu aiki "Me kake nufi danine wai,shikenan kawai sabida ta fadi magana seka wani yarda? Ni wlhy yau sekasan nayi da ita" hafsat ce ta matso ta sanya hannunta ta b'anb'are hannun zeezee a wuyan rigar muhammad tace bayan ta sanya hannu ta tura ta baya ta kuma nunata da d'an yatsa "Wlhy yau ne na farko kuma na qarshe dazaki ci kwalar mijina,banza jaka da batasan darajar auren taba ma bare mujinta wai nan ita yar gayu ce muma yar boko,amma acikin sanin darajar aure dana muji ko alihi bata sani ba" mayarda kallonta tayi ga masu aikin gidan tace cikin tsawa "Ku kuma muna fukan Allah maza ku watse mun anan" sumsum suka wuce ta mayarda dubanta zuwaga muhammad "Yaa muhammad dan Allah kayi hakuri duk nice naja maka,inshaa Allah bazan kara kulataba bare ma na b'ata ranka" bece mata komai ba,uta kuwa zainab tamkar an dasata haka tayi tsaye qiqam a wurin,part na hafsa ya wuce ita kuwa ta wuce part dinta hafsa kuwa tabi bayanshi...... Wanka tayi ta saka qaramar rigar bacci,sallan isha kadai tayi tabishi dakinshi,tararwa tayi harya kwanta,jiki a mace taje ta kwanta bayanshi,babu riga ajikinshi se guntun boxers kawai yana cikin bargo,bargon itama tashiga ta kwanta a bayanshi,ta sanya hannunta data zuro a saman bayanshi ta rada masa a kunne "yaa muhammad are u not feeling hungry? Banza ya mata,jikinta ne yayi sanyi ganin idanshi a bude alamace ta fushi yake "yaa muhammad dan Allah kayi hakuri,inshaa Allah bazan qara ba,zainab ma wlhy itane take tsokanana,kuma itane ta tsaya agaban motar wai bazan fitaba,bayan ta hanani key dakace tabani wannan ma a hannun kawu na karba" kallon ta ya juyo yayi,ya dagata gaba daya yana daga kwancen ya daurata saman ruwan cikinsa,kunya dukta kamata yace cikin shan mur "Menene dalilinki na zuwa police station kina matsayin matana? Mesa basu dauki statement naki a gidan ba,beside u dn't even call and tell me,seda yayanki yayi tunanin kira ya sanarmun?" sadda kanta tayi kasa sabida harga Allah batada niyyan gaya masa "Kayi hakuri yaa muhammad,bazan qara ba inshaa Allah" nisawa yayi "Hafsat" wannan ne karo na farko daya kirata da murya me nuni da tabbacin kalamanshi,kuma da sunanta kai tsaye haka,wannan ya sanya gaba daya jikinta ya mace ta kalleshi da lumsassun idanunta, dakyar tace "Na'am yaa muh'd" "Karki qara dukan zainab,kuma karna karajin kunyi fada,kota takaleki ki mata banxa,kuna bani damuwa da yawa hafsat,duka fa satinki d'aya agidan kuma ke nake gani da hankali a wurin ki nake saka ran zanji sanyi na samu nutsuwa,shine zaki biyewa zee kuta rigima a kusada hadi manku,kuma har ta wulakantamun mutunci agabansu" kwantar da kanta tayi asaman girjinsa tana hawaye cikeda kunya,tace "yaa muhammad dan Allah kayi hakuri wlhy bazan qara ba inshaa Allah,wannan ma kuskure ne" Dago kanta yayi ya qura mata ido ita kuwa sam ta kasa had'a idanta da nasa "Dago nashi kan yayi ya jona bakinsa da nata,d'auke numfashi tayi gaba d'aya lokaci daya kasala ya saukar mata,a hankali ya kwantar da ita d'ayan b'angaren har lokacin bakinsu yana had'e dana juna,cikin kwanciyar hankali yake sarrafa bakin nata,ta kasa koda magana kuma kunya ya sanya ta kasa sakewa dashi beside harga Allah batasan yanda ake wani kiss ba,sosai yayi kissin nata harta gaji sabida rashin sabo,ta kasa tureshi se kawai ta soma kuka,pulling out yayi ya kalleta,hannubya sanya ya share mata hawayen daya gangaro mata,runtse idanta tayi cikeda jin nauyinsa miqewa yayi ya rage fitilar dakin ya rage dim light kawai,ya dawo ya kwanta kusa da ita ya matsota sosai jikinsa,bakin nasa ya kara hadawa da nata,wannan bakin nata ya jima yana daukar masa hankali,hannunsa ya sanya ya dage yar guntuwar rigarta ya shafi flat tommy nata a hankali,wani numfashi taja sabida yanayin dataji ajikinta bata taba tsintar kanta cikin irin wannan yanayinba haka yaci gaba da shafata a hankali har zuwa saman lallausan girjinta, breast naya ya soma sarrafa ita kuwa ta kasa magana,yana mamakin duk girmansu suna tsaye qiqam, bakinshi ya daura gaba daya akan breast din nata wanda saqon dayake batan yagama haukata tunaninta gaba daya,kawai kuka ta saka masa janyewa yayi ya dagota sosai jikinsa "Hafsat kukan me kuma haka lapiya kuwa? Sekace ba mijinki bane ni na sunnah?" kukan tane ya kara yawa "yaa muhammad tsoro nakeji?" kallon mamaki ya mata "Haba hafsat tsoro kuma sekace wacce bata saba ba" kasa cewa dashi komai tayi shi kuwa ya sanya harshensa a kunnenta cikeda kwarewa,haka ya dinga bata wahala se kuka take jikinta kuwa sosai yake rawa,tasan menene aure takuma san wannan shine babban jigon auren amma ta rasa dalilin wannan haukacewar datake tunanin tayi,wataqil hakan baze rasa nasaba da rashin kawowa cewar ze aikata mata hakan yanzu ba, koda ya qara daura hannunshi saman breast nata rikewa tayi "yaa muhammad dan manzan Allah kayi hakuri,wlhy ban saba ba,ban iyaba wlhy tsoro nakeji,idan sabida namaka laifi ne aina baka hakuri dan Allah karufamun asiri kaji,Allah na tuba bazan kuma ba" mamakinta ne da tausayinta ya kamashi "to ki dena kuka,bazan qara miki ba kinji" da sauri ta gyada masa kai taja da baya,janyota ya qarayi jikinshi,yana mamakin wannan uban rawan da jikinta keyi ganuwar zufa duk sanyin ac gashi dama lokacin sanyi,haka ya rungumeta ya dinga patting bayanta a hankali harta soma bacci,amma tana baccinne a tsora ce,kura mata ido yayi yana me yaba kyawun halittar ta,sumar kanta tada baje ya sanye hannu ya janye mata sannan ya manna mata sumba a goshi ya kara matse ta a jikin shi,yana jin wani yanayi mara misaltuwa. *Sekunmun uzuri na koma makaranta yanzu* Mom Nu'aiym [2/18, 8:49 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* *Wannan shafin naki ne, kanwata Aisha ta ma'aiki,Allah yabar mana qauna ameen*        30 Da asuba kuwa hafsa Allah ciwon jiki ya kawo mata ziyara sabida ansha duka,duk yayinda zatayi juyi seta ji tamkar kasusuwan ta zasu tsage,aikam kuka ta saka cikin bacci muhammad  yaji sheshekar kukanta,tashi yayi ya kunna bed side lamp dake bedroom din ya janyota jikinshi,qara ta kuma sakawa cikin muryan kuka tace "Nashiga uku yaa muhammad da zafi fa" jikinsa ya daurata ya kalleta cikeda kulawa ya furta "Hafsat lafiya kuwa meya sameki?" cikin kukan tace "Yaa muhammad jikin duka ciwo yake mun,da k'yar nake juyawa yanzu bana ma iya juyawa" "Cikeda tausayi yace "subhanalahh kinje kinyi dambe da manyan mata sun zo zasu hallaka mun ke a banza,Allah duk abunda ya sameki bazan musu lamuni ba,tsami ne jikinki yayi sabida baki sababa wannan ba halin mutanen kirki bane,yanzu tashi muyi sallah sena gasa miki jikin naki" qara narkewa tayi "Ni bazan iya tashi ba wlhy" kwantar da ita yayi yazo yayi sallah sannan ya kunna heater ya ebo ruwan zafi,ya dakko qaramun towel rub ya saka acikin ruwan zafin sannan se ya kunna babbar fitilan d'akin zama yayi ya dinga dannan mata ruwan zafin kota ina idan ya daura seya huce yake sake tsomawa a ruwan ya jikoshi, se kukan shagwab'a takeyi  wai zafi takeji, bayan ya idar ya taimaka mata tayi sallah,sannan yace wanka zatayi a ruwan zafi,shagwab'ar ta somayi har tana kiran daddy "Dan Allah yaa muhammad kayi hak"uri Allah wani baccin nakeji" kallonta yayi sosai yasha mur batare da yayi magana yaje ya dakko towel,duguwar rigarsa daya saka mata tayi sallah ya zare yakuma zare mata guntuwar rigar dake jikinta  runtse idonta tayi cikin wata madifaffiyar kunya,ji tayi ya d'agata cak gashi yau ko pant babu ajikinta,acikin bahon daya hada mata ruwan zafi ya sakata, aciki yaukam poojah baki ya mutu,shi kuwa gogan har mamakin yanda yake mata yakeyi,be tab'a tunanin  mace zata bautar dashi har haka ba, ita kuwa tamkar qasa ya tsage ta shige,haka ya gama gargasa mata jikinta ya cireta ya daura mata towel,yanda ya kasa magana haka itama ta kasa magana,a haka ya zurata a cikin bargon,ya zauna yana bubbuga bayanta a hankali cikeda lici da rarrashi sekace wata ta goye,bacci ne me nauyi yayi awon gaba da ita shikuwa ya tashi yaje yayi wanka yakira waya ya ordering musu abinci daga season 7,ba ita ta farka ba se wuraren 10:am, da salatin annabi ta tashi Alhamdulillab jikin ba wani tsami se wanda ba'a rasa ba,tunawa da abubuwan dasuka faru jiyane ya sanyata runtse idanta, da sauri tabar d'akin taje ta shirya cikin wata jar atamfa me ruwan madara ajiki,ba kadan tayi kyau ba, tayi parking gashinta a tsakita ta daura dankwalinta ya zauna daram kai kace a saman kan nata aka haliccesa, pink lipstic ta saka a dan tsukakken bakinta ta shafa kwalli da powder kawai,se turarukan qamshi data feshe jikinta dashi, takalmi me d'an tsini ta saka tafito da tafiyar ta me daukar hankali,a parlor ta sameshi zaune yaudai kasa kallansa tayi ta sauke idanta aqasa cikin azama, karasowa tayi cikon parlor din ta zauna daga nesa dashi sosai tace murya can a maqale "yaa muhammad an tashi lapiya" kallonta yayi amma be ansataba,jin shiru ya sanya ya ta d'ago,da hannu taga yana mata nuni akan tazo,gwiwa a sace ta tashi zuwa inda yake,kusa da shi ta zauna ta sadda kanta a qasa tana wasa da yan yatsunta,tsayawa yayi yana nazarin ta,sannan