*AZAAD JUNAID* The young Billionaire Na Jeeddah Aliyu *Haske Writers Association* *mg's skincare* Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩 Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaranjiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️ Shin kinafama da Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata? Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫 Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare duk wnd yy using set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali😘just start placing ur orders dearies DNT be left behind Available product👇 Herbal whitening black soap:3k Beauty kit:11k Blacksoap/molato whitening soap: 3500 Bridal kit:20k Muna maraba da masu siyan daya ko sari Chat 08062991549 Call 08064532391 Facebook: mg's skincare Instagram:glow_with_mgs Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩 Then @mgs skincare gat you covered 💯 Now is time to glow😍 Pamper ur skin🦵 Shine like bride👰🏻‍♀ Glow🧖‍♀️ 💯 tested nd trusted🤝 Guarantee Sannan munada frames masu kyau shima siyan daya ko sari 07046881166 08062991549 Sannan gamai bukatan abinci, cakes,meatpie,samosa nd spring rolls, traditional juices nabiki shima yy hanzari yy mgn 08062991549 Mungode🤝 Free Page 1.... "Wai ke Salima wacce irin mace ce sau nawa zan faɗa miki ban amince da wannan tafiyar taki ba?" Ta cikin mirror da take zaune a gabanshi tana gyara daurin d'an kwalin dank'areren lace da ke jikinta ta aika mishi Kallon uku saura kwa6o tare da ta6e bakinta. Kana ta mik'e ta nufi wata k'atuwar show glass mai d'auke da tarin designers shoes & handbags tsaye tai ta k'urawa show glass ɗin idanu tana nazari wanda ya dace tasa Ta d'auki half cover golden in colour na company lamis elwan tare da handbag ɗinsu. Ta ra6a gefenshi ta wuce abinta sosai hakan ya k'ara linka masa 6acin rai da yake ciki, ya dunkule hannunshi na dama ya nushi bango d'akin ba tun yau ba yake nukurkusa bakin cikin matarshi Salima wacce shi kanshi a yanzu ya fara yarda da tafi k'arfin shi. Bai isa ya faɗa ta ji ba tabbas a wannan karon zai tabbatar mata da shi ke iko da ita ba ita ke iko dashi ba. Cikin zafin nama ya bi bayanta da k'arfi yake taka steps hakan ne yasa yai nasarar cin mata a downstairs parlor. "Salima! Yadda ya kira sunanta da k'arfi yasa housemaid ɗin da ke cikin parlor suka fice da sauri ba tare da sun bari ya had'a idanu dasu ba. Nanny Lacey da ke zaune a dinning room tana ba wa k'aramar 'yar su Ahlam abinci tai sauri daukarta ta nufi d'akin yara da ita. "Wannan wane irin wulak'anci ne ina magana za ki fita ki bar ni wato ga mahaukaci ko?" Ya k'arasa magana yana huci. "Look Azaad Kar ka nemi tashin hankali dani domin karshenta za ka dawo kana regretting. Ta faɗa ba tare da ta juyo ta dube shi ba ta ci gaba da tafiya. "Da gaske nake yi ban amince ba asalima inaso ki rubuta resigning letter, lokaci ya yi da za ki zama full housewife ki kula da tarbiyyar 'ya'yanki domin gaba d'aya tarbiyyar su a gur6ace take. Kina kallon abin da ya faru yau a school ɗinsu yaushe aka haifi Anisa da har za tai dambe da schoolteacher ɗinsu..... "Enough is enough Azaad! Ta katse shi cikin tsawa da tada murya tuni sautin muryar ta ya kere nashi kana ta ci gaba da faɗin "Na fahimce dukan da aka yiwa Anisa kai ko a jikinka asalima so kake yi ka d'auki laifi kachokan! Ka dora min. Idan har kana jin ba za ka iya sauya mata school ba, to ni zan iya domin sani kanka ne ban dogara da abin hannunka ba.... "Ya ishe ki Salima! Nace ya isa! Har sau nawa kike so a sauyawa Anisa makaranta sa'o'inta suna aji huɗu a secondary amma ita tana jss three shin hakan Kaɗai bai isa ya haska miki lalaci 'yar ki ya yi yawa ba?" "Yar ta Azaad kace 'yar ta wato ni Kaɗai Allah ya ɗorawa tarbiyya yara kai ubansu ba da kai ba ko?" "Kwarai kuwa domin kece uwa ke ya dace ki zauna gida cikin 'ya'yanki ki kula dasu ba ni ba. Abin da ya rataya akaina shine hakkin ci da sha kuma dai-dai gwargwado na tsare muku su. sannan ki tuna ina da hakki akanki sai mu share watani uku Salima ban had'a shinfid'a dake ba. Angaya miki ni dutse ne ko waliyi da bana buk'atar mace?" "Yanzu kan na fahimce inda ka dosa Azaad kawai ka fito fili ka faɗa min ba ka so ci gabana. Allah ya rufa min asiri na dogara da kaina bana tsayawa jiran sai kayi min, shine kake so ka tauye ni to bari ka ji inaso aikina domin bana ko tantama da banida kud'i ko na fito gidan babu da ba yadda za a yi kai ɗin ka aure ni. Cike da takaici yake K'are mata kallo ko wane furunci dake fitowa daga bakinta k'ara mishi 6acin rai yake yi, shi mutum ne da bayaso hayaniya yana da matuk'ar sanyi hali shiyasa a koda yaushe Salima take zantar da hukunci kuma dole ya bi koda hakan bai masa dad'i ba. Amma tsabar sanyi halinsa ba zai ta6a bari ta fahimci hakan ba, ita kuma anata 6acewar basira take gani kamar tsoronta yake yi. "Ki sani Salima furuncin nan kin sha faɗa min shi ba sau daya ba, ba sau biyu ba. Kin faɗa min shi bila'adadin, kuma yana cikin kalamin ki da ke matuk'ar sosan rai "ka ga Azaad ka bar ni haka nagaji da saurare tsofaffin maganganun ka, domin duk ciki abin da ka faɗa babu sabon abu a wurina kana bata lokaci ne kawai. Ta gyara mayafin jikinta wanda shi babu duk d'aya ta buɗe k'ofa ta fice abinta, ya bi k'ofar da ta fita da kallo zuciyarsa tamkar za ta fasa k'irjinshi ta fito ya d'auki dogon lokaci tsaya a falon kafin sake haura upstairs saidai a wannan karo tangamemen bangare shi ya nufa katon parlor na farko ya fara wucewa kafin ya iso na biyu wanda yafi na farko tsaruwa saidai na farkon yafi girma, ya buɗe k'ofar gilashi wacce za ta sada shi da Master bedroom ɗinshi, kaitsaye resting chair ya nufa ya zauna, ya shiga shafar kwantattace saje shi da hannunshi na dama. Ya rasa a duniya me Salima take nema ne duk wani jin dad'i duniya Allah ya bashi ya tara dukiyar da har jikokin 'ya'yanta za su mora to me ya rage da za ta nema face lahirarta. Kuma gaba d'aya a tsarinta babu lahira a ciki a shekaru 16 da aure har kawo yau ɗinan ba wani abu da zai bugi k'irji yace ya samu na farin ciki, kullum rayuwarshi a k'unci take gashi Allah ya bashi duniya amma ya ga-gara samun farin ciki ya tashi maraya ba uwa ba uba a wurin haihuwar shi mahaifiyarshi Hindu ta rasu, a hannun kakar shi Jadda ya taso wacce ta haifi mahaifiyarshi yana degree shi na farko ya rasa mahaifin shi wanda ya rasu yabar tarin dukiya ta fitar hankali, da kuma tarin 'ya'ya domin yabar matan aure uku mahaifiyar Azaad ce ta uku bayan rasuwar ta ne ya sake wani aure, Kuma duk a cikinsu ita ce mai d'a d'aya Azaad. Azaad Junaid matashi ne ne d'an shekara 47 cikakke business tycoon ne wanda tauraronsa ke haskawa a faɗin duniya. Ya mallaki dukiya wacce shi kanshi a yanzu bai san adadinta ba. Azaad Junaid mutum ne mai matuk'ar sauk'in kai ba za ka fahimci hakan ba har sai ka zauna dashi. Azaad yana da matuk'ar kyauta da alkhairi ga tallakawa yana kyautatawa na k'asa dashi yana da gaskiya da rik'on amana, mutum ne mai rik'o da addini sai dai san baya daukar reni yana son a girmama shi matuk'a. Babbar matsala shi a duniya ita ce matarshi Salima sun yi aure a bisa so da k'auna, Salima mace mai zurfin ilmin boko na addini ne ya yi k'aranci a gareta, ba yadda ban yi ba akan ta zurfafa ilmin nata na addini amma abin yaci turo dole yana ji yana gani ya zuba mata idanu. Ga wasu Dabi'u da halayenta da take dasu, sun sha ban-ban da na matan hausa/fulani mace ce mai bala'in girman kai da dogon buri babban burinta sunanta ya zagaya duniya, tayi fice fiyye da mijinta. Mahaifinta mai kud'in gaske ne kuma ita ce babban 'yar shi sai k'anneta maza uku sai Wanda suke 'yan uba su biyar maza biyu mata uku. Salima tayi karatu mai zurfi akan kasuwanci saboda kwarewar da iya kasuwanci yasa mahaifinta Alhaji Kabir Dala tun kafin ya rasu ya mik'a mata ragamar kula da babban kamfaninsa na building and contracting company wanda a halin yanzu ita ce mafi rinjayi hannu jari a company. Burinta ta mallake company ita Kaɗai, sai da 'yan uwanta sun amincewa su sayar mata da hannun jarinsu tasha alwashi sai ta mallaki company kamar yadda ta mallaki wasu k'anana companies ɗin nasu. Azaad Junaid ya haɗu da Salima ne a wani meeting a birnin tarayya Abuja, dukansu su na neman contract d'aya na gina wasu gidaje a nan birnin tarayya Abuja tun kafin su fara gabatar da meeting ɗin ya ji firar da Salima take yi da wata colleague ɗinta yadda samun contract ɗin yake da matuk'ar muhimmanci a gareta da irin hasara da za ta tanka idan ta rasa shi, saboda har makudan kud'ad'e ta yi bribery ɗin wasu daga mukarabai gwanati. Duk abin da take faɗa batasan cewa akan kunne Azaad Junaid sai kawai ya yi sanyyaye murmushi domin yasan muddin ya ri gata gabatar da presentation shine zai sami contract ɗin, tausayi ta bashi matuk'a ba tare da sanin ta ba yasa aka bata contract ɗin duk da akwai 'yan kwangila da suka fi ta amma kasancewar the young Billionaire ne ya yi magana sai aka bata, a lokaci ba k'aramin dad'i da farin ciki ta ji ba. Suna fitowa daga conference room ta mik'a mishi tattasan hannunta da nufi su yi shaking hands sai ya ɗaga mata yatsun shi biyu, ya wuce wurin motar shi tun daga lokaci ta dinga bibbiyar shi har ta sami nasarar suka k'ula alak'a ta friendship daga bisani abuta ta rikide ta koma soyayya. Azaad Junaid yana matuk'ar son Salima ita ma haka abin yake a wurinta, ko wane su commitment ya yi mishi yawa kullum cikin neman duniya suke. Sai su share dogon lokaci ba su haɗu ko a waya su na d'ibar kwanaki ba su yi waya wa junan su ba. Suna kawai sun yi aure a haka ta haifi Anisa tun tana jinjira ta mik'a ragamar kula da ita a hannu Nanny Lacey Anisa tana da shakaru 6 ta sake haifar Airah wacce ita ma ta bi ayarin tawali'u hannun Nanny Lacey, tun daga haifar Airah tace ta gama haihuwa Allah da ikonsa babu zato ba tsanmani sai ga ciki Ahlam ba yadda bataso tayi abortion amma ciki yak'i ya fita, a lokaci ba k'aramin tashin hankali suka yi ita da Azaad ba sai da ya kai fagge furta mata muddin ta zubar mishi da ciki a bakin aure ta shine dole ta hak'ura. Duk a cikin yaranta Ahlam ta fiso rashin samun kulawarta duk watani tara ne da ita amma duka bai fi sau biyu ko uku da tasha nono Salima ba. Shiyasa babu wata shakuwa a tsakanin su daga Nanny Lacey sai siblings ɗinta sai Kuma Daddynta Kaɗai tasani. Saboda duk yawan commitment ɗinshi ya kan ware lokaci na musanmman ya zauna tare da yaranshi wani lokaci har daukar su yake yi tare da Nanny Lacey wacece ta maye musu gurbin uwa su fita kasashe waje yawon buɗa ido. Anisa ta taso da masiffafen girman kai da faɗin rai ga d'an banza rashin kunya da fitsara, kowa kallon bai isa ba take mishi kullum Madam Salima cikin sauya mata school take ko Kaɗan bataso a faɗi laifin yaranta, dama bahaushe yace inda saniyar gaba tasha ruwa anan ta baya za ta sha, duk wani iskanci na Anisa K'anwar ta Airah ta kwashe tass duk da haka Airah tafi ta dama domin ita idan Nanny Lacey ta tsawa ta mata tana ji. Ba yadda Jadda ba tayi da Azaad ya k'ara aure amma yak'i saboda duk duniya ba abin da Madam Salima ta tsana irin kishiya, sai kuma ta taki sa'a da Azaad Junaid ba shi da ra'ayi mace fiyye da d'aya. Shiyasa take tsula tsiyarta iya son ranta yanzu haka Jadda bata da daraja da za ta shiga bangare ta alhali su na rayuwa a gida d'aya asalima ba wacce ta tsana irinta saboda kawai tana faɗa mata gaskiya sai ta d'auki k'iyayyar duniya ta ɗorawa mata. K'arfaffiyar ajiyar zuciya Azaad Junaid ya sauke kafin ya mik'e ya sauya kaya jikinsa zuwa tsadaddiyar shadda getzner ash colour, ya ɗora hula zanna bukar wanda ta dace da kayan jikinsa. Ya saka penny loafers a k'afarshi yayin da yake fitar da sihirtattace k'amshi designer perfume na poundland black dust, ya tattara wasu documents da ke kan center table tare da wayoyin shi har guda uku. A hankali yake taka steps duk da ranshi babu dad'i ba kowa bane zai fahimci hakan ba, saboda koda yaushe fuskarshi a murtuk'e take bashida yawan fara'a ko abu ya yi mishi dad'i sai dai kawai ya yi murmushi, ba kowa a downstairs parlor muddin yana gida housemaids ba su kai da kawo ko wane su zai ya kame kanshi, musanmman yau da gida yake a hartsune dole su yi taka-tsan-tsan. Tun daga main gate direbanshi mr Richard ya hango shi da ya tashi ya jawo mota ya iso daff dashi kafin mr Richard ya fito ya buɗe mishi k'ofa ya budewa kanshi. ******************* Kuka take yi sosai tana d'auke da marar lafiyar K'anwata Amal wacce bata motsi, wuyanta ya langwa6e ya yi baya bata da ban-banci da matatciya tunaninta ma ta mutu ne. Cikin hak'i ta shiga d'akin kakarsu wacce ta haifi mahaifinta tsabar tashin hankali da take ciki yasa ta manta da dokar da Dadda ta shinfid'a musu na hanasu shiga mata d'aki daga ita har k'anneta guda biyu twins Amal da Amrah. Ta ban kad'a curtain da k'ani mahaifinta ta fara yada ganinta akan shi, da sauri ta nufe wurinshi cikin muryar kuka take magana. "Baffa Don Allah ka taimaka ka duba min Amal bata numfashi na shiga uku Baffa ba dai Amal ta mutu ba?" "Ke! Ya daka mata tsawa yana muzurai kamar zai kife ta da mari, cikin hargowa ya ci gaba da faɗin. "Kar ki sake ki kawo ta kusa dani. Na duba ta ni likita ne ko ke ba ki san hanyar asibiti bane?" saboda tsabar iskaci da rashin mutunci za ki kawo min ita" "Allah yasa ta mutu mu rage mugun iri jinin arna" Hajja Dadda ce ta faɗa tana baro wajen zamanta sai lokaci Aslamiyya tasan da zamanta a falo, a fusace cikin rashin tausayi ta dank'e dantse hannun Aslamiyya ta hankad'a ta waje da k'arfi daga ita har Amal ɗin take d'auke da ita suka faɗi yayin da Aslamiyya ta faɗa kan hannunta na hagu, ta kwalla k'ara Amal kuma kanta ya buge sumunti hakan ne ya haddasa mata jan dogon numfashi ta farfado daga suman da tayi, duk da tsananin zogi da hannun Aslamiyya ke mata hakan bai hana mata rerafawa akan gwiwoyinta biyu ta jawo Amal cikin jikinta a matuk'ar tsorace ta ɗago ta tace. "Amal! Amal! Kina ji na kuwa?" Don Allah idan kina ji na ki buɗe idanuwanki nagani, Amal karki mutu ki bar mu. Muna matuk'ar buk'atarki ni da Amrah ki tuna ba mu da kowa sai junan mu. Don girman Allah ki tashi kin ji K'anwata?" Cikin tsananin zafin ciwo Amal ta shiga k'ok'arin buɗe idanuwan nata dake rufe ruff! Da kyar da sudin goshi tai nasarar buɗe su sai dai dishi-dishi take gani Aslamiyya. *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske Writers Association. Top Ten Takun Haske Batch: A Free page 2.... Tafiya mai nisa gaske suka yi kamar za su bar gari, kafin suka nufe wani katafare kamfaninsa na sarafa danye gold mai suna AJ Gold Company ba wai iya sarafawa company ya tsaya ba. Yana siye tsofaffin gold ya mayar dashi new model, su na kuma siyarwa. Gate ɗin company Kaɗai abin kallo ne za ka yi zaton shima da gold ɗin aka k'era shi, sakamakon yadda yake shek'i da daukar ido. Da sauri securities dake tsa-tsaye birjik su na ba wa company tsaro, biyu daga cikinsu suka wangale musu gate. Sai daff da k'ofar reception mr Richard ya yi parking d'aya daga cikin security dake tsaro k'ofar ya hanzarta buɗewa Azaad Junaid k'ofar mota ya fito cikin tsananin miskilancinsa da k'assaita ya ɗagawa ma'aikatan da ke mik'a masa gaisuwa hannu, k'ofar reception ɗin ta tsuge kanta kasancewar ta gilashi ce. Kaitsaye ya nufi elevator ya hau wanda zai sada shi da office ɗinshi dake hawa na 6 mutane biyu ne suka take masa baya har izuwa cikin tangamemen office ɗin nasa. ***************** Gani Amal ta buɗe idanuwanta yasa Aslamiyya ta sauke k'arfaffiyar ajiyar zuciya, ta shiga k'ok'arin ɗaga ta sai dai kashh! Ta kasa sakamakon yadda ta ji hannunta ya rik'e kamar an daure mata shi da igiya. Sai kawai ta fashe da kuka mai ta6a zuciya ta kifa kanta akan cikin Amal ta ci gaba da rera kukanta, Amrah ce ta shigo gidan bakinta d'auke da sallama hannunta rik'e da bak'ar leda mai d'auke da koko da ta siyo musu, su karya kumallo. Kafin ta k'arasa sallamar idanuwanta suka yi tozali da siblings ɗinta zube a tsakar gida ga Aslamiyya tana ta faman kuka batasan lokaci da ta jefar ledar koko ba, ya buge bango ledar ta fashe kokon ya malale akan sumunti, ta kwasa da gudu ta nufi wajensu. Aslamiyya na ganinta ta ɗago idanuwanta da suka fara renewa zuwa jajayye. "Subhanalillah! Miyya me ya faru ne me kuke yi anan kuka me kike yi?" Kusan a tare Amrah ta jero mata wad'annan tari tambayoyi ba ko shed'awa. "Amal ce ta suma na zaci ko ta mutu ne na kawo ta wurin Dadda ta duba ta, shine ta hankad'o ni waje" Ajiyar zuciya Amrah ta sauke cike da tausayi 'yan uwanta. Har sai yaushe Allah zai yanke musu wannan bak'ar wahala da suke ciki?" Kullum addu'ata da fatanta Allah ya kawo wanda zai za me musu bango majingina, ya yi musu gatan da suka rasa. wanda zai fitar dasu daga bala'in k'unci da tsangwama da suke ciki. Ranta a 6ace ta ɗago Aslamiyya ta mik'ar da ita tsaye "Daina kuka Miyya in da sabo yaci ace kin saba da tozarci da ake mana, a gidanan. Da wahala tana kisa da tuni an shafe babin mu a doron duniya, sai Kuma gashi ubangiji ya yi mana tsawon rai duk da yadda akeso kawo k'arshen numfashin mu. Ta k'arasa magana tare da sunkuyawa ta ci-ci6i Amal da ke kwance tana numfashi guda-guda, tsabar yadda ciwo ,ya cinyeta yasa ta dawo tamkar 'yar shekara huɗu ba 13 uku ba. Ta nufi d'akin da ya kasance mallakin su a gidan. Za ka sha matuk'ar mamaki ace d'akin da suke ciki mai rai ke kwana a cikinsa amma su ko a jikinsu saboda sun ri ga da sun saba da rayuwa a ciki. Akan wasu tulin tsomakarai wanda su ne suka kasance wurin kwanciyarsu Amrah ta shinfid'e Amal idanuwanta taff da hawaye sai k'ok'ari danne su take bataso Miyya ta gani, duk da kasancewar ita ce k'arama amma tafi Miyya k'arfin zuciya Aslamiyya irin jinsi mutane nan ne masu raguwar zuciya da rauni batada hayaniya ko Kaɗan ga sanyi hali kamar ruwan fridge, ga ta da matuk'ar hak'uri duk abin da za ai mata bata ta6a tankawa sai dai taci kukanta in tagaji tai shiru. Rayuwarta gaba d'aya ba abin da tasani ta kuma saba da shi irin kuka. Duk cikin su uku Amrah ce kawai halinsu ya ban-banta da nasu ita ma Amal halinta sak! Irin na Miyya ne. Amrah ta dubi Aslamiyya da ke tsaye a jikin k'ofa tana ci gaba da aikin nata na kuka tace. "Wai Miyya ba za ki hak'ura ki daina kuka nan haka ba?" Wallahi ki yiwa kanki k'iyamulaili ki adana raguwar hawayenki kada su k'are akan wad'anan mugaye mutane azzalumai da babu burbushin imani a zuk'atansu" Sai da Miyya ta ja majina da ke k'ok'arin fito mata ta k'ofufin hanci ta maida ta inda ta fito, ta kuma ja dogon karan hancinta da yatsunta biyu kana ta k'arasa shiga d'akin ta zauna kusa da Amal, ta shiga shafa kanta a hankali Amal ta ɗago farare idanuwanta ta dubi yayar tasu wacce ta maye musu gurbin uwa da uba tasaki mata murmushin k'arfin hali ita ma Miyya murmushi tayi hawaye na zuba akan kumatunta. "Sannu Amal Allah ya ba ki lafiya Allah ya kawo miki k'arshen wannan ciwo, Allah ya canza mana k'addarar mu ya kawo mana sauyi wata rana mu d'and'ani rayuwar farin ciki. Da sauri Amrah ta durkusa ta rungume Miyya suka fashe da kuka, ba ka ji komai sai sautin kukansu gwanin ban tausayi, sai da suka ci kuka iya son ransu kafin su rarrashi kansu. Sai lokaci Amrah ta tuna da kokon su na naira hamsi da ta zubar zuciyarta tai mugun bugawa saboda tasan sanadin tashin ciwon Amal hadda yunwa a ciki, zubur ta tashi ta nufi k'ofar fita Miyya na kwalla mata kira ko juyowa ba tai yi ba ta fice daga gidan. ******************** Tun shigowar shi office ɗinsa ya kasa aiwatar da aikin komai ga tarin files zube akan desk da zai yi signing up. Amma ya ga-gara tabuk'a komai cire hular kanshi ya yi, ya aje akan desk ɗin ya shiga shafar suma kanshi. Damuwa tana neman tai mishi yawa tsoronshi daya kada ciwon hawan jini ko ciwon zuciya, ya kama shi. Ga dukiya mai tarin yawa Allah ya albarkace shi da ita amma ya ga-gara samun farin ciki da natsuwar zuciya kullum cikin k'unci da 6acin rai yake. K'arar k'ararawa da ya karad'e office ɗin nashi ya dawo dashi daga duniyar tunani da ya nutse, ya kai duban shi akan allon cctv da ya ke iya gani wanda keso shigowar office ɗin, amininsa kuma MD na company sa Abdul-hakeem Daura ya gani tsaye yana jira ya buɗe masa k'ofa ya shigo, kasancewar k'ofar tana using da code dole sai in shi ya buɗewa mutum zai iya shigowa da remote control ya yi amfani k'ofar ta zuge kanta Abdul-hakeem ya baiyana. Duk faɗin duniya ba shi da wani amini d'an uwa sai Abdul-hakeem saboda 'yan uwanshi da suka had'a uba ba k'aunarshi suke yi ba. Su na bak'in ciki da hasada da daukakkar da Allah ya yi mishi. Burinsu a kullum bai wuce su sami hanyar da za su kawo k'arshen sa. Da shigowar Abdul-hakeem ya yi tsaye ya saka Azaad gaba yana kallo, nan take ya fahimci halin damuwa da yake ciki. ko bai tambaye shi ba yana da tabbaci Madam Salima ce damuwar shi, saboda duk faɗin duniya ita ce matsalarshi ita ce mai jefa shi halin damuwa. Ya girgiza kai haɗi da jan kujera dake kallon Azaad ya zauna. "Aj ya kamata ka dinga sassautawa kanka yawan tunani kada ya zo ya shafi lafiyarka. Tunani ba shi bane solution ɗin matsalolin ka ba. Azaad ya ja gwaron numfashi kana ya lashe lips ɗinsa, cikin zazzak'ar muryarsa mai dad'i da tafiyar da ruhin mai sauraren shi yace. "Ni kaina ba so tunani nake yi ba Abdul zuwa min kawai yake yi. matsaloli su min yawa ga na 'yan uwana ga na iyalina da wane zan ji?" Yanzu duk wanda ya gani zai dauki cewa na fi kowa farin ciki a duniya saboda ina da tarin dukiya ba asan cewa wani tallaka wanda bai da ci yau balle na gobe ya fi ni domin shi, yana samun natsuwar da kwanciyar hankali daga iyalinsa. "Zance na gaskiya Aj kaine ka za6awa kanka wannan matsala, Salima ba za ta ta6a sauyawa ba. To saboda me kai ba za ka nemowa kanka mafita ba?" Tun yaushe ni da Jadda muke ba ka shawara ka k'ara aure amma ka k'i sai ka zauna bak'in ciki mace d'aya ya kashe ka. "Please Abdul-hakeem ka fahimce matsalata ba ta k'arin aure bace. sai fa ka ji dad'i abu kake neman k'arinsa. "Matsalarka kenan Aj idan aka yi gabas sai kayi yamma, dole fa sai ka cire tsoron Salima ko don farfado da tarbiyyar 'ya'yanka ka tuna yaranka mata ne dole su na buk'ata ingantattaciyar tarbiyya. Idan mahaifiyarsu ta kasa sai ka nemo wacce za ta maye gurbinta mana. Mik'ewa Azaad Junaid ya yi hannayenshi zube cikin aljihun wandonshi, ya taka a natse zuwa gaban widow da ke kallon titi. Yaye labule idanuwanshi suka sauka akan motoci da ke kai da komuwa. Shima Abdul-hakeem mik'ewa ya yi ya isa daff dashi kana ya dafa kafad'arsa. "Ka yarda dani Aj aure shine yafi dacewa da kai ka tuna kullum shekarunmu k'ara tafiya suke yi dole sai muna samun natsuwar da kwanciyar hankali, so ka ga kenan don ka k'aro aure ba wani abu bane. Allah yasani kayi hak'uri iya hak'uri da Salima lokaci ya yi da za ka d'and'ani zak'i da gard'i dake cikin aure" D'an gajere murmushi Azaad Junaid ya yi wanda ya tsaya iya fatar bakinshi, kana ya juya yana facing Abdul-hakeem. "To naji idan ma na amince zan k'aro aure wa zan aura?" Sani kanka ne Abdul tun daga lokaci da na auri Salima ko mafalki ban ta6a kallo wata 'ya mace naji ina sonta ba. Ta ya ya ka ke tunani zan yi aure?" "Mtsss...! Abdul-hakeem ya ja siririn tsaki da ke baiyanar da takaicinsa a fili. "Ba dole bane sai ka ji son mace za ka aure ta ba, kai da za ka yi auren huci haushi ina ruwanka da soyayya. Alhaji ka amince kawai ka ga aiki da cikawa ni da kaina zan nemo ma matashiyar budurwa wacce Nonuwanta suke tsaye cakk! Ka sha shagali abinka. Zaro idanuwa Azaad Junaid ya yi tamkar ya ga abin tsoro kana yasa dariya wanda rabon da ya yi irinta har ya manta. *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A Free press 3.... Amrah na fita bata zarce a ko ina ba sai wani k'aramin super market, kamar za tayi siyaya sai da taga hankali mutane baya kanta. Ta dinga tsintar biscuits da Madara na sachet tana cusawa cikin zaninta batare da ta bari an ganta ba ta fice da mugun sauri. Gudun kada a ganota da fitarta ta kwasa da gudun bala'in ta nufi gida, cikin sa'a babu kowa a tsakar gida tai wuff! Ta shige d'akinsu kamar wacce aka jefo. Daga Aslamiyya har Amal sai da suka firgita domin a zatonsu ko Dadda ce. Kallo daya za ka yi wa Amrah ka gano bata da gaskiya sai wuk'i-wuk'i take da idanu kanta a k'asa ta k'araso cikin d'akin. Ta cire hijab tare da kayan da ta sato ta ajiye ta d'auki wani tsohon kofi wanda tun na aure mahaifiyarsu ne bata ce dasu k'ala ba ta fita gindin famfo ta nufa ta taro ruwa rabin kofi. Koda ta dawo d'akin Aslamiyya tana jujjuya biscuits da madara ɗin. "Ga ruwa ki k'adawa Amal madara ta haɗa da biscuit ko da na koma wajen mai koko ya k'are shine na siyo mana madara da biscuits sai dai na manta ban siyo sugar ba. Sai da na iso k'ofar gida na tuna. Tana magana Aslamiyya ta k'ure ta da manyan idanuwanta, sai da ta saki 6oyayyen numfashi kafin tace. "Ina kika sami kud'i Amrah?" Iya sanina naira hamsi muke dashi kin Kuma ri ga da kin siyo koko ya zube" "Keɗai miyya kin cika bincike wallahi" "Bincike dole ne Amrah banaso wani mugun abu ya faru daku saboda 6ata gari sun yi yawa mutane basu da imani. "Uhm...miyya ki dinga kyautata zato Abba Saleem ne ya bani kud'in wankau da nayi mu su na kwanaki, da basu biya ni ba. To shine Ina dawowa daga siye koko na haɗu shi a k'ofar gidanshi ya bani" "Amrah!" "Miyya!" Amrah ta kira sunanta kaman yadda Aslamiyya ta kira ta, har tana had'awa da turo baki. "Amrah idanuwanki sun nuna min akawai rashin gaskiya da kika yi faɗa min me kika aikata?" "Da zan shigo na haɗu da Baffa Sani a k'ofar gida nai kaman ban ganshi ba shine yaso ya dake ni dalili da yasa na shigo da gudu kenan baya ga wannan ban yi komi ba. "Ya yi miki kyau Amrah duk abun da na hane ki ba za ki hanu ba ko?". "I'm sorry mommana! Cewar Amrah tana rik'e k'unneta da hannunta daya yayin da ɗayan ke rik'e da cup. Miyya ta yarda da k'arya da Amrah ta shara mata dalili kuwa tasan tana bin bashin kud'in wankau gidan Maman Saleem. Sai kawai ta mik'a hannunta ta kar6i cup ɗin ta haɗa mu su madara, Amal ta fara ba wa tasha ta k'oshi saboda iya ruwan madara take iya sha. ********************** Sosai Azaad Junaid yake kyakyata dariya Abdul-hakeem ya rik'e baki yana kallonshi. Saboda shi bai ga abin dariya ba, da kyar ya yi controlled dariyar tashi, kana ya nufi water dispenser ya tsiyaya a handle cup ya sha fiyye da rabin ruwan. "You're insane Abdul in ban da kana mahaukaci ko zan yi aure sai na rasa wacce zan aura sai k'aramar yarinya?" Murmushi Abdul-hakeem ya yi kafin ya nufi kujera da ya tashi akai ya sake zama, ya dubi Azaad da girar ido a ɗage... "Gata nake so nai ma Aj ka samu ka more garar da muka dad'e muna kwasa" "Na yafe idan kana so mai nonuwan a tsaye ka nemi abarka, ni kuma nai maka alk'awari ni ne zan biya kud'in sadaki" "Wai gatse kake min?" "Miye abin gatse anan Abdul naga kaman ka fi ni buk'ata" Ya k'arasa magana yana gintse baki. "Shikenan Aj tun da ba ka so a yanzu amma nasan komai dare dadewa sai ka nemi hakan. "Allah ya tsare ni da abin kunya" "K'ara sunnah shine abin kunya?" "Ba haka nake nufi ba auren k'aramar yarinya ne ba zan iya ba. "Are you sure?" Abdul-hakeem ya faɗa yana