👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA*👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq*✍🏿 *MARUBUCIYAR* 👇🏿 Kasancewar Tafiyarsu makaranta na tunkarowa ya sanyasu shiga busy sosai Hafiz yake taka rawar gani a tafiyar da su Zarah zasuyi makaranta A yanzu sun gama Shirya koma yau Jabir ya kaisu Shopping mall Wanda shi ya biya musu kudin sayayyar komai itadai Zarah a sanyaye take yayinda Asma'u ke d'aukar musu komai da zasu buk'ata. Bayan sun gama ya biya kudin suka kama hanyar gida Bayan shigar Asma'u gidan sun tab'a Hira sosai tsakanin Zarah da Hafiz Bayan nan tayi mishi Godiya akan irin hidimar da yake mata murmushi ya sakar mata ya ce. "Komai nayi miki ban fad'i ba matata har na k'agara ranar nan tazo bansan wani irin farinciki zan shiga ba ranar da muka zama mata da miji" Murmushi Zarah tayi tare da rufe fuska kunya ta baibayeta. "Cikin Sauri ta bud'e murfin motar tare da fita " Dariya yayi tare da girgiza kai Dan kunyar ta Zarahn tashi ba k'aramun burgesa take ba yanason mace mai kunya a rayuwa(exectly wlh kunya ado ce ga y'a mace maza da dama suna son mace mai kunya Rashin kunyar y'a mace ba wayewa bace Allahsa mu dace") yaune tafiyar su Zarah makaranta tunda suka tashi cikin farinciki suke su dukansu Bayan sungama Parking d'in komai d'insu an saka a boot din motar hafiz . nasiha sosai mai shiga jiki Malam ya dinga musu Bayan suma su maman su Asmy sunyi musu nasiha Mama Rabi ko ko Allah ya kiyaye batace ba sai bak'inciki take dubu goma Malam ya basu tare da cewa sunyi wani abun dashi. Dukansu sosai sukayi kyau cikin manyan hijabai Asmy ma tayi kyau Dan itama masha Allah badai kyauba a hanya Hafiz sai satar kallon Zarah yake har suka isa Zaria kai tsaye cikin Makarantar A B U suka nufa. Asmy ita ta dinga shigar musu da kayansu hostel din da aka kama musu Zarah ko tana gaban motar Hafiz ne ya mik'o mata kwalin waya biyu Duka iri d'aya Tare da cewa . "ga wayarki keda Asmy please dia karkice bazaki amsa ba saboda bazan juri Rashin jin muryarki a kusa dani ba Kuma hasalima An sanya mana Aure ina da hakkin da zan d'auki hidimarki" Amsar kwalin wayar Zarah tare da cewa "Hakane ya Hafiz nagode Hakika kaid'in ka taka rawar gani a cikin rayuwa ta babu abunda zance dakai Sai fatan alkhairi da nasara a rayuwa mungode" Murmushi yayi najin dadi tare da mik'a mata 20k yace gashi ba yawa ku fara chachaftawa da wannan" "girgiza kai tayi tare d'ago da dara daran idanuwanta "a a a ya Hafiz wlh bazan amsa ba hidimar tayi yawa." "kamo lallausan hannunta yayi tare da damk'a mata kudin a hannu Wanda tunda ya tab'a hannun Zarah taji wani irin shock saida ta rumtse ido kafin ta daidaita nutsuwarta tayi saurin kwace hannunta Tare da b'ata fuska ta ce " "Meyasa zaka rik'emun hannu ya Hafiz Bayan ni ba maharramarka bace"hade hannayenshi waje biyu Alamun rok'o ya ce "am sorry my Zarah by mistake ne bansan nayi ba" " Uhm" kawai tace tare da bude motar ta ce "Ka tafi karkayi dare fa kaga hanya ba kyau" "korata ake kenan"cikin murmushi ta bashi amsa da "Nina isa Banki mu shekara haka ba" 'ta fad'a ta na rufe fuska " murmushin jin dad'i yayi cike da kewarta Hafiz ya juya yabar makaranta Inda Zarah ta kama hanyar hostel d'insu. ta na shiga ta samu Asmy Harta cire hijab din ta na shirya musu kaya "Kallon d'akin tayi ta ce. " wai nufinki mu kadai ne kenan a dakin" "Wlhko Nima haka nagani naga duk ba a fara zuwa ba Kinsan Monday ake fara lectures ba kowa zai zo kamar haka ba" "Kice mu iyayen azarb'ab'i mune farko farko ta fad'a tana cire hijab din jikinta " Dariya asmy tayi ta ce "Keko abunka ga farin shiga Dariya Itama Zarah tayi tare suka kimtsa komai kafin Zarah ta mik'awa Asmy wayar da ya Hafiz ya saya musu zo kuga murna wajen Asmy hada tsalle ta Rungume Zarah. " itama Zarah cikin farincikin take bud'e wayar suka ga iPhone 6+ ce Duka iri daya dubawa sukayi kowacce Duka an sanya sim ganin ba chaji gashi ba wuta ya sanyasu ajewa sai Chan wajen 8 aka kawo wuta nan suka sanya wawowin chaji salla Zarah tayi tare tare da hayewa kan bed tace. "nikam bacci zanyi wlh nagaji" Asmy ce ta ce "Chab aini nan inkinga na kwanta to wayar nan ta cika Na duddura abubuwa a ciki har what's app saina bud'e komin dare. " Dariya Zarah tayi ta ce "aifa abun nema ya samu nikam bacci ma zanyi waya bata dameniba sosai Idan kin d'auko abubuwan nima ki daukoman amma what's app kadai zaki budemun sannan kiyimun down load din Qur'an na ji da na karantawa" " To" Asmy ta fad'a ta ce "Mu sarakan zumudi Allah sama akwai data a sim din " Juyawa Zarah tayi tare da kwanciya ta ce . "Allahsa ma babu muga ta tsiya kiyi ,zaman hofi" "Insha Allahu ma akwai muguwa Asmy ta fad'a tana Mikewa itama tare da Fara Sallar bacci ne ya kwashe Zarah cike da gajiya. Ranar Monday suka fara Lectures Sosai Dukansu suka maida hankalinsu ga karatunsu Zarah suna waya da Hafiz Sosai Kuma suna chat dukda ba Sosai take hawaba saboda ba wasu mutanen chat gareta ba. danma Asmy tayiwa wata kawarsu da sukayi sec magana ta bada number su aka sanyasu grp din makaranta anan ne ma wasu ke binsu PC har suke chat amma dukda haka Zarah saita yini bata hau online ba. Karatu suke sosai ba kama hannun yaro yanzu hostel din ya fara cika da mutane Dakinsu ma sunsamu Karin wata Mutum guda zaituna. Cikin marairaicewa ta ce "Yaya Dan Allah ka bari na tafi A B U din wlh yaya banason karatu a America plx harfa sun bani admissions kuma ma har anfara lectures yaya Dan Allah" "Chuchu bazan barki kiyi karatu anan k'asar ba fa Ga yanda na tsara tare zamu tafi america a gidana zakiyi karatunki amma ban lamunce na barki ki tafi Zaria karatu ba Nafison kiyi a gaba na na sanya miki ido saboda wannan rawar kan naki Dan kiyi abunda kikeso shiyasa ai kikak'i cike KASU kika zab'i ki tafi Zaria sannan banason kiyi karatu a kasar nan sanin kanki ne to bazaki ba A B U din ba na gama magana" "kuka Chuchu ta sanya tare da Fara birgima ta sangarta sosai ta ke kuka da diddira kafa Ammy ce ta shigo ta ce . " Subhanalla Me akayiwa Auta ta ke wannan kukan "MD dake zauna baice uffan ba sai maida hankalinshi ga kallon da yake yayi" Chuchu ce cikin sangarta ta ce"Ammy yaya ne ya ce "Wai bazan tafi Zaria karatu ba dole sai dai mu tafi america tare Bayan ni banason nesa dake Ammy plx ki ce ya barni " "Kallon MD Ammy ta yi ta ce " me yasa bazaka barta ba babana tunda harta samu kuma ta nuna Chan din take so ka barta ta tafi kawai nima banason tayi nesa dani saboda kaga gidan kadaici zaiyimun yawane ba Abbanku Zainab na gidan mijinta kaima ka tafi sai anganka please Babban yaya ka barmun ita " Jan numfashi Yayi tare Dagowa ya harari Chuchu dake Kuka jikin Ammy ya ce. "Allah Ammy kin sangarta Yarinyar nan jifa irin tabarar da takeyiwa mutane" Dariya Ammy tayi ta ce "Ah muka sangarta ta dai duk gidan nan wa ya fi sangarta Maryam sama da kai " "Ummmm to Taci arzikinki Ammy na yarda Tayi Chan d'in Allah kiyaye Amma Tana cigaba da irin wannan shigar Saidai taga na cireta Nayi mata Aure " ya fad'a yana kallon matsatsun Riga da wandon dake jikinta Tsallen murna Chuchu ta buga tare da rugawa ta Rungumeshi ta ce. "Thnks Babban Yaya Uba Allah ya k'ara girma bazan sake ba sannan tayi Dariya ta ce hhh yaya Ai ko kayimun Auren bazan zaunaba y'ar k'arama dani kuna kaini kafin ku dawo ma na rigaku gudowa " Duk miskilancin MD saida ya d'an dara tare da Kai mata "Dukan wasa a baya ya ce. " Kin rainani ko chuchun yaya shiyasa kika fad'amun haka" "Ammey ma tayi Dariya tare da girgiza kai ta ce "Allah shiryaki Auta" Dariya Chuchu tayi tare da mik'ewa ta Ruga cikin tana tsallan murna nan ta kira Aunty Zey ta mata albishir yaya Ya amince.. A nan take MD ya kira Wani Abokinshi dayake lecturar makarantar ta Cikin waya yayi mishi bayanin komai take ya ce Ai ba matsala tunda ta samu registration Banki kawai za Aje ayi" PA d'inshi Ya kira Tare da sanyashi yaje yayiwa Chuchu registration saida yaga ya gama yi mata komai tukwana Ammy ce ta Kalleshi da damuwa a fuskarta ta ce. "Baba na wai ya maganar bincike game da kisan mahaifinku naga Har yanzu bakayi wani Abu ba yaci ace angano kowaye yayi mana Wannan d'anyen Aikin" "numfashi Ya fesar tare da cewa " Insha Allahu Mamy Gaskiya zatayi halinta inaji a jikina nan kusa akwai abun al'ajabin da zaizo bada jimawa ba akwai shirin da nake akan Lamarin " Goge hawayen da ya zubo mata Ammy tayi tare da cewa"Allah dai ya Toni.Asirin ko suwaye sukayi mana wannan d'anyen aikin insha Allahu bazasu gama da duniya lafiya ba Sannan asirinsu saiya tono" "Ameeeen MD ya fad'a tare da mik'ewa zai shiga Bedroom d'inshi dake gidan " da mamaki ammy ta Kalleshi ta ce "Ina kuma zaka Bayan Matarka na gari"......✍🏿 *Domin magana da marubuciyar 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 💑 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 MALLAKAR *Hajara L Sadeq* *_TEAM GAWURTATTU BIYAR_* 🅿️.........*15 & 16* Ta na gidansu Ammy"tsaki Ammy taja tare da cewa "Allah ya kyauta " D'an murmushin gefen baki yayi tare da girgiza kai ya wuce ciki. "Kwance take saman bed din Dakinsu ta na chat da Hafiz d'inta ya na bata labarin abun Dariya labarai masu sanya nishad'i sosai takejin dad'in chat d'in " Asmy ce da ke Dafa musu indomie a k'aramun gas d'insu ta ce " "Uhm Manya chat yayi dad'i sai Murmushi ake " "Kede bari wani labari ne ya Hafiz yake bani na ban Dariya" ta na sauke indomie d'in Asmy ta ce. "Ai naga alama kam Sauko muci kafin ta huce " kashe datar tayi tare da Saukowa nan suka faracin indomie d'in kasancewar dare ne. "suna cikin ci y'ar d'akin su zaituna ta dawo K'arewa shigarta kallo Zarah tayi taci uban attachment ta sanya matsatsun kaya girgiza kai tayi tare da Cigaba da abunda take Dan ta lura yarinyar ba tarbiya gareta ba hakan yasa ko maganar kirki bata had'asu inba Sannu ba . Sannu tayi musu Zarah ta amsa da yawwa " Asmy ce ma dayake suna Dan mutunci suka Dan tab'a Hira yayinda Zarah tayi kwanciyar ta dan gobe tun 8 suke da lectures . Washegari tunda safe ta shirya 7:40 tayi mata a class saboda 8 suke da lectures Bayan lecturer d'insu ya fita Mikewa tayi tare da fitowa jikin wani block ta zauna tare da fiddo hand out d'inta ta fara Duba abubuwan da akayi musu sosai. Sallama taji anyi mata batare da ta d'agoba ta amsa "zan iya zama Malama Zarah " Dagowa tayi tare da Kallonshi class mate d'insu ne amma tayi mamakin yanda yasan sunanta " "Matsa masa tayi tare da cewa zaka iya zama mana" Bayan ya zauna Har lokacin karatunta take "cike da burgewa ya ce " Gaskiya Malama Zarah kin burgeni wlh Tunda kika shigo makarantar nan na lura da kwazo da nutsuwarki Da yawan dalibai ba karatu ke.kawosu ba makaranta amma ke yanda kike dagewa yasanya nayi sha'awar Ko zakiyi abota dani Dan nima na k'aru saboda course d'inmu d'aya kuma math tana bani wahala sosai " Murmushi Zarah tayi masa tare da kallonta ta lura yana da nutsuwa daga ganinsa kasan d'an Babban gidane ta ce "Badamuwa Allah sa mu karu da juna Saidai bansan sunan malamin nawa ba " Cikin barkwanci ya ce "Ah dalibinki dai ai kece malamar sunana Yusuf muna zaune a garin Abuja tare da iyaye na karatu ya kawoni Zaria bansan kowaba" "Ah kace Babana ne Saidai na kiraka da Baba " Dariya Yusuf yayi ya ce "Wow kice da y'ata nake tare Gaskiya nayi sa'ar haihuwar wannan santaleliyar d'iya Kinga dole ayimun biyayya Sannan Abban na zaki dinga Cemun ba Baba ba " Duk yanda Zarah taso ta fusge saida ya sanyata Dariya ta ce "Eh Gaskiya ne Abba na Amma naga Abban nawa akwai iyayi da surutu fa " Dariya yayi tare da bude book dinsa ya ce "Wlh daughter karatun da akayi yau kwata kwata bangane ba idan kin gane ki koyamun please" “bari na duba naga ko zan iya ta fad'a ta na amsa tare da Fara gwada masa dalla_dalla kamar ita ce lecturar sosai Yusuf ya gane fiye da yanda Malam ma ya koya a aji shi kanshi ya sake da baiwar kokari irin na Zarah gashi dai tare aka koya musu amma saika rantse malamin ma a Wajenta ya koya. Saida ta gama koya masa komai "wow amma daughter nagode Wlh daga yau kinzama malamata ki godewa Allah yayi miki baiwar da ba kowa ya sameta ba Kyau Ilimi tarbiya uwa uba addini " "Muje dai yanzu class za a shiga wata lectures ba surutun ba Abba na" ta fad'a tana Mikewa Shima Mikewa yayi yana Dariya tare da Amsar jakar dake hannunta "wara idanu tayi ta ce . " so kake ace y'a ta sanya uba rik'e jaka ai sai a sanyamu a news "Shima dariyar yayi tare da amsar jakar ya ce " Kinga sai muyi suna yanda za ayi ta zancenmu muzama cele". Har suka isa Class din suna Hirar barkwanci duk miskilancin Zarah har mamaki nayi yanda ta sakarwa Yusuf kodan ance Gamon jini daban yake. Da suka gama lecture ma tare suka fito Inda sukaje capteria sukaci abinci kafin Zarah ta wuce hostel Bayan ya amshi numberta. Shakuwa ce da abokantaka ta shiga tsakanin Zarah da Yusuf yazama closed fried d'inta Asmy har mamaki ta ke yanda Zarah ta sakarwa Yusuf fuska duk sanda bai gane wani Abu ba ita take zaunawa ta fahimtar dashi sosai yake amfanuwa da Zarah. Cikin sati guda da Fara lecture a makarantar har amfara sanin Zarah saboda kokarinta Inda tayi wasu kawaye su biyu hibba da Jamila suma yabawa da tarbiyarsu ta sanya Zarah fara abuta dasu amma fa ba wai Chan ba saboda Har yanzu miskilancin ta ya na nan na Rashin son magana idan y'an maganar sukazo saikayi mamakin yanda take magana . A yanzu Hankalinta kwance yake Hartama fara mancewa da su Mama Rabi Saidai tunanin babanta da take. Suna waya da Hafiz Ya ce "Dear wai bazakije ku bud'e account ba Yaci ace kun bud'e ko Dan saboda scholarship sannan idan za ayi muku aike fa account yafi sauki akan Sai an Aiko muku" "A rufda cikin da take a kwance ta ce " To ya Hafiz Insha Allahu gobe Monday sai muje mu bud'e ko" "Yawwa matas Shiyasa nake sonki gobe kuje ku bud'e Ki bud'e a access " "To ta fad'a tare da cewa gashi ba musan ko ina ba bamu tab'a fita ba " "Ina abokin naki da kike bani labari Abba ko to shi zai iya sani kice ya rakaki " "To " ta fad'a sun tab'a Hira Kad'an kafin ta kashe wayar a yanzu Hafiz ya Riga ya fara zama wani bangare na jikinta tun bata sonshi yanzu har taji ta fara sonshi saboda soyayya da kulawa da yake nuna mata. Washegari Bayan fitowarsu daga lecture suka shirya Fita domin Suje su bud'e account around 1 suka tafi Yusuf yayi musu rakiya Napep suka hau su Ukku Inda shi Yusuf ya hau gaba. Nan napep d'insu ta fara tafiya Yusuf ne ya jiyo cikin barkwanci ya ce "Daugher Kinga kuwa Yanda kikayi kyau na jima banga macen da hijab ke yiwa kyau kamarki ba ked'in ta musamman ce fa " "Dariya tayi tare da cewa " baka rabo da barkwanci Abba na Kana uba amma ka maida y'ar jikarka" "Y'ar Dariya yayi ya ce " Ai Gaskiya Ce dole a fad'a y'artawa ta daban ce Shiyasa idan na tashi Aurar da ita mutum na daban zan aurawa saboda ked'in Matar manya ce ba yara ba wlh daughter " "Murmushi tayi tare da girgiza kai ta ce " kadai kalli gabanka karka fad'i kaja mana " Bayan Asmy ta gama waya Ta ce "Ai Gaskiya ka fad'a ko Abbanmu"Dariya yayi tare da cewa " Eh mana Bestynmu "nan suka cigaba da hirarsu su Ukku yawaici duk ta barkwanci ce. Sunzo daidai round din da zasubi ya kaisu Banki Sukaji mai napep d'in ya tsaya " Abun hankalinsu duk yana dumin da suke "Asmy ta ce Lafiya Malam yanaga ka tsaya" Mai napep d'in ya ce "Kuyi hakuri Hajiya Inajin wani Babban mutum ne zai wuce a wajen shiyasa chunkoso yayi yawa sai motocinsu sun gama wucewa tukwana a bamu hanya". Cikin jin Haushi Zarah ta ce " Yanzu haka zamuyi ta tsayuwa a titi saboda kawai wani zai wuce dan fin arziki za a tsaida mu". "Kuyi hakuri Hajiya ya muka iya " Daidai lokacin da wulfa_wulfam motocin suka fara gittawa ta wajen "Kallon motocin da tunda uwarta ta haifeta Bata tab'a gani ba Asmy ta gani wara idanu tayi tare da cewa " Kan uban Chan waiko shugaban k'asane ya shigo garin? Yusuf ne dake gaba ya ce "Kan ube Wlh MD ne ya shigo garin nan Chab dole a tsaida mutane Innalillahi inama zan gansa ido da ido MD a Zaria to me ya kawosa" "Zarah ce ta ja tsaki Ta ce " Shi waye da za ace sabodashi za a tsaida mutane saboda shi yanzu fa Banki suna gab da tashi ta fad'a ta na duba Agogon hannunta " "Yusuf ya jiwo ya ce " "Wai kina nufin bakisan MD ba kina Nigeria Amma baki Kallon Television da labarai ko? " Tab'e zarah tayi ta ce "nidai ban wani sansa ba Asmy ma ta ce nima kam " Yusuf sarkin bada labari juyowa yayi yare da cewa aiko yau zan baku labarinshi saboda ni fans dinsa ne ina karanta tarihinshi sosai". wani shahararren matashin mai kud'i ne iyayenshi suna zaune a garin Kaduna Mahaifiyarshi asalinta y'ar India ce a Chan mahaifinshi ya ganta ya auro ta shiyasa da kin gansa zakiga asalin ba indiye kannansa biyu mata sosai yake sonsu da ji dasu na manta sunansu , Compononyn da gayen nan ya mallaka nan Nigeria da ma k'asashen k'etare da kadarori gidajen mai kudade na ban mamaki ke kanki saikinyi mamaki gashi matashi Dan bazai wuce 38 years ba Amma wlh Inajin gayen nan shi yazo na biyu a kudi a negeria su kansu manyan durkusa masa suke Dan wasu Mahaukatan kud'ine ke garesa duk wajen Da kikaje kikaga an rubuta MD to mallakinsa ne wajen Shopping mall ko da park_park babu jahar da baya dasu a wannan k'asar tamu Ga shi ya had'u Iya had'uwa y'an mata da dama karkiga yanda suke rudewa a kansa Kwanaki a labarai da nagani Wata tana shirin kashe kanta saboda iyayenta zasu aura mata wani Dan uwanta shegiyar yarinyar nan wai MD takeson mutumin da baisan da zaman ta ba Mutum ne mai matuk'ar ji da kansa d'an gayu ne na Bugawa a jarida miskili ne na karshe Dan Ance a waje saiya yini baiyiwa mutane magana ba Amma ance yana magana da family dinsa sosai nidai tunda nake bantaba ga dariyar MD ba a hotunan da nake gani nasa Dan bantaba ganinsa ido da ido ba yana da manyan company a Abuja Amma ance mafi yawan harkokinsa a America ya ke yinsu yanzu haka a Chan yake da zama Saidai Naji ance Allah yayiwa mahaifinshi rasuwa shekaruun baya sosai Wanda ake zargin kashesa akayi to kunji takaitaccen Tarihin MD matashi da kudi Wannan shine kirarinsa". Tunda ya fara maganar Zarah take Jan tsaki Inda yana gamawa ta kuma Jan wani tsakin tare da cewa "To waya tambayeka Tarihinsa ina ruwanmu dashi ka zauna sai zuba kake mana akan wani chan banza " wara idanu Yusuf yayi ya ce "MD dinne banza Zarah" Tsaki taja Dan sosai takejin zafin tsayuwar nan tasu ta ce. "To me zankirashi dashi Bayan ya tsaida mu a titi yanzu haka Ina tunanin Banki sun tashi" ta fad'a ta na Jan tsaki tare da kauda kai tanajin haushin wannan banzan MD din da aka fad'a Wanda ya tsaida su kusan Awa guda a titi" "Chab ba ruwana wlh security dinsa suka jiki Saidai kiji ina cewa A mota muka hadu " "Asmy ce ta kwashe da Dariya tare da cewa " lallai Abbanmu kace duk uba da d'iyar da ake ajesa za ayi" "Chab ina ake ta uba idan ta fito lafiya sai acigaba da ubantakan" "Dariya Asmy tayi ta ce " Kaidai anyi matsoraci wlh nima saida ka fad'a na tuna da shopping mall d'insa da na tab'a gani a kano sannan a funtua ma ai akwai gidajen mansa har biyu Saida ka fad'a nagesu" "Chab ai yana da Mahaukatan gidajen mai kalli Chan ya fad'a yana nuna mata wani had'adden gidan mai sabo mai d'aukar kai Ashirin Ya ce " Karanta Chan ma me aka rubuta wancen ma nasa ne"dagawa Asmy tayi ta Kalla ta ce "Aikuwa wlh amma dai nima nayi mamakin Mahaukatan kudin matashin nan ya na da mata amma? " Wara hannu Yusuf yayi ya ce "wannanne dai bansaniba Anya ya rasa mata ma kuwa Amma dai ko wacece Matar zatasha miskilanci" Dariya asmy tayi ta ce "Gaskiya kam " sai sannan motocin MD suka gama wucewa Mai napep d'insu ya tada suka isa Zarah ta cika tayi Fam Asmy na mata Dariya ta ce. "Ran manya ya b'aci ayi hakuri ya muka iya k'asar nan Indai kai talaka ne Ai saida kayi hakuri" "koda suka isa Banki harsun tashi sosai Zarah ta k'ara k'uluwa tana tsinewa wannan shegen MD din da ya tsaidasu ji take kamar ta kurma ihu Dan Haushi Wata napep din suka Tara tare da komawa Zarah sai cika take batsewa Dan taji haushin b'ata lokaci ta da sukayi a banza a hofi. Dan ita tana daraja lokaci da ace tsawon lokacin da suka 'bata a tsaye da ko karatu ta tsaya tayi bata amfana ba. saida suka tsaya kasuwa sukayi sayayyar kayan miya da Abubuwan da zasu buk'ata Dan karsuyi fitowar banza sune basu koma makaranta ba sai wajen magriba . Koda isarsu makaranta sosai sukayi mamakin chinchirindon student wasu ana wawwatsewa ita dai Zarah bata tsaya ma kallonsu ba . Cikin jin Haushi ta isa hostel d'insu Asmy na mata fad'an akan ita da ta sani da hakuri yanzu kuma itace take mita akan Abunda baikai ya kawoba Ta ce " gobe ba saimuje mu bud'e ba Tunda safe ba" "Zarah bata kula taba saboda ita kanta batasan ya akayi ba takejin haushin b'ata lokacin da sukayi suna isa hostel sunyi mamaki ganin bak'in kaya a Bangaren da ba kowa Uban jibgin kaya akwatuna kamar Lefe banda uban provison Kallon juna sukayi da mamaki Asmy ta ce " to fa ko bakuwa muka samu a d'akin namu '". Basu k'arasa magana ba sukaji shigowarta dukansu Juyawa sukayi tare da Kallon matashiyar budurwar da baza wuce sa'anninsuba sanye da Doguwar Riga mai shegen tsada da kyau sai fara'a take sosai daga ganinta kasan tana da tsananin fara'a Murmushi ta sakar musu tare da karasa shigowa d'akin saurin fusgewa sukayi da Kallon da suke mata suka zauna bakin gadon su suna huta gajiyar da suka kwaso cikin girmamawa ta ce sannunku ko kune Wanda muke d'aki d'aya"......✍🏿 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 🅿️............*17 & 18* Murmushin suka mayar mata Asmy ta ce "Eh mune Sannu da zuwa" Yawwa Chuchu ta fad'a tare da cewa. "suna na Maryam Dikko ana cemun Chuchu ko kuma ku kirani da chuchun yaya dan nafison a kirani da haka kufa". "Ni suna nan Asma'u ana Cemun Asmy ita kuma wannan " Zarah y'ar uwata ce"Asmy ta fad'a ta na nuna Zarah "Wow nice name Sunan Ammy na ne Fatima Zarah" Saidai na kirata da momcy "Chuchu ta fad'a cikin iyayinta da ya zame mata jiki. " Murmushin da batayi niya ba Zarah ta sakar mata tare da cire hijab Dan taje tayi sallah "Asmy ta ce " Wow kice ke y'ar gata ce Gaki ga mom d'inki" "Ah sosai ma a gatana nazo school d'innan Saidai naga momcyn nawa kamar batason magana dani? "An d'an bata mata rai ne shiyasa " cewar Asmy Zarah ko Smile ta sakar mata tare da cewa"Ba haka bane Daughter Ykk anzo lafiya " "Alhmdllh momcy sorry ko Naji ance an bata maki rai ko waye dai Wanda ko wacce ta bata miki ran nan bata kyauta ba gsky kiyi hakuri ko" "Dariyar da bata shirya ba Zarah tayi Dan ta lura akwaita da surutu ta ce " shikenan na hakura daughter sunci arzikinki" "Wayar Chuchu ce ta yi ringing Cikin Sauri ta d'aga kiran Ganin ammynta ce ya sanyata " murna ta ce. "Hello my Ammy na " Daga bangaren Ammy ta ce "Na am Autar Ammy kinganni nan daga tafiyarki har na fara kewa" "Dariya Chuchu tayi tare da cewa" Wayyo Ammy na tun ba Aje ko ina ba har kin fara missing Nima da banjima ba Amma kadaicinki duk ya isheni "ta fad'a ta na turo baki. Sun tab'a Hira da Ammy cikin so da k'aunar juna Daga nan kuma ta kira Yayanta Bayan ya d'auka ta ce " yaya Ya hanya kunkoma lfy" "Alhmdllh ya fad'a tare da cewa " ki tsaya kiyi karatun kirki karki sake na kamaki da matsala na sanya a sa miki ido sosai banda biyewa kawayen banza da samarin banza na sameki da haka cireki zanyi" "toh yaya bazanyi ko d'aya ba daga ciki " Shima sun tab'a Hira tukwana ta kashe. Washe gari tare da Asmy suka wuce lectures saboda course d'insu d'aya itakuma Zarah ta tsaya tayi musu girki saboda sai 10 take da lectures. Cikin k'ank'anin lokaci Su Asmy suka saba da Chuchu Wanda duk ita Chuchu din take shishige musu ita dai tunda taga Zarah taji ta kwanta mata a rai. Itama Zarah din Chuchu ta kwanta mata a rai Saidai Abunda ke bata Haushi game da ita irin shigar da take kullum da k'aramun gyle bata tab'a ganinta da hijab ba sannan bata tab'a ganin ta dauki Alquran da sunan wai tayi karatu kullum cikin jin kid'a take ta lura yarinyar sangartattace ta Bugawa a jarida Saidai Inda take burge ta ta na da kamun kai sosai. Sosai y'an mata keson abokantaka da Chuchu saboda lokacin da MD ya kawota sunsan Kanwarsa ce ta bangarenta ko bata kula kowa saboda ita daman haka take bata fiya mu amula da mutane ba sai Wanda jininsu ya zo d'aya. Da Yamma suna zaune a Harabar hostel din suna shan daddad'an iskan dake kadawa Yayinda Alquran ke hannun Zarah cikin zazzak'ar muryarta Mai dadin sauraro ta ke rerawa ". " Chuchu ce dake sauraronta sosai ta burgeta yanda take zuba kiri'a shiru tayi ta na sauraronta wayarta ce Tayi ringing saurin dubawa tayi ta ga yaya MD aiko cikin farinciki ta daga tare da cewa. "Yaya na I really miss you so much yaya " Daga bangaren MD yaja numfashi tare da cewa "miss you too chuchun yaya Ya kike ya school d'in kina dai maida hankali kuma ba wata matsala ba abunda kike bukata" "alhmdllh yaya na ba wata matsala kuma ina maida hankali sosai " good girl haka nakesonji wani karatu nake ji daga gefenki ko? "Eh yaya momcy ce Ke yin karatu sunan Ammy gareta yaya karka ganta ta had'u da kyau Ga Ilimi Ko na baka ku gaisa" Tsaki yaja daga bangarensa tare da cewa "kin fara rainani ko ni zaki cewa zaki bawa wata mu gaisa " yana gama fad'ar haka ya kashe wayar . Chuchu ko Dariya tayi ta ce "Allah barmun kai yaya na " Asmy ce ta ce "Na lura dai kina ji da wannan Yayan naki sosai fa" "Kamar mai jira Chuchu ta gyara zama tare da cewa . " kaiii ai fin sosai ma ina son yaya sosai shidin ba matsayin yaya kadai yake a wajena ba shi din uba ne ya na sona da kaunata sosai nima ina sonshi sosai matsayi biyu yake a wajena yaya kuma uba Dan tun wata na biyu a ciki mahaifina ya rasu bansansa ba yaya na kadai ya mayemun gurbinshi shidin na musamman ne a cikin mutane" "Allahsrk Allah ya jikan Baba ya mishi Rahama Gaskiya dole kiso Yayan nan naki da yawa Allah ya k'ara had'a kanku" Cewar Asmy " "amen Chuchu ta amsa ta na cigaba da sauraron karatun Zarah" Dukda karatu ta ke amma Zarah na sauraronsu Taji abunda Suke fad'a saida takai daidai Inda takeson tsayawa tukwana ta ninke Alk'uran din Chuchu jira ta ke ta gama daman cewa ta yi" "Gaskiya momcy kin hadu ta ko ina wlh bantaba Jin kiri'ar karatu mai dad'in wannan ba kina da murya mai zaki Dan Allah Ko zaki dinga yimun k'arin karatu Dan wlh hizif d'ina ko Talatin bankai ba " "Da murmushi a fuskar Zarah ta ce " me zai hana daughter insha Allahu indai kina so daga yanzu ma saimu fara" Cikin farinciki Chuchu ta ce "Wow ngd momcy a shirye nake yanzu ma mu fara" Daga yasin suka fara Dan karatun ya tafi yanda suke so. Washegari a tare sukaje suka bud'e account Inda ita Chuchu rakiya ce kawai tayi musu. Tun daga ranar Zarah ta zama Malamar Chuchu kullum rabin shafi take Kara mata kuma sosai take fahimta idan ta bata hadda sai ta d'ora mata wani shakuwa Ce da abokantaka ta k'ara shiga tsakaninsu ta musamman hatta lecture din da bata ganeba wajen Zarah take zaunawa tayi mata bayani" Sannan yanzu Chuchu ta nutsu ta koyi wasu daga dabi'un Zarah yanzu itama hijab take sanyawa dukda ba Koda yaushe ba da wasu kide kide duk ta rage ji Zaune yake a garden d'in gidansa ya na shakar daddad'an iskan dake kadawa cike da ni'ima. lilo din da yake kai ya na jujjuyasa har wani lumshe ido yake zazzak'ar muryarta Take dawo masa a kwalwa hatta karatun da yaji tanayi yaji ya na masa gizau ya rasa ya akayi ba tunda yaji muryar mai karatun nan take dawo masa ba a kwalwa Tsaki ya ja a ransa tare da saurin barin tunanin da yake. Ya na nan zaune Jabir yazo yayi mamakin yau yanda fuskar abokin nasa a warware "Zaunawa yayi Inda suka shiga d'an hirar Kasuwancinsu" "MD ne ya ce " Ina son a shiryamun tafiya America gobe "okay Kai d'aya za ashirya maka ko tare da Amera " Sai sannan MD ya tuna da Amira tsaki yaja saboda haushinta da yakeji tunda ta tafi gidansu bata leko ba ya ce " "Ni d'aya zaka shiryamun ta na gidansu" da mamaki jaber ya ce. "Wai kana nufin tun sanda ta tafi bata dawo ba kusan two weeks lallai Abokina ka na hakuri wlh wai meyasa ba zaka bi shawarar Ammy ba akan ka k'ara Aure Kaga dai na farko Auren nan naka da Amera shekara Tara kenan bata tab'a d'ora girki ba da niyyar wai ta girkawa mijinta abinci ba Sannan ita ba haihuwa ta tab'ayi ba bare ka ce zaka zauna da ita Dan d'iyanta sanin kanka ne kunje Asibiti yafi sau nawa ance matsalar daga gareta ne dukda kana boye mata why zaka zauna mace d'aya ta dinga baka wahala tunda ka Aure ta Banbancinka da gwouro Kad'an ne kana da kudi da komai da zaka mori rayuwarka da su MD kayi tunani" "Nauyayyar Ajiyar zuciya MD ya sauke ya ce. " bazaka gane bane Jabir bazan tab'a yiwa Amera kishiya ba Dan bata haihuwa da misalin ace nine bana haihuwar itama haka zata zauna dani sannan har yanzu banga wace macen da zance wai ina da ra ayin aura ba" Numfasawa yayi saboda doguwar magana da bai saba ba sannan ya ce . "Amera na da kishi sosai bazata iya zama da kishiya ba sannan ina son matata bazanso abunda zai b'ata mata rai ba hasalima ni a tsarin rayuwata ban tsara auran macen da ta wuce d'aya ba mace d'aya nake da ra'ayin zama da ita kuma Babu saki a tsari na karma ka k'ara zomun da irin wannan maganar" "Shidai Jabir mamaki yaki barin fuskarsa zai d'aga baki yayi magana MD ya d'aga masa hannu dage kafada yayi tare da tashi Dan takaicin abokin nashi ya zauna mace d'aya na wahalsheshi. Washe gari MD ya bar k'asar Bayan Yaje yayiwa Ammynsa bankwana ya wuce america. Amera ko jin shiru mijin nata bai kirataba saida ta gama shiriritarta da yawonta iyayenta ko y'an komai kayi daidai ne cikinsu ba Wanda zaice shirya ki koma gidan mijinki. kiranshi tayi a waya taji layinshi na k'asar baya shiga Ta na kiran na America taga ya shiga amma baya d'auka sai sannan ta gane ya tafi america kenan . Aiko cikin rana tsaka ta d'auko akwatin kayanta cikin K'ananan kayan da ke jikinta ta d'ora mayafi tare da fitowa cikin Sauri iyayen da ke palour duk kallonta sukayi dadynta ya ce " " ina zuwa da tsakar ranar nan my merah"Tana Sauri ta bar palourn ya ce "Dad America na tafi gidan mijina bye saimun dawo " . ta na gama fad'ar haka tabar palour ta na fita ta kwalawa driver kira cikin Masifa da bala i ta rufeshi da fada akan zai bata mata lokaci shidai hakuri ya dinga bata Dan tun tana gidan ba mutunci garetaba ka tab'ata yanzu kayi ta aikinka Kai tsaye Airport ya wuce da ita. Koda ta isa America sosai Tasha fama kafin ta shawo kan mijin nata Dan ya nuna mata b'acin ranshi a fili kuma yayi zuciya da jikinta sosai hakan ya dinga damun Amera saida kyal ta samu ta na kuka ya hakura Dan tasan logar mijin nata ba abunda ya tsana sama da kukan mace . ranar dai amera ta d'an daure ba raki ba komai har Dan kanshi ya rabu da ita ya rasa wani irin mutum ne shi shekara Tara da Aure amma har yanzu baitab'a sanin gamsuwar da maza kecewa sunayi ba a tattare da matan su. Karatun su Zarah sosai yake gudu Dan yanzu haka harsun fara exam sosai suka maida hankalinsu ga karatunsu Masha Allah sun gama Exams lafiya sai kuma jiran result Inda kowa ya tafi gidansu dominyi Hutu dazasu rabu su Ukku saida sukaji ba dadi Chuchu hada hawaye A haka dai suka rabu akan zasu dinga waya Bayan sunyi musayar number" Chuchu tunda ta koma sosai Ammy taji dad'in irin shigar data ganta da ita ta hijab sosai taji dad'in sauyawar dabi'un na y'artata Wanda tun farko tasan sakacinta ne . Tunda Chuchu tazo bata da labari sai na Zarah nan Tabawa Ammy labarin karatun da Zarah ke koya mata yanzu har sunyi hizif Talatin sosai Ammy tayi murnar Haduwar y'artata da mutanen kwarai Itama har cikin ranta taji wannan zarar ta kwanta mata a rai sanyawa tayi ta kira mata ita Aiko cikin Sauri Chuchu ta kira mata ita Zarah na d'auka cikin d'oki Chuchu ta ce. "Momcy ga Ammy na zakuyi magana" ta fad'a ta na bawa Ammy wayar ". cikin nutsuwa Zarah ta gaishe da Ammy'inda Ammy ta amsa mata cikin Fara'a tare da yi mata Godiya akan Karatun da take koyawa Chuchu" cewa tayi" ba komai Ammy Ai anzama d'aya "sosai Ammy taji Zarah ta kwanta a ranta Dukda bata ganta a fili ba Amma a d'abi'unta da yanayin yanda taji muryarta sai taji ta na sha'awar Had'a zuri'a da ita a ranta ta ce " "inama ina da wani d'an da zai sota Bayan MD da na had'asu da ita Dan tasan MD kam yayi nisa ta ma hakura da masa maganar Karin Aure Dan tasan ba yi ba zaiyi. A haka har lokacin hutunsu ya k'are suka koma makaranta sai farincikin ganin juna suke nan aka d'ora daga Inda aka tsaya har suka cinye second semister Bayan sun koma wani hutun suna dawowa suka shiga aji biyu a lokacin ne kuma Hafiz zai tafi karo karatu England ranar da yazo mata bankwana school duk yayi sanyi Kallonshi tayi ta ce . "ya Hafiz naga duk kayi sanyi" Dagowa yayi tare da kallonta ya ce"kawai tafiyar nan da zanyi sainakejin gabana na fad'uwa kamar bazan dawo na taddaki ba sai nakejin kamar wani Abu zai shiga tsakaninmu ko wani zai raba mu Wanda bazan tab'a iya jurewa hakan ba" "Cikin tausasa murya Zarah ta ce " ka daina wannan tunanin ya Hafiz babu Wanda ya isa ya shiga tsakaninmu kaid'in ka zamemun wani bangare na jikina kayimun abunda ba kowa yayimun a rayuwa ba ka tsayemun a karatu na ni d'in y'ar halak ce ba butulu ba ya Hafiz bazan tab'a butulce maka ba insha Allahu zaka dawo muyi auranmu ta fad'a ta na rufe fuska" Sai sannan Hafiz ya sauke ajiyar zuciya Tare da sakin rai sunjima suna Hira kafin yayi mata bankwana cike da kewar juna suka rabu " Koda ta koma hostel duk tayi sanyi Samun Chuchu tayi ta na cika ta na batsewa tare da Harararta. "d'an murmushi Zarah tayi ta ce " yau kuma wa ya tab'o mana chuchun yaya" tana cigaba da turo baki ta ce "Ke ce mana momcy" wara idanu tayi ta ce. "Ni kuma to me nayi" Wancen mutumin mana da kika tsaya dashi kwata_kwata ba class d'inki bane yanzu asmy ke Cemun wai dashi aka sanya miki Aure kinji yanda Naji wlh kwata_kwata bakuyi match ba momcy ke Matar manya ce Wlh Harna fara kishi Dan da yaya na kika dace ba wancen bak'in ba....✍🏿 _07026166536_ *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo*_🤙🏿 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 🅿️............*19 & 20* "Bata fuska Zarah tayi Jin shirmen da Chuchu take Dan a shirme ta dauki maganar wata maganar ta kawo musu Dan son barin zancen. Tunda Hafiz ya tafi kullum cikin waya suke da Zarah tare da video call Yau Zarah ta tashi da ciwon ciki hakan ya nuna mata zuwan perioud dintane sosai take murkashi akan Gado Dan su Asmy suna lecture Duk ta had'a zufa a haka har suka dawo suka sameta sosai suka shiga tashin hankali musamman Chuchu da batasan da larurar Zarah ba Dan kwanakin baya ciwon ya d'an lafa. Da damuwa ta ce " subhanallahi me yake damunki momcy"Asmy ce dake mikar da Zarah ta ce perioud dintane yazo mu maza mu kaita Asibiti bari na taro napep " Da mamaki Chuchu ta ce " Daman haka yake yi mata? "Eh haka take Asmy ta fad'a tare da saurin fita Dan ta taro napep inda Chuchu ta shiga Jerawa Zarah Sannu. Asibiti mafi kusa suka nufa Inda Asmy tayiwa Dr d'in bayanin abunda ke damun Zarah allura akayi mata Bayan Bacci ya kwasheta ta na tashi taji da sauki haka suka koma hostel Chuchu dukda tsorata Dan ita duk perioud din da take bata tabajin ciwon ciki ba Saidai taji kasala. Tundaga lokacin abun Zarah ya k'ara worse a halin yanzu har suma ta ke Asibitin da suke zuwa Dr d'in harya ganesu wani zuwa da sukayi ya cewa Asmy . "a Gaskiya ko yarinyar nan ta na samun sauki tofa dole sai wani Abu ya shiga tsakanin ta da wani?wara idanu Asmy tayi ta ce. " What Dr kenan yanzu ba maganin da za a bata"Babu maganin ciwon nan kamar yanda na fad'a hakan ne kawai maganin da zan baku shawara tayi Aure zata daina " "Ajiyar zuciya Asmy ta sauke ta ce " mungode dr"Ranar sun koma hostel Asmy ta kalli Zarah lokacin ta na kurbar tea ta ce. "Sis waikinsan me dr ya ce Ko kina daina ciwon cikin nan sai kiyi Aure sainakejin inama saida akayi aurenki da Hafiz kafin ki fara makaranta Dan wlh ciwon nan naki ya fara bani tsoro da safe fa har suma kikayi" "Cike da damuwa Zarah ta ce " Ni kaina ciwon nan ya na damuna karkiga idan perioud d'ina ya matso irin fad'uwar gaban da nakeji Asmy Aikin gama ya Riga ya gama dole ne nayi hakuri har na k'arasa karatu na Shima ya k'arasa nasa" Tsaye ya ke waya na K'are a kunnansa daga ka gansa ka San ranshi a matuk'ar b'ace yake tashin hankali k'arara a fuskarsa ya ce. "what ka na nufin an sanya an kashe Alh sammani?banji me akace daga d'ayan b'angaren ba saiji nayi cikin Sauri ya ce. " gani nan zuwa k'asar yanzunnan ka sanar da DPO abunda ke faruwa a maza a tari abun da wuri kafin Su gudu a tabbatar an kama su" Ya na Gama fad'ar haka ya katse kiran Tare kiran PA dinsa ya ce a shirya masa tafiyar gaggawa daga Inda yake tare da Escort dinsa suka wuce Aiport ba tare da ya koma ma gida ba yayi wa Amera bankwana Dan Zuwan emergency ne. Kasancewar kwazo da dagewa da kuma ilimin addini ya sanya aka bawa Zarah Amera ta makarantar Sauri take sosai Dan zasuje wata musabaqa ta students din makarantu a Polytechnic Kaduna Sosai tayi kyau cikin Zumbuleliyar Hijab d'inta har k'asa mai hannu maroon" Tare da daura Nik'ab tare da Asmy suka tafi Dan tayi mata rakiya Chuchu ko ta na gida Dan weekend ne kuma yawaici a kd takeyinsa. Kasancewar a motar makaranta suka tafi cikin k'ank'anin lokaci suka isa Inda aka fara gudanar da Musabaqa ko wasu makarantu har akazo kan makarantar su Zarah Inda Zarah ta wakilcesu cikin muryarta mai dad'in sauraro tare da qiri'arta ta fara karatun da aka tambayeta duk Inda aka janyo saita k'arasa batare da gargadaba ba Kuma zallar tajwid take fitarwa Sosai ta burge mutane da dama dake wajen. Motocin Escord dinsa Guda goma suka sanya motar da yake ciki tsakiya shi kadai ne a motar sai driver . sunzo daidai zasu gitta ta poly MD yajiyo karatun muryar da ta kasa barin kwalwarsa cikin Sauri ya cewa "Driver ya tsaya" tsayawar yayi yayinda sauran motocin ma suka tsaya gabaki d'aya ya mayar da hankalinsa ga zazzak'ar muryarta karatun da yake jiyowa har wani lumshe ido yake Sosai muryar ke shiga ta na ratsa duk wani sassa na jikinsa suna nan tsaye ya na sauraronta muryar da tabbas ya San muryar da yaji ce a lokacin da yake waya da Chuchu. sosai yaji ya na son cigaba da sauraron karatun daga mamallakiyar wannan zazzakar muryar saida suka kwashe minti Talatin tsaye kafin ta gama karatun sai sannan MD ya dawo hankalinsa. ji yake kamar ya dawwama cikin sauraron muryar ta Cikin Sauri kuma ya tuno da abunda ya kawosa Umartar driver yayi da yaja su tafi. Zarah ko Bayan ta gama karatu kabbara kawai ake daga karshe dai ita ta ciyo musu na d'aya Wanda hakan yasa makarantar suka kara alfaharin da ita Dan sannan ne karo na farko a Musabakar makarantu state din da aka fara ciwo musu na d'aya Zarah ta samu kyautoci da dama daga wajen manyan da suka halacci wajen. Koda za a koma A motar makaranta kin shiga sukayi Dan suna son su biya gidan su chuchu Dan tun d'azu ta ke kiransu akan d'an Allah Ammy tace suzo Mai napep suka Tara Inda sukayi ciniki da shi akan ya kaisu G R A. Gudu sosai suke shararawa a titi yayinda waya na K'are a kunnansa DPO ne ya ce . "Ranka ya dad'e sun Kufce mana Yanzu haka Suna Hanyar da kake bi karka yarda su tsere zaka gansu a mashin sun rufe fuska su biyu suka rage sauran sun gudu" Cikin masifa MD ya Ce "Aikinme kuke har zaku kasa kama k'ananan y'an iskan da basu da aiki sai kashe jinin y'an uwanmu musulmi bil'adama ". tsaki yaja tare da katse kiran yace driver Kara gudu "Sunzo daidai Wani round about MD ta Cikin glass ya Hango su cikin Sauri ya zage glass din tare da fiddo bindigarsa Ya saitasu ji kake tassss ya harbesu a gefen hannu d'ayanma haka Shi kanshi MD rumtse ido yayi Dan wannan ne karo na farko da ya tab'a harbi a rasuwarsa. Hakan yayi daidai da isowar su Zarah wajen Akan idonsu Harbin ya afku saida basuga mai Harbin ba Sosai suka rude Zarah ta kankame Asmy tare da fasa Kara Dan iya tsawon rayuwarta bata tab'a ganin irin wannan ba Mutane filis a kasa jina jina akan idonsu aka harbesu. Ita kanta saida Asmy ta girgiza karkame juna sukayi tare da karanto duk addu'ar da tazo bakinsu dan basu tabajin anyi harbi a gabansu ba lura da hakan mai napep din ya juyo ya ce "Ku nutsu Wannan abun ba Bak'on Abu bane a Saidai kawai Allah kyauta" Asmy ce tayi k'arfin halin cewa "da gangan fa aka harbesu suna Tafiyarsu Dan zalinci ," girgiza kai napep din yayi ya ce " a Lamarin k'asar nan sai dai addua MD ne a cikin motar kuma ina kallonsa ta cikin glass shi yayi harbin Kunga ko a kudin sa ba abunda aka isa ayi hatta gwamnatin a hannunsu ta ke Saidai hakuri kawai " MD Zarah ta maimaita a cikin zuciyarta lokaci guda taji wata irin matsanancin tsanar mai sunan a rayuwarta ta tsani mutumin da baisan darajar d'an adam ba bazata tab'a mance da sunan ba mutumin da ya tsaidasu a Zaria da zasuje Banki. Sosai taji wata irin tsanarsa dukda bata sansa ba a fuska Amma taji a duniya babu mahalukin da ta tsana sama dashi cikin rud'u ta ce "mai Napep juya damu ka maidamu tashar motar Zaria" Juyasu mai napep din yayi har lokacin Zarah A rude ta ke Har suka isa Tasha Inda suka hau motar Zaria Dan komawa school jikinta bai bar kyarma ba "Ajiyar zuciya ya sauke daga zaunen da yake tare da maida bindigar ma ajinta a take nan motar y'an sanda suka ido DPO da kanshi ya lek'a ta glass tare da sarawa MD ya ce. " da ana samun irinka a cikin k'asar nan da an zauna lafiya Allah ya k'ara tsarewa sannan ya k'ara girma yanzu zamu wuce dasu police station ko asibiti bazamu kaisu ba harsai azaba ta ishesu sun fad'a ogansu dake sanyasu wannan aikin". "Jinjina kai MD yayi tare da cewa " kar ayi Sakaci dasu a matsesu har saisun fad'a ko waye duk bayanin da aka samu a kirayeni " Har suka isa hostel Zarah na kyarma Inda suna isa ta lulluba saboda zazzabin tsorata da ya zubar mata Asmy ta dinga Lallashinta akan karta sanya abun a ranta ya hanata bacci "Zarah na hawaye ta ce " dole na damu Asmy Jinin musulmi fa aka kashe a gaba na Asmy bantabajin tsanar wani d'an adam ba a rayuwata sama da MD d'innan da aka fad'a na tsanesa na tsana jininsa na tsani Wanda ya shafesa saboda duk mutumin da zai iya kashe jinin musulmi ya chancahnci tsana mai muni daga wajena "ta fad'a ta na rumtse ido. Ta na ganin abunda ya faru na dawo mata a cikin kwalwarta. Lumshe ido yayi jikin Ammynsa ya na jin dad'in zama kusa da mahaifiyar tasa Albarka Sosai Ammy ta shiga sanyawa d'an nata a bisa Namijin kokarin da yayi Dan kafin ya Iso ma Har sungani a television live Chuchu ma sosai tayi alfaharin da irin taimakon da yayan nata yake bayarwa ta fannin Yak'i da y'an ta'addan da suka hana k'asarmu zaman lafiya. Ammy ce ta kalli chuchu ta ce " Wai har yanzu su momcyn taki Basu iso ba lafiya". Lalubo wayarta Chuchu tayi cikin damuwa tare da cewa"nima tun d'azu jiransu nake jira Bayan na shirya musu abubuwa ta fad'a ta na kiran Zarah" Asmy ce ta d'auka dan zarah duk ta rikice mata cikin shagwaba Chuchu ta ce "Wai me ya tsaidaku nasanfa tun d'azu aka gama Musabaqa kufa kawai nake jira " cikin sanyi Asmy ta ce "am so sorry sis wlh matsala aka samu wani Abu ne ya firgitar damu yanzu haka muna Zaria Kinga Zarah nan ma bata lafiya zazzabi ke damunta" Cikin tsananin damuwa Chuchu ta ce "Subhanallahi me ya faru ya jikin momcy din " da sauki Haba ai yau munga tashin hankali maganar bata fad'uwa a waya bace saidai kindawo"Cewar Asmy . Sosai Chuchu ta rude "Ammy ce ta ce " Lafiya Kuwa"wlh Ammy wai wani Abu ya rud'ar dasu suka koma yanzu haka momcy ba lafiya bari kawai na wuce school din yanzu hankali na bai nutsu ba " Ta fad'a tare da saurin Rugawa ta sanyo k'atuwar hijab din da suka dinka tare da Zarah tundaga Fitowarta MD ya bita da Kallon mamaki Kasa shiru yayi ya ce . "Ammy yau Chuchu ce da hijab " Dariya Ammy tayi ta ce "Au ashe ban baka labari ba Ai yanzu Chuchu an nutsu kawa tayi Malama Yanzu haka ta tafi hizif arba'in Karin karatu takeyi mata wannan shigar banza da kide kide da raye raye duk ta dainasu " "wow but Gaskiya Naji dadi ko wacece wannan Malamar ta chanchanci tukuci daga gareni". Cikin farinciki Chuchu ta ce "Wlh yaya danma baka ganta ba ta had'u Ga kyau Ga addini ga Ilimi itace amera d'in school d'inmu yanzu haka musabak'a ce sukazo ita ta wakilce y'an makarantarmu zancen da nake maka Yanzu haka ita ta ciyo musu na daya barima ka gani sunna sun dora Yanzunnan ta fad'a ta na kamo sunna daidai Inda Zarah ke karatu sanye cikin niqab ". Maida hankalinshi MD yayi ga television d'in sosai gabansa ya tsananta fad'uwa jin muryar da yajiyo dazu d'ince gabaki d'aya hankalinsa ya maida ga sauraron daddad'an karatun da baitab'a sauraron karatun da ya bashi nutsuwa da annashuwa irinsa ba Sannan ya kafa mata idany Sanye take cikin Zumbuleliyar hijab fuskarta ba abunda kake gani hatta kwayar idanunta wannan Karin a rufe suke cikin nikab nauyayyar Ajiyar zuciya ya sauke tare da Kallon Chuchu ya ce . " ko ita ce muryar da najiwo Daga gefenki kwanaki"Cikin murna Chuchu ta ce "Eh itace yaya Zarah kenan kawata ce sunan ammy gareta yaya Ai saima ka ganta ido da ido nasan saita tafi da imaninka ta had'u sosai yayana ka ganta saika rude Dan da kai tayi match tafi Aunty Amera komai" Wani banzan kallo ya watsa na kin rainamun wayau tare da janyo kunnanta ya murde da karfi ya ce......✍🏿 *hmmm muje zuwa Fans ba a fara komai ba yanzu salon wasan zai fara Kudai kawai Karku gaji da comment sharhi tare da sharing akwai daddadar tafiya nan gaba* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* _*TEAM GAWURTATTU BIYAR*_💃 *SHAFIN NAN NA SADAUKAR DASHI GA DAUKAKIN MASOYA A DUK INDA SUKE NAJI DADI KWARAI DA YANDA KUKE NUNAWA LITTATAFAINA SOYAYYA KUSANI NIMA INAYIMUKU SON FISABILILLAHI MASOYAN ASALI WANNAN PAGE DIN NAKU NE KYAUTA*😝 🅿️............*21 & 22* "Ina wasa dake Chuchu ni kike fad'awa haka na k'arajin maganar nan bakinki zan zaneki" D'an Kara Ta saki tare da cewa "Auch sorry Babban yaya bazan sake ba" Kafin ya sakar mata kunnen ya ce . "Bazaki koma ba Yau sai jibi week end ya k'are badan Chuchu ba taso ta zauna Dan bazata musawa Yayan nata ba Amma gabak'i d'aya hankalinta ya tafi wajensu Zarah. suna nan zaune a palour suna y'ar tab'a Hira Har aka k'are nuno Musabakar A television Knoking da suka jiyone ya sanya Chuchu saurin Mikewa tare da zuwa ta bude. Wani wawan tsalle ta daka ganin Hajiya kaka tare da su Adil da Ruky " dakyal ta Bari suka karaso palourn saboda d'oki MD ko gabanshi ne ya fad'i ganin zuwan Hajiya kaka gidan yasan shikenan yanzu kuma zata addabeshi akan Maganar k'ara Aure. Sosai Ammy tayi murnar ganinsu nan ta shiga musu lale marhaban Bayan sun gaisa an cika musu gabansu da abubuwan makuleshe Chuchu suna mak'ale ita da Ruky da bazata wuce sa anninta ba suna Hirar yaushe gamo. MD ne ya kalli Hajiya fuska ba walwala ya ce "Sannu da zuwa Hajiya anzo lafiya". tab'e baki tayi tare da k'are masa kallo ta ce "Lafiya salamamme ina ita gimbiyar taka ko har yanzu bata haihu ba " "Ya na had'e fuska ya ce " Daga zuwanki ba ko gaisawar kirki Hajiya " "eh ba gaisuwar ai wannan zuwan da kaga nayi zuwan Kane na kashin kanka tunda ita Fatima ta kasa tab'uka komai ta na tsoranka karka tsireta to ni bazanji tsoronka ba idan kaga na bar nan garin nan tofa sai naga haihuwar shegiyar yarinyar nan idan ba haka ba Da Rukayya zan hadaka Auren zumunci sai Inga ta tsiya. " Ba MD ba hatta ruky saida ta d'ago jin maganar Hajiya kasa tayi da kanta Dan Ita kanta tasan karya take tace batason MD amma kuma tasan MD bazai tab'a sonta ba yafi karfinta kuma ma ita tana da Wanda takeso " "Shiko gogan Mikewa yayi ba tare da ya nuna Alamun damuwa a fuskarsa ba ya haye stairs da Kallo Hajiya ta bishi ta na Jan tsaki" Chuchu ko Dariya tayi kasa kasa tare da tsunkunin Ruky ta ce "Kaji amarya a gidan yaya MD" . harara ta maka mata Arif ko Tunda ya shigo ya ke kallon sahibar ta sa Chuchu ta message yayi mata magana da su kebe Dagowa tayi suka hada ido tare da sakarwa juna murmushi Ya Mike ya fita Ta na ganin haka itama ta bisa "tab'e baki Hajiya tayi ta ce. " kuma Kunzo ku fad'amun abunda ke tsakaninku Dan na gaji duk Aurar da ku zanyi yara sun girma sun bunkasa a gida Suna gogayya da iyayensu"cewar Hajiya ta na Jan tsaki Ammy dai murmushi kawai take. Washegari asubanci MD yayi yabar garin daga shi sai Jabir kamar koda yaushe tafiyar sirri sukayi har suka isa garin gombe. Daga gombe ma nayi mamaki irin dajin da suka Yanka kafin Su isa wani k'aramun kauye karshen kauyen naga tafkeken gida flat da ya tsaru Inda suka kutsa motarsu cikin gidan Zaune yake gaban wani dattijon mutum Wanda bazai haura shekaru 65 ba ko fi a kwance ya ke yayinda idanunsa suke a bud'e Babu abunda yake motsi a cikin jikinsa sai y'ar yatsarsa Gadon da yake MD ya hau tare da kamo hannun dattijon ya rike gam gam ya na murzawa Shima shi yake kallon dattijon ba abunda yake sakar masa sai Murmushi ". Muryarshi na rawa Alamun damuwa k'arara a fuskarsa ya ce" Allah ya baka lafiya Insha Allahu Inajin a jikina wahalar nan taka ta kusa zuwa karshe da izinin ubangiji " "Lumshe ido yayi tare da budesu Alamun yaji dadin abunda ya fada " wani Dattijon ne ya shigo Shima da bazai wuce sa'annin na kwancen ba . "Kallonshi MD yayi ya ce " Sannu Baba A Gaskiya ba abunda zance da ku sai Godiya Allah ya saka da alkhairi jikin nashi na ga ya fara sauki masha Allah". Da Fara a tsohon ya ce "muke da Godiya a wajenka ranka ya dad'e kai ka gama yi mana komai Allah dai ya basa lfy yanzu kam ana samun cigaba sosai Dan jiya har hannunshi saida ya motsa " "Nauyayyar Ajiyar zuciya MD ya sauke ya ce " Baba inason a ninka akan saukar da ake masa Ya tashi daga duk sati ya koma duk kwana biyu "sannan ya mik'a masa mak'udan kudi ya ce " gashi a k'ara rabawa malamai da kuma makarantu a ninka sadakokin da ake ". *** Tsaye yake sai safa da marwa yake waya na K'are a kunnashi cikin tsananin tashin hankali ya ke cewa " garinya har aka bari aka kama su baushe Aiko muddin suna hannun hukuma akwai babbar matsala sannan shi MD din zanyi maganinsa ina zuwa karka damu bazasu tab'a Tuna Wanda ya sanyasu aikinba ko za a kashesu". Ya na Gama wayar cikin Sauri ya bar gidan tare da wucewa wajen tsafinsu Dan a rufewa su baushe baki. Da dare aka kirasa akace aiki ya gama ranka ya dad'e sunkasa fad'a "Dariyar mugunta ya kwashe da ita ya ce " suna wasa dani basu San waye Alhaji mudan ba manya ma mun gagara baresu kanana kanana sannan shi MD zaisan ya shiga gonata ubanshi ma na gama dashi bare shi darajar soyayyar da y'ata kawai take masa yake ci nasan muddin na kashesa zata shiga mugun hali wanda bazan juri hakan ba saboda soyayyar da nakeyiwa Amera y'a daya tilo amma badan haka ba Da na jima da shafe Tarihinsa a cikin rayuwa k'aramun kwari"ya k'arasa fad'a ya na kecewa da wata dariyar irin ta su ta mugaye. Ran Monday Chuchu ta koma school koda ta je a lokacin Zarah taji sauk'i da damuwa ta ce " wlh hankali na duk a tashe yake me ya ke faruwa? "Haba daughter Ai zuwanmu kadunar nan munga tashin hankali nan suka bata labarin abunda suka gani sannan Zarah ta d'ora da cewa . " wlh Chuchu bantaba Jin tsanar wani mahaluki ba sama da MD d'innan na tsanesa na tsani duk Wanda ya shafesa zubar da jinin mumuni guda d'aya wasane Chuchu yaza ayi k'asarmu ta zauna lafiya ana zubar da jinin musulmai a gabanmufa mugun mutumin nan ya harbe bayin Allah suna Tafiyarsu basuji ba basu gani ba " .rumtse idonta Chuchu tayi Jin Yanda Zarah ke aibanta Yayan nata mafi soyuwa a gareta Cike da damuwa ta ce "Amma bai kamata ace kin yanke hukunci batare da kin bincika ba kika sani ko masu laifi ne " Wani banzan kallo Zarah ta watsa mata tare da cewa "Ai daman haka za ace tunda Mai kud'ine komai yayi daidaine Ta haka aka karesa kenan to ai idan duniya ta karesa zaiyi bayani a lahira mugu azzalumi macuci makashin mutane ko kema kina goyon bayansa ne" Kara rumtse idonta Chuchu tayi Jin bazata iya d'aukar wannan mugayen kalaman ga yayantaba ya sanya ta tashi tashi tare da komawa gadonta ta kwanta tare da rumtse ido Tanajin zafin maganganun da Zara ke yi akan Yayan nata . Tabbas inko hakane dole ta boyewa Zarah cewar ita kanwar MD ce Dan yanda taga tsanarsa k'arara a idonta tasan Kanwarsa ce Zata iya rabuwa da ita Wanda bazata juri hakan ba Dan a tarenta da Zarah ta koyi abubuwa da dama na karuwa A halin yanzu su Zara sun gama Exams Inda sukayi hutun second semester da sun dawo level3 zasu shiga. Koda ta koma gida a kofar gida ta tarar da Baba cikin farinciki ta je ta gaishe da mahaifin nata ya amsa mata ya na sanya mata Albarka sun tab'a Hira sosai ta y’a da uba kafin ta wuce cikin gidan Ta na shiga khairat ta rugo da gudu tare da Rungume ta ta ce "oyoyoy Aunty Zarah Sannu da zuwa" itama Rungume y'ar uwar tata tayi ta ce "Sannu my khairat ykk ya makarantar kina dai zuwa ko" gyada mata kai tayi tare da Amsar akwatinta ta shigar mata dashi ciki. Mama rabi ce ta lek'o daga daki jiyo Zarah da tayi da Fara a Zarah ta ce "Mama ina yini" tsaki taja tare da cewa "da baki ganni lfy ba andawo daga yawon katuwancin ko Har wani kiba da kyau aka k'ara hmm muna nan dai muna jiran kishin dan abun nan ba banza ba akwai lauje cikin nad'i". Girgiza kai kawai Zarah tayi Dan tasaba da kalaman nan ta na shiga daki Nan ta fitowa da khairat tsarabarta Godiya tayi mata jin bataji Safiya ba a gidan ya sanyata cewa " waini ina Safiya tunda na shigo banjitaba"tab'e baki khairat tayi ta ce . "Baba ya maida ita Batsari gidan Bappa samari ke zuwa Wajenta har a soro suke zance rannan Baba ya kamata wani na rungumarta ranar Tasha Duka a ranar ya kaita Batsari ya barota ya ce bazata k'ara dawowa garin nan ba ". Ajiyar zuciya Zarah ta sauke ta ce " Allah ya kyauta kedai Dan Allah khairat ki nutsu karki Shiga rayuwar nan marar kyau"murmushi tayi ta ce "Insha Allahu Aunty itama safiyar ai su Aunty Habiba ta ke biyawa" Bayan ta huta Corn flask ta jika tare da madara ta sha ta kwanta ba b'ata lokaci baccin gajiya ya kwasheta saboda akwai tsananin gajiya tattare da ita. Duka zazzaune suke a palourn hajiya,Ammy ,Adil,Chuchu,sai Ruky MD dake Danna waya Hajiya ta Kalla ta ce. "Wannan karin maganar da nazo da ita ba wasa Mustapha wlh wlh kaji na rantse shekara guda na baka idan Matar ka bata haihu ba ko bata samu ciki ba ko a kauye ne sai na nemo maka mata na aura maka ko ka fito mun da wacce kakeso amma Bazan juri cigaba da ganin wannan kayan takaicin ba Mace d'aya ta zauna ta na Juyaka macen ma ba y'ar arziki ba to wlh baka isa ba ni ba tsohuwar banza ba ce Na baka shekara guda idan ba haka ba zakaga irin hukuncin da zan yanke maka salamamme a haka kamar zai tab'uka abun kirki a ido kamar mai jarumta nanko solo ne fanko kawai Me Auren ya amfaneka dashi aikin banza aikin hofi " MD cikin tashin hankali ya ce "Haba Hajiya wai meyasa kike haka Haihuwa fa ta Allah ce Sannan Shekara guda fa Haba hajiya ke da kinzo saikin tayarmun da hankali" Ammy ce ta ce "karna karajin bakinka babana ba kaiba ko ni Hajiya ta na ikon yanke hukunci akaina Dan haka abunda ta fad'a Gaskiya ne ko ni kaina Dan ba yanda zanyi ne na kyaleka Dan haka karna karajin bakinka shekara guda aka baka ba wata guda ba duk wani adalcin da zamuyi munyi maka amma baka gani ba Dan haka Ina Bayan hukuncin da Hajiya ta yanke" Amma Ammy.."yimun shiru karka sake magana"Kallon Ammy kawai MD yake Dan Gaskiya hukuncin nan yayi masa tsauri ta ya ma za ace wai nanda shekara idan Amera ba ta haihu ba zaiyi Aure shi har akwaima macen da ta isa ya so ta har ya aure ta Bayan Amira ga kuma tashin hankalinshi na halin da Amira zata shiga ta samu labarin nan Dan ba abunda ya tsana sama da b'acin ran amirar sa ". Chuchu ko hukuncin nan yayi mata dadi hamdala ta sauke cikin d'oki ta ce " yo Hajiya wlh danma bakisani ba Aunty Amera fa Bata tab'a girki ba a gidan yaya Saidai su suyo abincin restaurant ga bata da aiki sai waya da Abokai da yawo kasash.....kasa k'arasa maganar tayi sakamakon tsawar da ya daka mata cikin tsananin Zafin rai ya ce "get out kafin na tattakaki ni sa ankine Ana magana ta kina sa baki Dan baki da tarbiya" Cikin Sauri Chuchu ta mik'e tare da saurin barin d'akin Dan ta tsorata da yanda Yayan nata yayi mata "ohh dan ta fada gaskiya shine zakayi mata tsawa to Komai dai me zakayi Saidai kayi amma hukuncin da na yanke banga ubanda ya isa ya take sa ba mu zuba mu gani mu da kai d'an halak ka fasa shege sai yanka sototon wofi salamamme bawan mace"......