ya sanya hannu ya janyota jikinshi "Hafsat kinyi kyau" kasa d'agowa tayi kuma batace komai ba se murmushi datayi kawai,hannun shi ya saka ya d'ago hab'ar ta fuskarta na kallon tashi ammabfir seta qi d'ago idanta sama ta sauke su qasa,murmushi yayi "Hafsat na wainikam wannan kunyar na menene e? Me kika jin kunyana sekace wacce bata saba rayuwa da namiji ba,kumama me namiki?" bata iya cewa dashi komai ba dai,harshe ya sanya ya lashi lips nata sannan ya cura bakinshi a nata,sosai yakejin dadin qamshin jikinta dakuma yanayin yanda kamshin numfashin datake saukewa yake, bakinta ma wani qamshin yakeyi dabesan dashiba, yaudai saqon da muhammad ke qoqarin turawa hafsat ta soma karb'ar sa, itama bazata iya misalta irin dad'in datakeji ba,wani abu takeji yana mata yawo acikin jijiyoyin jikinta wanda sam ta kasa gane ko menene, harshen ta ya kamo ya dinga tsotsa a hankali yana lasarsa tamkar wani swt,gaba daya ya gama kashe mata jikinta,a hankali kuma ya zura mata nasa harshen wanda ga mamakinsa kasayin komai tayi,aranshi yace kaddai hafsat batasan yanda ake asalin french kiss ba?,a hankali ya kama lips nata duka biyu ya tsota sannan yayi pulling out ga mamakinsa harta soma zubar da k'wallah,kuma yana gani jikinta duk yagama yin la'asar,harshe ya saka ya lashe hawayen tatas,sannan ya kwantar da kanta saman faffad'an qirjinsa yana bubbugawa a hankali,sunfi 10 mnts a haka kanya janyeta a hankali ya miqe zuwa dining yace da ita "Kizo kici abunci nina rigada na karya" Miqewa tayi taje gunshi ta zauna,tasa abuncin tayi a gaba amma ta kasa ci sam, kallanta yayi "A yi ordering wanda kikeso mana idan bazakici waffles da milk shake din ba ko?" kallonshi ta danyi "Noo zanci na gode sosai aida wannan ma" murmushin dayake rasa dalilinshi ya sakar mata "yaya jikin kuma?" "Da sauqi" ta bashi amsa a takaice dakyar ta iya gamawa da milkshake d'inta sannan ta tashi "Me zakaci lunch yaa muhammad?" "Keda bakida lafiya hafsat, ki bari da yamma muje mu siya mana" d'an turo baki tayi "Nifa kunya nakeji idan har aka ga mijina a restaurant yana cin abunci,ni aikin me nake agidan to? Nifa shiyasa duk kudina yake qarewa a garin koyon girki har chinese food na iya,so ni bazaka wani je siyan abunci ba ko ice cream da yoghurt kakeso kamun magana zan hada maka masu dadi a gida" kallonta yayi yanda ta dake se zuba take kawai dan yace ze siya abunci "Auren da saura watanshi biyar da sati uku,idan kika tafiyanki waye zena riqa dafamun abinci?" qirjinta ne yayi mummunan dokawa ita sam tama manta da wannan maganar,daurewa ta boye damuwar ta ta kalleshi tace "Sena ajiye zancen zamana lauya nazo na tare a gidan ka na soma yima matarka aikin girki,sabida kobama tare aika taba zama mijina ba zanso aganka da dukiyar ka da komai ba amma kana yawon restaurant" dama so yake yaga kota fara sansa amma seya ga akasin hakan,dannewa shima yayi yace "Ki shirya anjima zamuje kiga hajiyata,kuma nace dake inada yaro amma baki tambayar inda yake ba" "Kayi hakuri yaa muhammad,naga ban ganshi ba ne,na zata ka fada ne kawai yaya sunanshi?" "Komai sekin bada haquri kekam,sunansa Nu'aiym d'an wurin zeezee ne amma bata iya zama da yara sabida rashin kulawa shiyasa na maidashi wurin hajiyata" jinjina kanta tayi "How old is he?" kallonta yayi sannan yace "He's just 7" murmushi tayi "ohk barinje ktch" Abubuwa kala kala ta girka wa hajiyar ta muhammad, sannan kuma ta zuba acikin manya manyan warmers,wanka tayi ta caba ado acikin wani lesa ruwan zuma me digon ruwan madara ajiki,ba shakka tayi kyau wuraren karfe 4 na yamma suka fita agaban idan zeezee,ita tsoron kyawun nan na hafsat ke bata,yarinya sekace aljana qwafa tayi ta koma ciki,bayan sun dauki hanya dayake dukkansu su biyu a bayan mota suke,kuma motar dama irin ta manyan mutane dinnan ne me kaman parlor ba ruwan driver dasu,kallonta yayi "Hafsat wannan warmers meye acikinsu?" "girki ne nayiwa umma kala kala,zanje hannu rabana kaikuwa?" kallonta yayi yana mamakin fasaha irin nata amma beyi magana har suka isa,basa ganin komai sukam seda suka fito sannan tasha jinin jikinta da wannan tangamemen gidan,a haka suka shiga wani babban parlor me kyawun gaske anan tayi tuntub'e da hoton tsohon gwamnan garin da wata mata me matuqar kamanni da muhammad,se a sannan ta tuna sunan shi muhammad jalalludden Auwal,jalaluddeen Auwal Dange kuwa tsohon gwamnan jihar ne kuma ambassador a yanzu,se yanzu tunanin ta ya bata cewar lallai muhammad dan wani ne,saman suka haura inda anan suka fara cin karo da yaron muhammad da gudu kuwa ya rungumesa,daukarshi yayi suka wuce ciki kai tsaye,a wani parlor suka shiga da za'a iya kira da aljannar duniya a kasa tayi wa kanta mazauni ta sadda kanta qasa,matar data gani a parlor cikin goto itace zaune cikin shiga ta alfarma se fara'a takeyi sosai ta gaida ita cikeda nutsuwa cikin girmamawa,matar kuwa da fara'a ta amsa ta takuma tilas ta mata hawa a saman kujera amma sam se hafsa ta kasa wannan kunyar tabawa Ammy mamaki kasancewar tasan yanzu sam surukai basu da kunya,lokaci d'aya kuma taji hafsat ta kwanta mata a rai,suna haka aka soma shigowa da manyan warmers koda Ammy taji ita kawowa seta fad'ad'a fara'arta harga Allah taji sanyi har cikin ranta,ashe zata samu masu taimakonta koda tsufanta yasa ta kasa da tana damuwa da rashin Islaha a kusa da ita amma lokaci daya setake ganin idan hafsat na kusa bazati maraicin yara ba, godiya tayiwa hafsat sekace bame kudi ba kuma agaban hafsa ta zauna taci abuncin sosai,har tana cewa bata taba cin abuncin dataji dadin shi kamar wannan ba,muhammad dai se washe baki yakeyi,koda zasu tafi albarka ta saka musu tace da muhammad bayan hafsa tayi gaba "Kariqe matarka hannu bibbiyu muhammad kada ko bayan ba raina naji ka wulakanta yarin yarnan na yaba da kyawawan halayenta lokaci daya,matar mujahid da Amir kokuma matarka zainab babu wanda ya taba3 dafa ko indomie ya aikon da ita kokuma wacce bata hada wurin zama daya dani,inaso ka kula sosai ka zauna da uwar 'ya'ya ta gari kaji ko?"girgiza mata kanshi yayi sannan yamata sallama suka tafi,hafsa ko tasha kyaututtuka harda turaruka da laces,atamfofi da sarqar gwal.... A gida kuwa kai tsaye part dinshi yaje da hafsat yakira zee a waya tazo ta samesu,ko kallon hafsat batayiba daga tsaye kuma tace da muhammad "dadyn Nu'aiym gani lafiya kuwa" kallonta yayi yace "Zama zakiyi" zaman tayi ya kalle ta "Dama zancen raba kwana ne,na zabi kwana biyu a ko ina,sekuma zancen ra'ayin inda zaku riqa samu na,ni nafison duk wacce dake da kwana ta sameni a part dinnan nawa,bansan haya niya" kallon sheqeqe ta masa "Muhammad nifa bansan wulaknci wlhy, tunkan wannan matar tazo nafi 2yrs bana kwana wuri daya dakai,se yanzu tsabar raini zakace mu kasa kwana sekace gwad'an rama a faranti? Kaga nifa kasan bawai lalurar ka zanba ga kuma zuwana office,idan so kake mu fara kwana atare kabari ku gama angwanci nanda 6 month nice na yarda da wannan so karka damu" Amaimakon ya damu seyace "Kya iya tafiya dama shine kawai" miqewa tayi ko a kwalar riganta tayi waje,araina nace lallai zainab baki san meye kishi ba zaki sha mamaki kuwa loxx..... A b'angare shammaz kuwa dasu haleema rigima ake sosai,kuma su haleema sukayi rashin sa'a j.A ne lauyan shammaz,duk ya gama tattare kayanshi data sata se zare ido sukeyi kuma yace baze saketaba,ya shirya wulakan ta ta over ma. Da dare kuwa hafsat bataga muhammad ba har sha dayan dare duk ta damu, wayanta ta daga takirasa,yana wani shan qamshi ya daga kiran,cikin sanyi tace "Yaa muhammad lafiya kuwa,naga motarka amma banga kashigo cin dinner ba" gyaran murya yayi yace "Hafsat ki tambayi hadimanki inane kofar baya,idan suka nuna miki ki fito zakiga wata kofar ta baya nima ta part nawa wacce zata sadaki da cikin gidan nawa ki shigo tanan,na sanar dake cewar bana san hayaniyar en aikin nan fa,ki zomun da samosa inada fresh milk anan" Komai taje masa dashi amma bataje da shirin kwanciya ba, koda yazo ze kwanta seta masa sallama ya wani harareta "kizo mana mu kwanta ina zaki?" shagwab'ewa tayi "Yaa muhammad nifa banmayi shirin kwanci yaba" kallonta yakumayi ya miqe ya bude drawer yazaro wata rigar baccin mata,yazo yazaga bayanta ya zuge zip na rigarta,ya zuge na skirt ko motsi bata yiba,ya zubar dasu anan,bra dinta ya balle ya cillar gefe daya sannan atabayn ya zura hannuwanshi ya cafki dukiyar fulaninta hhhhqqqh taja wani numfashi ya daura gashin gemunsa saman wuyanta yana gogawa a hankali,sumane kawai hafsat batayi, juyo da ita yayi ya daura bakinsa saman kunnenta ya hura mata iska me dumi, sannan ya sanya harshe aciki,ci gaba yayi da lasar jikinta da harshen ta,hannunsa daya yana kan nipple nata yana murzawa cikeda salo da kwarewa sannan kuma dayan hannun ya riqe waist nata dashi, hafsat gigicewa tayi cikin wata murya ta furta "yaa muhammad zan fad'i" Daukarta yayi cak zuwa kan makeken gadon ya kwantar da ita yaci gaba da aika mata saqonni,hannunshi yakai ya lalubi cinyarta sannan ya gangara zuwa managan nata,bakinshi yana kan breast nata,ayya hafsa ta kusa macewa kan dadi lolx,tsoro