murmushi. Sai da Azaad ya nemi daya daga cikin cushion ɗin da ke cikin office ɗin ya zauna, kafin ya furta. "Hundred percent sure! Har Abdul-hakeem ya yi yunk'uri sake furta wata magana ya katse shi ta hanyar faɗin "Please Abdul mu ajiye zance mai nonuwa a tsaye mu yi aiki da ke gabanmu" Daga haka suka shiga tattaunawa aKan contract ɗin da suke, aiki akai. Sai yamma lis suka rabu Azaad ya nufo gidanshi a downstairs parlor ya tarar da Nanny Lacey tare da Ahlam ke wasa da toys ɗinta. Airah tana Assignment princess Aneesa kuma tana d'akinta, tana chat da friends ɗinta. Nanny Lacey ta gaida shi ya amsa ta hanya ɗaga mata hannu, Airah ta ɗago tare da furta. "Welcome Daddy! Ita ma hannu ya ɗaga mata kamar yadda ya yi wa Nanny Lacey, kaitsaye ya wuce bedroom ɗinshi dake upstairs. Wanka ya yi ya shirya cikin dark blue ɗin jallabiya ya wuce masallaci sai da ya sallaci sallar isha sannan ya dawo gida ya shiga 6angaren Jadda koda ya mai aikinta Mero ya tarar a falo, Jadda tana bedroom ɗinta. Direct d'akin ya nufa tana zaune akan sallaya da casbi a hannunta, ya nemi gefen gadonta ya zauna. Cikin natsatsiyar muryarshi ya gaidata ta amsa mishi cikin kulawa. Kana suka zarce da fira sai ga Mero ta shigo da k'aton tray mai d'auke da tsadaddin warmers ta sauke a gabanshi, tasake fita ta dauko mishi lemo da ruwa. Jadda da kanta tai mishi serving tuwon semovita da miyar agusi taji tantakwashi da tsokar busasshe kifi. Sosai ya ci tuwon saboda shi mutum ne mai matuk'ar son abincin mu na gargajiya sai dai kashh! Allah bai had'a shi da wacce ta iya ba. Madam Salima ko ruwan zafi na shan tea bata da lokaci dafawa. Duk wata kulawa da ya dace ta ba wa mijinta housemaids ke yi mishi ga Azaad da shegen kyamkyami. Kuma gaba d'aya 'yan aikinta Christan ne ba Musulma ko d'aya, shiyasa Azaad ya k'auracewa abincin 6angarenshi sai dai ya zo na Jadda ya cika cikinshi. Bayan ya kammala cin tuwonshi hadda su taune k'ashi Jadda ta tsare shi da kallon tausayi, har sai yaushe Azaad zai zama cikakken mutum?" Domin a ganinta bai cika mutum ba rabin mutum ne, tayi iya k'ok'arinta akan ya k'ara aure abin yaci turo dole tana ji tana gani ta zuba mishi ido, duk da al'amarin iyalinsa yana ci mata tuwo a kwarya kullum cikin masa addu'a take Allah ya kawo mishi sauya. "Anya kuwa Datti wannan rayuwa da ka za6awa kanka za ta fishe ka kuwa?" "Jadda in-sha-Allah nesa ta zo kusa domin na sanar da Salima ta ajiye aikinta.... "Dallah..! Rufe min baki sakaran banza nusari kullum cikin faɗar haka kake yi har yau ka sa aiwatar da komi. Saboda haka na ba ka nan da wata uku ko ta ajiye aikinta ta cikakkiyar matar aure ta amshi ragamar kula da gidanta hannun arna. Ko kuma ni na nemo maka wacce za ta kula min kai da yaranka" "Ki yi hak'uri Jadda in-sha-Allahu ba ma zai kai mu da haka ba . "Sai ta Kai mu domin ba ajiye aikinta za ta yi ba ni kuma idan har ba mutuwa tai min sauri ba sai na auro ma 'yar mutunci mai nagartattaciya tarbiyya. "Ni dai ina k'ara ba ki hak'uri Jadda" "Hak'urin ka na banza da wofi, ka dai ji na faɗa ma wata uku na ba ka, idan ba haka ba k'arin aure ya zame maka dole. Ba kuma shawartarka nake ba ko jin ra'ayinka. "Jadda rigima Keɗai sam bakyaso a zauna lafiya mu ajiye wannan zance ki sha maganinki" Ya k'arasa magana tare da dauko mata ledar maganinta da ke aje akan bedside drawer, bayan tasha magani ya shafa mata na ciwon k'afa sannan ya koma 6angareshi. Har zuwa lokaci madam Salima bata dawo gida ba, Kuma tun fitar ta da safe. Dama haka take yi in tafita sai baba ta gani take dawowa dabi'unta sam ba su yi kama dana musu aure ba, tafi Kama da masu zaman kansu. D'akin yara ya wuce ya tarar da Airah tana game a laptop princess Aneesa, tana aikin nata na chat ganinshi yasa ko wace ta dakatar da abin da take yi. *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A Free page 4.... Zaune suke a katafare falon farmhouse da ya kasance mallakin Alhaji Yusuf Junaid su taru ne kamar yadda suka saba taruwa a can baya. Domin gudanar da secret meeting ɗinsu. su 8 ne maza 6 mata biyu kowa ne fuskarshi a turbune da ka dube su za ka hango tsananin 6aci rai da suke ciki. Hakan ya samo asali ne da har yanzu sun kasa cimma dad'en burinsu akan d'an uwansu Azaad Junaid. D'aya daga cikinsu ne ya fara magana wanda da ganinshi yafi sauran mugunta da zafin rai, zuciyarsa na tafarfasa yace. "Tsakani da Allah nagaji da jiran gawon shanu, zuwa yanzu yaci ace mun shafe babin Azaad a ɗora k'asa kuna kallo dai yadda kullum k'ara daukaka yake yi dukiyarshi sai habbaka take yi kamar shuka ana zuba mata fertilizer mun kasa yi komai. Idan har dukanku kwakwalenku sun daina aiki ni zan sa ayi masa mai gaba d'aya haihuwa da hanji... "Dakata Ahmadu! Hajiya kubra ta katse shi a tsawace dama can kawarsu bata gamo ba, duk lokaci da suka haɗu sai sun yi uwar watsi. Ta ci gaba da faɗin "Kai miyasa ka cika fushi da daukar zafi?" Garin bak'ar zuciyar taka za ka iya kai mu ka baro kai mana shiru mu ji dalilin kiran gaggawa da muka samu daga babban yaya. "Ke Kubra ki shiga taitayinki dani nafi ki rashin mutunci wallahi... "Dallah ya isa haka ku kenan da zarar kun haɗu ba za ku ta6a rabuwa lafiya ba. Sai kun sai da hali. Alhaji Yusuf Junaid ne ya kawo k'arshen musayar yawun nasu. Ya ci gaba da faɗin. "Dalilin da yasa na me ganinku da gaggawa jiya ne Alhaji Buba ya zo min da labari wani shararren boka sha yanzu magani take. Aikinsa yana ci domin ya yi masa aiki cikin kwana uku buk'atarsa ta biya. Shine naga dacewar mu kai masa ziyara watakil adace ya kawar mana da Azaad. "Haba Yaya har yaushe za ku gano aikin bokaye nan duk k'arya da yaudara ne?" Kawai ku bar min wuka da nama ku ka aiki da cikawa 'yan ta'adda za nemo su yi mishi yanka rago. Hasheem ne ya yi magana yana hura hanci duk cikinsu shine mai k'anana shekaru. Alhaji Abdallah ne ya kar6e zance ta hanyar faɗin. "Kai dallah rufe mana baki idan har kai ba ka da hankali mu ba sakakkaru bane irinka, muddin muka sa aka kashe Azaad ta wannan hanya jami'an tsaro ba za su yi shiru ba, za su tsananta bincike kasancewar Azaad babban mai kud'i. Nan take za a gano mu. Saboda haka mu gwada zuwa wajen bokan ya kashe mana shi." "Shikenan Babban Yaya gaba ɗayan mu, mun amince gobe da sassafe sai mu shirya mu tafe k'auye da boka yake. Da wannan shawara suka kawo k'arshen secret meeting ɗin nasu. ********************** "Aneesa ina so ki bani aron kunnenki, ki saurare abin da zan faɗa. Azaad ya yi magana fuskarshi a daure tamau.. "Tam Daddy! Aneesa ta faɗa tare sadda kai k'asa tana wasa da wayar hannunta. "Daga yau mai kama da rana ta yau Kar ki sake bari na kama ki da laifi rashin ɗa'a a school ke ba iya school ba ko a gidanan naji labari kin ma wani daga cikin housemaids rashin kunya, za ki sha mamaki irin hukunci da zan zantar akanki. A dalili abin da kike yi aikatawa ga Airah nan ta fara koyi da halinki. Haka ku ke so rayuwarku ta dinga tafiya a baud'e?" Idan har ita mahaifiyarku bata damu tarbiyyarku ba, ni hakke ne da ya rayata a wuyana, da izzini ubangiji sai inda k'arfina ya k'are." Tun daga lokaci da ya fara magana har ya dasa aya bata ɗago ba jikinta sai rawa yake yi, saboda duk iya shegenta tana bala'in tsoran mahaifinta. Ta ɗago kanta da kyar bakinta na rawa tace. "Kayi hak'uri Dadda in-sha-Allahu na daina ba zan k'ara ba. "Da yafi miki. Ya faɗa a takaice kana ya juyo kan Airah wacce tuni tsoro ya gama bai-bayeta, dama tasan za a yi haka daga zarar ya gama da Aneesa kanta zai dawo. "Ke kuma da kike koyi da Aneesa miye abin burgewa a cikin halayenta da har za ki koya?" To bari ki ji duk irin hukunci da zan zantarwa da Aneesa kema irinshi zan maki. A matuk'ar tsorace Airah take kallon shi, har idanuwanta sun fara kawo ruwan hawaye. "Daddy Don Allah ka yi hak'uri ka yafe min sharrin shaidan ne. Ta k'arasa magana kamar za ta fashe da kuka, ya nemi kusa da ita ya zauna, a natse ya shiga yi musu nasiha ya kuma saka Aneesa ta rubuta apologies letter gobe ta kai school ɗinsu, sai around 9:40pm ya fito daga d'akinsu. Ya sauya kayan jikinsa zuwa na barci, ya dauko laptop ɗinshi ya yi switch on yana da online meeting sai misali k'arfe 11:30pm ya kammala yana cikin rufe laptop ɗin ya ji horn tara da k'arar buɗe gate, da sauri ya baro daga wajen zaman shi ya ye labulle widow ya lek'a ya hango madam Salima ta nufo cikin gida tana tafiya kamar bata kashi. Sosai ran Azaad ya 6aci yanzu fissibillahi matar arziki ce za ta fita tun safe sai dare za ta dawo. Zance na gaskiya ya kamata ya yi wa kanshi karatu ta natsu, idan har Salima ta kafe ba za ta bar aikinta ba. To tabbas kuwa zai bi shawarar Abdul-Hakeem da Jadda ko don saboda rayuwar 'ya'yanshi. Ya murzawa k'ofar d'akinshi key ya kwanta yasan ba nemanshi za ta yi ba. Da safe ma ta ri ga shi fita sosai hakan ya k'ara harzuk'a shi duk da hakan ba bakon abu bane a wurinshi. Cike da haushinta ya isa company. ***************** Koda safiya ta waye hannun Aslamiyya ya kumbura sumtum sai azabar ciwo yake mata, daren jiya ko runtsawa bata yi ba. A haka Dadda ta saka ta aikin gida Amrah kuma tai sammako bari gida ta tafi nemo musu abin karin kumallo. Koda Aslamiyya ta fito daga band'aki ta sace jiki ta fita. Tsintsiya ta dauko da ɗayan hannunta mai lafiya ta shiga sharar tsakar gida Dadda kuma ta kasa ta tsare sai antaya mata zagi take. "Yi maza ki kammala shara ki zo don uwarki arniya ki min wanke-wanke don ni babu ruwana da ciwon hannunki shegiya yarinya tsatso kafurai. Sosai zagi ya k'ona mata rai duk ta saba jin iri-irinsa daga bakin Dadda amma zuciyarta ta kasa sabawa, duk lokaci da tai musu irin zagin sai zuciyarta ta buga. Kuka take yi har hawayenta su na diga a floor. Da Amrah ta fito daga gida yau bata je super market ɗin jiya ba, sai ta nufi wani provision store kasancewar safiya ce babu mutane sosai a shagon sai kawai ta nemi gefe ta tsaya, kamar tana jiran wani sai kawai taga mai shagon ya fito da sauri da waya a kunnenshi tana gani ya fita ta afka shago ta dauko k'aton bread ta cusa cikin hijabinta, dai-dai mai shagon ya shigo ashe lokaci da ta shi ga shagonshi ya ganta shiyasa ya dawo. *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A Free Page 5.... Koda Aslamiyya ta kammala shara zuwa lokaci ta jigata matuk'a, ga yunwa ga azabar zogi da hannunta ke yi kamar zai tsinke. Duk da halin da take ciki bata fasa tattaro tulin wanke-wanke wanda ba na Dadda Kaɗai bane hadda na surukanta. Tun daga lokaci da ta fara wanke kwanuka har ta kammala kuka take yi idanuwanta sun yi luhu-luhu. Amrah tai ido biyu da mai shago da ya tare k'ofar fita, gabanta yai mummuna faɗuwa gani yadda mutume ya murtuk'e fuska ya haddasawa cikinta murd'awa. "Ke! uban me ya shigo dake shagona?" Yadda ya daka mata tsawa yana zare ido ta daburce ta rasa abin faɗa jikinta ya fara mahaukacin rawa. Gani haka ya fahimtar dashi bata da gaskiya musanmman da ya shiga K'are mata kallo ya ga hannuwanta cikin hijabinta tana kiciniya 6oye wani abu. "Menene a cikin hijabinki me kika sata fito dashi don ubanki?" Kusan tare ya watsa mata wad'annan jarin tambayoyi, tsora ne ya k'ara lullu6eta,ta tabbata yau dubunta ya cika, mai kwatar ta hannun wannan mutume mai zubin samudawa sai Allah. Ta shiga yawo da idanuwanta lugu da sako na shagon ko Allah zai sa taga hanyar fita kafin ta gama dube-dubenta ta ji an finko ta da k'arfi bai tsaya wata-wata ba ya cire mata hijab sai ga bread sakade a hamanta ta. Ta saki bread ɗin ya fado k'asa. "Don Allah malam kayi hak'uri wallahi ba halina bane yunwa da rashin gata yasa ni na sata maka bread... Tun kafin ta k'arasa magana ya kifa mata mari, wasu jajayyen taurari suka ma-maye ganinta cike da rashin imani ya shiga jibgarta kamar ya sami sa'anshi. Ya sukunce ta ya fito da ita waje yana mata ihun 6arauniya kafin kace kwa6o wurin ya cika da mutane yara 'yan makaranta sa'o'inta sai kallonta suke yi. Baki da hancinta na zubda jini Amrah bata k'ara shiga tashin hankali ba sai da taga mutume yana faɗawa mutane wai ko jiya ya gannta ta shigo mishi shago tana fita, ya nemi kud'insa dubu d'ari ya rasa saboda haka ta fito mishi da kud'insa ko ya mik'a ta hannun 'yan sanda. Sosai take kuka tana mishi magiya mutane da ke kallo abin da ke faruwa sai la'anta ta suke yi, gata k'aramar yarinya ace tana sata. Tana ji tana gani ya kwashe ta zuwa police station, tana kallonshi ya ba wa 'yan sanda statement ɗin k'arya wai ta sace mishi dubu d'ari. Ba tare da duba da k'aranci shekarunta ba suka jefa ta bayan kanta, cikin muryarta da ta disasshe saboda kuka tace. "Ku dubi girman Allah ku yi min rai wallahi azim ban d'auki kud'insa ba. Biredi na sata kuma tun a shago na ajiye mishi abinsa... "Ke! Rufe mana baki 6arauniyar banza da wofi daga ni idanuwanki za ki aikata, iri-irinku ne idan kun girma ku ke zama shararrun 'yan ta'adda. Wani dogon d'an sanda ne ya ke magana har yana nuna ta da kulkin hannunshi. Tun Amrah tana kuka da hawaye har ta dawo kukan zuci ga yunwa na nukurkusar hanjinta ga d'an banza duka da tasha hannun mutumen. Ga kuma tsoro shigowar ta hannun police domin abu ne da bai ta6a faruwa da ita ba. Duk k'anana sace-sace da take yi cikin gidaje da shaguna ba a ta6a kamata ba. ******************** Madam Salima tare da k'awarta Hafsat Shinkafi a office ɗinta dake cikin kamfaninta, asalin Hafsat 'yar jahar zamfara ce aure ne ya kawo ta Kano mijinta ya rasu ya barta da yara 4 bata sake yi aure ba, a ganinta aure zai ta kura ta ya hanata neman kud'i, duk wani gantali neman duniya tare suke yi abinsu. Dabi'unta da na Madam Salima sak iri daya babu ban-banci shiyasa k'awance su ya yi armashi. "Salima duk laifinki ne sau nawa ina faɗa miki ki fitar da yaranki k'asar waje su yi karatu za su fi samun cikakken kulawa, dukiyar nan Allah ya ba ki ita kullum cikin nema kike kina tarawa, to miye amfaninta idan 'ya'yanki ba su sakata sun wala ba?" Sai da Madam Salima ta shak'i iska kana ta fesar ta k'ofufin hancinta kafin tace. "Ba wai nak'i shawara ki bane Hafsat kema kinsan kafiya da taurin kai irin na Azaad, ba zai ta6a bari yaranshi su yi nesa da gida ba. Yanzu ɗin ma kullum a cikin tuhumata yake akan tarbiyyarsu. Ina gaya miki jiya da haukar shi ya motsa cewa ya yi sai na ajiye aikina ko uban me zan sama idan na zauna gida?" "Whats! Ki ajiye aikinki?" "Wallahi kuwa haka ya faɗa. Sai dai ko kusa bushak'insa bai yi tasiri akaina ba. "Zance na gaskiya Salima ki tashi tsaye domin sare-sarin hauka zubda miyau. Na fahimci manufar Azaad guda biyu ne dole ɗaya daga ciki ya kasance gaskiya na d'aya kodai so yake ya rusa ki yana bak'in ciki da yadda duniya ta fara haska tauraronki. Saboda ya ga kin fara kamo k'afarshi a arziki shine yake so yai miki k'afar ungulu. Na biyu Ko so yake ya k'aro aure.... "Dallah ya isa Hafsat haka! hasashen ki ne ya ba ki hakan. Azaad ba haka yake ba, kawai dai yana so na kar6i ragamar kula da gidana saboda yaranmu sun fara girma.... "Matsalarki kenan Salima har yau kin kasa buɗe idanuwanki ki fahimci gaskiya, kin yarda da Azaad ɗinan shi kuma Sam bai yarda dake ba, kin d'auki soyayyar duniya kin ɗora mishi shi Kuma ya gaji da zama dake duk wannan salo ya fito miki da shi ne saboda kin kasa haifa mishi d'a namiji wanda zai gaje shi, shiyasa ya fito miki ta wannan sigar "No....no... please Hafsat don't say that me ya kawo zance haifar namiji da rashin haihuwarshi?" Kar ki saka min shakku akan mijina mana. Ina miki korafi ne akan rashin jituwa da muke fuskanta a koda yaushe ke kuma kina neman shigowa da wani sabon al'amari. "Ba sabon al'amari bane Salima kece kika kasa gano hakan da kanki, ki yarda dani Salima akwai k'amshin gaskiya a cikin abubuwan da na lissafa miki. Shi zama yake yi ne gida naga kullum yana yawo a sama kamar tsuntsu yau yana wannan k'asar gobe yana waccan. Ko kuma ke Kaɗai Allah ya dorawa nauyin tarbiyyar yara?" Ki yi amfani da kwa-kwalwarki mana. Har Hafsat ta dasa aya a zance ta idanuwan Madam Salima na lumshe tana girgiza kanta, ta d'auki lokaci a haka kafin da sauri ta buɗe idanuwanta gabanta na mugun faɗuwa mik'ewa tayi da sauri tare da harde hannuwanta a k'irji sai ta kai bangon farko na office ɗinta ta dawo na k'arshe. Hafsat sai bin ta da kallo take gani safa da marwanta ba mai k'arewa bane yasa ta mik'e ta kamo hannunta "calm down k'awata.... Ta fincike hannun nata da k'arfi ta ja da baya tana wani girgiza kai, cikin kaushin murya tace. "Kina faɗar min mijina zai k'ara aure kuma kina gaya min I should calm down as how Hafsat tell me as how??" "Ni ban ce dake zai k'ara aure ba kawai I'm trying to get your brain clean up" Ajiyar zuciya tayi ta dako cike da izzarta da tak'ama ta iso gaban Hafsat ta dafa kafad'arta, tace. "Hafsat a rayuwata abu biyu nakeso neman kud'i da Azaad. Haka zalika abu biyu na tsana talauci da kishiya. Ki sani Azaad ba shida ra'ayi mace fiyye da d'aya haka zalika yana matuk'ar so 'ya'yanshi fiyye da son da ni nake musu, bai ta6a nuna min yana son haifar ɗa namiji ba. Da mace da namiji there are all equal to him ko yanzu ya bijiro da zance ajiye aikina a dalilin dambe da Aneesa tai da schoolteacher ɗinsu. Saboda haka tun wuri mu ajiye wannan zance, kafin maganganunki su yi tasiri a zuciyata" "Kenan kin amince za ki bi abin da yake so za ki mika ragamar kamfaninku ga 'yan uwanki, burinki na mallakar kamfanin ke Kaɗai ya bi iska?" Yatsine fuska tayi kana cikin zallan izgilanci tace. "Bari ki ji Hafsat ko ubana Kabir Dala da shine silar arziki na ace zai baro lahira ya zo duniya ya nemi na ajiye aikina billahil-azim ba zan masa biyayya ba, balle wani Azaad Junaid da yake tamkar steering mota sai yadda na juya shi. Lokaci ɗaya suka kwashe da dariyar shek'inyaci tare da tafawa, Hafsat ta shiga kod'ata tana zuba mata kirari. ****************** Fitowar Azaad Junaid da Abdul-hakeem Daura daga meeting wayar Abdul-hakeem tai ringing, ya ɗaga tare da k'arawa a kunnenshi. Muryar k'anwarshi Zainab ya ji tana rera kuka. "Will you shut up and tell me what exactly happened?" Shiru ya yi yana sauraren bayani da zainab take mishi, ya shiga furta "Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Zainab sau nawa zan faɗa miki ki daina tafiya mai nisa ba tare direba har sai kin kwarewa da driving, da yake kunnen k'ashi ne dake ki ka k'i ji. Shi Kenan ganina zuwa" Ya kashe waya ya mayar da dubanshi kan Azaad wanda ya tsare shi da idanuwa. "Zainab ce ta kirani wai ta buge wani d'an acha6a tana police station. "Subhanalillah....Allah yasa da sauk'i ka je kawai za mu yi waya" Cikin sauri Abdul-hakeem ya fice kaitsaye police station ɗin ya nufa, cikin yarda Allah d'an acha6a bai ji ciwo sosai ba machine ɗinsa ne ya yi damage cikin k'ank'ani lokaci Abdul-hakeem ya biya kud'in machine ɗin ya kuma yi bail ɗin K'anwar sa. Tun yana cikin office ɗin inspector ya ke ji kukan Amrah da magiyar da take wa 'yan sanda.... *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A 6.... Aslamiyya ta mik'e zubur ta nufi k'ofar gida, wannan fitar da tayi shine karo na shidda. Da taje k'ofar gida tayi tsaye tana kallon hanya ta ina Amrah za ta 6illo. Tun fitarta take jin matsananci tsoro haɗi da faɗuwar gaba. Ta je makota inda take sa ran gani Amrah yafi a kirga gashi Kuma tana tsoro ta fita daga unguwa zuwa nemanta, ta bar Amal ita Kaɗai saboda yanayi jikinta. Abin ka da ruwa-ruwa babu juriya sai afki kuka, lokaci zuwa lokaci take sharar hawaye gashi tun safe babu abinda suka ci, inda Allah ya taimake ta akwai raguwar sachet daya na madarar da jiya Amrah ta sato, ta k'adawa Amal. Da batasan inda za ta nemowa Amal abinda za ta ci ba. Sake komawa tai cikin gida tana shiga d'aki ta tarar da Amal zaune, da alama yau jikin nata da sauk'i jiki a sanyyaye ta zauna kusa da Amal k'ok'ari take ta 6oye mata hali da ake ciki. Saidai kashh! Tuni Amal ta gano damuwar da take ciki ga kuma idanuwanta da suka nuna tayi kuka. "Meke faruwa Miyya naga kamar kina cikin damuwa?" "Ba komai. Ta faɗa a takaice tare da kauda kanta tana kallon bangon d'aki. Amal ta matsa daff da ita ta kwantar da kanta aKan kafad'arta cikin sanyi muryarta mai kama da Aslamiyya sak tace. "Miyasa za ki 6oye min Miyya bayan ga idanuwanki nan sun nuna kin yi kuka?" "Amal tun safe da Amrah ta fita bata dawo ba. Wani irin fargaba haɗi da tsoro ke damuna. Ina tsoro kada wani mummuna abu ya sameta. Ta k'arashe magana tana hawaye. A hankali Amal ta sauke ajiyar zuciya kana tace. "Ki kwantar da hankalinki da yarda ubangiji ba abin da zai same ta. in-sha-Allah za ta dawo cikin k'oshin lafiya. "Allah yasa! Aslamiyya ta faɗa tana goge hawayen fuskarta. *************** Cakk.... Abdul-hakeem ya tsaya Yana kallon Amrah wacce ke ta faman rusa kuka, duk da yadda wani tsamurarre constable ke mata tsawa da hargagin ta rufe mu su baki ko ya maketa da kulkin hannunshi. Bata fasa kuka da magiya ba. Ya dawo da ganinshi akan inspector Sa'eed wanda rashin gaskiya ya baiyana 6aro-6aro akan fuskarshi. Gaba d'aya ya rud'e sai wani kame-kame yake yi. "Ranka ya dad'e sata tayi shine aka kawo ta nan. "Waye ya kawo ta, me kuma ta sata?" "Wani mutum ne yace kud'insa ta sace har kimani naira dubu d'ari, yarinyar tana da kafiya da taurin kai, tak'i ta faɗi inda ta 6oye kud'in" D'an murmushi gefen baki Abdul-hakeem ya yi. "Gaskiya inspector ba kasan aikinka ba wannan k'aramar yarinya ce za ta iya satar dubu d'ari?" "Ranka ya dad'e haka mai shago ya faɗa. "Kai kuma da yake kidahumi ne sai ka yarda. Kafin inspector Sa'eed yai magana Amrah ta riga shi ta hanyar cewa. "Wallahi-tallahi Abba ban d'auki kud'insa ba. Biredi na dauka kuma ya kar6e abinsa, Don Allah Abba ka taimake ni yadda Allah ya taimake ka, fitarda ni wurinan. Sosai Abdul-hakeem ya k'ure mata idanuwanshi babu ko kyaftawa, kyakkyawar yarinya fara tass...a shekrunta na haihuwa ba za ta zarce goma sha biyu zuwa sha uku sa'ar Sadiq ce second born ɗinsa. Tausayin ta ya yi mishi dirar mikiya, sai kawai ya rufe police ɗin da faɗa kaman zai dake su musanmman inspector Sa'eed, kasancewar D.P.O baya nan shine babba a wurin. Kamata ya yi ya tsananta bincike haka kawai daga kawo mishi 'yar mutane ya k'argame ta. Sai Kiran mai shago aka yi da ya zo shima ya rudewa ya yi gani attajirin mai kud'in da ya tsawa Amrah, daga k'arshe sai faɗan gaskiyar al'amarin ya yi. Ya dawo yana ba wa Amrah hak'uri. "Ka ga irinta ko inspector yanzu ina za ku da hakki yarinya nan kun zalince ta ba Kaɗan ba?" "A yi hak'uri Ranka ya dad'e sharrin shaidan ne. "Rufemin baki ba wani sharrin shaidan so zuciya ne da kar6a cin hanci da har abada ba za ku bar shi ba. Ke zo mu tafi Allah ya saka miki, yadda suka yi miki Allah yai musu haka nan. Jikin Amrah yana rawa ta fito daya daga cikin constable ya mik'a mata hijabinta da slippers, ta saka da sauri Abdul-hakeem ya rik'o hannunta har sun kai bak'in k'ofar fita, ya juyo ya dube su yana faɗin. "Maganar nan ba wai ta k'are iya nan ba, ku jira abin da zai biyo daga baya. Daga mai shago har inspector cikinsu ya hau k'ugi da mugun sauri suka bi bayan Abdul-hakeem, wanda ya har ya kai wajen da ya yi parking motarsa. "Ranka ya dad'e Don girman Allah kayi hak'uri ka rufa mana asiri" Cewar inspector har yana durkusawa k'asa. Amrah ta dubi Abdul-hakeem da kumburarrin idanuwanta tace. "Abba ka yafe musu dukkansu na fiso laifi domin da na bi nasihar da Miyya take min a kullum da hakan bata faru dani ba. Ta k'arashe magana wasu zafafan hawaye masu zafin gaske, suka gangaro saman kuncinta. Jikin Abdul-hakeem yai sanyi ya kalle inspector da har lokaci ya ke a durkushe. "Shikenan ku tashi ku tafi Allah ya so ku tana da kyakkyawar zuciya ta yafe muku da sai na koya maku hankali. Godiya suka shiga yi masa bai bi ta kansu ba ya buɗewa Amrah backseat ta shiga, saboda har lokaci takaicinsu bai k'arashe sakinsa ba. Zainab dake front seat wacce tun a police station bata furta uffan ba sai lokaci ta Sami damar waigawa gefen da Amrah take tace. "Ya sunanki wacce unguwa kike?" "Sunana Amrah a kawo nake. "Ke kuwa me ya kai ki satar biredi?" Shiru Amrah tai ta rasa amsar bata sai kawai ta shiga wasa da yatsu hannunta. "Amrah ki yi magana mana? A wannan karon Abdul-hakeem ne ya yi magana. Cikin zazzak'ar muryarta tace. "Saboda ba mu da abin da za mu ci nida 'yan uwana. "Ina iyayyenki?" "Abbana ya rasu tun Ina da 2yrs mamanmu kuma naji Dadda tace bayan mutuwar Abbanmu ta gudu tabar mu nida twins sisterna da Yayata Miyya, wacce ita ce take kula damu tun baya da muka rasa iyayyen mu. K'arfaffiyar ajiyar zuciya Hakeem ya yi sosai tausayinta ya k'ara lullu6e shi. Cikin sanyi murya yace. "Ina dangin mahaifinku dana mahaifiyarku da za su bar ku da yunwa Amrah za su iya kula da ci da shan ku, ba sai kin yi sata ba?" ""Hannun kakarmu wacce ta haifi Abbanmu muke ita kuma bata sonmu. Kullum cikin gana mana azaba take, dangin mahaifyarmu kuma ba musan su ba. Asalima ba musan gari da suke ba. Tsabar rud'ani da Hakeem ya shiga yasa ya kasa magana Zainab ce tai k'arfin halin cewa. "Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Ki ka ce mahaifiyar Abbanku, ke kuwa Amrah me ku ka aikata mata har haka da ta tsane ku. "Saboda Abbanmu ya aure mahaifiyar mu ba da saninta ba sannan kuma mahaifiyarmu ba Musulma bace. "Amrah wannan ba hujja bace da za ta dogaro da ita har ta tsane ku, ai ba laifinku bane na mahaifinku ne saboda shine ya yi mata ba dai-dai ba. Kuma babu inda addinin musulunci ya yi hani da aure wacce ba Musulma ba. Kawai dai kakarku muguwa ce azzaluma sai Allah ya yi muku sakay.... "Ya isa haka Zainab! Hakeem ya katse mata numfashi daga haka ba wanda ya sake magana a cikinsu, wani super market ya tsaya ya yi wa Amrah shopping na kayan tea da bread haɗi da indomie har dasu chocolate cake da biscuits. Tun a farkon layin unguwarsu tace ya sauke ta bai ce komai ba, ya yi parking ta fito shima fitowa Amrah tai mishi godiya har ta juya ya kira sunanta ya fito da shopping bags da kwalin indomie ya ajiye a gabanta bai ce komai ba ya shiga mota har ya yi reverse sai kuma ya tsaya ya kira ta, da ta zo ya mik'a mata card mai d'auke da phone numbers tare da company address ɗinsa. Ta koma wajen tulin kayan da ya ajiye mata ta ɗora kwalin indomie aka ta d'auki shopping bags, ta nufi gida sai da ta fara lekawa tsakar gida kamar yadda ta saba ta ga babu kowa tai wuff ta shige d'akinsu kasancewar su ne a farkon shigowa... ***************** Yau ma da wuri Azaad Junaid ya shigo gida, sai da ya lek'a 6angare Jadda saboda ya zame mishi al'ada duk dare sai ya je yaci abinci a wajenta sannan yake dawowa apartment ɗinsa. Sai da ya duba lafiyar yaranshi kafin ya nufi nashi d'aki, yana cikin online meeting ya ji an turo k'ofar d'akinsa. Ko bai ɗago ba yasan ko wacece ke da zarar shigo mishi d'aki a dai-dai wannan lokaci, shiyasa bai damu da sai ya kalli wanda ke shigowa ba. Cikin dakon k'assaita da nuna ita ɗin wata ce ta shigo ba ko sallama sai wani yatsina da take yi, sai uban k'amshi na fitar hankali dake fita daga jikinta sanye take da sleeping gown wacce ta sauka izuwa gwiwarta, cike da izza haɗi da tak'ama ta nemi gefen gado ta zauna. Ta ɗora k'afa daya kan daya, har ta zauna bai da niyar ɗagowa ya kalle ta balle tasa ran za tanka mata. Ta aika