✍🏿 *07026166536 hanya a bud'e take domin neman Karin bayani sharhi ko tambaya* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* *_TEAM GAWURTATTU BIYAR_*💃 🅿️............*23 & 24* Sosai Hajiya ta shiga f'ada Inda ta shiga ba tanan take fita ba Ganin haka ya sanya MD barin palour ya ma bar gidan gabak'i d'aya ya koma gidansa. Tunda yaje ba tunanin da ya ke sai maganganun Hajiya baijin zaiyi abunda Hajiya take so Amma kuma Tabbas yasan.muddin Amira bata haihu ba da gaske Hajiya Aure zatayi masa Dan ta isa da su hatta mahaifinsu da yana raye ita ke ikonshi bare shi sosai ya shiga kogin tunani sai Jan tsaki ya ke ya Ma rasa mafutar da zai samu. Jabir ne ya fad'o masa a rai Dan ba abunda ya ke boyewa aminin nasa tun pri sch ya na Danna masa kira ya ce ya na buk'atar ganinsa ya ce gasanan. Minti ashirin mai kyau jabir ya Iso cike da damuwa ya kalli abokin nasa ya ce. "Yadai Bloody akwai matsala ne naganka haka?" Numfashi MD yaja ya ce. "babba ma kuwa Jaber old woman d'in chan Ce tazo wai dole ta bani nan da shekara idan Amera bata samu ciki ba ko bata haihu ba Aure zatayimun sai kace wani yaro" ya k'arasa fad'a ya na Jan tsaki. Danne dariyarsa jaber yayi Dan kar asamu matsala a ranshi ya ce "Alhamdulilla anzo wajen" A fili kuwa cewa yayi. "to meye matsalar a ciki kawai kabi umarninta ka k'ara Auren kawai" wani banzan kallo ya watsa masa tare da cewa. "Baka da hankali Jabir Ni kakeyiwa maganar Karin Aure bani da tsarin Aje mata biyu sannan bazan iya hada Amera da wata ba kamar na yaudareta ne ka tuna irin soyayyar da takemun tun kafin muyi Aure tun a makaranta kai kanka sheda ne a USA wace irin soyayya ce bamuyi ba da Amera ta soni kamar ranta ita ta fara sona Tun bana sonta har nazo na fara sonta dukda mahaifinta ya nuna baya ta ayina lokacin haka ta nace har mukayi Aure Shine kake cewa nayi mata kishiya Dan ina butulu" "Tsaki Jabir yaja a Ransa a fili kuwa cewa yayi " ai babu butulci a maganar Aure da Allah ne halasta ka na da ikon auren ukku nan gaba a bayanta Sannan ko kayiwa Amera kishiya ita ta ja saboda ba wani hakkin Aure da ta ke saukewa sunan ta na sonka da kishin Kane amma da kaii da gwauro banbancin baida yawa" Tsaki MD ya ja ya kirashi Dan ya bashi shawara ya ma Kara chusa masa wata damuwar ya ce 'shikenan kawai bana buk'atar shawarar taka kaima nema kake ka kara samun damuwa"ya fada ya na kauda kai gefe. Kwantar da murya jaber yayi ya ce "Shikenan bloody yanzu maganar wannan ta wuce wace mafita kake tunanin zamu yanke" ai dalilin da ya sanya na kiraka neman mafutar nake"Ajiyar zuciya jaber ya sauke ya ce "Karka damu kafin nan da 1week zanyi tunani da nazarin nema maka mafitar da ta dace" Bayan sun gama zancen nan ne Jabir ya shiga yi masa hirar case d'in kisan Alh sammani Inda ya ke dora masa da cewa "har yanzu dai mutanen sunki fad'ar Wanda ya tura su suyi aikin harma an yanke musu hukuncin kisa ta hanyar harbi tunda sun amsa su sukayi kisan" Cikin jin dad'i md ya ce "Amma Naji dadi hukuncin da gwamnati ta yanke da ana musu irin haka da za a samu sassaucin ta'addancin nan to Dan sunsan Inma an kaisu gidan yarin guduwa suke ko kuma ma a fito dasu shiyasa suke cigaba da yanda suka ga dama a k'asar nan Dukda dai naso ace sun fad'a Wanda ya sanyasu Dan akwai Wanda nake zargi Allah dai ya k'ara zaunar da k'asarmu lafiya yayi mana maganinsu " ameeen Jabir ya amsa" Bayan barin Jaber gidan kwance yayi saman bed dinsa ya na jin murdawar da mararsa ke masa matsananciyar sha'awa na taso masa Dukda sanyin AC amma zufa yake rumtse ido yake ya na ciccije baki Dan ta fagen nan bashi da jarumta Sai mammatse kafafunsa ya ke saboda azabar felling ranar haka ya kwana sai Bayan asuba ya samu baccin wahala ya kwashesa. Ta bangaren Zarah ma yau tun yamma takejin felling na taso mata tunda taga wani saurayi da budurwa Bayan hostel d'insu suna tsotse_tsotse suka tayar mata da matsananciyar sha'awa dukda kallo daya tayi musu ta kauda kai. Kwance tayi a Gado ta na rurrumtse ido Ta rik'e mararta da ke fara juya mata "Asmy na ganin haka tasan Inda ciwon. ya dosa Chuchu da ke chatting da damuwa ta ce. " Subhanalla momcy lafiyanki qalau"Cikin k'arfin hali Zarah ta ce "am okay daughter zansamu relief" Sannu Asmy tayi mata dube duben maganin baccin ta fara nema taga basu taho dashi ba dafe goshi ta yi tare da saurin sanya hijab ta dauki dubu d'aya Dan taje ta sayo mata maganin Zarah mammatse kafafu kawai take Wanda hakan har ya bawa Chuchu mamaki saita tuno wani lokaci haka Yayan nata yake Dan tun bata gane matsalarsa ba Har ta gane kasancewar itace yawaicin mai hada masa tea da lemon tsami gadon da Zarah ta ke ta koma Tare da kama hannunta ta ce. " sorry momcy ko na hada maki tea da lemon tsami zakiji reliep .girgiza mata kai tayi batare da tayi magana ba ta na nan zaune gefenta ta na mata Sannu har Asmy ta dawo kallonta sukayi da take Jan tsaki Chuchu ta ce "kinsamu maganin?tsaki taja tare da cewa. " inaga wai duk chemist din da naje sai suce gwamnati ta hana sayar wa wai saboda masu sha Dan maye " "da mamaki Chuchu ta ce " wai daman maganin tari ne zaki sayo mata?Eh mana shi kadai ne ake samu har bacci ya d'auke ta idan ba haka ba haka zata yini tunda ba mai d'auke mata Kewa gareta ba" "Mai zai hana a bata ruwan tea da lemon tsami idan yaya na ya na haka shi yake sha" Cewar Chuchu girgiza kai Asmy tayi ta ce "maza yake yiwa amfani banda mace daman Dr ya bada shawarar bata maganin kuma Kinga an Rasa" ta fad'a da damuwa. Cike da tausayi Chuchu ta ce 'wayyo sorry momcy to me zai hana ta d'an yi wasa da gabanta ko ta samu relief" "Kallonta Asmy tayi ta ce "Ko hakan kikeyi Zarah tunda Kinga a bisa larura ne" dukda azabar da Zarah takeji bai hana ta girgiza kai ba ta ce "Karku damu zan samu sauk'i ba sainayi wannan ba sanin kanku ne ba kyau" Sosai cuchu ta k'ara jinjina addini da tarbiya irin ta Zarah Dan a yanda take da feeling ba kowace mace bace zata samu kanta. A haka ba bata fad'a halaka ba. Ranar sai bacci barawo ne cikin dare ya kwashi Zarah koda su Asmy suka tashi suka tashi Sallar asuba kin tashinta sukayi saboda ta huta bata samu bacci ba sai wajen 8 ta tashi garas Sannu sukayi mata ta amsa da murmushi ta ce "kunjiku fa kamar wata mai ciwo sannan ta duba agogo ta ce " ya Allah shine kukaki tadani nayi sallah"Chuchu ce ta ce "Ai munga bakiyi bacci ba shiyasa" dukda haka din ai da kuntadani ta fad'a tana Mikewa Dan zuwa ta dauro alwala. Yau koda ya tashi duk rai ba dadi Bayan ya shirya kamar ko yaushe a palour ya hakimce tare da kwanciya kan sopa lumshe idonshi yayi ba abunda ke fad'o masa a rai sai muryarta lokacin da take karatu har wani lumshe ido ya ke shi kanshi ya rasa dalilin da yasa muryar ta kasa barin kwalwarsa saurin barin wannan tunanin yayi a ranshi tare da Jan tsaki wayarsa ce tayi ringing dubawa yayi ya ga Amera ce tsaki ya ja tare da Aje wayar ta karashi ringing d'inta harta gama. Kira ta shiga yimai sosai har 5 missed call bai daga ba Jin shigowar message ya sanyashi Jan tsaki tare da d'aukar wayar ba tare da ya duba message d'inba ya Danna mata kira ringing d'aya yaji ta d'auka. Sautin kukanta ya fara jiyowa ta cikin waya tare da cewa "Haba honey tun shekaranjiya nake kiranka kak'i dagawa Nifa ya kamata ace ma nayi fushi ka taho batare da kayimun bankwana ba Amma kai kake fushi me nayi maka baby ko ka daina so na ne" "Cikin sigar lallashi ya ce " Kiyi shiru kinsan banason kukanki yanzu dai ya wuce ykk" yanajin daga bangaren ta ta sauke ajiyar zuciya ita har mamaki take yanda MD bai iya bada hakuri ta ce "am okay dear please yaushe zaka dawo kewarka duk ta isheni" "Lumshe ido yayi tare da budesu ya ce " ba rana sai nagama muhimmin aikin da ya kawoni" .Kamar mai shirin yi kuka ta ce "Haba honey wani aiki ne da bazaka k'arasa yinshi ba a nan please kasan banason zamanka a Nigeria ina kishin yanda y'an iskan karuwan matan nan ke kallonka please my husband ka dawo" "Cike da kosawa da magana ya ce" bana magana biyu Amera Kitaho kawai ki sameni idanma Kaduna ce bakya son zama saimu koma Abuja finally magana ta k'arshe" "Cike da takaici Amira ta ce " Bazan dawo Nigeria ba Honey duk Randa ka dawo ina nan ina jiranka amma Bazan dawo k'asar da za a dameni a Takuramun ba" "Tsaki MD ya ja Dan duk ta k'ara masa Haushi tsaki yaja tare da katse kiran yayi Wulli da wayar Dan itama duk ta gama chaza masa kai a ce ya na da mata amma bata biya masa buk'ata ai gaskiyar su ammy ne da suke cewa da shi da gauro ba banbanci. Saboda Hajiya kaka ya dagawa gidansu Dan kullum ya je zance d'aya ne Fada kullum hakan yasa yayi zamansa a gidansa ya na hutawarsa Dan Yawaicin rayuwarsa hutunsa kadanne idan ba Kaduna ba yazo duk Inda yaje harkar kasuwanci bata barinsa sakat. Kamar yanda jaber ya fad'a a one week din ya zo a lambun gidan suka zauna suna kurbar drink " Aje lemon dake hannunsa MD yayi ya ce "Ina sauraranka bloody wace shawarace ka ce kazo da ita". Ya na fuskartansa jaber ya ce " Shawara ce Na yanke wacce nake tunanin ita ce mafita a gareka mafi sauki shine kayi *Auren wata Tara* ?da mamaki MD ya ce "What *Auren wata Tara* kuma Kamar ya ban fahimce ka ba ka kullemun kai ina gudun Karin Auren shine zakazomun da maganar da na guda" "Murmushi Jabeer yayi tare da cewa of course wannan ita ce kad'ai damar da na hasaso maka zata zame maka mafita" "Har yanzu ka sanyani a duhu fa kayi mun bayani me Kake nufi da inyi *Auren wata tara"* Gyara zama jaber yayi tare da cewa yanzu zanyi maka bayani kuma nasan zaka fahimta "sannna ya d'ora da cewa.......✍🏿 *07026166536 domin magana da marubuciyar* *hmm yanzu fa salon wasan zai fara fans Kudai muje zuwa* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 🅿️............*25 & 26* "Aure zakayi a sirri batare da sanin Iyayenka ko wani naka ba ka Aje Matar a sirrance har kayi mata ciki Kaikuma saikayi musu albishir da Amera ta samu ciki tunda ka ga ta na chan America ita kuma Matar zakuyi yarjeniya da ita ne akan Zaka aure ta na Wata Tara zata Haifa maka d'a ko y'a saika saketa sannan zaka biyata mak'udan kudi amma fa dole Saidai a samu y'ar talakawa nakasassu wacce basu da cin yau basu na gobe a rudata da kudi" "Wani irin kallo MD ya dinga binsa dashi na baka da hankali kafin ya ce " "amma bantaba sanin jaber baka da hankali ba sai yau wannan ai ba mafita bace maganar shirmece kazomun da ita Sannan ni kakeyiwa ikirarin da Auren y'ar talakawa neman haihuwa hauka ne wannan shawarar batayi ba nema ma kake duk ka b'atamun rai" "Dage kafada jaber yayi ya ce " tunda hakan baiyi maka ba Ai shikenan amma kayi tunani wannan ce kawai mafita mafi sauki" ya na gama fad'ar haka ya Mike ya ce "na Wuce Abuja akwai meeting din da zamuyi da wasu y'an kasuwa zan wakilceka Dan kwana biyun nan ka zama wani gashinan dai" "MD ko tsaki ya ja ya na jin haushin wannan banzar shawarar da jaber ya kawo abun ma ya zama hauka ya fad'a ya na Jan tsaki" Mikewa yayi kamar wani zaki tare da fitowa excort dinsa na ganinsa sukayi saurin bin bayansa tare da bude masa mota kai tsaye gidansu ya nufa. A palour ya tarar da Hajiya ta mik'e kafa ruky na gefenta ta na chat ta na ganinsa ta tashi tare da cewa "Ina yini Yaya MD " ba tare da ya Kalleta ba ya ce "Lafiya" fuskarsa a hade ya gaishe da Hajiya ta amsa da fara'a "Ammy ce ta shigo itama gaisheta yayi Bayan ta amsa ta zauna ta na Duba news a jarida. Yayi minti Talatin ba tare da ya ce uffan ba Hajiya ce ta lura da akwai magana a bakinsa cewa ta yi " Yadai Naga kamar akwai magana a bakinka ka fad'a ta cikinka mana Malam " "Cikin hade rai ya ce " daman akan maganar nan ce da mukayi Hajiya please ki janye shekara guda yayi yawa sannan fa haihuwa ta Allah ce Insha Allahu muna addua kuma kuka tayamu da addua za a dace" "Wani banzan kallo Hajiya ta bisa dashi kafin ta ce. " ka gama na ce Ka gama sanin Allah ne zaka gwadamun to tun kafin a haifi uwarka da ubanka nasan wannan nasan haihuwa ta Allah ce kajini da kyau da kunnan basira bari kaji dai nayi maka ta Mahaukacin kare " "wallahi tallahi billahillazilla'ila ha illa huwa Matarka ta shekara bata haihu ba ko bata samu ciki ba Ko a kauye ne saina samo mata na aura maka ," "Ka ganni nan ni ba tsohuwar banza bace bana magana biyu kuma ka zuba ido ka gani badai ka na tsorantaba ta salamceka ba bazaka iya mata kishiya ba To ni nan da kaina zan Aura maka duk wacce tamun kuma dole ka zauna da ita ko ubanka da ya ke raye na sanya yayi Abu dole yayi bare kai k'aramun kwari ni wuce kaban wuri kayan takaici kawai shine hada wani daure fuska to a ganinka tsoranka zanji kome ko nima fatimar ce da kake zare mata ido ta kasa maka magana," " to ni ba ita bace wani had'e ranka na banza Sololon hofi ,gadara da iko da isa sai a waje a gida kuwa Tsigaggiyar matar da a tsaye kamar iccen kabari ta na Juyaka ita bama macen kirki ba ba wani kyau na azo a gani ba ba diri ba ba komai ba Abu k'ashi duk a waje Ko ina ma jin dad'i a wannan abar Har Kake like mata malam ga mata Duma Duma a gari sai ka zaba ka darje amma ka tsaya kana shashanci to wlh ka fita ido na in rufe Dan idan bakayi wasa ba idan bansa ka saketa ba kace ban haihu cikin Uwata da uba na da ruwan zamzam aka haifeni bada jini ba" Tunda Hajiya ta fara maganar MD ya cika yayi famm ga haushinshi na kushe masa mata da take Hade rai yayi sosai tare da kauda kai " Ammy ko shiru tayi sai d'an murmushi da tayi Dan gwara da Allah ya kawo Hajiya ko zata gyarawa MD zama " Mikewa yayi ba tare da ya k'ara kallon ko d'aya daga cikinsu ba ya fita Ya na Jan tsaki. "Da harara Hajiya ta bisa ta na tab'a hannu ta ce " ohh ni Rukayya kujibi dai don Allah a haka a ido kamar zai tab'uka abun kirki nanko ba asan Solon Soson wanka bane dani kake zancen aini ba tsohuwar banza ba ce da zan zuba ido ina ganin tabaranci shekara Tara ana Abu d'aya to Abu yazo karshe na gaji kuma munsanya k'afar wando d'aya daku. MD koda ya koma gidansa ba abunda yake ja sai tsaki tsohuwar nan kwata kwata zuwanta ya rikita masa lissafi gashi ba abun ya koma America ba Ta aiwatar da abunda takeso Dan yasan halin Hajiya sarai bata magana biyu sannan kome ta fad'a saita aikata sa Tsaki ya kumaja tunowa da wai zata aura masa y'ar kauye a ransa ya ce . "dako kinyi babbar nadama dagake har y'ar kauyen sannan ya kumajan tsaki ya na ganin kiran Amera itama duk haushinta yakeji bai d'auka ba saima kashe wayarsa da yayi Dan baya son damuwa tayi masa yawa". Waya ce k'are a kunnanta ta na Waya da Hafiz Bayan fitowarsu daga lectures cewa ta yi " ya Hafiz ka bari na isa hostel sai muyi magana" "Okay ya fad'a daga bangarenshi tare da cewa " ki kulamun da kanki" Saida suka fara biyawa capteria ita da Yusuf sukaci abinci tukwana ta wuce hostel d'insu shima. Ya wuce nashi. "ta na isa ganin su Asmy na lecture Gado ta mimmike tare da yi mishi flashing ya na kira nan suka shiga hira mai dadi Sosai hirar ke yiwa Zarah dadi a haka su Chuchu sukazo suka sameta Asmy ta ce " Uhm manya y'an love kenan' "Chuchu ko taja tsaki ta ce "Uhm Nifa na tsani wannan Hafiz din wlh momcy da yayana kika dace badashi ba please Ki auri yaya na" "Saurin katse kiran Zarah tayi ta na Dariya Dan karyaji abunda Chuchu ta ce ta ce " "kinganki daughter ki barni da ya Hafiz Dina ni yayimun ni wannan Yayan naki da kike kodasa har yau kinki ki nuna mana shi" Turo baki Chuchu tayi ta ce "Wlh da gaske karkiga yaya na ya had'u y'an mata da yawa ridinsa suke ya had'u ta ko ina gashi halinki d'aya dashi Shima miskili ne na Bugawa a jarida wlh kunyi match ta ko ina Shima ya na da irin larurarki Kinga Abu yazo daidai kenan" "Tab'e baki Zarah tayi ta ce " please ki daina had'ani dashi tunda dai ni yanzu na kama ya hafiz dina daurin aure kawai ya rage Ki hada sa da Asmy ta fad'a ta na Dariya " Dariya Chuchu tayi ta ce "Ai kece halinku yazo d'aya Kinga Ko dake yafi dacewa sannan ya Hafiz din da kike magana Ai ba daura Aure akayi ba sa Aure ba Aure bane kika sani ma ko ke rabon Yayan nawa ce" Nanndai sukaci gaba da Gardandaminsu suna Dariya Asmy ce ta ce "nikam zanso naga wannan yayan da ake fad'a sannan baki fad'a mana sunansa ba ? Gaban Chuchu ne ya fad'i tunowa da MD din da Zarah ta tsana Wani tunani yazo mata Ai basusan sunansa na Gaskiya ba hakan ya sanyata cewa. " sunansa yaya Mustapha"Nice name Asmy ta fad'a Zarah ko bama ta saurari sunanba Inda Chuchu tayi saurin barin zancen Dan kar suce ta nuna musu hotonshi dukda basu sanshi ba wata rana zasu iya cin karo da hoton a wani wajen ko media kuma Su gane ita Kanwarsa ce. Daga ranar nan MD bai Kara zuwa gidansu ba Dan Ya ce Sai Hajiya ta tafi saida ya kira Ammy kullum ya gaishe ta. Amera ma suna y'ar waya akai akai kewarta bata wani damesa ba Dan Inda sabo sun saba Suna ma aurata amma wani time d'in saisuyi wata hud'u basu hadu ba ita ala dole batason zuwa 9ja Wanda shikuma bazai juri hakan ba Dan family dinsa sun fiye masa komai a rayuwa . sannan wani karinma in ta tafiyarta yawo kashashe sai anganta shi kanshi wani Karin mamaki yake shin wani irin zaman aurene suke da Amira? Kowa haka yake da matarsa daman(nikam na ce MD ka tambayeni😆) Kira ne ya shigo wayarsa dubawa yayi ya ga Chuchu d'auka yayi Inda yaji sautin muryarta cikin shagwaba ta ce "I really miss you yaya please yaushe zaka kawo mani ziyara nayi missing naka sosai " numfashi yaja kamar bazai magana ba saikuma ya Ce . "ke meyasa bazaki zo duka ina Kaduna ina Zaria " Ta na shagwaba ta ce "Yaya wlh lectures ce ta dau zafi kasan level 3 akwai azabar karatu yanzu haka ko weekend din da nake samun zuwa ba Dama saboda yanzu har Saturday muna da lectures Friday da Sunday ne kad'ai ba ma lectures" "Okay Zan duba naga cikin week d'innan idan zan samu dama me kike buk'atar nazo miki dashi" tsalle ta daka tare da buga ihu su Zarah dake gefenta saida suka done kunne ta ce "Thnks so yaya na bana buk'atar komai kai kawai nake buk'atar gani" Kayataccen murmushi ya saki Dan a rayuwarsa ba abunda yakeso sama da farincikin ahalinsa musamman Chuchu da yake mugun ji da ita ya ce. "Zaki fasa mun kunne fa chuchun yaya " Dariya tayi ta ce "Sorry yaya duk murnar zakazo ne ta zautar da ni please yaushe zaka shigo" "Yau yaushe " Friday "okay to Sunday zanshigo insha Allah " Cikin d'okin farinciki ta ce Allah ya kaimu yaya na I love you so much". .suna gama wayar ta shiga d'okin murna nan Duk ta ishi su Zarah da zancen Yayanta zaizo ya kawo mata ziyara Dariya ma su Suka dinga mata Dan yanda duk ta rikice musu. Ran Sunday tun asuba Zarah ta dinga jin ciwon Mara Alamun zuwan perioud dinta sosai cikinta ke murda mata. su Asmy basu sani ba saida safe suka ganta ta na juyi wayyo cikina kawai take cewa duk Sannu suka shiga jera mata Zarah iya ciwon cikin da take bata tabajin irin na yau ba fashewa tayi da kuka ta ce. "Zan mutu ku taimakamun Mara ta ciki na wayyo Allah Baba " Cikin tashin hankali su Asmy suka sanya hijab d'insu Tare da kamata Chuchu ma duk ta rude fito da ita sukayi ta na murkashi kamar mai nakuda "Asmy taje ta taro napep Bayan sun fito daga hostel Chuchu na shirin shiga Asmy ta ce " ki koma kiyi mana Girki sis zata samu sauk'i zamu dawo ba jimawa" Badan Chuchu ba taso ta koma Dan ta tsorata da yanda ta ga Zarah Kai tsaye asibitin da ake kaita suka nufa Gado aka basu danshi kanshi Dr d'in dake duba ta wannan Karin yayi mamakin yanda take. allura yayi mata amma kamarma Kara ciwon ake Asmy duk ta rude banda hawaye ba abunda ta ke "Bayan Dr ya fito kallon Asmy yayi ya ce " me yasa tun farko bakuyi amfani da shawarar da na bayar ba Akwai fa matsala sperm ne ya tarar mata Wanda inba sa a ba sai anyi mata Aiki " "Ta na hawaye ta ce " Dr ba yanda zamuyi ne sannan Shi Wanda zata Aurar saura shekara bikinsu yanzu ya jikin nata"dage kafada yayi ya ce "nadai fad'a muku Gaskiya ta na ciki ki shiga munmayi mata allurar da ake mata ta daina yi mata Aiki ki shiga muga abunda Allah zaiyi. Ta na kuka Asmy ta shiga d'akin Inda ta samu Zarah a bakin toilet sai sheka amai take ita ta taimaka mata ta gyara wurin kafin ta koma gadon ta na kukan ciwon cikin Dan yanzu ta ma fara fita daga hayyacinta Ita kanta ji take yau kuma kila sunyi bankwana da duniya sabbatu kawai take yayinda Asmy na rik'e da hannunta ta na hawaye. Shigowarsu kenan garin zaria Inda suka nufi hanyar A B U da mota d'aya suka taho Dan baisan duk Inda yaje asan yazo gari wayar Jaber ce ta yi ringing ,dubawa yayi yaga number mahaifiyarsa cikin Sauri ya dauka cikin muryar tashin hankali ta ce " kana ina jabir kayi Sauri ka wuce Zaria mahaifinka yayi assident yanzu aka kirani aka shaidamun suna asibitin Zaria ina ma hanyar Zaria yanzu haka nayi ta Kiran layinka tun d'azu bata shiga " Cikin tashin hankali jaber ya ce "Subhanallahi Umma wani asibitin ai ina Zaria ma yanzu haka" bansan sunan asibitin ba Amma bari na baka Aisha ta fad'a maka kila ita ta rik'e wayar Umma ta bawa Aisha Inda ta fad'a masa sunan asibitin kafin ya katse kiran " Kallonta MD yayi ya ce "Lafiya" da damuwa a fuskar jaber ya ce "Ina fa lafiya wai Abbanmu yayi assident a hanyarsa yanzu haka ya na nan Zaria asibiti kawai ka wuce makarantar ni bari na sauka na wuce Asibitin" Da damuwa MD ya ce "Subhanallahi Allah ya takaita wahala mu wuce tare kawai ina ai tafiya ta zama biyu kuma" juyar da motar sukayi suka nufi asibitin. Sunsamu jikin na Abban da sauki raunuka ne ya d'anji kuma harma anyi masa d'inki tare da treatment a lokacin ma har ya samu bacci duk Ajiyar zuciya suka sauke Office d'in Dr d'in suka wuce kafin Su jira farkawarshi . suna nan harsu mamansu Jabir da Kanwarsa sukazo Inda su suka tsaya wajen Abban nasu su kuma sukayi zaune a office d'in Dr Aliyu kasancewar abokin jaber ne da jaber da Dr Aliyu suna Hira banda MD da yayi shiru ya na latsa waya haka nan yau d'innan yake jinsa wani iri. Banko k'ofar office d'in Asmy tayi cikin tsananin tashin hankali ta na kuka ta ce "dan girman Allah Dr kazo ka gani ka taimakamun kar y'ar uwata ta mutu yanzu haka ta suma bata cikin hayyacinta na shiga ukku na Dr ka taimakamun.......✍🏿 *Domin magana da marubuciyar sharhi tambaya ko kuma Karin bayani 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 🅿️............*27 & 28* Ta k'arasa fad'a ta na fashewa da kuka"kallonta Dr yayi tare da cewa . "kiyi hakuri y'ar uwa Nifa ba abunda zan iya yiwa yar uwarki na Riga na fad'a maki maganin ciwon ta muddin ba Aure tayi ba ba zata rabu da wannan larurar ba sannan dukta karema ta kai next month's batare da tayi Aure ba to Tabbas sai anyi mata Aiki Dan sperm din ya tarar mata yanda ba aso" Durk'ushewa Asmy tayi ta na kuka ta ce "Na shiga ukku ni Asma'u yanzu Dr Dan girman Allah muje kayi wani Abu a sume take fa". Mikewa dr yayi tare da cewa "muje " cikin Sauri Asmy ta mik'e ta bi bayansa "Kallon juna MD da jaber sukayi Sai kuma yayi k'asa da kansa ya na Danna waya Jaber ko shiru yayi ya na nazarin wani irin ciwo ne wannan? Dan ta samu reliep ya sanya dr yi mata allurar bacci Bayan ta farfado anyi sa a allurar tayi aiki harma bacci ya d'auke ta zaune Asmy tayi a gadon tayi tagumi Ta na tunanin mafita. Bayan komawar Dr office Bayan ya zauna Jaber ne ya kallesa ya ce " nikam na tambayeka mana Aliyu wace matsala ce Ke damun y'ar uwar yarinyar nan Naji kana maganar sai tayi aure ? Numfasawa Dr yayi ya ce "Ciwon mara ne take fama dashi lokacin period yanda na lura yarinyar Nada tsananin sha'awa kuma wlh abun mamaki karka ganta yarinya k'arama , " shekara Ukku kenan kusan duk wata sai ankawota nayi mata allura to a halin yanzu allurar da nake mata ta daina karbarta Sperm ne ya tarar mata Wanda indai ba wani Abu ya shiga tsakanin ta da namiji ba tofa ba wani magani da zamu iya mata Dan yanzu haka abun yayi worse dukta kare saima anyi mata Aiki nan gaba inhar basuyi abunda na fad'a ba" Numfashi jaber ya ja ya ce "Allah mai iko amma fa Gaskiya na tausayawa yarinyar nan Saidai kuma ina ga tafiya tazo daidai da zama " Dagowa yayi ya kalli MD dake Danna wayarsa dukda yanajin duk maganar da suke ya ce " Aboki me zai hana ka auri yarinyar nan kaga Kayi taimako kuma kaima ka yi solution matsalarka " Wani banzan kallo na ka rainamun hankali MD yayi masa tare da cewa "ka gama rainamun wayau Jaber ohh tunda taimakon zakayi kai me zai ha na ka aure ta " ya fad'a ya na Jan tsaki. "Look bloody ba haka ba ne Wlh Gaskiya nake fad'a maka baka da mafutar da ta wuce wacce na baka Kuma ka duba ka gani a yanda naga Y'ar uwar wannan yarinyar ta firgita zasu iya Amincewa da bukatarmu sannan kaga anyi Abu biyu ka biya bukatarka itama an biya mata tata kayi tunani" Tsaki MD yaja tare da cigaba da Danna wayarsa Dan shi a ganinshi jaber ya ma gama raina masa wayau. Dr ne ya ce "tsaya wai akanme kuke magana bangane ba" kallonsa jabir yayi ya ce. "Bari nayi maka bayani aboki Shi wannan da kake gani nasan ka sansa ba boyayyan mutum ba ne, to shekararsa Tara da Aure matarsa bata tab'a haihuwa ba a halin yanzu kuma iyayenshi sun bashi nan da shekara guda Idan matarsa bata haihu ba Kuma bata samu ciki ba to zasu masa aure Wanda shi kuma baida ra ayin mata biyu sannan ya na son matarsa bayasan abunda zai bata mata rai saboda ta na da tsananin kishi Wanda yakai har ta na ikirarin ya k'ara Aure zata iya kashe kanta ta kashe kishiyar kuma matsalar rashin haihuwar daga matar ne duk inda sukaje an aunasa anga lafiyarsa qalau to shine na bashi shawarar me zai hana yayi aure a b'oye na Wata Tara yayiwa Matar ciki harta haihu asirrance Sai ya saketa bayan anyi mata karyar abunda ta haifa ya rasu sai ya amshi abunda ta Haifa ya kai matsayin matarsa ta Haifa ita kuma ya biya ta da mak'udan kudi to ganin matsalar yarinyar nan ta kawomun wani tunani,me zai hana suyi yarjejeniya ya Aure ta na Wata taran idan ta haihu saiya saketa kaga kowannansu yayiwa kowa Amfani shine wai yaki Amincewa banda hakan taimakon kansa ne". Numfasawa dr din yayi ya na nazarin maganganun jaber kafin ya d'ago ya Ce" Tabbas kayi tunani mai kyau Abokina Saidai matsalar ka na ga zasu amince kuwa?. jinjina kai Jaber yayi ya ce "Ai gwada sa'a ce " dage kafada dr yayi ya ce "indai zasu amince nima zan taimaka muku ta bangarena wajen tsoratar dasu akan ciwon yanda zasu amince idan ya amince amma fa bro ina baka shawarar ka bi shawarar abokinka Indai muddin bazaka k'ara Aure ba to wannan ce kawai Mafita a gareka ". Numfashi mai k'arfi MD ya fesar tare da Dagowa ya kallesu Shima su d'in suke kallo Dafe kanshi yayi saboda sara masan da yake tunani yayi yaga Tabbas wannace mafitar ta k'arshe Cikin husky voice dinsa ya ce " Na amince" "Ajiyar zuciya Jaber ya sauke tare da Kallon Dr ya ce " Alhmdllh to yanzu ta ina zamu fara Dr"Shiru yayi dr kamar mai nazari kafin ya d'ago ya ce "Ku barmun sauran aikin bari kuga ta yanda zan fara". MD ko zafi yakeji acikin ransa ya na ayyana wannan chakwakiya da zasu fad'a. Nurse dinsa Dr ya kira a waya tare da fad'a mata Ta shigo masa da budurwar nan da tashigo dazu ta na kuka ta amsa da okay . Suna nan sunyi shiru Nurse ta shigo Tare da Asmy dake hawaye har lokacin " Umartar nurse din yayi da ta fita kafin ya duba kallonshi ga Asmy da murmsuhi ya nuna mata chairs din da ke gefenshi ya ce "zauna a nan zamuyi magana" Zama tayi Jaber ko tunda ta shigo ya ke kallonta sosai ta burgesa Numfasawa dr yayi tare da cewa. "kinsan abunda ya sanya na ce a kiraki Hakikanin Gaskiya Akwai matsala dangane da larurar y'ar uwarki,wanda muddin wani watan ya zagayo ba tare da Wani Abu ya shiga tsakanin ta da wani ba kamar yanda na fad'a tofa cikin biyun nan dole sai d'aya ya faru na farko dai ko dai ta rasa ranta saboda sanin kanki ne ciwon cikin nan ya sha kashewa na biyu kuma dole ne sai anyi mata Aiki Wanda aikin Shima ya na da matuk'ar matsala Dan kila wa kala ne ko a tashi ko a mutu sannan kudin aikin kanshi Ba anan ake ba sai anje India Wanda a k'alla zaku kashe sama da 30 millions" Tashin hankali ba agwada maka rana d'ora hannu a ka Asmy tayi ta ce "Na shiga ukku wayyo Allah na Dr ka taimakamun kar y'ar uwata ta mutu wlh bamu da kud'in aikin nan sannan Taya za ayi Ace Tayi mu'amula da wani namiji kafin lokacin nan Bayan ba Aure gareta ba Dr inba zina akeso tayi ba " ta k'arasa fad'a ta na kuka. Murmushin Gefen baki Dr yayi Dan Shirinshi ya hau kenan kafin ya ce . "Calm down mana sister ai akwai mafita da aka samu yanzunnan amma sai inkun amince idan baku amince ba Kuma saiku jirayi abunda zai faru gaba" cikin Sauri ta d'ago ta ce "Wace mafita ce dr wlh munma amince " "Kinga waddan biyun da ke zaune " ya fad'a ya na nuna mata su MD "Juyawa tayi ta kallesu sai yanzu ma ta San da wasu a office d'in ta juya ta kalli Dr ta ce. " na gansu Dr "yawwa to Kinga wancen ya shirya taimakon y'ar uwarki Shikuma ya na da larurar tsananin sha'awa ne matarsa bata k'asar ta na k'asar waje karo karatu saura wata Tara ta gama sch shine ya ce " zai taimaka ya Aure ta *Auren wata Tara* saiya saketa Kinga an taimaki juna ya taimaketa ta taimakeshi" Kallon MD dake zaune Asmy tayi saida ta zaro ido cin karo da kyakykyawan gaske a iya rayuwarta zata iya cewa bata tab'a cin karo da mutum Mai kyau kamarsa ba Ai ba indiye ne ma sak take gani a gabanta control d'in kanta tayi Dan karsu lura tayi kauyanci sannan ta kalli Dr ta ce. "Na amince indai hakan zai zama.silar ceton Rayuwar yar uwata Dr Saidai akwai baikon wani akanta Saura shekara guda Shima karatu yaje karawa ya na gamawa itama sannan ta gama sch d'inta za ayi Aurensu idan akaje da wannan Maganar mahaifinta bazasu amince ba Gaskiya " "Ai babu d'aya daga cikin iyayensu da zasu San da maganar nan Abu ne za ayi na sirri idan lokacin ya cika saiya saketa ta tafi tayi auranta Kinga asiri ya rufo ansamu mafita ba tare da ta fad'a halaka ba" D'agowa tayi ta ce "To wa zai wakilceta Dr " wannan ba matsala bace y'ar y'ar uwa indai kun amice a take a yau d'innan za a daura Auren " Jinjina kai tayi ta ce "Na amince duk Ajiyar zuciya suka sauke banda MD da duk Haushi ya isheshi yasan Hajiya kaka ce kawai ta jawo masa matsalar nan " Jabir ne ya ce . "to saimu jirayi farkawarta muji Amincewa daga gareta " Girgiza masa kai Asmy tayi ta ce. "a a a Karku jirayeta kawai a D'aura Bayan an daura zansan yanda zanyi na shawo kanta har ta amince amma yanzu kawai a daura ba matsala " "To alhmdllh komai yazo cikin Sauki yanzu zamuje masallaci a daura Auren Bayan fitowar Sallar La'asr sannan zanyi muku video din d'aurin Auren Dan ya zama hujja da shaida a garemu" "to mungode Allah saka da alkhairi Asmy ta fad'a tare da mik'ewa tace bari na koma Wajenta" murmushi Dr d'in yayi mata ya ce"muke da Godiya sis " ta na fita MD ya kalli Dr ya ce . "me yasa ka boye musu Gaskiya Dr da ka fad'a musu bukatarmu idan sun amince idan kuma basu amince ba a hakura kar ashiga hakkinsu fa" Mikewa dr yayi tare da cewa "karka damu Aboki ba wata matsala insha Allahu idan muka fad'a musu Gaskiya ba lalle su yarda ba amma kaga haka sun yarda cikin sauki" Zai sake magana Jaber ya Mike ya ce"is okay bloody ka tashi muje a d'aura kawai"Harararsa MD yayi tare da Jan tsaki ya Mike Dan haushinshi yake ji na lika masa koma wacece da zaiyi baima ganta ba Tsaki yaja Dan baidama buk'atar ganinta. Kai tsaye Unguwar su Dr Aliyu suka nufa Bayan MD ya rufe fuskarsa da face marks mahaifinshi sukayi sallama dashi ya fito Bayan sun gaisheshi ya amsa Dr Aliyu ya ce. " baba kaga wannan ya fad'a ya na nuna masa MD Baba ya ce Eh na gansa "yawwa to Abokina ne zaiyi jahadi na Auren wata y'ar gudun hijira to iyayensa sunki su amince da Auren shine ya taho wajena Dan mu taimaka a daura musu Aure inyaso daga baya Ya nemu yafiyarsu" "Kabbara mahaifinshi yayi ya ce " Allahu akhbar da ace ana samun irin wadannan ai da anzauna lafiya Gaskiya ne wannan jahadi ne zaiyi babba Sannan ya kalli MD ya ce . "yaro Allah yayi maka albarka Tabbas kaid'in da ne na kwarai insha Allahu a yanzu yanzunnan ba anjima ba za a daura muku Aure " murmushin k'arfin hali MD yayi jaber ko Hamdala kawai yake yanda komai yazo musu yanda basuyi zato ba. Bayan kammala Sallar la'asr Mahaifin Dr Aliyu ya bada sanarwa da akwai d'aurin auren da za ayi Nan ko mutane suka tattaru aka cika masallacin harda wajensa Dan Malam ashiru sananan mutum ne Bayan an kawo Goro Inda Liman ya zama wakilin Zarah shi kuma mahaifin Dr aliyu Malam ashiru ya zama waliyin MD. ganin An fara d'aurin Auren ya sanya Jabir saurin d'auko wayarsa tare da Fara yin video a take a nan aka Daura Auren *Zarah Yusuf* tare da Angonta *Mustapha dikko* Akan sadaki Naira Dubu d'ari biyar.......✍🏿 *💃💃yanzu salon wasan zai soma wakana fans wancen duk sharan fagene yanzu muka shiga chakwakiyar Auren wata Tara Kudai ku kasance dani miss hajjo danjin karashin wannan K'ayaitaccen littafin da yazo da salo mai rikitarwa* *kamar yanda kuka sani littafin nan d'aya yake daga cikin gawurtattu biyar page d'aya ya rage mana mu gama free page daga page 30 zan tsaya da free page Wanda ya biya ne kad'ai yake da daman k'arasa karanta wannan zazzakan labarin da yazo daga zazzakan alkalamin miss hajo ga tsarin yanda biyan nan yake a kasa idan kun duba don neman karin bayani ku tuntube ni Akan number wayata kamar haka 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 🅿️............*29 & 30* Daga wajen d'aurin Auren MD ko jaber bai Kara waiwaya ba ya wuce Gidanshi dake nan low-cost Zaria Dan kanshi duk Sara masa yake. Bayan komawarsu jaber asibitin kiran Asmy Dr yasa akayi a office d'inshi jaber ya mik'a mata wayarsa tare nuna mata video din amsa tayi ta na Kalla gabanta na fad'uwa Dan batasan yanda zasu wanshe da Zarah ba " Tura video din tayi a wayarta itama Dan ya zame.mata hujja sadakin a embleme ya mik'a mata tare da cewa . "ga sadakin dubu d'ari biyar ne chif" Amsa Asmy tayi tare da Sanyawa jaka duk tayi sanyi ta kalli Dr ta ce "Sai Abu na gaba da bamuyi ba takardar yarjejeniya " girgiza mata kai sukayi jaber ya ce "Ba ma buk'atar wannan ma'u sannan ki bani numberki mun k'arasa sauran maganganun a waya" Kwafe masa numberta tayi Bayan yayi save tata Shima tayi save a sanyaye ta koma d'akin da Zarah take har lokacin Bacci take tagumi tayi hawayen tausayin aminiyar tata na zubo mata Zarah ita ce bata farka ba sai Asuba koda ta tashi jikin nata Alhmdllh ba ciwon cikin sosai. A hankali ta mik'e ganin Asmy gefenta ta na bacci toilet ta nufa ta gyara jikinta ta na fitowa ta iske Asmy ta mik'e ta na mika Kallon juna sukayi Asmy ta ce. "Harkin tashi kenan ya jikin to" Alhmdllh kenan saida muka kwana Asibiti"Wlhko ai ciwon nan naki ya tsoratani Zarah ta fad'a tana shiga toilet Dan yin alwala Bayan ta fito tayi salla ita dai zarah ta yi tagumi Tun lokacin Asmy take son yiwa Zarah bayani amma ta kasa Sai tazo zata mata bayani sai ta kasa Wajen 7:00 Zarah ta ce "waike meye kikeson ki fad'amun tun asuba kin kasa karkija inyi zaton ko wani abun ne ya faru". Numfasawa Asmy tayi dak'yal ta iya d'aga baki ta ce " daman Zarah "saikuma tayi shiru daman me?ta fad'a ta na tsatsareta da ido" Dak'yal ta iya jarumta ta ce "ta ce . "Daman Dr ne ya ce ciwon cikin naki yayi worse sosai sannan Allurar da ake maki ta daina maki aiki muddin next month yazo a haka batare da wani Abu ya shiga tsakaninki da wani ba to dole sai anyi miki aikin 30 millions kuma aikin ya na da hatsarin gaske" Sosai tashin hankali ya bayyana k'arara a fuskarsa Zarah ta ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Wannan wace irin jarabawa ce Asmy yanzu ni me.zai had'ani da wani namiji kafin one months Ni da ba Aure gareni ba Sannan Aikin 30 millions fa kikace Asmy wani irin aiki ne wannan". Numfasawa Asmy tayi ta ce " Eh Zarah haka Dr ya ce Saidai akwai mafita "cikin sauri ta d'ago ta ce " wace mafita Asmy?Wani abokin Dr ne da yazo ya tausaya halin da kike ciki shine ya ce Wai idan zaki amince zai Aureki na wata Tara kafin lokacin bikinki da ya Hafiz saiya sakeki Kinga Asiri ya rufu hankali kwance". Wani banzan kallo ta dinga bin Asmy dashi kafin ta d'ago ta ce "bantaba sanin baki da hankali ba Asmy sai yanzu wannan wace irin banzar magana ne angaya miki Aure abun wasa ne ko kuma ciwo hauka ne to Bari kiji ko zan mutu bazan tab'a yarda da wannan shirmen banzan ba ko a garin gab'a gab'a anyi haka wlh ni kinma b'atamun rai yanda baki tunani " ta fad'a ta na Jan dogon tsaki. Sosai gaba Asmy ya bada daram hankalinta in yayi dubu ya tashi ta ce "Amma Zarah...daga mata hannu tayi ta ce " ya isa indai akan wannan banzar maganar ce Karki sake mun maganarta " Ta fad'a ta na mik'ewa tare da sanya Hijab d'inta ta ce "Kinja Asibitinma ya fita a raina tashi mu tafi " Amma aikin bari Dr d'in yazo ya sallamesu"Ke saiki jira har ya zo ya sallameki ni na tafi ta fad'a ta na nufar hanyar kofa. Daidai fitarta yayi da daidai da shigowar Jaber d'akin da Kallo ya bita harta fice daga Ward din wanda ko fuskarta bai gani ba juya Kallonshi yayi ga Asmy da tayi tsuru a d'akin ya ce . "hartaji sauki kenan naga fitarta ina zata?hostel wlh ya jaber taki amincewa nan ta fad'a masa yanda sukayi da ita " kallonta yayi ya ce "Karki damu sannan karki fad'a mata ki barta a haka din duk abunda zai wakana ya zamana muna shiryasa ni Dake tunda na lura Amaryar tamu kamar ta na da taurin kai". Murmushi kawai tayi ta ce " haka take in ta burkuce amma tana da saukin kai bari na bita "Ledar da ya shigo da ita ya mik'a mata ya ce " daman break fast ne na shigo muku dashi"Da farko kin amsa Asmy tayi saida taga yana ta mata magiya kafin ta amsa Bayan taje tayiwa Dr bankwana ta bar asibitin kafin ma ta isa wajen asibitin har Zarah ta tafi wata napep din ta tsaida ta wuce makaranta. koda ta isa kwance ta tarar da Zarah Chuchu na gefenta ta na bata ruwan tea ta na shigowa Zarah ta kauda kai ta na kunbure kunbure girgiza kai kawai Asmy tayi tare da zama Chuchu ta Kalleta ta ce . "ya mai jikin jiya nayi ta Kiranki ki fad'amun asibitin da kuke nazo amma kashe " wlhko chaji ne bandashi har yanzu wayar tawa ta mace gashi tata Kinga bamu tafi da ita ba " "ayya shiya sanya Ai da sauki ma wlh karkiga jiya banyi barcin kirki ba duk hankali na na wajenku sannan Yaya na ma da yace zaizo nayi ta kiranshi Shima kashe duk raina ya gama b'aci jiya da kadaici na yini na kwana". Murmushi akwai Asmy tayi ta ce " kilan wani uzurin ne ya rikeshi"Wama ya sani kuma fa wlh yaya baya magana biyu abun yaban mamaki sosai "duk maganar da suke Zarah bata ce uffan ba saima Kallon Chuchu da tayi ta ce " kin sanyamun wayata chaji?eh ta fad'a tare da tashi ta miko mata ta ce "anyi ta Kiranki ganin kiran yayi yawa ya sanya na ma kashe ". bud'e wayar Zarah tayi ta ga missed call d'in ya Hafiz Kusan goma cikin Sauri ta Danna masa kira Ring biyu ya d'auka ta na jin Ajiyar zuciyar da ya sauke tare da cewa . "ina kika sanya wayarki my love jiya na yini da darura " Ajiyar zuciya ta sauke ta na lumshe ido ta ce "ta mutu ne ba chaji ya Hafiz ina kwana ya sch din" . Alhmdllh Habibaty har Naji sanyi kinsan na d'auka ko ba lafiya ba sai tunaninki nake"murmushi tayi ta ce "Lafiya qalau nima da tunaninka na yini" ta fad'a ta na rufe fuska ". Daga bangarensa yayi Dariya ya ce " ai dai nesa ta kusa zuwa kusa nan da one year munzama mata da miji"rufe fuska Zarah tayi kamar ya na gabanta tare da katse kiran Dan ya bata kunya ma . Ganin yinin ranar yanda Zarah ta share Asmy ya sanya bataji dad'i ba Ta ce "Na ce Kiyi Hakuri Zarah Daman zaki iya fushi dani tunda maganar ta wuce ba shikenan ba" murmushi Zarah tayi ta ce "Ya wuce Asmy kinban Haushi ne nayi mamaki da maganar ta fito daga bakinki saikace baki da hankalii" . turo baki Asmy tayi ya ce "Naji dai yanzu abar maganar" a take suka shirya sukaci gaba da hirarsu Wanda asmy hankalinta duk baya gurin. *** "To ba saurin nake ba bloody kaifa komai kafison ayishi cikin ujila ba ina hanyar zuwa gidan ba minti biyu yayi yawa na iso " " jaber ya fad'a daga wayar "tsaki MD yaja tare da katse kiran ya na tsaye harabar gidan flat house ne Me kyau baida wani girma sosai Saida ya tsaru parking space d'in gidan zai d'auki mota Ukku ya na tsaye motar jaber ta shigo gidan Bayan yayi parking shiga gaba yayi da zasu fita ya tsaya ya mik'awa me gadin kudi tare da cewa . " A cigaba da kula da tsaftar gidan yanda ya kamata "to ranka ya dad'e insha Allahu Nagode Allah ya k'ara girma" kai tsaye Hanyar kd suka nufa jaber ya Kalleshi ya ce "bazamuje mu gaisa da Chuchu ba" Bana ra'ayin hakan "ya fad'a yana cigaba da latsa wayarsa " Girgiza kai kawai jaber yayi tare da cigaba da driving Dan ya lura ranshi kamar bace tafiyar 30 minutes ta kaisu garin kd Wanda kai tsaye gidan sa suka nufa Bayan ya saukesa jaber ya wuce gidansu Dan tun safe aka Sallami babanshi shi kuma md ciki ya shiga Dan ya huta. Kwance yayi kan makeken Royal bed dinsa mai matuk'ar d'aukar hankali ya yi pillow da hannayenshi biyu bacci yake so ya daukesa amma ya rasa dalilin da muryar qiri'arta yarinyar ke dawo masa a kunne lumshe idonsa yayi. Jin ringing d'in wayarsa da ya bude ba jimawa ta dawo dashi daga duniyar tunanin da ya Lula d'aukar wayar yayi ganin Chuchu ce ya sanyashi d'auka "yaya na jiya shine ka shanyani nayi ta jiranka har girki mai dadi nayi maka amma bakazo ba " ta k'arasa fad'a cikin shagwaba " Cikin muryarsa da bayason yin magana ya ce "wani uziri ne ya hanani zuwa chuchun yaya next time na tashi zuwa Saidai kawai ki ganni kwatsam" Yana jin ta sauke ajiyar zuciya kafin ta ce "To shikenan yaya Ai Inajin next week ma zanzo gida saboda munyi waya da Ruky tace next week zasu tafi Dan naje muyi bankwana " to shikenan Allah ya kawoki lafiya "ya fad'a Dan bayason hayaniya. Kiran Amera ne ya biyo baya Bayan gama wayarsa da Chuchu kamar bazai daga ba saikuma ya d'auka " kuka yaji ta fashe dashi Wanda yakejinshi har cikin ransa tsayawa yayi ya na sauraronta har saida ta gama kafin ta tsagaita cike da kissa ta ce. "Haba Honey Bayan kasan nayi missing naka shine zakayi zamanka anan please yaushe zaka dawo kasan banason zamanka a Nigeria ko wace banza ta dinga kallemunkai please mijina ka dawo kewarka duk ta isheni. " Ke me zai hana bazaki taho ba Inda nake Dan in kin ganni a America to fa saina gama muhimmin aikin da ya kawoni " "Haba honey yanzu ka na nufin bazaka dawo ba yanzu akwai muhimmin aikin da ya fini daman me zai hana bazaka k'arasa aikin a nan America ba dole sai Nigeria " ta k'arasa fad'a ya na jin shashekar kukanta". Don son kwantar mata da hankali ya sanyashi kasa da murya ya ce "Aikin bazaiyu ba a Chan my meera ki taho kawai nima ina bukatarki kusa dani kinfi kowa sanin haka Gobe ki taho saiki sauka Abuja" "Ni wlh honey bazanzo Nigeria yanzu ba idan nazo dinma in banda chazamun kai ba abunda ake sannan a isheni da maganar Rashin haihuwa Bayan ta Allah ce Nifa tun last time da nazo Sunan Daddyn Zey karkaga irin Rashin mutuncin da tsohuwar nan tayimun Hada cewa wai Aure zata sanyaka kayi na shanyeka na gama dakai sannan itama Ammy Ai Naji kwanaki kus_kus din so take kayi Aure to wlh ba abunda zai maidoni Nigeria kusa wancen zuwan ma da kaga nayi Dan nayi kewar iyaye na ne kawai akanme zanzo Bayan family dinka ba k'aunata suke ba dan wlh tsohuwa ko yarinya ta kawomun wargi ba kyalewa zanyi ba Hakanan kawai a doramun hawan jini da yarintata" Sosai ran MD ya b'aci Cikin b'acin rai ya ce "Da Allah iya mutane shiru stupid kawai iyayen nawa kike fad'awa haka Dan baki da kunya kar alasa kizo din kiyi shekara ta Annabi nuhu tunda America din garin ubanki ce " ya k'arasa fad'a ya na Jan tsaki. Kuka Amera ta fashe dashi ta ce "ni kake zagin uba na MD yau Ni ka zaga" tsaki ya ja tare da katse kiran Dan ta bata masa rai ya jima ya na Jan tsoka. Kasancewar ya rike ranar da chuchu ta fada masa su hajiya zasu tafi around 11am ya shiga da motarsa harabar gidansu Hango motar Adil tare da su Hajiya da su Chuchu a wajen ya sanyashi karasawa"Ina kwana hajiya "Lafiya qalau Mustapha mu kuma muntafi sai Allah yayi mana dawowa ko kuma kunje dukda Bason zuwa kuke cikin dangin Ku ba kowa gareku ba a Kaduna in banda Aikin gwamnati da kasuwanci da ya kawo mahaifinku duk dangin mahaifinku suna Maiduguri amma tsabar shak'iyanci saiku Shekara biyu ko Ukku baku taka garinba Dan lalacewa Ai wlh duk laifin Fatima ne Ai lokacin da ran Mariganyi yana tiso keyarku kuna zuwa" Murmushi yayi ya ce "za a gyara Hajjajunah " itama Ammy murmushi tayi ta ce "Insha Allah Hajiya zamuzo nan kusa " Allah yasa Hajiya ta fad'a ta na sanya akwatinta cikin boot da Adil ya fito mata da ita tare da Chuchu hannu Adil ya mikawa MD sukayi musabaha ya ce "Yaya zamu wuce " "Okay Allah ya kiyaye Ya tsare hanya yanzu tundaga Chan Saida Hajiya ta tiso ka Dan Kawai ka d'aukesu maimakon A musu booking Fly hankali kwance". murmushi Adil yayi ya ce "Wlhko ya na iya na musa cibi ya zama Kari" Hajiya ce ta ce "Naji dai Komai zakace kace amma banga tukin da zan hau ba idan ba naka ba Sauran duk y,an kasada ne ka maza ka shigo mu tafi maiduguri ba zuwa kano bace karmuyi dare hanyar nan da ba kyau gareta ba". Ruky ta fara shiga Bayan sunyi hug din juna da Chuchu da takejin kamar tayi kuka Bye bye tayiwa Adil ta na narkewa jikin Ammy murmushi yayi mata na so da k'auna ya ce " Bye Dear sai munyi waya"itama mayar masa tayi ta ce "Allah ya maidaku lafiya " . Har zasu tafi Hajiya ta juyo ta kalli MD ta ce"kai kuma Ka fara lissafi yanzu saura wata sha d'aya ka bari lokacin da zan dawo garin nan zakayi mamakin d'anyen aikin da zanyi "ta na gama fad'a ta shiga Mota Adil ya ja har suka bar gidan suna daga musu hannu". Cikin suka koma Chuchu ta zauna gefen Ammy ta d'ora kanta bisa kafadarta " Gaishe da Ammy MD.yayi Bayan ta amsa Kallonnshi Chuchu tayi ta ce "Ina kwana yaya" Lafiya qalau "ya bata amsa tare da cewa jeki hadoman break fast " "to" ta amsa tare da wucewa kitchen. Kallonshi Ammy tayi ta ce "yaushe zaka koma ka baro Matarka ita kadai kayi zaune a nan" Ba yanxu ba Ammy bazan bar k'asar nan ba har sainagano Wanda sukayi kisan Alhaji sammani saboda sak irin harin da suka kawowa Abba Shima daidai zai shiga gidanshi da mota aka harbeshi akwai binciken da nake saina k'arasa tukwana". Saida Ammy ta Goge hawayenta tunowa da uban Yayan nata ta ce "Tabbas Wanda yayi kisan Alh sammani shi ya kashemun miji saboda alh sammani da Mahaifinku aminai ne bashi da aminin da ya fishi kuma insha Allahu asirinsu saiya tonu har kullum bazan daina muguwar addua a kansu ba Asirinsu zai tonu insha Allahu wlh karkaga yanda iyalanshi suka shiga wani hali abun tausayi har yanzu na tuna da Alhaji ji nake kamar mutuwar ta dawomun sabuwa " ta k'arasa fad'a ta na Goge hawayenta. Nan suka ci gaba da hirar rayuwar baya har Chuchu ta kawo masa Break fast din Bayan ta Aje d'akinta ta shiga sai ganinta yayi ta fito da hijab tare da hand bag a hannunta Kallon Ammy tayi ta ce "Na wuce ammy" MD ne ba wasa a fuskarsa ya ce "Ina zaki ? "Makaranta zankoma tun jiya nazo kuma muna da lectures Gobe" ki koma sai gobe "Ta na turo baki ta koma ciki Dan tasan Halin Yayan nata baisan musu Kallon Ammy yayi ya ce. " me akayi mata naga ta na bata rai"Tab'e baki Ammy tayi ta ce "Baiwuce akan Tafiyarsu Ruky da Adil ba kasan halinta indai suka tafi tazo tanayiwa mutane fushe fushe Saikace in cewa akayi ta shirya taje Chan tayi ma musu Hutu iyawa zatayi". ***** Tsaye take ta na gyara Tsayuwar hijab d'inta Bayan ta gama Kallon Asmy dake chat ta ce "Zanje bank na ciro kudi tunda bazaki raka ni ba" "A dawo lafiya " ta fad'a ta na cigaba da chat d'in ta Zarah na fita ta dannawa Jaber kira saida ta katse ya kira. "daga bangarensa ya ce " ya maganarmu ta tsaya ma'u lokaci fa naja ki duba yanzu two weeks da Auren nan Kar lokacin Yazo kuma ba ayi abunda ya kamata ba "numfashi Asmy ta ja ta ce " nima ina tsoron haka karka damu Insha Allahu gobe zan fito da ita k'arfe Bakwai ai yayi ko?eh yayi ma'u plx kiyi kokarin wannan "murmushi tayi ta ce " baka da case jaber ". *** Kwance ya ke saman bed duk sanyin AC din d'akin amma bayaji zufa ce kawai ke keto masa Rumtse idonsa kawai yake A haka jaber ya shigo ya samesa Da damuwa ya ce. " subhanalla bloody lafiya"lafiya "ya basa amsa cikin k'arfin hali tare da mik'ewa ya zauna" Takardu Jaber ya Aje tare da cewa "ga document din sun kammalu" okay Aje zan duba zuwa anjima "Shiru jaber yayi kafin ya Mike ya ce " saida safe "Gobe Zamu kai Chuchu School Around 4 haka saimu hadu a gida sannan ka fito da motarka mai tinted Dan bana son asan mun shiga garin". Ajiyar zuciya jaber ya sauke A ransa ya ce " Abu yazo yanda ake so"a fili kuwa murmushi yayi ya ce "Allah ya kaimu." Washegari kamar yanda ya fada karfe hud'u tayiwa jaber gidansu MD sosai Chuchu ta saki ranta Dan taji dad'in Yayan nata zai mayar da ita Nan suka kama hanyar Zaria sai doki take. Koda suka isa cikin Sauri Chuchu ta ce " Dan Allah yaya ku tsaya na kira maka Friends Dina ku gaisa Kullum ina musu zancenka "kama hannunta yayi ya ce " Ki bari ba yanzu ba chuchun yaya akwai Inda zamu please Kinji" Badan Chuchu ta so ba ta Turo baki ta ce "Yaya minti biyu yayi yawa fa" Girgiza mata kai yayi ya ce "Akwai Gidajen man da na bada aikin ayi zanje na dudduba aikin yanzu next time Ai zamu dawo" To shikenan yaya na Allah kiyaye saimunyi waya ta fad'a ta na Daga musu hannu"murmushi jaber yayi cikin zolaya ya ce "Ni baza ayi mun magana ba Amaryas" Harararsa tayi tare da turo baki gaba ta ce "Ai kai munjima da batawa dakai" Ta fad'a tare da Yin gaba. Zarah kadai ta tarar a hostel cike da murna suka Rungume juna Zarah tayi mata Sannu da zuwa ta amsa ta na mik'a mata leda ta ce "Gashi takwararki ta ce Na kawo maki Sannan ta na gaisheki sosai tunda ke kinki zuwa gaisheta" murmushi Zarah tayi ta ce "Amma nagode Gaskiya dole na shirya naje na gaishe da Ammy na" Murmushi Chuchu tayi ta ce "Yadai kamata ina Asmy " ta fita ta na Waya kinsan iskancin yanzu da ta tarka waya a waje "Dariya Chuchu tayi ta ce " Munafukar bari tazo in tsareta inji da ubanwaye take wannan wayar. Asmy na shigowa itama suka Rungume juna da Chuchu Ta ce "wai da ubanwa Kike wayar munafurci kwanannan" Dariya tayi ta ce "Au kun samun ido kenan ina tsarabarmu " Harararta tayi ta ce "da yake aikena kikayi momcy na kadai nayiwa tsaraba" iyye lallai da sake Gaskiya kabilancin nan da ake gwadamun yayi yawafa ta fad'a ta na kwale hijab d'inta. Asmy ta rasa dabarar da zatayi su fita da Zarah ga magriba na gabatowa wata dabara ce ta fad'o mata Kallonta ta yi ta ce "Sis Dan Allah zaki rakani Gidan wata kawar Mama dazu take Kira na take Cemun naje na amso mata sako saina d'ora a mota a kai mata". Kamar Zarah bazatayi magana ba sai kuma taje ki bari mana sai gobe yanzu magriba nayi" A a a ai goben za a d'ora mota akai yanzu ta ce naje na amso"Shiru Zarah tayi sai kuma ta ce "okay To " . Ajiyar zuciya Asmy ta sauke kallonta Chuchu ta yi ta ce "Ni baza ayimun tayin rakiyar ba" murmushi Asmy tayi ta ce "Sorry sis to shirya mu tafi " girgiza kai tayi ta ce "wasa nake maki na gaji Wlh " boyayyar Ajiyar zuciya Asmy ta sauke tare da mik'ewa Ta kalli Zarah ta ce "Kije kiyi wanka nima yanzu nayi saimu tafi" . wani kallo Zarah ta mata ta ce "Ba wani wanka da zanyi malama sai zan kwanta" Asmy na kwantar da murya ta ce "Haba sis Kinga fita zamuyi sannan tunfa wankan safe da kikayi ga zufa" . Mikewa Zarah tayi ta ce "Kuma hakane zafi ma nakeji wlh Inajin akwai hadari kasa ta fad'a ta na cire kaya tare da daura towel ta wuce toilet din hostel Dan tayi wanka ba ayi minti goma ba ta fito d'aure da towel tare da Shiryawa cikin Wata doguwar rigar atamfa Street gown d'inkin sosai ya kamata yayi mata das a jiki. Chuchu ce ta Kalleta ta ce " wow karkiga yanda kayan nan sukayi miki kyau momcy kyan shigar nan ki fita da gyale wlh amma saiki kama ki zumbula k'atuwar hijab kamar wata matar Liman". murmushi Zarah tayi ta ce "Chab ai ko bakin hostel baxan iya fita da shigar nan ba bare waje ta fad'a ta na bud'e gogaggiyar hijab d'inta red har kasa sosai Tayi mata kyau ta haskata ganin ana kiran Magriba ya sanyata tada salla daman tayi alwala Bayan ta gama Kallon Asmy tayi dake chat ta ce " ke bazakiyi sallarba" Gyada mata kai ta yi ta ce "Eh banayi Ammafa hijab din tayi miki kyau kodan red din Abu da d'aukar ido" . muje dai yanzu kar dare yayi Zarah ta fad'a "okay Asmy ta fad'a tare da saurin fita Kiran jaber tayi ta ce " turomun address d'in Gidan ta message gamu nan". Ganin fitowar Zarah ya sanyata saurin katse kiran suna fitowa sun tsaida napep Asmy taga shigowar message wayarta dubawa tayi taga ya turo mata address din gidan hada number gidan"Mai napep din ta fada wa address din suka kama hanya. suna isa Bayan ta biya mai adaidaitan Kallon gidan ta tsayayi Zarah ya had'u sosai Hakanan bata San dalili ba Taji gabanta ya fad'i harsuka isa gidan gabanta banda fad'uwa ba abunda yake. A palourn gidan suka yada zango ganin ba kowa ya sanya Zarah Kallon Asmy ta ce "Sis ya na Ga gidan ba kowa ko Alamun mutane ba aji ". ba ta rufe baki ba taga fitowar wani yana fara'a Kallon Asmy tayi taga itama fara'ar take masa Bayan ya karaso Kallon Zarah yayi ya na ganinta Ya gane Itace Matar MD kenan sosai shi kanshi saida gabanshi ya fad'i cin karo da kyakyawar fuskarta mai d'auke da kwarjini da haiba ga dimple dinta da suka lotsa suka k'ara fito mata da ainahin Kyaunta a ranshi ya ce . "Daman wannan zuk'ek'iyar ce mukayiwa haka Chabd'i Amma wlh da nasan haka take tun farko da ni nayi dabara na aureta kuma ba sakin ta ba zanyi wlh" saurin kauda wannan tunanin yayi tare da kirkirar murmushi ya ce " ku shigo mana kun tsaya a nan"Mikewa Asmy tayi Tare da kallon Zarah ta ce "Taho muje" a a kawai shiga ki fito"ta fad'a cikin k'arfin hali"bata rai Asmy tayi ta ce "Saikace sayar dake nace zanyi Ki taho muje ta na ciki ita tace muje wannan din d'anta ne fa" Jin haka ya sanya zarah Mikewa gabanta na fad'uwa Har suka gitta jaber ya na binta da Kallo wani bedroom taga sun nufa. Turata cikin d'akin Asmy tayi tare da Rufewa ita da jaber suka sanya key Da mamaki Zarah take kallon kofar tare da bubbugawa ta ce. "Meye haka Asmy ki bud'e sanin kanki ne bansan wannan wasan Bata gama rufe bakinta ba Ta ga fitowar Shi daga bathtoom. sanye da towel Da ya tsaya masa iya cinya Ai bama ta tsaya k'are masa kallo ba ta k'walla ihu tare da Fara bubbuga k'ofar ta ce " ki bud'e Asmy"Kallonta MD ya tsayayi da mamaki Wacece kuma wannan Takardar da yaga an Aje masa ne akan table ya sanyashi d'agawa rubutun jaber ya gani a takardar an rubuta. "Mungama namu aikin kuma saura naka Ango ga Amaryar ka nan har gida har dakinka dukda dai ita d'in jaruma ce Saida jarumin namiji good nigh Asha angonci lafiya" Saida MD ya k'arasa karanta takardar sai sannan ma ya tuno da yayi ma wani Aure a sirri Kallonta yayi da har lokacin Ta na kuka ta na buga kofar Murmushin gefen baki yayi ya ce. "Zaki San kin kawo kanki yarinya ko ba ke jarababbiya ba ce da kika biyoni har gida zakisan kin hadu da jarumin namiji stupid ". Ya na jin Yanda take kuka tana buga kofar tsaki ya ja har ya gama shafa lotion d'inshi cikin salo durk'ushewa a guri Zarah tayi ta na wani irin kuka shin me Asmy take nufi da hakan MD ko Kukan ne ya isheshi hakan ya sanyashi Mikewa cikin zafin nama tare da karasawa kofar ta na ganinshi ta fara ja da baya ta ma kasa d'aga baki tayi magana " Fardota Yayi Ta fad'a Jikinshi Baka iya Tantance irin yanayin da suka shiga dukansu biyu musamman MD da cin karo da tsayayyun breast d'inta dake.gogar masa k'irji. rumtse ido yayi lokaci guda yaji wani fitinannen felling na taso masa Dan shi daman mutum ne da k'aramun Abu ke Tado masa felling musamman breast . Zarah ko kuka ta fashe dashi zatayi magana ya ce "shittt pretending din ya isa Haka badai.ke kika kawo kanki ba bazan raga maki ba stupid kawai". ya fad'a tare da fusge hijab d'inta yayi Wulli da ita tashin hankali ba a gwada maka rana matuk'ar rudewa Zarah ta rude Zata iya cewa tsawon rayuwarta bata tab'a shiga tashin hankali kamar wannan ba kuka ta fashe dashi ta ce. " Dan Allah bawan Allah kayi hakuri karka rabani da mutunci na....bata k'arasa maganar ba sakamakon irin d'aukar da taga yayi mata MD jinta yayi shakwal.duk da yaga a ido kamar zatayi nauyi. bai dire ta ko ina ba sai kan bed kafinma tayi wani motsi ya bi ya danneta tare da sakar mata Duka nauyinshi cike da mugunta ya rabata da kayan jikinta komai cikin karfi da Mugunta yake yinsa. duk yanda Zarah taso bai rabata da kayan jikinta ba kasawa tayi saida ya zama daga ita sai bra sai pant jikinta Wanda a lokacin da za a Auna jinin Zarah ya hau d'ari Ukku tsabar rud'u MD sosai ya k'ara rikicewa cin karo da tsayayyun na shanunta Da suke a cike ai baisan lokacin da yaji wata irin tsananin sha'awa na fisgarsa ba Dan a rayuwarsa Ba abunda Suke tada masa feeling sama da breast (🙈)Cike da mugunta ya fara wasa dasu Wanda Zarah duk feeling d'inta wannan lokacin bataji ba sai zafi ma da take ji inbanda kuka ba abunda take tana Kokarin yanda zata kwaci kanta MD yayi minti ashirin ya na wasa da breast d'inta Da karfi ya rabata da sauran abunda ya rage na jikinta tare da wara mata k'afafu Cike da mugunta ya afka mata da karfi cike da mugunta ba romance ba komai. azabar zafin da tunda uwarta ta haifeta bata tabajin irin ta ba ce ta sanyata kwalla wani irin K'ara Wanda ihunta saida ya kauraye Duka ilahirin Gidan wani karan ta kuma kwallawa Wanda daga lokacin kuma bata k'ara sanin Inda hankalinta yake ba.......