ne ya kamata jin yana shiri zare mata pant gashi ya kutsa hannunshi acikin pant din yana aika saqonni hanyar murza mata abun saman a hankali "wayyo Allah yaa muhammad dan Allah kayi hakuri,wlhy tsoro nakeji, dan Allah kayi hakuri kai bakasan albarka ne,ka tausayamun dan Allah" Be saurareta ba ta zare jikinta da sauri ta takura can gefe,gogan fushi yayi ya fita parlor yabarta anan..... Mom Nu'aiym [2/19, 9:40 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*      31 Duk se hafsa taji ba dadi sam abunda ta masa,tsoro me tsanani ya kamata ganin yanda ya zuciya da abinda ta masa,ganin yafi 1 hour be dawo ba ya sanya ta daura towel tafito a prlor ta ganshi kwance saman carpet yayi pillor da trow pillow,kusa dashi ta kwanta ko fitilar bata kashe ba itama shi a wannan lokacin yamayi bacci abunshi,sosai tashige masa acikin jiki ta kwanta yanajinta amma seya mata tamkar bacci yakeyi,a hankali yakejin saukar hawayenta masu d'imi asaman qirjinshi,duk yanda yaso ya basar tausayinta ya hana,kanta ya daura asaman hannunshi daya miqe yace murya can qasa "Hafsat lafiya kukan me kike" amaimakon tabashi amsa seta qara sautin kukan nata, matseta yayi sosai "Gwara kimun komai ma akan wannan zubar hawayen dakike hafsat,wlhy bansan mesaba na tsani ganin kukan nan naki sam bana sansa wlhy,yana tayar mun da hankali over,dan Allah kiyi hakuri kinji,sanar dani meyake damunki?" Cikin muryan kuma tace "Bakai bane kake fushi dani,ni banso inga ina b'ata ranka kuma sannan ni tsoro nakeji" Kallonta yayi yaga idanta ma arufe yake ruf, yace "Kece banasan abunda kike mun hafsat,sekace yau kika fara ganin maza? Sam bakya kyautawa kanki abunda kikeyi wlhy kinsan kuwa haramunne yin hakan,nifa mijin kine" shiru tayi wannan ya sanya ya tashi ya koma daki ya barta agun ganin sam bawai yarda zatayi ba ga alama tsanar datake masa ya wuce tunanin me hankali,ta gano qarayin fushi yayi da ita,wannan ya sanya ta bi bayanshi tun a tsakiyar parlor din ta cillar da towel dake jikinta,qirjinta se dokawa yakeyi sabida tunawa datake abunda ta gani awurin wasu turawa masu sana'ar yada bf,ita tasha lalubawa batada wannan hanyar idan ko har irinshi za'a mata lallai ko mutuwa zatayi ba shakka.........Tana hawa saman gadon ya daka mata tsawa "Maza ki fice ki bani wuri,tunda tawa qiyayyar aranki hartakai ki hanani haqqina,kije can da tunanin wani na tunda haka kika zab'a" Amaimakon ta sauka se qara hawa tayi sanda taje kusa dashi dukda tanajin kunya ga side lamp a kunne ta daure tace "yaa muhammad ihu kuma da darennan wlhy bazan maka gaddama ba gani nan im all urs se yanda kayi dani" jikinshi ne yayi sanyi amma bece da ita komai ba,kwantawa tayi kusa dashi ya juya mata baya har yanzu fushi yakeyi,ta bayanshin ta kwanta ta rungumoshi jikinta,hannuwanta asaman girjinsa,tarasa dalilin dayasa takejin zuciyarta na azalzalarta akan tamasa yanda yakeso,batasan fushinsa akanta,shashafashi tashigayi tako ina,banza ya mata tafi minti goma tana shafar jikinsa yanda taga yana mata amma sam beko motsa ba,wannan abun be dameta ba murya na rawa tace "Yaa muhammad ina damunka ko?" dagowa yayi ya kalleta,sannan ya miqa hannu ya kashe lamp din dakin ya juyo mata sannan yace "Hafsa in tambayeki mana" bata nashi amsa ba yaci gaba "Wannan mijin nakine ya hanani sukuni? Kokuma shine aranki da har yanzu kin kasa sakin jikin ki dani? Yanzu a ganinki ke hakan ya dace? Haka ake wasan aure da miji?" cikin qunan rai yanzu ta dago ta kalleshi tace "Ban gane ba?" "Kina nufin baki iya wasanni ba,gaskia na gano shammaz dinnan jahili kika aura,kokuma haka kawai yake zuwa miki tamkar wani dabba,shiyasa baki san yanda ake wasa ba?" sosai zuciyar hafsat ke tafasa yanzu kam da kalaman muhammad miqewa tayi daga kan gadon ta kunna fitilar dakin ta ja kayanta ta saka tafice gaba daya daga part din tsaki yaja ya koma ya kwanta,sekuma ya kasa nutsuwa gaba daya ganin yanda ranta ya baci da kalamanshi yasanya yaji bayajin dadi gaba daya haka dai ya kwana yanata juyi be samu baccin ba......A b'angaren hafsa kuwa rai a b'ace taje part d'inta duk haqurinta yau kam saida tayi kuka sosai kuma, kodai gani yake cewar ita d'in yar iskace? Kuma me zata masa abun da taga yana mata shi take masa kuma shi ai bashida jiki irinna mata,kuka kam aranar ta shashi over,ba iyaka haka tun asuba takira huda ta gaya mata abunda yake damunta,dariya huda tayi tace "Kinga hafsat bafa abun damuwa bane ba wlhy,mijine kika samu irin nawa d'an duniya ne sosai tarayraya yake so,kuma fa kinga shi sam besan cewar baki taba yiba,karki dauki fushi dashi kuma karki gaya masa baki sababa ila kawai komai kika ya miki ki masa irinshi,karki saka wata kunya kinji ba,nonon dayake wasa dashi naki ai shima yana da nono,idan yasha naki yanda duk kika yayi ya lallasheshi kema haka zakiyi ko ina najikinshi nakine ki taba,kuma akwai namijin dashi sam baya san kunya asaman shimfidar sa,kya bari idan kun gama hutawa da jikin juna ki qatarata da kunyar ki,karnaji kin soma fushi da mijinki gaskia,jahilan mata sune gaba da wani fushi da mazajensu,ki nutsu da kyau ki kula inane idan kika tab'a ajikinshi yakejin dad'i seki naqalci yin abun kinji ni aiko?" nisawa tayi ta mata godiya sannan sukayi sallama.......ktchn ta fad'a tayi pizza,da oreo milk shake da abinda ta kula yafiso ra'ayinsu yazo d'aya wato samosa, koda karfe 8 am tayi ta kammala a gurguje taje tayi wanka ta sanya wata rigar kimono gawn red ta d'aura black headtie, black earings da black flate shoe ba shakka tayi kyau sosai ba kad'an ba,a wani fine basket ta shirya komai tanufi part d'inshi ta k'ofar baya,mamaki tayi ganin tana turawa taga kofar a bude,kanta ta tura kai tsaye zuwa ciki taje dining ta shirya komai sannan ta wuce ciki,rankon bacci yake kasancewar jiyan be samu yayi ba,tun asuba kuwa dayayi sallah yake bacci yanzu har 9:26 am yanata bacci,a hankali taje kusa dashi ta kwanta gefenshi,kwantar da kanta tayi adaidai kunnenshi ta riqa shafa bayanshi a hankali tana kiran sunanshi a kunnenshi cikin wani salo da murya qasa qasa" a hankali ya bud'e idanshi kamshin jikinta kawai daya shaqa seda yaja numfashi ya fesar,juyowa yayi ya fuskanceta sosai yace "Good morning wyfy,shine kika tasheni ko,bayan kene kika hanani bacci gaba d'aya jiya" Murmushi ta sakar masa "Sannu da tashi yaa muhammad" janyota yayi da qarfi ta fad'o jikinsa,hannu ya sanya ya laquce mata hanci "mesa zakimun fushi,bayan kinsan banasan ganin bacin ranki,seki ka hanani bacci gaba daya se yanzu kuma ina ramawa kinzo kin tasheni" murmushi tayi "yaa muhammad nifa ba wai fushi nayi ba,naga inata b'atama rai shine naga gwara inbarka ka huta" murmushi yayi shima "Baby karki qaramun fushi dan Allah kinga wlhy bacci gaba daya kasayi nayi se yanzu da safennan, nasamu nayi" murmushi kawai tayi ta gano ya gane cewan fushi tayi ba buqatar wani b'oye b'oye "kayi wanka semuje kaci breakfast ko?" murmushin shi yayi ya miqe ita ma ta wuce zuwa parlor domin jiranshi,koda suka gama breakfast kallonshi tayi "yaa muhammad baccin zaka koma ne?" "haka nakeso kaina nauyi yakemun" girgiza kanta tayi sannan tace "To bakomai barinje sena qara shigowa" juyawa yayi ciki kawai batare daya ce kala ba, ita kuwa zuwa tayi ta shirya cikin wasu kaya riga da wando masu santsi ta feshe jikonta da turaruka na alfarma sannan ta sanya hijab qatoto ta wuce kai tsaye part d'inshi,rufeshi tayi ruf sannan tawuce bed room nashi,ya kashe fitila ko ina yayi luf luf,kai tsaye zare hijab dinta tayi lalubenshi dayake bawai kamar duhun dare bane,yaye duvet din tayi ta shige ciki kai tsaye matsawa tayi tankwanta suna fuskantar juna kuma kusa dashi sosai,hannnunta yablalubo sabida yaji shigowarta yace "Baby kinzo tayani bacci ne?" kunyace ta kamata a hankali ta furta "Nima zuwa nayi rankon bacci,sam jiyan ban runtsa ba sabida b'ata maka rai danayi" matsowa yayi da ita jikinshi sosai yace "zo nan in sakaki bacci" matsawa itama tayi ganin yayi shiru tace "Yaa muhammad zansha" hannunta ya qaro d'amqowa "Mezaki sha hafsat?" cura kanta tayi acikin qirshin sa "Bakinka mana" ta bashi amsa kan nata yana cikin qirjinsa,hannu ya sanya ya tallafo kan nata ya manna bakinsa da nata,yau dai hafsat duk yanda muhammad ya mata haka take masa,a zatonsa yau d'in ta sakko ne, hannunshi yakai kan breast nata ya soma shafawa a hankali hafsat neman sheqewa takeyi koda yakai bakinsa ya soma tsotsan breast nata tafara mai sambatun dabata masan me take fadaba,wani feelings ne yake fizgarta dabatasan wane iri bane,lalubar kanshi take tako ina,muhammad ya isa na namiji yasan hanyar da ake bi da mace a sarrafata tasha dad'i babu inda baya lasa a jikinta,tun tana iya magana harta koma se numfarfashi takeyi, sam shi be kawo aranshi cewan wai hafsa vergin bace wannan ya sanya yamata hawan qafara ya shiga gaba d'aya,tsoro ne me tsanani da azaba suka kawo mata ziyarar bazata, shikuwa mamakin yake yanda hanyar take a toshe amma fa sabida ya matsu be tsaya wani tunanin ba ko kawo tausayi ya kutsa mata bil haqqi,tun tana cizo tana yakushin sa harta haqura,sam bebi