mishi da malalacin kallo, mai nuni da batasan darajarsa ko Kaɗan ba. Wani sai kad'awa k'afafuwanta take yi. Cikin gadara tace. "Azaad inaso nai magana da kai please can I have your attention?" Ya ci gaba da magana da yake da colleague ɗinsa da suke online meeting yai banza da ita, hakan ba k'aramin sosa mata rai ya yi ba. Abin ka da mai hurt temper har ta harzuk'e. "Da kai nake magana Azaad ka yi wani kunnen uwar shagu dani. kuma san na tsani ina magana ayi banza dani, kai kuma abin da ka fi kwarewa dashi kenan. Ta k'arashe magana cikin ɗaga murya, da sauri ya yi disconnected video call ɗin tare da rufe laptop ɗin. Gudun kada hankali colleague ɗinsa ya dawo kanshi har su fahimci abun da ke faruwa, A tsanake ya ɗora manyan idanuwanshi masu masifar daukar hankali akan kyakkyawar fuskarta da batada make up amma sai glowing take abinta. Yayin da hasken blue colour bulbs dake d'akin yana k'ara haskaka fuskarta ta, ya jefa mata kallon nan nashi mai sanyi da kashe jiki tare da faɗin. "Me kike nema a bedroom ɗina a dai-dai wannan lokaci?" "Na zo ne muyi magana akan sauyawa Aneesa school d'azu na aika P.A ɗina ya je school ɗinsu su ya kar6o min transferring letter ɗinta, sai ya dawo min da zance wai kayi magana da principal Aneesa za ta ci gaba da karatu a school ɗinta har da saka Aneesa ta rubuta apologies letter for what reason za ta ba da hak'uri?" "Tunda ta fara magana idanuwanshi ke kafe akanta babu ko kyaftawa yayin da wani tuk'uk'in bak'in ciki haɗi da takaicinta suka mishi dirar mikiya a karo na ba adadi, saboda ba yau ne ranar farko da ya fara jin hakan akanta ba... *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A Free page 7.... Ido biyu Amrah tai da Aslamiyya kallon tuhuma ta bin ta dashi har tasauke kwalin indomie da ke kanta, bata dauke idanuwanta daga kanta ba. Tana jin lokaci da Miyya ta sauke k'arfaffiyar ajiyar zuciya, ta buɗe baki a rud'e ta ce. "Subhanalillah....Amrah me same ki ne naga fuskarki da idanuwanki a kumbure?" Amrah ta sadda kai k'asa idanuwanta suka ci-ciko da hawaye tasan asirinta ya ri ga da tonu babu saura 6oye-6oye, cikin muryar kuka ta zube gaban Aslamiyya. "Don Allah kiyi hak'uri ki yafemin miyya nasan abin da na aikata ban kyauta miki ba, wallahi na tuba ba zan k'ara satar kayan kowa ba.... A matuk'ar tsorace Aslamiyya ta finciko kafand'unta ta mik'ar da ita tsaye. "Na shiga uku Amrah sata fa kika ce?" Amrah ta gyada kanta saboda kukan da yaci k'arfinta ba zai bata damar buɗe bakinta ba. "Kin cuceni Amrah kin yaudare ni wato ba gidan Maman Saleem kike zuwa tayata aiki ba, sata kike fita wayyo ni Miyya wacce irin rayuwa Amrah ta jefa kanta?" "Ban cuce ki ba Miyya asalima ina yi sata ne domin kare mutuncina sau uku Baban Saleem, yana yunk'uri lalata min rayuwa da taimakon ubangiji nake samun na kwace kaina. Haka ma gidan Maman Bobo sau babu adadi Bobo yana ta6a min k'irji. Na 6oye ban faɗa miki ba gudun kada ki shiga tashin hankali. Tun daga lokaci na daina shiga gidajen jama'a sai dai na bi shaguna na sato mana abin da za mu ci" Da sauri Aslamiyya ta rungume Amrah tana wani irin gunji kuka, kamar ranta zai fita. Amal da ke kwance sai kallonsu take tana shar6a hawaye. Bayan Amrah ta tsagaita da kukanta, ta shiga ba Miyya labarin taimakon da Abdul-hakeem ya yi mata. "Allah yasaka mishi da masauki a gidan aljanna firdausu! Ina gargadinki Amrah daga yau kar ki sake ta6a kayan kowa ba tare da sanin mai abu ba. Sata babban kask'anci ce tana zubar da mutunci da k'ima tana rusa darajar mutum a idanu jama'ar duniya, duk hali da muke ciki mu dogara da Allah sai ki ga ya kawo mana mafita ba tare da dabarar mu ba. "Na daina wallahi ba zan sake ba. Ai naga aya in-sha-Allah babu ni ba sata har abada" Aslamiyya ta sauke ajiyar zuciya tare da zaunawa kusa da Amal. **************** "Azaad da kai nake magana fa" Sai da ya sauke zazzafan numfashi kafin ya ce. "Saboda ni ne mahaifin Aneesa ni ke da cikakken iko akanta ba ke ba. "Wow! Thats good to hear that from you Azaad ashe kasan da haka ka keso rusa min career, ka ke so ka hana min business ɗina, Wato abin naka mugunta ne ko?" Ta k'arashe magana tana ɗage girar idanuwanta, da ka kalle shi za kasan cewa he's deeply in hurt babu komai a cikin zuciyarshi sai takaici da bak'in ciki how long zai ta kasancewar cikin wannan takaici da 6acin rai?" "Salima! Ya kira sunanta cikin zazzak'ar muryarshi ma'abociya sanyi, duk yadda ranshi ya kai da 6acin ba kasafai yake nunawa ba. Sai dai ya 6oye shiyasa duk ranar da aka kaishi mak'ura hukunci da zai dauka sai ya girgiza mutum, shiyasa bai cika yanke hukunci nan take ba saboda kaifi d'aya ne. "Ina da hak'uri Salima kema kinsan da wannan, kada ki yi amfani da hak'uri na ki yi min yadda kike so hakan ba dai-dai bane Salima ki tuna ni fa mijinki ne uban 'ya'yanki..... "Dallah ya isa! Ni ba wannan ne ya kawo ni dakinka ba, ka nace aKan lallai sai Aneesa ta yi karatu a school ɗin da banaso okay fine naji amma inaso kasani idan har zan zantarwa da hukunci akan yara ka nuna min ban isa ba, har kana faɗin kafini k'arfin iko akansu to hakan na nuni da babu amfani ka cilastani mik'a ragamar dukiya ta a hunnun wani. Don haka na faɗa da babbar murya ba zan ajiye aikina ba. "Shikenan naji abin da kika faɗa amma inaso ki sani ba cilasta ki nake ba umarni ne a matsayina na mijinki, idan har ke ba ki min biyayya ba. Nima babu amfani na bi son ranki. Saboda haka ki bi yanda ranki yake so nima na bi nawa anan za a tantatace waye gaba tsani ni da ke. Cikin izgilanci ta kece da dariyar reni, kana ta mik'e tsaye tana tafa hannuwanta, ta dube shi a wulak'anci ta ce. "Babu abin da za ka iya Azaad tun yaushe kake wannan 6a-6atun da cika baki, sai fa ka gama wannan cika bakin naka ka dawo kana rarrashi da bani hak'uri. "Shikenan naji Salima duk abin da za ki faɗa go ahead ba zan hanaki ba. Domin ban isa ba amma inaso ki rubuta ki ajiye ni Azaad Junaid sai na shayar dake zallan ruwan mamaki.....oya fita min daga d'aki I don't want any arguing with you just go and do what you want. "Zan fita dama ban shigo ba don in zauna d'akinka amma kafin in fita inaso ka dawo min da passport ɗina da ka d'auke na nema kaura wambai ban ganshi ba. Na kuma tabbatar kaine ka d'auka ka dawo min da kayana domin tafiyata babu fashi. "I say get out of my room before I loose my control.... "I'm not going anywhere until you return my passport. A fusace ya mik'e ya buɗe closet ɗinshi ya zura hannun cikin aljihun coat ɗinshi, ya ciro passport ɗinta ya jefa mata. "Ga tsiyar ki nan dauka ki fita min daga d'aki" "Hakan ya fi ma alkhairi da kunnu wutar da ba ka da ruwan kasheta. Ta faɗa tana wani shegen blushing na reni ta sunkuya ta d'auki passport ɗin, ta fice abinta cikin yanayi ko a jikina. Kasa ci gaba da meeting ɗin ya yi zuciyarsa sai tafarfasa take yi tabbas lokaci ya yi da zai nunawa Salima shi ba su-su bane kamar yadda ta dauka, sai yasaka ta nadama a bisa kowa ne furuncinta. Da wannan bak'in cikin nata ya kwanta. **************** *AFTER TWO DAYS*{BAYAN KWANA BIYU} Yau ne ya kasance ranar tafiyar Salima kasancewar morning flight za ta bi, batada niyar faɗawa Azaad tafiyarta saboda dama haka ta sabar mishi za ta bar k'asa batare da saninshi ba, sai ta isa k'asar da za ta sannan ta kira shi. Wani lokaci ma sai ta share wasu kwanaki kafin ta kira shi. Nanny Lacey janye da luggage ɗinta ita kuma tana biye da ita jikinta sanye da wide legs trouser tare belted top ta ɗora long black frock jacket ta yane kanta da multiple colour scarf, k'afarta sanye da kitten heel na company Hermes hannunta na dama rik'e da bolide handbag ita ma ta company hermes ɗin ne ga k'amshin designer perfumes dake fita daga jikinta. Cikin tafiyarta ta izza da tak'ama take saukowa daga stairs, dai-dai lokaci da Azaad ya fito daga 6angare shi zai shiga gem room suka haɗu ta dauke kanta tana mai ci gaba da kashewa Nanny Lacey gargadin ta kula da gida. Sosai jikinshi ya yi sanyi wato da gaske sai Salima tayi wannan tafiya da bayaso a natse ya kira sunanta gani batada niyar kula shi. "Salima! Kamar ba za ta tsaya ba sai kuma ta tsaya ta waigo fuskarta, a murtuk'e gudun kada yaga damarta ya kawo mata wargi. "Ina za ki je da sanyi safiya?" "Duk inda zan je is none your business please stop wasted my previous time to your silly questions. Ta juya kawai ta ci gaba da tafiya, ajiyar zuciya ya yi tare da fesar da zazzafar iska daga bakinshi ya biyo ta a baya a parking lot ya tarar da ita har ta shiga mota ya dafa k'ofa, da sauri ta kalle shi saboda bata ta6a tunani zai biyo ta ba. "Ina rok'onki a karo na ba adadi ki fasa wannan tafiya duk abin da kike so zan miki Salima. Ina da tarin dukiya mai yawan gaske miyasa za ki dinga wahalar da kanki?" "Saboda inaso nai building ɗin nawa future ba na dogara da kai ba. "Ke mace ce Salima wannan yawo bai Dace dake ba. "Kaine kake gani rashin dacewar shi" "Ina k'ara rok'onki da ki janye wannan tafiya" "Ba zai yu ba saboda na jima ina neman wannan opportunity ba kuma Zan yi wasa dashi ba. "Shin zan iya biyanki makudan kud'i domin ki yi handling business dinki ga siblings dinki, ki zauna gida ki kula min da kanki da yarana?" "Ba kud'inka nakeso ba ko wata k'addara taka ba nawa nake nama gumin jikina nakeso Kai ma kasan da wannan Azaad?" "Me kike nema Salima wallahi-azim zan miki, ni dai burina ki jinginar da wanna yawace-yawace da kike yi da sunan business ki zama full housewife" "You're dreaming Azaad. "I'm not Salima please accept my offer. "Wallahi-tallahi ba zai yu ba Ina business ne ba don komai ba sai don na tara tawa dukiya, babban burina nayi suna a duniya inaso a lissafa sunana a cikin mata masu kud'in duniya, saboda haka kabarni na tafi kana 6ata min lokaci a banza. "Shikenan Salima Allah ya tsare ya kai ki lafiya ya ba ki abin da kike je nema. Ni kuma Allah ya musanya min abin da na rasa Allah yasa wannan tafiyar taki ta zame mana buɗewar k'ofufin alkhairi ina miki fatan samun nasara a rayuwarki. Daga haka ya juya yayin da yake ji kamar zai kife k'asa sakamakon wani duhu da ya lullu6e wa ganinsa, tafiya kawai yake batare da yasan inda yake jefa k'afarshi ba. Yana wucewa Salima ta ja tsaki. "Mtsss.....aikin banza naga uban da ya isa ya hanani tafiya. Adaddafe Azaad Junaid ya isa master bedroom ɗinshi, ya kwanta akan tangamemen gadonshi. Zuciyarsa na wani irin bugawa a duk lokaci da ya tuna da irin hukunci da ya tanadarwa Salima indan har tai wannan tafiya. Gaba d'aya yini ranar a d'aki ya yi shi zazza6i mai zafin gaske ya lullu6e shi, bayan ga coffee ba abin da yasawa cikinsa. Gashi yana da very importance meeting sai Hakeem ya kira ya wakilce shi. Kusan kwana sa biyu a gida tare da yaranshi ko compound bai fita ba. Sai a kwana na uku ya fita office yana zaune a office ɗin nashi damuwa ta taro ta mishi yawa. Abdul-hakeem ya shigo d'auke da wasu files a hannunshi a natse ya shiga k'are mishi kallo ya rame sosai har ramar tashi ta baiyana k'arara akan kyakkyawar fuskarshi. "Aj wai meke damunka ne, ni fa ban yarda da wannan rashin lafiyar nan taka ba gaba d'aya ka sauya bakada wal-wala da kuzari sai d'an banza tunani ka faɗa min menene ke haddasa maka shiga wannan hali?" Sai da Azaad ya ja gwaron numfashi kana ya shafa kwantattace sajenshi, ya dauko d'aya daga cikin wayoyin shi ya danno wani ke66en folder batare da ya yi magana ba ya mikawa Hakeem. Jikinshi a sanyyaye ya kar6i wayan ya shiga karanta abin da ke rubuce, tun kafin ya k'arasa karatu ya ɗago a firgice yana kallon Azaad Wanda ya kauda kanshi yana kallon wani gun dabam. "Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Cewar Hakeem yana faɗa yana k'ara nanatawa gaba d'aya ya dimauce ya gigice har yana k'ok'arin fita daga hayyacinsa...... *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A Free page 8... Tsabar d'imaucewa da Hakeem ya yi yasa kasa tsayuwa akan kafafuwanshi, da sauri ya ja kujera dake fuskantar Azaad ya zauna. Sai ya yi yunk'uri furta magana bakinshi ya dinga kakkarwa, da kyar ya yi control ɗin kanshi ya sami damar furta. "Why Aj?" Shiru Azaad ya yi har zuwa lokaci bai d'auke hannunshi daga kan sajenshi ba, sai faman sha-shafa shi yake yi tamkar shafar ce za ta rage mishi radadi da k'unci da yake ciki a karo na biyu Hakeem yasake watsa mishi tulin tambayoyi. "Miyasa Aj, miyasa ka yanke irin wannan danye hukunci, miyasa ka bari shaitan ya rinjaye ka, ka yanke hukunci cikin fushi nasan Kuna matuk'ar son junanku Kai da Salima miyasa za ka sake ta alhali sakin zai iya cutar daku?" "Ba a ciki fushi na yanke wannan hukunci rabuwa da Salima ba Hakeem. Nayi iya k'ok'arina nagani hakan bata faru a tsakaninmu ba, amma tak'i bani haɗin Kai. "Amma sai nake gani kamar hakan bai dace ba Aj akwai hanyoyi da za a magance wannan matsala, ba wai sai lallai wannan da ka bi ba. "Hakeem na bita na rarrashe ta duk da ni nake da cikakken iko akanta amma kamar k'ara ingizata ake yi. Idan har nace zan cigaba da hak'uri da Salima menene makoma ta da yarana?" Salima ta za6i neman duniya fiyye da igiyoyin aurena. Shin Salima ita Kaɗai ce mace da ba zan rayu ba sai da ita?" "Ba Kaɗai bace Aj shiyasa tun farko na zo maka da shawarar Karin aure... "Ya isa Hakeem aikin gama ya riga ya gama babu saura komai a tsakaninmu domin text ɗin ka karanta tun ranar da ta bar k'asar nan, na turo mata a hali yanzu inaso na nemowa kaina farin ciki da narasa tun ganiyar kurciyata. Nima inaso na zama sarki a cikin fadar gidana, idan nace ayi sai ayi idan nace abari abi umarnina ba wai ni na bi ba. "Aj ni aganina ko don albarkaci yara bai kamata ka saketa ba. "Me take tsinanawa yara dukansu babu Wanda yasan dad'inta ita da babu duk daya yake a wurinsu, rabuwarmu ba abin da zai shafe su dashi. "Shikenan Allah yasa shi yafi zama alkhairi Allah ya musanya maka da wacce tafi ta wacce za ta kawo farin ciki a rayuwarka. "Amin thumma amin! Nagode Sosai da wannan addu'a taka Hakeem. in-sha-Allah rabuwarmu za kawo wani haske a rayuwata Ina jin hakan a jikina. Shiyasa na yanke shawara zan yi aure kafin ta dawo kuma na mik'a maka ragamar nemo min mata wacce ta fito gidan tarbiyya 'yar mutunci wacce za ta mutunta ni da yarana. Murmushi Abdul-hakeem ya yi farin cikinshi ya kasa 6oyuwa, ya taso da sauri ya rungume Azaad tare da furta. "Al-hamdu-lillah! Al-hamdu-lillah! Allah kaine abin godiya. Azaad ya janye shi daga jikinsa ya mik'e tsaye tara da saka hannuwanshi cikin aljihu, ya yi tattaki izuwa gaban fridge sai kuma ya tsaya tare da juyowa ya dube Hakeem kana ya ce. "Banso budurwa bazawara za ka nemo saboda za ta fi kulawa da yarana" Take annurin kan fuskar Hakeem ya gushe, ya dube shi da baki sake. "Amma wallahi Aj kai wawa ne, banda wawanci uban me za ka tsinta a jikin bazawara sauran wani. "Uban da ake tsinta a jikin kowa ce mace. "Look abokina kar ka 6ata goma biyar bata gyaru ba, kabar komai a hannuna wallahi-tallahi zan nemo maka wacce tafi dacewa da kai, in ma bazawarar ce ko budurwa muradinka dai 'yar mutunci mai ingantattaciyar tarbiyya. Azaad ya ja iska ya fesar daga bakinsa ba tare da yasake tankawa Hakeem ba, ya nufi k'ofar fita da sauri Hakeem ya bi bayansa. ****************** Zaune suke a gaban wani k'aton mushirinki boka wanda bashida kyau gani, ko Kaɗan. Wata katuwar kwarya a gabanshi mai d'auke da ruwa farare tass...sai tafarfasa suke alhali ba a kan wuta suke ba. Wani yare yake yi mai kama da buzanci can kuma ya tsaya da tsoki burutsunsa, kafin ya tattaro hankali da natsuwarsa akan Alhaji Yusuf Junaid tare da k'annesa uku da ya zo tare dasu don ayi komai akan idanuwansu. Sai kuma Alhaji Buba wanda shine ya yi musu jagoranci zuwa wajen bokan. Cikin muryasa mai amon sauti ya fara magana. "Tuni aka sanar dani zuwanku miyasa ku kayi gareje tun lokaci ba ku zo ba sai yau?" Alhaji Yusuf Junaid ya gyara zaman babban rigar shi, ya ce. "Tafiya ba zata ce ta zo min zuwa Abuja sai jiya na dawo. Shiru boka ya yi yana ta bin su da jajayyen idanuwanshi, kafin ya ɗaga gefen buzun fatar daminsa da yake zaune akai, ya dauko wata katuwar layya, ya jefata cikin kwayar a hankali layya take nutsewa cikin ruwan har nutse duka kana ya dawo da ganinshi akansu ya ce. "Kun zo nan ne domin kashe d'an uwanku Azaad Junaid, kun je wajen bokaye da malaman tsinbo bila'adadin amma ba ku yi nasara ba?" "Haka ne.... Ahmadu ya faɗa a hanzar ce. "A yau dad'add'e burinku zai cika ni nan zan cika muku shi amma a bisa sharadin, za ku biya naira miliyan uku za ku kawowa aljanu jini jariri sabuwar haihuwa, sai kuma shanu manya guda bakwai. Kafin Alhaji Yusuf Junaid ya yi magana Ahmadu ya riga shi ta hanyar cewa "Idan har za ka kawar mana dashi fiyye da abin da ka lissafa za mu yi maka mu dai burinmu, mutuwar Azaad Junaid domin ita Kaɗai ce hanyar da za ta sada mu da mafalkinmu. Boka ya kece da dariya mai kama da kukan aurakin jaki, sai da ya yi mai isarshi kafin ya ce. "Tabbas yau burinku zai cika ku zuba idanu ku sha kallo. Jefa hannunshi cikin ruwan yana jujjaya shi tare da kiran sunan Azaad Junaid, ba a d'auki dogon lokaci ba hotonshi ya baiyana a cikin ruwan yana tsaye ya kare waya a kunnenshi yana magana, boka ya dauko wata karamar wuka da ganinta za tai mugun kaifi ya dubi saitin zuciyar Azaad ya caka sai kawai Aslamiyya ta baiyana a gabanshi kafin wuka ta ta6i jikinta wuta ta kama kwaryar hatta da wukar dake hannun boka ci take da wuta, duk iya k'ok'arinsa naso ya jefar da ita ya kasa hannunshi sai ci yake da wuta da ya ji uwar bari ya zabura da gudu bala'in ya fita daga bukkarshi. kamar jira ake bokan ya fita kwaryar tai wani irin tsalle ta dire kasa ta tarwatse, wuta ta kama bukkar, su Alhaji Yusuf Junaid suka kwasa da gudu suka nufi k'ofar fita gashi k'ofar karama ce, sai tu-ture juna suke, da kyar Ahmadu ya samu ya ture Alhaji Buba da ya yi ba-bakere a jikin k'ofar shi bai fita bai kuma janye ba. Ahmadu yana samu ya ture shi gefe ya fice Alhaji Abdallah ya biyo bayan Ahmadu, har Alhaji Yusuf Junaid ya yunk'ura ya tashi daga faɗuwar da ya yi saboda lokaci da Ahmadu ya ture Alhaji Buba shi kuma ya faɗa masa, suka faɗi kasa a tare sai dai wani abin mamaki ya kasa tashi kamar wanda aka danne, shi ma Alhaji Buba ya gwada tashi ya kasa, su Ahmadu dake wajen bukkar sai ihu da neman agaji suke abin ka da dokar daji babu wanda zai ji su balle ya kawo musu d'auki. Alhaji Yusuf da Alhaji Buba su na ji su na gani wuta ta fara cin jikinsu, sai ihu suke tun su na ihu har suka sulele k'asa, bukkar kuma ta Kama gaba d'aya...... *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A Second to the last Free page 9... Los Angeles international airport {LAX} A tsakiyar dare jirgin da ya dauko su Salima ya yi landing a los Angeles international airport. Tsakiyar dare ne amma sai kamar lokaci safiya ta waye, Salima tana gaba Hafsat Shinkafi tana biye da ita a baya. Cab suka hau zuwa Roosevelt hotel wanda tun kafin zuwansu k'asar suka yi booking. Hotel ne mai mugun tsadar gaske Kuma a cikinsa ne za a gudanar da seminar da suka zo. Seminar ce ta manyan mata 'yan kasuwa na duniya duk wata gwaska Wanda ta amsa sunanta international business women tana wajen hatta da ticket ɗin shiga wurin idan ka ji makudan kud'i da ake siye ta sai ka girgiza, tun saukar Salima k'asar wayarta ke rufe. Tana zaune a room ɗinta jikinta sanye da bathrobe towel fitowar ta daga wanka kenan. Ta d'auki system ɗinta, ta shiga duba sak'oni email, anan taci karo da sakon Azaad Junaid a maimakon ta girgiza ko ta rud'e sai ma wani shegen blushing take, wanda ke nuni da ko Kaɗan sakinta da Azaad ya yi bai dame ta kawai dai tayi mamaki inda ya sami kwarin gwiwar rubuta mata message na saki har biyu. Ta kudurta a ranta bata saku ba domin a ganinta Azaad bai isa ya yanke hukunci shi Kaɗai ba ita ma tana da ikon ya ji nata ra'ayinta idan ta amince su rabu idan ta amince, shikenan sai ya saketa amma ba wai ya yi gaban kanshi ba. Sam bata amince wannan rabuwar ba. Saboda haka ta ci gaba da sabgoginta a dalili ta d'auki saki a matsayi shirme yasa ko sanar da aminiyarta Hafsat ba tayi ba. *************** Aslamiyya tare da Amrah su na duk'e a gindin famfo sai darza uban wanki suke yi, yau tun da asuban fari suka k'arya kumallo da wankin kayan Baffa Sani. Tuni Baffa ya daina kai wanki sai dai su yi masa, abin takaici gashi da gardawan 'ya'ya maza sai dai su Miyya su masa ba zai saka 'ya'yanshi ba. tsabar mugunta sai ya tara kaya da yawan gaske yake saka su wanki gashi yawanci tufafinshi duk babbar riga ne. Tun da asuba yana dawowa daga masallaci ya tisa su a gaba, duk sanyi da ake tsulawa bai dame shi ba ga ruwan tanki sun yi mugun sanyi kamar na fridge Amrah tana tsoma hannunta a ruwan taji mugun sanyi ya ratsa k'asusuwanta, ta fara you wa Baffa Allah ya isa miyya tana ji ta amma bata ce uffan ba. A haka suka ci gaba da wanke kayan sai wuraren karfe biyu suka kammala, zuwa lokaci sun gaji likisss..... Aslamiyya ta jik'a musu indomie da Hakeem ya siya musu su na cikin ci indomie ɗin suka ji muryar Dadda tana kwada musu kira. "Aslamiyya, Amrah uban me ku ke yi kunshe a d'aki ku fito maza ga nawa wanki na fito dashi, shegu yara marasa son aiki" Da sauri Aslamiyya ta fito jikinta sai rawa yake yi, Allah ya saka mata tsoro tsiya a rayuwarta Amrah kan zamanta tai tak'i fitowa, daga k'arshe sai Miyya ce tai wanki. Da taga akwai raguwar kumfa ta dauko nasu kaya ta zuba a ciki tana cikin wankewa Dadda ta fito, tana kyala ido taga Miyya tufafinsu ne take wankewa, ta fara surfa mata zagi. "Eh! Lallai Aslamiyya kin nuna min ke isasshiya ce nasaki wanki ki haɗo har naku, saboda ga sabulun banza ko?" Jikinta ya d'auki kyarma sai kakkarwa take yi, cikin muryarta mai cike da tsoro tace "Dadda wallahi ban saka sabulunki ba ruwan kumfa ne kawai ga ma raguwar sabulunki can na kai miki, k'ofar d'aki..... Sai da Dadda ta sakar mata bak'ar harara kafin ta shiga zazzaga mata ruwan masifa. "Rufemin baki shegiya yarinya tsinaniya wacce ta tsotsi nonon kafurci, shegu gur6attaci. Zo nan don uwarki arniya. Ta k'arashe magana tare da ya fito ta da hannu, tuni Aslamiyya tafara kuka, Amrah ce ta fito daga d'akinsu tana faɗar "Haba Dadda,! Wai me muka tare miki a duniya ne kullum sai kin k'ikk'iro da hanyar da za ki musguna mana, dad'in abin ba ki da wuka kankare zamowar mu jikokinki, saboda haka kema kina da had'i da jinin arna. Amrah ta k'arashe magana tana murguda baki. "Iyeee.....Amratu ni ki ke yiwa rashin kunya?" "Ba wani rashin kunya Dadda gaskiya ce na faɗa, kema ai kin zama arniya saboda abin da kike yi wani arne ba zai yi irinshi ba. Amrah bata gama rufe baki ba Dadda ta wawuro tsintsiya da nufi dukanta, Amrah tana ganin ta nufo wajenta ta 6alla da gudu tayi k'ofar gida, sai kawai ta dawo kan Miyya. "Ke kuma daga yau duk abin da kika san nawa ne a gidanan karki kuskura ki ta6a shi, yadda na tsani mutuwata haka na tsaneku. Ta k'arasa magana tare da fyadawa Miyya tsintsiyar aka, Aslamiyya ta durkusa k'asa tare da ɗora hannuwanta bisan kai, tana gunji kuka. ******************** Alhaji Yusuf Junaid tare da Alhaji Buba suka kone kurmusss.....a cikin bukkar boka, Alhaji Abdallah da Ahmadu sai ihu suke har bukkar ta cinye duka sai toka kawai da gawawakin su Alhaji da suka yi bak'i k'irin.... kamar an babbaka awakai. Boka kuma da ya zura da gudu ya shiga jaji, wuta da keci a hannunshi sai dad'a k'aruwa take yi a maimakon hannunshi yanzu kuma duka jikinsa ke ci da wuta, tun yana iya gudu har k'arfinshi ya K'are ya faɗi. Kamar fashewar bomb haka boka ya fashe naman jikinsa ya tarwatse gunduwa-gunduwa abin zallan tashin hankali. Alhaji Abdallah da Ahmadu basu k'ara shiga tashin hankali ba, sai da wuta ta mutu suka ga gawawakin su Alhaji kuka suke yi babu mai rarrashin wani daga k'arshe Ahmadu ya jawo motar da suka zo da ita suka tattaro gawawakin suka zuba sai k'auri ke tashi, tsawon rayuwarsu ba su ta6a ci karo da mutuwar mai tashin hankali iri wannan ba. Duk lokaci da suka tuna da musanbabin mutuwar tasu sai tashin hankalinsu ya k'ara linkawa. Gashi kuma ba su san me za su faɗawa iyalai su ba. Gara ma Alhaji Yusuf jininsu ne watakila abin ya zo musu da sauk'i sa6ani Alhaji Buba da yake 6are kuma fitattce d'an siyasa 'yan adawa za su iya cewa an had'a baki dasu sun kashe shi. Kaitsaye farmhouse ɗin Alhaji Yusuf suka nufo inda suka saba yi secret meeting ɗinsu har suka iso basu sami kwakwarar dabarar da za su yi ba. Sai kawai suka kira abokan kullin tugunsu, dukansu sun tsorata da jin afkuwar al'amari ko wane su fuskarshi ta bayyanar da firgici da yake ciki ga dai babbakakin gawawaki zube cikin mota sun rasa yadda za su yi dasu. Can Hasheem ya ja dogon fasali kana yace. "Ku bani aron hankalanku inaso ku sani muddin sanadin mutuwarsu ya bayyana, mu ma kashinmu ya bushe, Kuma ba lallai bane iyalinsu su yarda da labari yadda suka mutu ba. Saboda haka ku bar min komai a hannuna. "Sai ka faɗa mana dabarar taka mu ji?" Cewar Hajiya Kubra wacce ita da Alhaji Yusuf da Alhaji Abdallah uwarsu d'aya. A natse Hasheem ya shiga koro musu bayani plans ɗin nashi, take suka yi hamdallah tare da amincewa. *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *AZAAD JUNAID* _{ The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten Takun Haske Batch:A Last Free page. 10... A cikin dare mummunan labari ya riske iyalan Alhaji Yusuf Junaid tare da na Alhaji Buba sun yi mummunan accident, sun kone kurmusss.....ga baki daya iyalan sun shiga tashin hankali musanmman da suka ci karo da gawarwakinsu. Wannan duk shirin Hasheem ne su kansu 'yan uwanshi sun yabawa basirarsa matuk'a, tun a cikin daren mummuna labarin ya riske Azaad bawa Allah duk yabi ya rikice duk k'iyayyar da 'yan uwanshi ke nuna mishi hakan bai hana shi k'aunarsu ba. In ka ganshi sai ya ba ka tausayi kuka yake yi sha6e-sha6e da hawaye. A washe gari aka yi jana'izzarsu jama'a sun taro sosai, abinka da manyan mutane. A duk lokaci da Ahmadu da Alhaji Abdallah suka yi arba da Azaad sai gabansu ya yanke ya faɗi, wani irin mashahurin tsoronshi ya shige su, shiyasa duk inda suka ganshi zaune ba su zama a gun, gani suke kamar yana sane da abin da ya faru. Tun daga ranar da aka fara zaman makoki Azaad Junaid ya d'auki nauyi kawo abinci da za a ci haɗi da lemo har ma da ruwan sha, daga wani tsadadden restaurant ake kawowa. Bayan an yi sadakar bakwai kowa ya kama gabanshi sai raguwar 'yan uwa na jiki. ******************* A tsakiyar dare ciwon Amal ya tashi yau kuma da sabon safuri ya zo, don kuwa sai aman jini take, kakarin amanta ne ya tashi Miyya da Amrah a gigice Amrah ta kunna bulb haske ya gauraye d'akin kan shinfid'arsu duk ya 6aci da jini hakan ba k'aramin ɗaga musu hankali ya yi ba. Miyya sarkin kuka tuni hawaye suka wanke mata kuncinta. Yayin da numfashi Amal sai ya yi sama ya dawo kasa, Amrah ta buɗe k'ofa haɗi da fallawa da gudu ta nufi d'akin Dadda ta shiga knocking tana kuma kiran sunan Dadda. Dadda tana cikin mutane da basuda nauyin barci duk k'ank'anta motsi akan k'unneta, tun fara buga kofar ta ji ta sarai kawai biriss...tai da ita. Duk dauriya irin na Amrah sai da ta fashe da kuka, tasake ficewa da gudu ta nufi 6angaren Baffa Sani tashiga dukan k'ofa kamar