✍🏿 *Last free page 07026166536* 🙇🙅 *nan na kawo karshen free page na littafin Auren wata tara Wanda suka biya ne suke da damar ci gaba da karanta wannan kasaitaccen littafin ya da zamo d'aya daga cikin gawurtattu biyar domin Karin bayani a tuntube ni akan number waya ta kamar haka 07026166536 sai najiku masoyan Asali nasan babu kasaitacciyar da zataso ayi doguwar tafiyar nan ba tare da ita ba Mai cike da Abubuwan mamaki al'ajabi,nishad'i rud'u,fadakarwa,ilimantarwa,nusarwa da kuma tsantsar soyayyar ga yanda tsarin biyan yake zaku gani a k'asa sai mun had'e a paid group masoyan Asali masu ci da guminsu inji y'an magana sunce Sayan na gari maida kudi gida 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Bama son VTU Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 🅿️...........*31 & 32* Bayan komai ya lafa Sai sannan MD ya lura da aika_aikar da ya aikata bai tab'a tunanin Zai samu yarinyar a budurwa ba shiyasa har yayi mata mugunta a lokacin ana kiran asuba kunna glove din d'akin yayi Haske ya kauraye saida ya wara idanu ganin irin jinin da ya gani a zanin Gado Sosai ya rikice ganinta sume jijjigata ya fara Amma ba motsi rasa yanda zaiyi da ita yayi tagumi yayi ya sawa sarauta Allah ido,Firgit ya Mike tunowa da yanda yayiwa Amera a first night d'insu cikin Sauri ya jona ruwa a kettle kasancewar akwai nefa ruwan d'umi ya zuba a roba tare da d'iga ruwan Dettol da baya rabuwa dashi a toilet dinsa Cikin Sauri ya sungumeta tare da sanyata cikin ruwan ya fara gasata sosai yayi mamakin yanda ko motsi batayi ba Sosai yayi ta had'a ruwan zafi ya na gasata ko zai samu ta tashi amma ko motsi batayi ba cikin tashin hankali ya samu ya mata wanka Wanda bai yarda ya k'ara kallon surar jikin ta ba Dan gudun kara shiga wani hali Bayan ya gama mata ya fito da ita daman ya sauya bedsheet din kwantar da ita yayi tare da dauko mata rigar Amera dake gidan da suka taba zuwa sau daya ta kwana wani biki dan Sau daya ma ta taba zuwa gisan kasamcewar saita shekara nawa bata taka garin zaria ba ya sanya mata saida yayi wankan tsarki kafin yayi wani wankan ya fito Cikin Sauri ya shirya Zaune yayi bakin gadon ko zaiga farkawarta amma shiru Ganin Safiya ta fara ya sanyashi kabbara Salla a d'akin Dan ba damarma yaje masallaci. Har karfe Bakwai Zarah bata farka ba wanda hakan ya k'ara rud'ar da MD karfa na kashe y'ar mutane"ya fad'a cikin ransa"Saurin mikewa yayi tare da karasawa Inda take kwance numfashi ne kad'ai zai tabbatar maka da ta na raye "wani tunani ne ya fad'o masa yayi saurin daukarta tare da fitowa da ita harabar gidan a mota ya sanyata tare da shiga driver sit da gudu ya dannawa mai gadi horn ya zo ya bud'e masa bai zarce ko ina ba sai asibitin Dr Aliyu Emergency aka wuce da ita MD duk ya rud'e A office d'in Dr Aliyu ya zauna ya na dafe da kansa Bayan shigowar Dr kallonsa yayi ya ce " ina y'ar uwar tata ta ke? "Bansani ba Dr wani hali take ciki yanzu" ya fad'a damuwa k'arara a fuskarsa "Alhmdllh ba wani Abu bane rud'u ne da firgici ya sanyata tayi doguwar suma anjima zuwa 4 insha Allahu Zata tashi sannan za a rubuta mata magunguna Wanda zata dinga sha yanzu mun sanya mata drip " Boyayyar Ajiyar zuciya MD ya sauke Bayan fitar MD office d'in Dr yayi sauri ya kira jaber Bayan ya d'auka ya ce "kana ina Abokina yanzu Abokin ka ya kawo Zarah Asibitinmu ?Cikin tashin hankali jaber ya ce " what Asibiti Dr gamu nan zuwa yanzu"Minti goma ba ayi ba saiga Asmy da jaber sun shigo asibitin Asmy banda kuka ba abunda take Dan tun jiya ko bacci bata samu tayi ba saboda darurar halin da aminiyartata take ciki Dan ita kanta in banda tsoron kar wata guda ya cika hakan bata faru ba da ba abunda zaisa ta aikatama aminiyarta tata haka ta na kuka ta ce "Dr ina y'ar uwata?me ya sameta?. " Kwantar mata da hankali Dr yayi Ganin ta rude ya sanyashi kaita dakin da Zarah take kwance ta sameta Drip mak'ale ga tsintsiyar hannunta Batasan lokacin da ta fashe da wani irin kuka ba Ta ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un na shiga ukku ni Asmy Zarah ki yafe mun Na chucheki banyi hakan da wata manufa ba saidan soyayyar da nake maki sosai Asmy ta Rungume Zarah ta na wani irin kuka. Nan jaber Shima ya shigo idan ranshi yayi dubu ya b'aci ga dukkan alamu ta karfi MD yabi yarinyar nan lokaci guda yaji wani tausayinta ya mamayeshi sai yanzu yake Dana sanin abunda suka aikata shida Asmy baitab'a tunanin MD zaiyi wannan Rashin imaninba Cikin damuwa ya juya tare da Danna masa kira ringing biyu ya dauka. Cikin b'acin rai jaber ya ce " yanzu MD abunda kayiwa yarinyar Nan ka kyauta harta kai ga ka kwantar da ita gadon asibiti wannan wani irin Rashin imani ne"tsaki MD ya ja tare da katse kiran ya wullar da wayar Kujerar mai zaman banza D'ora kanshi yayi ga sitiyarin mota kwata kwata ya kasa samun nutsuwa tunda abunnan ya faru Haushin kanshi kawai yakeji da ya afkawa yarinya k'arama Why na aikata wannan me ya kaini " kwata kwata ji yayi kasarma ta fice masa a rai a take a lokacin ba tare da ya waiwayi gidanshi na Zaria ba ya wuce Kaduna password d'inshi kawai ya d'auka ya wuce Airport ba tare da bata lokaci ba jirginsu ya d'aga America. ******* Asmy banda kuka ba abunda ta ke jaber yayi Lallashin Amma a banza wajen k'arfe Ukku Da Rabi taga zarah ta fara motsi cikin Sauri Asmy ta mik'e tare da isa Inda take ta ce "Sis ki tashi Dan Allah" A hankali Zarah ta fara bud'e idanuwanta da sukayi mata mugun nauyi Harta k'arasa budesu karewa dakin kallo tayi ta tabbatar da gadon asibiti ne take kai rumtse idonta tayi abubuwan da suka faru ne suka dinga dawo mata "innalillahi wa inna ilaihiraji'un" ta shiga nanatawa "Tunaninta abunda ya faru duk mafarki ne Dan bata tab'a tunanin ko a mafarki ba Asmy zatayi mata haka Da kallo tabi Asmy dake tsaye a kanta tana kuka ta ma kasa magana " a fili ta ce "Kardai kice mun Gaskiya ne Asmy ba mafarki bane nake ,Aminiyata Dana d'auketa y'ar uwa tamkar wacce muka fito ciki d'aya za a had'a baki da ita aci Amanata a rabani da budurci na " girgiza mata kai Asmy ta fara cikin hawaye ta ce "Ki tsaya ki saurareni Zarah banyi hakan....tsawar da Zarah ta daka mata ce ta sanyata Had'iye maganar da tayi shirin fitowa daga bakinta cikin tsananin b'acin rai Zarah ta ce " Get out Ki fita bana son ganinki bana k'aunar ganinki Asmy kin cuceni kinci Amanata Allah ya isa tsakani na daku Ki fita kafin nayi maki abunda baki tunani bana k'aunar ganinki a kusa dani "ta k'arasa fad'a ta na Fashewa da kuka mai cin rai"Sosai hankalin Asmy ya tashi ta na kuka ita ma ta ce " Dan Allah ki saurareni Zarah kece shaida bazan tab'a chutar dake ba na aikata hakan ne a saboda ceton rayuwarki da kuma soyayyar da nake maki ki saurareni Dan girman Allah Zarah"wata tsawar Zarah ta kuma mata wacce ya sanya Asmy saurin barin dakin ta na kuka kai tsaye office d'in dr ta nufa ta na kuka ta ce "Ya zanyi dr Duka munyi hakan ne saboda ceton rayuwarta da kuma tsaron lafiyarta me yasa bazata fahimceni nayi mata bayani ba Dr y'ar uwata a halin yanzu babu wacce ta tsana sama dani ta ce Na tafi bata son gani na" ta k'arasa fad'a ta na durkushewa tare dayin kuka mai cin rai"Cikin lallashi dr Aliyu ya ce "Karki damu Zata huce a halin yanzu ta na cikin fushi ne kuma dole tayi fushi dake Asma'u bai kamata Kuyi mata haka ba Da kunbi ta shawara ta da zamu samu mu.lallab'ata ne har ta amince kafin komai ya wakana" ta na kuka ta ce "Dr kaifa kace one months yayi akwai matsala gudun wannan ne yasa Muka aikata hakan ya zanyi da rayuwata ne waini Zarah takeyiwa Allah ya isa" Lallashinta jaber yayi tare da cewa "tashi muje Na maidake school insha Allah za a kula da ita a halin yanzu ta na fushi dake ne Idan ta huce saiki dawo" girgiza masa kai Asmy tayi ta ce "ba Inda zanje nabar Zarah cikin halin nan jaber " Lallashinta yayi ya ce "Akwai nurse din da zasu kula da ita ganin naki ne zai k'ara fama mata ciwon rad'ad'in da take ji tunda nace maki ki taho muje karkimun musu ko so kike mutanen asibitin nan su fahimci halin da ake ciki irin kukan nan da kike" Ba dan Asmy ta so ba tabi jaber ya maida ita hostel tunda taje take kuka Chuchu duk ta damu ta isheta da tambayar ina Zarah Hakan ya sanyata yi mata karya ta ce "Tun jiya ta tafi funtua Matar babanta ce ba lfy ita kuma kukan da take batajin dadine"... Bayan fitar Asmy d'akin wani irin kuka Zarah take Tanaji daman mutuwa tayi ta huta budurcinta da take ta tsarewa tsawon shekaru take tsananin alfahari dashi tayiwa mijinta na Aure na sunna tanadi shine a halin yanzu ta rasa shi a banza wani wanda baisan darajar d'an adam ba ya amsheshi kuma Had'in kai da Aminiyarta da ta yi matuk'ar yarda da ita " A haka nurse guda biyu da Dr Aliyu ya turo suka shigo Dak'yal suka samu suka lallasheta tabar kukan Dr Sakina ta ce "sister d'an mike muga kin iya tashi?Yunkurawa Zarah tayi zata Mike Azabar zafin da taji daga k'asar ta ne ya sanyata saurin rumtse ido tare da saurin komawa ta na hawaye ta ce " bazan iya ba Dr"Girgiza kai Dr Halima dake gefe tayi ta ce "Wlh mijin yarinyar nan bashi da imani Karkiga yanda aka kawota Na zaci ma sai anyi mata dinki Allah ya taimaka Bata k'aru ba" Dr Sakina ta girgiza kai ta ce "Ai mazan ne na yanzu jira suke Allah dai ya kyauta " Zarah ta na jinsu suna hirarsu ita dae batace uffan ba a ranta ta ce "Ai da mijin nau ne ma yayimun haka da da sauki amma wani Chan katon banza tsinanne a ranta ta ce " Allah ya isa tsakanina da kai mugu azzalumi macuci Fuskarsa da a halin yanzu babu mutumin da tafi tsana sama dashi ta shiga dawo mata Drip aka k'ara sanya mata kafin Su bata magunguna ta sha bayan sun taimaka mata sun mikar da ita dukda tana rurrumtse ido toilet suka shiga saida suka kara gasata cikin ruwan dumi da dettol da gishiri sosai dukda ta na ta musu raki bayan sun gama gasata ta danji dadi kadan wanda yanzu idan ta dafa bango ta na iya tafiya da kanta ta koma kan gadon Kazar da fruits din da Jaber ya kawo a bata Dr Halima ta shiga bata da kanta Wanda dak'yal da lallashi ta samu ta d'anci . Dr Halima ce da murmushi a fuskarta ta ce"sorry ko amarya ki saki ran mana tunda da sauki Ki daure kici kazar Zata taimaka maki"cikin sanyi murya ta ce "Aunty na k'oshi Inajin kamar zazzabi zai rufeni" Tab'a jikinta Dr tayi ta ce "Subhanallahi Ga zafi nan jikinki Bari na hada allura nayi miki zata taimaka maki nan Dr ta had'a tayiwa Zarah allura dukda ta na matsar k'walla akayi allurar yunkurawa tayi zata Mike Dr Halima ta ce " ina kuma zaki Keda baki lafiya"hawaye na bin k'umcinta ta ce"alwala zanyi na rama sallolin da banyiba"Okay Kibi a hankali kinji kanwata "Gyada mata kai Zarah tayi Dan ta lura Matar Nada sakin fuska kuma ga Alamun babbace Dan daga ganinta kasan bazata rasa yara ba Saida Zarah ta rama sallolin ta gabak'i d'aya a zaune kafin ta mik'e ta koma kan gadon blanket Ta rufa mata tare da cewa" ki kwanta yanzu bari zanje na duba patient kinji"Bayan fitar Dr Halima Zarah banda hawaye ba abunda take ta na jin shigowar Jaber tayi saurin maida idanuwanta ta rufe kamar mai bacci nanko ba bacci take ba banda tafarfasa zuciyarta ba abunda take Jaber ganin ta samu bacci Ajiyar zuciya ya sauke tare da Aje ledar kayan sawa da ya sayo mata da su brush da Maclean. Kwanan Zarah ukku a asibiti wanda Dr Halima ta dinga kula da ita tamkar k'anwarta cikin kwanakin nan harsun saba da Zarah Dan ta lura Matar na da kirki Kullum sai Asmy tazo amma Zarah bata bata ma kofar da zatayi mata magana tsananin fushi take da ita marar musaltuwa yanzu taji sauk'i harma ta fara takawa zazzabin ma yanzu yayi sauki Saidai damuwa da tayi mata yawa Dan duk ta rame Yau ma da Yamma suna zaune Dr Halima na bare mata ayaba Asmy ta shigo A sanyaye Zarah ta na Dagowa ta ganta lokaci guda ta b'ata rai tare da cewa "Ficemun da gani Asmy bana k'aunar ganinki kafin nayi maki abunda baki tunani" Asmy na hawaye ta ce "Ni kike kora Zarah me yasa bazaki tsaya ki fahimceni ba," bazan fahimcekiba bazan tab'a fahimtarki ba har a bada ki Ficemun da gani tunda burinki ya cika ai shikenan ki rabu da ni karki Kara takurawa rayuwata kuma ya isa haka"ta k'arasa fad'a ta na fashewa da kuka Itama Asmy tana kuka ta ce "zan tafi Zarah bazan k'ara takurawa rayuwarki ba kamar yanda kika fada " ta fad'a ta na kuka tare da Juyawa cikin Sauri tabar asibitin "Bayan fitar asmy Dr Ta kalli Zarah dake Kuka ta ce" na tambayeki mana kanwata"Goge hawayenta Zarah tayi Dan yanzu kuma ta rage kukan Saidai na zuci ta ce "Ina ji Aunty" Me ya sanya duk sanda Yarinyar nan tazo kike korarta ta damu dake sosai matuka sannan me yasa tsawon kwanakinki Ukku Asibiti banga mijinki ko wani nashi ba ko wani naki yazo duba ki in banda saurayin nan dake hidima dake kuma na tambayeki kince ba mijinki bane please karkice na yi maki shishigi abun ne ya bani mamaki" Kuka ne ya kubcewa Zarah Dan bata da Amsar tambayar da dr Halima ke mata saida ta tsagaita kukan Kamo hannunta Dr Halima tayi ta ce "Ki daukeni tamkar yaya ko uwa Zarah Bazan tab'a yada sirrinki ba ina son taimakonkine dukda bansan ko kina da buk'atar hakan ba Amma please ina son ki fad'amun Gaskiya akan Lamarin nan ko fyad'e akayi maki??Nanma shiru Zarah bata bata amsa ba jin bazata bata amsa ba ya sanya Dr Halima rabuwa da ita. Washegari dr ya shigo Tare da Jaber a bayanshi Zarah na ganin jaber ta kauda kai Dan Shima ji take ta tsaneshi saboda ta ganeshi sarai shine Wanda ya fito daga d'akin da Asmy ta wullata Yana murmushi ya ce " Sannu ko Zarah ya k'arfin jikin"wani banzan Kallo ta watsa masa tare da kauda kai tana Jan tsaki"Murmushi sukayi shida Dr ganin yanda ta masa dr Ne ya ce "ya jikin Zarah yanzu bakyajin komai ko" Gyada mishi kai tayi ta ce "Eh Dr inason komawa gida Dan Allah ka sallameni" Zaunawa kan chairs din dake d'akin sukayi tare da fuskartarta ya ce "Yau za'a sallameki Zarah amma kafin nan Dan Allah ina son ki nutsu zamuyi magana " Kamar bazata Yi magana ba sai kuma ta ce "inajinka..... Zaune yayi a makeken Palourn shi bayan saukarsa k'asar ko hutawa baiyi ba Yayi awa guda amma baiji d'uriyar Amera ba hakan bai damesaba ba hayewa yayi stairs Bayan yayi wanka Kwance Yayi kan makeken gadonshi tare da lumshe ido Darensu na jiya ne shida Zarah ya shiga dawo mashi a kwalwa shekara Tara ya na mu'amula da Amera Amma baitab'ajin gamsuwa da ni'ima irin Ta wannan yarinyar ba mirginawa yayi yana tuno irin Zumarta da ya lasa jiya tunowa yayi da tsayayyun breast d'inta manya wanda suka fara firgitasa shi daman mutum ne mai tsananin son breast rumtse idonsa yayi ganin lokaci guda zai rikitama kansa. Lissafi tunani ya kumayi yanzu ko ta na wani hali Lokaci guda mood dinsa ya sauya Saikuma ya ce " Ai ba laifi na bane ita ta kawo kanta"ya fad'a ya na dage kafad'a ya k'ulla wannan ya since wancen a haka har wani bacci mai dad'i yayi awon gaba dashi cike da gajiya..... D'ago da rinannun idanunta tayi da suka sauya kala tsabar bacin rai tayi Bayan ta gama sauraron bayanin da Dr yayi mata Wanda takejin maganganun tamkar almara cikin tsananin b'acin rai Ta ce.........✍🏿 *07026166536 domin magana da marubuciyar* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 🅿️.........*33 & 34* "Kana nufin Dr Had'in baki kukayi batare da izini na ba kuka dauramun Aure ?daman lokacin da Asmy tayimun maganar nan kunrigama kun gama komai sannan ta fashe da kuka ta ce " Wlh Dr banyarda ba Saidai a farke.Auren "Lallashinta sosai suka shigayi cikin magana mai dadi da kwantar da hankali har Dr ya samu Zarah ta tsagaita kukan Dagowa tayi da rinannun idanunta da sukayi mata ja ta ce " ya na Ina Dr ku sa ya rubuta takardar saki ya bani kamar yanda kuka k'ulla Auren haka zaku since Dan wlh bazan iya kai tsawon wata Tara da Auren mugun azzalumi macucin mutumin nan ba"numfashi Dr ya ja ya ce "Karki damu Zarah zai sakeki Ai ba Aure bane kamar ko wanne Aure ne akayi a bisa larura insha Allahu karki damu baza akai wata Tara ba sannan ya d'ora da cewa Dan Allah karki kullaci y'ar uwarki batayi hakan Dan komai ba saidan k'aunar da take maki ki nutsu kiyi tunani Zarah Asmy bata chanchanci haka daga gareki ba" Zarah batace uffan ba Dan har yanzu Abun nan ciwo yake mata sai Mikewa da tayi Dr ya bita da Kallo ya ce "Ina zaki kuma" Hostel "ta fad'a ta na kauda kai" d'an murmushi yayi ya ce "to Malama Zarah kin Sallami kanki Da kanki kenan" Turo baki tayi batace uffan ba "Jaber ne yayi murmushi ya ce " Muje na saukeki "wani banzan kallo ta watsa masa tare da Jan tsaki ta ce" bana buk'ata "Saida ya kumshe dariyarsa Dr ne ya ce " To ni na kaiki ko nima fushin ake dani"Ta na kauda kai ta ce "Zan tari napep naje ba sai an kaini ba " da kyal Dr ya samu ya shawo kanta ta yarda shi ya kaita amma jaber firr kiyawa tayi a lokacin da Aka sallameta Dr Halima bata kan Aiki Taso suyi bankwana amma kuma bakomai ai tunda suna da number wayar juna sun dinga gaisawa. Har suka isa makaranta Zarah bata magana shine de sai zuba yake ya na bata kamalai masu kwantar da hankali akan wannan din ba wani Abu bane Tayi hakuri ta dauki hakan ba komai ba ita dai jinshi kawai take ya na sauketa Ya ce "To Malama Zarah sai ankawo mana ziyara k,o?,Wani kallo tayi mata tare da kauda kai tayi gaba batace uffan ba Dan Shima mugun haushinsa takeji shikam murmushi yayi harga Allah yarinyar na burgesa sai yanzu yake Danasanin k'in Aurenta shi da kanshi da yayi (Nikam nace Gaskiya Dr da jaber kun rainawa zarah wayau ) Zarah na isa hostel bata iske kowaba hakan ya tabbatar mata da Suna lectures Cire hijab d'inta tayi Tare da hayewa Gado Bayan ta jona wayarta chaji da tayi kwana hud'u rufe Ta na nan Kwance ba bacci take ba tunanin rayuwarta take tun daga farko tanajin zafi a cikin zuciyarta Ji take inama tana da wanda zata fadawa sirrinta taji sanyi Goge hawayenta tayi ta ce " Allah ya jikan ki Mamana ke kad'aice sirrina kuma a halin yanzu bakya raye dukda ban sanki ban san wani naki ba ko da danginki na gani da zanji sanyi a raina" Around 2pm Chuchu da Asmy suka shigo Bayan dawowansu daga lectures sosai suka yi murnar ganin Zarah da farinciki Chuchu ta ce "Kindawo kenan momcy Sannu da dawowa ya mai jikin" Dagowa tayi ta Kalleta tunani tayi wane ba lfy Hakanan dai tayi mata murmushi ta ce "Da sauki" Allah ya k'ara sauki Ai Asmy ke Cemun Matar babanki ce ba lfy "jinjina mata kai kawai Zarah tayi Asmy ce ta ce " kindawo lfy Zarah"banza zarah tayi mata tare da Juyawa ta lumshe ido kamar mai bacci sosai hakan ya bawa Chuchu mamaki Dan tsawon rayuwarta bata tab'a ganin haka tsakanin wannan y'an uwanba Dan ita duk daukarta cousin sisters ne badai tayi magana ba. Tunda zarah ta dawo bata da wata walwala sanyinta ya karu fiye da Wanda take dashi Batayiwa Asmy magana Wanda hakan sosai yake damun Asmy Chuchu ma harta fahimta koda ta tambayi Asmy me ya had'asu cewa tayi sundanyi fadane zasu shirya.... yau Zarah Bayan fitowarsu daga lectures zaune tayi bakin wani block book ne hannunta amma kwata_kwata Hankalinta baya ga littafin ta Lula duniyar tunani har abokinta Yusuf yazo ya zauna bata sani ba saida yayi mata tabi tukwana ta dawo hayyacinta kirkirar murmushi tayi ta ce "yaushe kazo" Zaunawa yayi ya ce"tund'azu naga kina ta tunani wai Me ya faru ne daughter naga kina yawan tunani kwanannan baki da walwala"Murmushi kawai tayi ta ce "Bakomai wai muna da lectures Anjima kuwa?Girgiza kai yayi ya ce " a a a malamin ya d'agata ya maida gobe da Yamma kuma ya ce C a zaiyi"okay to daman nazata za ayi shiyasa na zauna bari na wuce hostel Dan na gaji "tare suka Mike suna tafe ya na mata hira harsuka isa hostel bata iske su Asmy ba hakan ya sanya ta d'ora indomie a gas Dan yunwa takeji ta na gamaci ta lalubo wayarta ta kunna waya sosai suka sha waya da ya Hafiz d'inta Wanda duk yawaici shine mai maganar tun a wayar ya lura da Kamar bata cikin yanayi mai dadi cewa yayi wai me yake faruwa ne my Zarah kwana biyun nan bana gane maki" murmushi ta kirkira ta ce "Bakomai ya Hafiz wai saura wata nawa ka gama school din nasan ai zaka rigani gamawa" Daga bangarensa ya ce "Saura shekara daya da Dan wani Abu my amarya ko harkin kagarane kema Kamar yanda na nakagara naga zuwan ranar Aurenmu Zarah Allah kadai yasan kalan son da nake maki duk ranar da Allah ya cikamun burina muka.mallaki juna matsayin mata da miji bansan wani irin farinciki zan shiga ji nake ranar kwana zanyi ina maki kukan farinciki" sosai gaban Zarah ya fad'i tayi Sauri ta fusge ta ce "Uhm ya Hafiz kenan kuka kuma sai kace wani yaro" eh mana my Zarah ba dole nayi kukan farinciki ba Allah ya mallakamun ke.matsayin mata ked'in ai allurace a cikin ruwa "Murmushi kawai ta kirkira gabanta na fad'uwa ta ce " Uhm ina zuwa na daura girki karyayi 'kauri "tukwana ta katse in banda Fad'uwa ba abunda gabanta yake Tunani take Ya Hafiz Idan bai sameta a budurwa ba ya zatayi Bayan Ya yarda da ita 100% batasan lokacin da wasu hawaye masu d'umi zuka zubo mata ba ta ce " Allah ya isa budurcina da Wani marar sanin darajar mutum ne ya amsheshi ba ya Hafiz mai kaunata ba ,"ta jima ta na kuka. Zaune yake a palour ya na operating system Yaji shigowar Amera Ido kawai ya d'aga ya Kalleta daga sama har kasa tare da maida kanshi ga abunda yake sosai Amera tayi mamakin MD ba tare da damuwar komai ba ta k'arasa gabanshi tare da Rungumeshi ta gefe ta ce "My honey yaushe ka dawo I really miss you so much Wlh duk kewarka ta isheni" Dagowa yayi tare da kallonta fuskarshi ba walwala ya kira sunanta ya ce "Amera" Na'am my honey"ta fad'a ta na Lafewa jikinshi "Sau nawa zan hanaki shigar banzan nan kina fita da su sannan yawan nan da kike barkatai batare da izini na ba ya fara isata" Cikin shagwaba ta ce "Haba honey please me shigar nan tayi sannan baka taba yimun maganar fita da nake ba sanin kanka ne dai bazanyi abunda baida kyauba tunda kafi kowa sanin halina haba saikace dai ana zugaka fisabilillah naga kwanannan Duk nema kake ka shigo mana da dabi'un hausawa gidan nan Gaskiya ni banaso ka bari muci gaba da rayuwar turawanmu kawai" Kallonta kawai ya tsayayi da mamaki Yama rasa amsar da zai bata girgiza mata kai kawai yayi yaci gaba da abunda yake.kwabe fuska tayi ta ce "Haba honey ko dokin gani na bakayi sai wani shan k'amshi kake"Mikewa yayi ya ce " please merah ki barni ina buk'atar hutawa ya fad'a tare da barin Wajen ya haye stairs ya wuce Bedroom dinsa Ganin haka ya sanya Amera binshi ta ce "Wai meye haka Honey Sai wani chanzamun kake " MD ya ce "Amma dai na fad'a maki ina buk'atar hutawa ko ?Ta gefe ta Rungumeshi ta ce " amma dai kasan ina buk'atar hakkina ko?da mamaki ya bita da Kallo sai kuma yayi wani murmushi Alamun na mugunta.....ranar Amera ta gurzu iya gurzuwa Dan MD bai saurara mata ba kuka kam da Dana sanin me ya kaita ta shashi ba Adadi Bayan komai ya lafa ya wucewarshi toilet Bayan yayi wanka ya ya fito Gado ya tadda ita ta na maida numfashi tama kasa Tashi batare da ya ma sake waiwayarta ba ya bar gidan zuciyarshi chunkushe ba dad'i Amera ko dak'yal ta yunkura ta shiga toilet ta na Jan tsaki ta ce "mugu kawai jarababbe ko uban me ya kaini neman wani hakki wajen wannan da daman jira yake ya turmusheka da mugunta".. .. Zarah na zaune a wajen hostel ta na karatun alqur'ani Asmy ta zo ta zauna wajen Ta na kallon ta zauna Zarah ta mik'e da niyyar zata bar wajen Mikewa Asmy tayi tare da Rik'e mata Bayan hijab cikin kuka ta ce "Ko wani bazai fahimceni ba bantaba tunanin ke zaki kasa fahimtata ba Zarah bakyamun magana dakin ganni waje zaki tashi me nayi maki na baki hakuri akan abunnan da ya faru wlh tallahi Zarah banyi abunnan da wata manufa ba sai Dan Soyayyar da nake maki wacce nakejin bazan jure ganinki cikin wani hali ba ko kuma na rasaki nayi hakan ne saboda ganin shine kawai damar da ta rage mana ta k'arshe Zarah ked'in wacce muka fito ciki d'aya haka nakejinki bazan tab'a abunda zai chutar dake ba ko wani naga zai chutar dake Sai Inda k'arfina ya k'are bare ni na chutar dake da kaina Zarah ribar me zanci na rokeki Dan girman Allah kiyi hakuri ki yafemun ki daina fushin nan dani Bazan cigaba da jurar wannan fushin daga gareki ba wlh duk Naji rayuwar makarantar ma ta Ficemun a rain ki fahimci please Zarah na rokeki da girman Allah.".......✍🏿 *Domin magana da marubuciyar 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss hajo ce*_🤙🏿 🅿️...........*35 & 36* Sosai zuciyar Zarah ta karye Batasan lokacin da ta Rungume Asmy ba saikuma ta sanya kuka Itama Asmy hawaye take tare da cewa"kiyi hakuri ki yafeman Zarah"tsagaita kukanta Zarah tayi ta ce "ban kullaceki da komai ba Asmy komai ya wuce Saidai takaicin abunda ya faru yaki barin kwalwata" zaunawa sukayi Asmy ta Goge mata hawayen ta ce "Ki cire wannan tunanin a ranki Zarah Dan Allah ki d'auki hakan a neman lafiyarki ne komai ya faru kuma ai ba zina kikai ba a bisa Aure komai ya faru" murmushi mai ciwo Zarah tayi ta ce "Amma dai kinsan na rasa budurcina dame kike tunanin zanyi tak'ama dashi gidan Aure na Asmy wani tanadi zanjema mijina dashi Bayan budurcin da ko wace y'a mace mai mutunci ke San kaiwa gidan Aurenta na rasashi ga Wanda baisan Darajarshi ba" ta k'arasa fad'a ta na rufe baki sakamakon kukan da yazo mata"Rungumeta Asmy tayi ta ce "ki daina damuwa da wannan Zarah Zamuje ayi miki d'inki kafin lokacin bikin bazai tab'a fahimta ba sannan Allah zai rufa maki asiri tunda yasan da niyyar da hakan ta faru" da mamaki Zarah ke kallon Asmy ta ce "d'inki kuma Asmy kina ganin to ba matsala bazai fahimta ba" Ta na kama hannunta ta ce "E insha Allahu bazai fahimta ba bazaima tab'a fahimta ba saboda A budurwa zai sameki " Boyayyar Ajiyar zuciya Zarah ta sauke saitaji kashi Sittin na cikin Darin damuwarta ta ragu Itama Asmy Ajiyar zuciya ta sauke Zarah ce ta ce "To yanzu yaza ayi ku farke Auren nan Asmy please tunda Mai faruwa ta Riga ta faru kawai a farke " Karki damu zanyi waya da Jaber akan Baki amince da *Auren wata taran* da suke ikirarin an daura ba kawai su Aiko maki takardarki"Tsaki Zarah ta ja tana tunowa da bayanin da Dr yayi mata wai akan matarshi na karatu "Asmy ce ta kira Jaber Bayan sun gaisa tayi mashi bayani akan Suna buk'atar takardar Zarah " Da mamaki jaber ya ce ,"Amma dai kinsan ba haka mukayi dake ba Wata Tara mukayi daku please Asma'u kar a dinga maida hannun agogo baya tunda Kinga Duka abunnan taimakon juna ne akayi tunda shi ya taimaketa ya biya mata bukatarta Karku kasance masu San kanku mana Kenan shikenan ku bukatarku ta biya shi ko oho ko"Sosai ran Asmy ya b'aci.cikin tsananin b'acin rai Ta ce "to yi mana Gori jaber sannan bazamu yarda da wani *Auren wata Tara* ba dole ne zai saketa komai zakuce Saidai kuce a lokacin ma tashin hankali ne ya sanya har na Amince muku Dan haka wlh dole ya saketa " Daga bangaren jaber Shima cikin b'acin ran ya ce "Daman ance d'an adaman butulu tunda munbiya muku bukatarku y'ar uwarki ta fita daga halin mutuwa ko rayuwa dole ki fad'i haka" Zarah ce ta Goge hawayen dake zubo mata Dan tanajin komai amsar wayar tayi tare da cewa"Allah ya kaimu wata Taran da rai da lfy "Sannan ta katse kiran kallon Asmy tayi dake huci ta ce " ki rabu da su sis yana da Gaskiya tunda kin Riga kunyi yarjejeniya Kinga harya farayi mana gorin sun biya mana buk'ata ki rabu dasu Allah ya kaimu wata taran"Sosai Asmy tayi sanyi ta ce "Amma dai Zarah ai basubi ba ta yanda zamu amince ba farawa da iyawa Anfara da kwanciya gadon asibiti na tabbatar da karfi yabi dake please ki barni dasu daidai nake dasu" A ranta Zarah ta ce "Inma kasheni yayi aike kika jamun tunda da baku had'a baki kin turani d'akin ai da haka bata faru ba a fili kuma cewa tayi " kawai kibar maganar ta wuce ki barsu wata taran,"Asmy ce ta ce "To shikenan sadakinki fa 500k na account d'ina na tura miki ko?cike da takaici Zarah ta ce " kibarsu a account d'in naki sakin hirar sukayi Dan Zarah bata ma son yawan firar...."Daga ranar Asmy da Zarah suka shirya kamar basu tab'a samun sabani ba Chuchu ma taji dad'in shiryawar tasu dukda batasan dalilin da ya had'asu fad'a ba....yau perioud din Zarah yazo Wanda sosai tayi mamakin neman ciwon mararta da tayi ta rasa sai Kad'an Kad'an da takeji Asmy ma sosai taji dad'in hakan Zarah ko sai yanzu ta k'ara gaskatar da maganar Dr d'in da duk daukarta Had'in baki ne kawai kwance tayi Kamar mai bacci nanko tunani ne kawai ta ke saitaji damuwarta duk ta ragu Cikin kwana Ukku Ta gama perioud dinta hankali kwance ita kanta hankalinta ya kwanta Asmy ma sosai hankalinta ya kwanta Dan tsoranta Allah tsoranta ace Ciki ya shiga Dan tasan sau d'aya ma.ana iya d'aukar ciki itakam Zarah Daman ko Kad'an bata kawo wannan tunanin a ranta ba ta cigaba da harkokinta tayikamar komai bai faru ba nan ko abun yana nan k'asar zuciyarta... MD na Kwance around 9:50pm yaji kiran jaber kamar bazai d'auka ba sai kuma ya d'auka daga bangaren jaber ya ce "Bloody bansanka Da Rashin tausayi ba a sanin da nayi maka Kayiwa yarinya irin wannan Abun Dan Rashin tausayi Ka tsallakema kabar k'asar kaje Chan kaci gaba da rayuwarka ita ko oho ko wani hali ma ta shiga kenan ko,to yanzu ka na neman ka bata mana shirin da mukayi Dan wlh daga wannan Karin kuma bazan k'ara sa baki na a case dinka ba Inma y'ar kauye Hajiya zata aura maka Saidai ta aura maka wlh ga babbar dama ta sameka kana wasa da ita ya rage naka sauran sannan harsun fara zancen ka sake ta dak'yal na samu na lallaba dukda bansan sun hakura ba ko oho"tsaki MD yaja cikin d'aga murya ya ce " To saime Jaber Mtwsss a saketa din mana kowa ya kama gabanshi Dan ni hankalina ba wani kwanciya yayi da wannan Auren ba"Da mamaki jaber ya ce "Oh haka kace kenan okay yayi kyau ina jiran sakin Alhmdll daman haka nakesonji kowa ya kama gabanshi kuma na fitar da hannu na Daga Lamarin nan daga yau" ya na Gama fad'ar haka ya katse kiran"MD ko tunani ne ya shigayi"Tabbas gaskiyar jaber ne wannan dama ce ta k'arshe idan baiyi abunda ya kamata ba yanaji yana gani Hajiya kaka zatayi abunda taga dama a kanshi"To yanzu yaza ayi Bayan yarinyar yasan fushi take dashi"Tsaki yaja mood d'insu na ranar ya shiga dawo masa lokaci guda kuma yaji wani fitinannen feeling na taso masa harga Allah bai isa yayi karyaba a mu'amularshi da yarinyar yasan meye gamsuwa rumtse idonsa kawai Yake Kallon Amera yayi dake gefenshi tana bacci Tare da rungumota ko Dan ya rage zafi cikin bacci Amera taji irin abunda MD keyi mata cikin Masifa ta ce "Wai meye haka honey bacci fa nake meye haka Kasan dai a gajiye nake tunda na kwanta tun 10pm " MD da a matuk'ar bukace yake kwantar da murya yayi yana kissing d'inta ya ce "Please my merah help me I need you ki bari Kad'an zanyi" ya fad'a cikin Wata irin kasalalliyar murya Amera ko Mikewa tayi tare da cewa "nidai wlh na gaji Haba Ayi mutum bashi da aiki sai Abu d'aya wannan jarabar dame tayi kama.shekara Tara ai yaci ace yanzu ka fara hakura da abunnan kai dama baka gajiya" ta fad'a cike da Rashin kunya"MD ko ranshi ne ya b'aci sosai Cikin fad'a ya ce "Get out Ki fitarmun daga daki Kuma ki rubuta ki Aje daga rana irin ta yau Bazan k'ara neman wani Abu wajenki ba zakisan ni in d'ane ki jika jikin naki kisha me nake moruwa da jikin naki daman stupid kawai marar Ilimi ko aikin Ubanme kikayi da zakice kin gaji in banda yawan birthday da dinner da yawo gidan kawaye da bama musulmai ba ubanme kika iya ibadarma yinta kike yanda ya kamata "kuka Amera ta fashe dashi Tare da cewa " Ni kake cewa haka yau MD Daman nasan zuga ka ake kwanannan kakemun Rashin mutunci to duk ubanda ke zuga ka dinma zanganshi sannan jiki ai nawa ne kuma nace banaso daman ance d'an Adam butulu shekara Tara kana moruwa dole ka fad'i haka idan bani ba wace mace ce Zata zauna dakai a irin wannan yanayin naka kullum Abu d'aya ba sassautawa in banda ina da kwarin arziki ta tuni ban rarakeba To wlh bazan iya ba Ai bani kadai bace mace a duniya"ta k'arasa fad'a ta na Jan tsaki"Idan ran MD yayi dubu ya b'aci baisan lokacin da ya wanke ta da Mari ba tare da nuna ta da yatsa ya ce "Ni kike fad'awa haka Amera Dan baki da Ilimi mijinki na Aure na sunna Aiko zakisan na haihu zakisan ni d'ane sannan zakisan ba ke kad'ai bace mace a duniya " Sosai Amera ta tsorata da mijin nata abar kaunarta Tsawa ya k'ara daka mata ba shiri ta bar d'akin hada tuntube MD ko ranshi ne yayi mugun b'aci ranar bacci sai barawo yana dawowa daga Sallar asuba Bayan yayi wanka Ya shirya tare d'aukar password d'inshi ya bar gidan Gaba d'aya baima waiwayo Amera ba Dan ta gama bata masa rai Kai tsaye Aiport ya nufa. zaune take Gaban Lecturer d'insu Bayan kiranta da yasa akayi tunda Ta shigo tayi k'asa da kanta ta na wasa da y'an yatsun hannunta shiko wani irin kallo yake binta dashi Na kurulla har wani Had'iye yau Yake "ya ce " Zarah Yusuf ko"?eh"ta fad'a gabanta na fad'uwa Dan kar ace wani abun tayi "Murmushi Sulaiman yayi ya ce "Ki saki jiki mana sai d'ari_d'ari Kike Ni ba mutum bane mai tsanani ina da saukin kai daman Kiranki ne nayi Dan na fad'a maki sirrin dake zuciya ta a Gaskiya Zarah tun sanda kika shigo makarantar nan Naji kin kwantamun arai nake sonki soyayya ta Aure bata yaudara ba Tun kina aji daya naso Na fad'a maki amma kwarjinin da kikemun yasanya na kasa Sai yau Allah yayi na fallasar da sirrin zuciya ta fatan za'a amshi tayina hannu bibbiyu" sosai Zarah tayi mamakin jin maganar da ta fito daga bakinshi da mamaki take binshi da Kallo tama rasa abun cewa sai k'asa da kanta da tayi gabanta na fad'uwa Suleman ya ce "Yadai kinyi shiru Zarah ko baki amshi tayin da nayi maki bane" Batasan lokacin da ta furta Kalmar "zanyi tunani tukun" ta na gama fad'ar haka tabar office d'in gabanta na fad'uwa "kawayenta ne hibba Da Jamcy da suka rakota suna ganinta sukayi kanta hibba ta ce " Lafiya me ya ce maki naga kin fito a rikice kinsan mutumin nan ba mutuncin kirki ya isheshi ba"Ajiyar zuciya Zarah ta sauke tare da cewa "Kudai kawai muje wlh abun yaban mamaki wai mutumin nan zaice ya na sona" wara idanu sukayi a tare suka ce "so " Sai Kuma hibba tayi Dariya ta ce "chab Wlh ki amince masa idan ba haka ba Zai Kadake a last paper baida mutunci wlh kuma d'an iskane na Bugawa a jarida haka sukayi Da wata budurwa yayata ta na bani labari daga tak'i amince masa wlh Ya kada ita a last paper kuma da gangan Dan Ance kokari gareta" wara idanu Zarah tayi ta ce "Na shiga ukku kuma shine kike cewa Na amince masa Bayan kinsan d'an iska ne " jamcy ce ta dafa ta ta ce "Karki damu ai ba kowa ake Kalla ayima zancen iskanci ba yanzu dai fad'a mana yanda kukayi dashi...nan ta basu labarin yanda sukayi hibba ta ce " To wlh tunda kikaji ya ce Aurenki zaiyi ki rabu dashi bazai maki zancen banza ba sannan kuma yana ganinki amerar makaranta kinsan ance d'an iska baya Auren y'ar uwarta y'ar iska Shima tagari yake nema wlh da gaske yake Dan tun sanda ake lecture na lura da irin kallon k'urullar da yake maki nasan sonki yake ki rabu dashi kawai kuyi soyayya "tab'e baki Zarah tayi ta ce"Bama sai Inda ya k'ara gani na ba.....Koda Tabawa su Asmy labari suma irin yanda Su hibba suka fad'a mata haka asmy ta bata shawara ita dai jinsu kawai take Amma batajin zata iya soyayya da wannan Bayan akwai baikon Aurenta da Hafiz (Nikam nace again kuma ga auran md akanki)Chuchu kuwa cewa tayi"Karki biyeshi momcy bazai kada ke ba Inma ya kada ke ai akwai Allah Duk mutumin da Akace Dan iska ne kaji tsoransa kinganninan bana k'aunar Dan iska shiyasa ko huld'a banayi dasu tunda nazo makarantar nan ba kowa nake abota dashi ba Saboda tsaro ku kadaine zance aminai na kuma Dan na yarda daku 100% na tabbatar kudin mutanen kirki ne kuma tare na daku na k'aru da abubuwa Dan haka Ina baki shawarar kawai kice masa an sanya miki Aure a wuce wajen"Zarah ta ce "Daman Chuchu duk jinsu nake wlh shawararki ita ce shawarar kirki sai sannan Asmy ta ce " Kuma fa hakane "a zuciyarta Asmy ta ce " Astagfurillah to ya matsayin Auren nan na Zarah yake a musulunce laifi ne tayi mu'amula da maza"wata zuciyar ta ce "Mata ai Aure duk Aure ne ko wayar da take Da hafiz haramun ne" Sosai taji gabanta ya bada daram Zarah ko bata tab'a kawo wani Aure a kanta ba harkar gabanta kawai take Dan mancewa ma take da wani Aure a kanta Dan bata d'auki Auren Aure ba dukda ta na da ilimi....Yau Zarah ta shirya tayi kyau sosai Cikin doguwar rigarta Abaya Black mai shegen kyau hijab ta d'auko zata sanya Chuchu ta rik'e hijab tare da cewa "Haba Momcy kici gayun nan ki sanya hijab Allah ban yarda ba gyale zakisa ai ba matsatsun kaya bane sannan Ko larabawa ai sanyawa suke har suyi salla ma dashi please ki yafa gyalen wlh sai kinfi kyau" Badan Zarah taso ba dole ta yafa gyalen nanko Chuchu ta shiga koda da tana cewa "Wow Momcy wlh kin hadu yanda kikasan wata first Lady taho muyi hoto ta fad'a tana shiga snap" Murmushi kawai Zarah tayi nan ta shiga kashe musu hotuna masu kyau chuchu ce ta ce "Wlh momcy karkiga yanda kikayi kyau aikedin Matar manya ce wlh ba yara ba da yaya na kika dace bada kowaba" Harararta Zarah tayi ta ce "ba nace ki daina had'ani da Yayan naki ba ni ta Hafiz ce ta fad'a tana mata far da ido" Dariya Chuchu tayi ta ce "Ki dai bar cika baki kika sani ma ked'in ko rabon Yayan nawa ce Saikiga Hafiz dinma ya mutu" Wara idanu Zarah tayi tare da Kai mata Dukan Wasa a baya ta ce "Ta Allah ba taki ba muguwa Ya Hafiz dina bazai mutuba sai yaga ma Auren jikokinmu" Dariya Chuchu tayi ta ce "Ah su jikoki manya sai mu gani Har na hangoki gidan yayana " Sanin Zarah ta biyewa Chuchu sai ta fasa fitar ya sanyata girgiza kai kawai ta fita ta ce "Dan yanzu Sauri nake ai zan dawo tare da fita daman Asmy ta fita yi musu chefane kai tsaye napep ta Tara Inda ta fad'a masa sunan unguwar da zai kaita kamar yanda Dr Halima ta turo mata sunan unguwa ta na isa Ta kirata ta ce " Aunty na iso nan tayi mata kwatancen Inda take"Dr Halima ta ce "okay ga yarinyata nan zata zo ta taho dake" Zarah na nan tsaye taga wata yarinya da bazata wuce sa'ar khairat din gidansu ba Ta na ganinta ta gane y'ar Dr Halima ce saboda kamar da suke Yarinyar ta gaishe da Zarah ta amsa mata da murmushi Tare da kama hannunta har suka Isa gidan Cikin mutuntawa Dr Halima ta tari Zarah tare da cewa"oyoyoyo Amarya Yau dai Allah yayi Gaki a gidana "Murmushi Zarah tayi tana zama ta ce " ina yini Aunty munsameku lfy"Alhmdllh Zarah ya kwana da yawa kin bace ko ya amarci"Murmushi kawai Zarah tayi ta na kasa da kanta kafin kace me an cika mata gabanta da abubuwa har mamaki tayi irin tarbar da aka mata Inda Dr Halima ta tsareta saida ta cicci wasu sosai Zarah ta yaba da kirkin Matar wajen magriba Zarah ta ce mata zata tafi sosai Dr Halima ta cikata Da abubuwan Arziki su turarruka masu kamshi sai Godiya take mata akan ziyarar da ta kawo mata ita dai murmushi take har waje ta rakota tare da cewa"A dai cigaba da hakuri Zarah zaman Aure d'an hakuri ne Sannan ki dinga yiwa mijinki biyayya Allah babu ruwansa da bakyason Auren zai kamaki da laifin hakkin mijinki muddin kina tauye masa"da mamaki Zarah ta d'ago ta na kallon Dr Halima gabanta na fad'uwa ta ce "Dr kina nufin kinsan komai " Ganin yanda ta rikice lokaci guda ya bawa Dr Dariya ta dafa ta ta ce "Baki d'auke ni y'ar uwa ba kenan ina son ki daukeni yar uwa a garin Nan kamar yanda dr aliyu ya fadamun bakisan kowa nan garin ba Aure ne ya kawoki sannan shima mijin aiki ne ya kawoshi garin Zarah Ai Dr ya fad'amun komai ya ce " Auren ne bakiso shysa ma ranar Har hakan ta faru kiyi hakuri ki zauna da mijinki lfy kinji kanwata "Boyayyar Ajiyar zuciya Zarah ta sauke a zuciyarta ta ce " Dr d'innan Allah ya hore masa iya tsara karya Munafiki da Aikin lawyer ko jarida ya dace bada Asibiti ba a fili kuwa murmushi tayi ta ce "Insha Allahu Aunty ki koma zan samu abun hawa" To nagode a gaida mai Gidan nima saina shigo gidan naki insha Allah"sannan ta mik'a mata 500 tace gashi kiyi abun hawa"Kin amsa Zarah tayi ba yanda batayi da itaba amma taki amsa Cikin unguwar taci gaba da tafiya Dan bataga Alamun samun abun hawa nan kusa ba ga kiraye kirayen magriba da Aka fara tana cikin tafiya Taji parking d'in mota bayanta bata waigaba saboda a matuk'ar firgice ta ke "keeeee" Ta ji anfada Wanda ya tabbatar mata da ita ake da wata zazzak'ar murya Saurin Juyawa tayi Ganin fuskar da bazata tab'a mantawaba da ita ba a rayuwarta ya sanya gabanta fad'uwa tare karawa saurinta volume Binta yayi yana kiran keeeee amma bata waigo ba Zarah batayi aune ba saiji tayi anyi charab an d'auketa wutsil wutsiltu ta fara tana yagushinshi tuni hawaye harsun wanke mata fuska ta ce "Meye haka Malam ka ajeni " Baimasan tanayiba bai direta ko ina ba sai Gaban mota tare da rufewa ya zagaya tashiga driver sit ya tada motar a guje yabar wajen.....✍🏿 _Ki saya da zuciya daya y'ar uwa Dan girman Allah kar a fitarmun da Littafi kud'in karantawa kuka biya ba na mallaka ba_ *07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️...........*37 & 38* Amota ba abunda Zarah take in banda kuka har suka isa gidan jin an tsaidar motar ya sanyata saurin Dagowa da idanunta da suka gaji da kuka Kallonshi tayi taga yana shirin fita cikin Sauri ta riko hannunshi tare da fashewa da kuka ta ce "Dan girman Allah bawan Allah ka maidani Inda ka daukoni " Kallonta MD ya tsayayi Tsaki yaja a ranshi yace "Yarinyar nan case Ce tazo ta ishi mutane da kuka mtwss" ba wasa fuskarsa ya ce "fita ki biyoni" sakin hannunshi tayi tare da hade rai Ta Goge hawayenta ta kalli gefe tana kumburi ta ce "ba Inda zani saika maidani Inda ka daukeni " Fita MD yayi tare da zagayawa ya bud'e side d'inta ya ce "Bazaki fito ba kenan" Kauda kai tayi ta ce "ba Inda zani akanme ka ganni a titi kawai ka satoni inba kidnapping Dina zakayi ba "mamaki yayi ganin yanda yarinyar ke masa magana kai tsaye ba wani shakku ko tsoronsa ba yunkurawa yayi zai d'auketa ganin haka ya sanya Zarah saurin fitowa har kamar ta fad'i "Gaba yayi ta na biye dashi Dukda bin da take din na tsoro ne Dan ba zata manta da gidan ba Ga kuma duhun magriba da ya fara kasancewar ya rigata shiga koda ta shiga Zaune ta samesa a palour ya hakimce ya lumshe ido kamar mai bacci cikin b'acin rai Zarah ta nufi Inda yake tare da kama k'agu cikin jarabar da bata San ta na da ita ba ta ce " wai Malam me kake nufi da ni ne ka maidani Inda ka daukeni dare nayi"Yi MD yayi kamar bada shi take ba dukda ya na jinta "Sosai hakan ya b'atawa Zarah rai cikin daga murya ta ce " da kai nake fa"Dod'e kunnanshi yayi tare da bude idanuwanshi ya sauke a nata da itama din shi take kallo Ya ce "Karki lalatamun Kunne kin isheni da ihu please"Kallonshi ta tsayayi da mamaki ta ce " to in bakason na lalata maka kunne ka maidani mana "sosai MD ya fara gajiya da maganganunta hakan ya sanyashi Mikewa tare da wucewa bedroom dinsa batare da ya waiwayeta ba hakan sosai ya Kara k'ona ran Zarah tsawon rayuwarta ba a tab'a mata rainin wayau irin haka ba kwafa tayi tare da Jan tsaki ta nufi kofa Ga mamaki koda ta murda a rufe taji dube dube ta fara ina zataga makullin amma babu hawaye nabin kumcinta nan ta zauna tana ta sak'e sake a ranta shin me mutumin nan yake nufi da ita zai wani satota ya kawota gida daga ita saishi inbanda tsabar iskanci da rainin hankali tafi minti goma tana sak'e sake ganin bai fito ba Kuma ba alamarsa ya sanyata ta bishi d'akin da ya shiga ta murda handle din taji a bud'e kutsa kanta tayi koda ta shiga Salla ta tarar dashi yanayi sai sannan ta duba hand bag d'inta tare da dauko wayarta ta duba taga har 8 ga missed call din Asmy har hudu tsaki taja dan duk asmyn ta janyo mata wannan alk'ak'aid'in lura tayi harma anyi isha'i kenan itama Sallar takeso tayi amma Babban kwanciyar hankalinta ta koma hostel Ta na nan zaune har ya gama sallolinshi ya Mike Zai fita Binshi tayi tare da hade rai Ta ce "Wai kai kurma ne da zanyi ta maimaita maka magana d'aya ne ka maidani Inda ka daukoni" Ba tare da MD ya Kalleta ba Kuma bai tanka mata ba yabi ta gefenta ya wuce ta nan tsaye ranta in yayi dubu ya b'aci taga dawowarshi rik'e da Take away guda biyu Ta gefenta ya k'ara rabawa yabi ya wuce Kan Table din dake gefen gadonshi ya Aje take away din tare da janyo plate din da ya shigo dashi ya juye priderice lafiyayya da tasha vegetables cinyar Kaza a sama Kallonta yayi da tayi tsaye tana banka masa harara yayi tare da cewa "Zo ki d'auka" Harara ta banka masa tare da Jan tsaki ta ce "Bazanci ba na sani ma ko poison ka sanya mun naci na mutu to bazanci ba Kuma kazo ka budemun kofa na fita" bataga alamar ko jin Haushi a tattare dashi ba sai gani tayi ya d'auka ya faraci yanda yake cin abincin cikin salo ita kanta saida ya bata mamaki saikace wata mace tana ganinshi ta gefen ido Rabi ma baici ba taga ya Aje tare da rufewa da wani plate din fresh milk ya tsiyaya a cup tare da Fara sha Bayan ya sha ruwa ta na nan tsaye taga ya Mike tare da cire jallabiyar dake jikinsa Ya rage Dagashi sai singlet da gajeran wando saurin kauda kai tayi saboda wani irin yanayi da ta tsinci kanta bata tab'a ganin namiji haka ba saurin rumtse idonta tayi Dak'yal ta iya control d'in kanta Ta bud'e idonta satar Kallonshi tayi taga harma ya haye kan bed yana latsa waya a ranta ta ce "Daga d'an iska sai mutumin nan Baikoji kunyar zama Haka a gaba na ba Kodan Indiyawa ba kunya ta ishesu ba a ranta ta ce " daka Kalleshi kaga Ba indiye to ya akayi kuma Naji hausa radam a bakinsa tsaki taja a ranta ta kuma cewa "Ina ruwana ma mtwwss" Dak'yal ta iya d'aga baki ta ce "Malam wai me kake nufi da nine ka tashi ka budemun na koma gida" a ranshi yaja tsaki ya ce "Sudai mata duk Inda suke matsala ne Mtwsss idiot tana neman ta samun ciwon kai" Bai ce mata uffan ba cikin daga murya ta ce "Wai mahaukaciya ka maidani kome dakai nake magana fa " Dagowa MD yayi Dan ranshi ya fara b'aci kallonta yayi tare fito da makullin motarshi dake gefenshi ya ce "Zoki amsa" Zarah har ranta ta d'auka makullin ne zai bata Aiko cikin Sauri ta matsa tare da mika hannu da niyyar Amsa taji ya Fard'o ta ta fad'a jikinsa Wani shock ne ya ziyarce su gabak'i d'ayansu musamman MD da yaji tudun manyan na shanunta na gogar k'irjinshi Zarah ko dak'yal ta iya d'aga baki ta ce "Meye haka ka sakeni bansan iskanci fa" Kamar maiyin rad'a ya ce "Abunda kike so ne zanyi miki Shine kika kasa cewa nayi maki kika isheni da Haushi bari na taimaka maki ya fa'da yana kokarin Rabata da rigar jikinta " Tuni hawaye harsun wanke mata fuska ta ce "Wlh ni banas...bata k'arasa fad'a ba sakamakon Jin bakinsa da tayi cikin nata sosai ta tsorata da irin tsotsar da yake yiwa bakinta jin hannunshi cikin rigarta yana wasa da na shanunta jikinta ya mutu tayi lakwas sosai take amsar sak'on nashi sosai Abun keyi mata dadi Hartama mance da Wanda take tare romance d'inta yake sosai Cikin salo da kwarewa Wanda sak'on sosai yake shigar Zarah Ta Riga ta ruftiya batasan lokacin da ta fara mayar masa da martanin da batasan ma ta iya ba hakan ba k'aramun Kara rikitar da MD yayi ba iya rikicewa sun zauce bakajin komai ga nishi da gurnaninsu a D'akin Sundau tsawon lokaci suna romance Din juna kafin labari ya sauya Salo Sosai Zarah ta fara kuka Dan sai sannan ta dawo cikin hayyacinta Sosai MD yake Abu d'aya batare da kakkautawaba tun 8 na dare shine bai tashi a kanta ba sai 10pm sannan ya samu gamsuwa lokacin Zarah Tayi kukan harta gaji Dan wannan lokacin ma taji azaba dukda bata kai ta first night dinta ba Bayan komai ya lafa mirginawa MD yayi yana maida numfashi Zarah ko Tama gaji da kukan hawaye kawai take a ranta tana ja masa Allah ya isa dak'yal ta yunkura ta mik'e ta shiga toilet ruwan d'imi ta had'a ta shiga saida ta gasa jikinta sosai kafin tayi wankan tsarki ta fito tana tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ganin idonshi lumshe kamar mai bacci ya sanyata saurin cire towl din tare da mayar da doguwar rigar jikintaba ta yafa beil din irin nad'in larabawa a dardumar da ta gani shinfid'e ta tayar da salla saida tayi magriba Har isha i ta na cikin nafilfilu bacci na wartarta tana Tasbihi a haka har baccci barawo ya saceta a kan sallayar duk abunda take MD akan idonsa saida yaga har bacci ya d'auketa kafin ya Mike toilet ya fad'a Bayan Shima yayi wankan ya fito ya shirya cikin shigar bacci Kallonta ya tsayayi yanda ta takure waje guda kamar bazai tab'ata ba sai kuma ya yunkura a hankali ya d'auketa tare da kwantar da ita kan gadon yayi mamakin yanda bata tashi ga Alamun ta na da nauyin bacci kwance yayi kan Doguwar kujera wani bacci mai dad'i yayi awon gaba dashi Wanda ya jima baiyi irin sa ba........lokacin da ya tashi Tuni gari har ya fara Haske sosai yayi mamakin makara sallah da yayi duba Agogon bangon dake manne a d'akin yayi Yaga har 7:16am cikin Sauri ya Mike Tare da shiga toilet Ya dauro alwala Bayan ya gama salla kallonta yayi da har lokacin Bacci take Tsaki yaja tare da karasawa Inda take Da Hannu ya bubbugi kafarta tare da cewa "Keeeeee" Cikin gigin bacci Zarah ta tashi Dan ba k'aramar gajiya ya Tara mata ba dak'yal ta iya Mikewa da Addu'ar tashi daga bacci a bakinta tare da Yin wata irin mik'a gabak'i d'aya ta bankaro da kirjinta saurin kauda kai MD yayi Dan muddin yaci gaba da kallonta akwai matsala tsaki yaja a ranshi Dan daukarshi da gangan tayi itako bama tasan da wanzuwarshi wajenba Saida bacci ya saketa kafin ta Kalleshi Sai Kuma ta kauda kai tana jan tsaki MD yajita sarai ya nuna baiji ba saboda tsawon rayuwarsa Ba abunda ya tsana sama da ayi masa tsaki Toilet ta shiga Bayan tayi alwala tana gunguni ta fito najin haushin makara salla da tayi Bayan ta gama salla ta zauna tana lazumi tana idarwa ta mik'e taga harya fita zaunawa tayi tare da Yin tagumi Tana karewa d'akin kallo Hankalinta ne ya kawo mata su Asmy kila na chan suna nemanta ga wayarta silent take Jakarta ta hango Chan kasa cikin Sauri ta k'arasa tare da daukowa ta dawo ta zauna tana fito da wayarta wara idanu tayi ganin missed call d'in Asmy kusan sha biyar har wajen karfe ukku ana kira ga na Chuchu ma Yafi goma Banda na Hafiz Shima rututu gabanta ne ya bada daram To me ma zata ce Musu ina zatace ta kwana tsaki taja ta ce mugu azzalumi kawai ya satoni Dan zalinci tana juyi da wayarta kiran Hafiz ya shigo kamar bazata dauka ba saikuma ta d'auka cikin sanyin murya tana ji daga bangarensa ya sauke ajiyar zuciya Tare da cewa "My luv ina kika sanya wayar jiya nayi ta kira Baki d'auka kinsan kin sabarmun sai Naji muryarki nake iya Bacci "cikin sanyi ta ce " Sorry ya Hafiz nayi bacci ne da wuri jiyan ina kwana"Lafiya qalau my love fatan kin tashi lafiya "Alhmdllh yau baka da lectures safe ne " Yanzu nake shirin Tafiya Hankalina bai kwanta bane sai yanzu ya kwanta da Naji muryarki gimbiyar tawa "kasaitaccen murmushi ta saki Wanda ya lotsar da dimples d'inta " Daidai shigowar MD da leda a hannunsu kallo d'aya yayi mata yaga yanda take magana kasa kasa tana murmushi Ledar ya Aje tare da Yin hanyar fita kamar bashi yayi maganarba ya ce"Idan kin shirya kya iya fitowa "bai jira me zata ce ba ya fice katse wayar Zarah tayi Bayan sunyi bankwana taje ta daga Ledar daya shigo da ita latsetsiyar doguwar Riga ce mai.kyau da gyalenta sai brush da kuma take away din Indomie da kwai" tsaki taja tare da cewa "ko wa yace masa ina buk'atar Wasu kayan inbanda tsabar kinibibi har wata indomie ce a take away " ta fad'a tana kuma Jan wani tsakin Brush tafarayowa Bayan ta fito ta Dauki indomie d'in taci Dan yunwa take ji cikinta banda karan yunwa ba abunda yake Tana gamaci cikin minti baifi sha biyar ba tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar daya sayo mata ta ninke tata tare da sakawa cikin Ledar waccen wayarta da d'auka ta hand bag d'inta ta rataya Bayan ta yafa beil din rigar sosai rigar tayi mata kyau ko madubi bata tsaya duba ba ta fito Zaune ta tarar dashi Da kayan exercises jikinsa yana rik'e da remote hankalinshi na kan tv gefenshi taja tsaya ta hade rai kamar bata tab'a Dariya ba Shiru tayi batayi magana ba Ganin Shima bazai yi mata magana ba agogon dake manne a palourn ta duba taga 8:40 gashi 10 take da lectures ya sanyata cewa "ka budemun Na tafi ina da lectures " Baice mata uffan ba kusan 5 minutes hakan sosai ya k'ara Kular da Zarah Chan kuma taga ya Mike yayi Hanyar Bedroom dinsa ta na tsaye ta cika tayi Fam gajiya tayi da tsayuwar ta zauna ta sawa sarauta Allah ido tayi tagumi Ba ayi 10 minutes ba Taji fitowarshi Ta gefen ido ta Kalleshi taga ya shirya cikin wasu K'ananan kaya kauda kanta gefe tayi hanyar kofa taga yayi tare da cewa "follow me" Yayi ficewarsa tsaki taja ta ce "Aikin banza Sai wani shan k'amshi Da gadara da isa yake saikace ba shine jiya ya gama....saikuma ta rufe bakinta ta tashi cikin Sauri tabi bayansa Parking space Taga ya nufa Tana nan tsaye har yazo Inda take daidai Inda take Ya tsaya Tare da bude mata front sit ta ciki Ajiyar zuciya ta sauke Tare da shiga Suka d'auki Hanya cikinsu bamai cewa uffan " Ina ne Inda kiken"ta tsinkayi muryarsa "tana kauda kai ta ce " A B U"Daga haka ba Wanda ya k'ara cewa uffan har Suka isa Bud'ewa tayi ta fita tare da banka masa kofar da karfi kamar zata karye tayi gaba da Kallo ya bita Tare da Jan tsaki Ya ce "Stupid Matsala kawai"Allah ya sanyama tinted ne motar ba Wanda yasan shine ya juya yabar sch din. Zarah ko tana fitowa daga motar taci.karo da Asmy da Chuchu Alamun sun fito daga lectures Bin motar da Kallo Chuchu tayi Itama Asmy haka Zarah ko gabanta saida ya fad'i ganin irin yanda Chuchu kebin motar da Kallo Har sukaga ficewar motar daga wajen da mamaki suke Kallon Zarah Chuchu ce tayi k'arfin halin cewa ..