da ita ta hanyar wai itadin budurwa bace, Sanda ya nutsu tukunnan kusan 40 mnts yana abu daya sannan yakula da aika aikar daya mata har lokacin kuwa kuka take ba qaqqautawa, fitila ya kunno lokaci daya qirjinsa ya doka,innalillahi wa inna ilahirajiun itace kalmar daya furta,sannan komai ya fara dawo masa,tabbas wannan yarinyar bata taba tarawa da namiji ba se yanzu,inko hakane na aikata mata barna, ga shigar sauri gakuma dadewa ana murzarta,ban daki ya fada yacika bawo da ruwan d'imi dettol ya zuba kadan sannan ya dawo har lokacin kuka takeyi,daukarta jikinta duk ya gama mutuwa,ya wuce toilet din da ita uwar qara ta saka sanda tashiga ruwan zafin "yaa muhammad dan Allah idan laifi namaka kayi hakuri,Allah bazan qaraba,da zafi wlhy,da zafi sosai" tausayinta yaji ya kamashi "Kiyi hakuri hafsat na,dena kukan haka wlhy bansan baki sababa bane ai,da bazan miki da zafi ba,yanzu kuwa wannan kadai ze baki relief daure kinji?" kukanta taci gaba dayi shida kanshi ya mata wanka ya tayata tayi wankan tsalki sannan ya daukota zuwa other bed room din sabida wannan gadon ba tarihin bedsheet nashi...... Har wannan lokacin hafsa kuka takeyi sabida ba kadan ba take jin wurin yana mata zoqi,ganin haka ya sanya ya kira Dr. abdul kai tsaye,bayan sun gaisa yace dashi "D. Abdul hafsat ce aka dan samu garaje wlhy,bansan wai ajiyemun ita kawai akayiba ,yanzu dai ataqaice naji mata raunuka zance,wane pain reliver zata sha?" dariya doctor yayi "Zan maka txt na magun gunan,kuma kabata lokaci irin kwana huku raunin ya warke kasan mata" godiya ya masa sukayi sallama, txt kawai ya aikawa drive yaje ya kawo maganin Tea yake bata tana kurba a hankali har wannan lokacin kuka takeyi,ya kalleta cike da kula wa "Hafsat kiyi hakuri ki dena kukan haka kinji idan kika sha maganin ze dena miki zugi" Bata kulashiba haka tashanye tea din yabata maganin tasha sannan yankwantar da ita,qememe kuwa taqi yarda tashiga jikinsa sosai,ita adole wai ze qara mata,kallonta yayi "Mesa zaki takure acan?" Banza ta masa ya kara matsowa "Dan Allah yaa muhammad karkace zaka qaramun wlhy da zafi,har yanzu azaba nakeji" murmushi yamata ganin tana Girma tana wawta, "Bazan qara miki ba mana,nonon kawai zansha sekimun kalar kukan dakikayi sanda nake shanshi d'azu ko har dadin ma bakya so?" hannayenta ta saka ta rufe fuskarta tana murmushi tana hawaye tace "Ai shima yaudara ne banaso" tafada har tana maqe kafad'a...... Mom Nu'aiym [2/20, 9:17 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* *Khadeejah mb keba baiwa kyautar wannan page din,kin cancanci fiye da haka,bazan tab'a manta alkhairin kiba,Allah bar zumunci* 32 Se yamma likis sannan suka farka daga bacci, da sauri suka gabatar da sallah hafsa se dingishi takeyi wurin na mata zogi,zaunar da ita yayi kusa dashi yace bayan ya tattare nutsuwarta zuwa gareshi "Hafsa inaso ki sanar dani gaskia,kin sanni banasan karya kin taba tarawa da wani namiji?" shiru ta masa kawai seyaga kamar bataji dadin maganar ba "Abunda yasanya na tambaya ba komai bane sedan ganin kin taba aure gashi kuma nazo na sameki cikakkiyar budurwa,na tabbatar hafsa ba'a yin budurci so biyu,kowace mace budurci daya ne" sadda kanta tayi a qasa tace "Iya tsawon zamana daya shaam ko bangare na be tab'a shiga ba da sunan kwana,hasalima ko kan shinfida ta be tab'a zama bare kwanci,ni banida shirgin samari kuma ko a india ban taba dating wani ba,ni ban tab'a koda hada bakina dana wani ba bare nasan yanda ake yin koda kiss ne,kayi hakuri danaketa b'ata maka ranka,wlhy ba raini bane ban iya bane" ga mamakinta se gani tayi ya rungumeta yana hawaye "Nasan ban cuci 'yar kowa ba Allah baze bari na cutu ba,na tabbatar hasken rayuwata zezomun a sanda bana tsammani lallai hafsa ke haske ce a gareni,Allah yayi miki albarka,Allah ya daukaka ki,Allah ya sanya alkhairi me tarin yawa acikin rayuwarki" Shiru tayi bata fahimci inda ya dosa ba,dago wa ya daura hannayensa akan kafadarta "Sanar dani yanzu inane yake damunki? Ina yake miki ciwo ajiki" sauke kanta tayi kasa tace cikin rawar murya "Cikin jiki nane yakemun zugi yaa muhammad,dan Allah karkace zaka qaramun wlhy da akwai zafi sosai" rungu meta yayi tsam ajikinshi "Sannu baby na,bazan qara miki da zafi ba amma bazan iya hakura dake ba" Turo baki tayi "Ni ka kaini gun momy na mata sati biyu hutu zanje" aranshi yace naso ganin quruciyar yarinyar nan "Anan zaki zauna sekin warke,bakiga yanda kike tafiya ba,idan kikace zaki je momy zata gane komai" Zaro idanta tayi waje "Aikam baza niba,to yan aikin gidannan fa suma zasu gane ni ko?" murmushi yamata har mamaki rashin wayonta ke bashi daga gani a sangarce ta tashi "su bazasu gane ba ai,amma nizan gane" dariya tayi ta kwantar da kanta a saman qirjinshi "Yaa muhammad yunwa nakeji fa sosai" "Me zakici nida kaina zan dafa miki" murmushi tayi "Nice zan dafa mana kawai tayani zakayi,ni bangarenane bansan zuwa" "hafsa komai munada a ktchn na wannan bangaren fa,amma ki zauna zan dafa mana indomie shi kadai na iya" murmushi tamasa bataso tace masa noo seda ya miqe tace cikin sigar wasa "Allah ka iya soya kwai,sabida ni bazanci ba kwai ba" bqnza ya mata kawai ya wuce... Maryam kwance asaman cinyar shaam tana narka shagwab'a,ita lallai seyaje da ita Abj bazata zauna ita kadai ba,kallanta yayi sosai yace "Maryam bazaki gane bane,bawai tafiyar ne bansan muyi dake ba wahala nake guje miki,tafiyar aiki ne fa" shura qafanta ta somayi ita lallai seta bishi,tallafo kanta yayi "Naji zanje dake kukan ya isa haka shi kenan?" kan tayi magana sega haleema nan kamar an jefo ta "Wani salon wulakncin ne kuma, a ranar girkina kazo ka tare anan?" kallonta yai sosai "Yau kwarton naki baze zo bane kike zare ido haka? Kuma waye yace dake kinada girki anan gidan ne? Dakike tafiya yawon duniya kiyi one month ko fiye baki san kinada girki ba se yanzu?" zuwa tayi tabure maryam a jikinshi "Inka isa kaci haqqina shegiya nake,wlhy dabanci zan maka anan gidan in baka tashi mun wuce ba"taci kwalar shi,maryam kuwa kai tsaye ta sharara mata mari "A gabana zakici zarafin mijina har haka,wlhy idan bakiyi waje ba zan miki ila,jaka kawai" zare ido tayi tayi cikin maryam, ai kuwa dukan tsiya maryam ta mata shammaz na tsaye se dariya yakeyi ganin yanda aka jibgi haleema,jikinnan na bleeching duk yayi rudu rudu yayi jajir,haka tafita da gudu sekace hauka sabon kamu,kallonta yayi "ki dena dambe maryama banaso,sannan kiyi shirin yin watanni uku,wannan takuramu zatayi qasar zamu bar mata koya kika gani?" tsallen murna ta daka ta haye saman jikin shi. *Bayan kwana biyu* Kwance hafsat take asaman resting chair tanacin banana, Muhammad yashigo ya sameta,fuskarnana a murtuqe,dauke kanta tayi sannan cikin tsoro tace "Ina wuni yaa muhammad?" kallonta yayi yace "Idan kin gama gudun nawa seki shirya nabaki awanni biyu zamu bar garin zuwa kaduna,kuma watanni biyu zamuyi acan" arazane ta kalleshi,tasan ta masa laifi tunda ta samu ta gudo suke wasan buya,dimin ko ko abinci sedai ta aika masa yaune shima ya shigo "yaa muhammad kayi hakuri,kowa fa bsan zanyi tafi yaba,se kawai aji bana garin?" "Nine kad'ai nakeda ikon sanin inda zaki da sanda zakije,so please banasan gaddama" haka taje tana parking tana kuka hadda shura qafa kuwa ita kad'ai,ta kira momy da umma dukta sanar dasu suka mata fatan alkhairi,har bayan ya shigo daya dawo tana nan tana mita tana shagwa ba,bata masan ya shigo ba,seta dinga maganganu tana shagwaba ita kadai,dariya ta bashi yakoma parlor yayi me isarsa sannan ya dawo "Ki fito muje idan kin shirya" batace komai ba ta soma janyo akwatinta bama wasu kayan ta eba ba,suna shiga mota dayake yau shi yake tuqi da kanshi sega Zee "J.A ina zakaje wai naga ana fitowa da akwatuna" kallon sheqeqe ya mata "Zamuje honeey moon na watanni biyu kinada matsala da wannan ne?" kanne idan ta tayi cikin jin zafin kala mansa tace "Banida hurumun sanin shige da ficen ka ne?" hara rarta yayi "Tun kwana hudu dasuka wuce rabon daki duba ni,ko wani abin kike buqata sedai kimun txt mesaage, kedai kawai kiji alert, meye naki da tafiya na? Ina kuma kece kikace na huta harna tsawon 6 month so ki barni plss" kan tayi magana ya soma riverse haka taja da baya su kuwa suka bar harabar gidan ...... A hanya kuwa bame wa wani magana,hafsa tanajin yunwa amma batayi masa magana ba wai ita adole fushi take, koda suma isa kaduna ta galabaita over, a moringa hotel sukayi masauki,har sukaje dakinsu kowa bewa wani magana,dama muhammad ya iya miskilanci kwanciyarshi yayi ya mata banza,dama kuma se bayan isha suka isa,kuka ta saka masa tana shura kafa,dagowa yayi ya kalleta "Hafsa lafiya dai" cikin kukan tace "Allah ni ka maidani gida,yunwa nakeji karna mutu a banza" dariya yayi "Da karki fada dai,tashi muje mu siyo kaza da fura" kallonshi tayi "Ni dai yau shinkafa zanci" waya yayi a reception aka kawo mata,sosai taci taje tayi wanka sannan ta dawo,kwanciya tayi can gefen gadon a takure,matsawa yayi sosai kusa da ita ya kamo hannunta "Hafsat wai mesa kike bani wahala ne? Kinsa nayi shirin tafiya batare dana