za ta karyata a bisa dole Baffa Sani ya taso ya buɗe mata, tun kafin ta sanar dashi dalilin knocking ɗinta ya d'auke ta da bahagon mari, ya kuma shiga surfa mata zagi. "Ka ga 'yar iska yarinya bashin uwarki naci da za ki dinga gana min azaba ta hanyar duka min k'ofa a sulusili dare?" Duk da taji zafin marinta da ya yi hakan bai san ta fasa faɗar. "Baffa ciwon Amal ne ya tashi yau har da aman jini take yi..... "Amal ɗin taci uwarta ba aman jini take yi ba Allah yasa ta amayar da 'yan hanjinta ba abin da ya shafe ni maza 6ace min da gani tun kafin na murd'e miki wuya. Amrah ta fashe da matsananci kuka ta durkusa, tana rokon Baffa magiyarta ya taso da mai d'akinsa Habiba, cikin murya wanda aka katsewa barci ta ce. "Wai meke faruwa ne Alhaji?" "Nida 'yar banzar yarinya nan ce Amrah wai Amal ce batada lafiya shine don tagadi iskanci gaba da baya take min wannan mahaukacin knocking. "Mtss..... lallai Alhaji Amrah ta rena ka banda reni Ina ruwanka da rashin lafiyar Amal da za ta katse mana barci. Baffa Sani ya yi kwanfa tare da maida k'ofarshi ya rufe ruff.....dole Amrah ta tashi ta dawo d'akinsu. Aslamiyya na d'auke da kan Amal a cinyarta har zuwa lokaci numfashinta bai dai-daita ba. Sai kawai suka saka Amal gaba su na rera kuka, sai zuwa asuba Amal ta daina gurnani da take yi kamar wacce tai barci, sai kawai Aslamiyya ta shinfid'eta ta fita waje ta dauro alwala, ita ma Amrah alwalar tayo suka yi sallah su na kammala sallah Amrah ta dubi Aslamiyya ta ce. "Miyya bai dace mu bar Amal haka ba kamata ya yi mu kai ta asibiti, saboda tun da take ciwo nan bata ta6a aman jini ba. "Nima nayi wannan tunani Amrah saidai zuwan namu bai da amfani saboda komai sai da kud'i, mu kuma ba mu dasu. "Duk da haka Miyya mu gwada kaita zai fi da mu barta gida tana sha wuya . "Shikenan je ki nemo adaidaita bari na canza mata kayan jikinta duk sun 6aci da jini. Daga haka Amrah ta fice jefi-jefi take haɗuwa da mutane unguwa saidai ba wanda ya ce da ita kazal.....tana tsaye a bakin titi har gari ya fara haske bata samu adaidaita ba, kamar daga sama taji an anbace sunanta. "Amrah me kike neman da sassafe nan akan titi?" Da sauri ta waiga sai kawai taci karo da fuskar mutume nan mai shago da ta yi wa satar bread, cikin sanyi murya ta gaida shi ya amsa kana ta faɗa mishi dalilin fitowarta da taimakonshi ta sami adaidaita, ya kuma biyota zuwa gidan nasu tashiga gida suka fito da Amal lokaci da za su fito da ita Dadda tana tsaye a k'ofar d'akinta ta kalle su ta watsar. Lokaci da suka fito da Amal kamar matatciya, sosai Bello mai shago ya tausaya musu saboda tun ranar da al'amari nan ya faru tsakaninsa da Amrah ya yi nadama. Ya kuma kudurta a ranshi duk ranar da ya haɗu da ita zai taimaka mata kuma ya rok'e ta gafara, shiyasa yana ganinta ya biyo ta. Kaitsaye Nassarawa hospital suka wuce da ita a emergency, kasancewar dama ko acan baya anan ake kawota. Har zuwa lokaci Bello mai shago yana tare dasu, hatta da katin gani likita shi ya biya musu k'udi, bayan likita ya duba ta ya basu zungureriyar takarda, mai d'auke da list ɗin magunguna da drip haɗe da allurai da za su siyo. Amrah ta kalle miyya a hankali ta ce. "Bari naje Bello yana jira na a waje mu siyo magani ki kula da ita yanzu nan zan dawo" "Amrah waye wannan mutume da mu ka zo tare dashi?" Miyya ta aika mata da tambaya tare da tsare ta da idanuwanta. Ajiyar zuciya Amrah tayi kafin ta faɗa mata waye shi. "Amrah bakinsan mutume nan ba bai kamata ki yi sauri yarda dashi ba. "Nasani Miyya amma dole ce tasani yin hakan amma nai miki alk'awari kula da kaina in-sha-Allah ba zan yi abinda zai ta6a martaba ba. "Shikenan ki je amma ki faɗa masa duk abinda ya kashe mana dangin kud'i, rance ne za mu nemo mu biya shi daga baya. Amrah ta fito waje rik'e da prescription, da tunani ina za ta nemo kud'i saboda k'arya ta yi wa Aslamiyya na cewa za su je siyan magani ita da Bello domin tun a wajen siyen kati suka rabu dashi. Kafin ya tafi ya bata dubu biyu. Tana fitowa daga asibiti pharmacy ta wuce aka buga lissafi kud'in magani kusan dubu ashiri da biyu da d'ari bakwai, gashi dubu biyu ce da ita duk yadda taso su kar6i dubu biyu ɗin su bata Koda drip da allurai ne in ta kawo ciko kud'in su bata raguwar magani, amma suka k'i daga k'arshe korar kare suka yi mata, kusan saida ta yawace duka pharmacy dake wajen har ta sadakat....sai ta tuna da complementry card ɗin da Hakeem ya bata da sauri ta nufi bakin titi ta tari adaidaita sai gida, a gigice ta shiga gida, ta tararda Dadda zaune a tsakar gida, ko kallo bata isheta ba. Ta shiga d'akinsu a gaugauce tafara neman card ɗin, tasha bak'ar wahala kafin ta gano inda ta ajiye. Ajiyar zuciya ta sauke yafi a kirga da ta gano card ɗin. Da gudu ta fito Dadda sai kwalla mata kira take, a tunanina ko Amal ta mutu ne shine dalili shigowar Amrah a rikice ta kuma sake ficewa a firgice, Amrah tana jin duk kira da take mata tai banza da ita. Wayar d'an adaidaita ta ara ta shigar da number Abdul-hakeem, lokaci da kiranta ya shigo wayar shi yana tare da Azaad Junaid su na tattaunawa aKan zance neman matar aure da yasa Hakeem ɗin ya nemo masa, tai ringing har ta tsinke Hakeem bai ɗaga ba. Amrah ba ta hak'ura ba sai mai-maita kira take, can taji an yi picking tasa kuka cikin muryar kuka ta ce. "Don Allah ina magana da uncle Hakeem ne?" "Shine wacece? "Amrah ce yarinyar da a kwanakin baya ka yi bailing ɗinta a police station" "Subhanalillah..... Amrah lafiya me kike yi wa kuka Allah yasa ba satar ce kika k'ara yi ba?" Cikin shasshekar kuka ta faɗa mishi dalilin kira nashi da tayi, sosai tausayinta ya lullu6e shi tsabar tausayawa ko sallama bai yi wa Azaad ba ya fita, da mugun speed ya iso Nassarawa hospital ya ma ri ga Amrah isowa yana tsaye ya hangota da sauri ya nufi wajenta. Ya kar6i prescription ɗin ya je ya siyo magunguna ɗin sannan suka dunguma zuwa emergency, sosai mamaki ya lullu6e Aslamiyya na gani Amrah tare da wani babban mutum, nan take aka wuce da Amrah d'aki na musanmman likitoci suka dukufa akanta. Cikin hukunci ubangiji numfashinta ya dawo normal. Tun zuwan Hakeem asibiti yake kallon Aslamiyya, dai-dai da second d'aya bai d'auke ganinshi daga kanta ba. Har sai da Miyya tagano da kanta yana kallonta duk sai ta bi ta tsalgu. Sai kawai ta shige bathroom tai zamanta a ciki, gani haka yasa fita ya siyo musu abinci sai da ya tabbatar da ya yi musu duk wani abu ya dace kafin ya wuce gida. ***************** A washe gari ya sauya musu asibiti zuwa ta kud'i, Al'awwab spine care shine private hospital ɗin da Hakeem ya kai Amal. Asibiti ne mai tsadar gaske suna da kwararu likitoci har da turawa dama ciwon zuciya ne ke damunta an haife ta da hole a zuciya{rami} wanda tun haihuwar ta ya kamata ayi mata surgery amma rashin gata ya hana. Tana girma ne ramin yana k'ara girma shine dalili da yasa ta fara aman jini. Ba tare da 6ata lokaci ba Hakeem ya biya milliyan goma da aka buk'ata ranar Miyya tasha kuka domin abinda suka yi shekaru suna nema sai gashi Allah ya kawo Hakeem rayuwarsu, babu haɗin iya balle na Baba yai musu. Cikin yarda ubangiji aka yiwa Amal surgery kuma ana sa ran nasara. Satin su biyu a hospital ko kare bai zo ba daga dangin mahaifinsu babu kuma wanda ya damu da sani hali da suke ciki. Kullum addu'ar Dadda Allah yasa sun shiga duniya kenan bata fatan su dawo mata gida. Sosai Amal ta sami sauk'i ta murmure kamar ba ita ba hatta da jikinta ya fara dawowa, har zuwa lokaci Hakeem da matarsa Zaliha ke dawainiya dasu, Zainab K'anwar Hakeem ke taya Miyya kwana Amrah Kuma ta koma gidan Hakeem da zama Lokaci da Zaliha ta ji labarinsu sai da ta zubda hawaye, shiyasa ta d'auke su tamkar 'yan uwanta na jini. Kusan kullum indan Hakeem ya zo asibiti sai Miyya tai mishi godiya, baya cewa uffan saidai yasaki mata k'ayatattace murmushi. A sati na uku aka yi discharge ɗin su kai tsaye Hakeem ya nufo gidanshi dasu Sosai hakan ya daurewa miyya kai, tana da kawaici shiyasa bata tambaye shi dalili kawo su gidanshi da ya yi ba. Zaliha ta ware musu d'akinsu dabam.....an k'awata shi da komai na more rayuwa, sai suka tsince kansu a cikin wata sabuwar rayuwa wacce ba su ta6a mafalkinta ba. Yau satinsu biyu a gidan tuni su Amal da Amrah sun zama 'yan gida musanmman da ya kasance Rayham second born ɗin Hakeem sa'arsu ce. Miyya ce Kaɗai ta kasa sakin jikinta, a kullum burinta su bar gidan duk da bak'ar wahala da suke sha a hannun Dadda ta gwamaci su koma can domin nan ne asali da tunshe su. A wani yammaci ne Miyya da Zainab su na zaune a d'aki, Rayham ta shigo ta sanarda Miyya Daddy yana kiranta. Nan take ta ji wani matsananci faɗuwar gaba, ta saka hijabinta. Lokaci da ta shigo falon faɗuwar gabata ya tsananta har wani duhu-duhu take gani. Da fuskar Baffa Sani ta fara cin karo yana zaune yasha babbar riga brown colour, sai kuma Dadda wacce tun da tashigo ta kalleta ta watsar. Cikin sanyi murya tai sallama Hakeem tare da Zaliha suka amsa mata, ta nemi sama center carpet ta zauna murya can k'asa ta gaida Baffa da Dadda ba wanda ya amsa mata a cikinsu. Kaitsaye Baffa Sani ya fara faɗar abin da ya kawo su. "Aslamiyya dama mun zo ne domin mu yarda kwallon mangwaro mu huta da kuda, tun daga ranar da Usman ya bijerewa mahaifinmu ya auro uwarki muke d'and'anar bakin cikinsa, sanadin bakin cikinsa mahaifinmu ya rasa ranshi, a duk lokaci da na kyala ido na ganku ji nake kamar na kashe ku. Kwatsam....sai ga wannan bawar Allah ya zo mana da zance aurenki dama muna neman kai dake shiyasa babu 6ata lokaci na amince yau ɗinan aka daura miki aure, Kuma ina mai tabbatar miki daga ke har shegun k'anneki banaso ko kusa da katangar gidana na ganku. Ku sa aranku wannan shine danginku dama can shegiyar yarinya nan Amratu ta sha faɗar ke ce uwarsu ke ce ubansu, yanzu kuma ga dangin kun samu. Da sauri Miyya ta ɗago idanuwanta da babu komai a cikinsu sai tsoro, ta kafe Baffa dasu ji take kamar wani yare ne yake mata ba hausa ba........ *TOP 10 TAKUN HASKE BATCH A*💪 *ALBISHIRIN KU MUTANEN KIRKI? KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION* *TAZO MUKU DA SABON TAKU, SABUWAR FITA, SABON KARUWA, SABON ILIMI, SABON NISHAƊI SABON KARATU SABON AJI.* *INDA SUKA ZO MUKU DA K'YAYATATUN LITTATTAFAI GUDA 7, WANDA ZASU NISHADANTAR DAKU SU FADAKAR DAKU. WANDA GWARAZAN MARABUTAN KU ZASU GABATAR* *IBTISAM:- NA AYUSHER MUH'D* *WATA SOYAYYA:- NA OUM HANAN* *WASU MAZAN:- NA BILLY S FARI💎* *NIDA RAHEEMA:- NA ASMY B ALIYU👄* *ZO GARE NI:- NA HAJJA CE👈* *KUKAN ZUCI:- NA SLIMZY* *AZAAD JUNAID (the young billionaire):-NA JEEDDAH ALIYU* *TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A BASU TSAYA NAN BA, ZASU GABATAR MUKU DA WASU SHIRYE SHIRYENSU* KALOLIN GIRKI TARE DA:- *DEEJARH BERVER* SHIRIN YADDA AKE HADA MAGUNGUNAN KARIN NI'IMA DA INFECTION (NI'IMARKI A TAFIN HANNUNKI) TARE DA *MAMAN KHADIJA* SHIRIN TSAFTA YADDA ZAKI GYARA JIKINKI DA MATSALOLIN JINI TARE DA:- *UMMI AISHA* *ZASU KARA MUKU HASKE AKAN ABUBUWA DA SUKA SHA KANKU, MATSALAR AURATAYYA MATSALAR INFECTION, MATSALAR NI'IMA, MATSALAR FUTAR ISKAR GABA, MATSALOLI DA DAMA.* *DUK ZAMU GABATAR DA WANNAN KARATU NE TA HANYAR WAYOYIN SADARWA, WATO WHATSAPP GROUP'S* GARABASA MAI CIKE DA ALBARKA DA KUMA KARUWA. GABA D'AYA WANNAN AJI ZAIZO MUKU NE AKAN 500 naira only...Nair ɗari biyal kacal. *GA MAI BUKATAR BIYAWA KANSA KO KANWA KO MATA KO YAN UWA YA KASANCEWA DA TAKUN HASKE TOP 10 BATCH A* *SAI YA TURA KUDINSA TA* 2083371244 Zenith Bank Aisha M.Salis *Seka tura shedar biyan kud'inka zuwaga wannan lambar* +447894142004 *Ko kuma tura katin waya na MTN ta wannan number👇🏼👇🏼* 07043079282 *Shaidar biya ta wannan* 07065283730 *DUK AKAN 500NAIRA ONLY MACCEN DA TA'ISA TA SAN KANTA BAZATA BAR DAMAR NAN TA WUCETA BA!* *ƳAN NIGER🇳🇪, ZAKU IYA TURA KUƊINKU 550F TA NITA, AMANA, AL'IZZA, BENIF KO ZEINA GA WANNAN LAMBAR* +227 96 91 36 36 *SUNA* RAHINA daga Niamey. *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya naira 200 kacal ba idan kina\kana buk'ata sai ku tura kudinku ta 2083371244 Asha M.Salis Zenith Bank sai ku tura shaidar biyan kud'in zuwa ga wannan lambar +447894142004 ko katin waya na MTN ta wannan number 07043079282 shaidar biya ta 07065283730* *AJ* 11... "Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Miyya ta faɗa a firgice, sai k'ara zare idanuwa take yi tare da bin su Baffa Sani da kallon tsoro. Dadda ta rafka mata katuwar harara cikin masifa ta ce. "Ka ji min marar kunya yarinya mugun abu muka aikata da za ki bi mu da innalillahi wa'aina illahim raji'un! To bari ki ji aure dai ne an riga an daura kuma ko kinaso ko bakyaso k'arshen zaman mu dake ya zo. Saboda haka tun wuri ki rufawa kanki asiri ki kar6i k'addararki a hannu don ni nan da kika gani ba zan jure cigaba da zama daku ina tuna bak'in cikin da sanadin auren uwarku ya haifar min" "Daina 6ata yawun bakinki Dadda domin ko za ta mutu zaman aure nan ya zame mata dole Shi din ban da kyau d'an maciji da ya rud'e shi me zai tsinta a wurinki, sau nawa ina ba dake sadaka ana barina dake. Ina tabbatar miki ba ma buk'atarki daga ke har k'anneki ku k'addara cewa ba ku ta6a saninmu ba. Ku saka aranku bamu da wata alak'a daku. Tun da Baffa Sani ya fara magana Miyya ta fashe da kuka wani irin k'unci da bak'in cikin take ji marar misaltuwa, bata ta6a tsanmani k'iyayyar da suke musu har ta kai mizani haka ba. Hakeem ya yi sanyayyar ajiyar zuciya yana mamaki wannan wacce irin k'iyayya ce me yara k'anana kamar su Miyya su ka yi da suka can-canci tsana irin wannan, abin takaicin shine daga kakarsu wacce ta haifi mahaifinsu da k'anishi uwa daya uba daya shi Kaɗai ne k'anishi a duniya wai su ne ke nuna musu wannan zazzafar k'iyayya. Shi tun da yake a duniya bai ta6a jin inda aka hukunta wani akan laifi wani ba, sai akan su Miyya saboda kawai mahaifinsu ya aure Christan ta kuma haifesu an Kuma waye gari mahaifin nasu baya duniya, shine suke fuskantar wannan tasku. Ya sake sauke ajiyar zuciya a karo na biyu cikin sanyi murya ya ce. "Baffa ni dama burina Miyya ta ji zance aure nan daga bakinku, to Al-hamdu-lillah! Ta Kuma ji iya wannan nake buk'ata daga gareku. Kamar yadda na faɗa muku tun ranar da naje da buk'atar neman aureta, zan rik'eta ita da k'anneta bisa amana, zan kula dasu na basu tarbiyya tamkar 'ya'ya da na haifa. Kuma in-sha-Allah zan kasance mai rik'e wannan alk'awari. Fuska Dadda ta tanke ta dubi Hakeem ta ce. "Da ka rik'e su amana da kada ka rik'e su ni wannan bai shafe mu ba, idan ma ka ga dama ba iya ci amanarsu ba, ka yanka su kaci wannan ba damuwar mu bace. Ni dai inaso ka k'ara jaddada musu basu ba gidana dama dole ce tasani zama da 'ya'ya kafira 'ya'ya da aka daura auren uwarsu a coci, saboda haka yanzu sun dawo mallakinka..... Cikin matsananci kuka Miyya take kallon Dadda tana girgiza kai tana faɗin. "Haba Dadda! Haba Dadda duk da kasancewar mu 'ya'ya kafira ki tuna cewa kafira nan ita Kaɗai ba za ta samar da 'ya'ya ba dole sai tare da namiji. Wannan namiji kuma shine d'anki jinin jikinki ashe kuwa ko duk duniya za su taru su juya mana baya ke bai kamata ki wofitar damu ba. Dadda duk musgunawa da kike mana wallahi-tallahi ban ta6a jin tsanarki a zuciyata ba. Na saka araina wata rana za ki hak'ura ki so mu ashe tunanina ne ya bani hakan..... "Ke! Baffa Sani ya daka mata tsawa. "To tunaninki ya gayamiki k'arya har gaba da abada ba za mu ta6a sonku ba, na Kuma faɗa banaso ko katangar gidana ku ra6a. Dadda tashi mu tafi. Ya k'arashe magana yana kama hannun Dadda ta mik'e da kyar saboda tana fama da ciwon k'afafuwa. Miyya tana gani haka takara sautin kukanta, tana faɗar "Baffa Don Allah kada ku tafi ku bar mu hannun Wanda bamu gama saninshi ba, gara zama daku koda za ku yanka naman jikinmu ku yi gunduwa-gunduwa dashi. Ku dubi girman Allah Kar ku bar mu a gidanan. "Mtsss..... shegiyar yarinya bak'ar ja'ira can ku k'arasa mu kam Allah rabamu da jafa'i, Allah yasa k'addarar mutuwarku tana hannunshi dare yau ya fara shan farfesunki, dama duk a cikin ɗiyan Usmanu kinfi debo kamani kafirar uwarki. Cewar Baffa Sani har yana had'awa da galla mata harara da idanuwanshi, masu kama da na mujiya. Jin furuncinshi na k'arshe yasa Miyya ta k'ara fashewa da kuka, ta rarrafa ta kama k'afar Dadda. "Haba Dadda wannan wace irin rayuwa ce ku ke k'ok'arin jefa mu ciki, idan aure ku keso ku yi min ku aurardani gun wanda ku ke da cikkake sani akansa. Ba wannan ba da ku kanku ku ke zarginsa da yankar kai.... Da sauri Hakeem ya mik'e ya nufi Miyya, ya durkusa a gabanta cikin sanyayya murya ya ce. "Aslamiyya ki kalle ni da kyau ban yi kama da wanda zai iya cutar da ko dabba balle mutum d'an adam mai darajar, haɗuwata daku wani babban al'amari ne wanda haɗi ne na Allah, ki d'auki haɗuwarmu a matsayin k'addararre al'amari. Har Miyya ta buɗe baki za tai magana ta ji saukar abu akan fuskarta, Baffa Sani ya jefa mata buddle ɗin 'yan one-one thousand. "Ga sadakinki nan indan kin ga dama ki kyasta musu ashana ki k'ona. Yana k'arashe magana ya ja Dadda suka fice kamar makaho da dan jagora, har Miyya ta yunk'ura ta bi su Zaliha ta baro wajen zamanta da sauri ta rik'eta. Ita kuma sai turjewa take yi, kururuwar kukanta ne yasa Amrah da Amal suka fito daga d'akinsu, hankalinsu a tashe har su na had'a baki wajen tambayar dalilin kukanta. Zaliha ce tai k'arfin halin faɗa musu a maimakon Miyya taga tashin hankalinsu sai kawai taga bayyanar farin cikinsu a fili, duk sai taji tausayin kanta saboda ta fahimci jin dad'i da hutun da ya fara ratsa 'yan uwata, yasa idanuwansu rufewa basa hango mata babban k'alubali da yake tunk'aro rayuwarta. Sai kawai ta zare hannun Zaliha daga rik'on da tai mata, ta kwasa da gudu ta shige d'akin da ya kasance mallakinsu. Ta murza key. Ita babban abin da ya daure mata kai bai wuce yadda Zaliha bata nuna ta ji zafin aureta da Hakeem ya yi ba. Al'amarin nasu ko shakka babu akwai lauje cikin nad'i. Idan ba wata manufa a ciki wacce sakaryar mace ce za aiwa kishiya ta nuna halin ko in kula musanmman a wannan zamani da mata suke da mugun zafin kishi. Tun Miyya tana kuka da hawaye har hawayenta suka kafe ta dawo kukan zuci, duk knocking da magiyar da ake mata bai sa ta buɗe musu k'ofa ba. ******************* Azaad ya fito daga bathroom daure da brown towel, hakan ya bayyanar da muscles ɗinshi haɗi da six packs ɗinshi a jere jikinshi a murd'e yake ba sai an gayamaka mai k'arfi bane kai da kanka za ka gane. Cikinshi a shafe yake kamar baya cin abinci, alhali idan ya sami tuwo abin ba kyau. Irin jikin Azaad Junaid bature yai wa lak'abi da invested triangle body shape. Azaad yana da matsakaici tsayi yana dauke da round face fatar jikinshi chocolate colour ce tsananin hutun da ya ratsa shi, yasa fatar shi take shek'i, babban abin da yake burge mata a jikinsa la66anshi da suke pink idanuwanshi masu girman gaske, suna dauke da eyes ball brown colour, kamar dai na magge gashin kanshi bak'in wulik dashi. A natse yake tsane raguwar ruwan wanka da ke jikinsa, tsakanin jiya da yau ya rasa gane kanshi, musanmman idan ya tuna da jiya aka daura mishi aure da yarinyar da baisan ta ba. Babban tashin hankalinshi bai wuce yadda zai rayu da wata mace ba Salimarshi ba. Duk da yana da yak'ini akan Hakeem ba zai mishi za6en tumun dare ba. Lokaci da ya zo mishi da zance yarinyar ya faɗa mishi cewar har da yara biyu take da, shiyasa nan take ya amince da aurenta domin yana gani tun da har tana da yara za ta fi ba wa yaranshi kulawar da yakeso. Shima ya yi alk'awari zamewa nata yara uba kasancewar Hakeem ya faɗa mishi mahaifinsu ya rasu. Ya shirya cikin dark grey suit bai saka coat ɗin ba ya rik'e ta a hannu, jikinsa na fitar da k'amshi turaren avon ever truth, walking majestically ya sauko downstairs parlor yaranshi na zaune a dining room su na taking break fast food. "Good morning Daddy! Suka faɗa a tare cikin sakin fuska har yana had'awa da murmushi, ya amsa musu. "Morning my beautiful babies. Daddy zai yi tafiya amma ba zai wuce two to three weeks ba, uncle Hakeem zai kawo muku new Aunt za ta dinga kulawa daku kafin na dawo, ina so ku girmama ta kada wanda ya sake ya yi mata rashin kunya. Aneesah tai dropping fork ɗin hannunta, kana kafe Daddynta da idanuwanta, can kuma ta ta6e baki tana yatsinar fuska ta ce. "Daddy me za mu yi da new Aunt baya ga Nanny Lacey, tana kula damu dai-dai gwargwado iyawarta in fact mommy bataso kwashe-kwashe you have to ask her first.... "Aneesah! Ya kira sunanta a fusace saboda ya tsani ko sunan Salima a anbata mishi nan take ya ji wani irin 6acin rai..... *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya naira 200 kacal ba idan kina\kana buk'ata sai ku tura kudinku ta 2083371244 Aisha M.Salis Zenith Bank sai ku tura shaidar biyan kud'in zuwa ga wannan lambar +447894142004 ko katin waya na MTN ta wannan number 07043079282 shaidar biya ta 07065283730* *AJ* _{The young billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Wattpad:-jeedddahaliyu Haske writers Association. Top Ten takun Haske Batch:A 12... Ya nunata da yatsa cikin kakkausar murya ya ce "Bana cike da iskaci Aneesah ki natsu ki san waye a gabanki, nan gidana ne ba na Salima ba. Ni nake da ikon nasa ayi ni kuma nake da ikon hanawa, don haka wannan ya zama kashedi na k'arshe idan ina magana ki sako min zance mommynku" Sosai Aneesah ta tsorata da yadda Azaad yake mata magana cikin kaushin murya, a tunaninta kafin ma ya kammala magana zai wanka mata mari, saboda tsawon rayuwarta ba ta6a gani yana magana irin haka ba. Cike da tsoro ta baro wajen zamanta ta durkusa gabanshi, saboda duk iskacinta tana matuk'ar tsoron Daddynta. "I'm sorry Daddy wallahi ban faɗi wannan magana don na 6ata ma rai ba. Nayi ne saboda sani halin mommy da nayi za ta iya dawowa ku sami matsala akan hakan. Daddy ina matuk'ar sonku kai da mommy ko Kaɗan banso abin da zai kawo sa6ani a tsakaninku, amma in-sha-Allah ba zan sake maka maganarta ba" Ta k'arashe magana tana hawaye, mik'ar da ita tsaye ya yi tare da goge mata hawaye kuncinta yana alhini ranar da za ta sami labarin rabuwarshi da Salima. "It's okay princess ke ɗin ce wani lokaci kin cika faɗar shirme" "Ka yi hak'uri Daddy ba zan sake ba. "Shikenan amma inaso ki sa aranki duk abin da nake yi Ina yi ne domin farin cikinu da inganta tarbiyyarku, inaso ku zama yara nagari abin alfaharin iyayye. Saboda haka duk wani abu marar kyau princess ki daina kin ga ke ce babba k'anneki dake suke koyi" "in-sha-Allah Daddy na daina duk abin da ka keso shi zan yi. Ya sauke sanyayyar ajiyar zuciya tare da sumbatar for head ɗinta, ya mik'awa Airah hannu wacce tai tsuru-tsuru da idanuwa ya ce "zo nan Mamana naga duk kin yi wani iri" Kamar jira take yi ta taso da sauri ta rungumeshi, ya game su duka biyu ya rungume tsawon lokaci yana jin ɗumin jikin yaranshi, yayin da k'aunarsu mai tsanani gaske ke ratsa ko wane sasshe na jikinsa. Ya buɗe baki a hankali ya ce da Airah. "Mamana je ki kira min Nanny Lacey ta zo min da Ahlam inaso naganta kafin na tafi. Da sauri ta nufi d'akin Nanny Lacey sai gashi sun dawo tare tana d'auke da Ahlam, sai da ta fara gaidashi kana ta mik'a mishi Ahlam ya kar6e ya mannata a k'irjinshi a hankali yake shafa gadon bayanta, ita kuma lafe ya ke6e gefe da Nanny Lacey a natse ya sanar da ita zance aure da ya yi da zuwan amaryar tashi nan da 'yan wasu kwanaki. Ya faɗa mata ne domin akwai yarda mai k'arfi a tsakaninsu. Tun farkon aurenshi da Salima take tare dasu basu ta6a samunta da cin amanarsu ba. Sai dai ya 6oye mata zance rabuwarsu da Salima a ganinshi wannan sirri ne a tsakaninsu bai kamata kowa ya sani ba. Sosai Nanny Lacey ta kad'u da jin zance aurenshi saboda, tafi kowa sani bak'in kishin Madam Salima, akan Azaad komai za ta iya aikatawa. Jikinta yai matuk'ar sanyi cikin tausasa murya ta taya shi murna, ya ji dad'i sosai yadda ta nuna farin cikinta akan auren nashi. Mak'udan kud'in ya bata kamar yadda ya saba bari a duk Lokaci zai yi tafiya duk da akwai wadatatce komai na buk'ata a gidan. 