✍🏿 07026166536 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️.............*39 & 40* "Ina kika shiga tun jiya hankalinmu tashe munyi ta kira bakya d'auka kuma yanzu motar waye naga ya saukeki momcy hada sauya kaya" Banda fad'uwa babu abunda gaban Zarah yake wannan tirkiya da Chuchu ke shirinyi mata Asmy ce tayi charab ta ce "Ohh wai ko uncle Abba ne yazo Naga motarsa ce" Cikin Sauri Zarah ta ce "Eh eh shine yazo jiya nafita ya kirani ya ce yazo garin shine ya tafi dani Funtua muka gaisa dasu Aunty Yau ya maidoni saboda lecture" Ajiyar zuciyar Asmy ta sauke ta kalli Chuchu ta ce "k,'anin mahaifinta ne" Ajiyar zuciya Chuchu ta sauke ta ce "Ayya Allahsrk ai da kinkiramu momcy karkiga yanda na damu"Zarah ta ce " wayarce A silent kuma ina zuwa ban waiwayeta ba shiyasa "Chuchu tace " Allah sarki "wayarta ce tayi ringing dubawa tayi ta ga Yayanta cikin Sauri ta d'auka "basuji me akace mata daga dayan bangarennasa sai tsalle suka ji ta daka tare da Cewa " Da gaske Yaya na gani nan yanxu yanzunnan Dan Allah karka tafi"yana katse wayar ta kallesu cikin d'oki ta ce "yayana ne ya shigo garin yace bazai Iso ba nan na samesa a Hanya bari nayi Sauri karya wuce ta fad'a tana barin Wajen batare da ta jirayi amsarsu ba " tana tafiya a tare suka sauke ajiyar zuciya Asmy taja hannun Zarah suka wuce hostel ko zama basuyi ba Asmy ta ce "Ina kika kwana Zarah"... Nan Zarah ta fad'a mata abunda ya faru " Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Wlh hankalina duk bai kwanta ba sai yanzu " Allah ya sanyama nayiwa Chuchu dabara Dan kartayi miki wata fassarar ta daban "Uhm kawai Zarah ta ce tare da kwanciya ta lumshe ido " Da damuwa Asmy ta kama hannunta ta ce "Are you okay Dia Bakyajin komai " Gyada mata kai Zarah tayi ta ce "Am okay" Asmy ce ta ce "Amma dai kinyi Amfani da maganin hana d'aukar ciki ko?cikin Sauri Zarah ta mik'e gabantane ya bada daram ta dafe daidai saitin zuciyarta ta ce " Na shiganga bansha ba wlh kina ganin sau dayan nan saina iya d'aukar ciki"Asmy ta ce "Chab Aiko wlh mu nemo ki dinga sha Dan Wlh Ana iya d'aukar ciki indai muna San asirinmu ya rufu tunda dai sun dage sai wata taran ya cika yanzu yaza ayi?Zarah ta ce " ke zaki fad'a"Asmy ta ce "idan mukaje chemist ko asibiti da niyyar saya za a iya mana mummunar fahimta sannan Kinga ba sanin Wanda baida illa mukayiba bare mu kasada mu saya kai tsaye karkije kisha abunda zaiyi miki illa shawara mafi sauki ita ce Ina wannan Dr Halima da jiya kikacemun gidanta kikaje me zai hana ki mata magana ta rubuta miki Tunda Dr ce kuma Kinga D'aukar Matar Aure take maki(Nikam Hajjo nace da Ba ta Auren bace) kamar yanda kika ban labari yanzu" Ajiyar zuciya Zarah ta sauke ta ce "Kuma hakane bari na jaraba " .........cikin shagwaba ta ce "I really miss you yaya na na fa d'auka zolayata kake nayi mamakin jin wai kazo Zaria gashi naga ko security baka taho dasu ba baka tsoron Mugaye kake yawo ba Escord please nidai ka daina yawo haka kaikadai" Kallon ta yayi Ya ce "To aku sarkin surutu kingama " Dariya tayi ta ce "Gaskiya ce Yaya kadaina yawo kai d'aya "lakutar kumatunta yayi ya ce " To Autar mu ya school din "Alhmdllh yaya lecture ta dau zafi Next week zamu fara exams hutun 2weeks zamuyi mu dawo mu shiga level 4" wow Karatunki yana Sauri Auta ki dage sosai zanyi miki special gift insha Allahu idan kika gama "Ihu ta buga tare da cewa " yeyeyeye my yaya Shiyasa nake sonka wlh insha Allah zan dage ai bantaba samun c o ko d'aya ba yaya Ina maida hankali kuma momcy ta na taimakamun sosai Dan duk abunda ban ganeba ita ke koyamun kuma na gane Ai yaya Kai kanka sai kayi mamakin baiwar kokari irin na Momcy Wlh idan tana bayani saika d'auka wata professor ce ga Ilimin addini idan tana rera karatu saika d'auka a madina take tsabar iya qiri'a nima fa ita keyi mun karin karatu yanzu haka natafi hizif hamsin yaya gashi ta had'u Tana kyau sosa....is okay uwar zuba zaiiizaiii ba full stop ina rabaki da shegen surutun nan fa ya fad'a ya na Jan kunnanta "Aucchhh yaya da zafi ta fad'a Sosai suka sha Hira da kanwartasa dukda ba Sosai yake biyewa surutuntaba dukda a mota ne sunjima kafin Suyi bankwana Bayan yayi mata transfer 200k har bakin get d'in makaranta ya ajeta kafin ya juya daman saida yaje gida ya sauya mota tukwana Suka hadu Dan karma ta gane motarsa ce Dan waccen ba kowa ya sansa da ita ba Ita Chuchu bama tasan gidanshi na Zaria ba Dan garuruwan da yake da gidaje Allah yayi yawa dasu Kai tsaye Kaduna ya nufa Dan ya k'agara yaga Ammynsa saboda lokacin da ya dawo daga America Kano ya sauka ya d'auko hanya ne ta kawosa Zaria har ya had'u da Zarah dukda da farko ba ganeta yayi sosai ba dalilin ma daya kawoshi zaria....." Haba Zarah me ya kaiki ga planning yarinyarki karama Auren farko ko haihuwa bakiyi ba Kice wai kina son kiyi planning Gaskiya ina baki shawarar ki bari saikin haihu tukwana"Dr Halima ta fad'a daga cikin wayar "Marairaicewa Zarah tayi ta ce " Ba haka bane Aunty Ina school ne to na kusa kammalawa Dan kar nasha wahala Shiyasa nace zanyi kona shekara ne kafin na gama"wannan ba wani Babban uzuri bane kanwata mutum nawa suke hada karatu da haihuwa Tukunnama mijin naki ya amince"Cikin Sauri Zarah ta ce "Eh Shima yace nayi" kin tabbatar kuwa Zarah?Eh Aunty shiyace"Okay to shikenan gobe idan naje wajen Aiki zan sai maki maganin da zakiyi amfani dashi saiki sameni a asibitin ki amsa nayi maki bayani wajen 12 na rana haka "Nauyayyar Ajiyar zuciya ta sauke ta ce " nagode Aunty "washegari Daidai lokacin taje asibitin kasancewar shigar Hijab da nikab tayi hakan yasa ba Wanda ya ganeta har Dr Aliyu Office din dr Halima taje Bayan sun gaisa nan ta bata maganin da tsarin yanda zata sha Godiya sosai Zarah tayi wa Dr Halima saida ta biya kasuwa tayi musu Sayayyar chefane kafin ta koma tana zuwa Chuchu ta d'ora musu miya Dan provision d'insu hade yake daman tare suke girki....da misalin goman dare kwance Zarah ta ke ta lumshe ido mood d'insu na Daren jiya ya shiga dawo mata cikin kwalwa wani felling na taso mata saurin barin tunanin tayi Dan zata iya shiga wani hali taja tsaki ta ce mugu kawai " waye mugun"cewar chuchu"Ta d'auka a zuci tayi maganar ashe a fili ne "k'in bata amsa tayi Sai Juyawa tayi ta kwanta........" Ammy kenan Bakya missing Dina kenan shiyasa har kike cewa Na fiya zarya "Shafa kanshi Ammy tayi ta ce " Ba haka bane Babana Dan karka dinga shiga hakkin ita Matar taka"Tsaki yaja a ranshi Dan tunowa da irin rainin wayan da Amera tayi masa ya ce "Ai Ammy ita ce batason zuwa shiyasa " sannan ya d'ora kansa bisa kafadarta kamar wani k'aramun yaro ya ce "Uhm Ammy yunwa nake ji" Murmushi d'auke da fuskarta ta ce "Me kake son Kaci Baban Ammy" Murmushi yayi yana Shafa sajensa ya ce "Tuwo Miyar kubewa"da Daren nan Babana " Cewar Ammy"Eh Ammy "Tana shirin Mikewa Ta ce " Bari Naje na girka maka tunda akwai kayan hadi Dan tasan Dan nata bayacin abincin Maid House idan yana nan daman Chuchu keyi masa girki ko kuma yaci na restaurant "(nikam nace meye marabar dambe da fad'a") kamo hannun Ammy yayi ya ce "da wasa nake maki Ammy taya zan wahalar da Ammy na guda "indai kana so babana ka bari nayi maka " girgiza kai yayi tare da mik'ewa ya ce "Da wasa nake Ammy Hug d'inta yayi ya ce " Good night Dear mom"Shafa kanshi tayi ta ce "Have a nice dream my Beloved son god bless you " koda ya kwanta Kasa baccci yayi tunanin mood dinsa da yarinyar na Daren jiya ya shiga dawo masa lokaci guda yaji Yana neman burkutawa kansa lissafi Tsaki yaja a ranshi ya ce "Stupid kawai marar Kunya mata matsala ne Wlh " Kafin kuma ya ce "Amma yarinyar ta na Da dad'i over" Lumshe ido yayi ya ce "Zan kwashi gara kafin 9 months din stupid kawai villager girl " (Nikam nace kaidai ka sani MD). Washegari Azahar a Gombe tayi masa Daga shi sai Jaber kamar yanda suke zuwa haka suka isa a sirrance. Kallon dattijon dake kwance kamar ko yaushe MD yayi shiko yana ganinshi ya Fad'ad'a fara'arsa dukda baya iya komai Amma daga ganin fuskarsa zakasan yana cikin farinciki "Shima murmushin MD ya mayar masa tare da kamo hannunshi ya murza a hankali ya ce " Sannu ko Baba"Lumshe masa ido yayi tare da bud'ewa "Kamashi MD yayi ya tasar dashi Fruit ya dinga bashi a baki yana ci yana yi masa murmushi Har saida ya koshi ya daina Amsa tukwana ya d'auko Handchiep ya Goge masa baki kafin ya kwantar dashi Kallon dattijon dake gefenshi yayi ya ce " jiki ya fara sauki sosai naga"Da fara a tsohon ya ce "Alhmdllh yanzu kam Kamar ma ya dawo hayyacinshi Dan wani lokacin saika samesa yana kuka wani lokacin kuma murmushi sannan yanzu har motsa hannunsa yanayi ya ma fara amfani da hannun" jinjina kai MD yayi ya ce "Insha Allahu zai dawo daidai da yardar ubangiji Ai Babu Abunda yafi k'arfin Allah Sannan Shima na Asibitin a dinga basa magungunan Baba Karka gajiya Kaima Ladarka na wajen Allah " Tsohon ya ce "Insha Allahu kaima dai Allah yayi maka albarka ya kareka daga sharrin makiya da mahassada " Ameen MD ya fad'a Koda ya Mike Zai tashi sai na kwancen ya kamo hannunta Juyawa MD yayi ya Kallesa saiyaga hawaye nabin kumcinsa cikin Sauri ya koma ya zauna tare da Rik'e hannun tsohon cikin muryar girmamawa ya ce "Kayi hakuri Baba Zandawo insha Allahu bada jimawa ba zaka samu sauk'i da yardar ubangiji"Ta ido dattijon ya nuna masa da ya gamsu kafin ya saki hannun nasa.....a hanyarsu ta zuwa Airport Jaber ne ya ce " bawan Allan nan yana bani tausayi wlh tsawon shekaru A haka Kaiba matacce ba kaiba mai rai ba Kuma ga dukkan Alamu sihiri ne mai k'arfi akayi masa Allah dai ya basa lafiya"Ameen Kawai MD ya ce "Jaber ne ya ce " Bloody ya maganarmu ta rannan Ina takardar sakin Zarah"Ka cire hannunka a maganar kawai "Cewar MD " da mamaki jaber ya ce "ohh haka kace amma dai kasan nine jadanin Shirin ko ?lumshe ido MD yayi kafin ya bud'e ya ce " Eh nace ka cire hannunka kawai "Jinjina kai Jaber yayi ya ce " Hmmmm Na cire daga yau insha Allahu"koda suka isa kd Gidansu ya wuce Ammy ce ta Kallesa ta ce "ya naga kamar akwai alamar gajiya a tattare dakai"eh Wlh Ammy daga Gombe nake " Ammy ta ce "Ah dole ka gaji kam Ya Jikin na Baban to?dan tasan shi kadai ne ke kaishi gombe"Alhmdll Ammy Da sauki za ace yanzu kam an fara samun cigaba sosai" Cikin tausayawa Ammy ta ce "Allah sarki Bawan Allah ana ta kankarar zunubi Allah dai ya basa lafiya nima ina son Samun lokaci naje ba dama ya kamata ace munkoma mun dubasa Allah dai ya basa lafiya Gaskiya duniya ba Gaskiya wlh A kassara mutum shekara da shekaru tsohon Allah wata Allah Dan tsohon nan a k'alla zaiyi uba dani aka kassara bawan Allah a zaune Allah dai yayi mana tsari da makiya na fili Dana boye Shiyasa nake ta ce maka ku dage da addu'a babana mutanen yanzu ba Gaskiya Allah ya kare munkai ya tsaremun kai babana ya k'ara maka zuciyar imanin irin taimakon da kake Allah ya k'ara maka budin da zaka ninka fiye da na da " ameen Ammynah "MD ya fad'a... Washegari Zarah ce zaune tanayiwa Chuchu kitso Wanda dak'yal ta samu ake mata wai batason kitso kodan yawan gashin da sulbi Dan Sai a daure ita Zarah har mamaki take gashin Chuchu sak na India wa amma Kuma gata ita Bak'a ce bata da Haske sosai Bayan ta gama yi mata Wayar ta ce tayi ringing ganin ya Hafiz ne ya sanyata saurin d'auka Hira suka shigayi sosai yake zuba kalamai masu dadi dukda ba maida masa take ba Sosai Dan kunyarsa take ji kawarta ce Hibba ta shigo Bayan sun gaisa da Chuchu Da Asmy da ta gama sallar la'asr kusa da Zarah ta zauna katse wayar tayi tare da kallonta ta ce " Manya daga ina "Murmushi kawai hibba tayi ta ce " Gaku manya turoni akayi Malam Umar ya ce Kije wai "Da mamaki Zarah ta ce " Mlm Umar kuma Niko me zai had'ani dashi kofa magana bayi muke ba "Wara hannu tayi ta ce " Nima kin tambayeni kije kiji"chuchu ce tayi dariya ta ce "Ko shima yana ciki dai wai ya maganar mlm sulaiman dinnan ya kuka kare dashi" Asmy tayi dariya ta ce "Nima na manta nayi mata wannan tambayar " Hibba tayi dariya ta ce "Kila yaga ba sarki sai Allah ya hakura" Tabe baki zarah tayi ce "Ni harnama mance dashi bana yarda ma mu hadu dashi idan ya aika a kirani kuma ba zuwa nake ba " Hibba ta ce"Ki daibi a hankali wlh karya kada ke"chuchu taja tsaki ta ce "kufa duk laifinkune ma da kuke tsorata da irinsu wlh dan sunga ba a kaisu sama shiyasa suke wannan iskancin ya kada ita d'in ya gani wlh sainayi hanyar da za a kaisa sama sai yayi ta aikinsa" duk dariya sukayiwa chuchu wai zaiyi ta aikinsa Hijab d'inta ta sanya har kasa tare suka isa har office d'in Inda hibba ta tsaya daga waje shiga Zarah tayi Bayan ta gaishesa ya amsa tare da nuna mata kujera da ta zauna a sanyaye ta zauna wayarsa dake kan table tayi ringing cikin Sauri ya d'auka Ita dai bataji me sukace ba saiji tayi ya mik'o mata wayar akan ta amsa"Nuna kanta tayi ta ce "Ni,?Eh amshi zakuyi magana " a sanyaye ta amshi wayar tare da karawa a kunnanta "ki sameni a Gidan da na kawoki Rannan karki wuce 30 minutes "ta tsinkayi muryarsa daga cikin wayar" satar kallon Mlm tayi taga hankalinsa baya ma wajen "Murguda masa baki tayi tare da cewa " Idan fa naki ?ki ganni a makarantar yanzu na daukeki ta karfi"tsaki taja tare da cewa "to bazanzo ba aini ba y'ar iska bace " Sosai yayi mamakin jin furucin nata ya ce "Okay nine d'an iskan kenan?turo baki gaba tayi ta ce "oho dai Sai Anjima nidai ba Inda zanje " okay kijirayi zuwana Nan da 1 hour bakizo ba Zakiyi mamakina villager girl kawai"Yana gama Fad'ar Hakan ya katse kiran.......✍🏿 07026166536 domin magana da marubuciyar kai tsaye *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️..........*41 & 42* bin wayar tayi da Kallo tana mamakin k'arfin hali irin na mutumin nan ya dinga Abu gadara_gadara kamar wani ubanta Tsaki taja Ta ce "Ko ina ma yasan Mlm Umar" Tsoro ne ya kamata tunowa da ya ce nan da 1hour zaizo karfa da gaske yake karyazo yayi mata abunda zaija mata adinga mata Cece kuce Dan ta lura ba kunya ta ishi mutumin ba kar mutane suna ganinta da mutunci suzo sun fara zarginta Tsaki taja tanajin haushin Abunda yace mata wai villager A sanyaye ta mik'e tabar office d'in Bayan ta mayar wa da Mlm Umar wayarsa kai tsaye hostel ta nufa a sanyaye daka kalleta kasan tana cikin damuwa shiru tayi tare da Yin tagumi Asmy ce ta ce "Lafiya naga tunda kika dawo kinyi shiru" Tana turo baki ta ce "da sauki dai" Satar kallon Chuchu tayi taga hankalinta nakan waya chat take tana Dariya ya sanya Ta fad'awa Asmy Yanda sukayi a waya k'asa da murya Asmy tayi ta ce "Ki shirya ki tafi kawai karki yarda yana zuwa school d'innan Dan last time ma da aka saukeki wlh wasu harsun fara cece kuce wai daman ustazan nan Kunfi iskanci a boye har fad'a saida mukayi da wata Kiyi Sauri" Ajiyar zuciya Zarah ta sauke ta ce "To shikenan Chuchu fa yazamuyi da ita" Ki barni nasan Abunda zance mata "Cewar Asmy cikin k'ank'anin lokaci Zarah ta shirya cikin atamfarta Riga da sicket Ta d'ora hijab d'inta doguwa mai hannu Pink Fuskarnan tata fresh ba komai sai kwalli Bayan ta dauki hand back d'inta da wayarta zata fita Chuchu ce ta ce " ina zuwa momcy"Asmy tayi. Charaf ta ce "Cikin gari zataje gidan kanwar mamanmu Mijinta yayi tafiya zataje ta tayata kwana" okay Adawo lfy"cewar Chuchu"Koda Zarah ta isa cikin gidan tayi minti biyar tana tsaye ta kasa knoking Dak'yal dai ta tattara jarumta tayi knoking sau d'aya Saida a ka dau kusan Minti Bakwai kafin taji karar bud'ewa duk Haushi ya isheta tana Jan tsaki tsaye ta ganshi kamar kullum sanye cikin K'ananan kaya "tana ganinshi ta murtuke tare da hade rai " Shiko murmushin gefen baki yayi tare da raba mata gefe Alamun tazo ta wuce Kamar bazata wuce ba sai kuma ta shiga tana turo baki Dan tadau aniyar wata magana bazata had'ata dashi ba Tunda Dan wulakanci ne Kan Sopa ta zauna tare da d'ora kafa d'aya kan d'aya ta kauda kai Shima zaunawa yayi kan sopa Yana kurbar drink a cup hankalinshi nakan Kwallo da ake nunowa a gidan television Sunkai minti Ashirin cikinsu ba Wanda yayi magana Shi MD harma ya manta da halittarta a wajen saida yaji ringing d'in wayarta d'an satar kallonta yayi yaga tana Zage jika tare da dauko wayarta cikin Sauri tayi murmushi tare da d'aga kiran cikin cool voice d'inta ta ce "ya Hafiz Ina yini" Shidai MD yana satar kallonta yanda Take wayar tana lumshe ido Baidamu da hakan ba kiran Sallar magriba ne ya tayar dashi Tare da barin gidan ya wuce masallaci Zarah ma wayar tayi masa bankwana saijan tsaki ta ke ta ce "Mutumin nan ya rainama mutane wayau wlh mtww " Toilet din palourn ta shiga tayi alwala Bayan ta fito ta tada salla a carpet din dake palour tayi sallarta bataji shigowar MD ba sai Bayan isha'i itama Bayan ta gama isha'i nan ta zauna tana latsa wayarta Tana chat "Keee" ta tsinkayi muryarsa daga samanta"A ranta ta maimaita keee lallaima watau bazai iya Fad'ar sunanta ba Aiko bazan amsa ba ta fad'a tanayin kwafa tare da cigaba da chat dinta kamar ma ba da ita yake ba "Saida MD ya ce keeee sau Ukku batare da ta d'ago ba hakan sosai ya bakanta masa Yunkurawa yayi tare warce wayar Dake hannunta ya ce " Ba magana nake maki ba"Dagowa tayi ta tsatsareshi da dara daran idanunta tare da turo baki ta ce "To ai banji ka kira suna na ba ?Ohh saina kira sunanki kenan zaki amsa mun? " Eh saboda ba Suna na kee ba Suna na Zarah"Binta da wani irin kallo yayi kafin yaja k'aramun tsaki ya ce "To bazankiraki da sunan naki ba da ke din nayi niyyar Kiranki "Zarah da ta cika tayi Fam Tsaki taja tare da kauda kai " murde mata baki yayi da karfi Wanda saida ta k'walla Kara kafin ya saki ya ce Daga yau ki karayimun tsaki kiga abunda zanyi maki stupid kawai "Idanun Zarah na zubar da hawaye ta ce " Allah ya isa"Wara idanu yayi tare da nuna kasa ya ce "Ni??Tana kuka Ta ce " Eh "Ganin ya yunkuro zai chafeka ya sanyata saurin Mikewa tare da rugawa tayi hanyar fita tana murdawa taji a kulle gashi ya biyota da gudu ta Ruga Tayi Wani Bedroom taja zata rufe kenan Ya turo kofar da k'arfin Kara ta fasa tare da rugawa tayi karshen d'akin tana kuka ta ce " Dan Allah kayi hakuri bada kai nake ba"wani murmushi yayi wanda bazata taba cewa yayishi ba tare da cewa "Na lura baki da kunya saina saita miki zama" Ya fad'a tare da binta chafka d'aya yayi mata ya damkota Tare da bajewa kan Gado a tare suka sauke wata nauyayyar Ajiyar zuciya kafin Zarah ta fara kiciciniyar kwatar kanta amma ta kasa Cikin salo MD ya fara romance d'inta Wanda tuni jikinta ya mutu batasan lokacin da Fara mayar masa ba Dan tama mance da Wanda take tare sun dau Minti arba'in suna romance kafin labari ya sauya salo wannan Karin kam Zarah ko Kukan babu Dan Abun dadi yayi mata sosai Suke Abu D'aya MD bai sarara mata ba sai kusan 1:00am Bayan komai ya lafa kankameta yayi a jikinshi kafin wani bacci mai dad'i yayi awon gaba dashi duk yanda Zarah taso ta cire jikinta daga jikinshi kasawa tayi Dan karfinta da nashi ba d'aya ba haka dai ta hakura itama har baccin ya kwasheta.....a hankali yake bud'e idanunsa harya k'arasa budesu Kallonta yayi dake jikinshi Wanda baisan ma yayi hakan ba A hankali ya zame jikinshi daga nata toilet ya shiga saida ya fara wanka Kafin ya daro alwala ya fito jallabiya Ya sanya tare da tada sallah Bayan ya gama zaune yayi wajen ya na istigfari A hankali ta bud'e idanunwanta Hasken data gano daga Window ne ya tabbatar mata da Safiya tayi mik'ewa tayi zata zauna Dan ta mik'e Daidai idonsu Ya startse Cikin na juna cikin Sauri ta koma ta rufe jikinta har fuskarta Dan ba komai jikinta batasan ya akayi ba Yau wata irin kunyarsa takeji shiko girgiza kai kawai yayi tare da mik'ewa yabar dakin Tanajin fitarsa Ta sauke Ajiyar zuciya tare da mik'ewa cikin Sauri ta fad'a toilet tayi wanka tare da brush da alwala Tana fitowa lotiion da ta gani a jikin mirror din ta hau shafawa tayi mamakin yawan Kayan shafar kamar na mace Bayan ta gama Kayanta na jiya ta Mayar Tare da tada salla cikinta banda karar yunwa ba abunda yake yi mata Palour ta fito Inda ta samesa waya k'are a kunnansa ga alamar waya yake kujerar nesa dashi ta zauna tana kasa da kanta Bata yarda ko ido biyu su hada Bayan ya gama wayar kallo d'aya yayi mata sai kuma Ya kauda kai ba ayi minti goma ba Sukaji knoking Mikewa yayi tare da zuwa ya amso take away din Ajewa yayi kan table batare da ya Kalleta ba ya ce"Zoki d'auka kiyi break fast"A sanyaye ta mik'e shi kanshi har mamakin wannan kunyar data tashi da ita yau yake tana bud'ewa taga taliya ce lafiyayyan Samanta da kifi cikin Sauri ta rufe tare da Ajewa ta ce "Na koshi?For why ?Hakanan bana cin Kifi " kamar bazai amsa mata ba saikuma ya ce alright ga dayan take away din d'auka "Na koshi idan nakoma school zanyi break fast a Chan " Dagowa yayi ya Kalleta ya ce "Zaki iya girkawa a kitchen akwai komai" kamar bazatayi magana ba sai kuma ta Kalleshi ta ce "Ina kitchen d'in" da yatsa ya nuna mata hanya Inda ya nuna matan ta nufa cikin k'ank'anin lokaci ta fara sarrafa Dahuwar indomie Dan itace Abu mafi sauki da zata ce Zata girka Wayarshice take ta ringing yana ganin Amera ce ta isheshi da kira ga text message d'inta rututu tsaki yaja Dan har yanzu kule yake da ita daga karshe ma kashe wayar yayi Dan karta dameshi ba ayi minti Goma ba ta fito hannunta dauke da plate din Indomie Da ta sha vegetables ta kwai a Samanta Tunda ta shigo k'amshin girki mai dadi ya cika masa girki har wani lumshe ido yake Zarah ko ba b'ata lokaci ta fara cin abincinta Saida ta kusa rabi tukwana ta d'ago ta Kallesa taga hankalinshi na kan laptop tabe baki tayi ta ce "Bismillah " Harara ya banka mata Tare da cewa "Nayi maki kama da Wanda zaici wannan jagolgwalon naki" Murmushi kawai tayi tare da cewa "Ai daman fita hakkinkane nayi na musulunci tunda bakaci ai shikenan " ta fad'a tana cigaba da cin abincinta hankali kwance MD ganin Tana gab da cinyewa gashi har ga Allah Kanshin abincin Ya Dakeshi da yawa zaizo yayi taste kallonta yayi yaga ta kusa cinyewa gashi baison Raini daga wajen yarinya hakan ya sanyashi linke Laptop d'inshi tare da cewa "Zoki kaimun laptop d'innan daki" kamar zatayi bataji ba saikuma ta mik'e taje ta d'auka tare da nufar d'akin yana ganin shigarta ya sauke ajiyar zuciya Tare da yunkurawa ya kai one spoon bakinsa lumshe ido yayi jin special girkin da ya mance yaushe ya tab'a cin irinsa Dan dadi dukda yana yawan cin indomie amma zai iya cewa bai tabajin mai dad'in wannan ba "Jin Fitowarta ya sanyashi saurin komawa kujerar da yake ya wani had'e Rai itako murmushi tayi dukda bata ga sanda ya ciba D'aukar plate din Tayi Tare da nufar hanyar Kofa Dan takaiwa mai gadi ta Riga ta k'oshi" ina zaki?Ta tsinkayi muryarsa "Mai gadi zan kaiwa sauran na k'oshi" Dawo ki Aje Ba sai kinkai masa ba ki kai kitchen ki Aje Ko ki zubar "Amma ai fariya ba kyau ma bari na kai masa "wani kallo ya watsa mata turo baki tayi dayin gunguni " Nuna kanshi da hannu yayi Alamun ni"Cikin Sauri ta ce "To me nayi maka kuma " Ta fad'a tana Kara turo baki"Okay zakiga abun da kikamun ya fad'a yana Mikewa cikin Sauri ta hade rai Tare da cewa "Nifa ba abunda nayi maka Saidai kawai idan Zalina kake son ci " ganin ya nufo ta ya sanyata saurin Aje plate din kasa tare da rugawa tayi bedroom murmushi Kad'an yayi tare da d'aukar plate din indomie d'in yakoma kujerar da yake Ya zauna ya fara ci a hankali yana lumshe ido Alamun dad'in ya kai masa karo Zarah jin shiru bai biyota ba ya sanyata sauke ajiyar zuciya Wayarta da taga Ya aje kan centre table ta d'auka da Jakarta daman hijab d'inta na jikinta ta fito wara idanu tayi ganinshi zaune ya na cin indomie d'in da tayi saura yana ganinta Ya wani had'e rai Itako Dariya ta babbake da ita hada rik'e ciki kallonta ya tsayayi da mamaki yanda take dariyar shi kanshi saida ta bashi mamaki daman tana Dariya har haka kenan?ya tambayi kanshi sai kuma ya kalli indomie d'in hannunshi ya tabbatar da ita takewa Dariya Kara hade rai yayi tare da cewa "Keeee meye haka" Cikin Sauri Zarah ta daidaita nutsuwarta Tana Boye sauran dariyarta ta ce "Bakomai naga kana cin jagolgolo ne shiyasa Nayi Dariya" Tsaki yaja tare da banka mata wata Hararar ya ce "Da yake ke Kika zo da indomie d'in da bazanci ba ko?Tana boye dariyarta ta ce " A a a yi hakuri kayan Kane nima arziki ne naci Thnks "ta fad'a tana daidaita tsayuwar Hijab d'inta tare da Yin hanyar Fita tana turawa taji arufe ta waiga ko zataga makullin amma babu Kallonshi tayi da ya mik'e ta ce " Zan tafi school ina da lectures Yanzu karna makara please zoka budemun "ba inda zaki Bazakiyi lectures d'inba Yau "yana gama Fad'ar haka yayi shigowarshi bedroom batare da ya waiwayeta ba..........✍🏿 *07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo Ce*_🤙🏿 🅿️.... ..*43 & 44* Tsaye tayi Mamaki yagama cika ta Abun mutumin nan ma ita girmame Mata yake ganin tsayuwar bazata fisheshetaba ya sanyata komawa ciki tunowa tayi da bata sha maganin da Dr Halima ta rubuta mata ba cikin Sauri taje ta d'auko ruwa a bottle tare da fiddo maganin daga Jakarta Ta b'alla ta sha Tare da mayarwa...da misalin K'arfe sha biyu saura MD ya fito daga d'akin sanye cikin Wata shigar kallo d'aya tayi masa ta kauda kai duk Haushi yake bata "Ki girkamun Tuwo Miyar Agushi zansa a kawo miki abubuwan da zaki buk'ata yanzu" ya fad'a yana sanya cover shoues d'inshi "Dagowa tayi ta Kalleshi kamar bazatayi magana ba sai kuma ta kauda kai ta ce "Ai ni ba y'ar aikinka bace " kallonta yayi ya ce "Okay bazakiyi ba kenan" Turo baki tayi ta ce "Eh " Matsowa yayi Dab da ita kamar zai shige jikinta saurin Mikewa tayi tare da ja da baya ta ce "Meye haka" Binta ya yi har saida yayi mata rumfa saurin rumtse idonta tayi da karfi kafin tayi wani Abu saijin bakinshi cikin nata tayi ya dau minti ashirin yana kissing d'inta daga tsaye tuni jikinta yayi lakwas Ganin tsayuwar bazata fishshesu ba Ya sanyashi daukarta sukutum tare da Yin bedroom da ita.....Bayan komai ya lafa ya fito daga wanka yana cikin sabon shiri kauda kai Zarah tayi tare da Yin shiru tana tunanin wannan wace irin rayuwace ta tsinci kanta a ciki kamarfa tana cin Amanar Hafiz ne mutumin da ya taka rawar gani a cikin rayuwarta Wanda inbanda bada silar sa ba da karatunma Saidai taga anayi Goge hawayen da taji sun zubo mata tayi tana wannan tunanin har MD ya gama shiryawa tsinkayar muryarshi tayi da cewa "zan fita Yanzun ma ko bazaki girka ba a d'ora daga Inda aka tsaya " turo baki tayi tare da gunguni kasa kasa ta kauda kai "Matsowa dab da ita yayi ya ce " Keee ?Dagowa tayi tare da Kallonshi da dara daran idanunta Saikuma ta kauda kai Dan Inda tana kallon cikin idonshi ji take bazata iya gaya masa magana ba ta ce "Na gaya maka ba suna na kee ba suna na zarah meyasa bazaka kirani da suna na ba in banda cin fuska" yanda tayi maganar ne cikin sanyi ya sanyashi Saukowa ya ce "Bazan iya kiran sunan naki ba kai tsaye shiyasa yafimun sauki na kiraki da kee" Kallonshi tayi ta ce "saboda me bazaka iya Fad'ar sunan ba " saboda Sunan wacce ta kawoni duniya ne ina daraja sunan da martaba shi yanda bazan iya fad'ar sunan kai tsaye ba "wara idanu tayi sai kuma ta turo baki ta ce " To ai indai kana daraja mai sunan bai kamata Ace kana kiranta da keee ba sannan kuma kana yi mata mugunta da cin zalinta kodan darajar sunan kamar yanda ka fad'a "Murmushin da bai fito fili ba yayi ya ce " to da wani suna kike son na kiraki dashi?babu kawai ka kirani da Zarah bana son keee din please "Mikewa yayi ya ce " Zan Kiraki da Mamy"Yana gama fad'ar hakan yabar dakin "Mamy ta maimaita a cikin zuciyarta Yanda ya Fad'a sunan saika rantse a bakinsa aka rada tabe baki tayi tare da mik'ewa taje ta sake wanka tana turo baki ta mayar da kayan dake jikinta dukda wani iri takeji da ma Chan da take rayuwar kunci a gidansu ita ma'abociyar tsafta Ce Dan bata tab'a fita da kaya da datti....kafin 3 ta gyara gidan tsaftsaf ta sanya air freshener Dan taga babu turaren wutan kamar yanda ya fad'a haka ya turo driver da kayan girkin Tuwon da ya fad'a ta girka da Miyar Agushi Bayan ta gama ta jera a dining Tana cikin Sallar la'asr taga shigowarshi bata daga Ta Kalleshi ba har ya wuce Ba ayi minti goma ba taga fitowarshi cikin wasu K'ananan kaya na hutawa a gida Dan wandon ko gwuiwa bai kai ba ita kanta mamakin tsafta irin ta mutumin nan take kullum cikin wanka da sauya kaya yake kamar kwado da baya ma mura duk cikin ranta take maganar nan shiko MD tunda yashigo yake Karewa gidan kallo yanda yayi tsaftsaf ga k'amshi dake tashi har wani lumshe ido Yake karo na farko da yarinyar tayi Abu ya burgeshi Dan har a ranshi yana son tsafta Dining ya wuce ya d'aga cooler din Yaga tuwo ne da Miyar agushi k'amshi duk ya cika masa Hanci nan ya zauna ya take cikinshi shi kanshi saida yayi mamakin iya girki na yarinyar Kamar a hotel ga Tuwon ya tuku A Rayuwarshi MD yana son tuwo da abincin gargajiya amma baya samunsu yanda yakeso shi kanshi yayi mamaki yanda yarinya karama ta iya girki haka tayi tuwo da miya lafiya qalau ita kadai Dan yasan ko Chuchu da Ammy ke kokarin Koya mata girki ta iya abubuwa amma bata iya tuwo haka ba bare Amera da zai iya cewa tsawon rayuwarsu ko ruwan tea bai tab'a ganin ta dafa ba"duk cikin Zuciyarsa yake wannan tunannikan baisan ya cinye na plate din da ya zubo ba saida yazo zai dauka yaga babu wara idanu yayi tare da lumshe ido palour ya dawo ya zauna Tab'e baki Zarah tayi a ranta ta ce "sai kace y'ar aikinshi Ko sannu" bata gama tunanin wannan ba ta tsinkayi muryarshi da cewa "Thnks" Bata mayar masa ba sai sauke ajiyar zuciya da tayi a ranta ta ce "Kamar yasan tunanin da nake " Ganin yamma nayi gashi baida niyar mayar da ita ga Asmy dake kiranta akan meyasa bazata taho ba tana son tamashi magana amma kuma ta rasa sunan da zata kirashi dashi Dan ita ko sunan shi bata sani ba tayi minti biyar tana sak'e sake kafin tayi k'arfin halin cewa "kar dare yayi Bankoma school ba gashi ka rufe kofar" Banza yayi mata kamar badashi take ba "Kamar bazata k'ara magana ba Dan Haushi turo baki tayi gaba ta ce " da kaifa nake Ka budemun Na tafi "Nanma banza yayi mata Zarah Haushi kamar ya kashe ta Ta ce " Magana fa nake maka kuma nasan kana jina "Tsaki yaja a ranshi ya. Ce matsala kafin ya Kalleta ya ce " Wai Dan Allah ke burinki kawai kiga kin sanyamun ciwon kai kin isheni da magana bakisan suna na bane "Haushi kamar ya kashe zarah Amma kuma dole ta kwantas tunda so take ya bud'e mata ta ce " To ai bansan sunan ka ba "Okay to ki kirani da Kaii!?Turo baki tayi ta ce " Ai Ni bazan iya kiran mutum da haka ba ko na girmeshi bare Wanda ya girmeni"Murmushin da baizo fuska ba yayi Dan daman son gwadata yake ya ce "Ashe Kina da hankali suna na Mustapha zaki iya kirana da haka" kasa tayi da kanta ta ce "Bazan iya kiran sunan Babba da sunanshi kai tsaye ba " da mamaki yake kallonta kafin ya ce "To dame zaki kirani " shiru tayi saikuma ta d'ago ta ce "Saidai na kiraka da ya Musty" Wow ya fad'a a cikin ranshi Dan yanda ta fad'a sunan sosai yaji sunan ya burgeshi kamar a bakinta aka rada ya Musty "lumshe ido yayi kafin ya bud'e ya sakar mata murmushin da bai San yayi ba ya ce " Nice name"Mamaki ne ya cika Zarah a ranta ta ce "Daman yana murmushi kenan " Dan bata tab'a ganin murmushinshi irin haka ba Sosai taga yayi kyau da murmushi dukda ba Kallon fina_finan India take ba Saidai wani time d'in idan taje gidan su Asmy tana kallo Itama tadan Kalla Kad'an saitaga ya koma mata kamar y'an Fina finan India Dan zata iya ranstewa a cikin India wan ma shi star ne tab'e baki tayi a ranta ta ce "Kyau ba hali me kyau Anyi ba ayi ba kenan" duk yanda Zarah taso MD ya barta ta tafi school banza yayi mata Sai hakura tayi da dare ko harta kwanta dayan d'akin ta zata a dayan zai kwana cikin bacci taji yanayi mata abubuwan da ya saba yi tayi kamar bacci take dukda tana jinshi Daren ranar bata bashi hadin kai ko Kad'an ba.....da misalin Goma na safe tana waya da Hafiz ya shigo d'akin kallo d'aya yayi mata ya kauda kai tare da Aje ledar hannunshi ya fice da Kallo ta bisa Cikin wayar ta ce "Ina zuwa ya Hafiz " Bayan ta katse daga Ledar tayi taga kayan sawa ne kala kusan goma Rik'e hab'a tayi ta ce "Wai me mutumin nan yake nufi da ni ne " Wanka tayi ta dauki d'aya daga cikin rigunan tasa a palour ta samesa yana kallo kamar zatayi kuka ta ce "Wai me kake nufi dani ne Kwana na biyu a gidan nan kak'i barina na tafi makaranta lectures sai wuceni take Bayan next week zamu Fara Exams" kin dawo gidan ne da zama shiyasa bazaki cigaba da zaman hostel ba ?da mamaki ta kalleshi ta ce"kamar ya"Kamar yanda kikaji na fada "Kame k'ugu tayi ta ce " wlh bazata sabu ba me kake nufi Ai a yarjejeniyar da kukayi babu haka"Okay basu fad'a maki haka ba kenan to ni a yarjejeniya ta akwai haka "Aurenki nayi na Wata Tara Dan haka a gidan nan zaki zauna Har wata taran ya cika ke zaki dinga mun girki gyaran gida da sauransu idan lokacin ya cika sai kowa ya kama gabanshi daga lokacin idan kika hadu dani ma a hanya karki nuna kin taba Sani na amma yanzu a k'ark'ashin iko na kike"tunda ya fara maganar Zarah take kallonsa mamaki ya gama cikata Kamar zata fashe da kuka ta ce " Wlh baka isa ba ni ba ayi haka dani ba sannan ba wani girki da zandinga maka tunda ba y'ar aiki bace ni ka bud'emun na fita Allah kona Tara maka mutane"tsaki yaja Dan ta fara isarsa shi wani lokacin har mamaki yake yanda har yake Dan biye yarinyar a yanda baisan magana jin ta fara ihu ne ya daka mata Tsawa yace "meye haka baki da hankali" Cikin kuka ta ce "kome zakace Saidai kace wlh ka budemun kona Tara maka mutane " Ganin zata sanya mashi ciwon Kaine ya sanyashi saurin fardota ta fad'o cikinshi duk sanda taso kwatar kanta kasawa tayi Dan baiyi mata ruk'on wasa ba hade bakinsu yayi waje D'aya Ya dau Minti Talatin yana yanda yaso da ita a palourn tuni bakin mutuniyar ya mutu batasan lokacin da ta fara mayar masa da martani ba saida ya bari ta Nutsa sosai kafin yayi saurin tashi akanta tare da tureta ya ce " daman shine kike so " Numfashi ta mayar jin Abunda yace ya sanyata turo baki ta ce "Ai bance maka ina so ba kainema za a ace kana so kuma idan ba haka ba karka k'ara tabani mana ni daman ba so nake ba" tsaki yaja tare da hade fuska tamau Dan karma yarinya karama ta kawo masa raini bai karabin ta kanta ba ya bar gidan tsaki taja tashi tayi ta sha tea da bread din da ta gani a kan dining tana sha tana Jan tsaki Bayan ta gama kwance tayi a palourn tana maida numfashi wani irin feeling takeji yana taso mata ba k'aramar kasala ya tada mata ya tafi ya Barta ba ta jima tana rurrumtse ido da matse cinyoyi kafin bacci ya d'auketa a wajen around 2 ya shigo gidan ganin tana bacci baibi ta kanta ba ya wuce ciki wayarsa ce tayi ringing sosai yayi mamakin ganin Abban Amera ne ke kiran d'auka yayi ciki_ciki ya gaisheshi ya amsa cikin gadara ya ce "me ya hadaka da Amera ta kirani tana kuka wai ka tafi ka barta tsawon kwanaki baka kiranta baka kulata a Gaskiya banji dadi ba Dan Duk duniya bani da wacce tafi Amera Dan da a bata mata rai gwara ran dubunnai mutane su b'aci akanme za a dorawa yarinyata karama tension duk hakurin da take ta zauna dakai tsawon shekaru baka haihuwa amma ka rasa dame zaka saka mata saida musgunawa to bazan lamunci haka ba idan gajiya kayi da ita ka mayarmun da ita ni bangaji da ita ba " ya k'arasa fad'a yana huci sosai ran MD ya b'aci Dan daman yasan Mutumin ba dattako ta isheshi ba Shima cikin gadara ya ce "Abunda ya kamata a matsayin ka na babba ka tambayi abunda ya had'a bawai fad'a da kumfan baki ba akan Abunda baka da masaniya sannan duk hukunci da ka yanke yayi ina jira" Cikin masifa Abban Amera ya ce "Marar mutunci ni zakayiwa Rashin kunya to zaka gani hukuncin da zan yanke din ka saurareni" tsaki MD yaja tare da katse kiran ranshi Idan yayi dubu ya b'aci koda ya fito lokacin Zarah harta tashi tana ciki tana salla koda ta fito kallo d'aya tayi mashi ta kauda kai ganin irin yanda ya murtuke kamar bazaitayi magana ba saikuma ta ce"D'an Allah ka budemun Na tafi"Tsawar da ya daka mata ce ta sanyata saurin zabura cike da masifa ya ce "da Allah yimun shiru karki k'aramun Damuwa Stupid kawai " Sosai Zarah ta zabura Kuka ta fashe dashi tare da Durk'ushewa a wajen Sosai kukan nata ya dameshi Dan a Rayuwarshi baya son sauraran kuka A ranshi ya ce "Sudai mata matsala ce Ina Waccen matsalar na k'ara jajib'o wata matsalar mtwssss " jin kukan nata yayi yawa ya sanyashi Jan tsaki tare da cewa "Jeki shirya kizo ki tafi stupid kawai karki samun ciwon kai" Cikin Sauri ta mik'e dukda taji haushin zagin da yayi mata amma ai fita take son tayi Jakarta da waya kawai ta d'auko daman hijab d'inta a jikinta ta fito kallo d'aya yayi mata ya tilla mata key din d'akin hada tuntube tayi Sauri ta d'auka tare da saurin bud'ewa Ajiyar zuciya Ta sauke Bayan Fitowarta bata waiwayi ko gidan ba cikin Sauri ta fita Takoyi sa a tayi saurin samun abun hawa shiko MD Bayan fitarta ko minti biyar ba ayi ba ya Mike yayiwa driver dinsa waya yana zuwa ya daukesa suka kama hanyar kd a hanya Amera ta kirasa kamar bazai daga ba saikuma yadaga daga cikin wayar ya tsinkayi muryarta cikin kuka take maganar "Honey Dan Allah kayi hakuri ka yafemun wlh bazan iya jurar fushin ka ba please" tsaki yaja kamar bazai tanka mata ba ya ce "shi Baban naki da kika kira kika had'ani dashi a tunaninki.Duka na zaiyi kome"" Tana kuka ta ce "Kayi hakuri wlh banzata zaidau abun da zafi ba shiyasa na zata zai baka hakuri ne sai naga ya kira ni wai nataho gida kayi hakuri please mijina ka yafe mun" okay tunda ya ce Ki tafi gidan saikibi umarninshi ai "yana gama fad'ar haka ya kashe wayar Yana Jan tsaki....sati na zagayowa su zarah suka fama Exams d'insu ta second semester Wanda Dasun dawo level 4 zasu shiga sosai suka mayar da hankalinsa ga karatunsu dukda a sanyaye take Dan kullum da feeling take kwana take tashi sosai take buk'atar irin Abunda ya Musty yake mata dukda zaman da sukayi da wani jituwa suke ba harsuka gama Exams bata Kara ganinshi ba Daman ba numberta gareshi ba Koda suka koma gida Abu saiya Kara gaba sosai feeling d'inta ke karuwa ita kanta har mamaki take a haka dai a daddafe har hutunsu ya k'are suka Goma school Inda suka d'ora karatunsu daga Inda suka tsaya ganin har sati guda da dawowa Chuchu bata dawo ba ga sunyi kiran layin ta ba network yaudai sunyi sa a Asmy na kira ta d'auka Bayan sun gaisa Asmy ta ce " Lafiya baki dawo ba Bayan lectures harta kankama "a sanyaye taji muryar Chuchu ta ce " wlh sis Ammy ce batajin dadi two days shiyasa bazan iya dawowaba saitaji sauki"cike da damuwa Asmy ta ce "Subhanallahi Ai bamu sani ba Da munzo Allah ya bata lafiya insha Allah gobe zaki ganmu ga Zarah" Bayan Zarah ta amsa itama cike da damuwa ta ce "Allah ya bata lafiya gobe gamunan insha Allah" washegari Around 12pm suka Isa Kaduna Bayan sun kirata suka fad'a mata Inda suke Driver ta turo ya d'aukesu Har gidansu koda suka sosai sukayi mamakin girma da Kyau da fad'i irin na gidan su Chuchu mamaki duk ya gama cika su daman Chuchu cikin wannan daular take amma baka tab'a cewa Suna da kudi yanda bata da girman kai da isa da nuna ita ko wacece "(nikam nace Zarah Ai daman isa ta Wanda bai isa bace Wanda ya isa bayayi)Bayan fitowarsu daga motar Suka ga Fitowar Chuchu da gudu ta rugo tare da hug d'insu d'aya Bayan daya ta ce " ashe da Gaske zakuzo kai amma nayi farincikin zuwanku wlh sannunku da zuwa yau dai Ammy zata ga takwararta kuzo mu k'arasa ciki ta fad'a tana kama hannununsu farinciki duk ya rud'ar da ita murmushi Zarah tayi ta ce "Nima harna k'agara naga Ammynmu " har suka k'arasa Katoton palourn gidan Chuchu na musu iyayin irin farincikin ganinsu da tayi Bayan sun zauna ta mik'e ta ce "Bari naje ciki na fad'a mata kun Iso" Ba ayi minti biyar ba sai gashi sun fito su biyu Chuchu ta kamo hannun Ammy sosai gaban Zarah ya fad'i ganin Matar Da ke fitowa tare da chuchu .......✍🏿 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙 🅿️........*45 & 46* Sak taga Matar kamarta daya Da ya Musty kamar yanda take ce masa ba banbanci kamar an tsaga Kara an karya lallai Allah yayi kama a nan ta fad'a cikin ranta Cikin fara a Ammy tayi welcoming d'insu Bayan ta zauna Har kasa suka Duka suka ce "Ina yini Ammy ya jiki" Alhamdulilla jiki da sauki ya hanya kunshawo tafiya ko sannunku ko "Murmushi sukayi Chuchu ce ta shigo Tare da maid house din gidan ubayen kulol A hannunsu da kayan makuleshe daka Kalleta zagaka tana cikin farinciki zaunawa tayi gefen Zarah tana kama hannunta ta ce " Ammy Kinga takwarar taki fa "Cikin fara a Ammy ta ce " Ah masha Allah Ba shakka takwara taho kusa dani "ba musu Zarah ta je gefen Ammy ta zauna kallo d'aya Ammy tayiwa Zarah taji yarinyar ta shiga ranta over duba da irin nutsuwarta ga hankali uwa uba tarbiya sosai Ammy ta kwadaitu da hada zuri'a a Zarah taji inama tana da wani d'an namiji da ta had'ata dashi Sosai Ammy ta dinga nan nan da su Zarah an cika musu gaba da abubuwa Wanda suka rasa ma yanda zasuyi da su Sosai Chuchu da Ammy suka karrama su a gidan kamar wasu sarki Sai wajen La'asr Sukayi musu bankwana Ammy ta ce " Har tafiya yarana ai na zata Kwana zakuyi mana"murmushi Zarah ta yi ta ce "Ai zamu dawo Ammy Allah ya k'ara sauki" Ameen y'an kirki mungode mungode Allah bar zumunci nagode sosai wlh"Murmushi sukayi su kansu har mamakin irin godiyar da Ammy take musu suna nan tsaye Chuchu ta fito da k'atuwar leda a hannunta har rinjayarta take Hijab a jikinta Tana kwabe fuska ta ce "Muje to momcy amma wlh ni nafison ku kwanar mana fa" Hararar wasa Zarah tayi mata ta ce "Bana fad'a maki zamu dawo ba" Badan Chuchu ta so ba ce "Muje to driver ya kaiku" Dubu ashirin Ammy ta zago ajika tare da mik'awa Asmy ta ce "Gashi nan kunyi transfort" girgiza kai sukayi suka ce "Allah Ammy ki bari " ba yanda Ammy batayi dasu ba su amsa sai Chuchu ta amsar musu da niyyar idan sun fita Ta basu suna fita Chuchu ta hau kwalawa driver kira Yakai nawa amma bata ganshi ba Kallon Mai bawa flowers ruwa tayi ta ce "Wai ina sani ya shiga ne " cikin girmamawa ya ce "ranki ya dad'e ya fita ba jimawa gidan marayu mai gida ya aike sa"okay Yayan bai dawo ba kenan" Eh ya fad'a "Kallonsu Asmy chuchu tayi ta ce " Dan Alla ku jira yayana ya dawo ku gaisa"gwalo idanu Zarah ta yi ta ce "Ki duba time fa Chuchu karfe biyar saura kinsan hanyar nan tayi dare ba kyau ki bari sai wani time d'in kawai " cikin shagwaba Chuchu ta ce "Amma banso baku gaisa da yayana ba wlh To ku bari driver ya dawo yanzu saiya mayar daku har Zaria " Asmy ta Kalleta ta ce "Ki bari Chuchu kawai mungode mun koma a motar haya wlh kar dare yayi "to ku bari na d'auko mota mana na kaiku garrage din Kunga kun rage tafiya" Dariya Zarah tayi ta ce "Ai bazan hau tukin ki ba wlh " itama dariyar Asmy tayi ta ce "Chab Bafa zanhau ba wlh nima in kin ganni lahira kaini akayi kawai kina wannan rawan kan ki kifar damu" Dariyar da bata shirya ba Chuchu tayi ta ce "Wlh na iya shekara nawa ina driving Kudai kawai tunda kunkawo k'abli da ba Adi muje na rakaku " A tare suka fito Su Ukku suna tafe suna Hira Sosai sukayi nisa amma basu samu abun hawa ba Daman kuma haka yanayin unguwar yake samun abun hawa akwai wahala musamman magriba tayi "Kallon Chuchu take hucin gajiya Zarah tayi ta ce " ki koma Chuchu mungode wlh Kinga mu biyu ne ke kuma ke kad'aice jifa tafiyar da kikayi zamu samu abun hawa fa "Tana hak'i Chuchu ta ce " kuma hakane Amma nafison naga samun abun hawanku tukwana "murmushi Zarah tayi mata ta ce " karki damu dia zamu samu"Ledar hannunta Chuchu ta saka kudin aciki Dan karsu gani tare da dungurawa Asmy ta ce "Hajjaju amshi ke zakiyi dakon kayan nan Dan wlh momcy na bazata wahala ba " Harararta Asmy tayi ta ce "Sannu mai momcy kinjama bazan dauka ba saidai momcyn taki ta d'auka"marairaicewa Chuchu tayi ta ce " Sorry Besty wasa nake maki "Saida sukayi hug din juna tukwana Chuchu ta juya tana musu Godiya Suma suka kama hanya Inda idan Zarah ta gaji Asmy ta amshi Ledar Dan akwai nauyi kayan saida suka daga sukaga atamfofi ne da shaddoji sai kayan costimetics jinjina kai Asmy tayi ta ce " Gaskiya ammyn nan Nada kirki wlh basu da girman kai Sam na masu kudi"Itadai Zarah murmushi kawai tayi sosai suka tsorata har bayan magriba basu samu abun hawa ba ga tafiyar da suka sha Dan ko gidansu Chuchu basa hangowa zarah sai hak'i take ta ce "Wlh na gaji nikam" Daurewa zamuyi muyi ta tafiya ko Allah yasa a dace Haka suka dinga tafiya ba Alamun abun hawa Sai manyan motoci jefi jefi dake gittawa titin suna tafe sukaga wata mota dalleliyar mota har tayi gaba sai kuma suka ga ta dawo gabansu ta tsaya gefensu inda suke sauri_sauri gudu gudu sukayi Dan a tsorace suke "Mamy " ta tsinkayi muryarsa saida tayi shock a wajen jin muryar da batayi tsammani ba ko a mafarki cikin dauriya da k'arfin hali ta juyo Idanunsu ne ya sartse cikin na juna ta Cikin glass din da aka Zage yake kallonta saurin barin Kallonshi tayi saboda gabanta dake fad'uwa gashi ta kasa gaba ta kasa baya Asmy ma kallonsu ta tsayayi tana son ta tuno Inda tasan fuskar cikin Sauri ta tuno Tabbas shine Mustapha mijin Zarah na *AUREN WATA TARA* "jaber ne ya fito da fara arsa ya ce " manya ne a gari yau kenan Me kukazoyi Asmy "ba tare da kallesaba Dan tun sanda Sukayi cheche kuce din wannan a waya tayi block dinsa ta ce"wani gida ne muka je nan Ciki "ina zaku yanzu?Zaria " ta fad'a "Okay ku shigo " mu tafi naga magriba ta wuce sannan samun hawa a unguwar nan Abu ne mai wahala "cikin Sauri Zarah ta ce " a a zamu koma da Kanmu" ranki ya dad'e kiyi hakuri ku shigo mu mikaku ko garrage ne"ya fad'a da sigar zolaya "Tana kauda kai Zarah ta ce " mungode amma zamu koma da kanmu" "zungurarta Asmy tayi tare da Hararar ta kasa kasa ta ce " ke wai baki da hankali ne duk wuyar da muka sha Munsamu sauki zaki wani ce a a to wlh Saidai na tafi na barki anan amma na gaji"harararta Zarah tayi "MD ne da ya gaji da tsayuwa ya ce " wai tsayuwar me keke Malam ka tsaidamu in basusan a taimakesu ka rabu da su man ha a ka tsaida mutane a titi"Dagowa Zarah tayi ta Kalleshi daidai Shima ita d'in yake kallo cike da takaicin da jin haushi ta hararesa tare da murguda baki taja tsaki tare da Yin gaba abunta ta ce "Ke kuma da baki da zuciya saiki shiga a wulakantaki"Sosai Asmy tayi mamakin Zarah Bayan wuyar da suka sha sannan ma ina ta sani a Kaduna ga duhu ys fara za a taimakesu ta tsaya shine zata k'iya jaber ne ya ce " Rabu da ita ki shigo muje "girgiza kai tayi ta ce " kawai kuje bazan tafi na barta ba "MD ne daga mota ya sauko ya ce " Ki shiga kuje "da mamaki jaber ya ce Kaikuma fa " Hararar da yayi masa ne ya kusa sanyashi Dariya Itama Asmyn saida ta kusa dariyar shiga tayi Ita da jaber Inda suka Tada mota Suka bar wajen shi kuma ya bita da harta fara nisa ya ce "Mamy" Banza tayi masa tanajin haushin disgin da yayi musu "Mamy " ya k'ara maimaitawa "bata waiwayoba haka baisa ran amsa ba " Cikin Sauri yabi bayanta Taku baiyi biyar ba ya cimmata Tare da shan gabanta wani irin Kallo tayi masa sai kuma ta kauda kai tana turo baki "Ta ce " ka bani hanya zan wuce "tsaki yaja tare da cewa " Ke wace iri ce Wai ina zaki da magribar nan angaya maki kd Zaria ce da zaki tafi ke d'aya da dare a kasa Ke uwar y'an Zuciya "turo baki tayi tare da cewa " to ina ruwanka Inma.me zai sameni...bata k'arasa fad'a ba sakamakon murde mata baki da yayi cike da mugunta saida ta saki Kara kafin ya saki ya ce "Ni sa'anki ne da kika rainani ko wace magana kike fad'amun ko Dan Kinga ina d'an sake miki fuska an gaya maki ko wace magana ake fad'amun stupid kawai" durkushewa a wajen Zarah tayi batasan lokacin da wani kuka Yazo mata ba Dan sosai taji zafin murde mata bakin da yayi "sosai kukan nata ya bawa MD Haushi ya rasa wace irin yarinya ce wannan Ganin tana shirin Mikewa tabar wajen ya sanyashi saurin ruko hannunta kokarin fusgewa ta fara ya rik'e gam ganin tana wasting time nasa ya sanyashi rungumota gam a k'irjinshi a tare suka sauke nauyayyar Ajiyar zuciya Zarah ko shiru tayi sai Lafewa da tayi tana shak'ar daddad'an k'amshin turarenshi mai sanyaya zuciya Wayarshi ya lalubo tare da dannawa wata number kira ringing biyu aka daga wayar yayiwa Wanda ya kira bayanin Inda yake Ba ayi minti biyar ba saiga lafceciyar mota fake a wajen An fito an bud'e masa back seat tare ya shiga da ita dukda turjewar da ta fara suna shiga Driver yayiwa motar key suka bar wajen Hade kanta da guiwa tayi ta fara kuka na babu gaira babu dalili tsaki yaja a ranshi ya ce " sudai mata matsala ce wlh ita wannan matsalar tata ma tafi ta kowa mtwss"jin kukan ya fara damunshi ya sanyashi saurin janyota Jikinshi tare matseta tsam kamar zai maida ita ciki gidanshi dake nan g r a ya umarta driver da ya kaisu Bayan sun isa har lokacin shashekar Zarah take jin an tsaida motar ya sanyata saurin Dagowa Kallon wajen tayi daga mota kafin ta kalli MD da a ka bud'e masa yake shirin fita saurin ruko hannunshi tayi ta ce "Ina ne ka kawoni nan kuma" ba tare da ya Kalleta ba ya ce sayar dake nazoyi dukda Zarah tasan wasa yake mata bai hanata tsorata ba marairaicewa tayi ta ce "Dan Allah kayi hakuri ka maidani Makaranta Dare nayi " Banza yayi mata ganin ya fita Ya sanyata saurin fita itama ta bishi baya tana karewa katafaran gidan Kallo Aljannar duniya kenan"ta fad'a cikin ranta binshi ta dingayi cikin Sauri duk Inda ya nufa Dan taji akwai karnika a gidan kuma ita daman ba abunda ta tsana sama da k'are ganin yayi mata nisa ga haushin Karen dake tunkarowa ya sanyata saurin Rugawa a guje Aiko nan Karen ya biyota Dan tayi gudu daukarsa bata Gaskiya ihu Zarah ta fasa tare da rugawa taje ta kankame MD tsam ta fashe da kuka tana yarfe hannu ta gama rikicewa daidai lokacin da Karen ya Iso Inda suke yana haushi murmushi MD yayi ya ce "matsoraciya a ransa common kare ya firgita ta Cikin kuka ta ce " Dan Allah ya Musty ka taimakamun kar Karen nan ya cijeni wlh tsoronsa nake please mubar gidan nan Dan Allah "ta fad'a ta na k'ara kankamesa " Shafa bayanta yayi yana Daddab'a cikin sigar lallashi batare da yace mata uffan ba shafa kan Karen yayi Tare da ce masa yabar wajen Lokaci guda Karen yabar wajen Ajiyar zuciya Zarah ta sauke Dan Allah kadai yasan irin yanda zuciyarta ke Bugawa saboda tsoro "matsoraciya saiki sakeni tunda na kori Karen kuma daga yau Kika karayimun musu ko na fad'a magana kika maida ga da abunda zan hadaki ina da ire_irensu sunfi goma" cike da kunya ta zame jikinta daga nashi turo baki tayi Jin Abunda ya ce "wara idanu yayi tare da nuna kanshi da yatsa ya ce " ni kikewa"cikin shagwabar da ta zame mata jiki duk sanda tazo mata ta ce "Nifa ba da kai nake ba " ta k'arasa fad'a hawaye na sauka daga idanunta "Had'iye kukan ya fad'a yana kama hannunta " kamar an d'auke nefa haka ta Had'iye kukan shi kanshi har Dariya taso ta bashi ya fusge "harsuka isa katafaran palourn gaban Zarah na fad'uwa saida ta kusa kauyanci cin karo da hadaddun turkey furnitures d'in da suke shake a palourn komai na palourn y'an waje ne bazaka tab'a cewa a Nigeria kake ba "a rakube ta zauna d'aya daga cikin kujerun palourn tana ta kalle_kalle a wayance Wanda bazaka tab'a cewa tanayi ba a ranta ta ce " Wasu na cikin wahala wasu bama susan anayi ba jifa Dan Allah wannan lafcecen gida da kayan cikinsa kamar baza a mutu ba "zaki iya tashi kije kiyi salla kafin na dawo ga bedroom Chan" ta tsinkayi muryarshi data dawo da ita daga duniyar tunanin da ta Lula Firgit ta Kalleshi kamar mai shirin fashewa da kuka ta ce "Amma kuma ni kad'ai zaka bari a gidan nan ni tsoro nakeji wlh karnikan nan karsu shigo Su cinyeni ni kadai" murmushin da baikai fuska ba yayi ya ce "bazan jima ba zandawo babu abunda zasu maki bazasu shigo nan ba " Badan taso ba ta ce "To Amma karka jima Dan Allah " Ba tare da ya amsa ta ba yayi Hanyar waje tanajin fitarshi ta turo baki tare bin kofar da harara ta ce "Mugu Allah saiya sakamun ta fad'a tana nufar d'akin da ya nuna mata Dan tayi salla Nanma saida tayi kauyanci cin karo da kayan alatun dake dakin ga gaban mirror din dake shake da kayan shafa irir_iri tab'e baki tayi cikin Sauri ta shiga toilet tayi alwala ta fito Bayan ta tada salla cikin Sauri ta bar d'akin Dan ji take a tsorace take palourn ta dawo ta zauna Kan kujera tare da Yin tagumi sai Bayan isha i Taji tsayuwar mota lek'awa tayi ta window taga shine cikin Sauri ta koma ta zauna harya shigo Mikewa tayi ta ce " yawwa nazo mu tafi ya Musty?Batare da ya Kalleta ba ya ce "Sai gobe " yana gama fad'ar haka ya Aje take away din da ya shigo dashi tare da Yin hanyar dayan bedroom d'in da Kallo ta bishi har ya wuce Tana turo baki ta daga wayata da Asmy ke kira daga bangaren Asmy ta ce "Wai kina ina harna dawo tun d'azu " Ina kd "ta fad'a kasa kasa" Kd kuma to me ya zaunar dake "Ya ce sai gobe " ta fad'a tana shirin fashewa da kuka "Daga bangaren Asmy tayi Dariya " Au cewa zakiyi Amarci za a sha keda Angon naki"Dogon tsaki Zarah taja cike da jin Haushi ta ce "Banza y'ar iska Allah kiyaye wannan ya zama mijina " kit ta kashe wayar tana Jan tsuka Daren ranar dai taga MD baida shirin maida ita gashi tunda ya shiga bai fito ba Bayan tayi Sallar isha I a palourn bacci ya kwasheta cike da gajiya gararanbar da suka sha A waje MD ko daman tuni yayi bacci Dan yau akwai gajiya a tare dashi Dan dawowarshi metting kenan daga Abuja suka had'u dasu Zarah washegari Around 10 Zarah ta shirya tana palour Tana jiran fitowarshi ya fito ya maida ita Cikin tsadaddan shaddarsa ya fito yasha shiga ta alfarma ta manyan mutane kallo d'aya Zarah tayi masa tayi saurin k'asa da kanta saboda gabanta dake fad'uwa sosai taga yayi wani irin masifar kyau a sanyaye ta ce "Ina kwana" muntashi lafiya ya fad'a yana karasowa palourn "Tare da cewa " Kinyi break fast ko?gyada mishi kai tayi "eh " Okay to muje a saukeki "Cikin farinciki Zarah ta d'ago ta ce " Thnks "Dan tayi mamaki dazai maida ita cikin Sauri saikuma ta ce " Naga bakayi break ba fa"Eh bana ra'ayi ya fad'a "Dan azumi yake tab'e baki Zarah tayi tare da mik'ewa ta ce " kai ka sani miskili kawai" a tare suka jera suka fito gwanin sha'awa kamar wasu masoya Dan sosai naga matching d'insu Shigowar Mota ya sanyasu tsayawa bin motar MD yayi da Kallo harta karaso parking space d'in yana kallon motar Kafin yaga fitowar Amera cikin shigar da ta saba ta K'ananan kaya driver yana rik'e da Akwatinta shock a wajen Amera tayi ganin mijinta sun fito tare da wata daga cikin gidan lokaci guda idonta ya rufe wani azababben kishi ya taso mata dak'yal ta iya daidaita numfashinta dake sartse mata cikin bala'i da masifa ta tunkaro Inda suke Wanda har lokacin suma kallonta suke musamman MD da yayi mamakin zuwanta Zarah ko tuni cikinta ya Dori ruwa Ganin yanda take tunkarosu " Tsaye Amera tayi tare da daure k'aramun beil din da ta yafa a kugu ta ce "Yau akwai kutumar bura uba a garin nan kace yau akwai tashin bomb a kaduna wanda zai tashi da uban kowa Wace karuwar y'ar Iskar ce wannan Mustapha ?......