tashi ba,me na miki kike guduna,bakida labarin kalar azabtar dani daki kayi na kwanaki biyunnan dan Allah karki qara mun hakanan,har abinci kasa ci nayi kwana biyunnan" runtse idanta tayi cikin sanyin jiki tace "kai hakuri bazan qara ba" hannu ya sanya ya shafi gefen fuskarta sannan ya tallafo kanta ya matsa sosai kusa da ita ya tsoma bakinsa a nata bata hanashi ba haka kawai takejin itama tayi matukar missing nashi, sosai ta tsotsi harshensa, ya muhammad kuwa bata inda baya lasar hafsa har ogan lasanya harshe yana lasa a hankali, hafsat yau dai duk seda takira yan garinsu tsabar dadin datakeji,kusa da kunnenta yazo sosai yaje "Hafsat zanji dadi idan kika sanya harshen kinnan me laushi kikai wasa da breast nawa inaso plsa kiyi" daurewa tayi ta laluba kuwa duk yanda taga yana mata idan yana shan breast nata haka itama ta masa, suka lalace atare ranar taga ihun dadi kuwa mara adadi, zancen dai yasha banban ne sanda yazo shiga ta marairace fuska jikinta na rawa tace "yaa muhammad kayi hakuri,wannan da zafi wasan yafi dadi" kallonta yayi dukda sunkashe fitilar yankwantar da murya ya rungumota jikinshi sosai "Hafsat wannan shine auren ai,kuma bazan miki da zafi ba i promise,wancen ma bansan baki saba bane dana miki sannu, idan kika saki jikinki bazakiji zafi ba sam" batace komai ba ya koma samanta a hankali, bazatace bataji zafiba kamar yanda bazatace bata ji dadi ba wanda babu irinshi kuwa wannan karon seda yagama taji zafi kad'an,Kallonta yayi bayan ya kunna fitilar wayarshi yace "Hafsa Allah ya barmun ke kinji,ni'imomin jikinki na dabanne,Allah ya qara miki dad'i" batace komai ba se "Zansha ruwa yaa muhammad" ruwan ya bata sannan ya dauketa zuwa bathroom. Mom Nu'aiym [2/21, 9:02 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 33 Washe gari kuwa haka suka tashi cikeda gajiyan tafiya,duk motsi daya da hafsat zatayi kuwa idan J.A na kanta,break fast ma dankanshi ya zauna ya feeding nata seda tayi dam abinta,sannan ya kalleta yace "Banasanki da yawan wahala hafsat,wannan ya sanya nazo dake nan garin sabida ki huta na kula bakya san zama gu daya" kallonshi tayi da fara'a "Amma da gaske zamu dade anan?" murmushi yayi "Ba wani dadewa dazamuyi nanda kwana biyu zamuje abj,daganan kuma muyi kwanaki biyar se mu wuce lagos bayan sati daya mu wuce london" zaro idanta tayi waje "Da gaske yaa muhammad,to kuma zancen kayan sawa fa? Tsaki yaja cikin tsokana yace "'yar qauye siya zamuyi sekace sanda mukazo duniya da kaya mukazo, har dubai zamuje yawo" turo bakinta tayi "Allah ni ba yar kauye bane kuma bazan maje dakai ba,ni skt zan koma abuna" murmushi yayi "kina burgeni hafsat,rigimanki sam baya qarewa wlhy,wasa nake aike ba er qauye bace yar birni ce,kiyi hakuri muje tare kinji" shagwab'e fuska tayi "Zakamun doki?" waro idanshi yayi waje "Lallai ma hafsatuwalle,doki fa?" shura qafa ta soma yi "Allah ni doki nake so kamun kuma idan baka mun ba bazan ma qara cin abunci ba" Duqawa yayi irin na yara da sauri ta dare ya dinga zagaye d'akin suna qyalqyale dariya atare...... *London soyayya me tsafta suke gabatarwa batare da kowa yasan cewan san d'an uwansa yake ba,shaquwa kuma me tsananin gaske ta shige tsakaninsu bazaka tab'a tunanin cewar ba auren soyayya bane sukayi, hafsat tana samun tsananin kulawa a wurin muhammad.... Wani yammaci hafsa ta siyo samosa da kanta tazo ta zauna kusa da muhammad,kallonta yayi duk tayi wani b'ulb'ul tayi ja se sheqi takeyi yace "'yar lukuta sammun samosar ko?" kallonshi ta dago tayi da yake yana kan kujera ita kuwa a saman carpet ta baje "Bazan sammaka bafa,baka gaba abunda kamun ai cewa kayi bazaka raka niba" banza ya mata ta zauna ta cinye samosar tas,aikam kan kace meye wannan harta soma kwarara uban amai tun tana iya tashi har yakai ta kasa,tsoro me tsanani ya kama muhammad,dakyar aman ya tsagaita taje d'aki ta kwanta se numfarfashi take da k'yar seda dare ta samun kanta,haka ya kwana yana jinyar ta,washe gari kuwa asuban fari tace ita agida zatayi samosa taci,ba yanda beyi ba ta kafe dole ya sa mata ido,aikam shima tana gama ci shima se amai,daga nanfa hafsat komai taci se amai lokaci daya dukta rame tayi baqi, muhammad dai daya gaji kaita asibiti yayi gwajin farko aka tabbatar masa ciki ne da ita watanninsa uku,a yanayin irgawarsa kuwa tun tarawarsu ta farko ta samu cikin,sabida yanzu kusan watansu biyu da sati biyu basa skt,kuma kwana biyu da tarawarsu suka bar qasar,wani irin farin cikine mara misaltuwa ya ziyar cesa seya tuna da maganar zee zee "J.A aurenka qaddara ne,cikin Nu'aiym ma qaddara ne,bazan qara haihuwa dakai ba wlhy,jiran ka nake ka sakeni in koma in auri masoyina na haqiqa abin qaunata,shina shiryawa zama uban yarana ba kai ba,wlhy na tsaneka J.A koda baka sakeni ba sena lalata mahaifata bazan qara haihuwaba kuma bazan kula ma da nuaiym ba kaje da yaronka" qwallan daya gangaro masa ya share yayi murmushi,koda sukaje gida dagata sama yayi cak yana ihun murna,kallonshi kawai takeyi sabida bata san meke faruwa ba,hasalima haushi ya bata batada lapiya yana wani ihun murna "Hafsa na kin gamamun komai,na dade ina san in qara haifar yaro jinina,ina san yara Allah beyiba se yanzu wlhy kin gamamun komai kece hasken rayuwata,na gode Allah dakika zamto part of my life" kallon sosai ta masa tace "yaa muhammad meya faru?" "ur pregnant my hafcy,and im so happy,i so much love my unborn baby" "ciki kuma" ta nanata a sarari,nida nake period kuma ka sani zakace ciki" a rude ya kira doctor akace su dawo,dubawa akayi haka nata tsarin yazo aka barta akan magunguna suka juya gida..... *Nigeria* Tunda suka dawo muhammad ya tare a part din hafsa,se rawar qafa yakeyi,motsi daya biyu seya furta "I love my unborn child,mamakinsa hafsa kullum cikin yinshi take wato dai da gaske yaa muhammad baze tab'a santa ba,ita haka zata qare duk mazan data aura basa santa,wannan mugum shuraim tsabar mugunta ya kashe mata uncle say,kullum yanzu setayi kukan rashin uncle say,dukkuwa da yake muhammad na matuqar kulawa da ita.... *Bayan watanni shida cur da auren muhammad da hafsat* Da safe muhammad na tashi yaga hafsat gaba daya ta fito da akwatunanta ta jere ko saman mirror dinta ba komai ta kwashe komai, kallon mamaki ya mata "Hafsat lafiya dai?" murmushi ta sakar masa "kacika mantuwa yaa muhammad,yaufa watanni shida cur da auren mu" mamakin aane ya qaru yace "To shine me hafsat?" juyowa tayi da kallon raini,da cikinta daya rigada ya fito tace "Gadai takar danmu nan na agreement,lokaci ya cika watanni shida,kuma indai ba neman magana zan tsaya yiba meye ze kaini kuma zaman dole,tunda har yau bakaji kana sona ba,kuma baka tab'a furtawa ba,kaga dama alqawari na maka cewar idan wata shida ta cika bakaji kana sona ba kuma baka furta ba,zan sake maka mararka kayi fitsari gidanmu zanje ka sauwaqe mun" wata iska me zafi yaja ya kuma fesar sannan ya dafe kanshi ya miqe yazo kusa da ita ya dafa kafadarta "Haba hafsat,yanzu ke dama da gaske kike wannan maganar" dago itanta tayi ta saka acikin nashi.."Da ana wasa da agreement da akayi arubuce har akayi sign ajiki? Kokai sanda mukayi na aure dakai ka manta ne,kalleni muhammad wlhy bari kaji inna zauna dakai baka sona shegiya nake,yaronka dakake tafadar kanaso kuma rabone,inshaa Allah zan baka abunka ina haihuwa so ka aikomun takardana danni yanzu gidanmu zani. Mom nuaiym [2/22, 9:11 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                              34 Qura mata muhammad yayi gama daya ta gama rud'ar dashi,kanshi se wani juya masa yakeyi yama kasan cewa komai "Nace ka sallameni malam nikan hanya nake nakuma rigada na shirya" zuwa yayi gabanta yana kallonta kallo daya zaka masa ka gano cewar hankalinsa baya jikinsa "Baby meye haka wai? Nine nace dake bana sanki? Wlhy ina sanki hafsat ina sanki sosai ba kadan ba,tun ranar dana fara ganinki naji ina sanki dan Allah ki janye wannan maganar" murtuqe fuska tayi "Na rantse da Allah yau senaje gidan mu, tayaya ma kai bakayi wasa da agreement namu na farko ba ni zanyi yanzu,ka manta roqon dana maka amma ka nace ko ka manta har tsohon my suruki to be yaje ya roqeka amma kayi mirsisi shan sigarin akuya,wlhy Allah tu da baka sona yau sena tafi" zare idanshi "Hafsa rantsuwa fa kike ta kwalawa? Cewa namiki bana sanki wlhy ina sanki sosai fiye da tunaninki,bakya ganin yanda nake kula wa dake hafsat na?" shwqeqe ta kalleshi ."kake dai kulawa na cikinka dake jikina J.A amma bani ba" mamakin jin takirashi da wannan sunan ya kasheshi a tsaye ya kasa koda motsi, haka taja akwatunanta kwaya biyu tayi gaba dasu se waje,shikam ma yana tsaye a gun tamkar an dasashi yakasa koda motsi sabida sam be kawo zata masa hakan ba,kuma ya hango seriousness a idanta,mota ta figa tsiyace tayi waje.......     