6angare Jadda ya shiga yai mata sallama har ya juya zai fita ta dakatar dashi ta hanyar faɗin "Zo ka zauna Datti zan yi magana da kai" A natse ya dawo ya zauna daff...da ita. "Datti indan lissafina ya tafi dai-dai yau kwana goma da daura maka aure, saidai abin da ban fahimta ba har sai zuwa yaushe amaryar taka za ta tare?" Murmushi ya yi wanda ya tsaya iya fatar bakinsa, ya yi shiru kamar mai nazari kafin ya ce. "Jadda nayi magana da Hakeem ya ce cikin sati nan za ta tare amma za ki iya bincikarshi da kanki. "Shikenan tashi ka tafi Allah ya tsare yasa ayi kyakkyawar tafiya" "Amin thumma amin! Ya faɗa tare da sa kai ya fita bakinshi d'auke da addu'ar fita daga gida. *************** Tun daga ranar da Miyya ta ji zance aurenta ta tashi hankalinta, yayin da Aunty Zaliha take bin ta da rarrashi haɗi da nasiha sannu a hankali nasiharta tafara tasiri akanta. Hakan yasaka Aunty Zaliha ta dukufa wajen gyarata idan ka ga yanda Miyya ta dawo da matuk'ar wahala ka iya gane nan take. Tayi bul-bul k'irjinta ya k'ara cika, fatar jikinta tayi smooth gwanin sha'awa ita kanta sau dama idan ta shiga wanka sai ta 6ata dogon lokaci gaban mirror tana kallon yadda jikinta ya dawo ita kanta tana jin sha'awar kanta balle ga lafiyayye namiji ya yi arba da ita.. Zaune take gaban dressing mirror fitowarta daga wanka kenan, jikinta na fitarda sihirtattace k'amshi saboda ko wanka za tayi sai Aunty Zaliha ta zuba mata kalolin turaruka wanka daban-dabam shiyasa duk idan ta zauna sai tabar k'amshinta. Aunty Zaliha ta shigo rik'e da ma-dai-daci cup tana shigowa Miyya ta 6ata fuska saboda ta riga da tasan kwanan zance. "Kar6i ki shanye ki bani cup" Bata yi gardama ba ta amsa ta shanye tass ta mik'a mata cup, aunty Zaliha tana murmushi ta juya ta fita. Miyya ta bi ta da kallo har yau ta kasa daina mamakinta. ***************** "Hasheem Kaɗai bi lamari nan a natse cikin hikima da dabara, wallahi-tallahi Azaad ya fi ka shu'umanci. Kana dai kallon irin mutuwar k'as-k'anci da Babban Yaya da Alhaji Buba suka yi ko kare gidana bana fatar ya yi irinta. Ahmadu ya faɗa yana share d'an uban gumin da ya tsatsafo mishi a goshi, ya rasa dalili ko sunan Azaad ya anbata sai ya tsinci kanshi cikin mugun yanayi. "Mtsss.... Kaɗai Yaya Ahmadu an yi matsoraci ni nan da ka ganni ba Azaad ba ko uwarshi dake lahira da za ta dawo duniya sai na wulak'anta rayuwarta, balle wani k'aramin gwaro irinsa. Jin furuncinshi yasa Alhaji Abdallah ya girgiza kai sai da ya k'are mishi kallo kafin ya ce. "Kaɗai bi a hankali kamar yadda Ahmadu ya faɗa Hasheem. Gudun kada allura ta tono galma, da za ku d'auki shawarata da nace mu hak'ura da son ganin baya Azaad, saboda ba tun yau ake ruwa k'asa tana shanyewa ba. Ku duba tsawon lokaci da muka d'auka muna binsa da bi ta da k'uli sai asarar dukiyoyinmu muke yi wurin malaman tsinbo da bokaye a banza. Har ta kai da mun fara rasa rayukanmu, tsakani da Allah banaso nayi mutuwa irinta su Babban Yaya mu je gidan shahararru bokaye har ma da matsafa ko yau ɗinan mu je wurin wani matsafi, da idanuwanku kun ga abin da ya faru ya kira sunan Azaad a madubin tsafinsa a maimakon ya fito shi Kaɗai sai ya fito tare da aljanarsa dake bashi kariya. Dakyar mu kasha saboda haka magani bari kar a fara ni mu dai ri ga da mun fara amma Kuma lokaci bai k'ure mana ba mu rufawa kanmu asiri mu watsar da makaman yak'inmu, ko don gudun mutuwar wulak'anci.. "Dakata Alhaji Abdallah! Hasheem ya faɗa cikin tsawa tamkar yana yi da sa'anshi. "Tun farko ba kidahumancin ku ne ya jawo ba. Na sha faɗa muku bokayenku duk makaryata ne, basu iya komai ba sai gilla k'arya. Ku bani dama za ku ga aiki da cikawa zan nemo professional killers su cika masa aiki kyaftawa gira su turo shi garin da ba a dawowa. "Shikenan ku je Allah ya bada sa'a saidai inason ku sani a wannan karo kuma a wannan tafiya ba dani ba, saboda gani ga wane ya isa wane tsoron Allah. Cewar Alhaji Abdallah yana k'arashe magana ya Kade babbar rigarshi ya k'ara gaba, gaba ɗayansu suka bi shi da kallo kafin su sake dawowa da natsuwarsu kan Hasheem, wanda ya fito da karan sigari ya jefa baki yana shirin cinna mata wuta Hajiya Kubra ta dakatar dashi. "Kar ka sake ka kuna mana sigari anan domin ba so warinta nake yi ba yanzu nan sai ta ɗaga min hankali, ka bari sai ka fita can waje ka kunna abarka. Ya galla mata harara kana ya yi kwafa tare da cizo la66anshi na k'asa, yana jinjina ranarda duk tashigo hannunshi irin wulak'anci da zai shuka mata dole ya cire sigarin ba don ranshi naso ba. Ahmadu kan ya kasa yak'i da zuciyarsa sai ya ji kamar ya bi bayan Alhaji Abdallah sai kuma wata zuciya ta kwa6e shi gara ya zauna ayi dashi gudun kada giwa ta faɗi aci nama ba dashi ba. Kuma ai ba wurin boka za a je ba balle Aljanar Azaad ta kashe su. *************** A yau Hakeem ya yanke shawarar ya faɗawa Miyya gaskiyar al'amarin, saboda yana so ta tare kafin Azaad ya dawo daga business trip ɗin da ya tafi. Shiyasa ya aika kiranta lokaci da sak'on ya risketa sai da taji matsananci faɗuwar gaba. Tsawon lokaci da ya aika kiranta ta kasa tashi ta je sai tufka da warwara take yi saboda tun daga ranar da taji zancen aurenta dashi take wasan 6oya koda kuskure bata bari suka haɗu ba. Shi kanshi Hakeem yana shakkar yadda zai faɗa mata wannan bak'on al'amarin saboda sun yi wasa da hankalinta ba Kaɗan ba. Amma dole ce tasa su yin hakan. "Wai Miyya ba za ki fito daga d'akin bane ko sai Abban Rayhan ya zo da kanshi?" Muryar Aunty Zaliha ce ta dawo da ita daga duniyar tunani da ta lula, cikin sanyi jiki ta fito sanye da dogon hijab har k'asa tana shigowa falon ta sadda kanta k'asa can nesa dasu ta nema ta zauna, ta shiga wasa da babban yatsar k'afarta ta dama. Hakeem ya rasa ta inda zai fara kama bakin zare sai musu- musu yake da baki kamar mai jan casbi, can dai ya yi ta ɗiya maza ya yi gyaran murya kana ya ce. "Da farkon dai zan fara cewa dake Aslamiyya ki yi hak'uri domin akwai abubuwa da yawa da ya kamata ki sani kafin yau sai dai na 6oye miki ne na bi ki da yadda kika fahimci al'amari ba don komai ba sai don ki sami natsuwa da kwanciyar hankali to Al-hamdu-lillah burina ya cika. Miyya dangane da zancen aurenmu dake ba gaskiya bane amma zancen an d'aura miki aure gaskiya ne. A zahirin gaskiya ba dani aka d'aura miki aure ba da aminina ne kuma d'an uwana Azaad Junaid. A firgice Miyya ta ciro kanta daga k'asa ta jefawa Hakeem wani irin rikittace kallo mai cike da tarin tambayoyi hakan yasa ya gintse bakinshi ya kasa ci gaba da magana... *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 13... Kallo d'aya za ka yiwa Miyya ka gano ba k'aramin firgici da tashi hankali take ciki ba. Ta kasa gasgata abin da kunneta ya ji daga bakin Hakeem gani take yi kamar wasa ne yake yi, kawai so yake ya gwadata shiyasa ya bijiro mata da wannan zance mai kama da almara. Gani ta kasa furta kalma ko d'aya daga bakinta yasa Hakeem ya ci gaba da faɗar "Azaad mutumin kirki ne abokina ne tun na yarinta nasan shi ciki da waje da yana da wata matsala ko gacci da ba zan nema mishi aurenki ba. "Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Hasbunallahu wal'imal wakil.....Ni kan na shiga uku ni Miyya wai meke shirin faruwa da rayuwata ne?" "Alkhairi Miyya Alkhairi ne yake bibbiyarki, wallahi-tallahi da Azaad yana da wata matsala ina da tabbacin Abban Rayhan ba zai shige mishi gaba wajen naman aurenki ba... "Ya isa nace ya isheku haka! an gayamuku rayuwata kwallo ce da za ku dinga jefata raga a duk lokaci da ku kaso?" Ko an gayamuku don banida gata yana nufi ku yi wasa da zuciyata yadda ku ga dama?" Kasa ci gaba da magana tayi sakamakon wani irin nauyi da k'irjinta ya yi kamar an ɗora mata dutsi, tasa hannu ta dafe saitin zuciyarta da ke bugawa da k'arfin gaske. Aunty Zaliha ta taso da sauri ta ɗagota kana ta mik'ar da ita tsaye. Miyya ta kalli Aunty Zaliha da idanuwanta suka fara komawa jajjaye muryarta na rawa ta ce. "Sake ni Aunty Zaliha duk abin da ku ka yi min ba zan ga laifinku ba. Domin da Baffana da kakata ba su ba ku k'ofa ba da ba za ku yi wasa da hankalina har haka ba. Ban ta6a jin haushi kasancewata marar gata ba sai yau. Da ina da gata ko Kaɗan ba za ku kwatata rikita min hankali da tunani ba. "Miyya please Kar ki yi mana mummuna fahimta da fari ki natsu na fahimtar da ke ta yadda za ki fahimci lamarin cikin sauk'i. "Haba uncle Hakeem ya ka ke magana tamkar kana nufi babu zuciya a k'irjina. Miyasa tun farko ba ka fito min a mutum ba. Sai ka yi amfani da rud'add'iyar hanya ka rud'a zuciya da tunanina?" "Nasani Miyya ta yanda mu ka fito miki ba mu kyauta ba. Amma inaso ki sani mu yi hakan ne a dalili ta yanda ki ka fahimci al'amari, mun za6i mu 6oye miki ne saboda ki sami natsuwa da kwanciyar hankali. Ba mu yi haka don cutarwa a gareki ba mu yi ne domin samuwar farin cikinki. Miyya Ina da yak'ini akan Azaad Junaid zai inganta rayuwarki, zai ba ki duk wani farin ciki da kika rasa haɗi da gatan da kike kirara kin rasa. Allah shine shedata na d'auki ke da 'yan uwanki tamkar 'ya'ya da na haifa idan har zan iya cutar dasu to tabbas zan cutar daku. "Na ji uncle Hakeem ba za ka iya cutar dani a zahiri ba amma kasani ka cutar dani a badili, da tun farko ka umarce ni da na aure abokinka nan take zan amince ba tare da dogon tunani ba. Domin hallaci da ka yi min ni da 'yan uwana ka can-canci ka bani umarni na bi. Ka tuna Uncle kaine ka ceto rayuwar 'yar uwanta Amal a lokaci dangin mahaifinmu suke so labarin mutuwarta ya riske su. Ka sanya su makarantar islamiyya da boko ka yi musu gatan da Baffa da Dadda suka kasa yi mana shin wannan Kaɗai bai isa ya haska maka girman da k'ima da kake dashi a idanuwana ba. Fargaba ta d'aya uncle shima Azaad ɗin da saninshi ka auro masa ni ko shima wasa da hankali ka yi mishi kamar dai yanda ka yi min?" Wani irin faɗuwar gaba Hakeem ya ji ya kasa koda kwakkwaran motsi sai kawai ya tsare Miyya da idanuwanshi ya rasa abin faɗa gani haka yasa Miyya ta ce. "Kar ka damu uncle Hakeem tawa k'addara ce ta zo da haka. Kafin ya lalla6o abin faɗa ta cire hannun Aunty Zaliha daga rik'e ta da tayi, ta nufi d'akinsu. Hakeem ya kalli Aunty Zaliha yai mata nuni da ta bi ta har ta buɗe baki za tayi magana ya tari numfashinta. "Je ki kawai Zaliha ki k'arasa faɗa mata anjima za mu rakata gidan mijinta. "Amma Kuma Abban Rayhan..... "Kar ki ce komai Zaliha kawai ki yi abin da nace. "Shikenan. Ta faɗa ba don ranta yaso ba. *********** LOS ANGELES. Su Madam Salima an kammala taro successfully, burinta ya cika ta haɗu da manya-manya jiga-jigai 'yan kasuwa na duniya babu wani kwakkwaran bincike ta dinga zuba hannu jari a duk wani company da ya yi mata. Anan ta haɗu da wata fitattaciyar 'yar kasuwa mai suna Roseline Yaqub Gambella 'yar asalin kasar ethiopian. kasancewar Miss Gambella ta yi suna sosai a duniya kusan ita ce ita the most popular business woman ta biyu a duniya ta shahara a kasuwanci ba Kaɗan ba. Ita ce special guest a taro tun daga lokaci da madam Salima ta kyala ido ta ganta taji tanaso kula alak'ar kasuwanci da ita. Saboda haka ta shiga bibbiyar ta sai a rana ta k'arshe da za a kammala taron ta sami damar haɗuwa da ita, cikin kwantar da kai madam Salima ta nemi da su k'ula k'awance har ta nemi miss Gambella da tasaka hannun jari a company ta da farko miss Gambella bata so ba, saboda ko sunan k'asar Nigeria bata so ta ji an anbata mata, sakamakon wani babban al'amari da ya faru da rayuwarta a can. Wanda har yau ta kasa mantawa balle ta goge shi daga zuciyarta. Yanda madam Salima dinga rarrashinta yasa ta amince, ba don ranta yana so ba sai don wani tunani da ya faɗo mata,ta ware manyan kud'ad'e tai investing hakan a wurin madam Salima ba k'aramar nasara bace domin da yawa su na so tai investing a kamfanoninsu amma basu sami wannan damar ba. Shiyasa alfarinta da izzarta suka k'ara linkawa, tana gani wani tudu ne ta fara takawa na nassarar cika burinta. Washe gari da suka kammala taro ta sake lulawa kasar Turkey, ko tunani yaranta da ta baro bata yi tun lokaci da ta baro gida Nigeria kusan three weeks kenan bata kira waya ta ji lafiyar su ba. Ko Kaɗan yara basu dameta ba ko tana gida ba wani kulawa suke samu daga gareta ba. Sai ta share kwanaki bata saka su a ido ba alhali suna gida d'aya, babu abinda ya dameta tana d'akinta suna nasu kuma bata basu damar zuwa mata bedroom ba. ko shekara d'ari za su yi basu gannta ba, ba su isa su je nemanta a bedroom ɗinta ba. Shiyasa babu shakuwa irin ta uwa da 'ya'yanta a tsakaninsu. A takaice ma mugun tsoronta suke yi. ***************** Misali k'arfe biyar da rabi na yamma aunty Zaliha ta shiga d'akin da Miyya, ta tararda ita ta zabga tagumi ta dukufa tunani makomarta a gidan mutumin da ta ji an kiranshi da suna Azaad. Tashin hankalinta bai wuce Uncle Hakeem ya ce a wurinshi za ta bar Amrah da Amal a cewer shi sai ya ga ta kwantar da hankalinta a gidan mijinta, sannan zai dawo dasu hannunta. Taso tai mishi turjiya saidai kwarjinishi ya hanata. Dafa kafad'arta da Aunty Zaliha ta yi yasa natsuwarta ta dawo jikinta. "Tashi mu tafi Abban Rayhan yana jiran mu a parking lot" Miyya ta 6ata fuska tamkar za tasa kuka, sai kawai tayi k'ok'arin danne hawayenta bata so ta yi kuka gudun jefa k'annaita a damuwa. Batare da ta ce komai ta mik'e already ta shirya cikin Abaya maroon colour, tayi rolling da veil ɗin rigar. Aunty Zaliha ta rik'o hannunta a falo suka iske su Amrah su na jiran fitowarsu. kaitsaye parking lot suka nufa inda Hakeem ke zaman jiran fitowarsu, Amal ta buɗe k'ofar mota aunty Zaliha ta zaunar da ita sai lokaci tai k'arfin hali ɗago idanuwanta ta dubi 'yan uwanta wanda ko Kaɗan bata ga damuwa rabuwarsu da ita akan fuskokinsu ba. Sai ma farin ciki da ta ga su na yi ta girgiza kanta tana mamakin kurciyarsu. Su har sun ga abin farin ciki anan gudun kada ta rusa musu farin cikin nasu yasa ta dangana ta mik'awa ubangiji al'amuranta, abu d'aya tasa aranta muddin 'yan uwanta za suyi farin ciki to kuwa za ta sadaukar da nata. Har Hakeem ya ja mota suna ɗaga mata hannu. Bata mayar musu ba domin gani take da ta mayar musu sun rabu kenan har abada. Suna tafiya Hakeem da Zaliha na mata nasiha da haka suka iso katafare tangamemen Azaad Junaid mansion, tun daga bakin gate ɗin gidan ta gano wata daula duniya ce ta shigo wacce ko a mafalkinta bata zaci za ta tsinci kanta a ciki ba. Kasancewar securities ɗin gidan su san Hakeem da kuma matsayinsa a wurin Azaad Junaid yasa nan take suka buɗe masa gate ya wuce gate na d'aya kana ya zarce na biyu anan ma buɗe masa aka yi sai daff da shiga k'ofar main falo ya yi parking Aunty Zaliha ce ta fara fitowa kana ta buɗewa Miyya k'ofa wacce ta dawo tamkar jini baya gudana a sassa jikinta, idanuwa da gangar jikinta kawai ke aiki yayin da tunani da natsuwarta suka kaura a gareta. Hakeem ya wuce gaba suka mara mishi baya door bell ya danna cikin abin da bai fi 60 seconds ba Nanny Lacey ta buɗe k'ofa...... *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 14... A babban falon gidan suka zauna. Nanny Lacey ta kawo musu ruwan sha da juice. Murya can k'asa Hakeem ya gabatar mata da Miyya. Ya kuma k'ara gargadinta kada ta faɗawa kowa matsayinta a gidan duk da k'asa-kasa ya yi magana kuma cikin harshen turanci ba wani turanci kirki take ji ba amma ta fahimci abin da yake faɗi. Sosai ta k'ara shiga damuwa har ta fara zanci zuci "oh! Ni Miyya naga takaina wannan wane irin aure ne ya Rabbi ka taimake ni ka bani ikon cinye wannan jarabawa" "Miyya wannan ita ce Nanny Lacey ita ke kula da cikin gidanan tasan komai akanki, sannu a hankali za ta sanarda ke abin da Azaad yake so da wanda baya so za ta kuma warware miki duk wani abu da ya shige miki duhu. Miyya ta ɗago da idanuwanta ta kalli Hakeem kana tasake sadda kanta k'asa, batare da tace komai ba. Hakeem ya umarci Nanny Lacey da ta kira mishi Aneesah da Airah. Ko wace tana d'akinta a k'unshe sun ri ga da sun saba da zaman d'aki idan basu d'aki suna study room. In ko ka ga sun fito downstairs parlor abinci za su ci ko kuma malami da ke faɗa musu karatu al'qur'ani ne ya zo. Rayuwarsu a tak'ure take basu san komai ba sai karatu gara Princess Aneesah tana chat da school mates ɗinta. Shima a 6oye take yi saboda dokar Daddy ce bai amince da social media platform ba, shiyasa take taka tsan-tsa kada ya gani. Airah ce ta fara fitowa tana sanye da pink belted top ta sauka iya guiwarta, ta yane kanta da white scarf kafafuwanta sanye cikin black thongs slippers irin masu taushin gaske. Da gudu ta k'arasa saukowa daga kan staircase tana zuwa ta faɗa jikin Hakeem, ta rungumeshi tana dariya kana ta ce. "Welcome uncle I miss you so much! "I miss you too baby girl how are you doing?" "I'm fine uncle. Ta dawo da ganinta akan fuskar aunty Zaliha ta gaidata zaliha ta amsa mata cikin sakin fuska, Aneesah ta sauko tana murmushi jikinta sanye da sky blue three quarter haɗe da white armless top gaban rigar na d'auke da zane teddy bear, kanta ba d'an kwali gashi kanta ya sha gyara tayi matuk'ar kyau duk da fuskarta ba makeup. Da fara'a ta k'araso ta ce. "Good evening uncle. Good evening aunty" Kusan a tare suka amsa mata kana Hakeem ya nuna mata kusa dashi. "Princess zo ki zauna we have to talk" Da sauri ta zauna tana mai ci gaba da murmushi su na matuk'ar k'aunar Hakeem saboda yana sake musu sosai fiyye da yadda iyayyensu ke musu gashi da wasa da dariya akwai shak'uwa mai k'arfi a tsakaninsu a duk lokaci da ya zo gidan ya kan 6ata lokaci mai yawa a tare dasu. "Daddy kafin ya tafi ya faɗi maku zan zo muku da new Aunt ko?" Hakeem ya faɗa yana kallon fuskokinsu, domin ya ga yana yi da suka Kar6i zance nashi. Airah tai sauri faɗi. "Yes uncle amma har yanzu ba ka kawo ta ba. "Gata can na zo muku da ita tana da kirki sosai hope ba za ku yi mata rashin kunya ba?" Ya k'arashe magana tare da pointing Miyya da finger shi, kusan a tare suka kalle side ɗin da ya nuna. Airah ta tashi sauri ta nufi wajen Miyya tare da sa hannunta ta ɗago fuskarta. "Wow! She's very beautiful I like her uncle Hakeem. Airah ta faɗa very excited. Yayin da Aneesah ta yatsine fuska tare da mak'e kafad'arta irin I don't care attitude ɗinan. Kusa da ita Airah ta zauna ta shige jikinta Miyya dai sai murmushin yak'e take yi. "Uncle wannan ita ce kuwa new aunt Daddy ya ce ka kawo mana because na ganta k'arama wannan she's just my age mate fa?" Da sauri Hakeem ya tarin numfashinta ta hanyar faɗin. "Da kyau miss complainer dama nasan za a yi haka to friend na kawo miki kawai ki kwantar da hankalinki tana da kirki za ki ji dad'in k'awance da ita. Ta mik'e tare da kallon uncle a ɗage ta ce. "Uncle bari na tafi zan yi karatu I have a test tomorrow. Daga haka ta nufi staircase ta haura da gudu kusan su duka suka bi ta da kallo, kafin ya dawo da ganinshi akan Nanny Lacey ya mik'a mata makulli mota ta daukowa Miyya luggage ɗinta a mota ya gyara zaman shi tare da kiran sunanta. "Aslamiyya!" "Na'am! Ta amsa can k'asan mak'oshi. "Ki yi hak'uri da duk abin da za ki gani a gidanan na dad'i ko kuma sa6aninsa. Ko wane mataki na nasara a rayuwa ba zai zo cikin sauk'i ba dole akwai wasu challenges ki sa aranki Aneesah tana d'aya daga cikin challenges da za ki fuskanta anan gidan. dangane da ci gaba da karatunki kuma in-sha-Allah idan Azaad, ya dawo daga tafiya mu yi magana akai. Ta kasa amsa mishi sakamakon kuka da yake shiri kwace mata, alhali bata shiryawa zuwansa ba. Nanny Lacey ta shigo janye da luggage ɗinta. Hakeem ya kalleta duk tausayinta ya kama shi da kyar ya iya buɗe baki ya ce. "Kada ki sa damuwa aranki Miyya I know you're a strong girl you can do it tashi ki bi Nanny Lacey za ta nuna miki d'akinki. Da kyar ta mik'e tsaye sakamakon yadda kafafuwanta suka yi mata nauyi, Airah ta rik'e mata hannu Nanny Lacey ta wuce gaba suka biyo ta a baya. Ɗaya daga cikin rooms ɗin da ke downstairs Nanny Lacey ta kaita bata yi ganganci kaita upstairs ba, saboda gudun abin da zai iya faruwa idan madam Salima ta dawo. ***** **** ***** Hasheem tare da professional killers ɗin da ya gayyato tun daga cross river, yana tsare musu yadda yake so kisan Azaad Junaid ya kasance, cikin muryarshi m cike da zallan mugunta yake magana. "Azaad zai dawo Nigeria nan da two weeks da zarar ya fito daga airport akan hanyarsa ta zuwa gidanshi nakeso ku kundume shi banaso a sami kuskure komai k'ank'antarshi ku hal6e shi a kai kamar yadda muka tsara" "Don't worry sir Hasheem king Kevin bai ta6a missing target ba kawai ka tanadi remaining balance ɗinshi yana kammala maka aiki zai koma inda ya fito. "Kar ka damu Tajo kud'i ba matsalata bane tun da na bashi rabi raguwar ma za a cika masa. **** ***** **** A cikin kwanaki huɗu da Miyya tai a gidan tayi sabo da Airah da Nanny Lacey sai Kuma Ahlam wacce da farko bata yarda da ita, amma yanzu koda yaushe tana wajenta hakan ba k'aramin dad'i Nanny Lacey ta ji ba. Ko ba komai Miyya ta fara rage mata wani nauyi. A wajen Aneesah ne har yanzu ba wani canji inda za su yi haɗu sau dubu a downstairs parlor ba za yi wa Miyya magana ba. Saidai ita Miyya tai mata kuma ba lallai bane ta amsa. Kasancewar yau Saturday babu school Airah ta shigo d'akin Miyya rik'e da story book a hannunta. "Pretty zo mu je garden na karanta miki story book ɗinan yana da dad'i sosai" Miyya ta ɗago daga gyarawa Ahlam gashinta da take yi tana murmushi ta ce. "Keɗai Airah bakya gajiya da karatu kamar wata alhudada ba kuma na faɗi miki ki daina kirana da pretty ba. "Ni fa nafi jin dad'i kiranki da Pretty fiyye da ko wane suna, kema da sannu za ki zo ki saba saboda gidanan ba mu da wani aiki da ya wuce karatu. Dariya mai d'an sauti Miyya tayi, kafin ta ce. "Inaso karatu Airah amma ba iri wanda ku ke yi ba ace Dan adam bashida hutu a rayuwarshi sai na karatu ai sai kwakwalwar mutum ta cushe. "Mu ai ya zame mana jiki ba abin da kwakwalwar mu zai yi. Tun da ba ki so story ki zo mu je mu yi wasa 'yar 6oya irin na jiya naji dad'inshi sosai. "Bari na kammala gyarawa Ahlam gashinta sai mu je amma fa yau za a rufewa idanu, don na fahimci Airah ba k'aramin wayau ne dake ba. Miyya ta k'arashe magana tana hararata. Dariya Airah tayi har tana had'awa da rungume Miyya, a duk lokaci da suke tare Airah na tsintar kanta cikin farin ciki da nishadi zuwan Miyya ba k'aramin sauyi ya kawowa rayuwarta ba. Tana k'arasa gyarawa Ahlam kai suka fita a compound, Miyya ta cire d'an kwali kanta ta rufewa Airah idanuwa ta gudu bayan flowers ta 6oye yayin da Airah take ta faman lalla6e nemanta. Aneesah ta gaji da kwanciyar a d'aki ta fito a balcony tayi tsaye hannuwanta rungume a k'irjinta cike da sha'awa take kallon Miyya da Airah da ke wasan su cikin nishadi da kwanciyar hankali har batasan lokaci da ta fara murmushi ba. Sosai irin wasani nan ke burgeta saboda tun a yarinta ba a basu damar yi sa ba. Tana so ta sauka k'asa ta je su yi da ita amma tana ji tafi k'arfin yin wasa da Miyya kasancewata housemaid. Ana ta tunani Miyya 'yar aiki ce shiyasa har yau ta kasa sakin jiki da ita duk da a wasu lukata tana matuk'ar burgeta. Sai daff da magarib suka dawo cikin gida bayan sun kammala sallah, Airah tai matashi kai da cinyoyin Miyya sai surutu take zuba mata ita ko sai murmushi take yi zafi-zafi take tankawa. Nanny Lacey ta shigo rik'e da waya a hannunta ta mik'awa Airah. "Daddy is on the line" Ta faɗa lokaci da ta bata wayar cike da zumudi Airah ta kar6i wayar ta kara a kunneta. A hankali take magana Daddynta tamkar ba Airah ba sarkin surutu, kamar daga sama miyya ta ji tana faɗin. "Daddy in bai wa pretty waya ita ma ta faɗa maka abin da take so, ka siyo mata nata tsaraba?" Rass....rass....gaban Miyya ya shiga dukan tara-tara ba bu shiri ta dafe k'irjinta da hannunta na hagu ok *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 15.... "D'an dakata mana Mamana" ya faɗa kamar mai koyon magana. Ta fasa cire wayar daga kunneta. "Ba sai kin bata waya ba duk abin da na siyo miki ita ma zan siyo mata irinshi. "To Daddy amma yaushe za ka dawo?" "Maybe next week. "Okay Daddy take care I love you. "Love you too my baby bye. Ya datse kira Airah ta ciro wayar ta mik'awa Nanny Lacey da ke tsaye tana jiranta, Miyya ta kalli Airah na wani lokaci kafin a hankali ta saki ajiyar zuciya saboda ko Kaɗan bata shiryawa magana da Azaad Junaid ba. Tun sanda Airah ta nuna mata hotonshi ta ganshi babban mutum, kuma kyakyawan gaske mai cike da haiba da kwarjini, take jin tsoro da fargaba haɗuwa dashi. Sosai taga wauta Uncle Hakeem na had'a shi aure da ita ba sai an faɗa mata ba ita da kanta ta gano ba level ɗinta bane. "Yadai pretty tunani Amrah da Amal ki ke yi ko?" Airah ta faɗa tare da lek'a fuskar Miyya. Shiru tayi ta kasa bata amsa sai kawai Airah ta ci gaba da faɗin. "Ba nace ki bari na faɗawa Nanny Lacey ta kira uncle Hakeem ya kawo miki su ba, kin ce a'a amma kuma sai tunaninsu ki ke yi. Miyya ta sake jan numfashi kana ta sauke cikin muryarta mai cike da natsuwa ta ce. "Tashi mu yi sallar isha yau da wuri nakeso na kwanta" Daga haka Airah bata sake magana ba sai kawai ta bi umarninta. A kwana a tashi lokaci yana ta tafiya Miyya har tayi cika two weeks a gidan, sosai shak'uwa da k'auna mai k'arfi ta shiga tsakaninta da Airah da Ahlam har ta kai a yanzu a d'akinta suke kwana. A koda yaushe idan taga Nanny Lacey a kitchen ta kan je ta tayata girki, sosai ta sami kar6uwa a wajen housemaids ɗin gida kowa k'aunarta yake yi saboda Miyya mutum ce mai saurin shiga rai. A two weeks da tayi da yana yi mu'amalarta da mutane gidan za ka zaci ta shekara da saninsu. Miyya tana da hak'uri uwa-uba sanyi hali gata shiru-shiru magana ma wahala take mata ga yawan murmushi saidai akwai saurin yin kuka. Rashin kulata da Aneesah ke yi ba k'aramin damunta yake yi ba. Har cikin ranta take ji k'aunarta shiyasa a duk lokaci da ta ga Aneesah ta sauk'o k'asa sai ta gaidata, burinta su sami kyakkyawar mu'amala. Tun Aneesah bata amsawa har ta zo yanzu tana amsawa saidai a gajarce. Yau ma dukansu suna zaune a downstairs parlor, suna cin pancake da Miyya tai musu Aneesah ta sauk'o cike da yanga wacce ta zame mata jiki ta kalle su ta d'auke kai, ta nemi kujera da ke nesa dasu ta zauna tare da crossing legs ɗinta. Miyya ta dubeta tana murmushi ta ce. "Barka da fitowa Aneey" Sai da ta yatsine fuska tukun kafin ta amsa da "Sannu! Miyya ta d'auki plate ta zuba mata pancake ta sauke Ahlam daga jikinta, ta nufi wajenta ta mik'a mata. "Aneey ga pancake nai mana ci ki ji ko ya yi dad'i?" Ta faɗa da yalwatattace murmushi akan innocent face ɗinta, shiru Aneesah tayi tana tattance irin kalar wulak'anci da za ta yi mata. Sai kawai ta buge plate ya faɗi pancake ɗin ya zube akan tiles, cikin tsawa ta ce. "How dare you to bring me this trash ban faɗa miki ba ki daina shiga harkana ba?" Ko dole ne sai na kula ki what kind heartless you're?" Tuni idanuwan Miyya suka kawo ruwa sai k'ok'ari hana su zubowa take yi, Airah ta taso cikin fushi ba k'aramin haushi take ji ba a duk lokaci da Aneesah ta yiwa Miyya wulak'anci. "Wai miye haka ne Aneey ke ko Kaɗan ba a miki abin kirki ne sai kin ma mutum wulak'anci, wallahi da nice pretty da tuni na tattara ki na zubar a bola. A fusace Aneesah ta mik'e ta nuna Airah da yatsa tana faɗi "Hey...watch your tongue "An k'i ɗin sai ki zo ki dakeni. Airah ta faɗa tana galla mata harara. Sosai hakan ya k'ara harzuk'ata ta soma zazzaga masifa. "Tuni nagano Airah kin fiso stranger akan ni 'yar uwarki ta jini, kwatata kin daina kulani saboda ita amma ba komai ki jira mommy ta dawo wallahi sai tabar gidanan. Ta k'arasa magana muryarta yana rawa kamar za ta fashe da kuka. "Tun kafin mommy ta dawo ki zo ki fitar da ita ai kema kin isa ko?" Airah ta faɗa a fusace kuma cikin shouting. Da sauri Miyya ta jawo hannunta. "Miye haka Airah yayarki ce fa?" Bai dai-dai bane ki faɗa mata irin wannan magana. Kafin Airah tai magana Aneesah ta rigata ta hanyar furta. "Ba wani nan duk ke ce kika janyo kafin zuwanki gidanan Airah bata isa na faɗa ta faɗa ba, saboda haka dole ki bar gidanan. "Ba isa ki ba wallahi Aneey you're not a Daddy saboda shi keda iko zantarda hukunci Kuma shine silar zuwanta gidanan. Ita ma Airah ta faɗa a fusace. "Airah please ya isa haka tun farko laifina ne da na kasa daina shiga sabgarta. Miyya ta faɗa cikin sanyi murya kana ta kalli Aneesah ta haɗe hannuwanta alamar rok'o. "Ki yi hak'uri Aneey tun da bakyaso ba zan k'ara ba kinji?" "Haba pretty miye na bata hak'uri ita ya dace ta ba ki hak'uri ba ke ki ba. Airah tayi magana cike da jin haushi hak'uri da Miyya take bata. "A'a Airah laifina ne dole na bata hak'uri. Ina k'ara ba ki hak'uri Aneey. "Go to hell!!! Aneesah ta faɗa cikin ihu wanda ya janyo hankali Nanny Lacey ta fito da gudu daga d'akinta, tana tambayar meke faruwa. Aneesah bata bi ta kanta ba ranta a mugun 6ace ta juya da gudu ta haura staircase ta shige d'akinta. Airah ce tai mata bayani Miyya kuma ta duk'a ta shiga tsince pancake ɗin da Aneesah ta zubar. Hak'uri Nanny Lacey ta bata. "Its ok Nanny. Ta faɗa a gajarce tare da nufar kitchen ta kai plate, za ta fito dai-dai Airah ta shigo tana zuwa ta rungumeta cikin taushin murya ta ce. "I'm sorry pretty karki damu da abin da Aneesah take miki, bata da halin kirki she's very bad girl... Da sauri Miyya tasaki wa Airah duddu a gadon bayanta tare da faɗin. "Za mu 6ata Airah idan kina faɗawa yayarki kalaman rashin ɗa'a. "Ouchh.... pretty da zafi fa. Ta faɗa cikin shagwa6a tana shafa gun da Miyya da buga. "Sorry.... Cewar Miyya tana dariya kana suka fito daga kitchen ɗin, Airah ta kalli Miyya with serious face ta ce. "Ni fa pretty na ganoki kin fi so wannan arrogant Aneey akaina" Murmushi kawai Miyya tayi ta d'an ture Airah, ta wuce d'akinta. Miyya bata daddara ba da yamma ta ga Aneesah bata fito ba sai kawai ta sulelewa Airah ta nufi d'akinta, sai tayi niyyar knocking sai kuma ta fasa tayi haka kusan sau uku sai a na huɗu tayi knocking on. "Yes come in the door is open" Ta tsikayo muryar Aneesah daga ciki, ta danne zuciyarta ta tura k'ofa wannan shine karo na farko da ta fara shiga d'akinta. Tana bibiyar Aneesah ne saboda ta fahimci saboda su Azaad Junaid ya aure ta. Don haka ta k'udurta aranta za ta yi hak'uri ta bi ko wace hanya da za su sami jituwa a tsakaninsu. "Assalamu Alaikum! Da sauri Aneesah ta ɗago idanuwanta taga game ɗin da take yi a wayarta, fuskarta ta kasa 6oye mamaki gani Miyya a d'akinta nan take ta daure fuska. "Aneey