✍🏿 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️.......*47 & 48* "Na ce Wace y'ar kutumar uban ce wannan Mustapha " Kallonta MD ya tsayayi da mamaki Ganin bazai bata amsa ba Amera ji tayi kamar a mafarki cikin zafin nama tayi kukan kura tare da shako wuyan Zarah cikin wani irin Hargagi ta ce "zakisan kin shiga gona ta Dan kutumar ubanki shegiya y'ar iska karuwa yau saidai uwarki ta haifi wata amma yau d'innan saikin bakunci lahira tunda har kika iya bin mijina bakisan Kallon mijina ma mace batayi bare har na ganku tare Tabbas ajaline ya kawoki gidan nan Dan saidai a fitar da gawarki daga gidan nan billahillazilla'ila illa huwa" iya rudewa Zarah ta rude ga ta kasa kwatar kanta daga shak'ar da Amera tayi mata Cikin b'acin rai MD ya daka mata Tsawa ya ce "Sakarta Amera kafin ranki ya b'aci banason hauka" Cikin kuka da Hargagi Amera ta ce "Wlh saina kasheta " Kokarin kwatar Zarah MD ya fara amma ya kasa saboda cike da zuciya Amera tayi ruko ganin zata illatata Dan harta fara numfaffashi ya sanya MD d'auke Amera da wani irin gigitaccen Mari Wanda ba shiri ta saki Zarah tana dafe kumcinta ta ce "Ni ka Mara Mustapha " An mareki din stupid mahaukaciya da kishi zai haukatar dake kasheta zakiyi ko Me?ka fad'a kome zaka fad'a indai akan wannan ne na shirya wlh kaji na rantse saina kashe tsinanniyar yarinyar nan saidai nima a kasheni munafiki maci amana ashe Fasik'anci kake shiyasa kake tahowa k'asar kak'i waiwayata ashe karuwai kake kawomun har cikin gida wlh da wani ne ya bani labari bani na gani da idona ba zan yarda ba fasiki maci ama....bata k'arasa maganar ba sakamakon Saukar Marin da taji Tass tass har guda Ukku "wani ihu ta buga tare da nuna kanta ta ce " ni ka mara akan wannan karuwar mustapha Aiko zakasan ka mareni ta fad'a tana tunkarar Inda Zarah ta durkushe ta na Maida numfashi sosai kalaman Amera ke dakar mata zuciya ganin tayo Wajenta ne ya sanyata saurin tashi ta boye Bayan MD sai Lokacin ta samu damar fashewa da kuka "Wlh Amera kika k'ara tab'ata zakiga b'acin raina yanda bakiyi tunaniba wai hauka ne kike kome me kike shirin aikatawa saboda kishi ya rufe maki ido" Cikin kuka Amera ta ce "zakaga hauka Mustapha zakasan ka taboni ka jira fitowa ta ta fad'a kamar wata mahaukaciya tare da Yin hanyar Ciki ganin haka ya sanya Zarah rudewa cikin kuka ta ce " Dan Allah ka fitar dani daga gidannan na shiga ukku "MD Yama rasa yanda zanyi Cikin Sauri ya nufi parking space tare da dauko mota Zarah hada tuntub'enta wajen shiga tana shiga sukaga fitowar Amera hannu d'aya da tabarya hannu d'aya kuma lafceciyar wuk'a mai kamar Adda iya rudewa Zarah ta rude Duk Addu'ar da tazo bakinta yi take cikin kuka ta ce " Kayi Sauri karta karaso na shiga ukku ni Fatima Wannan wace irin masifa ce "ta fad'a tana fashewa da kuka da karfi yaja motar Horn D'aya yayi mai gadi ya bud'e masa da gudu Amera ta nufo su tana ihu tabarya da wuk'a a hannunta ta ce " ka bud'e musu get suka Fita wlh a bakin aikinka"lokacin har motarsu ta fita Wata nauyayyar Ajiyar zuciya Zarah ta sauke amma dukda haka gabanta fad'uwa yake MD ko mamaki ne cike a ranshi bai tab'a tunanin haukan kishin Amera yakai haka ba wata irin zufa ce Ke keto masa Har suka isa Zaria cikinsu ba Wanda yace uffan daidai kofar A B U yayi parking Tare da ciro bandir din y'an Dubu dubu ya mik'a Mata girgiza kai tayi har lokacin gabanta fad'uwa yake ta ce "a a nagode " wani irin kallo yayi mata tare da cewa "Bana bada Abu a a mayarmun doka ta ce wannan ki kiyaye kinga damar ki yaddasu ko kiyi sadaka wannan ba damuwata ba ce " Amsa Zarah tayi harzata fita Ya riko hannunta Wanda dukda suna cikin tashin hankali bai hanashi jin shock ba makulli ya damka mata ya ce "Ki kwashe kayanki ki koma Gidana dake nan karna dawo na iske baki koma ba" Tana shirin fashewa da kuka ta ce "Dan Allah karkace saina koma wlh banajin dad'in zaman Chan" Umarni na baki ba shawara ba sannan karki koma kiga Abunda zai faru"hawaye na zuba a idonta ta ce "To taya zan iya zama a wannan gidan ni d'aya wlh ni bazan iya zama ba " wani tunani ne yazo masa kuma hakane bazata iya zama gidan nanba ita daya Dagowa yayi da Kalleta Da har lokaci hawaye basubar zarya a idonta ba ya ce "Gobe zanshigo Garin Around 4 Idan na tafi saiki koma hostel din hakan yayi miki ai ko?saita samu kanta da daga masa kai " A hankali ta fita daga motar harta bace masa gani baibar kallonta ba kafin ya sauke ajiyar zuciya kanshi ya had'a da sitiyarin mota yayi minti goma batare da ya dago ba ya rasa abunda yake masa dadi Dak'yal ya iya tashi yayi driving ya juya Kd tun a hanya yakejin ringing wayarsa bai dagaba ganin missed call d'in yayi yawa ya sanyashi dubawa yana ganin Number Ammy ce saida gabanshi ya fad'i a sanyaye ya d'aga sabon kiran d'aya shigo "Duk Inda kake kazo ka sameni a gida yanzunnan " Yanayin yanda Ammy tayi maganar ya tabbatar masa da tana cikin fushi a sanyaye ya ce "Gani nan zuwa ammy'" Bata amsa ba ta katse kiran "numfashi mai zafi ya fesar kafin yaci gaba da driving cikin Rashin nutsuwa Koda ya isa kd kai tsaye gidansu ya nufa A palour ya tarar da Ammy sai Chuchu gefenta tana Danna waya Amera na Kan sopa itama ta hade kai da gwuiwa tana kuka girgiza kai kawai yayi Dan yanzu kam ya tabbatar da kishin Amera ya wuce yanda yake Tunani Kennan Ammy tazo ta sanarwa " waje ya samu a palourn ya zauna Ba yabo ba fallasa Ammy ta amsa gaisuwar da yayi mata sannan Chuchu ta gaisheshi kamar ko yaushe yanda take gaisheshi Ajiyar zuciya Ammy ta sauke tare da Kallon MD ta ce "Yanzu Amera take zomun da wata magana wacce ta kusan girman tunani na hakane gaske ne koko?Batare da nuna alamun damuwa ba ya ce " wace magana kenan Ammy"Kallon Amera Dake kuka har lokacin Ammy tayi ta ce "maimaita abunda kika fad'amun " Kamar mai jira cikin kuka Amera ta ce "da Mace na kama su a gida na " Da mamaki MD yake kallonta Cike da mamaki ya ce "Kika kamamu Amera fa kikace zaki iya rantsewa da Qur'an Akan kin kamani da wata mace " Tana kuka ta ce "ba kamawa na iskanci ba Ai kamawa na bahaushe kun fito tare kaida ita daga pournmu"Kallon mamaki Ammy da Chuchu suka dinga binta da su Chuchu ta ja dogon tsuka ta ce " Daman ba na fad'a maki ba Ammy saikace dai bakisan halin yaya ba nasan wallahi yaya bazai tab'a aikata abunda tazo ta fad'a ba sharri ne kawai take neman K'ulla masa dan munafurci Mtwsss "daga mata hannu Ammy tayi ta ce " Karna karajin bakinki a nan Auta Amera sa'arkice karna kumajin bakinki a maganar nan "Tana turo baki Chuchu ta tashi tare da gallawa Amera harara da itama Amerar hararartata ta ke Dan daman Chan basa jituwa tabar palourn tana Jan tsoka maida hankalinta wajen Amera ammy tayi ta ce " Fad'amun gaskiyar abunda ya faru"Har lokacin kuka ta ke....nan ta labartawa Ammy komai da ta gani iya gaskiyarta har tafiyar da yayi da ita da shakar da tayiwa yarinyar.Kallon MD Ammy tayi ta ce "Hakane babana" Batare da tsoro ko shakku ba ya ce "Hakane Ammy" Me ya hadaka da mace babana har cikin gidanka kuma Alhalin ba kowa a gidan"?Tambayar da tun farko ya kamata tayi Amma ta kasa"ya fad'a ya na Hararar Amera "To yanzu fad'a mana meye alakarta da ita "Numfashi yaja kamar bazai magana ba saikuma.ya d'ago ya ce " Kanwar Jaber ce Tare suka zo bata da lafiya ya dawo da ita daga Asibiti sai akayi mashi kiran gaggawa Compony kasancewar gidana ne Inda yafi kusa da Inda yake shine ya nufo gidana da ita ya tafi kasancewar bata lafiya Saiyace ta jirashi anan kafin ya dawo ganin ya jima ne ya sanya nace bari mu fito Kawai na sanya driver ya kaita gida shine fa "Salati Ammy tayi ta na kallon Amera ta ce " Tofa kinji Kike tada jijiyoyin wuya yanzu Dan Allah wannan dame yayi kama Wannan wani irin zafin kishi ne gareki Amera ba bincike ba komai kin kama y'ar mutane da Duka bama lafiya gareta ba yanzu Dan Allah iyayenta muna mutunci dasu sukaji zasuji dadi kuwa?Goge hawayenta Amera tayi ta ce "Kiyi hakuri ammy bankawo komai a raina bane sharrin shaidan ne " tab'e baki Ammy tayi ta ce Allah kiyaye "ta Mike tabar palourn cike da jin Haushi Matsowa tayi kusa da MD da ya lumshe idonshi tayi cikin sigar Ban hakuri ta ce " Kayi hakuri honey Dan Allah"Bai tanka mata ba haka bai bata amsa ba "Tana shirin fashewa da kuka ta ce " Please honey Dan Allah ka yafemun kasan kome nayi nayishine saboda sonda nake maka tsananin kishin Kane ya sa na aikata komai "Dagowa yayi lokaci guda d'aya Kalleta yaga irin yanda idonta yayi ja " girgiza kai yayi ya ce "kishi hauka ne Amera?haka ake kishi?yanxu da kin Kashe y'ar mutane ki ce me ?So kike ki ja mana bala'i ,sannan ji maganganun batancin da kika dinga fad'amun matsayina na mijinki hakan da kikayi tarbiya ce,Ko angaya maki haka ake kishi" kama hannunshi Tayi tana kuka ta ce "Kayi hakuri honey bana iya control d'in Kaine ne akan kishin da nake maka " tab'e baki yayi baice Mata komai ba "Kayi hakuri Dan Allah Karkayi fushi?Dagowa yayi yaga yanda tayi kalar tausayi lokaci guda saiya sakar mata murmushi ya ce " ya wuce my merah"Ajiyar zuciya ta sauke tare da kwancewa jikinshi ta Ce"Thnks mijin da yafi na kowa "a hankali ya zame jikinshi da nata Dan kar Ammy ta fito a tare sukaje sukayiwa Ammy bankwana sannan suka kama hanyar gidansa a hanya MD sai mamaki yake yanda ya iya shirya k'aryar wannan around 10pm suna zaune a palour ta narke masa a jiki ta ce " Honey baka tambayeni ya akayi na dawo yau ba"yana wasa da gashin kanta ya ce "saikin fad'a" Cikin farinciki ta ce "Gajiya nayi da zaman kadaici kuma bazan juri Rashin ka a kusa dani ba shiyasa na yanke shawarar biyo mijina ko na samu lada " Kin kyauta "ya fad'a " Nan suka Dan tab'a Hira Kad'an kafin suje su kwanta sosai Amera tayi mamakin yanda MD baiyi kokarin yi mata komai ba a ranta ta ce "huta roro Allah ya taimakeni" Dan tasan irin wahalar da takesha musamman idan suka jima basa tare da wannan tunanin har bacci ya d'auketa Wanda Bata kawo komai a ranta ba. Dariya Asmy ta kwashe da ita Bayan ta gama sauraran labarin da Zarah ta bata ta ce "Kam amma Matar nan anyi y'ar iska wlh tabarya fa da Adda kikace yo ko dai k'aura ce?Duk yanda Zarah ta hade rai Dan sosai maganganun Amera suka daki zuciyarta na ce mata karuwa da tayi Jin Abunda Asmy ta ce batasan lokacin da tayi Dariya ba ta ce " Kai sis baki da dama wlh wai Kaura "Asmy na Dariya ta ce " to inba yar daba ko Kaura ba wazaiyi haka itadai wannan kishin nata na hauka ne Wlh Dan daga gani matarsa ce "tab'e baki Zarah tayi ta ce " oho dai koma me dinsa ce chanta matse musu"asmy ta ce"Ke matarsa ce ma Gaskiya tunda Kinga daman sunce akwai matarsa da ke karatu waje saura wata Tara ta gama kila Hutu ne tazo""Umm hakane na ganta da akwati kuma a zagin da tadinga mun ta ce mijinta dukda tashin hankali bai bari naji sauran abunda take fada ba Ni fa bama wannan yafi damu na ba yanzu Wai gobe Nakoma gidansa da kayana ni bansan yanda zanyi da wannan murdadden mutumin da kuka lakamunba wlh"Asmy na boye dariyarta ta ce "yazakiyi dole Kibi umarnin mijinki tunda haka ya ce " Dundu a baya Zarah ta kaimata ta ce "Bansan iskanci asmy Allah kiyaye wannan ya zama mijina " Asmy na Dariya ta ce "To yanzu me d'inkine inba mijinki ba "harara Zarah ta galla mata ta ce " Mijin wucin gadi dai harna k'agara 9 months d'innan yayi na huta wlh "Kedai fad'i Gaskiya Malama kemafa nasan harkar nan sonta kike har kiba kikayi irin kinsamu abunda kikeso " Asmy ta fad'a tana dariyar shak'iyanci saurin barin zancen Zarah tayi Dan karta b'allo mata ruwa...washe gari Zarah badan taso ba saidan Asmy ta karfafa mata akan taje karyazo makaranta ya jaza mata wani abun ya sanya Zarah shiryawa ta tafi gidan saida ta share gidan Tass lungu da sako tayi mooping dan taga yayi kura ta sanya tsintsiyar k'amshi da air freshener mai dad'in k'amshi kafin kace me gidan ya kaure da sanyin ni'ima ganin irin aikin da tayi ga zufa ya sanyata yin wanka a toilet din D'akin Bayan ta fito tayi Sallar Riga da sicket d'inta na atamfa da sukayi mugun amsar choculate colour din fatar ta ta mayar Sosai kayan suka kamata daman Chan Zarah Indai zata sanya kaya tofa saisun fito mata da shape d'inta Y'ar hoda da kwalli kawai ta zizara badan komai ba saidan sabo da intayi wanka saita shafa su sannan ta fesa daya daga cikin turarrukan da tagani a jikin mirror sosai ta feshe turaren hada mugunta taga bati Ganin bayanan ya sanyata sakin jiki ta fito palour ba hijab rasa abunda zatayi tayi hakan ya sanyata d'aukar wayarta ta fara chat sosai ta shagala da chat har batasan shigowar motarshi gidan ba saida taji karan shigowa ya sanyata saurin firgita ta kalli kofa Shigowa yake cikin shigar da ya saba ta turawa da suke mugun Yi masa kyau Kallo d'aya tayi masa tayi saurin kasa da kai MD sosai yaji dadi da ya iske gidan tsaf tsaf a rayuwarsa Ba abunda yakeso sama da tsafta har wani lumshe ido yake Dan sosai yakeji dad'in k'amshin na ratsa sa lokaci guda a rayuwarsa da yaji yarinyar ta burgesa Karasawa palourn yayi binta ya dingayi da Kallo da kayan jikinta da suka dameta Zarah dukda ba kallonsa take ba Amma saitaji kunyar shigar da tayi a fakaice ta d'ago tana Kallonshi Idanunsu suka sartse Cikin na juna samun kanshi yayi da sakar mata murmushinshi mai tsada gabanta na fad'uwa Tayi kasa da kanta jinta take duk a takure ta kasa koda magana daya lura da hakan ya sanyashi Zuwa kujerar da take tare da zaunawa dab kamar zai shige jikinta a hankali cikin husky voice dinsa ya rad'a mata "haka ake tarbar miji" Wara idanu tayi tare da Kallonshi sai kuma ta turo baki a ranta ta ce "Yau kuma da salon barikancin da kazo" murmushi yayi ganin yanda tayi saida ya basa Dariya Janyota yayi jikinshi tare da d'ora hannayenta gefen hips d'inta yana shafawa cikin wani irin salon da yaso rikitar da Zarah cikin salo yake shafa hips d'inta yana lumshe ido Yayinda Kanshi yake bisa kafadarta yana shinshina wuyanta bakinshi yakai saitin kunnanta tare da sanye harsheshi a ciki ya fara mata wani irin Abu ji take tsikar jikinta na tashi saurin rumtse ido tayi cikin kasalalliyar muryarsa ya rad'a mata a kunne ya ce........✍🏿 *07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 🅿️.........*49 & 50* "Kishiyarki ta ce a gaishe da ke " wara idanu Zarah tayi saikuma tayi Dariya tunowa Da Amera rufe bakinta tayi tana gumtse dariyar da tazo mata Kallonta ya tsayayi yanda take dariyar cikin nutsuwa jin ta gimtse ya sanyashi murmusawa ya ce "Ko na kira maki ita kiji da kunnanki"Tana Dariya ta girgiza kai" Murmushi yayi ya ce "Kina tsoranta ne?" Uhm saboda Kaura ce karta kasheni"wara idanu yayi cike da mamakin jin Abunda ta ce ya ce "Matar tawa ce Kaura" Dagowa tayi ta Kalleshi sai kuma ta turo baki tayi kasa da kai "d'an murmushi yayi ya ce " ni kike turowa baki Ko Duk kishi ne ya sanyaki haka?da mamakin jin Abunda ya fito daga bakinshi ta ce "Allah kiyaye " meye kikewa Allah kiyaye kishin nawa ne bakyayi "Gyada mashi kai tayi" wara idanu yayi ya ce "to meyasa nasan dai duk mace na kishin mijinta? Ai kai ba mijina ba ne " To me d'inki ne?Mijin wucin gadi ne ko kuma mijin *Auren wata Tara* kaga ko akanme zanyi kishinka "Dariyar da bai shirya ba MD yayi wara idanu tayi ganin yanda yake dariyar sosai yayi kyau da Dariya saida ya tsagaita kafin ya ce "mumu girl kin iya fadar magana daman har haka"harara ta maka masa kamar zatayi kuka cikin shagwaba ta ce " Ni ba mumu ba ce "Murmushi yayi ya ce " To Beauty ce?I don't know "ta fad'a tana shan magani" yanda tayin ne ya k'ara basa Dariya ya ce "Kin iya shagwaba daman kenan ?Batace uffan ba " shiru sukayi na Dan mintuna kafin ta d'ago ta Kallesa ta ce "Wai daman kana Dariya" Murmushi ya sakar mata yana lakutar kumatunta ya ce "Saita kama " marairaicewa tayi ta ce "tafiyi maka kyau akan had'e fuskar nan da kake ka dingayi " murmushin ya sake mayar mata ya ce "kina son ganin ina Dariya kenan "Samun kanta yayi Da daga mashi kai "to zan dingayi daga yau mumu girl ya fad'a yana Mikewa " kamar zatayi kuka ta ce "Ni Allah ka daina Cemun mumu bana so" To Mamy "ya fad'a yana shiga bedroom da kallo ta bisa har ya bacewa ganinsa kafin ta sauke ajiyar zuciya lumshe ido tayi a ranta cike da mamaki ta ce " Daman yana magana haka harda Dariya "samun kanta tayi da sakin murmushi sai wajen 6 ta ga ya fito da wasu K'ananan kayan da ya saba zama da su a gida a lokacin waya na K'are a kunnen ta tana saya da Hafiz da ya kira kallo d'aya tayi masa ta kauda kai tana cigaba da wayarta da Hafiz ta bangarenshi Shima kallo d'aya yayi mata ya zauna yana kallon Kwallo a makekiyar plasma din dake manne a d'akin cikin shagwaba ta ce " A a a Ya Hafiz Gaskiya ni bazanyi kamu ba banason bidi'a a bikin kawai walima zanyi "daga bangaren Hafiz ya na Dariya Ya ce " na manta fa ashe Amaryar tawa Malama ce Amma Dan Allah ki bari ko event d'aya ne ayi please abun zaifi kayatarwa"Girgiza kai tayi ta ce "a a a ya Hafiz kawai ka barshi ni Allah bazan iya kamu ba gwara ma kayi lunch kaida abokananka yafi" Eh kuma kin kawo shawara me kyau zanyi lunch din kawai yanzu me kike?bakomai?ina Asmy?gabantane ya fad'i ta rasa k'aryar da zatayi"ta ce "Uhm gata nan " Okay kwana biyu bamu gaisa ba b'ata mu gaisa "Gabanta ya k'ara bada daram Dagowar da zatayi ta sauke akan MD da ya kura mata ido ba ko k'iftawa in ina ta fara ta rasa abun cewa Chan kuma ga ce" Uhm tadan shiga toilet "okay to shikenan next time magaisa ki kulamun da kanki bye I love you" love you too"ta fad'a kasa kasa tana rufe fuska "Bani wayarki?ta tsinkayi Muryarshi daga sama" Da mamaki ta dinga Kallonshi kafin ta ce "wayata kuma ?Eh ko kurma ce Ke ?To saboda me zanbaka wayata " Saboda kin karya Dokar gidana ba ayimun waya a cikin gida dama ko waye sai anfita "Mamaki duk ya cika Zarah " a ranta tace waishi wannan wani irin mutum.ne mai siffa biyu dazu mutumin kirki yanzu ya koma wani Kamar mai tsaron wutar jahannama "Samun kanta tayi da cewa " Ai baka fad'amun ba da wannan dokan "yanzu ai kin sani" Danne fushinta tayi Dan batason rigima ta mik'a masa wayar ta na shan kunu"Amsa yayi yana cigaba da Kallo ba ayi minti biyar ba Kuma saitaga ya maido mata cikin Sauri ta amshi wayarta tana Sanyawa a jaka Mikewa tayi ta shiga bedroom ta na turo baki da dare Take away yayi musu sukaci Around 10 Zarah harta kwanta Amma bacci bai d'auke taba taji shigowarshi tana jinshi ya shiga wanka a ranta ta ce "shidai baya gajiya da wanka kamar kwado Saikuma ta ce " ai naga alama tsaftace tayi masa yawa "tana jinshi ya fito ya shafa lotion da turarruka masu sanyin k'amshi Gado ya zauna tare da janyo laptop dinsa ya fara operating cikin nutsuwa Zarah tana jinshi har bacci ya d'auketa jin saukar numfashinta Alamun bacci ya d'auketa ya sanyashi linke Laptop din ya maida ita gefe Dan tun dazu dauriya kawai yake amma a matse yake janyota yayi jikinshi tare da Fara Aika mata sakwanni Zarah cikin bacci taji abun kamar a mafarki tana farkawa taga gaske ne Zatayi magana yayi saurin hade bakinsu waje Daya....... MD shine Baidamu gamsuwa ba sai wajen Asuba Dan yarinyar jinta yake kullum kamar Kara mata dadi ake tamkar Zuma haka yakejinta gashi kuma mamakinshi na hakurinta duk yanda ta gaji da abun Bata nuna masa ta gaji cike da gajiya Zarah taje tayi wanka Dan sosai tayi likis ga Rashin bacci Shima Bayan yayi nashi wankan yayi alwala ya wuce masallaci Zarah na gama salla a sallayar baccin gajiya ya kwasheta yana dawowa ya isketa yanda ta takure take bacci saita basa Tausayi Daukarta yayi ya maida ita kan gadon a hankali Kafin Shima ya rungumota Bayan yaja musu blanket sune basu tashi ba sai 12Pm sosai Zarah tayi mamakin lokacin da suka kwashe suna bacci sai sannan ta tuno da tana da CA sosai hankalinta ya tashi gashi tasan Angama MD shigowarshi kenan d'akin Bayan ya shirya da dayan d'akin kallonta yayi ganin yanda ta firgice ya ce "Lafiya?Kamar zata fashe da kuka ta ce " text gareni yau tun 8 kuma yanzu har 12:30 "tunda C A ce ba saiku hade a Exams ba " Tana shirin fashewa da kuka ta ce "Yana da tsauri malamin Text din ita ke taimakawa " ya sunan Malamin "Umar" Umar Habibu"Cikin Sauri ta ce "Eh eh shi" Okay gobe zamuje saiya yi miki Tunda yanzu ta wuce "Ya yarda yayimun kuwa baya yarda fa ko assignment ya bayar kakai daga baya baya amsa bare text" Zaiyi maki karki sake musu "Shiru Zarah batare da tace uffan ba " yana gyara kwalar rigarsa ya ce "Akwai komai a kitchen ki girka Abunda yayi miki sai zuwa dare zandawo " Dan Allah na tafi hostel to "Ban bada umarni ba " ya fad'a yana barin d'akin "Dogon tsuka taja tare da kwaiwayar sa " ban bada umarni ba"ta fad'a tana yamutsa fuska tare da Jan tsaki ta ce saikace wani uba na "Koda ta fito palourn harya bar gidan Kitchen ta shiga ta girka lafiyayyan indomie da tasha vegetables da kwai sosai ta kimtsa cikinta kafin ta gyara gidan Dan Zarah Daman Chan ma'abuciyar tsafta ce ita aiki baya gunduranta Dan tayi training aiki a wajen Mama Rabi idanma batayi ba wani iri takejin jikinta Bayan ta gama tayi wanka tayi sallar Azahar what's app tahau ta d'an duba sakwanni kafin ta kwanta ta koma bacci Dan har yanzu Rashin baccin jiya bai gama Sakarta ba. Yanda ta lafe a jikinshi yana yi mata magana kasa kasa zai tabbatar maka da Lallashinta ne ya ke " Cikin muryar mai shirin fashewa da kuka ta ce "Amma Honey Jiya ma fa Cemun kayi bazaka kwana ba yanzu kuma kazo mun da wata magana Wai zakayi tafiya maiduri yaushe rabonka da garin sanadin Hajiya kaka ta k'ara takura maka Akan maganar Aure wanda kasan bazan taba juran hakan ba zan iya mutuwa akanka md dana zauna da kishiya sanin kankane bana kaunar hakan kasan ganinka yake tuno mata da abun please honey karkaje" murza hannunta yake ya ce "My Merah kenan Baki da zance saina kishi me ya kawo zuwana kuma da maganar kishiya kinsan na jima banjeba shine zanje mu gaisa da y'an uwa " Dak'yal da lallashi MD ya shawo kanta ta amince masa Akan zaiyi one week amma tace zata zauna ne a gidansu saida yaga tafiyarta kafin ya d'auki hanyar komawa Zaria kamar ko yaushe a motarshi da ba a Santa ba Kuma mai tinted koda ya isa ya iske gidan tsaf_tsaf Sannu yayi mata ganin harda lafiyayyan girki tayi...washegari Zaune suke a office d'in Mlm Umar ita dashi sosai Zarah tayi mamakin yanda Mlm Umar ya amince cikin Sauk'i hada fara'arshi akan zaiyi mata text D'in amma question d'inta Da ban ya rubuta mata nan ya mik'a mata MD na kallonta yanda take rubutu da kanta saida ta cika paper hada bayanta shi kanshi yayi mamakin kokarin yarinyar da kanta tayi abun nan in banda yana wajen da saiyace kwafa tayi Bayan tagama tayi submitted Kallonshi tayi ta ce "Zanwuce hostel ?karkije jirani jikin mota " Zarah na turo baki ta fita Tana fita ta kira Asmy ta fad'a mata Inda suke Bayan fitarta Kallon Mlm Umar MD yayi ya ce "Tana maida hankali yarinyar?Tana da kokari ai sosai aboki School d'innan ai babu mai matsala da Zarah ga girmama malamai yarinyar akwai Ilimi wlh ga nutsuwa ai inbanda mata na hud'u ai da na k'ara da ita wlh idan kunbani ma sai na saki guda" Tashi MD yayi tare dayi mashi musabaha ya ce "mun wuce sai anjima" Binshi da Kallo Mlm Umar yayi ya ce "Tofa ko meye alakarshi da yarinya naga mood dinsa ya chanza Dan nafada Dana yi ta hud'u da ita saiya tuna last time daya kirasa akan ya kira masa ita yace masa cousin sister dinsa ce " a bakin mota ya tarar da Zarah tare da Asmy suna ta hira suna Dariya Gaisheshi Asmy tayi ya amsa ba yabo ba fallasa horn yayiwa Zarah Bayan ya shiga Sakin hannunta Asmy tayi ta ce " Sai gobe kawai karki tsaidashi "Harararta Zarah tayi tana turo baki ta shiga gaba " Har suka isa ba mai cewa uffan suna isa ta iske dogayen riguna a palourn jibge kuma duk masu manyan kudi sai hijabai "ki kwashe ki kai bedroom d'inki " yana gama fad'ar haka ya wuce ciki..washegari Bayan tayi shirin tafiyarta makaranta 5k ya mik'a mata har zataki amsa tunowa da maganar da yayi mata rannan ya sanyata amsa tare da cewa "Thnks" Karfe nawa zaku gama lecture din?Karfe biyu?Okay "tana fita ta samu driver na jiranta cikin girmamawa ya ce " Hajiya barka da fitowa nine sabon driver d'in naki da zai dinga kaiki"Da mamaki take binshi da Kallo tana tunanin me.MD yake nufi koda suka gama lecture tana fitowa taga driver d'in tana Jan tsaki ta ce "Gaskiya nidai nema ake a takura rayuwata wlh" Cemashi tayi bari ta fito tana zuwa hostel ta samu Chuchu da Asmy cikin Sauri ta Ruga ta rungumesu ta ce "Daugher yaushe kikazo" dazu na shigo wlh duk nayi kewarki momcy sosai suka dinga hira Zarah harta ma manta da driver sai wajen 3 ta tuno Firgit ta mik'e ta ce "Subhanallahi na manta nabar driver waje sai Allah ya kaimu tayi saurin fad'a tare da barin dakin tana zuwa ta samu driver d'in bai tafi ba yana can Inda ta barsa tana shiga ya ja suka nufi gidan Bayan fitar Zarah d'akin da mamaki Chuchu ta ce " ina zata wai naga ta fita "Karyar da zatayiwa Chuchu Asmy ta nema ta rasa Chan kuma kome ta tuno tayi firgit ta ce.........✍🏿 *07026166536* _Masu fitarmun da Littafi bazanyi Allah ya isa ba saboda littafi amma ku sani hakkina kuke fitarwa batare da izini na ba duk Wanda ya saya kudin karantawa kadai ya biya ba na mallaka ba kusani dai sarai akwai hakki kowa yana da damar karantawa indai ya biya 300 kachal cikin nutsuwa da kwanciyar yafi ka tsintseshi a gantali ka karanta a gantalewa cikin Rashin nutsuwa _ *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 🅿️.........*51 & 52* "Kinsan na Fad'a maki akwai kanwar mamanmu anan to shine takoma gidanta da zama ta na d'an rage Mata ayyuka saboda mijinta baya nan" ayya kice yanzu munzama mu biyu Gaskiya zamuyi missing nata sosai wlh"cewar chuchu"wlhko ai bama kadanba danma ai ba koda yaushe take Chan ba zata dinga dawowa nan" dukda haka dai Chuchu ta fad'a...washegari Bayan dawowarta daga lectures around 5pm tana kwance Kan sopa ta na Karatun exams din dake tunkaro musu shikuma yana operating a system "Kallonta yayi yaga ta maida hankalinta ga karatun da take Bayan ya gama aikin da yake a laptop ya linke ya Aje tunani ne yake karfa yayi gudun gara ya fad'a gidan zago taya za ayi Ace wata biyar yanzu da Auren amma bata samu ciki ba gashi har saura wata hudu yarjejeniyar su ta kare a ranshi ya ce " kodai matsalar daga gareni take?Amma ai Duk asibitocin da naje sun gwadani lafiya ta qalau to me hakan yake nufi "wani tunani yazo masa ya ce " Karfa aikin banza nake Yarinyar nan da abunda takesha tunda wayayyace zaiyi wahala ta yarda ta dauki ciki "wata dabara ce ga fado masa yace bari nayi mata low nagani idan hakane " Mamy"ya kira sunanta a hankali "Aje littafin dake hannunta tayi ta ce " Na'am"Karatun nan tund'azu kike yaci ki bari inba so kike ki hardace littafin ba "murmushi tayi ta ce " Ai da zan samu dama ma na hardace book din da zanji dadi sosai "Uhm kaji dictionary" y'ar Dariya tayi Kad'an ta ce "Uhm"Na tambayeki zaki bani amsa"? Gyada mashi kai tayi ta ce " idan har na sani zan baka ,insha Allah"kina son yara kuwa?Murmushi tayi ta ce "Ina so mana sosaima kuwa " kice mijinki yaji dadi zaki Haifa mai yara da yawa"Gabanta ne ya bada daram tunowa da Hafiz "murmushin da ya lotsar da dimple dinta ta ce " insha Allah"tana rufe fuska "murmushi yayi ya ce " Kenan ni bazaki Haifa mun ba "Wara idanu tayi saikuma ta turo baki ta ce " Matarka kaima ta Haifa maka mana nima mijina zan haifawa "yana jinjina Yarinta irin ta Zarah ya ce " Ayya ni ai matata bata haihuwa shekararmu Tara da Aure amma ko b'atan wata bata tabayi ba "cikin muryar tausayawa ta marairaice ta ce " Ayya wlh harkun bani tausayi Allah ya baku mai amfani Amma kuma kai kana son yara ne"ina sonsu sosaima kuwa tun kafin nayi Aure nake da burin Son yara ina sonsu sosai Wanda har nake tunanin sonsune da yayimun yawa yasa Allah ya jarabceni har yanzu bai bani ba"girgiza masa kai tayi ta ce "kadaina wannan tunanin kasa a ranka lokacin samun sune kawai baiyi Aure,Da Haihuwa Abu ne da Allah ya sanya musu lokaci dole sai lokacin Su yayi tukwana sukan zowa bawa ina maka fatan Allah ya baka masu amfani" Murmushin da baiyi niyya ba ya sakar mata ya ce "Hakane To Allah ya kawo lokacin" a ranshi ya ce "Ga dukkan alamu ba abunda take sha amma Indai hakane Tabbas ina cikin jarabawa ya zanyi da Hajiya kaka?Tabbas dole ne duk yanda za ayi Amera ta koma America kafin na samu mafita " Tunanin me kake ?ya tsinkayi Muryar Zarah "murmushi ya sakar mata ya ce " bakomai Please zaki iya girkamun tuwo irin na rannan"Shiru tayi kamar bazatayi magana ba saikuma ta ce "akwai kayan Had'in ne?Eh akwai komai a ciki" Okay Badamuwa ta fad'a tana Mikewa da Kallo ya bita harta shiga kitchen din kafin ya sauke ajiyar zuciya a ranshi yana mamakin yanda yake sauya wasu dabi'un game da halayyarshi idan yana tare da ita har yake tsayawa yayi doguwar Hira da ita ko Dariya da murmushi Wanda ko a gida bakowani lokaci ba yake yinsu a ranshi ya ce "Saboda Yarinyar simple ce bata da hayaniya?wata zuciyar kuma ta ce " saboda ka chutar da ita a farkon mu'amularka da ita Wanda idan bangyara mu'amula ta da ita ba ko Bayan rabuwarmu zata rikeni mugu a cikin ranta "da wannan tunanin har aka kira Sallar magriba sai Bayan isha'i Zarah ta gama Tuwon da miya ta juye a warmer a dining ta jera Kafin taje tayi Sallar isha'i Bayan tayi wanka ta sanya doguwar Hijab d'inta ta fito Zaune ta tarar dashi a palour yana cin tuwon cikin nutsuwa sosai MD yaji dadin Tuwon fiye da na rannan sai lumshe ido yake da hannu yayi mata nuni da good kafin ya furta " Thnks"a hankali"murmushi kawai Zarah tayi batace komai ba "Bazakici ba ?Sai anjima ta fad'a " a hankali"Zoki zauna muci tare"girgiza masa kai tayi ta ce "A a a " Sanin kanki ne banason musu ko?a sanyaye ta k'arasa ta samu guri gefen k'asar da yake ta zauna "ko kefa mumu girl" Wata irin harara ta banka masa kafin ta maida kanta kasa tana turo baki"murmushi kawai yayi "Cike da jin kunya Zarah takecin abinci bata wani ci da yawa ba ta ce ta k'oshi ba yanda baiyi da ita ba akan tadawo amma takiya ganin zata sanya masa kuka ya sanyasa cewa" Shikenan rigimammiya"tana turo baki ta koma Daki wayarta ta janyo ganin missed call ya Hafiz ya sanya tabi kiran saida ta katse kafin ya kira Hira suka fara Sosai cikin Sauk'i da k'aunar juna sosai suke waya Zarah na kwance saman bed tayi rubda ciki batasan har lokacin da MD ya shigo dakinba ba saida ta tsinkayi muryarsa da cewa "bani wayar " Cikin kid'imewa Zarah ta kashe wayar tana addu'ar Kar Hafiz yaji muryar MD "Dan Alla meye haka wai dan Allah idanfa yaji muryarka me kake tunanin zai faru" tsaki yaja ya ce "so what Dan yaji muryata baki da Gaskiya kenan" Shine fa Wanda zan aura"ta fad'a kamar mai shirin yin kuka"Ni kuma Wanda kike Aura a yanzu ba ?saiki bambance ni dashi wayafi matsayi "Tana turo baki ta ce " Kai ai mijin wucin gadi ne shikuma shine mijina na har abada "kwabe mata bakin yayi ya ce " Ki dinga sanin maganar da zakiyimun hope kin fahimta ko nayi maki kama da sa an wasanki sannan ya fusge wayarta dake ringing yabar dakin"takaici ya ishi Zarah rasa me zatayi tayi kawai sai ta fashe da kuka ta ce "Allah ya isa mugu azzalumi saikace shine ya sayamun wayar da zai amshe wlh nidai an cuceni da aka lakabamun wannan alkakaidin ya zamemun k'arfen kafa ke Asmy kina Chan kina rayuwarki hankali kwance ni kin barni da kunci tana wannan sabbatunta a haka har bacci ya kwasheta MD ko Shima kwanciya yayi yana buk'atar Ta amma wannan Karin bazai jeba Dan karyaja raini a wajen yarinya k'arama harta gane larurarshi ta kawo mashi raini Irin yanda Amera tayi masa Dukda Amera intayi masa babbace ita ko wannan karamar yarinyar da auren wuri ya haifi kamarta bazai yarda ta samu damar raina sa ba...washegari koda ya tashi a daddaure ya tashi ya koma MD dinshi na ainahi Zarah na ganin haka ta kasa masa Rashin kunyar da taso masa akan wayarta saboda muddin tana ganinshi a haka tofa bazata iya gaya masa maganaba ta rasa ya akayi mutumin yake mata kwarjini duk maganar da taso fad'a masa wani lokacin saita kasa a haka ta tafi lecture d'inta batare da ko magana ta had'asu ba inbanda gaisheshinda tayi ya amsa ciki_ciki a sch Asmy ta ce " wai ya akayi nayi ta Kiran numberki kashe sannan ina wayarki"tsaki Zarah taja Dan daman haushin asmy din takeji Dan duk ita taja mata wannan Abun ta ce "Bansaniba" Dariya Asmy tayi ta ce "Allah baki hakuri bani na kar zoman ba rataya aka bani" Tsaki Zarah taja tare da shiga motar driver da yazo daukarta batare da tayiwa ma asmy bankwana ba da dare around 10 tana karatu ya kira sunanta amsa masa tayi ba yabo ba fallasa "Zoki amshi wayarki''ya fad'a yana fito da wayar daga aljihunshi Dan yasan fushin nan da take Na wayar ne " Cikin Sauri ya Mike tare da zuwa "ta mik'a hannunta kenan zata amsa wayar ta subce mata ji kake tasssssss " Hannu aka Zarah ta d'ora ta ce wayyo Allah na ta fashe "Ya Allah MD ya fad:'a kafin ya yunkura ya d'auko wayar da tayi kwatsa_kwatsa kasancewar tilles duba wayar yayi yaga ai tagama amfani Zarah ko tuni harta fara hawaye ta ce Ta lalace ko"Baice mata uffan ba sai zaro sim din da yayi ya ce " ta gama nawa wayar take na biyaki"Dukda taji zafi a ranta amma hakan bazaisa ta ce zata sanyashi ramuwa ba Girgiza kai tayi ta ce " a a a ba saika biya ni ba tsautsayine ko a hannuna ai zata iya fashewa "yayi mamakin jin furucin ta dan A tunaninshi tuburewa zatayi ta ce saiya biyata baice uffan ba sai rike sim d'inta da yayi washegari Zarah harta hakura da waya Bayan ta dawo daga lectures Sannu yayi mata ta zauna tana maida numfashi " Amshi "ya fad'a " Kallon abunda yake nuna mata tayi taga kwalin waya ne "Ta wacece" ta fad'a a hankali"taki "ya bata amsa kai tsaye " wara idanu tayi tace Ni kuma ai bance ka rama munba baxan ansa ba "ba ramuwa bace kyauta ce Na baki" make kafada tayi ta ce "a a bazan amsa ba " saboda me?saboda dalilin ka yardamun yasa ka sayamun"Girgiza mata kai yayi ya ce "Daman nayi niyya ne ki amsa karki k'aramun musu kinsan abunda banaso kenan" A sanyaye ta k'arasa ta amsa tare da cewa "Nagode Allah ya saka da Alkhairi ya k'ara budi" murmushi yayi mata yanajin dad'in addu'ar tata so da yawa ya kanyiwa Amera kyauta ta millions amma godiyarta dashi kawai Thnks sai su I love you Amma ji yarinyar nan yayi mata y'ar k'aramar kyauta da bata kai ta kawoba tana masa irin wannan godiyar "Amen " ya amsa Chan cikin k'asar zuciyarsa "Bud'e kwalin wayar tayi taga An rubuta iPhone 12pro max a jiki " Dukda batasan kudin waya ba tasan mai tsada ce dubawa tayi taga harya mayar mata da sim dinta a jiki numbers ta shiga taga bako d'aya tunowa da batasanya icloud ba ya sanyata Dagowa ta Kalleshi ta ce "Ya Musty Dan Allah ka iya d'ora icloud " kin rik'e password dinne"gyada mishi kai tayi ta ce "Eh log out kawai za ayi kuma banga wajenba " Okay kawo "zuwa tayi zata mik'a mai ya zaunar da ita gefenshi kugunsu waje Daya amsar wayar yayi tare da cewa " ki Kalla yanda ake ",,Tana Kallonshi ya shiga ta karantomai password dandanan ya hau komai d'inta ya dawo hamdala tayi ta ce " Alhmdllh kaga ban rasa komai nau ba hatta hotuna na sundawo "Murmushi yayi mata ya ce " Ai daman bazasu bace ba sannan na bada a gyaro maki wayarki gobe za a gyara "girgiza kai tayi ta ce " a a bama sai angyara ba Tunda komai ya dawo"watau kinyi sabuwar taya kenan shysa zakice kar agyaru"Y'ar Dariya tayi batace kome ba "kwantota yayi jikinshi tare da cire Dan kwalin dake kanta bakin gashinta mai matsakaicin tsawo da yasha gyara ya bayyana ga k'amshin mai dake tashi a hankali ya fara wasa da gashin itadai Zarah shiru tayi bata iya hanashi ba daga nan ya fara mata wasu irin abubuwan da ya saba ganin zai zarce ne kuma zai tada mata feeling ya sanyata marairaicewa ta ce " ka bari Dan Allah perioud nake"Sassautawa yayi Dan har a ranshi yaso yau ya Dana ya ce "Yaushe kika fara" d'azu ta fad'a cike da jin kunya"Kwana nawa kike gamawa"4 zuwa 5" ta fad'a cike da kosawa da tambayar a hankali Zarah ta zame jikinta daga nashi tare da mik'ewa ta ce "Good night" Okay Have a nice dream"ya fad'a yana lumshe ido tana zuwa wayarta ta jona charge ta kwanta tana lumshe ido harga Allah taji dad'in wayar daya bata sosai a ranta ta ce "Allahsrk rayuwa wai Zarah nice zan rik'e wannan wayar mai tsada" saikuma tabar wannan tunanin ta koma tunanin irin wahalar da take sha lokacin period a baya amma yanxu wai itace yanzu hankali kwance take perioud harta gama bako wani ciwon ciki...satin md guda a Zaria sosai yaji dadin zaman nan saboda ko ba komai yana hutawa sannan ya kashe wayoyinshi bare ko harkar business a dameshi Amera ma ba samunshi take ba dukda yace mata daman zai kashe wayoyinsa hakan yasa bai damu da halin da zata shiga ba saboda ya sanar mata zaman nashi anan sosai ya samu Hutu biyu gana moruwa da yake da Zarah gana hutawa ba Aikin da yake sosai yayi kyau cikin shigar da ya saba watau ta K'ananan kaya banda k'amshi ba abunda ke tashi daga gareshi cikin murna Zarah ta fito daga bedroom d'in sanye cikin lafcececiyar Hijab d'inta har k'asa wayarta ce kawai a hannunta Tare suka shiga baya Inda driver yashiga gaba ya jasu Har suka isa A B U bamai magana Zarah sai doki take Suna isa har ciki suka kaita inta da zata fita Ya damk'a mata Rafar y'an dubu dubu a hannu yi tayi kamar zata amsa sai tayi Sauri ta fita tana Dariya ta ce "Sai anjima " Girgiza kai MD yayi tare da mayar da kud'in ma ajinsu kai tsaye KD driver ya wuce dashi koda yaje bai samu Amera gida ba Bayan ya bud'e wayarsa ya kirata yake shaida mata ya dawo cikin murna ta ce "Gani nan honey daman gida naje kafin ka dawo" Gidan Ammy yaje suka gaisa kafin da magriba ya koma gidanshi yana zuwa ya samu Amera da gudu Tayi hug dinsa tana murnar ganinsa Saidaifa duk murnar a baki ne Dan ko ruwan Tarbar miji yayi tafiya bata kawo masa Inda sabo MD ya saba Dan in zaiyi tafiyar wata nawa indai zai dawo ko ruwa bata tarar shi dashi bare akai ga abinci da ko dahuwar indomie bata iya ba Saidai idan yace ta d'auko masa ruwa take d'auko masa...Sosai Zarah suka maida hankalinsu ga jarabawar da suke Kasancewar sun fara exams hankalinta gaba d'aya ta maidashi ga karatu a haka har suka gama Exams dinsu ta first semester Level 4 Inda zasuyi hutun wata biyu da sun dawo wata hud'u ya rage musu suyi final Exams koda suka isa gida gidan su Asmy ta fara sauka Bayan sun gaisa tadan huta ta wuce nasu gidan Dan daman tasan Baba na wajen aikinshi hakan yasa ta fara zuwa gidan su Asmy tana shiga da Sallama a bakinta ta shiga Mama Rabi da ke kan Kujera tana jin radio ta mik'e ta ce "Iyye Andawo daga yawon katuwancin kenan Ai muna nan dai muna jiran uhum Dan wlh rana d'aya ta barawo rana d'aya tame kaya Waye bai sani iskancin da kuke a jami'ar ba za Adawo ana mana wani bagu waike ishashiya mai Ilimi kin shiga jami'a ko to dad'in abun ansan komai dai ehe karshen dai alawa kasa karshen iskanci dai a d'auko cutar Sida ko kuma cikin shege Dan allurorinma da kuke idan Allah ya tashi tona muku asiri ba aiki suke ba......✍🏿 *07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo Ce*_🤙🏿 🅿️......*53 & 54* Dukda Zarah ta saba da maganganun Mama Rabi amma wannan Karin kam sunyi mata ciwo sosai Saida ta Goge hawaye Tabbas Rashin uwa Babban gibi ne a rayuwa ta tabbata da mahaifiyarta na raye da murna da farinciki da tarairaya zata tarbeta cike da kewarta da tayi tsawon kwanaki amma yanzu ta dawo Kalmar da za a fara tarbarta da ita ta muzanci Bayan ta Goge hawayen da suka zubo mata cikin k'arfin hali ta ce "Ina yini Mama" Dogon tsaki Mama Rabi taja ta ce "Yinin yana gidan su tsintacciyar uwarki da ba asan asalinta Dan Ubanki nace ina buk'atar gaisuwarkine Munafuka " Duk yanda Zarah taso daurewa kasawa tayi batasan lokacin data fashe da wani irin kuka ba Ta Ruga d'akinta kan katifarta tayi rubda ciki tana Kara fashewa da kuka wannan wace irin jarabace ta Mama Rabi mahaifiyarta da take ma kabari bata barta ba duk irin abunda zata mata baya mata ciwo kamar yanda take sanyo mahaifiyarta ji take yanzu kuma bazata iya jurar zagin da Mama Rabi ke yiwa mahaifiyarta ba dake k'asa kwance sosai take kuka kamar ranta zai fita tana Jin rad'ad'in zafin maraicin da ta tashi dashi na Rashin Mahaifiya ta jima tana kuka kafin bacci ya d'auketa Mama Rabi ko tsaki taja bak'inciki duk ya isheta ga na yaranta gardama_gardama sun giga a gida sunzama sanatoci Ba Aure duk Wanda yazo da anyi tare ya tafi gashi ko takardar sec basu da ita amma yarinyar da taso ta tagayyara ita ce Take neman shige mata gaba bayan ta sauke qur'ani yanzu kuma Hartana shirin gama jami,'a sannan ga Aurenta a sanye "girgiza kafa kawai take ta rasa yanda zatayi kafin ta mik'e ta sanya hijab d'inta tana huci ta ce " wlh bazaiyuba ashe ma na zama banza dole ne a fasa auran nan kuma dole.ne tayi abun kunyar da mashinshini ma nan gaba bazata samu ba dole ne tayi abun kunyar da duniya zata gani ta tsine mata mahaifin nata ma da take tutiyar yana kaunarta saikin zama abun kyama a garesa dani take zancen karamar kwaruwa "ta fad'a tare da fita daga gidan kamar zata tashi sama...Zarah cikin bacci taji dawowar Baba Firgit ta mik'e tare da fitowa tsakar gida cikin farinciki Baba ya tarbi Zarah ya na cewa " Oyoyo Zarah ta Sannu da zuwa andawo lafiya ya gajiya"Alhmdllh Baba na nayi kewarka sosai "murmushi yayi na so da k'aunar y'ar tashi ya ce " Nima nayi kewarki y'ar Amanar Baba yanzu dai bari na zauna na sha labarin makaranta "Dariya tayi ta ce " Aiko Baba zaka shashi"Bayan ya Aje ledar hannunshi a kujera ya zauna itakuma ta zauna tabarma nan suka shiga labari shida y'ar tashi sosai Zarah ta mance da bakincikin da Mama Rabi ta kumsa mata Tabbas da babu Baba da batasan halin da zata shiga ba Amma ko tana cikin bak'inciki idan ta tuna da mahaifinta mai kaunarta sai taji Kashi sittin na damuwarta ya ragu Cikin hirar ne yake tambayarta ya ce "Ina maman taku Naji banji taba tunda na shigo" bansaniba Baba kila ta fita Baba ina khairat bangantaba "Khairat tana makarantar kwana Ajiwa na Turata Dan nafison ta samu ingantaccen Ilimi a Chan boarding akan a nan dan kartayi shiririta " sosai Zarah taji dad'in tura khairat boarding school da Baba yayi Mama Rabi ita ce bata dawo ba sai Bayan isha i koda Malam ya tambayeta ina taje bata fad'a masa ba cewa tayi "makociyarmu ce ta tsohon gidansu Habiba ce ta rasu natafi Sutura ni kuma kaga Ba waya gareniba bare na kiraka ba " Batare da Baba ya kawo komai ba ya ce "Subhanallahi Allah ya jikanta ina su habibar ne naga suma basanan " Tana shiga daki ta ce "Eh basu dawo ba " girgiza kai yayi Dan shi kanshi yawon na su habiba na damunshi Wanda har mutane na cewa Dan ba Y'ayanshi bane yasa yake barinsu sakaka nanko Dan basusan anfi k'arfin shi bane indai ba zaunawa zaiyi gida yayi gadin su ba a gida baya mancewa ranar da ya dinga musu fad'a akan bleaching karshe Rashin kunya Habiba taso tamai duk girmanshi bata gani ba hakan shiyasa ya tsame yaranshi a hankali daga cikinsu kar tarbiyarsu ta gurbata ya mayar da khairat boarding ita kuma Safiya ya barta a Batsari washe gari Zarah tayi aikin gidan kamar ko yaushe idan ta dawo wajen 11 ta gama komai ta koma daki tana Dan dudduba wayarta da bata bari kowa ya Gani ba Asmy ta shigo d'akin Bayan ta zauna bakin katifar Kallonta Zarah tayi ta ce "Yanzu nake tunaninki a raina" nima wlh Naji shiru baki leko ba shiyasa na shigo "suntaba Hira sosai Cikin hirar ne Asmy ta ce " wai Zarah kina shan maganin nan kuwa"wani.magani"Zarah ta tambayeta "Wanda Dr Halima ta fad'a kenan" Ohhhh eh ina sha me kika gani"Bakomai daman Dan nayi maki tuni ne karki manta"murmushi Zarah tayi ta ce "Ai kozan manta da komai bazan manta da maganin nan ba kullum saina sha sa koda kuwa ina gida ne saboda tace ba a tsallaken sha sannan Kinga danaje saya na sayo na Wata biyu Wanda har hutunmu ya k'are ina sha " Ajiyar zuciya Asmy ta sauke ta ce "Alhamdulilla yanzu saura wata nawa wata taran ya cika wai lissaafina ya shige " Turo baki Zarah tayi ta ce "Keda kuka had'a aike zan tambaya" Dariya Asmy tayi ta ce"a a a kedai da kika d'ana Auran kika zama y'ar hannu ai ke zan tambaya"Harara Zarah ta galla mata ta ce "zanyi maganinki " Dariya Asmy tayi wayar Zarah ce tayi ringing tana ganin Chuchu ce mai. Kiran tayi saurin d'auka daga bangaren Chuchu cikin iyayinta ta ce "I really miss uh momcy shine daga jiya zuwa yau harkin manta dani nikam kina raina Kinga ina tashi daga bacci kena fara kira" da murmushi a fuskar Zarah ta ce "Nima kina raina daughter daman yanzu nake niyyar Kiranki kunkoma lafiya ya Ammy na fatan tana lafiya" Ammynki lafiyarta qalau tana gaisheki in banda bama kusa ai da na kai mata Dan jiyama har dare.muna ta hirarki"Sun tab'a Hira sosai da Chuchu kafin Asmy ta amshi wayar itama suka gaisa da Chuchu Bayan sun katse wayar Asmy ta na juya wayar Zarah ta ce "Wlh wayar nan tsada gareta Zarah karki yarda wani gidan nan ya gani idan suka gani zasu iya sace miki wlh ko kuma su miki munafurci wajen Baba ki boyeta sosai" hakane Asmy kinsan yanda za ayi sim Dina zan cire kawai na baki wayar ki boyomun ita gidanku "To ke ki rik'e wacce " akwai kudi a hannuna zan saya keypad Dan nima ina tsoron rik'e wayar nan a gidan nan "Hakane kuma wannanma shawarace Asmy tafada kafin ta ce " Allah dai ya sakawa mutumin nan wlh ga Alamun yana da kirki tunda har ya iya baki waya mai tsada haka "uhm kawai Zarah ta ce Asmy tab'a 3k ta ce idan ta samu Mai shiga kasuwa ya sayo mata key pad sannan ta bata tata ta tafi da ita ta ce idan tanason amfani da ita taje gidansu tayi haka ko akayi da magriba Asmy ta Aiko almajirinsu ya kawowa Zarah wayar Inda ta d'ora sim dinta a ciki kamar jira ake ta d'ora saiga kira ya shigo saida ta kusa katsewa kafin ta d'auka cikin k'asa da murya ta ce " ina yini ya Hafiz "Lafiya qalau my bride kin jini shiru kwana biyu wlh exams ce ta boyeni kinsan nan da wata Ukku na gama sch d'innan" bata San ya akayi ba Zarah taji gabanta ya fad'i cikin k'arfin hali ta ce "Amma karatun naku yayi saurifa yaya hafiz" Oh hakama zakice ai nazata cewa ma zakiyi ranakun basa gudu Naji bama kiyi d'okin da na fad'a maki na kusa dawowa ba ko my Zarah"ba haka bane ya Hafiz Ina farinciki mana ai nafi kowa farincikin son ganinka "sun tab'a Hira sosai kafin Su katse abokinta Yusuf ta kira Inda Shima.suka sha Hira kafin ta katse koda ta kwanta batasan ya akayi ba kawai taji ya Musty ya fad'o mata a rai a hankali ta ce " Ko yana ina "tsawon 3wks kenan rabonta dashi lokaci guda ta saki murmushin da batasan dalilin yinshi ba lumshe ido tayi kafin ta bud'e irin rayuwar da sukayi a gidan ta shiga dawo mata kafin bacci barawo yayi awon gaba da ita batare da ta shirya ba... " wai honey laifin me nayi maka ne yanzu duk ka daina kulani kuma yaushe rabon ma da ka nemu hakkinka waje na "ta fad'a kamar zatayi kuka " kwantota yayi jikinshi a hankali Dan yasanta da Sanya damuwa a rai ya ce "Nothing My Merah me kika gani" tana shigewa jikinshi ta ce "Ai naga yanzu baka kula dani sosai Kamar da sannan da ko na hanaka fushinka baya zuwa ko ina amma yanzu kafi wata nawa baka kusanceni ba Bayan da ko sati biyu baka jure hakan muddin muna tare" murmushin da ka gani zaka ma'anarshi yayi mata ya ce "Merah kenan na barki ki huta kawai" Kamar zatayi kuka ta ce " nasan har yanzu fushi kake dani Dan Allah honey kayi hakuri nima saidaga baya nayi regret din abunda nayi nasan ban kyauta ba please forgive me my love"ya wuce wannan na fad'a maki bakomai fa kinsan bansan ayita magana d'aya is okay please "Okay Thnks hakkina fa" a ranshi ya ce "Yau rigima kikeji Amera saina hakura da abu ki takalo Alhalin ba iya jurewa zakiyi ba " a fili kuwa cewa yayi "a gajiye nake bacci nakesonyi" Kuka ta fashe dashi na kissa ta ce "Allah ni ban yarda ba Ai nima ina da hakki a kanka Indai bakayi ba bazai tabbatarmun da ka huce ba " Dafe kanshi yayi da hannu kafin ya d'ago ya ce "Idan kikamun abunda bai kamata?ka dau mataki wlh na yarda" tayi saurin fad'a Daren ranar Amera ta yabawa aya zakinta Dan duk kwanakin da ya kwashe da kewar abun akanta ya juye dukda bai samu yanda yake so ba kamar yanda yake samu a wajen Zarah amma wannan Karin ba laifi Amera ta daure tayi jarumta ba raki ba komai har saida ya gaji Dan kanshi ya kyaleta shi kanshi yasan yau kam tayi juriya Bayan ya fito daga toilet sanye da towel kalllonta yayi da take maida numfashi ya ce "Sorry dear je kiyi wankan ko nayi miki" Girgiza kai tayi ta ce "zanyi da kaina honey Dan tasan halinshi sarai daga wankanma sai yace ayi second round sai maida numfashi Amera take a haka harta shiga toilet daman tasan za a Rina badan komai ba ma ta nemu hakan ba saidan ta tabbatar da ya huce Dan ba abunda ta tsana sama da fushin mijin nata abar kaunarta MD ko bayan fitarta lotion ya hau shafawa yana shafawa yayi murmushi ya ce " ko ya akayi ita Yarinyar take da jarumta dukda kasancewar ta yarinya k'arama takan iya daukar lalurata amma Amera da ta tafi shekara 30 har yanzu ta kasa daukata "Yana wannan tunanin har Amera ta fito ta bayanshi ta rungomshi ta ce " tunanin me kake honey "Murmushi ya sakar mata tare da lakutar kumatunta ya ce " tunaninki nake "Cikin farinciki Amera ta bashi peck a kumatu ta ce " Kamar ni a duk Inda nake da halin da nake tunaninka baya tab'a barin kwalwata mijin da yafi na kowa"... Zarah kam wannan hutun bataji dad'in shiba Dan kwata_kwata hankalinta baya waje guda ga aibu da bakaken maganganun da Mama Rabi take binta dashi kullum Saidai ta yini a d'aki Dan gidan su Asmy ma ba barinta take zuwa ba haka dai ta hakura take cigaba da yiwa Mama Rabi biyayya dukda wata zuciyar takan zugata akan tayi mata Rashin kunya musamman idan tana hada zaginta da mahaifiyarta sai wata zuciyarta ta ce "Kiyi hakuri kici gaba da yi mata biyayya wata rana sai labari da ma tayi miki Wanda yafi haka kin jure bare yanzu da bazaku maimaita shekarun da kukayi a baya ba" A daddafe dai har suka ci hutun wata guda Zarah har k'agara tayi su koma sch danma dadinta d'aya Baba cikin satin ne taje Batsari dangin mahaifinta tayi musu sati sosai sukaji dad'in zuwanta Dan daman duk a gidan suna k'aunar Zarah saboda nutsuwarta ranar da ta dawo gida ya rage saura 3weeks su koma sch sai doki take Inda Asmy ta ciro 100k a cikin kudin sadakin Zarah Wanda tare sukayi shawarar taje ta dinga Musu sayayyar provision da kayan sawa koda mamansu Asmy ta tambayesu kudin meye cewa tayi kudin schooler ne da aka basu Da daddare misalin Goma na Dare kwance take ta lulluba da blancket kasancewar sanyin da ake sosai ta kudunduna a bargo tana jin sanyi na ratsa kowani sassa na jikinta batasan ya akayi ba ya Musty yake fado mata a rai lumshe ido tayi kafin ta bud'e a hankali taji feeling na k'ok'arin taso mata rumtse ido tayi da karfi kafin ta bud'e ta ce Ya Allah "Kara lumshe ido tayi kamar mai bacci kafin ta saki murmushi a hankali kamar murya mai rad'a ta ce " Ka iya sarrafa Mace Allah sa ya hafiz shima ya kasance haka"sai kuma ta rufe baki ta ce "Subhanallahi me nake shirin Cewa" a haka dai tana sak'e sake har bacci barawo ya kwashesa. Cikin kwanakin nan ya rasa me yasanya yake yawan tunanin yarinyar musamman lokacin da yazo kwanciya bacci yauma kwance yake wajen 11 bacci yakeso yayi amma ya kasa Tunanin irin mood din da suke shiga lokacin da suke tare ya dingayi lumshe ido yayi kamar mai bacci a hankali ya furta "Sugar babe You are so sweet like Zuma koma abunda ya fita "sai kuma ya k'ara sakin murmushi yana tuno irin dramar da suke sha a gida a hankali ya ce " Yarinyartarta na burgeni"Saikuma Chan yaja tsaki ya ce "me yake damu na ne na zauna ina tunanin y'ar Ciki na mtwssss" (Nikam nace kajika MD kasan da y'ar cikin naka ce har kake eyane da ita😉)Kallon amera yayi dake sharar bacci a gefenshi peck ya bata a kumatu ya ce "I love you my one nd only wife " ya fad'a kamar rada kafin ya janyota jikinshi a hankali Dan karta tashi............✍🏿 07026166536 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss hajo ce*🤙🏿 👨‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👨‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* *BONUS PAGE*💃🏿😂 🅿️........