Gidan Abba haris tawa kanta masauki, a gaban gidan ta ganshi zaune yana karatun news paper,ganinta da akwatuna ya sanya gabanshi fad'uwa sabida dama suna tsammanin badan Allah yayi wannan auren ba,da sauri yazo ya karbi daya sukaje parlor seda suka gama gaisawa sannan yace "Lapiya dai kuleken abba da asubannan da akwatuna haka?" murmushin qarya tayi "Abba dama zeyi tafiyane kusan wata biyu, shine yace tunda lapiya be ishan ba nazo gidannan kanya dawo" wani ajiyar zuciya ya sauke sannan yace yana fara'a "Lallai kam hakan ya dace tunda kinyi nauyi" haka tashiga ciki se murna su khairi keyi dajin zata musu watanni biyu. Tunda safiyarnan yake kiran wayanta baya samu duk ya damu,da yamma ya shirya yaje gidan daddy a tsammaninshi tana can,ganin an masa tarba me kyau ana tambayar sa yasu hafsa se jikinsa ya qara yin sanyi, haka ya musu sallama sannan yafito ya nufi gidan Abba haris, koda abba ya ganshi mamaki yayi don kuwa hafsat cewa ta masa yama wuce,ya kalleshi bayan sun gaisa yace dashi "Ashe ka dawo,tace damu watanni biyu zakayi a tafiyar shiyasa kace tazo gida,ko tafiyar ta fasu ne?" Take ya gano b'oyewa iyayen ta gaskian maganar tayi sosa kanshi yayi "Ea wato Abba tafiyar ce dai ta fasu, shine harnaje kaduna na dawo senan da sati daya" "A toto Allah ya kaimu,tana ciki kuwa bismillah kaje parlor na na maka kiranta" haka ya wuce jiki a sanyaye yana yaba wayo irin na yarinyar wato ma cewa tawa iyayenta tafiya zeyi,yana zaune ta shigo tana turin ciki,ko sallama bata masa yau,kallonta yayi tazo ta zauna nesa dashi sosai, tasowa yayi cikeda da tsanaki ya zauna kusa da ita ya kamo hannun ta yace "Mesa zakiwa Abba qarya? Mesa bakiyi maganar ainahin abinda ya faru ba?" turo baki tayi tace bayan ta had'e girar sama data qasa "Kai ba kanada baki ba,mesa baka sanar dasu takardar sakina ka cike ba idan mukayi wata shida da aure,ka sani wlhy muhammad bazan maka lamuni ba,nika rubutamun takar dar saki na in huta da wannan rayuwar" Sassauta murya yayi yace "Haba mana hafsat na,dan Allah ki dena wannan zancen,tsakanina dake har gaban abada muna tare,mutuka raba" kallon shi tayi "yaa muhammad kasan wai me ake nufi da haqiqani? Tofa ni iyakar gaskia ta kenan,sedai kotu ta raba mun aurena dakai" Langwab'e kanshi yayi ya qasqantar da kai " Hafsat dan Allah kiyi hakuri,wlhy kece hasken rayuwata,kuma ki dena cewa bana sanki wlhy nafi sanki fiye da kaina da komai ma" Miqewa tayi "Ni banida lokacin ka,kaje ka aikomun da takardar sakina" ta barshi gun a zaune tayi ciki, a kunnen Abba yaji komai,yakuma fahimci da matsala karya suka masa,bari yayi yaga iya gudun ruwansu dukansu danya fahimci muhammad bawai niyyar sakin ne dashi ba. Haka dai muhammad yafi sati biyu yana yawo kullum seya yiwa hafsat magiya,sunbar su Abba akan yana zuwa dubata ne wai ayyuka sun mata yawa gwara ta zauna anan,yaudai dayaje yaga hafsat borin nata yafi na kullum se kawai ya wuce gidansu,kai tsaye part d'in mahaifiyarshi ya wuce tana zaune ta idar da sallah,kallonsa tayi tace "Baban mamana lapiya dai?" dafe kanshi yayi yace "Ammy Hafsat ce" da mamaki ta kalleshi "Meya samu hafsat me sunan me gida?" Hawayen daine suka kwaranyo daga idanshi dayaketa tarewa,kwashe komai yayi ya sanar da ita tun daga farko haduwarsu har kawo wannan abun daya faru "Haba me sunan me gida,tayaya ina ganinka da hankali zaka aikata hakan? Da iliminka da komai,zaka je kayi auren yarjeje niya hadda kafewa da iyayen yarinyar suma roqeka,shiyasa mana akayi aure cikin qanqanin lokaci wlhy ka bani kunya kuma ni maza ka bani wuri" da sauri ya d'ago ya kalleta yace cikin rudu "Ammy karkimun haka,kece gatana banida kowa seke,dan Allah ki baiwa hafsat hakuri wlhy Ammy ina santa sosai bazan iya zama babu ita ba" kallonshi tayi sosai ta jima tana nazarin kalamanshi sannan da yanayin shi,saboda bazata iya tuna when last taga yana kuka ba lallai lamarin babbane "Yanzu ya kakeso ayi?" "Ammy kije ki baiwa hafsat haquri,cewa fa tayi lallai sedai muje court" kan wani yayi magana se kawai wayanshi yayi qara,hafsa ce da sauri ya d'aga sabida batama d'aga wayarshi "Wai kazo inji Abba haris" tafada da kukan ta da komai,gayawa Ammy yayi ta ce ya jira suje tare. Koda sukaje Abba haris fad'a sosai yayiwa muhammad da hafsat sannan yace ko bayan ranshi karyaji ana zancen wannan agreements din kuma lallai hafsa seyaci mata mutunci,haka suka kwasa suka wuce gida Hafsat tanata uban kuka,acan ma Ammy hakuri ta ringa bata seda taga ta sauka sannan ta musu sallama. Cikin dare sun kwanta batare da kowa yawa dan uwansa magana ba,se kawai hafsat ta tashi tayita uban kuka,tana tausayawa kanta sabida ita kadai tasan wuyar datasha sabida rashin muhammad kusa da ita ta kasa gane wane kalan baqin jinine da ita maza basa santa,jin kukanta ya sanya ya tashi zaune,janyota yayi jikinsa yace "Haba hafsat,yanzu tsabar k'iyayyar da kikemun ne ya sanya kika zauna tsakiyan dare kina kuka,inama ace ina hanyar dazan sassauta miki wannan azabar wlhy danayi bazan iya rayuwa baki ba hafsat kece farin cikina wlhy ina matukar qaunarki ki yarda dani,ina sanki fiyeda tunaninki" banza ta masa ya riqota ya juyoda ita ta fuskan cesa sosai "Menene damuwanki dani hafsat? Mena miki wanda bakyaso? Mesa bakya sona" "yaa muhammad tsoro nakeji wlhy tsoro nakeji" hannunshi ya sanya ya d'ago mata hab'a "meyake bai tsoro? Tsoron me kikeji hafsat?" "Ina tsoron son danake maka,ina mamakin qaunar danake maka,ina mamakin zuciya ta,yanda nakeji game dakai ban tab'a jin hakan gameda ko wane namiji ba,wai kasan sanda nake gida bana bacci,juyi nake ina tunaninka,Idan ma na samu baccin ya d'aukeni yinshi nakeyi cikeda mafarkai barkatai duk naka,na saba da kwanci cikin ni'imtaccen jikin kannan,bana iya cin abunci sabida na saba munacin abincin a k'warya d'aya bana iya komai,wankan ma da kakemun bana iya yiwa kaina,kalli fa duk nayi baqi,yaa muhammad baka kula na rame ba,dan Allah karkamun kamar sauran maza ka soni niba dodo bace mutum ce,ka qaunaceni niba jab'a bace bare kace zaka guji wari,wlhy yaa muhammd se bayan naje gida na gano rayuwata a tarwatse take idan baka cikinta" Wani sanyi ne yaji yana ratsa ilahirin jikinshi rungumeta yayi tsaaam ya manna sumba a wuya "Ina sanki fiyeda tunaninki,ina qaunarki fiyeda yanda danakewa kaina,bakida ta biyu a wurina kuma bazaki taba samu va,wlhy ki yarda dani hafsat ina sanki sosai ki dena tsoro na ina kuma qaunarki fiyeda tunanin me tunani" murmushi ta masa,ta narke fuska sosai cikin shagwab'a tace "Yaa muhammad Nayi misaing nama wlhy,nasha wahala plss nika bani insha" "Bayan kin gama bani wahala,rashin na kusan sati biyu da kwanaki abana iya runtswa sena rama bazan baki ba" kwantar da kanta tayi saman qirjinsa "Dan Allah ka bani harshenka in tsotsa,nayi missing tsotsarshi sosai,duk sanda zansh swt sabida ya debemun kewar shi senaji taste din ba iri daya ba sam, kuma inaso insha wannan ta daura yatsanta saman lips nashi, da wannan ta nuna breast dinshi da kuma" seta rufe fuskarta da tafukan hannayenta duka biyu, dago da kanta yayi ya cura bakinshi acikin nata mamaki ta bashi yanda ta kaiwa harshensa cafka,tashiga tsotsa sekace wata zararriya, baji ba gani haka ta lasheshi,harshenta ne har saman wuyansa da kunnensa ranar dai muhammad ne ya zama starin mota itako driver,Har yan twins dinshi na qasan abar tabi tana tsotsa tana wasa da dasu, ihun dadi kam ya shashi ba adadi,daga qarshe suka faranta ran junansu basu suka saurarawa juna ba seda suka gaji over sannan tukunna,da shagwaba tace ita bacci zatayi dakyar ya lallab'ata tayi wanka,har sun kwanta tace dashi "yaa muhammad dan Allah duk abinda na maka wanda na sani da wanda ban saniba ka yafemun,kuma ko bayan bananan ka roqar mun yafiyar kowa,haka kawai se in riqajin kamar mutuwa zanyi" kallonta sosai yayi sannan yace bayn ya rungumeta "Meya kawo wannan maganar kuma hafsat na? Dan Allah ki dena inshaa Allah bazaki mutu yanzu ba" murnushi dai ta masa batace komai ba. Da Asuba juyin duniya yayi hafsa ta tashi tayi sallah amma shiru,haryaje masallaci ya dawo bata farka ba,ya dinga tashinta amma ina koda ya birki tota se kumfa yagani a bakinta idanta ya juye yayi fari fat ba alamun numfashi a tare da ita.... Mom Nu'aiym [2/23, 8:56 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 35 Gaba d'aya muhammad hankalinshi ya gama tashi, da gudunshi kuwa yayi hanyar waje,buzun megadinsu yace wa "Bani gawayi da sauri bani gawayi" cikin rashin fahimta me gadin yace "Ranka shi dad'e Me wuta kho mara hi?" cikin takaici yace mara dan Allah yi maza ka daka mun me yawa yanzunnan sauri nake,dashi aka daka gawayin yaje ya jute a cup ya zuba ruwan dimi, da sauri ya dawo ya goge mata baki ya ringa sanya cokali yana mata d'urensa a baki gashi bata cikin hayyacin ta, haka harya samu ta hafiye fiye da rabin shi,aikam segashi tafara amai me baqi da kore sosai sosai, tun tana iya yunkurawa harta soma yinsa daga kwance ganin wannan jiran baze haifar masa da komai ba ya sanya ya kwashe ta xuwa asibiti ya gano poison taci,duk ya gama diriri cewa kuma tunaninsa ya tsaya cak, karb'ar gaggawa aka mata a asibiti,kuma atake suka gano poison ne taci a abunci kuma me yawan gaske,muhammad na tsaye yana jiran fitowar doctor's d'in,waya aka masa akan ga Ammy tanata fitar da kumfa a baki,she's unconcious ma self,kukan gaske ya saka ya sanya aka kawo masa