cewa nayi amincin Allah ya tabbata agareki amma kuma kin kauda fuska addini musulunci babu kyau ai ma mutum sallama ya kasa amsawa" Miyya ta faɗa cikin tattausan lafazi jikin Aneesah ya yi sanyi ta juyo amma bata bari ta had'a ido da miyya ba ta ce "Wa'alaikum salaam! Shikenan ko?" Ta faɗa tana yatsine fuska. "Dama na zo ne na duba ki naga tun safe ba ki k'ara saukowa falon k'asa ba?" Shiru Aneesah tayi tana k'ara mamakin Miyya wacce irin zuciya ce a k'irjinta da take jure wulak'anci. "Aneey kin yi shiru ba ki ce komai ba, Ko dai har yanzu fushi kike yi dani?" "Bana fushi da mutane da basu da muhimmanci a gareni. Yadda tai magana bai ma Miyya dad'i ba don har hakan ya nuna akan fuskarta, amma sai ta daure ta sake cewa. "Na sani Aneey banida muhimmanci agareki amma ni kina da a wurina saboda muhimmancinki yasa har na dako k'afata a dakinki. Furuncinta ba k'aramin rikita tunani Aneesah ya yi ba, duk ta ji wani iri sai ta hana hakan tasiri akanta cikin muryar reni hankali da gatsali ta ce. "To naji za ki iya tafiya Ina buk'ata huta banaso damuwa. Ta k'arashe magana haɗi da pointing k'ofar fita da yatsanta, jikin a sanyyaye Miyya ta buɗe k'ofa ta fito karaf idanuwanta suka faɗa cikin na Airah da ke tsaye tayi folding hannuwanta a k'irji tana facing k'ofa. Ta ɗage girar ido tana kallonta kafin ta girgiza, ta ra6a ta gefenta ta shiga d'akin na Aneesah, jin k'arar buɗe k'ofa yasa Aneesah ta taso a fusace a tunanina ko Miyya ce ta sake dawowa sai idanuwanta suka sark'e da na Airah, ta galla mata harara kana ta koma ta kwanta ta bata baya. Airah tayi murmushi tare da zaunawa kusa da kafafuwanta cikin tattausa murya ta ce. "Aneey please wake up we have to talks. "About what??" Ta tambaye ta batare da tashi ba, balle ta kalleta. "Pretty! Airah ta faɗa a gajarce. Sai da Aneesah ta 6ata lokaci kafin ta tashi zaune tana mai k'ara tanke fuskarta. "Aneey zuwan pretty gidanan ta miki wani laifi ne da yasa kika tsane ta har haka?" "Banaso silly questions Airah. "Babu zance silly questions Aneey abin da kike yi kwatata bai dace ba, nasani haka kawai kika tsaneta alhali bata miki laifin komai ba. "Ni nace dake na tsaneta?" "Ba sai kin faɗa min ba Aneey ga alamomi nan a bayane, ko magana tai miki a lalace kike amsawa Ina laifin wanda ya damu da kai. "Wai ke Airah meke damunki ne huh?" zuwan wannan Miyya gaba daya kin canza, ba ki da zance sai nata wato ta zo ban bata fuska ba shine ta turo ki, da yake bakida kunya shine za ki zo ki cika min kunne Dan Allah tashi ki fita min daga d'aki banaso tak'ura. Haushinta ne ya turnuk'e Airah ta juya a fusace ta buɗe k'ofa da k'arfi, ta fita. A falon k'asa ta tararda da Miyya tana zaune Ahlam tana kwance akan cinyoyinta taso tai mata korafi akan zuwanta d'akin Aneesah sai kuma ta fasa, ta kalleta a natse ta ce. " Pretty ko za ki tashi mu tafi flat ɗin Jadda kwana biyu ba mu lek'a ta ba.?" Da sauri ta tashi dama tana sanye da gown na atamfa ta yane kanta da k'aramin veil. A falo suka iske Jadda tare da mai aikinta Mero, da yake wannan zuwan shine karo na uku da Miyya ta je 6angare Jadda. Da yake Jadda tasan komai akan Miyya, ta yaba matuk'a da hankali da natsuwarta Sosai taji ta kwanta mata a rai. Saidai fargabarta d'aya idan uban gayya Azaad ya dawo zai kar6e ta kuwa ya kuma zamanta da Madam Salima zai kasance?" Da yake Azaad bai faɗa mata ya saki Madam Salima ba. Shiyasa duk lokaci da suke je 6angarenta sai ta ke6e gefe d'aya da Miyya tayi mata nasiha. Sosai Miyya ke jin k'aunar Jadda a zuciyarta. **** ***** ****** Misali k'arfe biyu na dare ciwon mara mai tsanani ya tashi Aneesah, sai juyi take yi ita Kaɗai akan gado dama ga goganyar taku da raki tsiya ta 6are baki ta shiga rera kuka duk lokaci da za tayi menstruation sai tayi ta fama da ciwon mara. Tun tana kuka da k'aramin sauti har ta dawo tana yi da k'arfi, gani kuka ba zai mata magani komai ba ta d'auki wayarta, ta kira Nanny Lacey. Can cikin barci Miyya ta ji ringing ɗin wayar Nanny Lacey da Airah ta aro mata tayi waya da Amrah da Amal, ashe Airah ta manta bata mayar mata ba. Cikin magagin barci ta mik'a hannu ta d'auki wayar da ke aje akan bedside, da nufi tai switch off ɗinta sai kawai taci karo da sunan Aneesah gabanta ne ya fara faɗuwa, saboda tasan da wuya in kira na lafiya ne kasancewar da ta dauko wayar sai da dubi lokaci. Tai picking tare da karawa a kunneta cikin muryarta mai cike da barci ta ce. "Hello.....Aneey Miyya ce wayar Nanny Lacey tana hannuna kina bukatar wani abu ne ko na Kai mata wayar ne?" "Wayyo Allah pretty ki taimake ni zan mutu... Muryar Aneesah tai mata dirar mikiya a dodon kunneta, babu shiri ta wartsake daga raguwar barci da bai k'arasa sakinta ba. Cikin azama ta mik'e zaune. "Subhanalillah.....Aneey ba ki da lafiya ne?" "Mara ta ke ciwo dan girman Allah ki taimaka min ki kira Nanny Lacey. "Okay..gani nan zuwa. Ta faɗa cikin rawar murya a rikice ta saka thongs slippers ta buɗe k'ofa, a rud'e take haura staircase tana murd'a handle ta ji k'ofa ta buɗe, ta kutsa kai ta hango Aneesah kwance sai mul-mula take yi in ta kai k'arshen gado ta dawo farko da gudu ta nufe ta gaba ɗaya ra rungumo ta zuwa jikinta. "Sannu....sannu....Aneey kin sha magani kuwa?" Cikin tsananin zafin ciwo Aneesah ta girgiza kanta. "Akwai magani ne ko na tashi driver mu kai ki asibiti?" "Ki duba cikin bedside drawer yana ciki. Aiko kamar jira Miyya take yi ta ɗora kanta a pillow ta k'arasa da sauri ta binciko magani, ta buɗe fridge ta dauko water bottle hannunta na rawa ta 6alle murfi tare da 6allo magani ta ɗago Aneesah tasa mata a baki tasha. Sai faman sannu take mata. Aneesah sarkin raki ta bi ta k'am-k'ame Miyya, hakan da tayi sai ya k'arawa Miyya tausayinta, batasan lokaci da ta fara tayata kuka ba. Sai daff da asuba barci ya d'auke ta, kanta na bisa cinyoyin Miyya ita kuma ta jinginar da bayanta ga gado a haka tayi barci k'arar alarm da ya karad'e d'akin ya falkar da Miyya ta dauke kan Aneesah a hankali daga cinyoyinta ta ɗora a pillow kana ta wuce bathroom tayi koda ta kammala sallah Aneesah ta buɗe idanuwanta a hankali ta bi d'akin nata da kallo karaf idanuwanta ya sauka akan Miyya. Kwakwalwarta ta soma yi mata backwards ɗin abin da ya faru, da hanzari Miyya ta cire hijabi ta nufo wajenta. "Sannu Aneey ya jikin naki?" Da sauri ta rufe idanuwanta cike da tsan-tsan kunyar tunawa da irin wulak'anci da ta dinga yi wa Miyya, amma bata kunlace ta ba. Ta kuma taimake ta a lokaci da take tsananin buk'atar taimako. Kasa amsawa tayi sai kawai ta yunk'ura ta sauk'o daga gado batasan cewa lokaci da take barci period ɗinta ya zo gaba ɗaya sleeping dress ɗin jikinta da bedsheet ya lalace da jini. Da sauri ta runtse idanuwanta Miyya ta dafa kafad'arta cikin sanyi murya ta ce. "Sannu Aneey tun da ya zo ai lafiya ta samu bari na had'a miki ruwan wanka. Bata jira jin ta bakinta ba ta shiga bathroom da saurinta ta had'a mata ruwa kana ta fito da towel t mik'a mata, jikin Aneesah ya yi sanyi lak'ass...ta kar6i towel ɗin cike da kunya ta cire kayan jikinta tana rik'e da kayan ta shiga bathroom Koda ta fito Miyya ta canza mata bedsheet. Tana cikin saka kaya Miyya ta shiga bathroom babu kyama balle kyakyami ta wanke bedsheet da kayan da ta cire ta fito dasu cikin rubber bucket. Sosai Aneesah ta girgiza da gani hakan nan take ta tuna da ranar da ta fara menstruation hakan ne ya faru da ita a lokaci, madam Salima tana gida bata yi duba da shine ranar ta na farko ba ta 6al-6aleta da masifa, wai bata so k'azanta da sakarci haka ta fita abinta tabar ta sai Nanny Lacey ce ta taimaka mata ta kuma nuna mata yadda ake yi. Tsabar haushi abin da mommynta tayi mata yini tai tana kuka a d'aki sai gashi yau, wacce ta rena ta kuma tsana tayi mata abin da uwar da ta haife ta ta kasa yi mata. Har Miyya ta fita ta Sanya kayan a backyard ta dawo Aneesah tana tsaye gaban mirror tana zuba tunani. "Aneey ki kwanta ki huta yau ba sai kin je school ba tun da ba ki da lafiya bara na haɗu miki breakfast" Muryar Miyya ta dawo da ita natsuwarta, har Miyya ta juya ta ji Aneesah ta rungumeta ta baya tana shasshekar kuka cikin muryar kuka take faɗin. "I'm very sorry pretty please forgive me I know I hurt you several times, Dan Allah ki ce kin yafewa marar kirki Aneey... Da sauri Miyya ta juyo da ita ta rik'e hannayenta duka biyu ta kalli cikin idanuwanta tana murmushi, kana ta ce. "Na yafe miki Aneey dama ban ta6a rik'e ki a zuciya ta ba. Kawai nasaka araina rashin fahimta ne a tsakaninmu, Kuma wata rana za ki fahimce ni. "Thank you so much Pretty you're the simplest, sweetest and best person I ever come across in my entire thank you for having you in my life. Zuwanki alkhairi ne a gidanmu da ma rayuwarmu duka. Ta k'arasa magana tare da sake hugging Miyya tightly, tuni tasa Miyya 'yan mata hawaye Aneesah ce ta fara janye jikinta, tasa hannu ta goge hawayen kumatunta tana jin wani irin farin ciki da annashuwa wanda ta dad'e rabon da ta ji kanta a ciki. Miyya ta fice kaitsaye d'akinsu ta wuce koda ta shiga Airah ta fito daga wanka, a gurguje ta ba wa Airah labari abin da ya faru sosai Airah tai farin ciki jin Aneesah ta sauko har ta ba wa Miyya hak'uri. Daga ranar Miyya da Aneesah shak'uwa mai k'arfi ta shiga tsakaninsu suka dawo k'awaye, dukansu sun matsu daddy ya dawo akai miyya school ɗinsu. A cikin dare jirgin da Azaad Junaid ya shigo ya sauka a Malam Aminu Kano international airport..... *Not Edited!!* *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 16.... Azaad ya fito daga jirgi as usual fuskarshi a murtuk'e babu annuri ko Kaɗan. Ya shak'i sanyayye iskar mai dad'i gaske, kana ya saki ajiyar zuciya. Direbanshi mr Richard ya je daukarshi. Duk da yana cikin yana yi na rashin jin dad'i hakan, bai hanashi furta addu'ar neman tsari daga sharrin abin hawa ba. "Bismillahi majraha wa mursaha Inna Rabbi laa ya gafurum Rahim" Mr Richard ya buɗe mishi k'ofa ya kame a owners corner, tun shigar shi jirgi yake jin canji a jikinshi wanda ya rasa gane na menene. Ta 6angaren Hasheem Kuma ya sami labarin dawowar Azaad. Ya tura 'yan ta'adda da ya yo hiring su ka la6e a wajen Airport su na jiran fitowar Azaad. Akan idanuwansu Mr Richard ya fito daga cikin airport King Kevin ya duba agogon hannunshi k'arfe biyu da rabi yasaki kafirin murmushi, kana ya fito da silent pistol ya gyarata da kyau. Kana abokin aikinshi Tajo ya kai hannunshi da suna ya tashe mota, ya ji babu key da sauri ya kunna haske dake cikin motar ya ga babu key cike da zallan mamaki ya ke duba k'asan kafafuwanshi Koda ya subuce ya faɗi. Wasa-wasa key ɗin ya ci tudu ya ci rafi, da sauri dukan su suka fito daga mota Tajo sai faman lallu6e ajihunshi yake yi cike da takaici ya shure tayar mota tun su na iya hango hasken motar Azaad har ta 6ace musu fatt....su na ji su na gani mission ɗinsu ya yi failed. Babban abin da ya daure musu kai bai wuce lokaci da suka koma cikin mota ba sai ga key sakale a jikin mota, alamar yana nan a mazauninsa su ne Allah ya d'aukewa gani, shiyasa basu ganshi ba. Cikin kariyar ubangiji da tsarewarshi Azaad Junaid ya iso gidanshi, cikin k'oshin lafiya. Ya yi amfani da k'ofar baya ya shiga part ɗinshi dama haka yake yi duk lokaci da ya yi tafiya ya dawo cikin dare ta k'ofar yake bi. **** ***** ***** *A WASHE GARI* Tun Asuba da Miyya ta falka bata koma barci ba, ta zauna tana morning azkar, sai misali k'arfe 7:00am ta kammala. Ta sauya kayan jikinta zuwa wata half gown wacce ta sauka iya gwiwoyinta, d'an zamanta da Aneesah ta koyi amfani da english dress. Kitchen ta nufa ta tararda da Nanny Lacey tana fera Irish ta shiga taya ta cikin k'ank'ani lokaci suka kammala arranging table, kana ta wuce d'aki tayi wanka tana cikin sanya earrings. Aneesah ta shigo cikin school uniform, murmushi suka sakewa junansu. "Ina Airah?" Miyya ta faɗa tare da daukar perfume bottle tana fesawa jikin kayanta. "Tana Dining room ke muke jira za mu wuce school kada mu yi latti. "Okay mu tafi kawai dama na kammala shiryawa sai na tuna ban saka earrings ba shine na tsaya sakawa sai gashi kin shigo. Ta k'arashe magana tare nufar k'ofar fita Aneesah tana biyo ta baya a haka suka isa dining room, agurguje Aneesah tasha ruwan tea, Miyya tai musu rakiya zuwa parking lot idan direbansu ke zaman jiransu. Har motarsu ta fice daga gate ɗin gidan tana tsaye rungume da hannayenta a k'irji, sosai take sha'awar karatun boko saidai a duk lokaci da tuna Amrah da Amal suna zuwa school, sai taji wani irin dad'i marar misaltuwa ya lullu6e ta. Ko bata samu damar ci gaba da karatu ba tun da siblings ɗinta sun samu shikenan burinta ya cika. ta d'auki dogon lokaci a tsaye kafin ta dawo cikin gida. Sai misali k'arfe 11:45am Azaad Junaid ya falka daga barcin gajiya ya yi wanka ya shirya cikin brown jallabiya, ya saka flip flops a k'afarshi jikinsa na fitarda sihirtattace k'amshin turaren casual oud gold edition. Cikin takonshi na k'asaita yake saukowa daga staircase. K'amshin turarenshi da Nanny Lacey ta shak'a daga kitchen ya isar mata da sak'on dawowarshi. Da sauri ta wanke hannuwanta ta fito, ta iske shi tsakiyar falo tsaye. "Barka da dawowa Yalla6ai. Ta faɗa cikin hausarta da ta zauna daram a halshenta. Ya amsa mata ba tare da ya kalle ta ba. "Yalla6ai akwai abinci a dining room na zuba maka ne?" Ta faɗa kanta yana kallon k'asa. Sai da ya d'auki lokaci kafin ya jinjina kanshi, da mugun sauri ta nufi dining room. Miyya na zaune a d'aki rungume da Ahlam wacce ta lafe a jikinta tun jiya ta ji jikinta da zafi da safe da ta zo yi mata wanka ta ji jikin nata yafi jiya zafi a haka ta lalla6ata tai mata wanka ta shiryata cikin riga da wando ta ɗora mata cardigan akai. Lokaci da ta je had'a mata madara a kitchen, ta sanarda Nanny Lacey ta bata maganin zazza6i madarar ma Kaɗan tasha ta kauda fuska, sai kawai Miyya ta bata magani shine fa ta sake yin barci a cikin barci ta zabura kamar wacce ta tsorata, ta fara tsala kuka a rikice Miyya ta fito daga bathroom. Ta d'auke ta taji jikinta ya yi wani irin mugun zafi, kafin tayi wani yunk'uri Ahlam ta fara kwara mata amai ta baki da hancinta duk idan hankali Miyya yake ya tashi, da gudu ta fito da dukan k'arfinta take kwallawa Nanny Lacey kira. "Nanny Lacey! Nanny Lacey! zo ki gani jikin Ahlam ya yi tsanani sai amai ke fitowa ta baki da hancinta, na shiga uku Nanny Lacey kada wani abu ya sami ta... Idanuwan Miyya sun rufe sam bata lura da Azaad Junaid dake tsaye nesa da ita Kaɗan yana waya da Hakeem, hatta da Hakeem sai da ya ji ihunta, ta cikin waya nan take ya ji matsanancin faɗuwar gaba a nufinshi yanzu da suke waya yana yunk'urin baiyanawa Azaad wacce ya auro mishi sai gashi Miyya ta rage mishi aiki ta baiyana kanta. Tun kafin shi ɗin ya baiyyanata. A gigice Nanny Lacey ta fito daga dinning room hannunta rik'e da serving spoon tsabar rudewar da tayi manta da yana hannunta. Azaad ya waiga a zafafe inda Miyya ke tsaye ya ga wacece ke mishi wannan ihun na fitar hankali, dai-dai lokaci da Ahlam ta sake kwara wani amai gaba ɗaya ya wankewa Miyya jiki. Gudu-gudu ya iso wajen Nanny Lacey ta mik'a hannu za ta kar6e ta, sai kawai tsala ihu tare da k'am-k'ame Miyya. "Kawo ta nan" Cike da k'asaita ya yi magana tare da mik'a mata farare hannuwanshi tass.....da k'arfi Miyya ta kalle shi yadda take kallonshi ba ko kyaftawa zai tabbatar maka da ta tsorata matuk'a da ganinshi. Tsananin rudewar da tayi yasa bata lura da lokaci da ya iso kusa dasu ba. Yadda take kallonshi yai masifar bashi haushi. "Ke nace ki mik'o min ita! Ya faɗa cikin tsawa hakan ya tsorata Ahlam ta k'ara k'am-k'ameta, tana mai k'ara sautin kukanta. Jikin Miyya ya d'auki rawa ta shiga k'ok'ari ciro Ahlam daga jikinta yayin da ita kuma sai k'ara rirrik'eta take yi. Gani ba za ta iya rabata da jikinta cikin sauk'i ba yasa Azaad ya zagaya bayan Miyya don Ahlam taga fuskarshi. "Zo nan Ahlam zo wajen Daddy kinji?" Ya yi magana tare da rik'o hannunta, ta ɗago idanuwanta ta kalle shi kamar tana so tunawa da fuskarshi, sai kuma ta sake fashewa da kuka ta fincike daga rik'e mata hannu da ya yi. Wani irin mashahurin mamaki ya rufe shi saboda Ahlam bata ta6a mishi haka ba. Sosai shiga rud'ani wacece wannan yarinya menene alak'arta da gidanshi da har 'yarshi ta shak'u da ita har haka?" Take furuncin Hakeem ya faɗo mishi lokaci da yake waya dashi, ya ji lokaci da ya ce dashi "Aj Ina so mu yi magana ta fahimta akan amaryarka... Sai kawai ji sautin ihun Miyya dole ya katse kiran. Cikin tsananin tsoro mai cike da zallan tashin hankali Azaad Junaid ya dawo gaban Miyya ya ɗaga dara-dara manyan idanuwanshi, ya bi tun daga tsakiyar Kan Miyya har zuwa ga kafafuwanta da kallo..... *Not Edited!!* *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 17.... Yana yi yadda yake kallonta yasa ta k'ara rikicewa, yayin da Yana yinta ke sauyawa a hankali ta sauke idanuwanta k'asa, a dalili wani bak'on al'amari da take ji yana shigarta. Ci gaba da k'ureta da kallon kurilla ya yi, babu ko alama dake nuna shi ɗin zai d'auke rikitattun idanuwanshi daga kanta. Ya ja dogon numfashi kana ya sauke, a hankali ya girgiza kai so yake ya k'aryata zarginshi ko ta hali yaya, sai kawai ya ciro wayarshi, daga aljihu ya kira Dr Jannat ita ce likitar da ke kula da yaranshi. Ya dubi Miyya da raguwar mamaki da har yanzu ya kasa sakinsa cikin dakakkiyar muryarshi mai cike da k'asaita ya ce. "Je ki tsaftace mata jikinta kafin Doc ta k'araso. Da sauri Miyya ta nufi d'akinta da ita cikin k'ank'ani lokaci ta gyarawa Ahlam jikinta ita ma ta sauya kayan jikinta, kasancewar Ahlam bata da Kaya a d'akinta yasa ta lullu6e ta cikin towel ta fito sa6e da ita a kafad'a. Ta haura upstairs inda d'akin Ahlam yake babu ce kawai babu a d'akin. Duk wani abu na more rayuwa an zuba mata a ciki kama daga toys da teddy bear gasu nan birjik. Duk lokaci da Miyya ta shigo d'akin nata sai ta tsaye ta k'arasa masa kallo kusurwa-kusurwa, tana mamaki yarinyar da bata ko cika shekara d'aya ba ke da wannan tangamemen d'aki. Closet ɗinta ta buɗe mai d'auke da suturanta kala daban-dabam. Ta ciro pink gown tana cikin saka mata ta sake shak'a wani amai, gaba ɗaya rigar tasake lalacewa. Tsananin tausayinta ya sake kanainaye zuciyar Miyya, musanmman yadda take ta kakarin amai, dole ta sake komawa bathroom da ita ta wanke mata jikinta, ta kuma wanke gun da amai ya sami rigarta. Tana fitowa sa6e da ita a kafad'a Azaad tare da Doc Jannat su na shigowa. Miyya tai tsaye turuss...a bakin kofar bathroom ta kasa k'arasowa, suna had'a idanu ta ji wani iri yarrrr....tsigar jikinta ya tashi. "K'awo ta mana na duba ta" Sautin muryar Doc Jannat ya hankaltar da ita hali da take ciki. Ta tako a hankali kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki, ta mik'awa Doc Jannat ita da sauri Ahlam ta mak'alewa Miyya alamar bata zuwa, gani haka yasa Miyya ta dosana duwawunta a gefen gado yayin da Doc Jannat ta dukufa duba ta. A hankali Miyya ta ɗago idanuwanta ta saci kallon Azaad Junaid da ke tsaye a dai-dai k'ofar shigowa ya tattara hankalinshi akan wayar hannunshi. Jikinshi ya bashi cewa ana kallonshi yana ɗagowa Miyya na sauri sadda kanta k'asa, tuni ya gano ita ce mai kallon nashi. Doc Jannat ta kammala duba Ahlam ta fiddo da drip ta saka mata ihunta yasa Miyya ta ɗago babu shiri, Doc Jannat ta gani rik'e da hannun Ahlam tana, neman jijjiya, duk inda ta soka allura sai ta cire saboda, bata do gun da jijjiyar take ba. Ta saki ɗayan hannunta ta sake kama ɗayan. Duk lokaci da Doc ta soki hannun Ahlam sai Miyya ta runtse idanuwanta tamkar jikinta ne ake hudawa. Duk abin da ta ke yi Azaad yana kallonta ta gefen ido yadda take runtsar idanu yai masifar bashi dariya sai kawai ya yi murmushin gefen baki. Sau biyu doc Jannat tana sukar hannun Ahlam bata Sami jijjiya ɗin ba. Tana shirin yi na uku Miyya ta rik'e mata hannu tamkar za ta fashe da kuka ta ce. "Please Doc ki kyaleta haka mana, kalli dukan hannuwanta duk ki bi ki huda su kamar kin sami kwarya" Dakatawa Doc Jannat tayi ta ɗago da yawaltatce murmushi akan fuskarta ta ce. "Nima ba a so raina nake huda ta ba, ki yi hak'uri na k'arasa aikina. K'in sake ta tayi sai ma k'ara dank'e hannun nata tayi, yayin da idanuwanta suka ci-ciko da hawaye. "Ki barta tayi aiki kada ki 6ata mata lokaci" Muryar Azaad ta daki dodon kunneta, ta ɗago manyan idanuwanta ta galla mishi harara, don ba k'aramin haushinsa take ji ba. Tun shigowarsa yake tsaye yana dannar waya, kamar bai damu da taratsi kukan Ahlam ba. Ba don ranta ya so ba ta saki hannun Doc Jannat, tare da kauda fuskarta sai da Doc ta kammala mata fixing drip ɗin sannan ta dawo da ganinta akan Ahlam wacce ta lumshe idanuwanta alamar tanaso tayi barci. Gani haka yasa Azaad ya fita daga d'akin Doc Jannat tattara kayanta ta bi shi a baya. A downstairs parlor ya tsaya still idanuwanshi na kan wayarshi ya shiga tambayar Doc Jannat ciwon da ke damun Ahlam. "Zazza6in hak'ora ne ke damunta Yalla6ai zan dawo da yamma idan bata daina amai ba, gaskiya sai an sake k'ara mata wani drip" Ya jinjina kanshi. Doc Jannat ta mik'a mishi prescription ta tare da furta. "Kafin na dawo ayi k'ok'ari a siyo wad'annan magunguna. Nan ma sake jinjina kanshi ya yi bayan doc Jannat ta tafi, ya nufi 6angaren Jadda ya nufa zuciyarshi a cakude bayan ya gaisa da Jadda mero ta kawo mishi Karin kumallo ya d'an tsakura Kaɗan saboda damuwar da yake ciki, zance na gaskiya idan har hasashen shi ya hasaso masa gaskiya wannan tatsutsuwar yarinya da ya gani sa'ar Aneesah matashi to kuwa akwai matsala babba. Wannan ai abin kunya ne gotai-gotai dashi ya aure sa'ar 'yar cikinsa. Ai sai girma da k'imarshi su zube a idanu mutane duniya. Wayarshi ya dauko ya kira Hakeem ya zo yana so ganinshi gara ya zo su yi ta manya-manya daga tushe, kafin Hakeem ya iso ya kalli Jadda da ke mishi zance Aslamiyya kamar tasan abin da ke nukurkusar zuciyarsa. Rai 6ace ya fara magana. "Wai Jadda kina nufi wannan 'yar k'ank'anuwa yarinya da nagani ita ce matar tawa?" "Kwarai kuwa ita ce ai nice nace da Hakeem ya 6oye kada ya yi saurin baiyana maka da ita gudun kada kace tayi maka k'ank'anta, ka fasa auren ni kuma a duniya nan ta maliki yaumidini bana da buri da ya wuce ka k'ara aure kai da yaranka za ku sami kyakkyawar kulawa da gantalalliyar matarka ta kasa ba ku. Ajiyar zuciya mai k'arfi ya sauke tare da shafa kwantattace sajenshi wanda hakan ya zame masa dabi'a. Kafin ya tattaro natsuwashi wuri guda ya ce. "Jadda idan kina min hasashen kulawa to kin tafka kuskure domin wannan kwaila ba abinda za ta iya, azahirin gaskiya ni an cuceni tare da linkeni bai-bai saboda Hakeem ce min ya yi bazawara ce har da yara biyu. Ashe duk k'arya ce da yaudara saboda haka yadda yadda kawota haka zai dawo ya d'auki abarshi don ni ba mutumin banza bane balle araina min hankali" Hakeem da ya turo k'ofa zai shigo karaf furuncin Azaad na k'arshe ya sauka a kunnenshi, cikin mutuwar jiki yai sallama Jadda ce Kaɗai ta amsa Azaad kuma ya amsa a cikin zuciyarsa. Muryar Hakeem Kaɗai da ya ji saida ya k'ara linka masa 6acin rai da takaicinsa. Hakeem ya mik'a masa hannu da nufi su yi musabaha, ya kwada masa katuwar harara, ya kauda fuska. Hakeem ya mak'e kafad'a tare ta6e baki ya nemi cushion dake facing ɗinshi ya zauna, ya gaida Jadda ta amsa kana ya zarce da faɗin. "Jadda ki shiga cikin lamari nan saboda Aj ya dau zafi dani, ni kuma shawara da kika ɗorani akai na bi. Don haka kar ya sake ya ga laifina. "Wannan haka yake Hakeem tun kafin ka zo na faɗa na Kuma k'ara jadaddawa Aslamiyya tayi min d'ari bisa d'ari.... "Haba Jadda ya za ki faɗi haka gaskiya ni dai ba ai min adalci ba?" Kuma inaso kasani Hakeem saboda yarda da nayi maka yasa na ba ka ragamar rayuwata da ta iyalina sai gashi ka rusa wannan yarda. "Karka faɗi haka Aj domin wallahi-tallahi ban zantar da hukunci ba saida amincewar Jadda, aganina ko mayya Jadda ta nuna tanaso ka aura za ka amince da gaggawa ba tare da tambayar ba'asi ba. Balle yarinya mai cike da nagarta iri Aslamiyya wacce samun irinta a wannan zamani sai an sha matuk'ar wuya. Duk wani qualities da kakeso a jikin mace Aslamiyya tana dashi, ita ce mace da za ka faɗa ta ji, ka kafa doka ta bi ba tare da tayi fatali da ita ba. Ita ce za ta girmamaka ta mutunta igiyar aurenka ta kuma zame maka ma'adanar sirrinka, ta so ka ta k'aunace 'ya'yanka Aj kada ka bi rudin zuciya ka daure Dan Allah da manzonsa ka kar6i, Aslamiyya a matsayin matarka. Yarinya nan rayuwarta cike take da k'alubali a tunanina kaine za ka kawo mata sauyi a rayuwarta kamar yadda nake da yak'ini za ta kawo babban sauyi a rayuwar gidanka" Azaad ya dafe kokon kanshi saboda Hakeem da Jadda sun ri ga da sun gama daure shi da kalamansu. Yana matuk'ar k'aunar Jadda domin ita Kaɗai ta rage mishi ita ce yake kallo a matsayin mahaifiyarshi yayin da Hakeem yake da babban matsayi agareshi, abokinshi ne tun na yarinta duk wata gwagwarmayar rayuwa a tare suka yi shima maraye ne kamar shi saidai Hakeem yana da K'anwa daya kachal Zainab sa6ani shi da Jadda ce Kaɗai yake da sai shirgin 'yan uba da kullum burinsu su ga bayanshi. Kasa magana ya yi hakan ya bai wa Hakeem damar zayyane masa tarihin Miyya bai 6oye masa komai ba. Sosai ya ji ya tausaya musu ya kuma kudurta aranshi zai kula da ita a matsayi 'ya ba mata ba, har sai zuwa lokaci da za ta mallaki hankalin kanta ta yadda za ta iya 6ance-6ance tsakani abin da takeso da wanda bataso. Ya yi shiru bai sake magana ba sai ma jinginar da gadon bayanshi ya yi a jikinta ya lumshe idanuwanshi gani haka yasa Hakeem ya yi hamdallah domin shiru da ya yi shine amincewarsa da bai amince ba tashi kawai zai yi ya bar musu falon. **** ****** ***** Miyya tana rik'e da hannu Ahlam ko nan da can bata gusa ba, yanzu haka fitsari take ji amma ba za ta iya shiga bathroom ta barta Kaɗai ba. Sai da drip ya k'ara ta fita kiran Nanny Lacey ta zo ta cire mata sai lokaci ta faɗa bathroom ta rage nauyi tare da d'aura alwala saboda lokaci sallar Azhar ya yi har kuma zuwa lokaci Ahlam tana sharar barci abinta. Hatta da abinci Nanny Lacey ce ta kawowa Miyya a d'aki sai misali k'arfe uku Aneesah da Airah suka dawo daga school, sai lokaci su ka san Daddynsu ya dawo sosai suka shiga murna ganinshi. Yini daya kacal har Ahlam tayi rama tun tana mamaki rashin dawowar Azaad ya duba Ahlam har ta dawo tana zance zuci. "Wannan wane irin uba ne?" Fissibillahi 'yarka bata da lafiya ka kasa nuna kulawarka akai. Wani 6angare na zuciyarta ya ce. "Daina ganin laifinsa Miyya mahaifiyarta ta fi shi laifi kasancewar mace Kuma uwa amma ta iya tsallakewa uwar duniya ta bar 'yarta mai watani goma. Abin da ke d'aure mata Kai ya Kuma k'ara dumulmula mata tunani tare da hargitsa mata kwakwalwa, bai wuce tun zuwanta gida dai-dai da rana d'aya bata ta6a gani Madam Salima ta kira waya domin ta ji lafiyar yaranta. Dama Azaad kafin ya dawo kusan kullum sai yai waya dasu which means Azaad ya fi damu dasu fiyye da Madam Salima. Idan kuwa hasashenta ya kasance gaskiya tabbas Madam Salima batasan ciwon kanta ba, ta kuma san darajar 'ya'ya ba. Ta 6angaren Azaad Junaid yana damu sosai da son sani hali da Ahlam take ciki, ya tambayi Nanny Lacey ya kai sau uku ya jikinta sai ta ce dashi tana barci duk da haka hankalinshi bai kwanta ba, yana so ya je d'akinta ya gannta sai kuma ya tuna da Miyya tana d'akin baya so duk wani abu da zai danganta shi da ita. Gudun kada ta rena shi. misali k'arfe biyar na yamma ya Kira Doc Jannat ta zo ta k'ara duba Ahlam ta ji sauk'i sai da zafin jikinta da har yanzu bai rage ba. Amma ta daina amai duk da haka sai ta sake sa mata wani drip. Gani yadda Ahlam ta jigata ya k'ara linka masa haushi da tsanar Madam Salima, ya kuma jefa shi cikin nadama haɗi da danasani aurenta. Misali karfe 8:30pm ya 6aro flat ɗin Jadda ya kira Nanny Lacey ta kawo mishi Ahlam ya gannta yana part ɗinshi. Koda Nanny Lacey ta shigo d'akin Miyya har tayi shirin kwanciya barci saboda throughout bata huta ba tana ta fama da Ahlam. "Pretty har kin kwanta ne?" Cewar Nanny Lacey lokaci da takai dubata wurin da Miyya take kwance sanye da sleeping gown yayin da Ahlam take kwance akan cikinta, sai da tayi k'ok'ari tashi zaune kana ta amsa da cewa. "Eh! Nanny nagaji ne sosai ga Kuma barci da nake ji. "Ayya sannu pretty ai kina k'ok'ari sosai ba Kaɗan ba, dama Yalla6ai ne ya ce akawo mishi Ahlam ya gannta" Jin abin da ta faɗa yasa Miyya ta6e baki wato sai yanzu ya yi lokaci Ahlam ɗin, fuskarta babu wal-wala ta shiga k'ok'arin mik'awa Nanny Lacey Ahlam, yayin da Ahlam ta fasa ihu da sauri Miyya ta dawo da ita jikinta ta rungumeta tana shafar gadon bayanta. "Nanny ki faɗa mishi wallahi yau gaba ɗaya yarinya nan k'iyya take ji bata yarda da kowa ai dai kin ga yadda nake fama da ita ko bathroom ban isa na shiga na barta ba. "Nasani pretty daurewa za ki yi ki kai mishi ita tun da ni bata yarda dani. Da sauri Miyya ta kalli Nanny Lacey fuskarta cike da zallan mamakin furuncinta......... *Not Edited!!