*55 & 56* Washegari MD yana zaune yana hutawa a palour Amera na gefenshi suna zuba love Wayarshi tayi ringing dubawa yayi yaga Baba audu ne mai kula da tsohon nan na gombe cikin Sauri ya d'auka banji komai akace daga bangarenba saigani nayi ya Mike a matuk'ar firgice ya ce "Alhamdulilla Alhmdullillah Allah mungode maka gani nan zuwa yanzu " yana gama fad'ar haka ya katse kiran daka Kallesa kasan yana cikin farinciki Kallonshi Amera tayi ta ce "Honey ya naga ana kiranka duk kabi ka wani rude " Murmushi ya sakar mata ya ce "wani abun farinciki ne ya sameni " Da Fara a fuskarta ta ce"daga ina "Murmushi kawai ya sakar mata yace " zakiji idan na dawo "yana gama fad'ar haka ya fita da Kallo ta bishi kafin ta tab'e baki MD na fita jaber ya kira Inda Yayi mishi albishir kamar yanda Baba audu yayi masa a Airport suka had'u Ba bata lokaci jirginsu ya d'aga gombe kamar ko yaushe gidan suka isa sosai MD yayi farincikin samun lafiyar Baba a palour suka sameshi shida Baba audu da Matar shi tunda ya shigo Baba tsoho ya kafeshi da idanu sai Murmushi yake sakar masa Shima MD murmushin ya sakar masa Bayan sun zauna cike da girmamawa yace " ina yinin ku Baba"Lafiya qalau Yaron kirki anzo lafiya"Alhmdllh ya jikin Baba "ya fad'a yana kallon shi " Da murmushi a fuskarsa ya ce "Alhamdulilla yaron arziki hakika bani da bakin da zan gode muku a bisa ceton rayuwata da kukayi kunyimun abunda babu abunda zan iya cewa daku saidai fatan samun aljanna kuka ne yaci karfinsa cikin Sauri MD ya tashi ya koma kusa dashi tare da dafoshi ya ce " Dan Allah Baba kayi hakuri yau ranar da ya kamata kayi farinciki ne fiye da kowace rana tsawon shekaru Ashirin da wani abu kana kwance yau Allah ya tasheka ai farinciki ya kamata kayi Baba karka damu da abunda nayi maka ka daukeni tamkar jikanka Dan Allah kayi shiru bazanji dad'in ganinka kana kuka ba "Goge hawayen shi yayi ya ce " dole nayi kuka yaron nan tsawon shekara ashirin da wani Abu ina kwance kai kake kula dani sha na magani na da komai ai dole nayi kukan farinciki kafin ya damki hannunshi ya ce "Allah yayi maka albarka yaron nan yasa ka gama da duniya lafiya ya kareka daga sharrin makiya da mahassada ,Allah kareka daga sharrin makiya na jikinka da Wanda bana jikinka ba ,Allah raba ka da sharrin mahassada ,Allah ya biyaka da gidan Allah Nama rasa wace irin addua zanyi maka kayimun abunda Bazan tab'a mantawaba dashi ba a rayuwa kayimun abunda babu Wanda ya tab'amun a rayuwa Allah sa ka gama da duniya lafiya" Ameen kowa ya amsa nan yayita Jerawa MD adduo'i Bayan komai ya lafa an gaggaisa Jaber ya kalli tsohon ya ce "Baba ka tuna shekara ashirin da biyu da suka wuce abunda ya faru mun tsineka ne yashe a gefen titin a hanyar jigawa dajin Allah mukuma a lokacin ni da Amini na ya fad'a yana nuna MD da yayi k'asa da kansa ya ce mundawo daga garin kenan Wani bikin dangin mahaifi na da Abokina yayimun rakiya kasancewar tare muka taso tun yarinta a lokacin bamu da wasu shekarun kirki lokacin da muka tsinceka da farko mun tsorata Da ganinka Dan dajin nan babu alamar mutum a ciki Sai kukan tsintsayi da namun daji dak'yal dai mukayi shahada muka tsinceka kai tsaye wani local government da muke kusa da garin muka nufa dakai mai suna kazaure Inda muka kaika Asibiti da farko d'aukar mu baka da rai saida likitoci suka fara aiki akanka kafin Su fara ceto rayuwarka Satinmu guda a asibitin kazaure ganin ba wani cigaba sosai ya sanya muka wuce Asibitin kano dakai kasancewar munsanar da iyayenmu kuma suka kara mana karfin gwuiwa akan taimakon da mukayi yasa bamu samu wata matsala ba dukda kasancewar mu ba wasu manya ba watanka guda bakasan Inda kanka yake ba saboda saida akayi maka aikin Harbin da aka maka kafin Allah ya taimaka ka farfado koda ka farfado Kalmar farko daka furta shine a " Karku kasheni me nayi maka kake son hallaka rayuwata da ta iyalina"Dak'yal muka samu kabar sabbatun dak'yal ka yarda damu a lokacin Dan mun fad'a maka taimakonka zamuyi ka tambayemu a ina kake "Muka fad'a maka kano" Cikin tsananin rud'u ka ce "Ku fiddani daga garin nan indai taimakona kukeso Kuyi zai iya zowa har nan dinma ya kashe ni ina ina " Mamy Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Allah kasa bai kashe mun Mamy ba "Abunda kake maimaitawa kenan duk ka firgice akan Sai an fitar dakai daga kano saboda zasu iya biyoka nan yayi kusa da garinku " Ganin hakan duk hankalinmu ya tashi kuma muka lura kamar akwai wadanda ke harin rayuwarka rasa Inda zamu kaika mukayi gashi dukka firgice gombe shine garin da ya fadowa MD a rai a haka muka nufo gombe dakai Inda ya saya wannan gidan sannan ya samu wasu miskinai dashi da matarsa suna buk'atar wajen zama ya d'aukesu akan zasu kula dakai saboda tun sanda muka shigo garin kayi loosing memory a fahimtar mu ka manta komai sannan kuma ka daina magana wadannan mutanen su Suka dinga kula dakai da taimakon MD da adduo sa sadakokin da saukar qurr ani da aka dage Dan saidaga baya muka lura abun kamar akwai sihiri "Tofa kaji Baba a yanda muka sameka fatan kaima zakayi mana bayanin musan asalin waye kai" Tunda aka fara maganar yake Hawaye Kallonshi kawai su MD suke saida yakai karshe kafin ya d'ago ya ce"Na tuna lokacin nan yaron nan Wanda daga lokacin ban Kara sanin Inda kaina yake ba sai shekarun baya hud'u zuwa biyar Saidai bana iya komai sannan Ko nayi kokarin magana bana iyawa Bazan iya fada maku Tarihin rayuwata ba saboda tuno abun tamkar fama tsohon raunin da ke cikin zuciya ta Wanda bazai tab'a gogewa ba har abada Zadai ku iya sanin suna na "Abdussalam"Kuma haifaffan garin jigawa Wanda a halin yanzu babu garin da na tsana bana fatan ko wuce hanyarshi sama da garin nagode da taimakon da kukamun Saidai bazan iya fada muku takaicin labari na ba " Duk numfashi sukaja Inda MD ya ce "Karka damu Baba basaimunji komai ba yanzu ina kake son zama mu koma garinmu tare da Kai watau kaduna" girgiza masa kai yayi ya ce "A a yaro ka barni a nan hankali na yafi kwanciya a nan din " Ajiyar zuciya MD ya sauke yace shikenan Baba ba matsala saika zauna tare da su Baba audu koko a saya maka sabon gida idan kafison zaman kai d'aya "hawaye a fuskar sa ya ce " A a a nan dinma yayi indai ba takura su ba"Cikin Sauri Baba audu yace"ai muma bazamuso ka tafi ka barmu ba munriga ansaba "matarsama dattijuwa tace " Gaskiya kam an saba "MD bai bar garin ba saida ya bar musu mak'udan kudin da zasu buk'ata nan gaba sannan ya sanya aka sayowa Baba waya da sim Dan sun dinga gaisawa a hanya sai Farinciki yake yana mamakin wani irin Abu ne akayiwa tsohon nan da har yake gudun garinsu na haihuwa shi kanshi saboda tsaron tsohon ya sanya yake tahowa a sirrance koda suka isa kd har dare ya fara gidansu ya fara zuwa yayima Ammy albishir da samun lafiyar Baba Inda ya bata labarin abunda ya basu a takaice sosai Ammy tayi farinciki kuma tayi adduar Allah ya k'ara masa lafiya ta ce Insha Allahu Zata samu lokaci taje ta ga jikin nasa daga gidan ammy gidansa ya wuce lokacin Amera hartayi bacci saida ya shiga d'akin ta gane yadawo cikin hammar bacci ta mik'e ta ce " yaushe ka dawo honey"yanzu harkinyi bacci kenan"wlhko na gaji da jiranka na kwanta wai ina kaje haka "Wani waje ina tsohon nan da nake baki labarin mun tsinceshi da dad'ewa tun kafinma muyi Aure " Eh nagane"Shine ya warke ya samu lafiya"Tab'e baki Amera tayi ta ce "Kaidai honey baka gajiya da kwashekwashe wlh a tunanina tuni ka wurgar da talakan tsohon nan saikaje ka kwaso mana alkakai daga tsintar mutum a titi kawai ka daukeshi ka dinga hidima dashi Haba wannan Abu Dame yayi kama sai wahalshe da kanka da kayi ba dangin iya bana baba Nifa banason harka da talakkawa wlh Haba su goga maka karnin talauci " ta fad'a tana yamutsa fuska"girgiza kai kawai MD yayi Dan baiyi mamakin abunda ya fito daga bakin Amera ba Tun fil azal ita daman ta tsani talakka Wanda hakan d'abi'ar da ta taso da ita daga gidansu ne duk yanda yaso ya sauya ta amma hakan ya gagara "Baice mata uffan ba sai rage kayan jikinshi da yayi yanajinta tana gunguni a haka har yaji ta koma bacci girgiza kai kawai yayi yana mamakin yanda Amera ta tsani talaka take wulakanta mutane da batasan darajarsu ba " Bayan ya watsa ruwa gefenta ya kwanta baccin gajiya ya daukesa..washegari around 11 dare MD na kwance Amera na gefenshi tana chat da kawayenta Sai dariya take shiko ya lumshe ido babu wacce ke fad'o masa a rai sai Zarah a Gaskiya yana da buk'atar ta koba komai tana bashi abunda baya tab'a samunshi a wajen Amera koda kuwa zai shekara suna Abu d'aya "Lumshe ido yayi ya bud'e sai yaji Yana son jin muryarta tsaki yaja a ranshi , "Tunani yayi yanzu ai ko yaje zaria suna Hutu tunda ba sanin garin da take yayi ba Yasan dai tunda take zaman hostel to ba yar garin bace Kallon Amera yayi dake gefenshi tana chat ya ce " My Merah chat d'in ya isa kizo mu kwanta"Sorry honey ka kwanta wani labari ne luzy take bani ba yanzu zan kwanta ba "Shiru yayi bai kuma ce mata komai ba " Duk yanda yaso bacci ya d'auke sa kasa daukarsa yayi saboda a matuk'ar bukace yake sai wajen 12:00 yaji kwanciyar Amera janyota yayi jikinshi koya rage zafi Amera najin haka ta ce "Haba honey Dan Allah ka barni na gaji Wlh bacci nakeji" Kyaleta MD yayi badan komai ba saidan bayason takurata a ranshi yana mamakin saita dinga cewa ta gaji saikace wace ke wani aikin wahala na farko dai ita ba ma'aikaciya ba,ba y'ar kasuwa ba,ba wani aikin gida take ba macen da ko shara bazata ce ta tabayi ba ,Amma duk dare saita gama chat d'inta da kawaye tace ta gaji"Da wannan tunanin dak'yal ya samu bacci ya kwashesa washegari da misalin 4pm yana zaune a kujerar palourn su suna Hira da Ammy Chuchu ta shigo gidan "da fara'arta ta ce " Lah yaya Kaine two days bana ganinka karkaga yanda nayi missing dinka "murmushi ya sakar mata ya ce " Daga ina Haka Auta na ganki da jaka"gefenshi ta zauna ta ce "Daga gidan Aunty Zey nake kwana na biyu a Chan " Kice ziyara aka kai mata "Murmushi tayi ta ce" Eh Yaya "Ammy ce ta ce " Tofa keda kikace zakiyi sati me ya maidoki"Dariya tayi ta ce "kewarki ta dawo dani ammy Gani nayi bazan iya ba ina gari bana ganinki sainayi ta tunanin kewa zatayi miki yawa gasu y'an rainin wayan yaran nan na Aunty Zey nayi da su taho mu taho suyi maki kwana biyu sukaki wai Saidai in gidan Uncle zankaisu shiyasa na tahowata watau ni sun rainani"ta fad'a tana turo baki" murmushi Ammy tayi ta ce "Ai yaran nan sarkafar iyaye garesu shiyasa nama hakura da a kawomun su Dan ba zama ba zasuyi sun fiso su jisu kusa da iyayensu sai suje Chan su karata Tunda ga Auta ai nasan ke kin bani Yaranki ko" Dariya Chuchu tayi tare da rufe fuska ta ce "Kai Ammy Saidai yaran Yaya dai" Ohhh bazakiban ba kenan kun nunamun Yayan shine kawai nawa ko to shikenan Shima Allah ya kawo nasan kuga yanda nima zan gwada muku banbanci Dan Ko halawa na sayawa yaranshi bazan bawa naku Ba "Dariya Chuchu tayi ta ce " Kai Ammy Bafa haka nace ba "MD najin hirarsu bai tanka ba saida Ammy takawo zancen yaransa Yaji zuciyarsa wani iri a ranshi ya ce " Allah yasa nima ina da rabon ganin nawa yaran"ganin hirar zata sanya MD tunani ya sanya su sakin hirar suka kama wata MD ne ya kalli Chuchu ya ce "Tunda kika dawo Hutu bakije gida na ba why" Sorry yaya Aunty Amera na gidan shiyasa bana son zuwa "Bata fuska yayi ya ce " Ita ga dodonki ko?girgiza kai tayi ta ce "Yi hakuri Yaya ba haka bane" Saura kwana nawa hutun naku ya k'are "3weeks" Okay shirya mu tafi ki k'arasa hutun a gida na "Kamar zatayi kuka ta ce " Yaya Za abar Ammy ita kadai fa "Sanin Halin Chuchu sarai ba jituwa Suke da Amera ba ya sanya ta cewa" Kayi hakuri Babban yaya tayi maka kwana biyu nima banajin dad'in gidan ni kad'ai sai masu aiki "To shikenan Ammy" ya fad'a Ajiyar zuciya Chuchu ta sauke Kala biyu Chuchu ta d'auko suka tafi gidan MD dukda ranta bayaso a palour suka tarar da Amira ta harde kafa daya kan d'aya tana latsa waya y'ar aiki durkushe gabanta tana mata tausa a kafa "Tsaki Chuchu taja a ranta ta ce " kamar wata yar shugaban kasa mtwsss fuska murtuke ta zauna palour Bayan MD ya zauna Dagowa tayi tare da Fara Murmushi ta ce "Honey yaushe ka dawo" Yanzu "ya bata amsa yana lumshe ido " Tsawa ta dakawa me aikin ta ce "Bazaki tashi ki tafi ba kina ganin mijina ya dawo Dan kutumar ubanki zaki zauna a nan ban muku dokar cewar ko a bisa sabani idonku ya had'u da na mijina a bakin aikinka ba to kema yau aikinki ya k'are Dan haka kije na koreki daga yau na kuma ganinki a hanyar layin nan ma sai nasa an kama Duka ilahirin danginki " Cikin kid'imewa y'ar aikin ta fara kuka tana magiya ta ce "Dan girman Allah Hajiya kiyi hakuri wannan Aikin shine madogarata idan na rasashi bansan ya zanyi ba kiyi hakuri ki yafemun ina tsoron tashi ne karkice kuma nayi laifi shiyasa kimun rai Hajiya" D'auketa da wani irin Mari Amera tayi Wanda Marin saida ya tsoratar da Chuchu ta ce "Ni zan fad'a magana ki musa mun Dan Ubanki y'ar matsiyata dake zanyi musayar baki tana shirin Kara d'auketa da wani marin Chuchu tayi Sauri ta shige gabanta " Wani banzan kallo ta watsawa Chuchu ta ce "Ke kuma ina ruwanki matsa kiban waje" bazan matsa ba idan ke bakisan darajar d'an Adam ba ni na sani me yarinya tayi miki Dan zalinci zakiyi mata irin wannan Marin Dan kina tutiya da arziki kifa sani arzikin nan da kike tak'ama dashi Allah ne yake rabawa ga duk Wanda yaso suma talakkawan basu sukayi kansu ba Allah ne yayosu haka haka masu arzikinma Duka yin Allah ne akanme zaki dinga wulakantar da na kasa dake dandai kawai suna karkashinki"wani banzan kallo Amera ta watsa mata kafin ta ce "Allahu Akhbar ke kuma yaushe kika fara wa azi bamu da masaniya" banza Chuchu tayi mata tare da kama hannun yar aikin sukayi waje kudinta 20k dake hand bag d'inta ta bata tare da bata hakuri "kafin ta dawo Inda ta samu MD haka ta barsa kamar komai bai faru ba a ranta ta ce Wlh hada laifin yaya da ya bari Matar nan take iskanci yanda taso" Bata kuma waiwayar Amera ba tayi wucewarta D'akin da take sauka tana Jan tsakin Haushi da tsanar halin Amera "MD ko sai Bayan barin Chuchu wajen ya rufe Amera da fad'a akan Abunda take bata kyautawa " Nanfa ta tubure tace wlh kome zaice Saidai yace Amma indai akan wannan ne yanzu ta fara ganin bata bakinshine ma zaiyi rabuwa yayi da ita kwanan Chuchu biyu a gidan Wanda kamar a k'aya tayishi ta koma gida Koda ta koma ta bawa Ammy labarin abunda ya faru girgiza kai tayi ta ce "Rabu da ita duniya ce " MD ko yananan yana lissafin kwanakin da ya ragewa su Chuchu su koma makaranta. Kowa idan zai koma makaranta bak'inciki yake na rabuwa da gida banda Zarah dake d'okin komawarta sch Dan wannan Karin ba k'aramar takura Tasha ba wajen Mama Rabi ba Bugu amma akwai zagi da bakaken maganganu ga aiyuka dukda wannan baya damunta saboda ta saba yaune komawarsu sch Wanda tunda safe ta shirya Bayan Baba ya sallameta da abunda ke aljihunshi dukda dak'yal ta Amsa nan yayi mata nasihohi kamar yanda ya saba yi mata Bayan fitarshi ba jimawa itama ta shirya sosai taji dad'in Rashin ganin Mama Rabi a gidan Dan yanzu ta tarki yawo gidan su Asmy suka wuce Inda daga Chan suka wuce Tasha suka hau motar Zaria minti hamsin me kyau ya kaisu har hostel Bayan sun huta wayarta Zarah ta janyo tare da dannawa Chuchu kira ta ce "Ya dai daughter munfa shigo bamu ganki ba " Daga bangaren Chuchu ta ce "Haba daman nafison saikunzo nazo nima gani nan tahowa gobe daman nagama parking d'in komai na " Okay to muna Kallon Hanya ki gaishe da Ammy"zataji Zan fad'a mata insha Allah "washegari Chuchu ta shirya ta taho makaranta Wanda driver ne ya Kaita MD Bayan ya shigo gidansu ganin baiga Chuchu ba ya sanyashi tambayar Ammy ya ce " Ina Chuchu wai Ammy"Ai ta koma makaranta tun d'azu kenan batayi maka bankwana ba auta kenan Wani abun sai ita nafa zata tayi maka bankwana"Girgiza kai yayi ya ce "may be ta kira waya ta tana kulle" Koda ya koma gida tun a hanya yake jinshi cikin farincikin da ya rasa dalilinshi.........✍🏿 *Masu fitarmun da Littafi ina sane daku kuma ku sani ku da Allah tunda na fad'a basau d'aya ba sau biyu ba akan a daina fitarmun da Littafi duk mai buk'atar son karantawa Yana da damar saya ya karanta cikin nutsuwa da kwanciyar hankali* *ina bawa wadanda sukayi mun magana sukaji shiru hakuri nayi loosing chat Dina gabak'i d'aya babu d'aya Dana d'aga na sakonku please Wanda sukayi mun magana ko suka turo kati sukaji shiru su sakemun magana Please banyi hakan da gangan ba inbanda matsala da na samu ngd masoyan Asali ga masu buk'atar Karin bayani su tuntub'eni akan number wayata kamar haka 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️.........*57 & 58* Kwana biyu da komawar Zarah school MD ya rasa ta hanyar da zaije Zaria ga hankalinshi da ya tashi kiran da Hajiya tayi mishi tace ya saurari zuwanta karya zaci ta manta dukda Amera bata fiya damuwa da halin mijinta ke cikiba amma wannan Karin saida ta tambaya ta ce "Honey lafiya wai?Kallonta yayi ya ce " Me kika gani"Naga kamar akwai abunda ke damunka "Numfashi yaja ya ce " nothing kawai tafiya ce ta kamannine Germany to bana son na tafi na barki ne shiyasa saboda zanyi kewarki"murmushi Amera tayi cike da jin dadi ta ce "Kai honey saikace yau ka fara tafiye tafiye kayi tafiyarka wlh bakomai ni daman America nake son komawa na gaji da zaman Nigeria "da mamaki MD.yake kallonta a tunaninshi zatace Saidai su tafi tare ne ko ta kawo k'abli da ba Adi amma yaga cikin Sauk'i kamar ma.so take ya tafi girgiza kai kawai yayi ya ce " ko irin kewar nan tawa bakyajin zakiyi ko kamar ma.so kike na tafi'"Shigewa tayi jikinshi tace ba haka bane honey Kasan nafi kowa sonka da kaunarka da kuma kishinka kasan babu abunda zai hanani kewarka kawai dai Naji dad'in tafiyar taka ne saboda zaka bar k'asar nan ta sa ido y'an mata su daina kallemunkai shiyasa"Hmm Chan gemany din ba y'an mata kenan "Hade fuska tayi tamau tare da cewa " Aidai nasan yanda baka kula y'an mata anan ba Chan ma bazaka kuka su ba "zancen ki kenan Amera kullum magana d'aya yaci ace tsawon shekara goma kisan waye mijinki kinsan sarai babu macen da ta isa fa rud'e ni ke kad'aice tal daga ke ba k'ari to meye zaki dinga tada jijiyoyin wuya kullum magana d'aya kishiya kinsan da ina yi miki kishiya tsawon shekarun da mukayi dake da nayi ko kuma da kin taba samun labarin ina da y'an mata ko budurwa to why zaki dinga damun kanki " sosai Amera taji dad'in kalaman mijin nata da murmushi a fuskarta ta ce "Nasan da haka mijin da babu kamarsa ina son har kullum ka dinga rik'emun Amanata please MD wlh kasan bana son kishiya ina son kayimun alk'awarin bazaka tab'amun kishiya ba ko da Bayan rai nane please wlh Inajin da kayimun kishiya gwara ace ga ranar mutuwa ta tafiyumun sauki" ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka Rungumeta jikinshi MD yayi dukda ba Yau Amera ta saba irin wannan maganganun ba Amma yau d'innan ta karyar masa da zuciya yasan duk maganar dake fitowa bakinta da gaske take yasan ba karamun so amera take yi mishi ba Lallashinta ya shiga yi sosai Cikin kwantar da murya da kalamai masu dadi harya samu tayi shiru da dare koda yaga tayi bacci tashi yayi zaune ya kasa zaune ya kasa tsaye a ranshi ya ce "why Hajiya zakiyi mana haka me yasa kikeson ki ruguzamun farincikin mata,ina ruwanki da rashin haihuwa ta tunda ke kina da yaran meye ruwanki da nau,me yasa kike kokarin tarwatsa farincikina da na matata iska ya fezar me zafi zirga zirga ta fara a tsakiyar d'akin Tabbas dole ne ya samu mafita cikin Sauk'i ga yarinyar ma da jaber ya bada shawarar mafita da ita ba mafitar saima Kara rikita abubuwa da hakan yayi tsaki yaja a ranshi ya ce Tabbas dole ne yarinyar nan tayi ciki ko tana so ko bata so Dan bazan tab'a jurar ganin Merah cikin wani hali ba kwata kwata kanshi ya kulle Ta ko ina ya hasaso saiyaji ba mafita dole dai yarinyar nan da jaber ya makala masa ita zai samu mafita ta hanyar ta Bai samu bacci ba sai Chan cikin dare Bayan ya gama nafilfilu da adduo'i akan Allah kawo masa mafita a cikin rayuwarsa washegari koda ya tashi asuba har lokacin da ya dawo daga masallaci Amera bacci take a hankali yahau tashinta taki tashi data tashi saita koma cikin y'ar daga murya ya ce " wai bazaki tashi kiyi sallah ba Amera kin sani sarai banason Sallar safen nan da kike "Cikin gigin bacci ta ce " Dan Allah ka rabu dani bana yi "Dukda yayi mamakin yaushe ta fara perioud saiyayi tunanin ko cikin dare yazo mata kyaleta yayi yashiga wanka Bayan ya fito ya shirya cikin shigarsa ta kasaitattun kayan da ya saba sai baza k'amshi yake Yana cikin duba wasu document akan makekekiyar kujerar dake d'akin yaga tashinta kallo d'aya yayi mata yaci gaba da abunda yake yana ganin sanda ta fito Bayan tayi wanka yana kallonta saida ta gama shirinta tsaf hada kwalliya sosai yayi mamakin Ganin ta d'auko hijab da darduma ta kabbara Salla yasan wannan ba shine karo na farko ba da take haka Amma ya rasa dalilin da yasa yanxu yake ganin dabi'un nata a wani kala tunowa yayi da Zarah yarinya k'arama amma bai tab'a ganin lokacin salla ya wuce ta ba shi har mamaki yake Yanda yarinya k'arama take da wannnan ibadar Dan wani time d'in yanajinta raba dare Take tana k'iyamul laili shi kanshi yasan duk kokarin shi na ibada yarinyar ta shanyesa ta damesa yana cikin wannan tunanin kuma sai ya tuno da kiriar d'ayar yarinyar da muryarta ta kasa barin kwalwarsa lumshe ido yayi Dan shi a rayuwar sa yana son yaga mace mai Ilimi musamman ta had'a biyun na addini da kuma na boko yasandai Amera bangare daya yayi sa a tana da ilimin boko da wayewar da duk taron da yaje da ita na manya da manya ko k'asashen k'etare bata basa ruwa tana fiddashi kunya Dan baya da shakkar ko ina yaje da ita Saidai Inda ta samu tangarda bangaren ilimin addini yana cikin wannan tunanin tajita gefenshi ta rungomasa ta ce "Sannu honey good morning" morning too dear how was your night "Fine " ta basa amsa "kamar bazai magana ba saikuma ya d'ago ya Kalleta ya ce " Amera me yasa kika raina addini haka ,sau nawa zanyi kokarin sauyaki daga kan wannan muguwar dabiar "tashi Amira tayi tare da Fara gunguni ta ce " wlh honey ka tarki y'ar cewa kwanannan Wanda da baka dashi abubuwan da baka magana akansu a da yanzu komai nayi saikace banyiba daidai bansan me zanyiba yayi daidai"ta fad'a tana ficewa daga d'akin da Kallo ya bita kafin ya maida idonsa ga aikin da yake yace "Allah shiryeki" (nikam nace Amen )ba ayi awa guda ba yaga shigowarta d'akin tare da akwati ya yafa beil din doguwar rigar aka Kallonshi tayi ta ce "Honey nafa shirya" ba tare da ya kalle ta ba ya ce "Ina zuwa" America "ta basa amsa kai tsaye " Dukda mamakin abunda ta fad'a amma bai nuna mata ba "Allah ya kiyaye" ya bata amsa"Uhm to haka kawai zakace ba rakiya ba komai"Sai sannan ya d'ago ya Kalleta ya ce "Nida bansan da tafiyar taki yanzu ba Kuma bakiji addua nayi ba me kikeson nace " batare da ta k'ara cewa komai ba taje tayi hug dinsa tare bashi peck a kumatu ta ce "Bye honey sai munyi waya" tana gama fad'ar hakan tabar d'akin tana Sauri "Sai Bayan fitarta da awa Ukku sannan MD ya fita Escord dinsa suka biyo sa daga musu hannu yayi " Motarshi da ba kowa ya sansa da ita ba mai tinted ya hau Kafinma yayi horn security sun bud'e masa get yayiwa motarsa key sai Zaria koda ya isa gidansa ya nufa dukda. Yaga gidan yana buk'atar shara da mopping Dan ya fara kura tunani ya dingayi yanda zai hadu da yarinyar Dan yana tsananin buk'atarta wani tunani ne ya fad'o masa me zai hana yayi irin waccen dabarar da yayi na kiran Malam Umar ya ce a kira masa Zarah Yusuf Dan ya rik'e sunanta radam cikin ikon Allah yasan ta saikuma ya tuna kar Mlm din yayi zargin akwai abunda ke tsakaninsa da yarinyar Dan ya lura da irin kallon da yake masa tsaki yaja ya ce laifinane da ban Anshi number ta ba wani tunani ne ya fad'o masa kiran driver da ya d'aukar mata Wanda zai dinga kaita sch yayi Bayan ya d'auka ya amsa gaisuwarta a takaice ya ce "Da Allah ka rik'e yarinyar nan da kake daukowa daga makaranta" daga bangaren driver d'in ya ce "Eh ranka ya dad'e " okay gobe ina son kaje sch din lokacin tashinsu daga lectures kace ni na aikoka ka daukota"To shikenan ranka ya dad'e a Angama"daman Dan Zaria ne kuma baisan MD ba a fuska amma yasansa a baki washegari Zarah fitowarsu daga lectures kenan sun fito harabar da zasu wuce hostel taji ance "Hajiya " Bata amsa ba saboda batayi tunanin da ita ake ba cigaba da tafiya sukayi Ganin hakan ya sanya driver d'in binsu ya ce "Ranki ya dad'e ina yini" Yusuf ne ya Kalleta ya ce "da ke fa yake Daugher" Kallonsa tayi saita kalli driver dukda da farko bata Ganesa sosai ba Ta ce "Lafiya " Cikin girmamawa ya ce "Lafiya qlau Hajiya daman Alhaji ne ya turoni ya ce na daukoki nace maki shi ya Aiko ni" Numfashi Zarah taja tare da sauke ajiyar zuciya irin andameta ta ce "Ka ce masa nace bazanzo ba" Cikin girmamawa ya ce "Umarnine ya bani Hajiya Dan Allah ki daure kishigo "nima sako na baka ka kai masa ta fad'a tana yin gaba Hango su Chuchu da tayi Yusuf dai tsaye yayi yana mamakin me hakan ke nufi Kallon driver da yayi tsaye yayi ya ce " lafiya dai ko Malam "Lafiya " ya basa amsa daidai lokacin da wayarsa tayi ringing "dubawa yayi yaga oga ne Sosai hankalinsa ya tashi a sanyaye ga d'aga Daga bangaren MD ya ce " basu tashi ba ne"a sanyaye driver ya labartawa md yanda sukayi da ita"tsaki daga bangaren MD yaja ya ce "Ka bata wayar" ranka ya dad'e tabar wajen fa"ba ta yanda za ayi a bita da wayar"Kallon Yusuf yayi ya ce "Eh to ga wani nan Wanda na gansu tare kilan shi zai iya sanin yanda yayi ya kai mata wayar " saida MD yaja numfashi kafin ya ce "zankira nan da 5 minutse ka tabbatar an kai Mata wayar" yana fad'ar haka ya katse kiran kallon Yusuf yayi dake shirin barin Wajen ya ce "dan Allah Abokina ko zakayimun wani taimako ka mik'awa yarinyar da tabar wajen nan. Wayar" shiru Yusuf yayi Dan maza basa shiga hostel din mata kuma yaga harta shige hostel Hango su Asmy a wajen da yayi ya sanyashi amsa ya ce "badamuwa bari na ba y'an uwanta su kai mata" Yawwa Abokina na gode "su Asmy na karasowa yusuf ya mik'awa Asmy wayar ya ce " Dan Allah Zarah zaki mik'awa wayar idan kun shiga"ba tare da sun kawo komai a ransu ba ta ce "okay" suna shiga Lokacin Zarah na Danna waya "Gado Chuchu taje ta haye tana maida numfashi Dan kanta ke ciwo mik'awa Zarah k'aramar nokiar Asmy tayi ta ce " gashi Akace wai a baki"da mamaki Zarah ta ce "Nikuma" bata k'arasa maganar ba saka makon ringing d'in da wayar tayi Kallon number tayi taga An rubuta oga a jiki Kallon Asmy tayi itama ta Kalleta ta ce "Ki d'auka Inajin ko wayace zakiyi" da wa kuma"Zarah ta fad'a tana turo baki"ki amsa kiji ko meye cewar Asmy a sanyaye Zarah tayi picking call din"Jin shiru ya sanyata cewa Hello "Cikin sayayyar muryarta " Daga bangaren MD saida ya lumshe ido "Jin shiru ya k'ara sanya Zarah cewa " Hello ko ba aji"nan ma shiru Ba ansa dubawa tayi taga har lokacin ba a katse ba cike da jin Haushi ta ce "Zanfa kashe tunda baza ayi magana ba " Sai sannan MD yayi k'arfin halin cewa "Hey" saida gaban Zarah ya bada daram jin muryar da ta jima batajita ba saurin fusgewa tayi tare da hade rai tamau ta ce "waye" Mijinki ne"Ya bata amsa kai tsaye"Waro ido Zarah tayi kafin taturo baki kamar yana gabanta ta ce "Ni ai bani da miji budurwa ce" daga bangaren MD murmushi yayi ya ce "To Mijinki na Wata Tara" Hararar wayar tayi kafin ta maida kunnanta tana turo baki tayi shiru"Chan Bayan few seconds ya ce "na turo a daukeki kince bazakizo ba why?Ta tsinkayi muryarsa "Bana ra'ayi " Ra'ayin me?zuwan?Okay to ni ina ra'ayi "tsaki taja a ranta ta ce " Dan rainin wayau kawai to bazanzoba "a fili kuwa cewa tayi " saika hakura"bansan hakan ba "Hakurin?Eh" To sai kayi kuka"dukda baison yi Dariya saida ya danyi Wanda hartajiyo daga wayar ya ce "Kina son ganin kuka na?Gyada masa kai tayi kamar tana gabansa" magana zakiyi"Eh"saboda me '"Dan naga zaiyi maka kyau ko muni zaiyi maka"yar Dariya yayi ya ce "Aiko har abada bazaki ga kukan nawa ba" Uhm idan kuma nagani fa kace me"Kasaitaccen murmushi ya saki ya ce "bama zaki gani ba Ai har abada " Banda dai cika baki idan kuma na gani fa saikaji kunya ko "Murmushi ya k'ara saki ya ce " Daga ranar da kikaga kuka na zan mallaka maki katafaran gida na dake Abuja Wanda nafiji dashi a Duka gidajena"Dariya da bata shirya ba Zarah ta fashe dashi Dukda Chuchu hankalinta bai kansu saida ta d'ago ta Kalleta bare Asmy dake gefenta "Cikin murmushi ta ce " Nikuma nayi maka alk'awarin insha Allahu sai naga kukanka"Okay haka kika ce kenan"uhm"murmushi ya saki ya ce "Ki rubuta ki Aje " Kaima ka rubuta ka aje"ta mayar masa "Naji yanzu dai ki biyo driver please" Wai me zanyi maka idan nazo"har zai mata Tsawa saikuma ya tuna Lallashinta yakeson yayi tazo cikin k'asa da murya ya ce "Ina son ganin ki ne" Uhm haka dai kace"Hakane ma ai "ki biyosa please" Zan duba ta fad'a "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " saikinzo Mamy "Murmushin da bata shirya saki ba ta saki jin ya kirata da sunan da idan ya kira ta ta rasa dalili takejin dad'in sunan Bayan ya katse wayar kallonta Chuchu tayi ta ce " dawa kike waya haka nasan dai ba hafiz bane "Murmushi Zarah tayi mata ta ce " idan fa shine"nasan ma ba shi bane saboda baki sakin jiki kina Hira dashi harda Dariya haka karfa wani ne yake kokarin kwacewa Hafiz da yayana da ba ama sashi a file ba fada "Dariya Zarah tayi ta ce " Baki da dama Daughter bari na shirya zan wuce gidan Aunty "Kallonta Chuchu tayi ta ce " Aunty kuma Kina nufin wannan Karin ma Chan zaki koma nidai wlh banaso "ta fad'a tana turo baki gaba" Dan murmushin dake lotsar da dimple dinta Zarah tayi ta ce "Zan dawo ai daughter Asmy dai tagumi tayi ta Lula duniyar tuni tasan wannan wayar da Zarah take yanda ta sakar masa jiki ko Hafiz bata waya dashi haka Dan tagane mai kiran kallo d'aya Zarah tayi mata taga yanda ta dirmiya a duniyar tunani saida ta sake wanka Kafin ta shirya ta sanya atamfarta mai blue da fari Riga da sicket sannan ta zunbula hijab d'inta blue har kasa batayi make up ba taji wayar ta sake ringing tsaki taja a ranta kafin ta daga tana turo baki ta ce " gani nan fa"tana gama fad'ar hakan ta katse Kallon Chuchu tayi ta ce "Sai nadawo" Okay to momcy a dawo lfy"Tashi Asmy tayi ta ce "Muje na rakaki" tare suka fita Kallon Zarah Asmy tayi ta ce "Naga yanzu kin saki jiki da mutumin nan please kar haka ya baki damar da zaki fad'a masa garinmu saboda ina gudun matsala wlh gabana sai fad'uwa yake ga Hafiz da ya kusa dawowa ga bikinki na k'aratowa Zarah banason Asamu matsala banason na zama silar bullowar wata matsalar" ganin yanda tayi sanyi ya sanya Zarah yin murmushi ta ce "Karki damu sis ba wata matsala da zata faru insha Allahu karki damu ai komai ya kusa zowa karshe" hakane har bakin motar Asmy ta rakata suna isa gidan a bude ta iske kofar palourn tana turo baki ta shiga da Sallama a bakinta cikin miskilanci ya amsa sallamar kasa_kasa k'arasa shiga palourn Zarah tayi cikin sanyi tare da samun guri ta zauna Dagowa yayi ya Kalleta yaga ta wani had'e rai kamar ba itace ta gama Dariya a waya ba kamar ba zai magana ba saikuma ya ce "Ba gaisuwa ko Mamy" Sai sannan ta d'ago ta Kallesa kamar bazatayi magana ba saikuma ta ce "Ina yini" kasa_kasa "banaso tunda saida na roka " Turo baki gaba tayi tare da kauda kai "Ganin miskilanci takeji ya sanyashi kyaleta take away ya sanya aka yo musu kallo d'aya tayiwa abincin tace " na koshi"saboda me?ya tambayeta fuska ba wasa"banason cin abincin waje"Saina ina"Nafison na girka?ta bashi amsa kai tsaye "Okay kiyi hakuri ki daure kici yanzu kafin anjima za a kawo kayan amfani a kitchen din shiru tayi saikuma ta ce " na k'oshi banjin yunwa"Saikinci kinsan banason gardama "shiru tayi saida tayi minti kusan biyar kafin ta dauki take away din tana turo baki" a zuciyarshi ya ce "na lura yau wani miskilanci takeji Aiko gidan kikazo," Yinin ranar Zarah kin sake masa tayi tun Baidamu ba harya dawo kuma yana tunanin ko wani abun yayi mata Bayan magriba ya aika driver ya cika kitchen din da duk wani abun girki da za a buk'ata sannan ya cika fridge din kitchen din da kaji da su kayan miya Da sauran abubuwan da bazazu lalace ba a fridge Bayan isha suna zaune a palour Zarah na karanta alqur'ani cikin zuciyarta kallonta MD yayi yaga yanda ta maida hankalinta ga wayar har bata San yayi mata magana ba saida yaje ya amsa wayar kafin firrgit ta dawo hankalinta duba abunda take a wayar yayi yaga qur'ani ne take ciki mayar mata da wayar yayi tare da cewa Ki hadamun cope ki kaimun daki "Yana gama fad'ar haka yayi Hanyar d'akin saida ta gama surar da take kafin ta Aje wayar ta sata airplane cikin k'ank'anin lokaci ta hadamai had'adden tea Wanda yasha ganyayyaki Dan taga ganyayyakin hada tea a abubuwan da aka kawo Bayan ta gama a k'aramun cup ta zuba masa tare da nufa hanyar d'akin da yake saida tayi knoking ya bata umarnin shiga Zaune ta samesa laptop gabansa Dagashi sai kayan bacci a ranta ta ce " bashi da Aikin da ya wuce danna system "A sanyaye ta k'arasa d'akin tsaye tayi kamar bazatayi magana ba saikuma ta ce " gashi"shiru yayi na d'an second kafin ya d'ago ya Kalleta yanda ta wani had'e rai ya ce "A garinku haka ake kawowa miji abinci" Turo baki gaba tayi tare da kauda kai"a ranta ta ce "wani sabon duniyancin kuma da kazo dashi" tsinkayar muryarsa tayi da cewa "Zoki Aje" Ya nuna mata center Table d'in dake gefenshi"Yunkurawa tayi ta Aje zata Mike da hannu d'aya ya Fard'o ta jikinsa wara idanu tayi saikuma ta fara kokarin tashi daga kanshi"a kunne ya rada mata "wannan shashan maganin da kike na meye" Bakomai fa"ta fad'a kamar zatayi kuka Kara janyota yayi jikinsa yace "Ko duk kewa ta ce da kikayi" turo baki tayi gaba ta ce "Allah kiyaye ni nayi kewar...bata k'arasa fad'ar abunda takeson fad'a ba ya had'e bakinsu waje daya.....washegari da shirin sch ta tashi a lokacin yana kwance idonshi lumshe yanajin wata irin nutsuwa da rabonshi da ita tun rabuwarsu ta k'arshe da Zarah itako tana gaban mirror tana shafa ta Cikin mirror din yake kallon yanda take shafa hoda cikin nutsuwa dimple dinta two side ya karema kallo yanda suka lotsa sai sannan ya k'ara karewa fuskarta kallo ba fara bace Chan ba haka ba baka ba irin skin d'inta ne ake kira da choculate colour saboda yanda fatar tata take luf_luf babu kurji ko kwarzano a fuskar kamar bata shiga rana hips d'inta ya dinga kallo da hijab din data sanya ta d'an lafe mata a jiki " zan tafi?muryarta ce ta dawo dashi daga duniyar tunanin d'aya Lula "Nawa zaku fito lectures" 4pm"ta basa amsa"Okay 4:30 driver zaizo "shiru tayi " Bata basa amsa ba dan harga Allah basan kwana gidannan take ba "10k ya kirgo ya mik'o mata " Kin amsa tayi "hade fuska yayi yace " kinsan dai bansan musu"a sanyaye tace "akwai kudi a hannu na shiyasa " To wannan din nake son ki amsa "ya fad'a fuskarsa ba wasa" badan taso ba tasa hannu ta amsa ta ce "Nagode" tana gama fad'ar haka ta fita tana turo baki...tun daga ranar nan kullum Zarah anan gidan take kwana Saboda driver ke kaita sch ya maido ta MD ko koda yaushe yana gida Ba Inda yake zuwa daka Kallesa zakasan yana samun kulawa saboda har wani kib'a yayi fatar nan tasa ta k'ara fresh saboda yana samun abunda yakeson tako wani bangare ga wani time d'in idan ya sanya Zarah tayi masa girki tanayi saboda yanzu ya rage mata rainin wayau da yake da yanzu har sukan zauna su danyi Hira bangare guda kuma yanayin waya da Matar sa kullum dukda taga number nigeria bata fahimta ba saboda tasan wani lokacin idan yaje kasashe akwai abunda yake kashe kudi yayi number sa ta Nigeria tayi aiki Bayan two weeks Zarah ta tafi sch saboda saurin da take ta mance wayarta a d'akin MD na kwance yaji ringing d'in waya a jaka sai sannan ya lura da jakar wacece kyalewa yayi nan wayar tayi ta ringing ganin ringing d'in ya damesa ya sanyasa janyo jakar Dan ya d'auki wayar ya kashe gaba d'aya yana zage jakar yana fiddo wayar yaga an rubuta ya Hafiz a jiki tsaki yaja tare da kashe wayar gaba d'aya yazo zai maida kenan ya Hango magunguna a ciki kamar bazai d'auka ba saikuma ya d'auko guda ansha Rabi saura Rabi kenan duba maganin ya shigayi Inda ya shiga karantawa sosai yayi mamakin Ganin maganin hana d'aukar cikine d'auko sauran biyu yayi yaga duk irinsune "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un" ya fad'a a ransa a fili ya ce "watau aikin banza muke yarinyar nan ta fimu wayau duk plane d'in da muke wata da watanni ashe da abunda take sha no wonder ace har wata Bakwai saura wata biyu karewar yarjejeniyarmu ace bata samu ciki ba ," sosai yashiga jujjuya magungunan yanajin ba dadi a ransa ya ce "Yanzu ya zanyi lokaci na kurewa" Wani shiri ne ya fad'o masa a rai Tabbas dole yayi mata plane d'in da zata daina shan maganin nan saboda ko ba Dan sabodashi ba nan gaba zai iya yi mata illa ya lalata mata mahaifa tunda ba tab'a haihuwa tayi ba "Bayan Zara ta dawo daga lectures lokacin md baya gidan ya d'an lek'a gidan gonarsa dake garin Kai tsaye Zarah wayarta data manta ta nufa tayi mamakin ganinta kashe Dan bazata manta ba bata kashe ta barta ba saikuma tayi tunanin kukan ta tafi ta kashe din tana dubawa taga missed call d'in ya hafiz kiransa tayi Bayan ya kira suka sha y'ar Hira kafin ya k'ara jaddada mata da dawowarsa saura wata guda dukda gaban Zarah Saida ya fad'i amma hakan bai hanata nuna masa tana farinciki da hakan ba " Bayan sun katse duba wani missed call d'in tayi taga na Aunty Halima ce "Itama kiranta tayi Bayan sun gaisa tace " Amarya k'in bace ba ajinki kin yada auntyn naki"Murmushi d'auke da fuskar Zarah ta ce "ba haka bane Aunty kinsan koda yaushe kina raina" Murmushi tayi ta ce "Haba dai ai ni da kike raina aina nemiki turomun address din gidanki gobe insha Aah zankawo maki ziyara tunda ke baki zumunci" Gaban zarah saida ya fad'i Hakanan ta fusge ta ce "Kai amma Aunty Dana ji dadi zanturo maki ta message yanzu" Bayan sunyi bankwana gaban Zarah ya shiga fad'uwa ta ce "Ya zanyi da Matar nan Innalillahi" gashi bama tasan address din gidan ba fita Tai Inda ta tambayi mai gadi ya fad'a mata address din da lambar gidan nan taturawa Dr Halima text d'in address din gidan gabanta ta na fad'uwa sai Bayan magriba MD ya dawo "Kallonta yayi yaga kamar akwai abunda ke damunta cewa yayi lafiya dai ko?a sanyaye tace " Lafiya qalau Sannu"ywwa ko duk gajiyar sch din ce "murmushi ta kirkira ta ce " Wlh ko sai a slow level 4 d'innan ba sauki"Yana zauniya ya ce "Hakane daman kinsan aski idan yazo gaban goshi yafi zafi Allah sa dai a gama lafiya" Ameeeen ya Allah ngd "Wani course kike" Mass com "Wow " ya fad'a tare da Jinjina mata hannu ya ce "na Sara maki" dan murmushi tayi ta ce "Ko" Eh,mana"Tunowa yayi ba course d'insu d'aya da Chuchu ba a ranshi ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Nasanma bata Santa ba Tunda ba course d'insu d'aya ba " Wayarsa da yasa alarm kafin ya shigo tayi ringing dubawa yayi ya katse k'aran tare da karawa a kunnansa kamar mai yin waya ya ce "Hello Ya mai jikin" shiru yayi kafin ya ce "Subhanallahi kenan abun hartayi worse haka Gaskiya Aisha bata da hankali haukan me take taje tayi da shan maganin hana d'aukar ciki ai yanxu gashinan ya juyar mata da mahaifa tayiwa Allah shishigi ya gwada mata ikonsa yanxu gashinan ta rasa haihuwar ma gabak'i d'aya garin shirme a Gaskiya banjiye maka dadi ba aboki Allah ya kiyaye gaba" shiru yayi na d'an dakiku Alamun kamar yana sauraran bayani daga wayar sai kuma ya ce "Ah to da gaskiyarka kam gwara kayi Aurenka tunda ita ta sayawa kanta Allah ya kyauta ita kuma ya bata lafiya" Tunda ya fara wayar hankalin Zarah ke kan abunda yake cewa kasancewar da karfi karfi yake maganar sosai gabanta ya fad'i fahimtar abunda suke cewa da tayi a ranta ta ce "Na shiga ukku karfa na illata kaina" tanajin saida ya gama wayar kamar bazatayi magana ba Dan Duk ta rude saikuma tayi k'arfin hali ta ce "Dan Allah na tambayeka" Inajinki"Wannan Wanda kuke waya dashi kamar na lura matarsa ce keshan maganin planning ne yayi mata illa ko"a ranshi ya ce "Alhamdulilla anzo wajen a fili kuma cewa yayi"eh ya akayi " shiru tayi saikuma ta ce "Bakomai amma ta jima tana sha har yayi mata illa haka?Girgiza kai yayi ya ce " a a a ko shekara ba ayi ba tana shan gashi sabon Aure ne sukayi Yanzu yayi mata illa har an cire mata mahaifa"Sosai ta firgita ta kasa control d'in kanta cikin firgici ta ce "Innalillahi yanzu kenan shikenan bazata sake haihuwa ba Amma ba kowanne maganin yake illa ba ko?...........✍🏿 *Yau dai nasan ba korafin readmore yayi Kad'an*😄😐😐 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo Ce*_🤙🏿 🅿️.........*59 & 60* "Mafi yawaicin su suna yiwa mata illa wajen lalata mahaifarsu musamman idan ba ta kan ka'ida akayi amfani da su ba dukda ni ba likita bane amma nasan da hakan suna da illa sosai musamman ga Wanda basu tab'a haihuwa ba Suka fara da shansu yana juyar musu da mahaifa sosai" wata uwar zufa ce ta karyowa Zarah "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un " kawai take maimaitawa a cikin zuciyarta "Lura da hakan ya sanya MD cewa " Yadai naga kin firgice lafiya"Daidaita nutsuwarta ta so yi amma ta kasa Mikewa tayi ta ce "Lafiya" Tana barin palourn ya saki kasaitaccen murmushi na alamar cin nasara kenan "Zarah ko na shiga wata zufar ta k'ara karyo mata ta ce " na shiga ukku kar naje na lalata mahaifata da kaina Bayan babu burin da nake dashi a rayuwa sama da ganin jini na nima na zama Uwa"sosai ta fara zirga zirga duk ta rude janyo wayarta tayi tare da kiran Dr Halima koda ta kira kashe taji magungunan ta fiddo tare da sanya su a a toilet tayi floshing da ruwa washegari da Yamma MD na bedroom dinsa yana ayyuka a laptop yayinda Zarah na palour har lokacin a firgicin tsoron abunda ya faru da Matar nan da Md ya fad'a mata take wayarta ce tayi ringing dubawa tayi taga Aunty Halima Ajiyar zuciya ta sauke Bayan ta d'auka Nan take shaida mata suna kofar gida mai gadi ya hanata shigowa yace saida izinin masu gidan "ina zuwa" Zarah ta bata amsa tare da yafa beil ta fito bayani tayiwa mai gadin akan bakuwarta ce kafin ya bari su shigo sosai Zarah ta nunawa dr Halima.jin dad'in zuwanta Inda tayi welcoming d'inta sosai a basaja nan tagabatar mata da lafiyayyen abincin da ta girka na musamman Dak'yal ta samu ta d'an tsakura Kad'an lura da Zarah kamar bata cikin nutsuwa ya sanya Dr Halima daddabarta ta ce "Yadai kanwata lafiyarki qlau kuwa?saurin kirkirar murmushi Zarah tayi ta ce " lfyqlau Aunty "hmm kawai dr Halima tace Bayan few minutes Zarah ta kasa shiru Dagowa tayi ta kalli Dr Halima ta ce " Aunty wai Dan Allah da gaske maganin hana d'aukar cikin nan yana lalata mahaifa kuwa?saboda me kikamun wannan tambayar"shiru tayi saikuma ta dago ta ce "Naji labarin wata da yayi mata illa shiyasa" shiru Dr Halima tayi tasan dai Wanda ta rubuta mata bashi da wani side effects amma tasan yanda zatayi ta tsoratata Dan itama Bason shan da take take ba Dagowa tayi ta ce "bazanyi miki karya ba kanwata yawaicinsu suna da illa kuma suna lalata mahaifa sosai da zan baki shawara ko wannan din Dana rubuta maki ki daina amfani dashi zai iya baki matsala dukda bama fatan haka"sosai Zarah ta k'ara shiga tashin hankali a ranta ta ce " na bani Ni Fatima Wannan mutumin duk shi yake neman zakamun masifa da bamuyi *Auren wata Tara"nan ba da komai bai faru ba "Dak'yal ta iya daidaita nutsuwarta a sanyaye suka yi Hira da Dr Halima hartayi mata bankwana ta fita Inda ta Zarah tayi ta wurga ido ta rasa abunda zata bata gashi ta mik'e tana shirin fita" Mamy"ta tsinkayi muryarsa daga daki"Kallon Dr Halima tayi ta ce "yi hakuri Dan Allah Aunty naji yana kirana" Ohh waida duk zaman nan da nayi mijinki na nan ikon Allah to saikin fito "Murmushin yake kawai Zarah tayi tare da nufar d'akin da yake Kamar ko yaushe aikin d'aya daban ne yake using da system karasawa dakin tayi cikin nutsuwa ta ce " gani"Bandir din y'an dari biyar dake gefenshi an fiddosu ya mik'a mata tare da cewa "Anshi kiba bakuwar taki tayi kudin transport" saida Zarah ta Waro ido ganin uban kudi a ranta ta ce "Shi wai baisan darajar kudi ba " a fili kuwa cewa tayi sunyi yawa ai"Harararta yayi ya ce "Ke naba?tana turo baki ta amsa ta ce " Angode "kina turomun bakin nan na kusa maganinsu" Dan murmushi tayi tare da ficewa daga d'akin Inda ta samu Dr Halima na shirin fita mik'a mata kudin tayi ta ce "Gashi Aunty ya ce Kiyi kudin transport" Girgiza kai Dr Halima tayi ta ce "a a a wlh nagode kanwata bazan k'arba ba ai gobe bana dawo ba ana irin haka" Marairaicewa Zarah tayi ta ce "Dan Allah Aunty ki amsa bazaiji dadi ba Dak'yal Zarah ta samu ta amsa hijab d'inta ta sanya tare da fitowa Dan ta rakata cewa tayi ki koma basaikin raka ni ba " girgiza kai Zarah tayi ta ce "a a a Aunty muje" tare suka fita Inda a hanya Dr Halima sai nasiha take mata akan tabi mijinta "ita dai Zarah shiru tayi tana jinta a ranta ta ce " bakisan ciki ba Aunty da kinbar wa azin nan Auren da na lokaci ne kuma lokacin ya kusa karewa "sannan ta kara da cewa "kardai ki karashan maganin nan zai miki illah" nan nema zarah ta ce "insha Allah aunty bazan sake sha ba "ba suyi nisa ba ta samu napep Inda Zarah tayi mata Godiya tare da shaida mata zatazo insha Allah tare da Juyawa Dan ta koma gida Tazo tana gab da shiga gidan taji an kira sunanta daga baya Juyawa tayi Ganin Mlm sulaiman ne ya fito daga mota saida gabanta ya fad'i Dan ta manta rabon da ta ganshi ko a makaranta ma ta hangoshi sauya hanya take karasowa Inda take yayi tare da cewa " Malama Zarah kinyi wuyar gani"Kasa tayi da kanta Tare da cewa "Ina yini mlm" lafiya qalau me kikeyi anan"waigawa tayi ta kalli gidan saikuma ta dago ta rasa k'aryar da zatamai kawai sai ta ce "nazo wani gida ne " Okay muje na saukeki "saida ta d'an Zara dara_daran idanunta kafin tace " a a a Malam zankoma da kaina"saboda me?,saboda bana hawa motar maza"Dan murmushi yayi yana Kara Matsowa kusa da ita ya ce "Ga Alamun har yanzu ba a amshi tayin da nayi ba ko" gabanta na fad'uwa ta ce "Ba haka bane Malam an sanya Ranar Aure na ne" lokaci guda fuskarsa ta sauya a sanyaye ya ce "Allah sarki ashe na makaro Allah ya sanya alkhairi amma Gaskiya duk Namijin da ya sameki ya gama morewa a duniya Zarah ba k'aramun dace yayi ya more da komai na taya koma waye murna Gaskiya Dan samun kamarki cikin mata Sai an tona "" kasa tayi da kanta tana wasa da yatsun hannun ta ce "Nagode Malam zan wuce" Murmushi yayi ya ce "Bazaki yarda na rage maki hanya ba kenan" girgiza kai tayi ta ce "hakan ma nagode Mlm"to shikenan bari na wuce daman gidana yana nan sama da wancen layin zankoma gida ne na hangoki Sai Anjima ki k'ara dagewa dai wannan shine mai matsalar na karshe " Murmushi tayi ta ce "Insha Allahu ngd " ta juya zata shiga ta Hango Motar MD Na fitowa daga gidan ta Cikin mota ya dinga mata kallon mamaki yana karewa saurayin kallo tsaye yayi lokaci guda naga fuskarsa ta sauya har lokacin baibar kallonsu ta Cikin motar dashi yake kallonsu su basa ganinsa Zarah ko kallo d'aya tayi wa motar ta kauda kai Jan motarsa MD yayi da karfi tare da barin Wajen ya nufi gidan gonarsa Zarah ko saida taga tafiyar malaminsu kafin tashiga cikin gidan a ranta ta ce "Ji a baka kamar mutumin kirki k'ilama.sharri ne ake masa saikuma.tace " kodan a fuska ba a ganewa"MD shine bai dawo gidan ba sai Bayan isha'i lokacin Zarah harta kwanta kan bed din da littafin hisnul Muslim a hannunta tana karanta adduo'i shigowa MD yayi d'akin kallo d'aya tayi masa ta wutsiyar ido ta maida kanta ga abunda take sosai ya had'e rai tahau ba alamar wasa a fuskar tasa karasowa yayi d'akin ya Kalleta a murtuke ya ce "waye na ganku a kofar gida" Dagowa tayi tare da Kallonshi irin kallon mamaki kafin ta kauda kai ta ce "Meye ruwanka da koma waye?" ni sa'ankine zaki fad'awa maganar rainin hankali zakiyi mamakin abunda zan maki wlh kina mayarmun da magana son ranki "Murguda baki Zarah tayi tana Kara kauda kai"batai aune ba saiji tayi ya murde mata baki" ihu ta fasa tuni hawaye harsun wanke mata fuska Inda take ya zauna tare da matseta jikin allon gadon Dan Kara ta saki Cikin kuka ta ce "Me nayi maka kuma " Zaki fad'amun waye shi ko saina maki abunda bakiyi tunani ba "Malamin mu ne" ta fad'a cikin kuka"tsaki yaja tare da cewa"shine dan iskanci zaki Fara kawomun kazaman kartin maza kofar gida dan iskanci"Dukda tanajin zafin matsar da yayi mata bai hanata cewa ba "Nidai ba y'ar iska bace " wa yace maki yar iska?Kai "ta fad'a tana cigaba da kuka" Tsaki yaja tare da cewa "ke kikaji ai" Turo baki gaba tayi ganin ya d'an tashin daga wajen "kasa kasa ta ce " Allah ya isa?Jin abunda ta ce "ya sanyashi juyowa tare da nuna kansa ya ce " Dani kike"Girgiza kai tayi ta na hawaye ta ce "Ni ba abunda nace"aini Naji me kikace ya fad'a yana Kara matseta " ya ce maimaita abunda nace "cewa nayi akwai Allah" sassauta matsar da yayi mata yayi tare da Jan tsaki a ransa ya na shirin Mikewa a ranta ta ce "Mugu Azzulumi macuci Allah saiya sakamun" Zaro ido MD yayi tare da kallonta ya ce "Ni kike fad'awa haka?Sai sannan Zarah ta tuna a fili tayi maganar ja da baya tayi tare da cewa " Nifa Bada kai nake ba "Dan murmushin gefen baki yayi ya ce " zanyi maganinki yanzunnan"yana gama fad'ar hakan ya fara rage kayan jikinsa Zarah na ganin haka tasan yau shikenan ta shiga hannu"Tana shirin sauka daga gadon yabi ya danneta......sosai Zarah ta karbi wuta a wajen MD bata tabajin gundurar abun irin na yau ba Dan cike da mugunta MD ya dinga binta saida yayi awa biyar a kanta tun 9 sai 2 ta samu ya rabu da ita Shima Dan ta dinga fasa.masa kuka ne shi kanshi yasan yau ya kurewa yarinyar daman haka yakeso shiko ranshi fesssss Zarah ko tuni baki ya mutu ta k'ara tsorata da mutumin nan kwata_kwata bashi da wasa washageri gashi suna da lectures safe tun asuba bata koma bacci ba ga baccin dake idonta bana wasa bane ga gajiyar da MD ya Tara mata shiko yana kwance kan bed a gaggauce ta shirya Bayan ta had'a ruwan liptop bako madara haka Tasha saboda sauri take tana komawa d'akin hijab d'inta ta sanya Harzata fita ta tsinkayi muryarsa da cewa"karfe nawa zaki dawo "A tunaninta ma bacci yake saita taja gunguni a ranta kafin ta ce " 4 Kuma 2 suke da lectures ta fad'a masa hakane Dan ta sarara"Okay "kawai ya fad'a " tana fita driver har yazo Dan tuni yasan lokuta da take Da lectures koda Zarah ta gama lecture hostel ta wuce kallo d'aya zakayi mata kasan ba daidai take ba saboda ba k'aramun bacci bane a idonta tana shiga ta samu su Asmy na lunch kasancewar 2 lokacin suma basu jima da dawowa daga lectures ba kai tsaye bed ta haye tare da sauke ajiyar zuciya kwanciya tayi Chuchu ce ta ce 'Lafiya dai momcy"lafiya qlau bacci ne kawai nakeji wlh "ta fad'a tana juya musu baya tare da kwanciya ta cire hijab din jikinta Da kallo Asmy ta bita kafin ta ce "Ki sauko kiyi lunch tunda nasan daga lecture kike bakici komai ba " idan na tashi naci ta bata amsa bacci ne mai nauyi ya d'auki Zarah ita ce bata tashi ba sai 4:30 Dan koda Asmy ta ce Zata data ita chuchu tace ta rabu da ita tana tashi salla kawai tayi sai sannan taci abincin da su Asmy suka rage mata a cooler tana gamaci time.ta duba taga har biyar saura tunani tayi tasan drivern yazo kila harya tafi tsaki taja a ranta ta ce "Yau ba Inda zani wlh mugu kawai" har dare ganin Zarah bata da niyyar tafiya ya sanya Chuchu cewa "wai yau nan zaki kwana amma" Eh nan zan kwana"Alhmdllh daman ina son ki jiye mun harda Dan so nake na sauke kafin mu gama sch d'innan wlh"Murmushi Zarah tayi ta ce "Insha Allahu zama ki sauke kafin lokacin tunda Kinga yanzu hizif shida ya rage maki" Da daddare Zarah ta amshi haddar Chuchu Inda ta kuma Kara mata wani shafin driver ko tunda yazo yayi ta jira yaga bata nan ya koma ya fad'a ma ogansa bai ganta ba "Okay kawai md yace " Kd ya wuce Ranar Dan yanason ganin Ammynsa "washegari ya koma Zaria Bayan yayiwa Ammynsa bankwana " Zarah ko ranar ma so tayi ta k'ara kwana dandai kawai tana fitowa lectures ta had'u da driver da ba abunda zai maida ita tana zuwa ta samu MD ya hakimce a kan kujera a takaice ta gaisheta tare da wucewa ciki....after 3 weeks Rabin rayuwar md yanzu kam ta dawo Zaria saboda koda yaushe yana nanike da Zarah yana kwasar romo ko sch yanzu dak'yal yake barinta ta tafi Zarah ko tana nan tana lissafin sauran wata guda ra rage yarjejeniyarsu ta kare inda karatunsu ya rage wata biyu su gama tun daga lokacin da ta zubar da maganin nan bata Kara waiwayar sha ba kwata_kwata tunaninta ma baikawo mata komai a ranta ba harkar gabanta kawai take "Yauma dak'yal MD ya rabu da ita Dan a safenma yanzu ba d'aga mata yake ba cikin Sauri ta gama shirinta Zata wuce sch tana shirin fita Ya ce " kijira na saukeki hanyar nayi"to"ta fad'a a hankali tare da zaunawa gefen gadon tana nan harya gama shirinsa ya fito Cikin shigarsa ta alfarma da gayu sai baza k'amshi yake kallo d'aya Zarah tayi masa tayi kasa da kanta saboda gabanta dake tsananin fad'uwa a tare suka fita Inda ya shiga driver sit ta zaga ta shiga gaba sun fara tafiya kenan ta Hango wata yarinyar mai tallar ta aya a faranti cikin Sauri ta d'ago tare da cewa "Dan Allah ka tsaya zan saya abunchan" Kallonta yayi tare da Kallon abunda take nuna masa ya ce "me zakiyi da abunchan ya gama shan kura a titi jifa " Tana Shagwabe fuska ta ce "Nidai ina so" parking yayi tare da mik'a mata 1k ya ce Amshi ki saya zage glass din motar tayi cikin Sauri ya sadda kansa Dan karma wani ya gansa a ganesa Zarah ko mamakinsa tayi kamar wani marar Gaskiya Juyawa tayi ta kira mai ta ayar Inda ta saya ta 500 ta bar mata chanjin a leda aka sanya mata har lokacin kan MD sadde saida ta Zage glass din kafin ya d'ago ya tada motar sukayi gaba kasayin shiru Zarah tayi ta ce "Wai Dan Allah me yasa baka San ana ganinka yanzuma ka sadda kanka " Is not your business "ya fad'a yana cigaba da driving" Turo baki gaba tayi tare da Fara cin ta ayarta har wani lumshe ido take Dan sosai tayi mata dadi ita kanta mamaki take da bata tabajin sha'awar wannan Abun ba Amma yau sosai taji dadinta Ta wutsiyar ido MD yake kallonta yanda ta dage take gintsar Abu da shi baimasan menene ba "bismillah" ya tsinkayi muryarta"Alhmdllh kici kayanki""Ka dandana kaji da dadi "Girgiza kai yayi a takaice ya ce "Banajin irin abubuwan nan" tab'e baki tayi tare da cigaba da cin abunta har cikin makaranta ya kaita Daidai gab da hostel d'insu yayi parking sauran ta ayar ta sa a jaka tana shirin fita Ya ruko hannunta Tare da damk'a mata 5k a hannu ya ce "Ki dawo da wuri yau please da yazo ki biyosa kidaina tsaidasa" Kasa tayi da kanta Tare da cewa"Toh ngd"har lokacin bai saki hannunta ba Ganin irin yanda yake kallon hannun tare da murzasa tanason tayi magana amma kwarjini yau da yayi mata ya hanata Chan Bayan few minutes ya ce "Kidingayin lalle zaiyiwa hannunki kyau inason ganin lalle a hannun mace"gaban Zarah na fad'uwa ta d'ago ta Kallesa saikuma tayi saurin kasa da kanta samun kanta tayi da cewa " To kace Matarka ta dinga yi maka mana"Murmushin da bai shirya saki ba ya saki ya ce "Kenan sai matata zatayi mun" Eh"ta fad a hankali"wani murmushin ya k'ara saki ya ce "To Matar wata Tara nace ta dingayi yimun ba ta gidan ba" ba tare da ta Kallesa ba ta d'an turo baki gaba ta ce"Matar wata d'aya dai ai wata Tara baya ne yanzu saura wata d'aya ko ka manta"ina sane harkin k'agara lokacin yayi mu rabu ko"D'ago da dara daran idanunta tayi ta sauke a kansa saitayi saurin kasa da kanta ta ce "Ina makara karya hanani shiga" Okay "ya fad'a yana sakin hannunta bud'e motar tayi tare da fita Daidai idonta ya sauka akan Hafiz dake gaban motar Kad'an sosai taga ya kara kyau da kiba yasha shaddarsa ash mai shegen kyau Ya harde kafa d'aya kan d'aya a jikin sabuwar motarsa sosai gabanta ya tsananta fad'uwa da karfi dafe saitin zuciyarta tayi daidai sukayi ido hud'u da shidinma ita yake kallo bako k'iftawa sannan yana bin motar da ta sauka da Kallo a matuk'ar rude ta juya ta kalli MD dake cikin mota har lokacin yaki tafiya Shima Inda take kallon yake Kalla Juyawa tayi ta k'ara kallon Hafiz da Shima motar MD yake kallo dukda baya ganin Wanda ke ciki lokaci guda Zarah taga fuskarsa ta sauya Wanda Bata tab'a ganin hakan a tattare dashi ba kamar wacce kwai ya fashewa haka ta k'arasa Inda yake ta kalli bayanta ta kalli gabanta haka ta dingayi ga MD yaki tafiya cikin jarumta ta k'arasa Inda Hafiz yake da har lokacin kallonta yake ya kalli motar da ta sauka dak'yal ta iya tattaro jarumtar da bata San tana da ita ba ta ce " Ya Hafiz Kaine da gaske kuwa"Juyowa yayi ya kafeta Da idanu tare murtuke fuska tamau nuna motar da ta fito daga ita yayi cikin muryar b'acin rai ya ce...........✍🏿 07026166536 domin neman Karin bayani _Tofa ya kenan Ga MD ga kuma Hafiz_🙆 *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️...........