ita a wannan asibitin,poison iri daya suka sha,kuma irin wanda yake dadewa yana zagayar jikine kafin yafara aiki, Ita dai kam Ammy an samo matsala sabida yashiga jikinta sosai amma ita dai da sauqi,dama yana kashe wa slowly within 24 hours Allah yasa anyi saurin ganewa aka kawosu asibiti before d time,hafsat ce da sauqi sedai zasuyi inducing nata ta haihu sabida babyn ya mutu already,muhammad yasha kuka inda atake ya soma tunanin inda sukaci abinci jiya atare,sabida police report da ake buqata, se kaiwa da kawo wa yakeyi a parlor yabaro asibitin, yasan sunsha lemo gidansu hafsat amma banda hafsat shida Ammy ne kawai, in hakane shida ita ya dace su kamu banda hafsat,yama rasa tunanin dazeyi gaba d'aya,zama yayi ya dafe kanshi,can kuma se gabanshi ya fad'i tunawan da yayi an kawo musu yoghurt anan b'ngaren na hafsat dasuka dawo jiya kuma shi be shaba,sabida baya shan abu me sugar se sugar free,ko lemon na gidansu hafsat sparkling soda ne kawai yasha, zabura yayi yaje ya samu hasano,wacce itace ta kawo drink d'in,kallonta sosai yayi ya murtuqe fuska yace "Wannan milk da kika kawowa Ammy na dakuma hafsat jiya damuka dawo,daga ina ya fito?" Cikin rashin damuwa tace "Da safe ne jiya Karime tazo dasu guda biyu,tace wai kaine kace ta kawo nan kuma kar wanda yasha se hajiya natane,shine jiya naga Ammy babban baquwane kuma nasan batashan cock shika dai ne kuma a gidan se wannan shine na kawo musu daya daga cikin madarar" kallon sosai ya mata jeki ki kiramun karimen, miqewa tayi suka dawo tare da karimen "Waye ya baki madarar dakika kawo kika ce nine na baki kawo? Kuma yaushe mukayi dake cewar kar wanda yasha na hafsa ne?" ita dinma dai cikin rashin damuwa tace "yallab'ai ai haj zainab ce tace kaine kace abani in kawo,har cewa nayi da itan ai haj hafsat bata nan tace dani zata dawo ne a ranar wai shiyasa na isar da saqon naka" nisawa yayi ya soma gano da babbar matsala sabida wlhy ko zainab seta fuskanci hukunci "Ke hasano sanar dani ina dayar madarar da sauran wacce suka sha jiya?" gyaran zama tayi. "Suna nan acikin fridge har sauran rabin ma" "Jeki kawon su yanzu,ke kuma karime karbo kizo muje wurin zeezee din" Da sauri sukayj yanda yace.... A tsaye suke ya miqa mata madarar yace k'arbi kisha wannan,saqon dana baki ki kaiwa hafsat ne,tasha kuma ya mata aiki sosai,inda kika taimaka ma har Ammy tasha kuma duk sun kamu da sharrin ki,se kema kisha yanzu in ga ko zeyi aiki a naki jikin" zaro danta tayi waje,cikin tsiwa tace "Wlhy bazan shaba,kuma Allah ya sanya cikin ya zube gaba daya" be fahimci kalamanta ba ya sanya hannu ya kwasheta da kyakyawan mari yace cikin qaraji "Shine zaki zomun da hauka,shine zakiyi poisoning matana? Meta miki zaki kashe tq? Yanzu gashi sabida wani gruges na banza zaki mun hauka ki hada har uwata,rashin hankakin naki har ya kaiki ga tunanin yin kisan kai?" zare idanta tayi jin ya ambaci kisa tace "Nashiga ukuna ni zainab wlhy ni ban saka maganin kisa anan ba,na zubewar ciki ne kawai na saka mata" wanketa yayi da wani marin "shine zasuna riqan fitar da kumfa a baki,shine likitoci zasu tabbatar cewar deadly poison ne? Kuma inna zubar da cikine ya akayi yayi affecting har Ammy? Idan na zubar da cikine kema karbi kisha muga yanda ze miki" kin sha tayi se kuka da take tana rantse rantse akan na zubar da cikine, a fusace yace "Zanje da madarar nan aduba wlhy sena hallaka ki idan hakanne" yana barin dakin ta janyo wayarta ta kira qawarta data kawo mata maganin datake iqirarin na zubar da cikine wato *HALEMAH SHAMMAZ*. Mom Nu'aiym [2/25, 9:03 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 36 Da madarar yaje asibitin,gwajin farko aka tabbatar itace,hafsa tasha baqar wahala sabi acikinta aka yayyakan yaron cikin kusan 6 month ya soma girma sosai, haka aka ciro mata shi,kuka kam tasha shi,muhammad kuwa be duba dan gantakar dake tsakaninsa da zee ba ya sanya aka damqeta zuwa police station daga ita har qawarta haleema kuwa...... Ammy taji sauqi ba laifi sedai kam ita nata yazo da gaddama sabida hawan jininta ya tashi sosai kuma yaqi sauka,sedai adua,a bangaren hafsat kuwa kwance take tana sharar kwallah,ba wai wahalan datasha ba mutuwar yaron cikinta, sosai ta qwallafa ranta akan wannan cikin, tana nan khairii nata mata sannu sega muhammad nan, ficewa sukai gaba daya suka bar musu dakin, da sauri ta miqe zaune,shi kuwa ya kama hannunta ya riqe tausayinta ya sanya ya kasa maganq,rungume shi tayi tace "Yaa muhammad nashiga uku nq" tsamm ya qara matse ta ajikinshi yanajin tsananin tausayinta da sabuwar kaunarta na ratsa ilahirin jikinshi "Noo plss hafsat stop saying that baki shiga komai ba se alkhairi inshaa Allah sharrin su ze koma musu ne ki barsu kawai" ita batasan meya faru ba ta dago kanta ta kalleshi "su waye yaa muhammad?" be damu ba ya bata amsa "Su zeezee mana itana da matar yayanki haleema,sune sukayi poisoning naku keda Ammy da madarar da kukasha,kuma wlhy tunda suka mun asarar baby na sesun gane shayi ma ruwane wlhy" kasa magana tayi tsabar mamaki poison kuma? Ta nanata a ranta,ga mamakinta kuka taga muhammad yanayi sosai kuma,kasa yin kukan tayi ta soma bashi baki "Hafsat tsabar zainab batada hankali zatayi kisa,kisan ma wai mahaifiyata data haifeni da kuma matana mafi soyuwa agareni da yaron danafiso tunkan zuwanshi duniya,yanzu gashi tamun asaran shi wlhy sena hukuntata sena gane cewar doka tana aiki har cikin gida" Itadai bata iya magana ba sam. Bincike ya nuna cewar ita zainab batasan guban na kisa bane,haleema ne takawo mata a zuwan na zubar da cikine kawai,sannan batasan cewar tare da Ammy za'a shaba,ita kuwa haleema tasan na kisa acewarta tunda take da shaam hafsat ce take takura ta,yanzu dan taga ita bazata sameshiba shine ta hadashi da wata can ake wulakntata ita, tunda ta gane mijin Qawarta ne hafsat ta aura se kawai ta dinga zugata akan su hallaka hafsat,ganin bazata yadda da kisa ba ya sanya ta bullo ta hanyar a zubar mata cikin ashe fa dama kisan ne.......hafsat sun dawo gida duk sun samu lapiya,anan kuwa aka soma zana court inda atake sanida duk sunyi confessing aka yankewa zee zaman gidan kaso na wata uku ko tarar kudi naira dubu dari biyar yayinda aka yankewa haleemah zaman gidan kaso shekaru ashirin, tun a cotun ta haukace ta soma sambatu kuwa iri da iri, kamar wata zautacciya duk wani mugun aiki datakeyi haka ta dinga fada kuma tunkan ajata zuwa gidan kason Allah ya amshi ranta acikin dubannan mutane,wannan abin ya daga hankalin zeezee yayinda mahaifiyar haleema ta haukace a take ta wurgar da zani tayi waje,shammaz kam beso hakan ba sam yaso yaga tuban haleema ta koma ga Allah amna yazeyi haka Allah ya tsara tata kalar rayuwar,yayi kukan abubuwan data masa musamman daya kasance tana bin maza wanda ya dade yana zargin hakan, Zeezee kuwa ba irin hakuri daba ta baiwa muhammad ba amma yace sam baze hakuraba ya saketa saki daya...... Sosai hafsat ta tsorata da abubuwan dasuka faru, kallonta muhammad yayi sosai yagano tun fitar sa tana wurin daya barta,zama yayi kusa da ita ya kamo hannunta yace cikeda kulawa "Hafsat dan Allah ki mayarda komai ba komai ba,inshaa Allah zaki samu wani cikin,kuma ire iren su haleemah bazasu sake samun galaba akanki ba,Allah baze bari ba kinji" kwantar da kanta tayi saman qirjinsa tace "Ba wannan araina yaa muhammad tsoron duniya kawai nakeyi wlhy,ni a rayuwa mena yiwa haleemah dazata bini da wannan sharrin ban tab'ajin banji zafin mutuwar koda kiyashi ba kamar yanda sam banji zafin mutuwar haleemah ba, abubuwan data aikata sun firgitar dani ace arayuwa mutum ba Allah a ranshi? Baya tsoron mutuwa baya tsoron had'uwarsa da Allah sam,baka gudun cin hakkin mutane ka mayarda neman maza kamar shan pure water da aurenka,sata sekaje beran masallaci, yaudara ba komai bane,ni naji tsoro wlhy" kallon sosai ya mata "Nagodewa Allah daya bani ke a matsayin mata,yanzu zan qara da wani mamakin akan halayyar dan adam, zainab da kika gani yar aminin mahaifinane tana soyayya da wani saurayi aka ce seta aureni suna matuqar san juna kamar me,nima kuma inada budurwata sunanta khaleesat, kinsan yan siyasa suna dasan auren hadi tsakanin yayan masu kudi haka mahaifina ya dage akan sena auri zee, nasha zagi a wurin zeezee ba iyaka azatanta santa nake amma duk bana kulata,sabida mahaifina daya bani amanarta,saura kwana biyu daurin aurena da ita taje gun wannan saurayinta,ina zaune khamal yamun waya akan ya ganta hotel ita dashi sun shiga daki,mukazo nida shi a mota muka kwana haka kuwa se 10 na safe suka fito atare daga dakin ita bata ganni ba amma nina ganta sarai, haka na roki kamal akan ya bar maganar iya mu, aka daura aurena da zeee, har mukayi wata daya da sati biyu ban taba kwanciyar aure da ita ba,bansan meya sanya zee ta kawomun kanta ba sedaga baya,bayan ta haihu na fahimci cewar ta gano tanada ciki ne yasa tazomun kar wani abin ya taso,sabida na lissafa ba'a haifar yaro da 8 month kenan haduwar ta da wancen ta samu shigar ciki,haka akazo Nu'aiym se rikidewa yake yana komawa tsohon saurayinta sannan da karfi da yaji ta