* *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 18.... Cikin tsananin fusata Hasheem ya cakume collar rigar king Kevin yana k'ok'ari kai masa nushi gani haka yasa Tajo ya taso da sauri ya rik'e masa hannu domin ya tabbata idan har ya kuskura hannunshi ya sauka a jikin KK tabbas da wuya ya kai gobe. Yayin da KK yake kallonshi hankali kwance jira yake yi ya aikata abin da yake nufin aikatawa ya tashi kokon kanshi da alburushi. Tajo ya ja shi gefe yana bashi baki da kyar ya shawo kanshi ya k'ara musu two days idan har kwana biyu ya cika basu kashe masa Azaad Junaid ba, dole su dawo masa da kud'insa. Wanda daga Tajo har KK suke gani ba abu mai yuwa bane dawo da kud'i koda kuwa ba su sami nasarar cimma manufarsu ba. 6ata musu lokaci da baro garinsu da suka yi ba za su yi shi a banza ba. Idan har Hasheem ya kafe lallai sai sun dawo mishi kud'insa to kuwa haka yana nufin numfashinsa za bar gangar jikinsa. ***** **** ***** "Ya naga kin 6ata rai?" Nanny Lacey ta faɗa tana kallon Miyya wacce fuskarta ta baiyyanar da rashin walwalarta a fili ta ce. "Ki yi hak'uri Nanny bai kamata na shiga flat ɗinshi ba, gara na tsaya matsayina na mai kula da yaranshi" Cikin kwantar da murya Nanny Lacey haɗi da rarrashi ta ce. "Haba pretty miyasa za ki faɗi haka ne? Shi fa mijinki ne mallakinki idan har kika ce za ki dinga nisanta kanki dashi babu amfani auren naku kenan. "Ba laifina bane Nanny Lacey sai nake gani kamar shi ma ya fiso hakan" "Ba haka bane Pretty yalla6ai yana da sauk'i kai ta wani 6angare zan iya cewa yana da wuyar sha'ani. Amma ba za ki fahimce hakan ba har kin bai wa aurenku muhimmanci. "Nanny ba za ki gane bane shi ma fa yana da manufar da yasa ya aureni" "Ke yarinya ce k'arama pretty ba za ki yi saurin fahimtar wasu abubuwa cikin sauk'i ba. Ki sani na dauke ki tamkar jikata shiyasa nakeso ki sami rayuwa mai inganci. Rayuwar Yalla6ai Azaad tana tsanani buk'atar mai tallafa mata, Kuma kece za ki kawo wannan tallafi ki d'aure ki yi min biyayya bisa ko wane umarni da zan dinga ba ki, wallahi ba zan ta6a yi abin da zai cutarda ke ba. Shiru Miyya tayi tana nazari maganganu Nanny Lacey d'aya bayan d'aya hakan ne ya bai wa Nanny damar ci gaba da fayyace mata, yana yi rayuwar Azaad Junaid da ta iyalinsa. Kana ta zarce da rarrashinta da kalaman kwantarda hankali da haifar da natsuwa. Sosai jikin Miyya ya yi sanyi ta tsinci kanta da tausayawa su Amrah ko Kaɗan ba ta ji tausayi Azaad ba ganinta shi ya siyawa kanshi saboda shine miji madam Salima mata duk dokar da ya kafa mata dole ta bi koda ace ranta bayaso. Nanny Lacey ta d'an buge kafad'arta ta dawo natsuwarta ta sauke ajiyar zuciya. "Naga Ahlam ta sami barci ki kwanta kawai zan faɗa mishi kun yi barci amma dan Allah pretty da safe ki yi k'ok'ari ki kai mishi ita kinga shi ba girmanshi bane ya dinga zuwa d'aki nan ba kinji yarinyar kirki?" Miyya ta jinjina kanta amma a k'asan zuciyarta tana ji kamar ba za ta iya ba ta amsawa Nanny Lacey ne kawai don ta shafa mata lafiya. Nanny tai mata sai da safe ta fice kana Miyya ta maida kanta bisa pillow tare da rungume Ahlam cikin jikinta daga haka barci mai dad'i ya yi awon gaba da ita. Da fitar Nanny Lacey ta kira Azaad a waya ta faɗa mishi Ahlam tayi barci, duk sai ya ji ba dad'i saboda yana so yaga yanayi jikinta tun safe rabonshi da ita ya fi tsawon minti goma yana safa da marwa daga wannan kusrwa zuwa wannan, daga k'arshe yasaka flip flops a k'afarshi ya fito cikin takonshi na k'asaita d'akin Ahlam ya nufa duk da ba shi da tabbacin ko zai tararda ita, ko Kuma k'ofar d'akin tana a buɗe. A natse ya turo k'ofar luckily ta buɗe ya yi amfani da wayarshi ya haska d'akin idanuwanshi suka hasko masa kan gado Miyya rungume tsam....da Ahlam tamkar ita ce ta haifeta bai san adadin mintocin da ya d'auka yana kallonsu cike da sha'awa wani irin girma da matsayi ya ji zuciyarshi ta bai wa Miyya ya k'arasa daff dasu ya harde hannuwanshi yana mai ci gaba da kallonsu ji yake ko zai shekara a tsaye ba zai gaji da kallonsu ba. Irin kulawar da yake so ya ga Madam Salima tana bai wa yaranshi kenan saidai kashh...Salima bata da lokacinsu business ɗinta yafi mata muhimmanci fiyye da kula da yaranta sai gashi Allah ya kawo k'aramar yarinya mai k'anana shekaru ta magance masa wannan matsalar wacce bai ta6a tsanmani magance ta cikin sauk'i ba. Ya girgiza kanshi tare da hamdallah, kana ya fice daga d'akin yana shiga d'akinshi ya zarce bathroom ya yi alwala ya shiga zuba nafilfili tare da rokon ubangiji ya k'ara wanzar da farin ciki a rayuwarshi da ta iyalinsa. **** ****** ****** Washe gari da wuri Miyya ta tashi kamar yadda ta sabawa kanta, ta taimakawa Nanny Lacey suka had'a breakfast bayan Aneesah da Airah sun wuce school ta dawo d'aki tayi wanka ta shirya cikin tsadaddiyar material gown irin dinki ready made wanda ake zuwa dashi daga Dubai. Yana d'aya daga cikin kayan da Hakeem ya siya mata a yanzu kan hutu ya zauna a jikinta fatar jikinta ta k'ara haske sai shek'i take. Miyya 'yar duma-duma ce bata da tsayi sosai za a iya sakata a jerin gajeru, tana da doguwar fuska tana da hanci dai-dai gwargwado tana da yalwatatce gashin kai da na gira k'irjinta cike yake fam...ga Kuma manyan hips tubarakallah Ma-sha-Allah! Bata cika so d'an kwali ba shiyasa ta yane kanta da k'aramin veil da ya dace da kayan jikinta tana cikin fesa turare, Ahlam ta falka daga barci ta d'auke ta nufi bathroom da ita tai mata wanka, ta shiryata cikin red gown ta d'aure mata gashinta da red band, tayi matuk'ar kyau duk da ta d'an yi rama cikin hukunci na ubangiji yau da tashi babu zazza6i a jikinta. Ta d'auke ta suka fito downstairs parlor kaitsaye kitchen ta nufa ta tararda Nanny Lacey tana goge gas cooker yayin da Linda ke wanke plates ɗin da su Aneesah suka yi amfani dasu. zaunar da Ahlam tayi akan kitchen cabinets saboda tasan halinta ba yarda za ta yi wani ya d'auke ta ba. Ta kammala had'a madara a fida sake daukarta tayi suka fito zuwa parlor tana cikin bata ta shak'i k'amshinsa take ta ji faɗuwar gaba haɗi da tsoro ya ratsata, batasan lokaci da tayi wata 'yar shassheka kamar mai jin sanyi. Ta ɗago idanuwanta a hankali kamar wacce aka yi wa dole karaff... idanuwanta suka sark'e da nashi yana sanye da ash colour suit ya ɗora green colour necktie ya yi mishi balthus Knott style sosai kayan suka k'ara fitowa da shahararren kyawonshi. Da sauri ta janye idanuwanta daga gareshi, saboda Sam bata iya jure kallon cikin fitinannu idanuwanshi sosai suke rud'ata tare da cika mata nata idanuwa. Ya yi kamar bai gannta ba ya nufi dining room, da sauri Nanny Lacey ta fito daga kitchen ta kalli Miyya tai k'asa da murya kamar mai rada ta ce. "Pretty tashi ki je ki yi wa Yalla6ai Azaad serving tun da kina nan babu amfani na ci gaba da yi mishi. Wani iri kallo Miyya take mata baki buɗe kafin ita ma cikin rad'a ta ce. "Ni kuma Nanny haba Dan Allah miyasa kike so ki dinga jefani hurumin da ba nawa ba?" "Saboda ke matarsa ce pretty saboda irin wannan sakaci ya jawo wa Madam Salima zuwanki gidanan, har kika kafa fada mai girma ban kuma san me zai faru anan gaba ba. Miyya tai shiru tana wasa da fida da ke rik'e a hannunta, yayin da gabanta ke ci gaba da dukan tara-tara. "Tashi mana kada ki 6ata masa lokaci yana da kyau ki kiyaye wannan Yalla6ai bayaso wasa da lokaci. Batare da ta ce uffan ba ta tashi d'auke da Ahlam Nanny Lacey bata yi yunk'uri kar6a Ahlam ba, saboda tasan yana da buk'atar ganinta. Ta bi bayan Miyya da kallo tana tuna girman wannan aikin da Hakeem ya sakata tun tafiya ta yi nisa ta fara gani haske. Cikin tafiyarta ta natsuwa mai kama da yanga ta ratso cikin dining room ɗin, hankalinshi yana kan wayarshi yana duba sak'oni{messages} sallama ta fara yi cikin sanyi murya, kafin ta gaida shi. Can k'asan mak'oshi ya amsa mata lips ɗinshi haɗi da adams apples ɗinshi taga sun motsa ya shine ya bata tabbaci ya amsa mata. Ya ajiye wayarshi akan dining table ya mik'o mata santala-santala hannuwanshi tuni ta gano abin da yake nufi ta matsa kusa dashi tare da mik'a masa Ahlam, wacce taso tak'i zuwa ya fizgota da k'arfi ya shiga yi mata wasa. A fakace Miyya ta galla masa harara saboda ya bata haushi ta yadda ya fizge Ahlam ɗin. Batasan cewa duk abin da take yana ganinta ba. Haka zalika duk abin da ya faru tsakaninta da Nanny Lacey ya ji su sarai. Ta zari plate ta zuba masa soyayar doya da haɗin source na kidney & liver ta zuba masa kunu gyada a mug. Sannan ta kar6i Ahlam har ta juya kamar daga sama taji sautin muryarshi. "Nagode Sosai da irin kulawar da kike bai wa Ahlam idan buk'atar wani abu ta taso ki zo kaitsaye ki faɗa min. Miyya ta ja dogon numfashi tare da saukewa abin ya zo mata wani iri tarasa amsar da za ta bashi sai kawai tayi murmushi tare da juyawa ta fice daga dining room ɗin. Cike da natsuwa ya shiga cin abincinsa har ya kammala yana jin kansa kamar ba shi ba. Ya bi ta flat ɗin Jadda ya duba lafiyarta kana ya wuce office, yana shiga office ɗinshi Hakeem na danno kai dama tun d'azu yake dakon zuwanshi, shaking hands suka yi kafin ko wane su ya nemi matsugunni. "Ya ake ciki Aj mijin kwaila ya ka baro kwailar taka?" Hakeem ya faɗa yana k'unshe dariyar shek'inyaci. Azaad ya bata rai cike da miskilancinsa ya ce "Ban kira ka office ɗinan ba don ka karanta min iskaci ba. Na kira ne domin nasan menene matakin karatunta tana da buk'atar komawa makaranta, kasancewarta mai karancin shekaru bai kamata a tauye mata wannan damar ba. Hakeem ya saki murmushi yana kallon Azaad Junaid da girar ido a ɗage, shi Kaɗai yasan abin da yake karanta akan fuskarshi kafin ya ce. "Karatunta ya tsaya ne a matakin k'aramar sakandire {junior secondary School} Azaad ya ta6e baki cikin izza ya ce. "Sai abu na gaba gargadi ne ina fatar za ka natsu ka bani aron hankalinka saboda banaso ace sai na sake mai-maita gargadin nawa....... *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 19..... Hakeem ya k'ure shi da kallon mamaki kafin ya ta6e baki ya ce. "Karata gargadin naka kunne ke ji saboda haka ina saurarenka. Saida Azaad ya share 60 seconds kafin ya ce. "Sabon suna da naji ka kirani dashi Ida ka sake kirana dashi za mu kwashe za mu hau sama mu faɗo saboda haka ka kiyaye.... Kafin ya k'arasa magana Hakeem ya kwashe da dariyar mugunta har da su dafe ciki, Azaad ya tsare shi da idanuwa yana mamaki abin da yakewa dariya. Sai da Hakeem yaci dariya iya son ranshi sannan ya kalli Azaad da raguwar murmushi akan fuskarshi ya ce. "Ai yanzu Aj bakada suna da wuce mijin kwaila ko mijin mai nonuwa tsaye Kaɗai ka yi k'ok'ari ka kafa ka tsare ka bada himma nan da wata tara mu sami second Aj... Yadda Azaad ya zazzare idanuwa za ka yi tsanmani wani mugun abu Hakeem ya faɗa, gaba daya ya kasa koda kwakkwaran motsi wani irin tsoron Allah ya lullu6eshi. "Kai miye haka ka wani tsareni da jarababbun idanuwanka Miyya ce ba ta isa daukar ciki ba ko kaine kwanka ya daina fidda tsiro?" "Mtsss.....!! Azaad ya ja dogon tsaki kana ya ɗage girar ido yana yiwa Hakeem kallon kama rena ni. "Gaskiya Hakeem bata ta6a sani da k'asurgumin mahaukaci nake zaune ba sai yau. Har ni Azaad Junaid kake kwatatawa da haɗa shinfid'a da yarinya k'arama sa'ar 'yar cikina? Tsakani da Allah Hakeem ka cuceni and I'll never forgive you.... "D'an dakata mana abokina haramun ne don ka kwanta da sa'ar 'yar cikinka naga dai matarka ce ta sunnah mun shaida ka biya sadakinta, wallahi tun wuri kada ka sa girman kai ka cuce kanka ka ba kasan cewa masu k'anana shekaru nan sun fi juriya da jajircewa ba. D'aure fuska Azaad ya yi saboda ya fahimci damarshi da Hakeem yake gani ne yasa yake kawo mishi wannan zance banzan. "Hakeem please mu rufe wannan zance mu yi abin da yake gabanmu domin kana daff da k'ure min maleji" "To shikenan amma ina tabbatar maka muna nan dakai wata rana za ka canza shek'a ka yi wadak'arka ba tare da ka tuna da k'aranci shekarunta ba. "Aikin banza da wofi an gayamaka ni tsuntsu ne da zan canza shek'a dallah malam ka bani files ɗin na duba ko na bar ka da kayanka. Da sauri Hakeem ya mik'a masa documents ɗin hannunshi ya fizge da kar6i yana dubawa yana zabga tsaki, saboda ba k'aramin haushi Hakeem ya bashi ba. Yayin da Hakeem sai dariya yake yi k'asa-kasa. ***** **** **** A cikin kwanaki biyu Azaad ya nemawa Miyya gur6i karatu a school ɗin su Aneesah, saboda tsabar murna da Aneesah da Airah saida suka haɗa kwarya-kwayan party a d'akin Aneesah har da su saka music suka sha rawa abin da ba su ta6a yi ba tsawon rayuwarsu. Ranar da Miyya ta za ta fara zuwa school tsabar zumudi tun kiran asuba na farko ta falka duk da zumudi da take yi sai da ta shiga kitchen taya Nanny Lacey suka haɗa breakfast. Karfe 7:20am direba ya ajiye su lokaci da Miyya ta shiga aji ta kasa sakin jikinta irin dai bakunta nan da new students ke yi. Sai misali karfe uku suka dawo gida a gajiye ko wane su ya wuce d'akinshi, kawai Miyya tayi ta fito neman Ahlam wacce taci kukan nemanta tana ganinta tafara zillo hannuwanta da sauri Miyya ta sunkuceta ta ɗagata sama tana mata Wasa ita kuma sai wangale baki take yi. Da dare da Azaad ya fito ya yi dinner Nanny Lacey ta shiga har d'akin Miyya ta taso ta ta zo tai mishi serving wanda zuwa yanzu har ya bi jikin Miyya a natse za ta zuba mishi abinci tai tafiyarta abinta sau dama Nanny Lacey tana mata faɗa akan tafiyar da take yi ta barshi, ta kasa sabawar kanta da zaunawa idan yana ci abinci gani take yi kamar zai iya embarrassed ɗinta. Lokaci da Nanny Lacey ta faɗa mata tana kwance sanye da silky material gown mai armless, tasaki gashin kanta ita kanta Nanny da ta kalleta sai da taji ta burgeta matuk'a balle ga d'an namiji mai cikakkiyar lafiya. Turo baki tayi saboda sam bataso abin da zai kusanta ta dashi, ita Kaɗai tasan yanayi da take tsintar kanta a duk lokaci da ta ke6e daga ita sai shi. Mita tashi ga yi wa Nanny. "Nanny please ki barni na huta mana yau fa ne first day ɗina a school dole akwai gajiya a jikina, ga kuma assignment ɗin da aka bani yanzu nakeso nayi kika shigo. "Pretty yaushe kika zama stubborn girl huh?" "Ba haka bane Nanny naga da can kafin zuwana ke ce mai kula da abincinshi, yanzu ma tun da ina da uziri ba sai ki fanshe ni ba?" "Ba zan fashe ki ba kuma dole ki tashi ki ba mijinki abinci wannan ai sakarci ne da rashin sani ciwon kai tashi mana ina magana ki na zaune. Nanny ta k'arashe magana cikin tsawa babu shiri Miyya ta mik'e tsaye tare da daukar k'aramin mayafinta da ke aje a gefen gado{Lol..dama kusan mutuniyar taku da d'an banza tsoro kamar farar kura} jikinta har rawa yake yi saboda ta zaci bayan tsawa za ta ji saukar yatsun Nanny Lacey akan kumatunta. Cikin rashin kuzari ta isa dining room gaba ɗaya k'amshinsa ya cika dining ɗin, tayi sallama cikin siririyar murya kana ta d'an runsuna ta gaida shi ya amsa mata kamar yadda ya saba amsawa, ta zuba abinci a plate ta kai gabanshi, duk abin da take yi yana satar kallonta yayin da har yanzu jikinta bai daina rawa ba ta nufi fridge ta dauko ruwa da drinks, ta je ajiyewa ta take masa k'afa batare da ta lura da k'afar tashi ba. Sosai ta firgita cikin tsananin tsoro ta zabura, sai kawai k'afarta ta bugi kujerar da ke kusa da ita, tayi baya za ta faɗi cikin zafin nama ya rik'o hannunta. Daga zaune da yake bai tashi ba gashi yanayi da ya cafko hannunta taji zafi, ta runtse idanuwanta ga jikinta sai rawa yake yi kamar mai jin sanyi. "Ki dinga duba idan kike tafiya garin wannan rawar kan naki za ki illata kanki a wofi. Cike da k'asaita ya yi magana bai kuma kalleta ba. Miyya ta buɗe tsoratattacin idanuwanta ta sauke su akanshi mamaki ne ya kamata haɗi da kwankwato anyya kuwa shine ya yi magana?" Shine mana Miyya ba gashi nan rik'e da hannunki ba Kuma ai kin waye muryarshi ko a cikin magagin barci za ki iya sheidata. Ta ja gwaron numfashi tare da saukewa a sanyayye ta ja hannunta dake cikin nashi gani haka yasa ya sake ta. Sai lokaci ya ɗago mayatattun idanuwanshi ya kalleta dasu.... _Not Edited!!!_ *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 20... Dukkan jikin Miyya ya d'auki rawa komai yana neman kwance mata, ta rasa wane irin sirri ne a cikin idanuwanshi da duk lokaci da ta kalleshi noti kanta ke kwancewa. A hankali ta juya cikin sanyi jiki bata wuce tako biyu zuwa uku ba ta ji sautin muryarshi. "Ki faɗawa Nanny ta kai min hot coffee falona. Da k'arfi ta waiga ta kalleshi yana ci abincinshi hankali kwance, tasaki ajiyar zuciya kana ta k'arasa ficewa kaitsaye d'akin Nanny Lacey ta shiga ta sanarda ita sak'onshi. Har ta juya Nanny ta tsayar da ita. "Ai kin iya haɗa coffee ki je ki haɗa ki kai mishi a falonshi dake sama" "Ni Kuma Nanny ke fa yace ki kai mishi ba ni ba?" Murmushi Nanny Lacey tayi ta mik'e tsaye ta dafa kafad'ar Miyya, ta ce. "Daga yau ke ce za ki dinga kai mishi kuma banaso gardama ki je kawai ki yi abin da nasaki. "Nanny please ki daina sakani hurumin da ba nawa ba kina gani ko yanzu sai da ya yi min gori ya kirani da mai rawar kai" Ta k'arashe magana kamar za ta fashe da kuka. Nanny ta d'aure fuska tamau alamar babu wasa a tare da ita. "Pretty wai miyasa kike da taurin kai ne?" "Ba haka bane Nanny wallahi mutumin nan ko gaida shi nayi da kyar yake amsawa" "Koma menene wannan ba zai zama hujjar da za ki dogara da ita ki kasa kyautata mishi, a matsayinsa na mijinki. Pretty na fi ki shekaru dole na fi ki sani abin da ya dace da wanda bai dace ba dan haka ki shafawa kanki lafiya ki bi umarni da na ba ki. Kasa furtawa Nanny uffan tayi cikin yana yi na takaici ta juya ta buɗe k'ofa ta fita, zuciyarta tana wani iri tuk'uk'i duk k'ok'arinta na ta hanawa kanta zubda hawaye hakan bai samu ba sai da zafafan hawaye suka wanke kuncinta. Kitchen ta wuce tana haɗa mishi coffee tana shar6a hawaye ko Kaɗan bata k'aunar abin da zai haɗata da Azaad domin ita Kaɗai tasan hali da take shiga a duk lokaci tayi arba dashi. Ta kammala haɗa coffee ta daura mug ɗin aKan k'aramin tray, cikin tsoro take taka matattak'alar benen da zai sada ta da 6angarenshi da ta iso k'ofar falonshi na farko zuciya ta k'ara sautin bugawa fiyye da farko tahowarta, sai ta kai hannunta za ta turo k'ofa sai ta janye, da kyar ta rinjaye zuciyarta ta turo k'ofar ta wangale bugun zuciyarta ya k'ara tsananta cikin tako d'addaya ta fara takawa zuwa cikin ainihin falon. Bata tararda shi cikin falon ba hakan yasa ta sauke k'arfaffiyar ajiyar zuciya, ta dire tray ɗin kan center table ɗin da tagani a tsikyar falon. Ta juya abinta har ta rik'e handle ta tuna da Nanny ta ce da ita ba a falon farko za ta kai ba a falonshi na biyu ji tayi kamar ta ɗora hannu akai ta kurma ihu. Dawowa tayi dole ta sunkuce tray, ta nufi k'ofar glass ta tura batare da ta tsaya shawara ba kamar yadda tayi a farkon shigowarta, Yadda ya ɗago da sauri kalleta yasa ta daskare a tsaye ita bata k'arasa ba bata kuma koma inda tafito ba. Mamaki ganinta yake a dai-dai wannan lokaci a kuma falonshi da ko yaranshi basu ta6a shigar shi ba. Iyakacinsu su tsaya a falonshi na farko. Siririyar sallamarta ce ta katse mishi mamakin da yake. Ya amsa mata cikin taushin murya, sadda kai k'asa tayi ta kasa k'arasawa duk da ya amsa mata sallama. Ya maida ganinshi akan screen ɗin laptop da ke gabanshi, shiru-shiru bai ji ta k'araso ba ya ɗago kanshi ya ganta tsaye kamar an dasa ta ya kira ta ta hanyar ɗaga mata yatsanshi. Tafiya take ta doshi wajenshi yayin da kafafuwanta ke neman hard'ewa waje guda. Da taimakon Allah ta iso gabanshi. k'aramin center table ɗin da ke girke a gabanshi, ta ture tulin files ɗin da ta gani a gefe kana ta aje tray ɗin. Cikin sanyi murya ta ce. "Barka da hutawa Daddy" A natse ya ɗago idanuwanshi ya sauke su akan kyakkyawar fuskarta, sunan da ta kira shi dashi ne ya ji shi wani iri duk da ba yau ne karo na farko da aka kira shi sunan ba. Ya d'an waro idanu waje tare da shafo sajenshi. "Yauwa Sannu" Ya faɗa cikin izza da k'asaita. "Nanny ce ta ce na kawo maka coffee" "Uhmm... thanks! Ya faɗa a takaice yadda yake furta magana cikin izza da k'asaita yai masifar burgeta, har batasan lokaci da murmushi ya subuce mata ba. Har ta kai k'ofar fita ta waiwaya ta kalleshi sai kawai ta tsinci kanta da faɗar. "Daddy iya coffee kake buk'ata Koda akwai wani abu da za ai maka?" Jin muryarta ya sanya shi sake ɗagowa ya cire medical eyes glass, dake lullu6e da kwayar idanunshi hakan ya bashi damar k'are mata kallo from head to toe, ya lefe jikin resting chair da yake zaune tare da lumsashe idanuwanshi. Sai kawai Miyya ta harde hannuwanta a k'irjinta itama ta shiga kare mishi kallo, tana yaba kyawon halittarshi ganinshi take tamkar saurayi d'an shekara 25 idan ba farin sani kai mishi ba. Ba za ka ce shine ya haifi su Aneesah ba. Duk yadda taso ta dauke idanuwanta daga kanshi kafin ya buɗe nashi idanu hakan ya ga-gareta yana ɗago idanuwanshi shima samun kanshi ya yi da kallon cikin idanuwanta, take wani maganadisu ya tsarga musu a jiki tamkar an jona musu wutar lantarki, da sauri ta runtse idanuwanta da baya-baya ta isa ga bango falon ta jinginar da bayanta gudu kada ta faɗi. Wannan shine karo na farko da ta ta6a samun kanta cikin yanayi irin wannan. "Daddy in tafi?" Ta tambaye shi cikin lafazinta mai kama da na mai koyon magana. Samun kanshi ya yi da girgiza mata kai, a hankali ta baro jikin bango ta tunk'aro shi duk takonta d'aya sai ya ji faɗuwar gaba wanda ya rasa na menene. Ta kalleshi tana murmushi wanda ya k'ara jefashi cikin rud'ani. "Daddy me kake so ai maka ne?" Shiru kawai ya yi yana aikin kallonta turo d'an k'aramin bakinta, tayi wanda bata masan tayi ba muryarta cike da shagwa6a ta ce. "Daddy kayi magana mana" Sauri Kiriss numfashi Azaad ya fita daga gangar jikinsa da kyar ya iya dai-daita natsuwarsa, ya zuba mata idanuwanshi wanda suka soma sauya launi. "Za ki iya gyara min gado?" Ya faɗa cikin taushin murya. "Zan iya mana" Tayi magana tana k'ara k'awata fuskarta da yalwatatce murmushi, da hannunshi ya nuna mata Master bedroom ɗinshi wanda tsawon rayuwarshi madam Salima ce Kaɗai ke shigarshi sai kuma yau da shi da kanshi ya lamuncewa yarinyar da ya yi kirari da ba abin da zai yi da ita. D'akin ta nufa tana wani iri cat walks wanda za ka zaci da gangan take yi shi, alhali kuwa halitta ta ce a haka. Bai d'auke idanuwanshi daga kanta ba har saida ta shige d'akin ya daina ganinta kana ya yi ajiyar zuciya. Tana shigar bedroom ɗin ta ja tayi tsaye tana kallon haɗuwa da tsarin d'akin nashi ba k'aramin burgeta d'akin ya yi ba. Komai na d'akin very neat gado ba wani ya lalacewa da ya yi, sai kawai ta canza mishi bedsheet ta wanke bathroom. Koda ta dawo falo ya mik'ar da bayanshi ga jikin resting chair, ya ɗora kafafuwanshi akan center table idanuwanshi suna rufe, saida ta kalle mishi fuska iya son ranta kafin ta dai-daita muryarta ta furta. "Daddy na gama har bathroom na wanke maka" "Thank you! Ya faɗa cikin muryarshi da bata fita sosai saboda k'arfin izza da k'asaita, da kuma bakon al'amari dake yawo cikin jini da bargonsa. "Goodnight Daddy" "Goodnight! Ya furta can k'asan mak'oshi still idanuwanshi a rufe, ta taka a hankali ta nufi k'ofar fita tana daff da ficewa ta waiwaya ta kalleshi idanuwanshi fess...akanta tasaki mishi murmushi mai tsayawa a rai tare da rufu k'ofar. Tana ya fita ya ja k'arfaffiyar ajiyar zuciya gaba ɗaya jikinshi ya saki kasala ta lullu6eshi. Ya kasa ci gaba da aiki da yake yi sai tsallake tulin files ya yi ko ta kanta coffee da ta kawo mishi bai bi ba, ya shige bedroom, ya tsaya tsakk.....yana kallon yadda ta gyara mishi gado karo na farko a tsawon rayuwarshi da mace ta gyara mishi gado kasancewar bai yarda housemaids su shiga mishi d'akin kwana ba. Madam Salima kuma ko lokaci kanta bata da balle na gyara wani abu wai shi gado. Numfashi ya sake saukewa kana ya bi lafiyar gado. Da fitar Miyya ta zarce kitchen ta dauko rubar ruwa a dalili wani irin bushewa da mak'oshinta ya yi d'akin Ahlam da yanzu ya kasance nata ta nufa gefen gado ta zauna ta sha fiyye da rabin ruwan, ta ajiye raguwar bisa bedside kana ta nemi kusa da Ahlam ta kwanta tana runtse idanuwanta kyakkyawar fuskarshi ma'abociya kyau da kwarjini ta bayyana gareta da sauri ta buɗe idanun nata duk yadda taso barci ya d'auke ta hakan ya kasa samuwa. Ta 6angare Azaad shima hakan ce ta faru dashi sai misali karfe uku na dare barci ya d'auke shi, saidai wani abin mamaki gaba ɗaya barcin nashi ya raya shi ne cike da mafalkan Miyya, cikin tsananin firgita ya falka ya tashi zaune kana jinginar da jikinsa ga kan gado, yasa hannunshi yana shafar kwatattce sajenshi cikin yanayi na mamaki da Kuma al'ajabi yake backwards ɗin mafalkin nashi a hankali yabi jikin wando pajamas ɗin jikinsa da kallo, ba ko shakka wanka janabba ya Kama shi. Tun a farkon balagarshi rabon shi da ya yi mafalkin yana saduwa da mace sai yau ko yau ɗin da Miyya da yake yi wa kallon 'yar cikinsa. A gareshi wannan babban abin kunya ne wannan wacce irin masifa ce takeso kunnuwa rayuwarsa?" Ya sauk'o daga gado ya shiga bathroom zuciyarsa fal.....damuwa a haka ya tsaftace jikinsa wani abin mamaki wata irin natsuwa da gansuwa yake ji tamkar a fili ne ya rage mararshi ba a mafalki ba. Yadda ya sami wannan gansuwar a mafalki a wurinta, ya tabbata a bayyane zai sami fiyye da yadda ya samu a mafalki. Praymat ya shinfid'a ya shiga zuba nafilfili yana kai wa ubangiji mai kowa mai komai buk'atunsa. Misali karfe 7:15am Miyya ta fito downstairs parlor sanye da school uniform, tea