*61 & 62* "Motar waye naga an sauke ki," A matuk'ar firgice ta d'ago ta Kallesa sai kuma.ta kalli motar da har lokacin yaki tafiya sosai Zarah ta shiga rud'u "nace motar waye kika fito.daga ina kike tun d'azu nazo school d'innan ina jiranki ina kikaje?Zarah rudewar da tayi batasan sanda taji hawaye na zubo mata ba hangosu da Asmy tayi ya sanya gabanta fad'uwa tasan Hafiz yazo tun d'azu yake jiran Zarah dalilin karyar da zatayi masa ma ta rasa hakan ya sanyata kin fitowa Dan tunda ta fito ta ganshi tamaza ta koma yanzunma fitowa tayi Dan ta kirkira k'aryar da zata masa saita iske abunda ya k'ara tayar mata da hankali tundaga saukar Zarah a motar MD har zuwa yanzu da Hafiz ke daga mata murya akan idonta komai ya faru dak'yal tayi jarumta tare da karasawa Inda suke ta ce " Ya Hafiz Kaine kuwa da gaske ko gizau ne kake mun?Dukda Hafiz hankalinshi tashe yake bai hana yiwa Asmy murmushin k'arfin hali ba ya ce "Nayi 30 minutes a nan nayi ta Kiran layin ta kashe shiyasa na tsaya najirayi b'ullowarta ashe mugun Abu zangani dubi motar da aka sauke Zarah a ciki Asmy na tambayeta waye shine Kinga ta durkushe ta sanyamun kuka"Kallon motar Asmy tayi saikuma ta kalli Hafiz ta ce " wayyo ya Hafiz Motar malamin muce kasan itace amirar makaranta to shine dazu da safe aka gayyacesu 'a wata makaranta da za ayi safka shiyasa ya tafi da ita saboda shine shugaban mss din na makaranta kaga kuma sundawo inaga to sabani ma kukayi Dan itama bata wuce 30 minutes ba da fita"y'ar Ajiyar zuciya Hafiz ya sauke ya ce "Dukda haka bai kamata ta shiga ba motarsa ba sanadin yace yana sonta ne ko yayi sha'awar wani Abu daga gareta Gaskiya bazan lamunta da haka ba " Tsohone fa yaya Hafiz Ya haifeta sannanma matanshi hud'u kuma malami ne ustaz kuma ba ita kadai suka tafi ba yanzu haka da diyarsa a cikin motar "Ajiyar zuciya Hafiz ya sauke ya ce " Wlh har Naji sanyi karkiji yanda hankali na ya tashi Ina son Zarah sosai Asmy kinsan da haka Ina tsananin kishinta da zanso ko kuda bazan bari ya tab'a ta ba sannan Ko k'aramun yaro bazai kallemun ita ba please Ki dinga lurarmun da ita na damk'a miki amarta a hannunki "murmushi asmy ta saki. Ta ce Uhm su ya Hafiz manyan kishi karka damu ai aski yazo gaban goshi insha Allah nan da wata biyu munbar sch d'innan kaga kuwa kana gab da mallakar kayanka " kasaitaccen murmushi Hafiz ya saki ya ce "Gaskiya kinci kyauta fa " Y'ar Dariya Asmy tayi nan ta gaishe shi kafin ta wuce Lectures durkusawa Hafiz yayi daidai saitin kunnanta ya ce "Sorry my bride banzata haka abun yake ba kiyi hakuri" Shiru Zarah tayi ta cigaba da shasheka"Oh My god "ya fad'a yana daga kanshi kafin ya k'ara cewa " Kiyi Hakuri my Zarah Bazan sake ba Kinga laifinkine da bakiyimun bayani ba "Sai lokacin ta d'ago turo baki tayi tare da cewa " shine saika rufe ni da fad'a "wara idanu yayi ya ce " ni na isa nayiwa gimbiyata fad'a kiyi hakuri baki ma murnar gani na ki Mike please "Goge hawayenta tayi tare da mik'ewa Shima ya Mike murmushi suka sakarwa juna Zarah ta ce " amma kayi surprised Dina sosai ya Hafiz "Fuskarsa sauke da murmushi ya ce " Daman surprised d'inki naso yi shysa banfad'a maki na dawo ba "Yaushe ka dawo" Jiya Tun jiyan naso nazo naga gimbiyata yanda ta koma sai dare yayi Kinga Ko yanda kika k'ara kyau da komai my Zarah Gaskiya nayi sa'a fa ba kadanba "murmushi Zarah tayi tare da rufe fuska ta ce " kai ya Hafiz kaima ka k'ara kyau wlh"ai ban kaiki ba ke fa komai kika kara Ai ji nake kamar na janyo gama sch d'innan naku fa ji nake kamar a daura mana Aure yau"Nan ma Kara rufe fuska tayi ta ce "kana bani kunya fa ya Hafiz " Ai Gaskiya Ce dole na fad'a "karan tashin motar da tajine ya sanyata Kallon wurin a guje taga motar tabar wajen tab'e baki tayi a zuciyarta ta ce " ko ubanme ya tsaya tun d'azu yi mtwss"hafiz ko baima lura da tashin motar ba dan gaba daya hankalinsa yana gurin zarar sa sosai Zarah suka sha fira ita da Hafiz Wanda sosai ya dinga fallasa mata sirrin zuciyarsa da yanda ya matsu lokacin bikinsu yayi lectures din da bataje ta ba kenan Har lokacin sallah yayi yana nan yaje yayi salla ya dawo Hafiz shine bai tafi ba sai Bayan la'asar sosai yaji dadin arba da abar k'aunar tasa Zarah ko hostel ta koma ina ta samu Chuchu nayiwa Asmy kitso waje ta samu ta zauna tana hararar Chuchu ta ce "Shine ko kije ku gaisa" Tana turo baki ta ce "Na hangesa da na dawo daga lectures keda kikasan ni bamun yayiba har zanje mu wani gaisa ni banga abunda kika gani kikeso a jikin wannan mutumin ba wlh kikaga yayana saikin manta da wani Hafiz yayana ya had'u y'an mata har tuntube suke a kansa dashi kuka dace wlh tako ina kunyi match har cikin zuciya ta nake maganar nan wlh Zarah zanzo ki zama mallakin yayana saboda kece type dinsa yayana yana son mace mai ilimin addini da na boko,yana son mace mai kamun kai da Jan aji da tarbiya ,yana son mace mai tsafta gayu iya girki da sauran duk abunda yake so game da mace kina da su momcy tako ina kin hadu baki da makusa wlh Ammy ma tana son ki zama surukarta Saboda karkiga yanda take sonki" girgiza kai kawai Zarah tayi ta ce "Mubar maganar nan Chuchu kiyi mana fatan alkhairi kawai" tab'e baki ta kumayi Chuchu ta ce"Allah ya kaimu lokacin A nan Funtua ai za ayi ko?Eh "Insha Allahu tun satin bikin zantaho dukda ba son Angon nake ba" Dariya Asmy tayi ta ce "Kina yanda kikaso Chuchu wai Bason Angon kike ba keda bake zaki zauna dashi ba ita ai ta gani kuma tana so" y'ar Dariya Chuchu tayi ta ce "Allah da gaske nake kawai ina taya yayana bakincikin rasa ta da yayi ne" Asmy na Dariya ta ce "Auta baki da dama to shi Yayan naki cewa yayi yana sonta da zaki dinga tada jijiyoyin wuya" Ai nasan idan ya ganta din zaice yana so shiyasa "Sosai Asmy ta shiga yiwa Chuchu Dariya Inda suka dinga hirar Wanda Zarah bama tasan sunayi ba Dan tuni bacci yayi awon gaba da ita kallonta Asmy tayi tace " ikon Allah Daga Hira sai Bacci baccinma na la'asr"Chuchu ce ta ce "Jiyama wlh bata gama lecture ba tataho wai bacci takeji saida tayi kusan awa Ukku tana bacci" zuwan driver d'inta ne ma yasa na tasheta saboda Yusuf ya kirani yace ana kiranta"Asmy ta ce "Kuma fa wlh da bata da yawan bacci Zarah baccin rana ma ba fiya damunta yayi bare na la'asr " Kilan hada gajiya"hakane kuma Asmy ta fad'a "Zarah itace bata tashi ba sai magriba Shima saida Asmy ta tasheta tayi sallah Ranar a hostel ta kwana " kwananta biyu bata koma gidan MD ba Wanda sosai taji dad'in Rashin waiwayarta da baiyi ba cikin kwana na hud'u ta fito daga lectures ta Hango wata dalleliyar mota a gab da hostel d'insu har tayi gaba "mamy" ta tsinkayi muryarsa daga mota "harta tsaya saikuma ta juya ganin ta Cikin mota yayi mata magana amma da.Alamun saida ya Zage glass din motar waigawa tayi gabanta na fad'uwa Allah yasa ba Mutane sosai a wajen da batasan wasu mutanen suyi mata fassara harzatayi gaba saikuma ta tuno karya biyota ko ya kamata a gaba mutane ta shiga ukku Juyawa tayi kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ta nufi Inda motarsa take tana shirin shiga taji wasu y'an mata na gefenta wata daga cikinsu na cewa " Ai daman bana fad'a muku ba wlh salahan nan kamar na Allah sunfi shek'e ayarsu yanda suke so ana fakewa da hijab ana yanda akaso yanzu wlh idan ka fad'awa wani saiya karyataka amma da yake akan idonku ai kungani daman na fad'a muku amirar nan cikin wayau take barikancinta mune dai da muka fito namu fili aka fi gani"Juyawa Zarah tayi ta kallesu dukda maganar da ta jefe ta tayi mata ciwo girgiza kai tayi tare da yi musu murmushin da yafi kuka ciwo ta bud'e motar ta shiga taja ta rufe tana maida hawayen da suka zubo mata"Ko Kallon MD batayi ba ta hade kai da gwuiwa ta fara hawayen zarginta da wasu daga cikin sch din suka fara Wanda tasan duk shi ya ja mata Jan motar yayi batare da yabi ta kanta ba a hanya ganin har lokacin kamar kuka ta ke "ya sanyashi kallonta a takaice ya ce " me akayi maki"Kamar mai jira nan ta d'ago tana Goge hawaye Cikin muryarta ta shagwaba ta ce "Y'an sch d'inmu ne suka fara zargina akan daukata da kazo please kadaina zuwa sch d'inmu kar mutane su farayimun wani irin kallo" hankalinshi na kan driving din da yake ya ce "Bani naja maki suke zarginki ba samarin da kike kawowa suka ja maki yaushe na tab'a zuwa wajenki idan ba Yau ba?ni ba samarin da nake kawowa ko motar saurayi bantaba shiga ba ," ta fad'a tana turo baki"Shi Wanda yazo rannnan din har kina masa murmushi shiba saurayinki bane?ohhh ya Hafiz kake nufi?Harararta yayi ta gefen ido ya ce "Bansaniba" Murmushi tayi ta ce "Aishine Wanda zan aura wata guda da Gama school dina za Ayi bikin" tsaki yaja tare da cigaba da tukin sa "Tab'e baki Zarah tayi a ranta ta ce "Mai mugun hali kawai" Duk Auren da akace an daura Koda a wasa ne ya dauro kuma Aure ne ingantacce inhar ba rabuwa akayi ba Mu'amula da maza ko abunda yayi kama da makamancin haka haramun ne ki bari lokacin da Na rabu dake kinyi mu'amula da duk Wanda kikaga damar yi amma yanzu ina nusar dake girman zunubin da kike d'auka kuma nasan kema kinsan da hakan saboda kina da Ilimi karki d'auki nayi maganar nan da wata manufa a a in zakiyi mu'amula da maza dubu ba damuwa ta bace ina kiyaye miki ne fushin ubangiji"Yana gama fad'ar haka yayi parking tare da ficewarsa saboda sun Iso gida Zarah ko sosai jikinta yayi sanyi koda ta shiga cikin gidan harya shige bedroom dinsa tagumi tayi maganganun da yayi mata suna mata yawo a kwalwa ta jima kafin ta mik'e ta shiga tayi sallar la'asr da taji ankira a hanya Bayan ta gama sallah Qur'an ta d'auka tana cigaba da karantawa yunwar da tajine ta tuna mata da bataci abinci da rana ba yaye hijab d'inta tayi Kallon jikinta taayi taga doguwar rigar bata lafe ta ba Sosai taji dad'in ganin baya palourn Kitchen ta shiga ta girka Abu mai sauki sosai taci abincin Wanda har mamakin kanta tayi tasan dai bata da ci da Chan ma bare yanzu Bayan ta gama tayi hamdala kujera ta mik'e batasani ba har bacci ya d'auketa fitowa yayi daga Bedrom d'in sosai yayi mamakin ganinta tana baccin la'ar Wanda bai tab'a ganin haka a Wajenta ba Zaunawa yayi karewa sleeping face d'inta kallo yayi Yajima.yana kallonta wayarsa da tayi ringing ta dawo dashi daga duniyar tunanin d'aya Lula dubawa yayi yaga ,"My Merah"a jiki saida ta gama ringing kafin ya kirata sosai suka sha Hira irin ta mata da miji Wanda yawaici duk Amira ce mai surutun danshi ba ma'abucin son surutu bane har suka gama wayar bacci Zarah take Gashi yana son tashinta amma bayason katse mata baccin dayaje zai tab'ata saiya fasa sai Chan wajen 6 yaji farkawarta Bayan ta wartsake kallo d'aya tayi masa ta kauda kai tare da mik'ewa ta shiga d'akin cikin har isha'i bata fito ba Dan Sallama a Chan tayi tana gama salla ta kwanta bacci ya d'auketa Chan cikin dare taji MD nayi mata abunda ya saba kin biyesa tayi Dan kwana biyun nan abun ba dadi yake mata ba shi kad'ai yayi kidansa da tsalle Shi kanshi MD yayi mamakin yanda bata bashi attention ba ga kuma jin wani dadi da take karawa kwanakin nan haka rayuwa taci gaba Rabi a hostel rabi kuma a gidan MD Dan MD yanzu ya mayar da Zaria gida idan ka ganshi a kd tofa ziyara ce yakai musu A haka dai har wata guda Wanda yanzu wata Guda ya rage karewar yarjejeniyarsu A halin yanzu kallo d'aya zakayiwa Zarah kaga ta sauya saboda wani fresh da kyau da ta k'ara ta k'ara murjewa ga komai nata yayi b'ulb'ul saikuma bacci da take yawan yi Wanda ita kanta har mamakin wannan masifar baccin data sameta yauma tana kwance a gadonsu na hostel Tana bacci Chuchu ma tana gadonta tana karatu a Littafi kasancewar final exams dinsu dake tunkarowa duk sun maida hankalinsu ga karatun da suke Bayan dawowar Asmy daga Lectures Kallon Chuchu tayi ta ce "Badai Zarah yauma bataje lectures ba" Wlhko kinganta nan tun shigowarta da safe tana shiga lectures safe ta fito tun 10 take wannan bacci duba kiga yanzu har 2:15 na tashetama tayi sallah taki tashi sai rabuwa nayi da ita"Karasawa gadon Asmy tayi ta ce "Na rasa dalilin baccin nan da ta tarka na uban meye " ta fad'a tana bubbugar Zarah da karfi dak'yal ta samu ta tashi tana hade fuska Asmy ta ce "Ke yanxu Zarah Dan iskanci saida kikaga karatunmu yaxo karshe zakisa shiririta ki tarki wani bacci Ki dinga kin attending lectures to wlh bazan yarda da haka ba "Sorry uwata nadaina" Zarah ta fad'a tana Mikewa tare da Yin y'ar mik'a tayi hanyar toilet Dan ta dauro alwala "Chuchu ce tadanyi murmushi ta ce " Ai dole tace maki Mama kam yanda kike bada command irin y'ar nan taki"wlh ba haka bane abun ne ya fara bani Haushi bacci bacci saikace kasa"Wlh ko nima abun har mamaki yakeban kamar wacce tse_tse fly ya cixa kokuma wata me ciki ta zauna tayi ta bacci ba control" Gaban Asmy ne ya bada daram jin Abunda Chuchu tace Dan bata tab'a sanin bacci Alamun ciki bane Zarah ma dake fitowa daga toilet saida gabanta ya fad'i saikuma taja tsaki a ranta ga ce "Ni mema zai had'ani da wani ciki Allah na tuba wata takwas bansamu ba sai yanxu" Ta k'arasa shigowa "Daidai lokacin da Asmy ke cewa Chuchu " Ke waya fad'a maki mai ciki tana yawan bacci nidai ban tab'a jiba"Nima a novels karanta wlh "ta fad'a tana y'ar Dariya " Tsaki Asmy taja tace keda kike karanta novels dinma har kika sani"Murmushi Chuchu tayi ta ce "Hmm ai wlh ina mamakinku da kikace wai baku karatun novels ai novels duniya ne musamman kika hadu da mai dadi duk wata damuwarki jinta zakiyi ta yaye novels yana yaye damuwa yanda baki tunani wlh Ga dadi jinki kike kamar kiyi tsuntsuwa ki koma duniyarsu" Dariya Asmy tayi ta ce "Haka dai kike cewa nikam gani nake bazan iya zaunawa na karanta ba gani nake bata lokaci ne kema Rashin aikinyi ne kawai" hmmmm bazaki gane bane Matar nan"To Ganar dani "Dariya chuchu tayi ta ce '" Ai tunda kince bazaki iya ba shikenan"a a yanzu dai Naji bani wani na karanta Page d'aya Naji yanda abun yake"okay bari na dubo maki *Ni da yaya Arman* da na karanta kwanaki tun lokacin da ake typing dinsa na saya littafin yayi dadi over yanda baki tunani anzuba zallar Soyayya a cikin book dinnan an zuba basira kede bari ki karanta saikin bani labari "okay ban page d'aya Na gani" Wayarta Chuchu ta bud'e ta shiga tare da mik'a mata "karanta Page d'aya ma kadai ki bani labari "Ansar wayar Asmy tayi ta fara karantawa Zarah dai na jinsu har ta gama salla girgiza kai tayi ta ce "Ana shirin exams kina shirin koya mata karatun Littafi" Dariya Chuchu tayi ta ce "Page d'aya ne fa zata karanta momcy kema ko zaki karanta" Girgiza.kai tayi ta ce "Bani da time d'in wannan Exams na gabatomu ina ni ina fara karatun Littafi " Asmy ita da zata karanta Page d'aya ai batasan ta zarce har page biyar ba saida Chuchu ta warce wayarta ta ce " Yadai naga kinjima bani wayata chat zanyi"Cikin doki asmy tace "wayyo ya zaki lasamun Zuma a baki kuma ki barni Dan Allah ki bani naci gaba please banso ko da second d'aya a wuceni" Dariya Chuchu ta kwashe da ita ta ce "Keda kikace bani da aikinyi ai bazaki cigaba page daya nace ki karanta" ai bansan haka abun yake ba shiyasa nace haka wlh book din tundaga fara karanta Page d'aya ya tafi da imani na tundaga farkon salon soyayyarsu ya burgeni ba k'aramar love za a zuba a book d'innan ba da na lura Dan Allah ki bani na ida please "Dariya Chuchu tayi tace bari dai na tura maki ba Dan halinki ba Ai baki fara komai chakwakiyar love sai nan gaba Ayra da Arman Ai duniya ne Bari dai karna baki labari ki karanta da kanki" Zarah ce ta ce "Ikon Allah to ga wayata nima turamun Idan mungama exams na samu na karanta"Duka ba haka za ayi ba ku bari zansaya muku complete document a wajen marubuciyar saina tura muku ta what's app wannan doc din free page ne kuma.lokacin da na karanta a paid grp dintane Kunga ba Tarawa zanyi ba " Cikin doki asmy ta ce "Nidai fara turamun wannan din Kafin taturo cmplt din wlh marubuciyar ta iya salon labari mai d'aukar hankali" Dariya Chuchu tayi ta ce "Kaji uwar azarzabi ki bari na saya muku mana " A a aban yarda ba please ni bani number marubuciyar ya sunanta na maza na saya kar a barni a baya"Dariya Chuchu ta dake ta ce "aifa inaga haka din zanyi chan ku karata rubuta mata number tayi ta ce " Kiyi save da Hajara L Sadeq ko miss hajo"girgiza kai Zarah tayi ta ce "Kinji uwar ujila nima bani numberta sanda Nasamu time naso karantawa saina tuntubeta" Itama Rubuta mata number tayi ta ce "Na tura miki free page din ta what's app" Okay Thnks daughter "Zarah ta fad'a sai yamma driver yazo daukarta suka wuce Gidan MD tana lissafin sauran lokacin da ya rage mata ya saketa kowa ya kama gabansa sosai ta maida hankalinta ga karatun ta dukda yawan baccin da take bai hanata raba dare tana karatu dukda MD baya barinta sakewa a dare saboda koda yaushe yana nanike ita itako ta rabu dashi ne kawai Dan tasan na bankwana ne yake nan da one months kowa ya kama gabansa da idonsa ma bazai ganta ba tsaye take tana soya awarar kwai a kitchen tunda taji karnin kwan taji zuciyarta na tashi Tun tana daurewa harta kasa da gudu ta fito tare da rugawa palour ta fad'a toilet a guje nan ta fara kwarara amai MD yana palour yana mamakin me ya sameta bai tashi ba ya bita haryaga Fitowarta tana maida numfashi " Sannu"ya furta a hankali ta gyad'a masa kai tare da bajewa kan kujera tana ci gaba da maida numfashi "Baki da lafiya ne" ya k'ara maimaitawa "Girgiza kai tayi tare da yatsine fuska ta ce.........✍🏿 *07026166536 domin magana da marubuciyar kai tsaye* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️..........*63 & 64* "Lafiya ta qalau kawai ina suyar kwan ne karninsa ya dinga tasomun ya tayar mun da zuciya shine ya sanyani amai" okay Sorrry yanzu kin kashe gas din"girgiza masa kai tayi ta ce "a a a bazan iya komawa kitchen din ba" Mikewa yayi ya ce "okay bari ni na kaso " Bayan ya kaso gas din ya dawo "Kallonta ya dingayi yanda ta baje a kujera tana maida numfashi idonta Rufe kamar mai bacci jin shiru ya sanyashi lekata yaga Kamar bacci take " Mamy"ya kira sunanta A hankali"jin shiru ya tabbatar masa da tayi bacci"shiru yayi yana tunanin sauyin da ya gani tattare da ita cikin satittikan nan "Karewa beauty face d'inta kallo ya dingayi samun kanshi yayi da shafa Fuskarta tare da lotsa hannunsa a dimple dinta d'aya daya lotsa dukda kasancewar bacci ta ke " Black beauty "ya fad'a a hankali" After one week Hafiz ya zo ganinta A sch suka had'u kasancewar lokacin sun fito daga lectures farinciki d'auke da fuskarsa ya ce "Kinga ko yanda kika k'ara kyau da fresh kuwa my Zarah ko har amfara dilkan Amarcin ne" Rufe fuska tayi ta ce "Kai ya Hafiz ana sch ina aka samu daman dilka kawai idonka ne ke gane maka haka fa" Serious fa nake maki magana wlh kin k'ara kyau da fresh da komai ma"Uhm"Kawai Zarah tace cike da jin kunya sai wajen Yamma ya tafi Tukwana ta koma hostel Dan yau bata da niyyar komawa gidan MD Dan yanzu Abunda yake mata ba dadinsa take jiba ita kanta har mamaki take da yanda takeson abun Amma yanzu kwata_kwata ko feeling ta dainaji"Tana shiga Chuchu kadai ta tarar kwantawa tayi kan gadon ba bacci take ba duniyar tunani ta Lula Wanda a kasheta bazatace ga tunanin da take ba a haka har Asmy ta shigo"saida ta daddabata tukwana ta dawo "harya tafi Hafiz din" Eh "ta bata amsa a takaice" okay kunyi maganar shirye shiryen bikin dashi"Girgiza kai Zarah tayi ta ce "a a a " to saboda me Abu na tahowa yanzu ai ya kamata a fara tsara abubuwan tunda Kinga damun koma wata gudane za a k'ara ba wani isashen time"ku shirya kawai ni bani da wani shiri da zanyi ta fad'a tana hade fuska"Ikon Allah Asmy ta fad'a kafin ta ce "hmm kede kika sani" Bata kula ta ba Zarah da dare tana jin Suna dahuwar indomie Bayan sun gama Chuchu ta ce "Ki sauko muci momcy wai ko baki da lafiya" Girgiza mata kai Zarah tayi ta ce "Na koshi ina Lafiya kawai ina danjin kasala ne shiyasa" Gaban Asmy ne ya bada daram Kallon Zarah tayi ta ce "Kasala kuma?gyada mata kai tayi tare da juya mata baya " Chuchu ta ce "Ki sauko muci Bafa kici komai ba" na k'oshi banajin yunwa "Zarah ta fad'a tare da kauda kai Dan k'amshin abincin baiyi mata ba yana neman tasar mata da zuciya Asmy saida taga Chuchu ta fita tana waya tukwana takamo hannun Zarah tare da cewa " Sis kina shan wannan maganin nan kuwa?wani magani ?Zarah ta tambayeta ?Wanda Dr Halima ta rubuta maki mana"Sai sannan Zarah ta tuno ma da maganar cewa tayi "ohhh eh ina shansa ya akayi" Ajiyar zuciya Asmy ta sauke ta ce "Daman ina son fita kokontone tsoro nake Kar Aje ciki gareki naga duk kin sauya kwanannan" tsaki Zarah taja ta ce "Ke baki da hankalina wlh mai ciki kama da wa yake mema zai had'ani da ciki Bayan watan nan ma.Saida nayi perioud gashi ina shan magani kuma ma shida ba haihuwa yake ba karma ki damu kanki ba wani ciki da garan kawai ina tunanin Maleria ce Ke damuna" Ajiyar zuciya Asmy ta sauke ta ce "To gobe muje asibiti mana a gwada ki ko na cire zargin kokwantan da nake a raina" Ba Inda zani ni lafiya ta qalau please karki sake mun maganar nan marar ma'ana Asmy "washegari Bayan fitowarsu daga lecture driver yazo ya d'auketa koda ta isa bata samesa a gidan Ba dak'yal ta samu tayi sallah ta kwanta Dan wata gajiya a tattare da ita A sallayar da tayi salla a palour ta kwanta bacci ya d'auketa sai wajen 5pm MD ya shigo gidan dawowarsa daga kd kenan karewa d'akin kallo yayi tare da kallonta yanda ta dukunkune a kan prayer mat tana bacci harya k'arasa shigowa palourn yana mamakin baccin nan da ta tarka da sauyawar da tayi cikin satittikan nan ga wani fresh da take dukda MD baisan alamomin masu ciki ba Amma kawai zuciyarsa saita tsarga masa ko ciki gareta saurin barin tunanin nan yayi sanin irin magungunan da ta dinga d'irka tsawon watanni zaiyi wahala ta samu ciki a y'an shekarun nan ma Inma basu mata illa ba a nashi tunanin " a hankali ya shiga Kiran sunanta saida ya daddabata tukwana ta tashi tana murza ido harta gama wartsakewa kallonta MD yayi ya ce "Me yasa kike baccin yamma kinsan bakyau" Muryarta mai kama da ta mai bacci ta ce "Nima bansan ya d'auke ni ba ko har anyi la'ar ne" Tun dazu yanzu har 5 "Firgit Zarah ta mik'e ta ce " subhanalla tun fa 2 na kwanta har 5 banyi salla ba "Cikin Sauri ta wuce toilet din palourn Dan ta dauro alwala harta gama salla MD yana tunanin wani abu a ranshi Bayan ta salamce fuskantarta yayi ya ce " Na tambayeki mana?Inajinka"ta fad'a a hankali"Yaushe rabonki da perioud"Shiru tayi kamar mai nazari kafin ta ce "two weeks " Kin tabbatar kuwa?Gyada masa kai tayi ta ce "Eh" okay "kawai ya fad'a tare da maida kansa ya jingina da Bayan cushion yana lumshe ido a ransa ya ce " To me yake damunta'"ya rage sati guda yarjejeniyarsu Ta k'are cikinsu babu Wanda baiyi sanyi ba Musamman Zarah da takejin wani iri a ranta Hakan yasa yanzu suka rage Rashin jituwa ita da shi Amma kuma idan ta tuna Ta kusa rabuwa da Kalular Auren nan da aka lak'a mata saitaji sanyi a ranta bangaren Hafiz Sosai ya shiga shirye shiryen biki ba kama hannun yaro bangaren Zarah ko ba wani shirin da take Dan tayi wani irin sanyi sanyin ta na da ya dawo harma ya fi na da Asmy sai mita take akan halin ko in kula da take nunawa a bikin yauma suna zaune a jikin wani block cikin b'acin rai Ta ce "Wai me kike nufi Zarah duk sanda na d'auko miki maganar hidimar biki saiki banzatar dani " Kauda kai Zarah tayi tare da kwantar da kanta bisa cinya ta ce "Asmy Kuyi komai da kikaga ya dace please kidainayimun zancen bikin nan" kama hab'a Asmy tayi ta ce"Lallai Zarah yanda nake tunani kin wuce nan kamarya nadaina yi miki zancen bikinki me kike nufi wai ki fito fili ki fadamun"Zarah batasan dalili ba kawai saiji tayi hawaye sun fara zubo mata Wanda in za a kasheta bazatace ga dalilin kukan ta ba "Saurin kama hannunta Asmy Tai ta ce " subhanalla meye haka wai zarah"Fad'awa jikinta Zarah tayi tare da fashewa da kukan da taso rikewa "sosai Asmy ta rude ta fara cewa " meye haka Zarah karki tayarmun da hankali daga magana sai kuka me aka miki karkija hankalin mutane su dawo Kanmu please "Kasa mata magana Zarah tayi sai kuka da take Chuchu ce data hangosu ta Iso gurin ganin yanda Zarah ta lafe jikin Asmy tana shashekar Kuka ya sanyata cewa " subhanalla me akayi mata Asmy "cike da damuwa Asmy ta ce " wlh ba komai daga fara zancen biki kawai tahau mun kuka"Ikon Allah to ko batason bikin ne?kamarya su shekara hud'u suna soyayya da mutum biki yazo tace bataso ai bata isa ba abunda bazaiyu bane bama tana so kilan wani abun ne"Dak'yal suka samu Suka lallab'ata suka wuce hostel Wanda suna shiga ta fad'a Gado tare da Kara fashewa da sabon kuka Kallon juna Asmy da Chuchu sukayi sannan suka Kalleta zaune sukayi suna Kallon ikon Allah ba irin Lallashin da basuyi mata ba Amma batayi shiru Ba Saida ta gama kukanta mai isarta kafin ta Bari daka Kalleta kasan Tasha kuka Wayartaace dake hannun Asmy tayi ringing dubawa tayi taga Yusuf ne "D'auka tayi nan yake shaida mata driver ne yake jiran Zarah tun d'azu" okay gata nan "Asmy ta bashi amsa " dafa Zarah tayi da tayi shiru zuwa lokacin Chuchu na gefenta tana Lallashinta dukda basusan meya sanyata kuka ba Ta ce "Ki tashi driver na jiranki" banza tayi mata"saida ta maimaita ta ce "magana fa nake maki Zarah" tukwana ta tashi tare da Goge hawayenta cikin muryarta data fara dishashewa ta ce "Bani wayar to" Mik'a mata wayar Asmy tayi harta amsa saikuma ta riko hannunta ta ce "Ki fad'amun me yake damunki please Zarah baki da sirrin da zaki iya b'oyemun bai kamata ki boyemun wani abu meya ke damunki wai kwanannan"ba komai " ta fad'a tana goge sabon hawayen da ya zubo mata"Hmmm to wannan kukan da kike na meye"ba komai Kawai na tuno da Mamana ne da bansantaba shiyasa"ta fada tana Goge sabon hawayen daya zubo mata tayi saurin Mikewa tare da d'aukar wayarta ta ce "saida safe" saida tayi control d'in hawayen dake zarya a idanunta kafin ta fita amma kallo d'aya zakayi mata kasan tayi kuka shiru Chuchu tayi Jin Abunda Zarah ta ce saida tabar d'akin kafin ta kalli asmy da itama jikinta yayi sanyi ta ce "Me take nufi Asmy mamanta bata raye daman" eh tun wajen Haihuwarta ta rasu bata Santa ba ko a hoto saidai kawai anbamu labarin kamar yanda zarah take itama haka mahaifiyarta take banbancin ba kowa ne zai iya ganesaba hannun Matar uba ta tashi"hawaye harsun zubo a idon Chuchu ta ce "wayyo Allahsrk momcy gsky dole tayi kuka Rashin uwa ba k'aramun Abu bane kamarni Tun ina ciki bansan mahaifina ba Sai a hoto amma gwarani gaskiya akanta tunda ina da mahaifiya mancewa ma nake da rashin mahaifin da nayi saboda kallo biyu nakeyiwa yayana na uba da kuma na yaya shiya mayemun gurbin abba na amma Kuma wai ya kuke da ita ne dafa na d'auka gidanku d'aya saidaga banbanci sunan uban yasa nake tunanin ko cousin ne?Dan murmushi Asmy tayi ta ce " mubar maganar nan chuchu"Jin haka ya sanya Chuchu Jan bakinta tayi shiru karsuce tana musu shishigi Zarah ko kallo d'aya MD yayi mata yasan tayi kuka Saboda yanda idanunta sukayi ja ga kuma Rashin walwalarta data shigo da ita a hankali ya kirata da sunan da yake kiranta watau Mamy "Cikin sanyi ta d'ago ta Kallesa saita maida idanunta kasa " Baki da lafiya ne?Girgiza masa kai tayi"wani Abu akayi miki?nan ma girgiza kai tayi ,"To me ya sameki "kukan da ta dinga Rikewa ne tun a hanya ya Kufce mata batasan sanda ta fashe da sabon kuka ba " subhanalla ya fad'a tare da komawa Inda take ya kama hannunta ya ce "Me akayi miki" Shiru nan ma saici gaba da kukan da tayi "Janyota jikinshi MD yayi saboda a rayuwa ba abunda ya tsana sama da sauraran kuka kukanma na mace wannan yana d'aya daga cikin abunda Yasa ake ganin kamar Amera ke juya sa nan ko haka rayuwarsa take bayason ganin wani cikin damuwa musamman Wanda yake tare da su bare kuma Amera matarsa da suka zauna tsawon shekaru goma " shafa bayanta ya fara cikin sigar lallashi kamar wata baby Yana cikin Lallashinta Har yaji saukar numfashinta alamar tayi bacci Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya dinga kallonta yana nazarin meke damunta ya lura dai kamar akwai abunda ke damunta d'an karta tashi ya barta a jikinshi dukda yana buk'atar tashin Saida tayi baccinta ta gaji dukda a takure yake koda ta bud'e idanuwanta Kallon gefenta ta fara ya tabbatar mata da Cikin namiji take sai sannan tunaninta ya dawo mata cikin Sauri ta Zame jikinta a hankali daga nasa kallo d'aya tayi masa tayi kasa da kanta Tare da saurin Mikewa ta shige bedroom sallah kawai tayi danko yunwa bataji tarasa cikin kwanakin nan biyu abunda ke damunta ga tunanin mahaifiyarta da ya sanyata gaba sosai ta fara shiga kogin Dana sanin abunda ta aikata dukda tasan Asmy itace makasudin faruwar komai kwance tayi kan bed tare da lumshe ido kamar mai bacci Tana jin shigowarshi ta k'ara lumshe ido Zaunawa yayi gefen bed din tare da juye take away din d'aya sanya akayo musu a plate ya ce "taso kici abinci" Shiru tayi kamar mai bacci"Nasan kina jina kikamun banza ko Mamy"Kamar bazata tashi ba saikuma ta bud'e ido a hankali tare da mik'ewa ta tashi zaune tana jin kanta na ciwo kauda kai tayi bata bari sun had'a ido ba Plate din ya Aje gabanta tare da cewa"Ki juyo kici karya huce nasan ba abunda kikaci"a sanyaye ta ce "Na koshi?Baki isa ba sai kinci maza karki sake mun musu kinsan abunda bana so kenan"Sosai ta kwabe fuska kamar taga kashi haka ta fara cin abincin da ba dadinsa takeji ba Dak'yal tayi chokali shida ta Aje ta ce " na koshi"Kallonta ya dingayi yana Nazarinta a hankali "Ganin irin kallon da yake mata ya sanyata tsarguwa da kanta taki bari su hada ido" Kince kinyi perioud wannan watan? cike da kosawa ta gyad'a masa kai"shiru yayi kafin ya ce "Kishirya na kaiki Asibiti idanma Maleria ke damunki a baki magani" Kamar zatayi kuka ta ce "Ni wlh banason zuwa Asibitin lafiya ta qalau kaina ne kawai yake ciwo" Dage kafada MD yayi ya ce "Jikinki" yana gama fad'ar haka ya fita da harara ta bishi kafin taja tsaki kasa kasa tana tunanin tambayar da yayi mata sau biyu na perioud a ranta ta ce "Ko ina ruwansa da perioud dina "ba adau lokaci ba taga shigowarsa d'auke da ruwa a cup zaunawa yayi gefenta tare da b'allo parasitimol guda biyu ya ce " Anshi tana yamutsa fuska ta amsa Bayan ta amshi ruwan da ya mik'o mata saida ta rumtse ido kafin ta Had'iye saboda warin maganin da ya ke neman tayar mata da zuciya kakarin kamar zatayi amai yaga ta fara cikin Sauri ya d'aga pridge din d'akin ya fiddo fresh milk saurin budewa yayi tare da kafa mata a baki tana farasha taji ta dawo normal saida ta kusa Rabi kafin ta mai nuni da ta k'oshi janyewa yayi tare da kallonta ya ce"Ko bakiji dadi ba karki sha wani maganin da ya wuce wannan"Saboda me?Saboda haka nace maki"Shiru tayi tare da kwanciya ta juya masa baya"Ki tashi daga baccin nan na fad'a miki"Tana turo baki dukda baya ganinta ta ce "ba bacci ba zanyi" Da Dare tanaji MD ya fara yamutsarta ta fashe da kuka "Sosai MD yayi mamakin abunda bata tab'a masa ba kenan " Hakan yasa ya rabu da ita yana tunanin ko jikin nata ne dayan d'akin ya koma Zarah najin fitarsa ta sauke ajiyar Zuciya raba dare tayi tana salla Wanda yawaici duk adduarta akan mahaifiyarta ne Sosai take roka mata Rahama A wajen ubangiji saida taji bacci ya fara daukarta tukwana ta lallaba ta koma ta kwanta MD ko tunda ya koma ya kasa bacci yana tunanin sauyin yanayin yarinyar abunda bata tab'a masa yau tayi masa A ranshi ya ce "Kodai itama ta fara gajiya ne?To amma me yasa da Chan bata tab'a nuna Rashin So ga abunba sai yanzu" Karfa ciki ne da ita?kai gsky ba ciki bane saboda tace tayi perioud? Meke damunta ne?haka dai MD yayi ta sake sakensa "washegari Zarah duk yanda taso taje lectures MD ya hanata saboda yana tunanin bata da lafiya ita dai tasan lafiyarta qalau yanzu kam ba yanda ta iya ta hakura ta zauna saboda yanzu batasan yawan musu dashi tunda dai kowa ya kusa kama gabansa Ranar da ta cika wata Tara Cif da yarjejeniyarsu Aurensu Wanda MD mancewa ma da lokacin yayi Zarah ko tana sane sarai tunda safe Ta hada duk abunta da tasan nata ne a gidan ta sanya a akwati Kayan d'aya saya mata ta barsu a ciki Wanka kawai tayi hijab d'inta har k'asa bata shafa komai a fuskarta ba zallar ainahin Kyawun da Allah yayi mata ne bata samesa a palourn ba hakan ya tabbatar mata da yana ciki zaunawa tayi zaman jiransa ya fito ya furta mata Kalmar saki ko kuma ya bata takardar sakinta ko ta samu nutsuwa a cikin zuciyarta gashi Allah ya taimaketa kafin lokacin bikinta ta gama idda tayi minti sha biyar zaune kafin taji fitowarsa cikin shigarsa ta alfarma tunda ya shigo Palourn k'amshin turarenshi ya kauraye Duka ilahirin palourn lumshe ido Zarah tayi a ranta ta ce " Baya ragawa Turare"cikin Tafiyarsa ta izza ya Iso palourn "batare da ta Kallesa ba ta ce " Ina kwana"Morning muntashi lafiya"Steady"ta basa amsa a kad'aice "Kallon akwatin dake gefenta yayi ya ce " wannan fa "Cikin k'arfin hali ta ce " kaya na ne zankoma hostel "da izinin wa kuma saboda me?saboda Yarjejeniyar *Auren wata tara* yazo karshe yau wata Taran ya cika nasan kaima.kana lissafi ina jiran ka bani takardar saki na ne kafin na tafi"wani irin kallo MD yake binta dashi Wanda bazata iya fassara yanayin da yake ciki ba lokaci guda mood din fuskarsa ya sauya cikin dauriya ya ce"Kina nufin wata Tara ya cika da aurenmu?"Eh mana Ka lissafa mana ina tunanin ma harya so ya wuce" shiru MD yayi kafin ya d'ago ya ce"Bai cika ba ki koma Lokacin da ya cika zan sallameki da kaina?wani irin kallo Zarah ta dinga binshi dashi na ka rainamun wayau ta ce "Kamarya me kake nufi wlh ya cika kuma yau d'innan saika sakeni tunda ba a garin gab'a_gab'a muke ba " Dukda MD yayi mamakin jin furucin ta Wani murmushi ya saki da bazaka iya sanin na meye ba tare yin shiru ya lumshe ido cikin nutsuwa Hankali kwance"da karfi zuciyar Zarah ta dinga Bugawa bata San lokacin da ta fashe da kuka ba Ta ce "Wlh baka isa ba saika sakeni aiba haka mukayi daku ba,wannan ba adalci bane,kamar yanda a baya lokacin da naki Amincewa da Auren nan Abokinka yayi mana gori bada son raina ba harna amince yanzu kuma wata taran yayi kace bazaka sakeni ba wlh baku isa ba " ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka"Sosai take kuka kamar ranta zai fita MD jin kukan nata Yake har cikin ransa "Bar kukan indai kinason muyi magana ta fahimta" cikin Sauri Zarah ta bar kukan tare da Fara Goge hawayenta "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " Saki kike buk'ata ko?Gyada Masa kai tayi"Okay give me 2 minutes"ya fad'a tare da barin dakin ya shiga d'ayan ba ayi minti goma ba taga fitowarsa rik'e da takarda Yana linke ta dukda Zarah abunda take buk'ata a yanzu kenan saida gabanta ya fad'i k'arasa shigowa palourn yayi tare da makullin mota a hannunsa ya ce "Muje na saukeki" a sanyaye Zarah ta bisa parking space taga ya nufa ya fiddo mota nuni yayi mata da ta shiga Ciki ba musu ta shiga horn yayi mai gadi ya bud'e masa get tsit kakejin motar shiru bamai magana har suka isa cikin Makarantar daidai sanda yayi parking Dagowa yayi ya Kalleta daidai Shima ita d'in yake kallo Saurin kasa da kanta tayi "saida sukayi kusan 10 minute bame magana cikinsu kafin MD ya damko hannunta ya sanya mata takardar A hannunta Dagowa tayi tare da kallonsa ta kalli takardar hannunta da bai saki hannun ta ba har lokaci Bayan few minutes ta tsinkayi muryarsa da cew" Murna kike zamu rabu ko"Shiru Zarah tayi gabanta na fad'uwa "Murmushin da batasan ma anar sa ba taga ya sakar mata tare da sakin hannunta ya ce " Ina ne garinku?Shiru tayi saikuma ta ce"basaikaji ba"wani murmushin ya kuma saki ya ce "Bakison na halarci bikin naki kenan?Gyada masa kai tayi alamar eh"muga wayarki ya fad'a tare da amsa kwafar numberta yayi ya sanya a wayarsa Wanda duk bata lura da hakan ba kafin ya mik'a mata ya ce " Gashi Amarya sai wataran"Amsa tayi sosai tayi sanyi" Bud'e gaban motar tafi tare da fita a hankali harta fita MD baibar kallonta ba Itamadin so take ta Kallesa amma nauyi ya hanata Tanajin tashin motarsa ta juya ta dinga Kallon motar har ya bar wajen a sanyaye tayi hanyar hostel Asmy kadai ta samu a ciki tana ganinta ta taso tare da cewa "Ya sakeki dai ko?A sanyaye Zarah ta gyad'a mata kai" Alhmdllh "Asmy ta fad'a Tana shirin amsar takardar Zarah ta rik'e cikin rawar murya tace "bari na fara karantawa " Gabanta na fad'uwa ta warware takardar abunda ta gani ne a ciki ya kusan tarwatsa kwalwarta saida ta gama karantawa tsaf hannunta har karkarwa yake batasan sanda takardar ta zame kasa ba durk'ushewa a wajen Zarah tayi tare da fashewa da wani irin kuka mai cin rai kamar wacce aka aikowa sak'on mutuwa d'ora hannu aka tayi ta ce...✍ 07026166536 *JUMA'AT KAREEM* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_: 🤙🏿 🅿️.........*65 & 66* "na shiga ukku na lalace Asmy shikenan na bani na lalace na shiga ukku na " ta k'arasa fad'a a matuk'ar rude tana d'ora hannu biyu aka "a d'imauce Asmy ta Dauki takardar ta ce " me akayi Zarah"Da hannu ta nuna mata da ta karanta "kafin ta k'ara rushewa da wani kukan Bud'e takardar Asmy tayi gabanta na fad'uwa Ta fara Duba good handwriting dinsa da bai wuce layi shida ba fara karantawa tayi kamar haka" Ko a addinin Christian ba a Aure kan Aure bare addininmu na musulunci da ya haramta hakan Har yanzu har gobe da Aure na akanki basaina yi doguwar magana Ba nasan kina da Ilimi kinsan abunda yake fari da baki Ki rik'e mutuncinki na Matar Aure ban Aureki Dan in sakeki yanxu ba har sai na samu cikar buri na nima kamar yanda kika samu naki zan waiwayeki nan bada jimawa ba ina Kara tuna maki karki sake ki yarda ki bari a daura miki Aure da wani Bayan da igiyar Aure na a kanki bye ki huta lafiya black beauty " "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un" Asmy ta shiga maimaitawa tuni idanunta harsun cika da k'walla ta ce "Shikenan ya kashemu bake kika shiga ukku ba Nina shiga ukku Zarah Dana ja miki wannan Abun " ta fad'a itama tana fashewa da kukan sai ya zama.cikin su bamai Lallashin wani Asmy ce tayi dauriya ta mik'e cikin b'acin ran da tajima batayishi ba ta ce "Wlh basu isa ba Jirani naje gidan basu isa su maidamu y'an iska ba me suke nufi " ta fad'a tana wartar hijab d'inta ta fita Zarah ko sosai take kuka Tana Danasanin abunda suka aikata Tabbas sun tafka Babban kuskure da wauta yanzu yazatayi da rayuwarta?Bikinta da ya Hafiz fa ?Taya zai Aure ta Bayan da igiyar Auren wani a kanta?Taya zan iya yiwa Baba bayanin wannan Abun bak'inciki"da wani ido zan kalli mutane shikenan abunda nake gudun ya faru asirina zai tonu Baba banyi maka adalci ba naci amarka naci Amanar tarbiyar da yardar da ka ban....kuka ne yaci karfinta ta kasa k'arasa abunda take cewa a haka har Asmy ta dawo sai huci take "Kingansa?Zarah ta fad'a cikin muryar kuka" Ina fa gidan kulle da kwado ko get man babu "Innalillahi Mutumin nan ya cuceni ya gama da rayuwata Allah ya isa tsakani na dashi" Zarah ta fad'a tana kuka Wayarta Asmy ta dauka tare da dannawa jaber kira yana d'auka bama gaisuwa cikin jaraba ta fara cewa"Daman haka kuke ,K'ananan mutane ne ku daman bamu sani ba ,to wlh kunyi Gina kun tarda ruwa wlh baku isa ba wlh"Jaber da baisan wainar da ake toyawa ba cewa yayi"nutsu kiyimun bayani Dan Allah ma'u me yake faruwa wai"Ai kafi kowa sanin abunda ya faru tunda abokinka ne abunda nakeson ka sani wlh baku isa ba saiya saketa ya zaku mayar damu y'an iska"Wlh bansan abunda yake faruwa ba please Ki daure kimun bayani"a takaice Asmy ta basa labarin takardar da MD ya ba Zarah"Cike da damuwa Jaber ya ce "Subhanallahi ya bloody zaiyi haka Bayan ga Yarjejeniyar da mukayi Kuyi hakuri abun mai sauki ne bari na je gidansa zamuyi magana insha Allahu ko yau ban kiraki ba gobe zankiraki" tsaki Asmy taja tare da katse kiran tana huci Lallashin Zarah ta fara ta ce "Kiyi hakuri sis Wlh basu isa ba abunda bazaiyu ma bane ki kwantar da hankalinki" taya zan kwantar da hankali na Asmy?in kwantar da hankali na fa kikace ?Dan ba ke kika shiga chakwakiyar da na shiga ba shine zakice na kwantar da hankalina ina ni ina kwanciyar hankali Bayan Ban sansa ba "Kuka ne ya k'ara cin karfinta hawayen Dana sani ne suka shiga zuboma Asmy Tabbas duk halin da Zarah ta shiga ita ce sila,Rashin hankali da wautar ta ne ya sanya ta jefa y'ar uwarta aminiya a cikin halin da ta sosai takejin rad'ad'i sa zafi a cikin zuciyarta. Kwance yake ya lumshe kamar mai bacci " Me yasa na kasa sakinta?Ya tambayi kansa "Saboda Baka samu cikar burinka ba na dalilin Aurenta da kayi?wata zuciyar ta basa amsa " Amma kana ganin kayi mata adalci kuwa?wata zuciyar ta k'ara tambayarsa "rumtse ido yayi yanajin zafi da rad'ad'i a cikin zuciyarsa dukda sanyin AC bai hanashi zufa ba zafi yake ji sosai a cikin zuciyarsa na tausayin yarinyar Tabbas na cutar da ita ?To ka saketa mana Indai kana Tausayin halin da zata shiga?Girgiza kai ya fara da karfi ya furta 'I can't bazan iya ba bazan iya sakin ta ba ?saboda me tunda ba sonta kake ba hasalima Auren Yarjejeniya ne kukayi da ita "buga kanshi yayi sosai da hannu idanunta tuni sun sauya kala ga wani irin ciwo da sarawa da kansa yake a rayuwarsa bayason ya cuci wani,baya k'aunar ganin wani cikin damuwa ko wani hali,bare shi ya zama silar shigar wata cikin wani hali yasan shi da kanshi ya zalinci yarinyar muddin bai saketa ba " biro ya d'auko da ta k'ara Yafi sau goma yana son rubutawa amma ya kasa wurgar da biro din yayi Daren ranar MD ya koma kamar wani Mahaukaci bacci ko barawo baiyi shi ba Bangaren su Zarah ma haka ta kasance Dan bacci ko barawo batayishi ba ita da asmy musamman Asmy da take ganin itace duka silar faruwar hakan Inda Allah ya taimakesu ma Chuchu ta tafi weekend Kd bare ta fahimci halin da suke ciki Zarah ko yini daya harta rame sosai ta shiga Jerawa MD Allah ya isa na yaudararta da sukayi "Kasancewar Sunday basa lectures yasa sukayi zaune a d'akin kamar Wad'anda akayiwa mutuwa sunyi jugum zarah na hawaye rungomo Zarah Asmy tayi tare da Fara Lallashinta ta ce " Dan Allah kiyi bacci zazzabi na neman rufeki?ta fad'a tana tab'a jikinta shiru Zarah tayi bata bata amsa ba haka hawaye basu bar zuba daga idanunta ba Dak'yal Asmy ta dinga Lallashin Zarah a jikinta ta samu har bacci ya d'auketa Ajiyar zuciya ta sauke tanajin ba dadi a ranta da ta zama silar shiga damuwar aminiyartata ita kanta idan ta tuna abunda suka aikata a baya saitaji abun kamar a mafarki ko a almara bata tabajin anyi abunda suka yi ba...Wajen 10 Jabir ya isa gidan MD Saida ya jirasa kafin yaga fitowarsa kallo d'aya yayi masa yasan akwai abunda ke samunsa kafinma.su gaisa jaber ya ce "Abunda kayi ka kyauta MD ,me yasa kak'i sakin yarinyar nan bakasan hakan babbar barazana bace a rayuwarta ,me yasa zakayi mana haka ," tsaki MD yaja duk haushin kowama yaji yanayi ya ce "sau nawa zance babu ruwanka a maganar nan?da ruwana waya hadaka da ita?Waye jadalin Auren shine yanzu zakace babu ruwana to da ruwa na wlh baka isa ba zuwan nan da nayi bazan fita ba saida takardar Zarah Ai abun ba hauka bane yarinyar da ka dinga cewa an lakaba ma dalilin me yasa bazaka saketa ba?Cikin daga murya ya ce " ya isa Haka jaber kai ba uba na bane da zakazo kanamun fad'a akan Abunda ya shafi rayuwata saki ne bazan sake ta ba shikenan final magana karka k'ara zomun da maganar nan Aure dai a kaina yake ba akan kowaba Dan haka bazan sake ba please Karka k'aramun Damuwa"mamaki cike da fuskar jaber ya ce "Ni kake fad'awa haka MD " tsaki yaja tare da kauda kai"Murmushi mai ciwo jaber yayi ya ce "Laifina ne duk wannan nagode" yana gama fad'ar hakan ya tashi fuuuu yabar gidan rai bace sai Bayan fitar Jaber MD yaji baiji dadin abunda yayi masa ba abunda basu tab'a samu da abokin nasa ba Kuma yasan fushi yayi "amma ai shi yaja " ya fad'a yana dage kafada "Koda Asmy ta kira Jaber rasa amsar da zai bata yayi Yasan ba k'aramun zalinci sukayiwa yarinyar nan ba da wani ido zai kallesu " Tabbas MD yayi masa bazata bai tab'a tunanin zaiyi haka ba "Amma ai laifinka ne daka bashi wannan shawarar marar tushe da ma'ana shi kanshi jaber ba k'aramun Dana sanin wannan gurbatacciyar shawarar da ya bawa MD yayi ba yana ganin kiran Asmy yake kin d'aukar wayar karshe ma kashe wayarsa yayi Dan baisan abunda zaice musu ba Tashin hankalin da su Zarah suka shiga b'ata bakine cikin kwana biyu harta rame bacci ko Saidai barawo ita da Asmy saina rasa wanene yafi wani shiga tashin hankali koda Chuchu ta dawo weekend ta samesu kallo d'aya tayi musu tasan suna cikin damuwa koda ta tambayesu meke damunsu cemata sukayi ba komai bata Kara tambayarsa ba saboda tasan da abunda Suke boye mata tun watanninan a ranta tace tunda basu d'auke ni d'aya ba Ai shikenan" Jarabawar su Zarah tazo Wanda Dak'yal ta maida hankalinta ta fara rubuta jarabawar Wanda Rabi damuwa tayi mata yawa ta rasa abunda ke mata dadi a haka dai Har suka gama jarabawa Hafiz ko tun a waya ya lura da bata cikin walwala koda ya tambayeta ce masa tayi ba komai a haka dai har suka kammala Jarabawarsu Ta final ranar da suka gama kowa na farinciki zai koma gida Angama school banda zarah da hankalinta baya jikinta yaune ranar graduation dinsu na gama makaranta bata cikin walwala ko Kad'an gidansu Asmy sunzo Inda akayi bikin gamawarsu sch ana ta hotuna ko hoto daya Zarah batayi ba ko kawayenta sun janyota Zamewa take tana zaune sanye da rigarsu ta graduation da ankon material din da sukayi tana tunanin data saba Chuchu tazo tare da kama hannunta tace taho muje tun d'azu nake nemanki zaku gaisa da Ammy a kujerar manyan baki da aka karrama suka iske Ammy sanye cikin shiga ta manya ta alfarma ta manyan mutane idanunta sanye da farin medical glass tana ganin Zarah ta sakar mata murmushi kujerar kusa da Ammy Chuchu ta zaunar da Zarah ta ce "Ammy ga takwarar taki" Kama hannun Zarah Ammy tayi ta ce "Sannu ko takwara " A sanyaye Zarah tayi kasa da kanta ta ce "Ina yini Ammy anzo lafiya" lafiya qalau daughter congratulations ko Angama karatu lafiya Allah ya sanya alkhairi yasa mai amfani ne "Ameen Ammy ngd" ta fad'a a hankali sosai Ammy takeson Zarah har cikin ranta saboda nutsuwarta "Sosai ta dinga janta da hira Wanda Zarah duk nonnokewa take saboda ta rasa dalilin da yasa takejin kunyar Matar chuchu ce ta ce " Ammy amarya ce fa Bikinta za ayi Dasun koma gida nasandai zaki barni nayi sati a Chan"cikin fara a Ammy tace" Kai kai ashe amarya ce y'ar tawa to Allah ya sanya alkhairi ya bada zaman lafiya insha Allahu ai ko nima zan halarci bikin da yardar Allah "cike da jin kunya Zarah tayi kasa da kanta gabanta na fad'uwa tuno mata da bikin da akayi " Dariya Chuchu tayi ta ce "Ammy kunyarki takeji fa" hararar wasa Zarah tayi mata Ammy ta ce "wai takwara ai ko da baki kyauta mun ba keda ya kamata ki saki jiki dani ai munriga munzama d'aya Kinga zoma ki mana hoto a wayarki" Ammy ta fad'a tana kamo hannun Chuchu"sosai Chuchu tayiwa Ammy da Zarah hotuna masu kyau kamar y'a da uwa mutane sai kallonsu suke suna gulmar ko me ya had'a Zarah da uwar MD Wanda suka San chuchu saisuce dayake kawarta ce shysa Bayan Chuchu ta gama musu hotunan wata kawarsu taba wayar ta d'aukesu su Ukku sosai aka musu hotuna masu kyau kafin Ammy tace ta gaji zata tafi "Bayan Angama duk abunda ya kamata Inda aka shiga karrama dalibai Wanda Zarah tana d'aya daga cikin daliban da aka karrama sosai bikin yaye daliban yayi kyau fiye da tunanin mai karatu Lokacin da Ammy zata tafi s s d'inta mace a bayanta tana take mata baya Chuchu da asmy da Zarah ko sosai suka Rungume juna suna kukan rabuwa Dan ba k'aramun sabo sukayi ba " Ammy ce tace "ikon Allah to ku ya haka saikace Wanda zasuyi nesa da juna to tunda bakusan rabuwa ni ku taho mutafi daman neman y'an mata nake Kunga saikuje Chan a cigaba da kawancen" Maman su asmy ce da tin dazu suka gaisa da ita ta ce "Gaskiya kam Hajiya Saisu runkuta su tafi" Dak'yal suka rabu sunajin ba dadi a ransu Danma sunyiwa juna Alk'awarin ziyartar juna a kai a kai a mota Chuchu ta lafe jikin Ammy tana turo baki ta ce "Ammy nayi fushi da yaya ranar graduation dina guda amma yak'i zuwa" Shafa kanta Ammy tayi ta ce "Kiyiwa Yayanki uzuri Maryam kwanakin nan ni kaina bana gane masa ya zama wani iri ina tsammanin tunanin Abunda Hajiya ta fad'a ne yasan tana gab da zuwa shiya sanyashi cikin damuwa in banda abun babana meye abun damuwa a Aure Kuma Aurenma zab'i aka baka na rasa abunda ke damunsa akan yarinyar nan Amera bana gane masa yanzu haka tafi wata biyu bata k'asar shi yana nan a haka wai zaman Aure ne fisabilillah dandai karkayi magana ace kaima kana da y'ay'a mata saita zauna ta dinga abunda take so "ai Ammy wlh laifinki ne tsorantafa yakeji idan kika tilasta kika nuna masa b'acin ranki ba dole yayi Auren ba karkiji irin yanda nakeji idan na tuna da yaya wlh Rashin mata ta gari babbar illa ne ta Riga ta lalata rayuwar Dan uwana ni kad'ai nasan irin zafin da nakeji a raina yaya baiyi dacen Aure ba ammy" murmushin da yafi kuka ciwo Ammy tayi ta ce "Ni kadai nasan irin yanda nakeji a cikin Raina Maryam nidin uwa ce Addu'a kawai zan Kara dagewa da masa Dukda kullum cikin masa nake kema ki raya Yayanki da addua".... A sanyaye Zarah ta shiga cikin gidansu Ajiyar zuciya ta sauke ganin ba Mama Rabi tsakar gidan Sai Baba yanajin radio cikin farinciki da murna Baba ya tari y'ar tasa ba irin albarka da bai sanya mata ba. Sosai ya nuna mata jin dadinsa na kammaluwar karatun nata lafiya sannan ya bata hakuri akan Rashin halartarsa wajen " Murmushi tayi ta ce "Bakomai Baba wannan Karin Mama Rabi batayi alkaba'in da take yiwa Zarah ba saboda ganin Baba a takaice ta amsa gaisuwar da tayi mata Bayan Fitowarta daga d'akin Bayan Zarah ta huta Tayi wanka da dare Baba ya sanya aka kirawota Bayan ta zauna kallonta yayi ya ce " Zarah yau zan baki wasiyar da mahaifiyarki ta bani dukda na fad'a maki na adana maki ne har zuwa lokacin da ta wa'adanta watau lokacin Aurenki Alhmdllh yanzu ne lokacin da ya kamata na baki"Ya fad'a yana mik'a mata Awarwaron da zobanyar da ya sanya cikin k'aramun box hawaye ne suka zubowa Zarah tare da amsa sosai taji k'aunar awarwaron da zoben kuma tayiwa kanta alk'awarin kula dasu kamar ranta "Allah ya jikan mahaifiyarki yasa tana cikin Rahama " Ameen Baba"Zarah ta fad'a kafin ta ce"D'an Allah Baba kana da hoton Mamana ko d'aya ne?Yanajin tausayinta a ransa ya ce"Banda hoton mahaifiyarki Zarah ni kaina Inajin Haushi Rashin hotonta da bani dashi a lokacin bamu damu da hoto ba Tunda muka hadu da ita batayi wani hoto ba Saidai nakanji dadi idan na kalleki ked'in hoton ta ce Zarah idan kinason Kallon fuskar mahaifiyarki to ki kalli kanki ita zaki gani wani gamin idan ina kallonki sainaji kamar mahaifiyarki nake kallo saboda har zubin jikinki ba banbanci da nata sannan a lokacin ma da ta rasu Bazata wuce shekarunki ba kamar yanda kike d'innan har abun nan na gefen bakinki da suka lotsa (Dimples) ita ma haka suke banbanci nata d'aya ne ke kuma Duka biyun ni kaina nakanyi mamakin tsananin kamarki da mahaifiyarki ta baci zarah "Dan murmushi Zarah tayi sosai takanji dadi idan akace tana kama da mahaifiyarta sosai takejin dadi idan Baba na bata labarin mamanta cewa tayi " Baba Itama tana da hakuri ko?Murmushi Baba yayi ya ce "Hakurinta ya ninka naki Zarah kinsan dai rayuwa Ana cewa zomu zauna zomu saba ko ?To bantaba samun sabani da mahaifiyarki ba b'ata tab'a fushi dani ba ,bata tab'a yimun gardama ko musu ko kuma na fad'a magana ta mayar ba bamu tab'a fada ko na dak'ik'a d'aya da mahaifiyarki harta rasu shiyasa har kullum bazan tab'a mantawaba da mahaifiyarki ba Bantaba salla biyar ba ban roka mata Rahama wajen ubangiji ba Zarah y'ar aljanna ce ,tayi mutuwar shahada sannan ta rabu da mijinta lafiya ta rabu da mak'wafta da duk Wanda tayi mu'amula dasu lafiya Wanda nake da tabbacin iyayenta ma lafiya ta rabu dasu mutuwar mahaifiyarki ba mata ba hatta maza da idanunsu suka dinga kuka unguwar nan babu Wanda baiji mutuwar mahaifiyarki ba Allahsa ta huta"" Ameeen Baba "Ina son kiyi hakuri a gidan mijinki kamar yanda mahaifiyarki tayi zakici ribar zaman duniya Zarah har ko yaushe na kanyi alfahari dake matsayin kyautar da Allah yayi mun Na mallakamun ke a matsayin y'a ked'in y'a ce da kowani uba zaiyi alfaharin da kasancewarki y'a a gareshi Allah yayi miki albarka,Allah yayi miki albarka, Allah yayi miki Albarka Sannan ina son na sanar dake mun tsaida Ranar Aurenki da yaron nan d'an mutunci Hafiz Sati Ukku masu zuwa" Wata irin faduwa gaban Zarah yayi Jin an tsaida Aurenta Da Hafiz sati Ukku Bayan da Auren wani a kanta"kanta yayi wata irin sarawa Wanda ta kasa control d'in kanta a matuk'ar rude ta d'ago ta kalli Baba dake mata kallon mamaki ta ce.........✍🏿 07026166536 domin magana da marubuciyar kai tsaye *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️.........