sanya na maidashi gun mahaifiyata, sam banajin qin yaron se tausayi dayake bani sabida nasan bashi da gadona,kuma uwar ma ga cutar dashi,se nabi ta musulunci tunda akace idan har 6 month sun cika sannan aka haifi yaro koba naka bane anbar maka shi, har yau dum raini. Wayon da zee kemun bata san na san da wannan ba,in taqaice miki yau shekaru na hudu cur banyi kwanciyar aure da zee ba sam bata bari,roqona take in saketa taje ta komawa saurayinta,abinda ya sanya ban saketaba sabida indai zataje tofa sena sanarwa duniya yaronta ba nawa bane,sabida in tabbatar har D.N.A tst namana nidashi wani lokacin an tabbatar ba jinina ajikinshi ,so yanzu ke me zaki kira wannan? Mezata cewa Allah?" Mom Nu'aiym Se haquri ina busy ne kuyi manage da wannan. [2/28, 9:06 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 37 Rungumar sa hafsat tayi kawai ta soma kuka,be hanata kukan ba dan ya kula zuciyarta tanada rauni matuqa, haka tayita kukan har bacci ya saceta agin, kyakyawar fuskar ta kurun ya qurawa ido yana murmushi, aranshi yaji ya qaunar yarinyar tanada imani sosai banda haka a wannan zamanin ai abubuwan haka suke tafiya. *Bayan kwana biyu* A kitchen tana tsaye tana fere dankalin hausa tana shirin musu potatorita da hot coffee, mamakin rashin sanin mafakar muhammad takeyi jiya sam se waya ya mata zeje kano ya dawo kuma basu sake yin waya ta bincika ma baya part nashi ga wayanshi a kashe,wannan abin ya dameta matuqa,ata bayanta taji an rumgumota qamshin turarensa ma kadai ya isa sanar mata cewar shi dinne wani nannauyan ajiyan zuciya ta sauke ta juyo gaba daya ta sake wuqar dake hannunta ta ce cikin shagwab'a "Hubby ka tayarmun da hankali,ina ka shiga?" qugunta ya tallafo gaba daya ya manna mata sumba a wuya "Naje kano ne Swttest kuma ai na sanar dake,acan na jefar da waya na,yin wlcm back na sim cards ya dauki time,kuma dayar nabar charger anan ta dauke ba charge" turo baki tayi "Dukda haka sekamun waya da wani wayar,kofa abinci sena gagara ci,ina tunanin lafiya shiru,se messages naketa aika maka amma shiru" "Im so sorry habeebty,nayi laifi kuma bazan qara ba,yanzu mezan samu yunwa nakeji" "Barin gama hada wannan, zan maka milkshake seka ci abinci" janyota ya qarayi sosai ya rada mata a kunne "Dan Allah ki ajiye zancen girkinnan nifa yunwar ki nake ke nakesan ci" murmushi ta same masa cikin jin kunya,ya sake cewa "Kefa bazaki cini ki qoshi ba,nafi tuwo dadi kuma ai kinsan wannan" kanta ta cura acikin qirjinsa cikeda jin matukar kunyan yanda yake zaro magana sufa maza basuda kunya ko? Ta ayyana a ranta,batayi aune ba taji ya sure ta tana cillar da qafafuwa amma be direta ko inaba se saman gadon ta, cakulkuli yasoma yi mata,tun tana iya dariya harta soma sarqewa,yar guntuwar rigar jikinta ya cillar ya soma wasa da dukiyar fulaninta,runtse idanta tayi sabida kunya gashi akwai wadatuwar haske a dakin kasancewar rana ta somayi,batayi aune ba taji bakinshi akan breat nata wani numfashi taja ba shiri,wani sanyine ya ziyarceta da dadi wanda batasan ta ina suke zuwar mata ba,dayan hannun ya daura akan dayan breast din atake ta soma numfarfashi sama sama, ba shiri ta daura hannunta saman kanshi ta soma shafa a hankali tana masa surutai iri da iri, lasarta yaso mayi tako ina yana jin qarfin yin abun sabida yana ganin cewar qwazonsa da qwarewarsa be tashi a banza ba,sabida tanajin dadi kuma ta nuna masa tana jin dadin sosai, a haka yaketa mata wasanni har suka biya buqatarsu, bayan komai ya lafa ya kalleta yace "Hafcy naje na mayarda Nu'aiym gidan su babarsa na kuma sanar dasu niba dana bane,nama gayawa su hajiya kuma kowa na nuna masa shaidar jinin mu da akayi, yanzu kuma sekinyi haquri da abu biyu,na farko zaki kularmun da wannan gidan na tsawon shekara daya,na biyu kuma zakiyi rashina na kusan shekara daya,zan tafi london yin wani course shekara daya kumq ba hutu bare nayi tunanin zuwar muku hutu" daga kwancen datake ta zabura ta dafe qirji "Shekara daya yaa muhammad? So kakeyi in mutu ne wai? Ina zan iya zaman Niger baka nan? Kumama ninace dakai zan iya haqurin zama bana samu. Wannan abun dakake mun, nifa wlhy mutuwa zanyi ka sabamun da abun dadi ka wanice tafiya wai bama sati daya ba ko wata shekara,cab di wlhy bazan yarda nikam" kawai seta qara fashewa da wani uban kukan me ban tausayi,dakyar ya rarrasheta akan idan yaje da wata biyu ya mata alqawarin zata bi bayanshi dakyar tay masa shiru.......haka ya shirya ya tafi har a air port soso se kuka take shima dakyar ya iya boye kwallar dayakeyi. *Bayan watanni biyu* Tunda jirginsu ya sauka a london take ta faman raba ido ta hangoshi,se can ta ganshi cikin qananun kaya blue and whitw sun bala'in masa kyau,kasa tsaida hawayenta tayi sannan ba shiri ta ruga da gidu ta fada jikinshi tafi mintuna biyu bata sakeshi ba kaikace rabuwa zasuyi bawai haduwa sukayi ba yanzu, shima kanshi ta bashi tausayi,suna isa gidan dayake zama amatsayin haya wanka kawai tayi tasha fresh milk ta zauna kusa dashi, ba bata lokaci ta cura bakinta a nashi ta soma tsotsa,har mamakinta yake yanda ta zare yau ko kunyar ra ajiye a gefe,tayata yayi amma ga mamakinshi tafishi zaqewa se lasarsa takeyi tako ina,haka ma yau koda akazo gun manager itace ta hau samanshi, ta fayyace masa ayoyin dake kanta wanda ta shawo bayan tafiyar sa agin Ruma, yaji dadin hakan kuwa sabida muhammad mutum ne me wayewa yana san wayewar kuma. Kallonta yayi bayan sunyi wanka "Waini yau ina kunyar ne? Se zarewa naga kin qarayi" cikin rashin damuwa tace "Kunya tabi kewarka wlhy,sun gudu abinsu ni dama zaka qaramun irin na dazu dana gode" janyota yayi jikinshi yana dariya ya soma mata cakul kuli suna kwasar dariya, dataga bayada niyyan saurara mata itama ta soma masa suka dinga haukan dariya su kadai kan su soma wasa da trow pillows suna zagayar dakin da gudu.... Second to the last lage,anzo kqrshe ma saura page daya kacan....mom nu'aiym [3/3, 8:59 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅    Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)   Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*                                 38 Soyayya ake tsafta tacciya cikin jin dadi  da gamsar da juna ba kadan ba,a london hafsa ta soma master's dinta  tana renon cikinta dayake da watanni shida a wannan lokacin, sam barka zaka gansu ba fada ba tsangwamar juna,sun manta duk wata damuwa dake damunsu ada....Bayan watanni hudu kuwa hafsat ta haifi yarta kyakyawa me kamada mahaifinta,murna a wurin muhammad ba'a magana aka sakawa yarinyar suna Nana khadeeja wato sunan Ammy suna kiranta da suna Nana, sosai suke san yarsu kuma suke godewa kyautar da Allah ya musu,haka bayan tayi 40 days suka dawo niger gaba daya Ammy kam farin ciki ya kasa a kanta akan wannan jikar tata se washe baki takeyi. Maryam ma tanada ciki dukda ta kwana biyu bata samu ba,se bayan haihuwar hafsat da watanni hudu sannan ma ta haihu ta santola ya ranta kyakyawan gaske dayayo kamada sayyid matuqa,aka saka masa suna sayyeed ana kiransa da uncle say tun tashinsa,likita mahaifinshi kece dashi kasancewar yaci burin yaro yayi komai irinna kawunsa. *Bayan shekaru bakwai* Hafsat yaranta biyu da Nana da kuma Junior wanda shima sayyeed aka saka masa amma ana kiransa junior se uban qaton cikinta dake gabanta,ta bane tana ta faman shan rake,sabida cikin ba qaramun kwadayi ya sakar mata ba gashi yayi wani qato dashi,kallonga muhammad yayi yana dariya yace "Big Barrister haka akeyi wai abun bako tayi kinzo nan sabida karma ki samma wani raken ko?" dariya tayi "Kaga yaa daddyn junior nifa dankai na gudo kai ba cikiba amma komai kaga ina sha sekasha,yaudai bazan baka ba" tabe baki yayi "Ai nasan shan raken na meye mace da tsohon ciki se jarabar tsiya,ni yau karki wani ce zakizo mun part,bazan iya ba" turo baki tayi hadda kwallan gulma "Haba daddyn junior? Ni yaushe nayi jaraba? Gaskia ka dena banaso,kaga part din nakama bazan kara zuwa maka ba,kai kuma kaje ka nemi wanda ze maka girki" dariya yayi yace "wasa nake miki baby na,zomuje kiji wani abun" dakyar ta miqe ya ja hannunta seda sukaje daki ya kalleta yace "Nace jaraba kince noo,bayan kuma gashi nan ke dinnan jarabar ke damunki da tsohon cikinki amma kinsan yanda ake ayi jaraba, kin wani biyoni,to bazan ba" pillow ta janyo ta nausa masa,daga nan suka soma wasannin su,haka ta dale kanshi ta cinye abunta tass,yana matukar jin dadin rashin gazqwarta akan buqatunsa sam koda cikinnnan bata nuna masa qosawarta dashi akan kwanciya,ya sani yana takurata amna ya zeyi? Baya iya hakura da zumar hafsat kona kwana biyu, shiyasa kamar jaka haka take agunsa duk inda zasuje suna maqale da juna... Tammat bi hamdillah Abinda muka fada na amfani Allah ya sanya ku qaru kuma ku amfana dashi,Allah kuma ya sanya Alkhairi acikinsa,wanda mukayi kuskure Allah ya gafarta mana. Ina miqa godiya ga.. *Bakin rijiya's fan's group* *Taskar Billy g* *Duniyar makaranta* *Pherty zahra novels group* *sophie G novels group* *Inspring stories* *Haske fans group* Dama wanda ban fadi sunan su ba duk kuna raina. Mom Nu'aiym