kawai tasha saboda daren jiya bata samu wadatatce barci ba. A dalili tunanin Azaad Junaid da ya hanata sakatt..... *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 21..... Sai kai da komo Hasheem ya ke yi ya kasa zaune ya kasa tsaye, idanuwanshi sun kad'a sun yi jajir lokaci zuwa lokaci yake fesar da zazzafar iska daga bakinsa. Can kuma ya dunk'ule hannunshi na dama ya nushi tafin hannunshi na hagu ya yi hakan yafi a kirga. Tajo ya buɗe k'ofa saida KK ya fara wucewa sannan shi kuma ya biyo shi a baya, tun kafin su k'araso tsakiyar falon Hasheem ya nufe su da gaggawa 6acin ranshi ya kai koluluwa shiyasa yana zuwa ya chafko wuyan Tajo. "Ni za ku yaudara ni za ku cinyewa kud'i batare da kun min aiki da nasaku ba sannan har kai Tajo kake min barazana a waya?" Kafin Tajo ya yi yunk'uri kwatar kanshi Kk ya fito da pistol daga aljihun black leather jacket ɗin jikinsa, ya nuna Hasheem da ita cikin kakkausar muryar ya ce. "Sake shi ko na tashi kokon kanka da wannan. Da mugun sauri Hasheem ya saki Tajo jikinsa ya shiga kakkarwa. "Karka yi haka kk ka dawo min da kudina tun da kun kasa aiwatar da contract ɗin, na k'ara muku two days nan ma kun kasa komai kuma a gabanku Azaad Junaid zai wuce ba ku yi masa komai ba. Ko jiya ina la6e ina kallonku naga lokaci da ya fito daga gidanshi ya wuce ku amma ba ku yi masa komai ba. Hakan ke nuni da cewa ba za ku iya ba..... "Rufemin baki kafin na sauke dukkan fushina akanka Hasheem. Kana tsanmani kisan Azaad Junaid sauk'i ne dashi?" Kaine kake yi wa Azaad kallon sakarai amma shi yasan abin da ya taka. Shu'umancinsa ya zarce naka, zai fi maka alkhairi da ka hak'ura da son ganin bayansa. A cikin kwanaki biyu da ka k'ara mana kasan irin bala'o'in da muka dinga cin karo dasu a duk lokaci da muka yi yunk'uri sheke shi?" Jiya har dare muna la6e a jikin katangar kamfaninsa, a maimakon na kashe shi ni ne na kusa mutuwa saboda haka ka nemo wani yai maka wannan aiki, Amma inaso kasani duk yadda kake tunani Azaad Junaid ya zarcewa tunaninka. Kud'inka kuma k'arfi yaci idan ka matsa sai na dawo dasu to kasani komai zai iya faruwa daga ciki har da rasa rayuwarka. Saboda haka ka za6a ranka ko kud'inka?" "Ba zai yu ba kk kud'inan su na da yawa fa..... Kafin ya k'arasa magana kk ya buge tsakiyar kanshi da bindigar hannunshi, zafi da radadin azaba suka ratsa kwakwalwar Hasheem ya kurma ihun neman taimako tare da sulelewa k'asa yana dafe da fasashe kanshi da ke zubda jini, duk da haka kk bai kyaleshi ba saida ya har6eshi a k'afarshi ta dama yana k'ok'ari sake saki mashi wani harsashe a k'irji Tajo ya dakatar dashi ta hanyar jan shi da k'arfi suka fice daga falon. Kasancewar a gidan gona suke, gate yana da nisa da inda suke shiyasa duk ihu da kururuwar da Hasheem ke yi maigadi bai ji ba. Har jini ya buge shi ya some. ***** **** ****** A hankali take saukowa daga matattak'alar jirgi yayin da k'awarta Hafsat Shinkafi ke biye da ita kamar jela. Tun kafin su k'araso direbanta mr Michael ya buɗe musu k'ofufin mota duk lokaci da tai tafiya Mr Michael ne Kaɗai ke sani dawowarta. Duk gaisuwa da yake mata ko kallo bai isheta ba, sai Hajiya Hafsat ce ta amsa mishi. Sai da suka fara sauke Hafsat Shinkafi gidanta koda ta iso gidanta ana kiran sallar magarib. Cike da izza ta fito daga mota da azama mr Michael ya nufi k'ofar main parlor ya buɗe mata, jin k'arar takon takalminta ya sanya Nanny Lacey ɗagowa daga tattara toys ɗin da Ahlam da ta gama wasa dasu, gabanta ya yi mummunan faɗuwa sakamakon gani madam Salima. Jikinta na rawa ta gaidata tsabar girman kanta da izzarta basu bari ta amsa ba sai yatsunta guda biyu ta ɗagawa Nanny Lacey, ta haura staircase ta nufi 6angarenta. Nanny ta bi ta da kallo inda sabo ta saba da ɗagawa da izzar madam Salima. Yanzu duk tsawon shekaru da ta d'auka tana mata hidima da yaranta ace bata kallonta da gashin arziki, kusan watani biyu har da sati uku kenan da tayi tafiya ko a waya bata ta6a kiranta ta ji lafiyar yaranta ba. Hakazalika ta dawo ko ba za ta tayi lafiyarta ai ta tambaye na yaranta. Shigowar mr Michael janye da luggage ɗinta ya katsewa Nanny zance zuci da take. Ta kar6i trolley ɗin daga hannunshi ta kai mata d'akinta koda ta shigo tana cire kayan jikinta a hankali ta ajiye mata luggage ɗin har Nanny ta buɗe k'ofa za ta fita ta ji ta kira sunanta. "Nanny! "Yes madam! "Ki sanarda Azaad na dawo amma karki faɗawa yara ki bari sai zuwa gobe, saboda ina da buk'atar cikakken hutu. Tsabar takaicinta da ya lullu6e Nanny Lacey kasa magana tayi sai jinjina kanta tayi, har ta koma d'akinta tana yaba rashin k'awa zuci irin na madam Salima. Miyya ta fito daga wanka a gaugauce ta tsane raguwar ruwan jikinta ta zura doguwar riga da hijab tayi sallar magarib bata tashi ba har saida tayi sallar isha. Samun kanta tayi da yi simple makeup ta sanya wide legs trouser haɗi da pink bias top ta yane kanta da scarf jikinta na fitarda sanyayye kamshi. D'akin Aneesah ta shiga domin ta k'ara mata haske akan assignment ɗin da aka basu bayan su kammala assignment ɗin. Su kayi dinner sannan ta dawo d'akinta. Nanny Lacey na cikin goge dining table Azaad ya shigo cikin girmamawa suka gaisa, kana ta sanarda shi madam ta dawo nan take annurin kan fuskarshi ya d'auke cakk... kamar an yi ruwan sama an dauke, ita kanta Nanny ta lura da sauyawa tashi faratt d'aya. Bai ce da ita uffan ba ya nufi 6angarenshi. Har Miyya ta kwanta ta tuna da bata bai wa Daddy abinci ba ta tashi zubur, ta d'auki scarf ɗinta da ta cire ta fito downstairs parlor. Ta nemi cushion ta zauna tana jiran fitowarshi har 11:00pm ta buga bai fito ba. Batasan cewa yau a 6angaren Jadda ya yi dinner ba. Da taga ji da zama sai kawai ta yanke shawara ta kai mishi coffee. Tana sanda kamar 6arauniya haka take tattaka matattak'alar bene da zai sadata da 6angarenshi, tana zuwa k'ofar falo bata tsaya neman izzini ba ta buɗe ta shiga kanta tsaye ta wuce falonshi na biyu. Yana zaune da system a gabanshi yana gudanar da online meeting, sallamarta ce tasa shi ɗagowa, har ta k'araso inda yake zaune bai d'auke idanuwanshi daga kanta ba. A k'asan zuciyarshi yake yaba tsin-tsan kyau da tayi a cikin kwanaki nan completely ta sauya wa sanin da ya yi mata, gashi ta hanawa zuciya da gangar jikinsa natsuwa bashida aiki sai na tunaninta, idan har bai yi da gaske ba yarinya k'arama za ta zauta shi saboda haka zai taka mata birki, kada ta kai shi da aikata abin kunya. Ta sauke tray hannunta akan center table cikin sanyayya murya ta ce. "Daddy yau lafiya ba ka fito dinner ba?" Ya kalleta cikin d'aure fuska gudun kada taga damarshi, ya ce. "Naci a 6angaren Jadda. "Iyeee....ashe yau Daddy dad'i kaci. Ta faɗa tana dariya mai ban sha'awa...... *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 22.... Baisan lokaci ya da ya saki mata murmushi ba, a k'asan zuciyarshi so yake ya taka mata birki ta daina shigowa mishi part amma ya kasa furta mata sai kawai ya tsincin kanshi da faɗin. "Kema za ki iya zuwa ki ci dad'in. Ya k'arasa magana yana zuba mata idanuwanshi, masu rikita ta a duk lokaci da ya kalleta dasu. Ta rausayar da kai tana ci gaba da murmusawa cikin sigar shagwa6ar da murya ta ce. "Ba wani nan Daddy da kaso naci dad'in da ka zo min da nawa ko kuma lokaci da za ka je 6angarenta da ka aiko min da katin gayyata" Yadda take magana tai masifar tafiya da ruhi da gangar jikinsa, ya gama fahimta muddin bai da gaske ba tsaf k'aramar yarinya nan za ta zuzuta shi a hankali ya ɗago idanuwashi ya sauke su akan fuskarta wacce ke ta glowing cikin haske bulb ya saki murmushi tare da furta. "Wai ke bakya ji barci ne?" "Uhm..bana ji" Ta faɗa tana turo d'an k'aramin bakinta, hakan ya k'ara kunna wutar abin da yake ji akanta da sauri ya kauda fuskarshi yayin da gabanshi ke wani iri bugawa da k'arfi. Ya sauke numfashi kana ya nuna cushion ɗin da ke facing ɗinshi da hannunshi batare da ya yi magana ba. Da kanta ta fahimci abin da yake nufi cikin salon tafiyarta mai jan hankali ta nufi kujerar ta zauna, ta ɗago idanuwanta suka sark'e da nashi bugun zuciyarsu ya tsananta. Tai sauri runtse idanuwanta tana jan wahalallen numfashi. Ta sadda kanta k'asa. Shiru ya biyo baya shi bai tanka ta ita kuma bata sake yi magana ba ko wane su yana faman da bugun zuciya, Azaad ya kasa samun wadatatciyar natsuwa da zai ci gaba da gudanar da meeting ɗinshi lokaci zuwa lokaci take ɗagowa ta saci kallonshi kuma duk sanda ta ɗago idanuwashi na kafe akanta tamkar yana karanta wani abu, akanta ne. Rashin natsuwa da yake ji yasa sai faman shafar sajenshi yake yi can kuma cikin rikitatciyar murya ya ce. "Pretty ki je ki kwanta please kinsan gobe kina da school ko kinaso ki yi latti tashi ne?" Kamar jira take yi ya bata umarnin tashi ta mik'e zubur ta nufi k'ofar fita saida ta rik'e handle ta juya tare da faɗin. "Goodnight Daddy! "Goodnight" Ya faɗa kamar mai ciwo hak'ora. Ta k'arasa ficewa kamar yadda ta shiga part ɗin nashi cikin sand'a haka ta fito tana sand'a tana isa k'ofar d'akinta tai wuff....ta shige tare da rufu k'ofa. A tsorace take gudun kada tsautsayi ya gitta Aneesah ko Airah wani daga cikinsu ya gannta ta fito part ɗin Daddynsu, dole su tambaye me ta je yi a halin yanzu batasan amsar da za ta basu wacce za ta zama kariya agareta. Da wuri Miyya ta tashi kamar yadda ta saba ta shirya cikin school uniform ɗinta sosai uniform ɗin suka k'ara fidda kyawonta. Side by side suke tafiya ita da Aneesah zuwa parking lot kasancewar Airah tariga su fita tuni take zaune a mota tana zaman jiransu sai faman zabga tsaki da duba agogo take yi, saboda tana da presentation gashi suna so 6ata mata lokaci. Azaad Junaid da ke tsaye a balcony da mug ɗin coffee a hannunshi lokaci zuwa lokaci yake sipping idanuwanshi suka sauka akan fuskar Miyya dai-dai tana kai ma Aneesah duka a kafad'a da alama Aneesah ɗin tana tsokanar ta ne. Har suka isa gun mota suna wasa a tsakaninsu. Yayin da dai-dai da second d'aya bai d'auke idanuwanshi akanta ba. Gani yadda skirt ɗin uniform ɗinta ya tsaya iya gwiwoyinta, gashi d'an k'aramin hijabi half sunna suke sakawa ga hijabi yabi k'irjinta shiyasa ake iya gani satin cikakkun boobs ɗinta. Take ji wani iri mashahurin kishi wanda tsawon zamanshi da Salima bai ta6a ji kwatan-kwacinsa ba. Ga Salima ba iri banzar shigar da bata yi da sauri yasa ɗayan hannunshi ya dafe saitin zuciyarsa da ke mishi barazanar tsalle ta faɗo k'asa. "Na shiga uku ni Azaad meke shiri faruwa dani?" Ya faɗa a baiyane, yayin da fuskarshi ta bayyana tsoron da ke shigar shi ya sauke wata k'arfaffiyar ajiyar zuciya, jikinshi a mace ya nufi gym room{d'akin motsa jiki} gym mat machine ya fara hawa tsawon lokaci ya share akanshi kafin ya yi switch off ɗinsa. Jikinshi ya jik'e sharkaf da gumi. Direct bathroom ya wuce ya yi wanka cikin minti goma ya shirya cikin black suit yana cikin ɗora wrist watch, ya ji an turo k'ofa ta jikin mirror da yake tsaye ya hango madam Salima tana sanye da bathrobe ta ɗora small white towel akanta da alama fitowarta daga wanka kenan ta shigo part ɗin nashi. Yana arba da ita ya ji wani irin 6acin rai shiyasa yai sauri d'auke idanuwanshi akanta ya mayar bisa wrist watch ɗin. Ta k'araso cikin izza da jiji da kai ta zauna gefen gadonshi tai crossing legs ɗinta babu sallama balle ya ci daraja gaisuwa ta kalleshi cikin izzarta da tafi komai bashi haushi a tattara da ita ta fara magana kamar wacce aka yi wa dole. "Ina da tabbacin kana da masaniya da tun jiya na dawo, am very sure Nanny ta faɗa maka sak'on dawowata. Ta d'an dakata da magana tana wani yatsine fuska tana jiran ta ji ya fara apologies ɗinta sai taga kawai yana k'ok'arin saka derbies black cover shoe ɗinsa Kuma ta lura da tun lokaci da ta shigo ko kallonta bai yi ba. Hakan ba k'aramin sosa mata rai ya yi ba. Cikin fushi ta kira sunanshi. "Azaad! A hankali ya ɗago idanuwashi ya k'are mata kallo tass....kana ya cije lower lips ɗinshi tare da ɗage girar ido idan Azaad Junaid yana so yai mata mutum wulak'anci irin kallonan yake yi gani yake ba k'aramin koma baya bane a gareshi ya tsaya, musanya yawu da ita musanmman da yake da important meeting, saboda haka ya d'auki briefcase ɗinshi da ke aje akan bedside drawer ya nufi k'ofar fita cikin yanayi tafiyarshi ta k'asaita. "What hell think you're Azaad ina magana da kai you're ignored me?" Lets me tell I can take this anymore. Girgiza kanshi tare da buɗe k'ofa ya fice abinsa, ta taso cike da masifa ta biyo shi a baya tana ci gaba da zazzaga mishi masifa. "Azaad come back here I want to talk to you karka fita ka tsaya nace zan yi magana da kai banso wulak'anci you already know that. Har suka sauko downstairs parlor bai tsaya ba ita kuma bata fasa bin shi ba tana zubda ruwan rashin mutunci. Da gudu 'yan aikinsu suka watse Nanny Lacey ma d'akinta ta shige har da su murza key tana tsanmani, Azaad ya faɗawa madam zance aure da ya yi ne shine ta buɗe kwadon masifa da sanyi safiya. "Dole ka dawo ka ji da matsalata first kafin ka fita, ko kana da abin da yafini muhimmanci ne? Jin abin da ta faɗa yasa shi sakin handle ɗin k'ofa ya juyo a mugun fusace, cikin kakkausar murya ya ce. "Me kika ce Salima?" Yadda yai mata tambayar tasan ta reni ce da so gani k'arshenta, shiyasa ta kalleshi da murtuk'akk'iyar fuskarta. "Duk abin da na faɗa ka ji ni sarai....so no need to repeat.. Ta faɗa tana irin mak'e kafad'a da watsi da hannuwanta da ke nuni da zallan reni. "A tunanina Salima its over between us ko kin manta we're already divorce? Saboda haka ki fita harkana a hali yanzu kwata-kwata bana buk'atarki a rayuwata. Tun daga ranar da kika sa k'afa kika fita daga gidanan tare da yi fatali da umarni da rantsuwata ni kuma tun daga ranar I erased all the moment I'll have spend together.... "Ya isheka haka Azaad! Ta faɗa sounding very angry idanuwanta suka firfito, ta kuma finciko towel ɗin kanta tai jifa dashi tasoma tattaki ta nufo shi tare da nuna k'irjinta da yatsa gaba ɗaya mamakin maganganunshi take yi ta kasa yarda daga bakinsa suke fitowa. "Ni...ni Salima...Azaad kake gayyawa you erased all the moment I'll have spend together are you insane?" "Lokaci ne za ban-bance mana tsakani ni da ke waye mahaukaci. "To wallahi-tallahi bari ka ji Azaad ban amince da wannan saki ba saboda haka you have to cancel it, an gayamaka na shirya rabuwa da kaine?" You have to ask me first kafin ka yanke wannan banzar hukunci naka, saboda haka ni ban shiryawa rabuwa da kai ba because I want to spend the rest of my life with you so you better cancel that stupid divorce.... Cikin kad'uwa Azaad yake kallonta tare da waro idanuwanshi. "Ashe duk tsawon shekaru nan da kidahumar jahila nake zaune ban ta6a sani Salima ke k'asurgumar mahaukaciya bace sai yau da kika fito min da 6oyayyen asalinki. Inaso ki buɗe kunnuwanki ki saurareni da kyau wallahi-azim idan duk duniya nan za taru akaina na gama aurenki. Yana k'arasa magana ya juya cike da 6acin rai ya buɗe k'ofa da k'arfi ya fita yana bi sa hanyarshi ta zuwa kamfaninsa, na Gold Hakeem ya kirashi ya fesa mishi mummunan labari an har6en Hasheem a gidan gonar babban Yaya fasa zuwa company ya yi nufi prime hospital inda Hasheem yake likitoci sun duk'ufa ceto rayuwarshi, ana sa ran sai an cire mishi k'afa a dalili kwayoyin cuta sun shiga cikin raunin har sun ta6a naman k'afar tashi kasancewar har saida ya kwana ya yini kafin maigadi ya farga da hali da yake ciki. Madam Salima ta fi minti goma a tsaye ko kwakkwaran motsi ta kasa da kyar ta iya jan kafafuwanta da suka yi mata mugun nauyi har kamar ba nata ba. Har wani bishi-bishi take gani, ga zuciyarta dake mata mugun tuk'uk'i a haka ta soma tattaka matattak'alar bene duk lokaci da ta taka one stairs sai ta tsaya ta sauke wahalallen numfashi, kamar mai cutar asthma koda ta isa d'akinta ta jigata matuk'a, sai kawai ta kife akan tangamemen gadonta. Sai tayi yunk'uri yi kuka ko za ta ji sauk'i abin da take ji yana mata yawo a kahon zuciya, sai ta danne shi da k'arfin tsiya a ganinta zubda hawaye na rakwaye mata ne ba na iri-irinta jajirtattu bane. Idan har ta bar hawayenta suka zuba akan kumatunta hakan na nufi ta faɗi, kwata-kwata a tsarinta babu faɗuwa sai zallan nasara. Tabbas Azaad ya taro match kamar yadda ya faɗa ne idan duk duniya za su taru akanshi ya gama aurenta. Ita ma abin haka yake a wurinta idan duk duniya za su taru akanta yanzu ta fara zaman aure dashi. Yayin da shed'aniyar zuciyarta ta ce da ita "Haba Salima yaushe kika fara sakin jiki da har wani mahaluki zai haifar miki da damuwa?" Azaad ya k'ikk'iro wannan hanya ne domin ya sami lagonki ya rusa miki business career dinki idan kika bari yai nasara akanki shikenan babban company zai koma hannun 'yan uwanki, karki manta burinki ya ta'alak'a ne da son mallakarsa ke Kaɗai. Babu shiri ta mik'e zubur a lokaci d'aya k'arfi da kuzarinta da rasa na wancan gadin suka dawo jikinta tamkar ba abin da ya faru da ita a cikin k'ankani lokaci ta shirya cikin Indonesia gown mai adon sequence sai kyali da daukar ido take. Ta fice abinta daga gidan kaitsaye gidan aminiyarta Hafsat Shinkafi direba ya sauke ta.... *AZAAD JUNAID* _{The young Billionaire}_ Na Jeeddah Aliyu Top Ten Takun Haske Batch:A *Wannan littafi na kud'i ne yana daya daga cikin top ten takun haske don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ba domin mallakar littafan mu guda bakwai sai a tuntu6e wannan number* +447894142004 23.... Tun lokaci da ta fara labartawa Hafsat Shinkafi labari abin da ya faru, tai k'uru da idanuwa tana kallonta duk tsawon shekaru da tai da madam Salima batasan cewa bata da ilimin addini kwata-kwata ba. Ta zaci kawai dai bata yi zurfi a ciki ba ashe tunani da hasashenta ne ya bata hakan. Cabdijam.... lallai Salima jahila ce lamba d'aya wato ita tsabar ruwan boko da ta kwankwad'a da kuma cudanya da masu jajjaye kunnuwa ta kwashe dabi'unsu tsaf in banda hauka da jahilci a ina aka ta6a sakin mace har ta kusa gama iddah ta ce bata aminta da saki ba. Watakila bata ma san menene iddah ba. Ajiyar zuciya Hafsat ta sauke kana ta cire tagumin da tayi cikin natsuwa ta fara magana. "Gaskiya Salima kin tafka babban kuskure na 6oye min message ɗin da Azaad ya turo miki, da tun farko kin faɗa min da na wayar miki da kai. "Mtsss....dallah ya isa Hafsa ni fa kwata-kwata ban d'auke message ɗin da muhimmanci ba. Azaad bai isa ya yanke alak'ar aurenmu ba... "D'an dakata mana Salima! Hafsat ta faɗa da sauri tare da tasowa ta zauna daff da Salima kana ta zarce da faɗin. "Salima idan ke ba ki da ilmin addini ko tantama bana yi Azaad yana dashi. Kuma shi ɗin ba mahaukaci bane, a lissafi na saura kwanaki Kaɗan ki kammala iddarki idan har kika kammala ta batare da Azaad ya furta ya dawo dake ba. To ki sa aranki aure ke dashi hayatan-hayatan har sai ya sake biya sadaki an ɗora muku wani aure. Da Kuma saki uku ne ba za ki sake halatta agareshi ba har sai kin sake wani aure idan Allah ya kawo k'addarar rabuwarku da wancan mijin da kika aure sannan ne kike da damar sake aure Azaad Junaid. Salima babban abun da ya cuce ki rashin ilimin addini da kina dashi ko kusa ba za ki furta rashin amincewa da sakin da Azaad yai miki ba. Allah {S.W.T}ya halatta saki a hannun maza saboda mace tana da saurin fushi da saurin yanke hukunci. Mafi yawanci mata suna tafiyar da al'amuransu akan abinda zuciya ta raya musu. Amma shi namiji yana da zurfin tunani da hangen nesa, Kuma zai yi hasashe tare da yin aiki da hankali. "Dallah....ya isa haka Hafsat kin wani tsareni da dogon sarhi in fact kwakwalwarta ba za ta d'auke shi ba. Gara kawai ki faɗa min hanyar da zan bi na dai-daita al'murrana. Doguwar ajiyar zuciya Hafsat ta sauke tana girgiza kanta tabbas sai yau ta k'ara yarda da magana nan ta masu iya magana da ke cewa jahilci yafi hauka. "Salima ni fa ina k'ok'ari na haska miki haske ko za ki fita daga mummunan duhu da kike ciki, ke kuma kina danganta ni da dogon sarhi. Wallahi-tallahi idan har kika ci gaba da tafiya a haka gaba ɗaya al-amurranki ba za su dai-daita ba. Saidai su ta6ar6are gwara tun wuri ki natsu na ɗora ki akan hanya. "Na ji Hafsat amma ni wannan karatun naki zai shigeni ne bayan ki faɗi hanya da zai bi Azaad ya dawo da aurenmu. "Mtsss....wai Salima meke damunki ne huh?" Sai nayi gabas kiyi yamma yanzu nan ma ba hanyar ce nake faɗa miki ba. "Shikenan Hafsat ina sauraren ki. Ta faɗa cike da izza tare da nuna k'osawarta. Yayin da Hafsat ta gyara zamanta ta cigaba da faɗin. "Salima a halin yanzu dole sai kin sauke wannan girman kan naki da izza, ki bi hanyar maslaha ki karkato da hankali Azaad kafin iddarki ta cika ya dawo da aurenku karki sake iddarki ta cika bai dawo da ke ba. Idan har da gaske kina da burin ci gaba da zama matar Azaad Junaid dole ki sauke girman. Ki bashi hak'uri idan ta kama ki durkusa on your knees.... "Whats?" Hafsat kinsan abin da kike faɗa kuwa? No....no... Its can not be possible haba ki sake shawara ban da wannan na durkusa fa kika ce? "To ai shikenan tun da ba za ki iya ba amma inaso ki fara lissafa kanki a jerin zauwarawa, ki kuma fara hango Azaad Junaid da tsaleliyar amaryarshi. Zuciyar Madam Salima ta buga da k'arfi duk duniya ba abin da ta tsana irin ta ji an danganta Azaad ɗinta da wata mace ba ita ba. Cike da 6acin rai ta kalli Hafsat ta ce. "Hafsat zan dawo da Azaad gareni batare da na k'ask'antar da kaina ba, ki tuna ni mace ce mai k'arfin iko da izza ban ta6a yarda da faɗuwa ba sai nasara saboda haka Azaad zai dawo gareni ko yana so ko bayaso. "Salima karki yi ganganci domin iddarki tana daff da cika, ki tuna aiki da hankali yafi aiki da agogo. "Kai... Hafsat...kai! Gaba ɗaya kin isheni da zance iddah wai wacece wannan iddar da keso shiga tsakanina da mijina?" "Innalillahi wa'aina illahim raji'un! Hafsat ta faɗa tana tafa hannuwanta cike da kad'uwa take kallon madam Salima, kafin ta girgiza kai tana ta6e baki. "Ni dama nasan za ayi haka hasashena kuwa ya tabbata gaskiya, Salima iddar ce ba ki sani ba anyya kuwa Salima kina gudanarda addininki yadda shari'a ta sharad'a?" 6ata fuska tayi cike da izgilanci ta ce. "Banso maganar banza Hafsat za ki faɗa min wacece iddah ko na d'auki jakkata na bar miki gidanki?" "Uhmm....jahili ya fi mahaukaci hauka. Hafsat ta faɗa cikin zuciyarta a bayyane kuma sai ta ce. "Yanzu kuwa zan faɗa miki wacece iddah? Iddah ba mutum bace kamar yadda kika zata. "Idan har ba mutum bace to wacece ita ko aljana ce?" Madam Salima ta watsa mata tambaya tare da yatsine fuska. Hafsat bata bi ta kanta ba ta gyara zamanta ta tattaro natsuwa da dukkan hankalinta ta mayar dasu akan Salima. "Iddah ita ce zaman jira da mata ke yi bayan sun rabu da mazajensu kafin su sake yi wani aure. Ita kanta iddar kala biyu ce akwai iddar rasuwa akwai iddar rabuwa. "D'an dakata mana Hafsat ita iddar hadda ta mutuwa akwai? Cab.... gaskiya wannan iddar akwai rikitarwa. "A wurin marar ilimin kan tana da matuk'ar wahala fahimta amma a gun mai wadattace sani ba abin da ya fi ta sauk'i. "Ban fahimci ki ba Hafsat ki yi min magana da yare da hankali da tunanina zai d'auka?" "Idan har kinaso hankali da tunanina su dauka sai kin daina katse ni kawai ki buɗe kunnuwanki ki saurare abin da nake faɗa domin ke zai amfana ba ni ba, saboda ni nasan da wannan babin tun ina da shekaru goma sha uku a duniya. Sosai ran madam Salima ya fara 6aci tsakani da Allah ba don tanaso sani wacece iddar nan ba, da tuni ta wufce jakkarta tabar ma Hafsat Shinkafi gidanta. Gani yadda take cika tana batsewa yasa Hafsat bata jira jin ta bakinta ba ta ci gaba da cewa. "Iddar rasuwa ita ce bahaushe yake kira da takaba. Ita ɗin ma kala biyu ce akwai takabar mai ciki ita iddarta tana kammala ne daga lokaci da ta haihu. Wacce ba mai ciki ba Kuma zata zauna ne tsawon watani huɗu da kwanaki goma. Nau'in iddar rabuwa ta kasu kashi uku iddar mai ciki, da iddar mai jini haila sai Kuma mace da bata fara jini haila ba. Ko Kuma wacce ta fidda rai daga zuwan jini haila bima'ana tsohuwa. Iddar mace mai ciki za ta zauna ne har zuwa lokaci da ta haife ciki. Idan ta haihu to iddarta ta k'are Koda kuwa ranar da aka sake ta ɗin ne ta haihu. Iddar mace mai jini haila, sai tayi jini uku. Da zarar tayi jini uku shikenan iddarta ta kammala kamar ke kenan tafiyar da muka yi kin yi menstruation sau biyu yanzu da zarar kin sake yin wani kin gama iddarki sai fatan samun wani miji idan kina da sha'awar sake aure. Sai Kuma iddar tsohuwa ko k'aramar yarinya...... "Ya isa Hafsat ai kin riga kin faɗi iya abin da nakeso ji ki bar saura kawai idan natsuwata ta dawo jikina Kya faɗa min. Jikinta na rawa ta mik'e ta d'auki handbag ɗinta da ke aje akan center table, ta dubi Hafsat da idanuwanta da suka fara canza launi ta ce. "Hafsat zan tafi gida tabbas a yau ɗinan zan kira ki da albishir ɗin Azaad ya dawo da aurenmu. "Ina miki fatan haka Salima amma idan burinki ya cika ki nemi malamin addini, ya k'ara miki haske akan sha'ani addini kada ya zamana kina amsa suna musulunci ne kawai. Gaba ɗaya rayuwarki Salima neman duniya kawai kika sa gaba, kin manta da neman lahira al'hali lahira a duniya ake nemanta wallahi da zarar ka mutu shikenan.... "Nagode da shawara Hafsat. Ta katseta cikin k'osawa da zancenta, ta juya cikin tafiyar sauri koda ta fito direbanta yana zaune a mota yana jiran fitowar yana d'aya ɗaga k'a'idojinta duk idan ya kaita bai isa ya tafi ba dole ya zauna har ta gama abin da ta je yi. ***** ***** ******* Duk wani shige da fice na asibiti Azaad ne ya yi hatta da jini da za a yi wa Hasheem surgery nashi aka d'iba, ko Kaɗan bai so a cirewa Hasheem k'afa ba so ya yi ya fitar da shi waje, saida doctors ɗin suka yi connecting ɗinshi da wani asibiti dake Germany suka turo musu bayyanai Hasheem su ma sun bada shawarar a cire k'afar kawai saboda ta riga ta fara lalacewa. Daga k'arshe sai yanke k'afar aka yi, lokaci da aka fito da Hasheem daga theatre room Azaad har dasu kuka saboda ba k'aramin tausaya mishi ya yi ba. Saida ya ga an kammala komai sannan ya wuce kamfaninshi koda ya iso tuni Hakeem ya wakilce shi meeting ɗin da za su yi. Bayan sun Miyya sun dawo daga school suna zaune a downstairs parlor, Nanny Lacey ta fito daga kitchen sai lokaci take sanarda Aneesah da Airah dawowar Mommy. Nan take gaban Miyya ya faɗi duk wani annuri da ke kan fuskarta ya gushe, har wani zazza6i ta ji yana neman rufe ta. Daga Aneesah har Airah ba wanda ya nuna farin cikinshi da dawowar mommy ɗin, sai ma aikin gabansu da suka ci gaba da yi. bayan kamar minti goma da Nanny ta faɗa musu dawowar madam, suka ji karar buɗe k'ofa a zatonsu daddy ne ko wasu bak'i sai kawai suka yi tozali da madam Salima fuskarta a murtuk'e ko daga yanayi tafiyarta Kaɗai za ka gano irin zallan 6acin ran da take ciki. Miyya tana ɗago idanuwanta sai akan fuskarta kasa ci gaba da kallonta tayi shiyasa tai maza ta mayarda ganinta akan Ahlam da ke kwance a cinyoyinta tana barci. "Welcome mommy! Aneesah da Airah suka faɗa a tare yadda suka gaidata bai yi kama da gaisuwa irin ta uwa da 'ya'yanta ba. Daga haka ba wacce ta k'ara koda kallonta ne. Ita ma hannu kawai ta ɗaga musu ba wani kulawa balle ta nuna tayi kewarsu tana daff da fara taka matattak'alar bene idanuwanta suka hasko mata Miyya......