*67 & 68* "Sati Ukku fa baba"ta fada idonta na cikowa da k'walla " eh sati Ukku muka tsaida saboda shekara hud'u ba wasa ba munriga munshirya komai na biki da kayan daki tuni na tanada komai Saidai jiran rana Kina da matsala ne da hakan"Goge hawayen tayi ta ce"a a a Baba naga yayi kusa ne"Murmushin dattaku Baba yayi ya ce "baiyi kusa ba Zarah Iyayen yaron sun nuna yana son ne ayi abun wurwuri shiyasanya muka barshi a haka din " kasa tayi da kanta saida Baba ya k'ara mata nasihohi sosai kafin ya bata umarnin fita Zarah kamar jira take yace ta fita tana zuwa d'akinta tayi rubda ciki ta fashe da kuka Cikin kuka take cewa "Na shiga ukku ya zanyi da rayuwata taya ina musulmai zan yarda A daura mun Aure Bayan akwai Auren wani a kaina sannan ba idda ba komai ka cuceni Musty tsakanina dakai Sai Allah ya isa mugu azzalumi" Sosai take kuka Daren ranar bacci sai barawo ne ya d'auke ta washegari koda ta tashi da ciwon kai ta tashi saboda kukan da tasha Bayan tayi wanka d'akinta ta koma Dan yanzu kwata kwata zaman gidansu baya mata dadi Khairat ce Daman Suke Dan Hira da ita gashi itama Bata gidan bare Safiya yunwa takeji Amma tashin hankalin da take ciki tasa ta manta da abinci sosai ta Lula duniyar tunani "tana cikin wannan tunanin Asmy ta shigo saida ta daddabata tasan da zuwanta Firgit tayi ta mik'e tare da kallonta da Itamadin ita take kallo a sanyaye Asmy ta ce " Kinji Sati ukku aka sanya Aurenki da Hafiz yanzu nakeji wajen Mama"Naji"zarah ta fad'a kamar zata fashe da kuka "Tagumi Asmy tayi tare da lulawa duniyar tunani Wanda itama Zarah tagumin tayi Sunkai minti goma ba Wanda yayi magana kafin Asmy ta ce " nayi Danasanin *Auren wata taran* wannan da Akayi Zarah Bacci da idona jiya ya gagareni nasan duk ni na ja maki wannan tashin hankalin ji nake inama akaina wannan Abun ya faru bake ba Zarah akwai babbar matsala Bazaiyu ayi Auren nan ba muddin bai sakeki ba sannan koya sakeki dole saikinyi idda "murmushin da yafi kuka ciwo Zarah tayi Dan yanzu idanunta sun fara k'afewa da kukan ta ce " Hmmmm"Hawaye na sauka daga idon Asmy ta kamo hannunta ta ce "Dan Allah Zarah ki yafemun da nazama silar shigarki wannan hatsarin wlh tallahi da nasan haka zata faru da ko makamanciyar haka bazaiyu ba A lokacin sonki da tsoron rasaki ya sanya harna amince da Auren nan bansan abun nan zai zama Haka ba Zarah na cuceki naci Amanar.....rufe mata baki Zarah itama hawayen take ta ce " Kidaina cewa haka Asmy wlh ban rik'e ki da komai a zuciya ba na d'auki hakan a matsayin kaddarata kidaina cewa haka Wannan din ya zama sirri a tsakanin nidake karmu sake wani yaji labarin nan Asmy mun tafka Babban kuskure duk laifi na ne "Ba laifinki bane Zarah laifi nane yanzu menene mafita kwana nayi ina tunanin mafitar da zamu samu Amma kaina ya kulle" Bamuda mafitar da ta wuce Addua Komai ya Riga ya lalace Mafitarmu d'aya Allah shi kadai zamuyi ta roka Dan ba abunda yafi karfinsa shine kawai zai kawo mana mafita"cewar Zarah "wayarta ce tayi ringing kamar bazata dauka ba saita d'auka tana ganin Hafiz ne saida gabanta ya fad'i saida ta kusa gama ringing tukwana ta d'auka tana daidaita muryarta karya gane tana kuka " A sanyaye ta gaishesa ya amsa cikin so kauda tare da shaida mata yana k'ofar gidansu"ina zuwa"ta basa amsa tare da katse kiran kallon Asmy tayi ta ce "Hafiz ne yazo" Okay gyara fuskarki mu fita tare daman Mama tace mutaho tare saina wuce gida idan kin sallamesa kije gida Mama na nemanki"To"Zarah ta fad'a tare da mik'ewa saida ta wanko fuskarta kafin ta dawo ta sanya k'atuwar hijab d'inta Tare suka fita da Asmy Bayan Asmy ta gaishe da Hafiz tana shirin barin wajen ya ce "a a dawo babbar kawar Amarya ai wannan zuwan Naku ne ku biyu Naga Amaryar tawa bata shirya ba har yanzu gwara mu mu fara shirin karmu biya tata" murmushi Asmy tayi ta ce "Hakane kam" Zarah ko bata tanka ba saboda wani iri da take ji"Mota Hafiz ya shiga Ya d'auko invitation masu yawa mik'awa Asmy yayi ya ce "gashi Dan ku fara rabo da wuri" Saida Asmy ta wara idanu kafin tayi Dariya ta Ce"lallai ango wannan zumudi haka invitation da wuri to shikenan"murmushi yayi ya ce "Ai dole nayi zumudi kam Abun shekara hud'u ya rage sati Ukku ina zama ya ganni" hakane kam to Allah ga kaimu "Ameeen Sai Maganar event ko walima da kukeso Kuyi duk abunda kuke buk'ata ki rubuta gobe idan nazo saina amsa" To shikenan ranka ya dad'e"Asmy ta fad'a"Bayan barinta wajen sai sannan ya maida Kallonshi ga Zarah da tayi kasa da kanta cike da kulawa ya ce "Yadai my wife lfy?lafiya qlau ya Hafiz Ina kwana" Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Alhamdulilla an kammala sch lafiya ko to Allah ya taimaka jiya din naso zuwa wlh Wani kiran gaggawa ne akamun katsina shi ya hanani zuwa am sorry Kyautarki tana gida na mance da ita " murmushi ta kirkira ta ce "Ba komai Ai " Duk yanda Hafiz yake yiwa Zarah Hira kin sakin jiki tayi dashi Ganin hakan yasa ya tafi saita d'auka ko kunyarsa ce takeji Dan ya Santa akwai kunya Koda ta shiga gidansu Asmy Bayan ta gaishe da mamansu nan ta zaunar da ita ta fara bata magunguna Wanda tunda ta bata Zarah ta fahimci na meye ba ason ranta ba ta fara sha sai Dan batason yi mata musu Bayan nan ta d'ora tayi mata dilka ta amare sosai ita kanta tayi mamakin karuwar sanyin na Zarah Saita lak'anta hakan da Bikinta dake karasowa tundaga ranar kullum Zarah tana gidan su Asmy mamansu tana yi mata Dilka da magungunan gyara bangaren Mama Rabi ko Sosai Zarah tayi mamakin yanzu wani mutunci da take mata ba zagi ba komai har tana mata maganar shirye shiryen biki itama ta bata invitation tayi tata gayyatar ranar Zarah sossai mamaki ya cika ta Nan ta d'auko invitation din da chungum din da ya kawo mata daga baya ta bata tana mamakin wannan saukowar mutuncin na Mama Rabi na lokaci guda bangaren Baba ma sosai yayi mamakin yanda take nan nan da bikin kamar za ayi bikin diyarta a tunaninshi Zatayi bakin cikin kayan d'akin da akayiwa Zarah saiyaga itace mai cewa ma a k'ara wani abun ayi Abu na fita kunya sosai a ransa yaji dadin sauyawar tata har yana murnar kila yanxu ta sauya hali. Kallo d'aya zakayi masa ka lura yana cikin tsananin damuwa har wata rama yayi idonshi lumshe kamar mai bacci nanko tunani ne chunkushe a ransa Ya Lula duniyar tunani yaji wayarsa tayi ringing saida tagama ringing bai daga ba wani kiran ya k'ara shigowa kamar bazai duba ba saikuma ya janyo wayar a hankali tare da Kallon screen din wayar Ganin number Ammy ce ya sanyashi saurin picking a sanyaye ya gaishe ta ta amsa masa ba yabo ba fallasa tare da cewa "kana ina?Ina Abuja " Okay to kazo Hajiya na nemanka "yana kwance baisan lokacin ya Mike zaune ba a matuk'ar makance ya ce " Hajiya kuma Ammy tazo garin ne?Eh tazo tun jiya kuma tace kome kake karka wuce gobe bakazoba"Innalillahi wa inna ilaihiraji'un "ya shiga maimaitawa a cikin zuciyarsa Ammy bata jira amsarsaba ta kashe wayarsa dafe kansa dake tsananin sara masa yayi ya ce " Oh my god"Ya Hajiya takeso nayi da rayuwata ne Wai,dalilinta na shiga halin da nake ciki yanzu kuma ta k'ara zuwa ta k'ara jagula lissafi cikin Sauri ya lalubo number Amera ringing biyu ta d'auka "bai saurari abunda take cewa ba ya ce " kome kike kiyi gaggawar dawowa gida kafin nan kafin 12:na ranar gobe "Daga bangaren Amera ta ce " Subhanalla honey lafiya"Lafiya nadai fad'a maki ki baro k'asar nan "Saboda me honey wlh gobe ake fara bikin Chichilayo" MD ji yayi kamar ya shak'eta da wayar baisan lokacin da yace "uwar bikin chichilayo Dan Iskanci ina Miki maganar Serious zaki sakomun maganar wata tsinanniyar arniya ki zauna karkizo ki saurari abunda zai faru kishiyar da bakiso ita zaki tarar"Daga bangaren Amera wani irin bugawar zuciya taji batasan lokacin da ta fashe da kuka ba Ta ce " nashiga Ukku ni Sadiya me kake nufi honey bangane yaren naka ba "Tsaki yaja ya ce " ki sameni a Abuja gidana Dake life camp buzu quarters Hajiya tazo kuma kinfi kowa sanin zuwanta"yana gama fad'ar haka ya katse kiran yana jan tsaki Sosai yakejin haushin kansa da na kowama yanzu ta ina zan nemo yarinyar nan?ya tambayi kansa "lumshe ido yana tuno da Dadin yarinyar lokaci guda mood dinsa ya sauya dak'yal ya iya hada ruwan tea tare da matsa lemon tsami kusan goma Dan tun Bayan rabuwarsa da ita kullum saiya sha sa yake iya samun bacci ga tunaninta da yaki barin kwalwarsa daidai da second guda washegari tun karfe shida na safe MD yaji bugawar part din da yake tundaga bedroom dinsa yajiyo saboda wani irin knoking da ake da karfi jallabiyarsa ya zura tare da fitowa palourn yana bud'ewa yaci karo da Amera kallo d'aya yayi mata yasan a matuk'ar firgice take ga idanunta da sukayi ja jawur Fadowa jikinshi tayi tare da fashewa da wani irin kuka mai tsananin gaske sosai take kuka kamar ranta zai fita Wanda MD Jin kuka nata yake har cikin ransa sosai ya tausaya mata wannan nadaga cikin abunda yasa ake ganin kamar Amera ta gama dashi Bayason ganinta cikin wannan halin hakan yasa ko maganar Karin Aure bayaso Daddab'a bayanta yafara cikin sigar lallashi Dak'yal ya samu har suka k'arasa palourn Inda ya zaunar da ita Cikin kuka ta ce " Honey karkaga tashin hankalin Dana shiga ban iya bacci ba Jiya da Daren da ka kirani na tafi Airport Sai 1am jirginmu ya tashi dak'yal na iya kawo kaina nan honey mutuwa zanyi a kanka "Numfashi mai zafi MD ya fesar kafin ya d'ago ya Kalleta ya ce " kibar kukan nan bashi da amfani kalleni muyi magana ta fahimta "Cikin Sauri ta Goge hawayen tace ina sauraranka honey" Hajiya ce tazo kuma take nema na kinsan zancenta bai wuce na Rashin haihuwar da banayi akan na k'ara Aure to shine nake son mu samawa Kanmu mafita tun kafin Abu yazo yafi karfinmu kinsan halin Hajiya sarai"ya nemu ya biye mata maganar ta ta baya Dan karta k'ara shiga tashin hankali "Dukda haka saida hankalinta ya tashi cikin kuka ta ce " to yaya zamuyi Honey ina mafita Bansan yanda zamuyi da ita ba ni kaina na k'agara naga jini na Ina son haihuwar nan fiye da yanda baka zato honey Allah ne bai bani ba "ta k'arasa fad'a cikin kuka " cikin sigar lallashi ya ce "Akwai mafita" Firgit ta d'ago ta Kallesa ta ce "Wace mafita ce Honey" Zamu cewa Hajiya kina da ciki zamuje tare yanzu kiyi pretending din ciwo akwai maganin da zakisha Zai sanyaki amai Dan duk su tabbatar da abun kafin mu nemu mafita"cikin tsananin mamaki ta ce "Idanfa suka gane honey nan gaba Bayan munsan ba cikin garan ba" Ajiyar zuciyaya ya sauke yace kibarmun sauran abunda nakeson kiyi yanzu kenan kawai"Nauyayyar Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Shikenan honey zanyi hakan Allah yasama na samu cikin gasken kafin Su gane" Murmushi ya sakar mata ya ce "Ameeen My Merah" k'arfe 11am tayi musu a Palourn Ammy a lokacin kowa na palourn har Hajiya Har Aunty Zey da tazo Bayan an gaggaisa Amera ma wannan Karin cikin ladabi ta gaishe da su Hartana tambayar Zey ina su Mema Zey Ta ce "suna gidan kakarsu sunje mata yini" masha Allah na kwana biyu bangansu ba ai da sun yarda da sunyi mana Hutu muma"Murmushi zey tayi ta ce "Aikam dai" Chuchu ta k'asar ido take Hararar Amera a ranta ta ce "munafuka batayi mamakin yanda ta gaisa da zey ba saboda daman Chan ita Zey kamewa gareta har mutane suna cewa duk gidansu itace mai girman kai hakan yasa Amera ke shakkarta Dan tasan halinta ba shiga harkar mutane take ba Amma aka shiga tata akwai masifa " Ammy ce ta ce "Chuchu ki kawowa Amera abun Tabawa mana ga Alamun sunshawo hanya" Badan Chuchu ta so ba ta tashi tare da dauko mata juice ta koma Inda take tana Danna waya A cup Amera ta zuba ta fara sha tana cikin sha taji maganin da MD ya bata a mota ya taso mata cikin Sauri ta Aje cup din tare da yamutsa fuska "Ammy ce dake lura da ita ta ce " Lafiya dai ko?Tana yamutsa fuska tace "Naji Inajin amai....bata k'arasa fad'a ba Taji ya tunkaro mata da gudu ta Riga toilet din palourn nan ta fara kakarin amai harta samu ta danyi Kad'an Duka mutanen dake cikin palourn da Kallon mamaki suka bita Hajiya ta ce " Ikon Allah itafa wannan aman me take"Shiru MD yayi ya kyale ta "Har Amera ta fito daga toilet din tana Murmurdewa irin anji jikin nan cike da kulawa Ammy ta ce " Sannu yaushe kika fara irin haka?nafi sati biyu ina yi amma kwanannan yafi matsamun?kuma kunje Asibiti "?girgiza kai tayi ta ce " a a a Ammy bamuje ba"Hajiya ce ta ce "Kinji sakarkaru abunda ake nema shekara da shekaru ya samu shine zaku watsar kunjimun Sakarkarun yara kai kasan da haka shine baka sanar mana tun wuri ba " MD yasan sarai da shi Hajiya take ya kauda kai yana maida Kallonshi ga television "kaji da mugun halinka dai Hajiya ta fad'a tare da Kallon Amera ta ce " Sannu ko bari a kira likita ya duba ki "Murmushin jin dadi Amera tayi ta kwanta kan doguwar sopa tana maida numfashin karya Kallon Ammy Hajiya tayi ta ce " Fatima kirayo likita yazo ya duba yarinyar nan Allah sa abun alkhairi da muka jima muna jira ne ya samu"Murmushi Ammy tayi ta ce "To Hajiya " Nan Ammy ta kira Family Dr d'insu Akan tanason ganinshi zai duba patient "Har lokacin MD hankalinsa gabak'i baya ga y'an d'akin Har Dr yazo Wanda gaisawa kawai sukayi da MD ya shigo Inda Hajiya tayi masa bayanin gwajin da zaiwa Amera nan ya shiga gwadata Inda ya dauki jininta da awon fitsari yaje baima bar gidan ba ya tsaya a mota Bayan few minutes ya dawo rik'e da paper da murmushi a fuskarsa Hajiya na ganin haka ta washe baki ta ce " Kardai kace mun ciki ne Dr "Da fara a a fuskar Dr ya ce"Tana dauke da cikin Wata Biyu " Ai gudar da sukaji Hajiya ta rangadane ya kawo kowa ya maida hankalinta Wajenta "Alhmdll Alhmdllh Allah nagode maka ranar da nadade ina jira gashi tazo da raina da rayuwa kai amma yau rana ce da bazan tab'a mancewa da ita ba a rayuwa ashe da rabon zanga jinin Mustapha a rayuwa kai Allah na gode Maka " sosai Hajiya ta shiga sabbatunta na murna Ammy ma ita kadai tasan farincikin da ta shiga haka su Chuchu da Zey MD ta ido yayiwa Dr d'in jinjina Irin aikinsa yayi kyau murmushi dr yayi masa "Hajiya ce ta kalli MD da babu Alamun yayi farinciki da abunda aka fad'a ta ce " Ikon kaji mai mugun hali ayi maka wannan Babban Albishir da muka dad'e muna jira ka zauna haka sototo ko fara'a babu a fuskarka"Sai sannan MD ya kalli Hajiya Yana hade fuska ya ce "me kikeso nayi nagodewa Allah a cikin zuciya ta Bayan haka me zanyi kuma"tsaki Hajiya taja ta ce Wlh tunda nake rayuwa bantaba ga mutum mai irin bakin halinka ba shekara goma Kana neman haihuwa yanzu Allah ya kawo kaki nuna farincikinka ai nazata likitan dinnanma yau sai anyi mishi tukuici babba" Shiru MD yayi baice komai ba danshi hankalinshi ba anan yake ba "Ammy tayi mamakin yanda MD yayi da murmushi a fuskarta ta ce " Congratulations Baba na Allah ya rik'a"Ameen Ammy"ya fad'a ba walwala a fuskarsa "Zey ce ta ce " Congratulations yaya Gaskiya munyi murna wlh Allah ya raba lafiya"Murmushi itama ya sakar mata ya ce "Ameen sis" Cikin farinciki Chuchu ta ce "Congratulation yaya nayi farinciki Sosai wlh kaima zaka zama Daddy harna k'agara naga fitowar Babynka" Murmushi ya sakar mata Itama Mikewa yayi Ya ce "Ina zuwa Ammy " yana fita da Kallo Hajiya ta bisa tare da tab'e baki ta ce "Allah ya yaye maka wannan mugun Abu" nan fa Amera taga tarairayar wajen Hajiya da da bata kaunarta yanzu ita ce hada cewa me take so a girka mata Chuchu ma dukda basa shiri da Amera sosai taji dad'in samun cikin nata kuma ta tayata murna MD na fita suka had'u da Dr Jinjina masa yayi ya ce "Nagode Dr Dan Allah wannan din ya zama sirri tsakaninmu" Karka samu matsala ranka ya dad'e insha Allahu daga wajena bamaijin wannan maganar"Ajiyar zuciya Md ya sauke Bayan yayi de transfer 200k motarsa ya shiga tare da hade kansa da sitiyarin mota Jaber ne ya fad'o masa arai Tabbas dole ya neme sa dukda yasan har yanzu fushi yake dashi amma dole ya nemesa Dan shine kawai zai iya sama masa mafita dukda waccen mafitar tashi ita ta ruguza komai.. Yau tunda ta tashi takejin jikinta ba dadi ga wata irin kasala da takeji haka dai take daurewa amma ita kadai takejin yanda takeji ga bata iya cin abinci yanzu Kowa daka Kalleta saikagane ta zama so silent ga wani fari da kyau data Kara kowa sai ya lakanta hakan da dilkan amare ce da aka fara mata Sosai hankalinta yake tashe kasancewar Bikinta da Hafiz dake k'aratowa Dan yanzu idan bazata mance lissafin ba saura kwana goma ba wani shiri da take daga bangarenta Dan ko Anko bata fiddo ba haka rabon invitation daga ita har aminiyarta ta basa cikin walwala Musamman Asmy da har wata irin rama tayi Dan kullum da abunnan take kwana take tashi sai kowa ya lakanta hakan da rabuwa ce da zasuyi ya sanya sukayi sanyi yauma Zarah tana kwance Kanta keyi mata ciwo sosai Kamar zai tsage da gudu taji shigowar khairat tana cewa Aunty Zarah"Dukda ciwon kan da Zarah take bai hanata farincikin tarbar y'ar uwar tata ba Rungume juna sukayi Zarah ta ce "Badai har kunyi Hutu ba " Eh Aunty dawowata yanzu kenan bakiga ko unifoam ban cire ba ke na fara nema "Kama hannunta Zarah tayi ta ce " Gaskiya ne Autar Baba Ke boarding dinma amsarki tayi naga hada su kiba kikayi"Dariya tayi ta ce "Kai Aunty wlh ba dadi boarding din Bari naje na cire kaya akwai labari Allah ya taimakeni Ina nan za ayi bikin ki " Murmushi kawai Zarah ta mata tana barin d'akin ta koma ta kwanta koba komai taji dad'in zuwan khairat Dan ta samu Mai d'ebe mata kewa dukda Asmy kullum tana gidan ko kuma idan taje gidansu amma khairat ita har daki daya zasu iya kwana "ya rage saura sati d'aya biki aka kawo Lefe Sosai kowa ya yaba irin kokarin da Hafiz yayi kala hamsin ya zuba mata a akwati dangin babanta da makwafta sai yaba kayan suke Mama Rabi ma ko itace uwar zakalkalewa hada guda " A lokacin Zarah na kwance a gidan su Asmy Dan yau da zazzabi ta tashi Kiran Hafiz ne ya shigo wayarta Bayan ta d'auka ya ce "My love Kinga kaya sunyi maki dai ko ko a sauya sannan dinkunanki da zakisa da biki suna wajen tela katsina insha Allah gobe zasu Iso ina fatan suma zasuyi miki Dan na lura baki da shirin badawa shiyasa na bada maki"Banshiga gidan ba na Kalla ya Hafiz amma nasan sunyi Allah ya k'ara budi " Ai komai nayi maki ban fad'i ba Zarah kin chanchanci fiye da haka "Bayan sun gama wayar sosai Zarah ta fara hawayen tausayin kanta Hakika ta cutar da Hafiz ,ta yaudareshi,taci amanarsa ,batayi masa halacci ba yayi mata Rana tana shirin yi masa dare "dukda tasan ita kanta bada son ranta Hakan ya faru ba K'addarar ce ta zaba mata hakann taya zata iya fuskantar wani da wannan Maganar?Taya Kuma zata yarda A daura mata Aure kan Aure ?wannan wace irin kaddararriyar rayuwace ta tsinci kanta Batasan lokacin da hawaye masu d'umi suka shiga zubo mata ba Maman su Asmy ce ta shigo d'akin da take kwance kasancewar Asmy ta fita Sayayya kasuwa cike da kulawa ta ce "Taso Zarah ki daure kisha Maganin nan " Goge hawayenta tayi tare da mik'ewa zaune ta ce "To Mama" Girgiza kai Mama tayi ta ce "Yauma kukan ne kikayi ko Zarah?na rasa abunda yake damunki keda Asma'u tunda kuka dawo daga makarantar nan bana gane kanku idan tunanin rabuwa kuke ai baku rabu ba kuna tare Har abada Aure baya raba Abuta to na lura abun naku ma ya wuce yanda nake tunani" Shigowar Asmy d'akin ya sanya Mama kallonta tare da cewa "kema shigo" a sanyaye ta shigo d'akin duk ta rame itama zaunawa tayi gefen gadon dukansu sukayi kasa da kansu kamar wasu munafukai "Mama ta d'ora da cewa " Dan Allah ku saki jikinku ayi bikin nan cikin walwala Ke yanzu Asmy bake ce aminiyarta ba ko ita bata saki jiki ba aike yakamata ace kinzama kirjin biki kin jajirce a bikin kawarki amma sainaga kema din kamar kin fita solancewa sakarcine yanzu ina tsammanin ko rabon katin gayyata baku kaiwa kawayenku ba bacin Anko da baku raba ba wannan Asama kun lakanta hakan da kurewar lokaci To wlh nidai ina fad'a muku tun wuri ku nutsu kusan abunda kuke"a sanyaye Zarah ta ce "Insha Allah Mama" Asmy ma ta ce "Insha Allah Mama zamuyi rabon IV din Tunda da sauran time" Da dai yafiye muku maza ki Shanye ta fad'a tana mik'awa Zarah cup din da tunda taji warin abun taji zuciyarta na wani irin tashi tana kafawa a baki kurba d'aya tayi taji wani irin amai na tunkaromata a Guje ta tashi tare da rugawa tsakar gidan a makwararo ta durkushe nan ta fara sheka amai kamar zata amayar da y'ay'an cikinta daga Asmy har Mama biyota sukayi Inda suka sameta durkushe sai kwarara amai take kamar zata amayar da y'an cikinta.........✍ *Domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo Ce*_🤙🏿 🅿️.........*69 & 70* Da taimakon Asmy da mamansu ta gyara jikinta sosai ta d'an galabaita sannun kawai maman Asmy ke mata ta ce "Baki da lafiya daman?Gyada mata kai tayi ta ce " amma ba Sosai ba "Ikon Allah ai bamuga ta zama ba amarya ba lafiya maza shirya mu tafi Asibiti" A sanyaye ta ce "Mama Bafa wani Abu bane kaina ne kawai ke ciwo kuma nasha magani basai anje Asibiti ba " A a ban yarda ba shi kuma aman na meye ?rasa me zatace tayi ta ce "Wannan maganin ne Mama daman banason shansa shine kawai ya kawomun Tashin zuciya har nayi aman" to shikenan tunda kinki Aje asibitin Maganin nan kam dole ki dinga shansa saboda yafi kowanne amfani bazaki gane amfaninsa ba sai nan gaba "shiru tayi tana kasa da kanta Asmy da duk gabanta fad'uwa yake itafa zargin ciki takeyiwa Zarah Dan duk wasu alamomi na masu ciki take gani a tattare da ita tun a sch bare yanzu da suka dawo gida abun yayi gaba kama hannun Zarah tayi suka koma daki tare da rufe d'akin cike da damuwa Asmy ta ce " Zarah yaushe rabonki Da Perioud? saboda me kikamun wannan tambayar?saboda cire kokonta ki fad'amun Gaskiya "Ajiyar zuciya ta sauke ta ce " Rabon dai da nayi cikakken perioud wata Ukku idan yazo Kad'an yake zuwa kuma kwana daya ya tafi wata biyu baya nayi irin haka Wannan watan ne banyi ba ko kadan kuma naga lokacin ma da zanyi kamar ya wuce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Asmy ta shiga nanatawa ta ce " na shiga ukku Zarah Kardai ace ciki ne dake"a matuk'ar rude Zarah ta ce "Ciki kuma?Eh ciki ni duk alamomin masu ciki nake gani kamar tattare dake " dukda gabanta dake fad'uwa bai hanata Jan tsaki ba ta ce "Lallai baki da hankali Asmy me zai had'ani da ciki nikuwa Bayan nafada maki Watanni biyu baya nayi perioud kuma rabo na da Azzalumin mutumin nan wata Ukku taya kuma zan dauki ciki please kibar maganar nan kar tashin hankalin yayi mana yawa ga wancen bamu gama ba ki b'ullo wani"tagumi Asmy tayi ta ce " Zarah Bazan tabbatar ba har saimunje asibitin ki tashi muje a gwadaki idan akaga babu sannan ne hankalina zai kwanta Amma yanzu babu ni babu kwanciyar hankali"tsaki Zarah taja ta ce "Ba Inda zanje wlh Kuma ba wani ciki jikina Allah ya kiyaye Ya tsareni da Cikin azzalumin mutumin nan macuci ya cuce ni ya yaudare ni Allah ya isa tsakani na dashi " ta k'arasa fad'a hawaye na zuba daga idanunta "Naji ba ciki jikinki Zarah akwai matsala fa Auren nan na gabatowa na fara tunanin kawai mu fito mu fad'a Gaskiya bazai tab'a yiwa muna sane a daura Aure kan Aure ba" a matuk'ar firgice Zarah ta ce "Me kike nufi?ina nufin mu fuskanci su mama da maganar nan" wani banzan kallo na baki da hankali Zarah tayiwa Asmy tace "bantaba sanin baki da hankali ba sai yau taya kike tunanin zamu fuskanci iyayenmu da wannan Maganar hauka muke ,Sannan ya kike tunanin Baba zaiji Lamarin nan Duk wata yarda da Amincewa Baba ya Riga ya bani ya yarda dani 100% da wani ido zamu Kalleshi mu fad'a masa wannan Maganar cewa zanyi na Aurar da kaina kome ai bani da idon dazan iya Kallon Baba na fada masa wannan maganar" kuka ne ya kubce mata Inda ta had'a kai ta gwuiwa ta shiga rerewa gwanin ban tausayi.... Shiru jaber yayi kamar bazai magana ba saikuma ya Ce " A Gaskiya da nace Babu ruwana a sabgarnan bloody Saboda Gaskiya ba k'aramun b'atamun rai kayi ba last time anma ya wuce yanzu me.kake so ayi wannan hukuncin daka yanke nayiwa iyayen ka k'aryar Amera Nada ciki mai bullewa ce kuwa?Nima bansani ba Jaber na zab'i nayi hakan ne kawai saboda ragewa kaina damuwa ina cikin damuwar da bakowa zai fahimci yanda nakeji ba a cikin raina jaber kome nema yake ya jagulemun taya zan nemo yarinyar Chan ina tsananin buk'atarta a halin yanzu"Kaika bata komai tun farko MD me yasa baka sake ta ba tun farko data bukaci hakan da ka saketa da komai yazo da sauki sai mu samu wata manufar amma kin sakin nata da kayi k'alubale ne babba ta bangarenta ka cuceta sannan ta bangarenka kuma bangane abunda kake nufi nakin sakinta ba Yanzu haka Inaji ina gani saboda kai sai blocking din Asma'u nayi Bayan son yarinyar nake Har cikin raina ni kaina ka jazanun matsala wlh"duk yanda MD yake cikin damuwa Kuma yake neman shawarar jaber bai hanashi Jan tsaki ba ya ce "Mu koma magana me mahimmanci meye mafita kasan dai dakai aka k'ulla abunnan to dakai ya kamata a samu mafitar warware matsala" Ajiyar zuciya mai nauyi jaber ya sauke ya ce "Babu mafitar da ya wuce ka saketa" Bazan iya sakin ta ba"Ya fad'a kai tsaye "mamaki d'auke da fuskar Jaber ya ce " saboda me "Saboda ina tausayinta" Murmushi jaber yayi ya ce "Bloody kodai son yarinyar nan ka fara bamu sani ba " Tsaki MD yaja ya ce "kana da matsala Jaber nafada maka ina tausayin yarinyar ne ,na zalince ta farkon Haduwarmu ,sannan na zalince ta a karshen rabuwarmu dole ne na gyara mu'amula ta da ita karta rikeni a zuciyarta babu abunda nake bakin ciki a rayuwa kamar na mutu Da hakkin wani dole ne na nemi yarinyar nan Duk Inda take " numfashi jaber yaja yana ayyana yanayin abokin nasa Har wata rama yayi cewa yayi"Kasan garinsu ne"a a a "Tirk'ashi aiki ja" jaber ya fad'a kafin yace "To me zai hana na kira Asma'u a waya nasan zata d'auka saimu basu hakuri ka saketa ta Cikin wayar Inajin hakan zaifi sauki " wani irin kallo MD yayiwa jaber ya ce "so kake ayi ta maimaita maka magana d'aya To bazan sake ta ba " Ikon Allah to idan baka zaketa ba Me zaka mata ka saketa tayi Aurenta wannan shine adalci"tsaki MD yaja yana maida Kallonshi ga kofa ya rasa abunda yake masa dadi shiru Jabir yayi kafin ya d'ago ya ce "Muyi serious magana Dan Allah saboda me bazaka sake yarinyar nan ba kowa ya huta?Saboda ina zargin cikina a jikinta"ya basa amsa kai tsaye " wara idanu sosai jaber yayi ya ce "what ciki Kuma?Of course ciki?ya akayi kasan tana da ciki?Jabir ya tambayesa" Naga alamominsa ne tattare da ita a takaice yabawa jaber labarin sauyin daya dinga gani a Wajenta har aman da tayi"shiru Jabir yayi sosai ya Lula duniyar tunani kafin ya d'ago ya ce "Ana wata ga wata" Tabbas indai hakane akwai k'amshin Gaskiya to amma tun kafin ta tafi meyasa kak'i kaita Asibiti aka gwadata"naso hakan takiya nikuma banason in takurata hakan yasa na rabu da ita"Tabbas indai hakane ya zama.dole mu nemu garinsu sannan ya zama tilas a dakile Bikinta da nake tunanin ana gab dayi"a matuk'ar zabure MD yace "kana tunanin bikin ya kusa ne " Bama tunani bane confirm Bikinta yana kusa saboda bazan manta lokacin da muke waya da Asmy takan Cemun Bayan gama makarantar su bazai wuce da wata d'aya bikin Zarah ba "Sosai MD ya shiga sabon tashin hankalin da yafi Wanda yake ciki a matuk'ar firgice ya ce " Impossible bazaiyu ba wlh"Mikewa yayi kamar zai tashi sama tare da shiga d'akinshi yabar jaber a palour girgiza kai kawai jaber yayi ya Mike tare da fita daga gidan yana tunanin Yanayin abokin nasa Tabbas indai ba idonsa ne yayi masa karya ba kishi ne yake gani k'arara a idonsa a zuciyarsa ya ce "Ina zargin MD ya fara son yarinyar nan " amma Indai haka ne sonta MD yake Nayi al'ajabi babba Mutumin da bai tab'a fad'awa tarkon son mace ba Har y'ar president ta sosa bai amince mata ba manyan mata masu ji da kudi gayu,mulki,sarauta,y'ay'an manya masu fad'a aji a k'asar ,suna sonsa yana Disgasu amma lokaci guda ya fad'a soyayyar k'aramar yarinya kamar Zarah da ko fari na azo a gani bata dashi"saikuma wata zuciyar ta ce "Amma kuma ba mamaki saboda yarinyar tana da komai daza aso ta tana da sihirtaccen kyau Tako ina tacika ta had'u dukda ba fara bace sosai amma ta ninka wasu fararen kyau nesa ba kusa ba Tana da kyau ,sosai jaber ya dinga sake_sake a ransa ya saka wancen ya since wancen.....MD yana kwance Sosai yake jin wani irin zafi a cikin zuciyarsa rumtse idonsa yayi sosai da sukayi ja tsabar bacin rai " Tabbas dole na nemo ki duk Inda kike Mamy"ya fad'a a fili Wayarsace tayi ringing ganin Ammy ce ya sanyasa d'auka daga bangaren "Ammy ta ce " Kana ina Baba na wai kwana biyu rabonka da gida Tundaga ranar da akace Matarka Nada ciki baka Kara zuwa gidan nan ba me hakan ke nufi meke damunka wai watanninan na kasa gane maka kaida ya kamata kayi murna da farinciki kyautar da Allah yayi maka lokacin da bamuyi tsammani ba Amma kwata-kwata ka watsar Kamarma baka farinciki da samun cikin Amera "ba haka bane Ammy akwai Uzurrrukan da sukamun yawa ne a harkar kasuwanci na shiyasama amma kiyi hakuri anjima ina zuwa" hmmm harda uzurin dazai hanaka nuna farincikin babbar kyautar nan da Allah yayi maka"Numfashi ya fesar ya ce "Ba haka bane Ammy ina cikin tsananin farinciki da hakan kune bazaku kula da hakan ba " Hmm to Allah ya kyauta saikazo"to"Ammy ya fad'a Bayan gama wayar sosai ya Lula duniyar tunanin Zarah "ina take?ya tambayi kansa". Kwance take ta d'ora kanta saman cinyar Asmy Kallo d'aya zakayi mata kasan hankalinta a matuk'ar tashe yake Kahirat ce ta shigo gidan ta ce " Aunty Zarah Mama Habi(kanwar babanta)sunzo tace a kira mata ke ?Okay jira mu tafi tare "Zarah ta fad'a tana yunkurawa ta mik'e saboda bataji dad'i dauriya ce kawai take Kallon Asmy tayi ta ce " Natafi ba lalle na dawo ba gobe idan na samu lokaci na shigo"Gyada mata kai Asmy tayi da ita tamafi Zarah rama saboda ita kadai tasan yanda takeji ji take inama kome ya dawo baya ,ta gyara kuskuren data aikata ganin irin yanda Asmy ta tayar da hankalinta ya sanya Zarah ta manta da komai na itace silar shigarta wannan halin ta dauki hakan a matsayin kaddara da kuma wauta da k'uruciya sosai ita kanta take Danasanin sake ma mugun mutumin nan jiki da tayi Wanda a yanzu ba Wanda ta tsana takejin Haushi sama dashi koda suka isa gidansu Sosai ta iske y'an uwan babanta Na Batsari da Wanda suke Aure a wasu garuruwan duk sunzo kasancewar Baban Zarah yana da yayyu da kanne maza da mata sosai Cikin ladabi da jin kunya Zarah ta gaishe su a sanyaye "Mama Habi ta kamota ta ce " me yake damunki Zarah jibi yanda kika zama kallo d'aya nayi maki nasan bakya cikin kwanciyar hankali me yake damunki?Murmushi Zarah ta kirkira ta ce "Bakomai Mama " Hmmm kodai har yanzu Muguwar Matar nan tana musguna miki "Girgiza kai Zarah tayi ta ce Bakomai Mama " Hmmm ai duk mai hankali yasan ba cikin kwanciyar hankali kike ba Zarah tun farko laifin malam ne tun Bayan mutuwar mahaifiyar Yarinyar nan babu yanda banyi da shi ba akan ya bani ita na tafi da ita katsina mijina ba k'i ba zaiyi amma yak'i ya nuna shi yakeson ya Riki y'arsa baya son zamanta wajen kowa hakan yasa muka hakura muna sane da duk gallazawar da akewa yarinyar nan kawai in banda kar kayi magana ne ace ka fiya fad'a Shikenan yanzu dai komai yazo karshe tunda har Allah ya kawo lokaci zakiyi Aurenki ki huta yanzu fad'amun abubuwan da kike so "k'asa tayi da kanta muryarta na y'ar kakkarwa ta ce " bakomai Mama"ke d'ago ki kalleni nidin kamar uwa nake wajenki karkiji kunya ki fad'amun abunda kike so da choice d'inki na kayan d'akin"kamar zatayi kuka ta ce "Bakomai Mama" Ikon Allah to tashi kije"kamar jira take ta mik'e ta shiga D'akin wasu daga cikin y'an uwa sukayi Dariya sukace "Zarah kenan itadai ba ruwanta har yanzu kunya ce fa takeji" Mama Rabi ko tana d'aki ta cika tayi Fam jin Abunda Mama habi take cewa Daman Chan tasan ba wani jituwa suke ba Habiba ce dake gefe ta ce "Ni Mama wlh mamaki kike ban Wai me kike nufi da barin ayi Auren nan da zakiyi nidai wlh harga Allah ina bak'inciki da Hafiz d'innan da Zarah zata Aure Dan Babban gida ne babansa yana d'aya daga cikin manyan masu kud'in garin nan haba Mama taya za ayi yarinyar da Mukasan yarintarta da komai muka bata shekaru nesa ba kusa ba ace wai tazo ta rigamu Aure muna nan zaune ko gaisuwa babu Wanda yataba zuwa sannan kuma ace tayi Aure Inda zata huta haba Haba Mama ina tuno wannan bakin cikin ji nake kamar na hadiyi Zuciya" da hannu Mama Rabi tayi mata nuni tayi kasa kasa cikin k'asa da murya ta ce "A tunaninki haka zan zuba ido ayi Auren nan ina nan ina ganinku wacce ta tsonemun ido ta rigaku Aure Aurenma kuma gidan Hutu ai abunda bazaiyu bane kusa ido Kuyi kallo wasa na gaba Dole zan saki jiki ayi komai dani saboda idan Abu ya lalace kar a zarge ni kina gani dangin Malam ba wani kaunata suke ba so suke ayi tashin hankali Wanda ni ban shiryawa haka ba ... Zarah ko tana shiga daki ta zunduma duniyar tunani gani take abun kamar mafarki Bikinta da Hafiz Wanda inbanda wannan K'addarar ta afka da ba Wanda zai kaita farinciki amma Kuma yanzu Shine take fargabar Auren to wai yanzu haka zata zuba ido A daura mata Aure kan Aure batasan sanda wasu hawaye masu d'umi suka shiga zubo mata ba Cikin muryar kuka ta ce " Ya Allah ka kawomun mafita a cikin al'amarin nan kafi kowa sanin halin da nake ciki Kaine mai iko akan komai babu abunda ya gagari ikonka ya Allah Kakawo mafita ta yanda ban tsammaceta ba Allah na tuba Ka yafemun Ka cireni cikin kangin rayuwar nan nasan wannan din duk yana cikin jarabawa ta ne ya Allah ka sassautamun jarabowowin nan da suke bibiyata tun yarinta ka kuma bani ikon cinye su kuka ne yaci karfinta Sosai tashiga rera kuka Daren ranar Zarah raba dare tayi tana addu'ar Allah ya kawo mata mafita a cikin rayuwarta..... a halin yanzu y'an uwa da dangi na nesa da na kusa duk sunzo domin ayi kome dasu Maman Asmy ma sosai take taka muhimmiyar rawa a bikin nan da za ayi dangin Baban Zarah sai Godiya suke mata na jajircewa da tayi tamkar bikin y'arta za ayi Dan wani irin tsumi takeyiwa Zarah dukda kwana biyun nan ba lafiya gareta ba yauma da Hafiz yazo da dare dak'yal ta samu ta fita cike da damuwa ya ce "Wai Dan Allah me yake damunki ne my Zarah bana gane maki kwannanfa" Kasa tayi da kanta tana maida hawayen da suka zubo mata Dan karya gani kasancewar duhu ne cikin rawar murya ta ce "Bakomai kawai banajin dadi ne" subhanalla ankaiki asibitine"eh Maleria ce" ta basa amsa Dan karya ce saitaje asibiti Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Allah ya baki lfy please kidinga shan magani sosai yanda zaki warke da wuri saida biki ya matso Maleria zatayi mana cikas " Shiru tayi batace komai ba "Kamo hannunta yayi abunda bai tab'ayi ba cikin firgici ta d'ago ta Kallesa Duka hannun nata biyu ya rik'e yana kallonsu tare da murzawa cikin Sauri tayi saurin kwace hannunta ta kauda kai tana hade rai" Sai sannan Hafiz ya dawo cikin hayyacinshi ganin yanda ta had'e rai dukda duhu ne ya ce "Sorry" a sanyaye ta ce "Dare nayi" Okay Good Night dinkunan nan dai sunyi kyau ko?Gyada masa kai tayi dukda ko kallon d'inkin batayi ba saboda yanzu bata wannan take ba "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " Duk abunda kuke da buk'ata keda kawayenku kuyimun waya "Insha Allah " ta fada a sanyaye Bayan sunyi bankwana ta koma gida Nanma saida ta kafa sana'ar tata ta kuka tana jin bata kyautawa Hafiz ba a halin yanzu Zarah bata da wata mafita data wuce Ta Allah Shi kawai take jira yayi ikonsa akan Abun tasan ko giyar wake Tasha bata isa ta tunkari wani da wannan Maganar bare yanzu da biki ya rage saura kwana shida.... "Ammy ba haka bane kiyi hakuri Dan Allah"ya fad'a cikin ladabi"Bani ya kamata kaba hakuri ba Matarka da kayiwa laifi ita ya kamata kaba hakuri"laifi kuma Ammy to me nayi mata "Ohh tambaya ta ma kake me kayi mata Bayan banzatar da ita da kayi Tunda akace tana da ciki baka Kuma waiwayarta ba " Ba haka bane Ammy kumin uzuri please yanzu ina amerar take "Ta tafi Gidansu kasan halinta ba sake mana take ba washegari ta shirya ta ce " zata wuce gidansu Ta kwana biyu ta warke a chan'?"Niko ban hana ta ba nace Allah ya kiyaye nasan duk haushin abunda kayi mata ne yasa ta tafi"Zankirata Ammy ina Hajiya wai tunda na shigo ban ganta ba "Dazu ta fita Ta lek'a gidan Zainab ne " Okay Chuchu fa "bai rufe baki ba yaga shigowarta palourn hannunta rike da waya kai tsaye wajenshi ta nufa fuskar ta cike da fara'a ta ce " Lah yaya yaushe kazo ina yini"Alhmdllh Auta ya gidan"Lafiya qalau ta fad'a tana zaunawa gefenshi tare da cewa "Yaya kazo a Daidai tun safe na rasa shawarar Wanda zan nema bikin momcy ne ya taso za ayi Saturday d'innan ina son ne na tafi wednesday tun gobe ma naso na tafi wlh ammy ta hana wai sai wednesday to shine zanyi mata gudummawar jaka nakirata akan taturo mun hotonta na biki tace batayi ba gashi nafison nayi mata mai hoto to shine nake gani ko hoton waya zaiyi akwai hoton Dana tab'a mata a hostel kuma yayi clear sosai bari ka gani kaga idan zaiyi ayi dashi ko kuma Wanda muka tabayi tare Shima tayi kyau saikaga idan zaiyi a datse ni " ta fad'a tana nuna masa hotonta data tab'a mata da Abaya ta ce Kalli yaya Dan Allah kana ganin zaiyi "Amsar wayar yayi daidai idonshi yakai masa hotonta sanye cikin doguwar Riga Abaya ta yafa beil din rigar Dimple d'inta Duka sun lotsa sakamakon murmushin da tayi a hoton sosai hoton yayi masifar kyau Kallon mamaki ya dinga bin hoton dashi kafin ya d'ago ya kalli Chuchu da itama shidin take kallo ganin yanda ya rik'e wayar gam yana yiwa hoton wani irin kallon mai kama Dana mamaki maida Kallonshi yayi ga hoton Kara murza idonsa yayi Dan son tabbatarwa itadince kuwa koko gizau ne Tabbas ita ce " ya fad'a a ransa "Kafin ya sake Dagowa ya kalli Chuchu a karo na biyu ya ce.........✍🏿 07026166536 domin magana da marubuciyar kai tsaye *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️.........*71 & 72* "Daman ita ce momcy din taki?Gyada masa kai tayi ta ce " Eh ita ce Yaya"ita ce mai muryar nan kenan?Nanma sake gyada masa kai tayi"Maida Kallonshi yayi ga hoton yana mamakin kenan k'awar Chuchu ce da takeji dinnan da ita yayiwa haka sosai Abun yazo mai a bazata yanda bai tab'a kawowa a ranshi ba "Kallon Chuchu ya kumayi ya ce " sunan ta na Gaskiya"Zarah Yusuf yaya ko ka Santa ne Wai"Zarah Yusuf ya maimaita a ransa Tabbas ita d'ince "Kafin ya kalli Chuchu ya ce " ta ina zan Santa Bayan ba tab'a ganinta nayi ba "Eh yaya Amma kagani ko ta had'u sosai ko?Ba Laifi ya fad'a yana Mikewa " binshi tayi ta ce "Yaya ina zaka kuma Bayan baka bani shawarar abunda zanyi mata ba bakace hoton yayi asashi ba "duk yanda yayi miki kiyi amma karkiyi mai hoto ?,binshi tayi ganin ya nufin hanyar stairs ta ce " Yaya Saboda me nafison nayi mata me hoto"Saboda bazaiyi kyau ba da hoto please ki barni na huta "ya fad'a yana hayewa sama Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta koma palour gefen Ammy ta zauna tana d'ora kanta kafadarta ta ce " Ammy wai kinji yaya kar ayi me hoto ko ayi me sunan kawai"Amsar hoton Ammy tayi ta ce "Masha Allah hoton yayi kyau amma kiyi mata mai sunan kawai zaifi watak'ila batason saka hotontane kinsan y'ar tawa ustaziya ce " Murmushi Chuchu tayi sosai takejin dad'in yanda Ammy ke son kawar tata ta ce "To shikenan Ammy wai Kinga da yaya yaga hotonta wlh saida yayi ta Kalla Kinga yanda lokaci guda ya sauya kamar daman ya santa" Murmushi Ammy tayi ta ce "Yanzu ba wannan ba kiyi Sauri ki kira mai jakar kar lokaci ya k'ure " Mikewa tayi ta ce "Barima kawai na tafi da kaina na masa bayani Dan gobe nakeson su iso guda D'ari biyar ai sunyi ko Ammy,?" Ta fad'a tana yafa beil"Eh sunyi please ki dawo da wuri banda gudu da mota a titi"......MD tunda ya shiga d'akin ya rumtiya duniyar tunanin Zarah Bai tab'a tunanin Zarah zata kasance itace kawar Chuchu kuma ita ce mai Qiri'ar wannan data ki barin kwalwarsa "sosai yaji zuciyarsa ta k'ara chunkushewa a halin yanzu baya da buri da yake dashi fiye da na ganin yarinyar tunda suka rabu Baccin kirki baya iyayi batare da tunaninta a ransa Wanda shi kanshi har mamakin hakan yake amma sai ya lakanta hakan da tausayinta ne da yake A ransa ya ce Tabbas wannan babbar dama ce ta sameni da zanyi amfani da ita wajen Gano Address d'inta Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " wannan Karin da Chuchu zanyi amfani"Wayarsa ce tayi ringing Ganin Amera ce Ke kiran ya sanyashi picking baiyi mamakin kin masa maganar kin kulata da yayi kwana biyu Dan yasan indai tana gidansu bata da matsala bataki ya barta tayi wata a gida ba Bayan sun gama waya baice yaushe zata dawo ba haka batace masa zata dawo ba dukda tana son ganinshi. Yau Tuesday Zarah ta tashi da zazzabi kin fad'awa kowa tayi ciki harda Asmy ranar mai lalle tazo dak'yal ta daure akayi mata danma a gidan su Asmy akayi mata ba Mutane sosai sai wasu cousin sisters d'inta na wajen Baba da sukazo Akayi musu tare sosai K'unshin Zarah yayi masifar kyau sai sannan ta fito a Amaryar Washegari Laraba tunda Safe sukaje saloon dukda tana Kokarin nuna ba komai a fuskarta ana cikin yiwa Asmy Bayan Angama yiwa Zarah tana gefe wayarta ce tayi ringing dubawa tayi taga Chuchu ce "Bayan tayi picking daga bangaren Chuchu ta ce " yanzu zantaho sis ki turomun Address d'in gidan idan nazo Funtua wace unguwa zance"Sosai Zarah tayi kokari wajen daidaita Nutsuwarta ta ce "Jabiri Gidan Malam Yusuf Zakice " okay to gani nan insha Allah "Murmushin k'arfin hali Zarah tayi ta ce " Allah ya kawoku lafiya"Bayan sungama wayar angamawa Asmy gida suka wuce tare. K'aramar akwati chuchu ta zuba kayanta sai murna take yau zata hadu da su Zarah 50k Ammy Ta bata ta kai gudummawarta Dan tace bazata samu halarta ba Bayan ta fito Harabar parking space d'in gidan Driver ya saka mata akwatinta a boot MD ya fito fuska ba walwala "Karasawa Inda yataho tayi tana kamo hannunshi ta ce " yaya yanzu zan tafi daman kai nake nema "yana Kallon motar da zata tafi ya ce" Wani gari ne zaki?Funtua ne Yaya ka manta bikin momcy da na fad'a maka"yaushe ne d'aurin Auran Asabar ne " shine zaki tafi tun yau Dan azarbabi "kamar zatayi kuka ta ce " Dan Allah yaya karkace zaka hana wlh mune manyan kawaye idan banjeba tun yanzu sai yaushe"Dan tasan halinshi sarai sai yace zai hanata "Jim yayi kafin ya kalli driver ya ce " fito da kayanta Daga motar nan zankira Wanda zai kaita "Jaber ya dannawa kira Bayan ya d'auka ya ce " Bloody Dan Allah ba abunda kake yanzu"Daga bangaren jaber yace "bakomai ya akayi" Inba damuwa kazo gidanmu ina son ganinka"Okay gani nan zuwa kana gidan "Eh" Kallon Chuchu yayi ya ce "Koma ciki kafin yazo ya kaiki" To yaya "ta fad'a tare da Juyawa Dan ta lallab'ashi karyace bazata ba ba ayi 30 minutse ba Jaber ya Iso gidan a palourn sa na part dinsa dake gidan suka yada zango..shiru jaber yayi Bayan ya gama sauraren MD Dagowa yayi ya Kallesa ya ce " Allah ne ya kawo mana mafita cikin Sauk'i amma nayi mamakin yarinyar da iliminta da komai zata yarda a d'aura mata Aure kan Aure "Numfashi MD ya fesar ya ce " Ni kaina nayi mamakin ta dalilin sanin ilimin nata bazata yarda a d'aura auren ba Alhalin da igiyar Aure na akanta ya sanya harna rabu da ita kafin Allah ya kawo mana mafita amma kana gani komai na shirin jagulewa"Ai bazaiyu a daura Auren nan ba Tunda muka samu address d'inta ai mungama samun dama Dole ne za a fasa Auren nan "Cewar Jabir "nasan da hakan bazan tab'a yarda A tabka wannan Babban kuskuren ba Amma tayaya kake ganin zamu magance matsalar" Ka barmun komai a hannu na bloody yanzu ba zankai Chuchu garin ba Kuma zangano gidansu ai magana ta k'are"Numfashi mai zafi MD ya fesar ya ce "Allah fitar damu" Ameen bari naje na sauketa kawai kome kenan saina dawo "Gyada masa kai MD yayi yana lumshe ido kan Kujera Bayan tafiyar su Chuchu ya jima yana sake_sake a ransa gabak'i d'aya kanshi ma ya kulle akan Lamarin yarinyar nan lumshe ido yayi kafin ya bud'e ya ce " Allah yasa ta tabbata ciki ne da ita Ya rabbissamawati"ya fad'a yana daga hannu yana rokon Allah ji yayi duk duniya yanzu kuma ba abunda ayake da buk'ata irin yara sosai yaji soyayyar cikin dukda bai tabbarba shi kanshi da akwaishi ko babu Amma zuciyarsa tafi rinjaya masa Akan akwai cikin wayarsa ya lalubo daidai numberta da yayi save da "Mamy" ya dinga kallo kamar kullum sai yayi kamar zai Danna mata kira wata zuciyar ta hanesa Dan yasan har yanzu fushi take dashi lumshe ido yayi a hankali ya furta "Simple babe baki da hayaniya " Kara lumshe ido yayi tunowa da zazzak'ar qiri'arta Da har yanzu idan ya tuno yakanjita a tsakiyar kansa ya ce "Ashe kece mai zazzak'ar muryar nan" Juyar da kansa yayi gefe saikuma ya saki murmushi ya ce "Koya taji.lokacin da ta ga takardar nan" Samun kanshi yayi da tsananin Bukatarta a kusa dashi koba komai irin zaman da sukayi dukda na d'an lokaci ne yana yi masa dadi sosai dabi'un yarinyar da hallayarta yake burgeshi Kara juyi yayi kan kujerar ya bud'e idonsa ya ce "Ashe kece kika k'ara inganta rayuwar kanwata Tabbas baki chanchanci Rashin Kyautatawa daga gareni ba ,dole ne na gyara kuskuren da nayi a baya wata zuciyar tace masa " To idan fa Chuchu suka gane kayi mata haka ya zasuji"tsaki yaja ya ce "Ai ba Laifi na bane Laifin Jaber ne tun Farko daya kawo wannan muguwar shawarar " To me yasa ban Sake ta ba "Wata zuciyar ta basa amsa da " saboda kana tausayinta" "tausayi kamar ya " ya k'ara tambayar kansa "Tausayi irin na musulunci " idan kana tausayinta me yasa da yarjejeniyar auren ku ta kare kak'i sakinta ta auri wanda take sonsa yake sonta "Saboda ina son inganta rayuwarta" Shi wancen sani kayi da har bazai inganta rayuwarta ba "Suk shi daya yake maganganun nan da zuciyarsa "tsaki yaja tare da buga kansa da hannu da karfi ya ce "OH MY GOD" na zauna ina ta tunanin k'aramar yarinya zata chazamun kai ". Jaber yana sauke chuhu ya karema gidan kallo daga mata boot yayi ta fito da kayanta da kuma gudummawar jakunkunan da suke a wata k'atuwar leda zagayowa tayi Inda yake gaban mota bai fito ba ta ce " yaya Jaber Please ka fito ka taimakamun d'aukar akwatin nan wlh tayi nauyi "Harararta yayi ya ce " wannan Dan Abun ne bazaki iya d'auka ba Kice zasu kwana anan"Turo baki gaba tayi ta ce "Shiyasa banso Yaya yace kai zaka kaini ba wlh dan nasan kaima duk kusan halinku d'aya" Dariya yayi ya ce "Kome zakice kice " Tana shirin sake magana ta Hango Asmy ta fito daga gidansu ta nufo Inda take jaber na ganin asmy gabansa ya tsananta fad'uwa karta zo ta ganesa asirinsu ya tonu wajen Chuchu Dan yasan Sarai Asmy ba control gareta ba cikin Sauri bai saurari Chuchu ba yaja motar da karfi tare da saurin barin arear da Kallo Chuchu tabi motar Kafin ta tab'e baki Rungume juna sukayi da Asmy suna murnar ganin juna kafin Su wuce gidansu Inda Zarah take da gudu Suka Rungume juna suna Daukin ganin Juna Sosai Zarah ta d'an wartsake Dan tayi murnar ganin kawar tata sosai aka karrama Chuchu a gidansu Asmy fiye da tunanin mai karatu da dare yayi ma anan suka kwana Dan Zarah batason zuwa gidan su taro ya fara yawa washegari gidansu Zarah suka wuce sakamakon yawan nemanta da dangin babanta suke d'akin Zarah suka yada zango sosai Zarah ta nunawa Chuchu taji dad'in gudummawar jakunkunan da akayi gudummawar Ammy kuwa kin amsa tayi ba yanda Chuchu batayi da itaba amma taki amsa tace hidimar tayi yawa ganin jayayyar tasu tayi yawa ya sanya Chuchu Maida kudin jaka da niyyar ranar da za akaita ta had'a mata dasu ....Mama Rabi ce Gaban malamin ta (nikam nace boka dai)Cikin tashin hankali ta ce "Malam baki na da naka kace Auren nan Babu shi bazaiyu ba akwai Babban al'amarin dazai ruguza Auren Kace basainasa anyi komai ba Amma har yanzu banga Alamun lalacewar Auren nan ba har ana jibi d'aurin Aure hankalina fa a matuk'ar tashe yake Malam" buga kasa bokan yayi ya ce "Kina da gaggawa a kowani al'amari rabi na buga na buga amma amsar d'aya ce Auren nan babu shi Leko ki gani da idanunki " Lek'awa cikin kwaryar Rabi tayi ta ce "Malam ban fahimta ba " Da yatsa ya nuna mata ya ce "Kinga wancen na nesa da Hasken nan guda biyu Wanda ya fad'i d'innan" tace Eh "To shine mijin da ake shirin daura Auren ta Riga tayi masa nisa nesa ba kusa ba Babu Aure tsakaninsu" Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "To Malam hasken nan fa guda biyu Dana gani hannayensu rik'e Dana juna" Itace tare da Abokin rayuwarta tun sanda kikaban aikin nan Dana buga haka nake ganinsu Saidai naga Haske amma fuskokinsu sunki bayyanuwa "Cikin tsananin tashin hankali ta ce" Malam abokin rayuwarta kuma to meyasa Sukaki bayyanuwa sai Haske"Saboda suna da tsananin ibada da addu'a ko tsafi mutum yake tofa ina tabbatar maki bazasu tab'a Tab'uwa ba biyun nan ba kinsan ba irin aikin da ban maki ba kinsan yanda aiki na yake kamar yankan wuk'a to wannan Biyun bani da k'arfin ikon da zan iya musu asiri saboda babu Aljanin dazai iya tunkarar su yin kokarin hakan ma zai iya jawo mana asara babba Saidai a iya binciken da nayi su biyun suna da tsananin Kusanci da junansu sannan dukansu Haskene a cikin rayuwar kowannensu musamman ita Yarinyar da haskenta yafi nashi "uwar zufa ce ta ketowa Mama Rabi Cikin tashin hankali ta ce " Malam kace Haske ne su Duka biyun"Wannan maganar haka take kuma duk Inda kikaje haka za a fad'a maki"To Malam bazaiyu a raba su ba dan tun yanzu hankalina ya fara tashi aiduk Inda Haske yake alkhairi ne Taya za ayi Ace Zarah Haske ce kuma Shidinma ya zama Haske"Dariya yayi ya ce "Kina da tsananin hassada Rabi yanzu ki fad'a abunda ya kawoki " Goge uwar zufar data keto mata tayi ta ce "Malam Auren nan bana son yayu so nake ayi aikin da zai ji baya kaunarta ya tsaneta bazai iya Aurenta ba Wanda da kanshi zaizo ya furta hakan" Yana buga kasa irin tasu ta y'an tsubbu ya ce "Wannan mai sauki ne saboda yaron bashi da wani karfin ibada sosai A yanzu ma za a iya Gamawa dashi amma ina Kara tunasar dake kinyi gaggawa zaki k'ara daukawa kanki zunubi ne a banza Bayan Abun daman bazaiyu ba Auren nan babushi na fad'a maki tun farkon zuwanki da maganar nan" eh Malam nidai ayi aikin hankalina zaifi kwanciya"Dubu Biyar din da saida ta sayar da fantekun ta na Aure ta bashi da niyyar idan Aiki yaci zata cika masa sauran "......yau ta kama Juma'a kuma yaune Ranar da za a fara Event din bikin Wanda yau walima kawai za ayi tunda Zarah ta tashi yau ta tashi da zazzabi mai zafin gaske da ciwon kai ga tashin zuciya Chuchu da Asmy kadai suka sani basu fad'awa kowa ba har Wajen 12:PM tayi Tana kwance jikin Chuchu jikinta yayi zafi rauu cike da damuwa Chuchu ta ce " Kinki a kaiki Asibiti momcy taya zaki zauna jikinki da zafi haka "Girgiza mata kai tayi ta ce " zanji sauki"Asmy data shigo da Ruwan tea a hannunta data had'o mata ta ce "Ki tashi kisha zakiji k'arfin jikinki Kinga ba abunda kika ci tun safe" Nanma girgiza mata kai tayi ta ce "Na koshi bana son Cin komai Asmy " Matsowa Inda take Asmy tayi tare da Aje cup din ta tallabota ta ce "Bazaiyu ba saikinsha wlh kinji na rantse " badan Zarah ta so ba saidan yanda Asmy ta rantse dole saita sha ya sanyata yunkurawa ta karba a hankali Tana rumtse idon kanta dake mata ciwo "Kurba d'aya Tayi taji Madarar ta taso mata Batasan sanda ta saki cup d'inba sakamakon aman da taji ya taho mata da gudu ta Ruga tayi waje kafin ma ta k'arasa makwararar gidansu ta fara sheka amai Kamar zata amayar da y'an cikinta dangin Baban ta da na Mama Rabi da suka zo Duk Kallonta suka tsayayi Yanda Take kwarara amai Chuchu ce ta biyo ta ganin ba Wanda yayi yunkurin taimaka mata ya sanyata d'aukar butar data gani a tsakar gidan ta cika ruwa tare da nufar Inda take ta fara jera mata Sannu a lokacin ko magana bata iyayi Asmy ma wajen tayo su Suka taimaka mata ta gyara jikinta Daya daga cikin K'annan babanta ta ce " Keko Zahra'u Me yake damunki Irin wannan aman"shiru tayi ta kasa magana.Mama Habi ta ce "Dake fa ake" Dagowa tayi ta Kalleta ta ce "Bakomai Mama" A a daga ganinki kaga marar lafiya ni sai yanzu ma na lura maza shirya na kaiki Asibiti anyi ciwo ba magani ciwon ma kuma na amarya"Hakanan Zarah taji gabanta ya fad'i "Chuchu ce ta ce " Mama Anjima basai a kaita ba yanzu tad'an huta "Mama Habi tace " to shikenan Sai Anjima idan ta tashi kizo ki fad'amun "To Chuchu ta fad'a daki suka koma Inda Asmy ta dirmiya duniyar tunani tsoro da fargaba cike da ranta tsoranta Allah tsoranta ace Zarah ciki ne da ita tasan shikenan tasu ta gama " Chuchu ko lallaba Zarah tayi harta samu tayi bacci sai sannan ta sauke ajiyar zuciya ta Kalli Asmy ta ce "waiko tana da typord ne " Girgiza mata kai tayi ta ce " a a a "Ikon Allah kuma take Amai haka to Allah ya bata lafiya Gaskiya ya kamata Aje asibitin Kar wuri ya K'ure amarya ba lafiya " Shiru Asmy ta dirmiya duniyar tunani ganin haka ya sanya Chuchu janyo wayarta ta fara chat sai wajen la'asr Zarah ta farka ta tashi jikin da sauki Saidai kasala da ciwon kan Kad'an nan suka shiga yi mata Sannu har khairat data shigo Inda taje ta fad'awa Mama Habi Ta tashi "Da Abinci a plate Mama Habi ta shigo d'akin Bayan ta zauna Kallon Zarah tayi ta ce " Anshi kici Nasan ba abunda kikaci"Dagowa tayi kamar zatayi kuka ta ce "Na koshi Mama" wani kallo tayi mata ta ce "Baki isa ba Anshi maza kici kar ranki ya baci" Zarah tana amsar abincin kafin ma takai Baki taji zuciyarta ta tashi amai na shirin zo mata "Cikin Sauri ta mik'e tare da rugawa tayi waje duk da kallon mamaki Mama Habi dake zaune ta tab'a hannu ta ce " me nake gani haka ni Habiba"batayi amai sosai ba saboda ba komai cikinta nan fa Mutane aka fara ido ido musamman dangin Mama Rabi ita ko "Fitowa tayi ta ce " Subhanalla Zarah me nake gani haka kiyi amai da safe yanzu ma haka lafiya kike saikace mai ciki"Kallon da Mama Habi tayi mata ne ya sanyata yin shiru tsaki taja tace Tashi Muje ki sanya hijab d'inki muje Asibiti "tab'e baki Mama Rabi tayi ta koma ciki ita da y'an uwanta suna cewa " shidai abun duniya baya rufuwa kome akayi sai anjishi ba wani boye boye "girgiza kai Kawai Mama Habi tayi Da taimakonta ta shiga toilet Dan tayi wanka Bayan ta fito D'akin da su Zarah take ta shigo shigarsu kenan Khairat ta shigo Tare da Kallon Mama Habi ta ce " Mama Baba yace wai kije keda su Mama Zainabu Yana dakinshi"To kice masa ina zuwa ta fad'a tare da mik'ewa kallon su Chuchu tayi ta ce "ta shirya kafin na dawo" yanayin yanda suka samu Baba ne hankalinsu saida ya tashi dafe da kanshi kallo d'aya zakayi mashi kasan yana cikin tsananin damuwa "dak'yal K'anwar tashi da Yayar tashi suka karasa " Mama Zainabu ta ce "Lafiya dai Malam" Sai sannan ya d'ago ya ce "da sauki Zainabu Yanzun nan shigowar da kikaga nayi dangin yaron Chan ne sukazo akan wai Yaron ya ce ya fasa sun kasa gane kanshi tun jiya gidansu ba irin Fafatun da ba ayi ba karya maidasu kananan mutane amma ya murje ido ya ce " ya fasa Auren kuma ma aka kuskura aka daura zai iya sakinta a ranar Dan haka shine sukazo suka bamu hakuri akan muyi hakuri a d'auki abun matsayin kaddara wlh hankali na matuk'ar tashe yake ina farincikin zan Aurar da Amanar Allah Murnata ta koma ciki wlh nayi mamakin yaron nan yanda lokaci guda zaice ya fasa saida ya bari ana gobe d'aurin Aure kafin a sanya Ranar Auren karkiga irin rawar k'afar da yake gaba d'aya hankali na ya tashi kaina ya kulle na rasa ta Inda ma zan fara"Cikin tsananin tashin hankali Suka rafka Salati Mama Habi ta mik'e ta ce "Allah ya kiyaye yaron nan ba yaudarar yarinyar nan yayi ba Yayi mata ciki yace ya fasa" ciki"Baba Da ?Mama Zainabu suka fad'a lokaci guda hankali tashe "Yo eh mana ciki inba ciki ba me zaisa yarinya tayi ta kwarara amai Tun safe sannan kuma yazo lokaci guda yace ya fasa ai wannan ba maganar d'auka bace da walaki Goro a miya" Girgixa kai Baba yayi yana dafe saitin zuciyarsa da Yakejin wani irin zafi a dabarbarcewa ya ce "Ba haka bane Habiba na yarda da Zarah d'ari bisa d'ari bazatayi abunda bai dace ba na d'auki hakan a matsayin kaddara Da rubutun Allah ya rubuta ba mijin ta bane Dan haka ku hada lefensu ku mayar musu Har gida" Kallon Mama Zainabu Mama Habi tayi ta ce "Kije ke da su Kande ku mayar musu da kayansu ni kuma bari muje Asibiti wlh abunda nake zargi ya tabbata basu isa ba Saidai duniya ta zagemu amma bai isa yayi wannan yaudarar ba yaci bulus tana komawa d'akin ta samu Zara harta sanya hijab cikin muryar b'acin rai Dan ita daman zafi gareta ta ce " Wuce mu tafi "Asmy ce ta ce " Bari na rakaku Mama"Kallon Chuchu tayi ta ce "Ita kuma bakuwar ki barta ita kadai ki bari mu dawo A tare suka fita da Zarah hankalinta duk a tashe koda suka isa Asibiti Mama Habi cewa likitan yayi " Yi mata awon ciki"Gaban Zarah Ya bada daram Kallon Mama habi tayi tana so tayi magana taga yanda ta had'e fuska ya sanyata shiru Fitsarinta Dr ya d'auka Bayan yasa tayo a wata k'aramar kwalba ya tafi awo tagumi Zarah tayi Gabanta na tsananta fad'uwa ba ayi 20 minutes ba dr ya dawo Y'an rubuce rubuce yayi kafin ya d'ago ya kalli Mama Rabi ya mik'a mata takardar"Amsa tayi tace "Ba gane rubututtukan nan naku nake ba Dr fad'amun abunda ke damunta" Murmushi yayi ya ce "To shikenan Mama " Tana D'auke Da ciki ne Na wata Ukku da sati Ukku"Cikin tsananin tashin hankali Zarah ta d'ago ta kalli Dr Ta ce "Ciki kuma Dr" eh idan baki Yarda da result d'inmu ba zaki iya zuwa wani asibitin a aunaki amma Tabbas ciki ne dake na Wata hud'u ba Sati d'aya "Tashin hankali ne ya ziyarci zuciyar Zarah Wanda Bata tabajin irinshi ba a iya Rayuwarta ba " Batasan sanda Ta d'ora hannu aka ba Tana shirin kurma ihu cikin b'acin rai Mama Habi ta kwabe mata baki ta ce "Yiwa mutane shiru tashi muje" ta fad'a tana wartar hannunta "Sukayi waje kuka Zarah takeson tayi Amma tashin hankali yasa ta nemu kukan ta rasa Suna fita harabar asibitin Mama Habi ta ce " Tonon asiri ne zakiyi mana a Asibiti kowa ya fahimci halin da ake ciki ai ba yanzu ya kamata kiyi kuka ba yana nan gaba "Kuka Zarah ta fashe dashi Sosai ta ce " Wlh Mama karya yake bani da wani ciki sharri ne kawai zaiyi mini"d'auketa da Mari Mama Habi tayi cikin b'acin rai Ta ce "Yi mana tonon Asiri a titi Zakiyi bayani idan mukaje gida gaban mahaifinki bani ba " Tsaida mai napep sukayi suka shiga hade kai da gwuiwa Zarah tayi ta shiga rera kukan tausayin kanta Tabbas indai da gaske ciki ne da ita Musty ya cuceta ya gama da ita ya cuci rayuwarta "batasan sun isa gida ba Saiji tayi Mama Habi ta Ja hannunta bata dire ta ko ina ba sai d'akin Baba Kujerar Dake d'akin ta wullar da Ita tana huci ta ce " Kin cuce mu Zarah kin b'ata mana sunan zuri'a ana tunanin wuta a makera ashe a masak'a za'a sameta Kinban mamaki ko a mafarki ban tab'a tunanin zakiyi mana haka ba kin cuce mu kin cuci mahaifinki kin cuci mahaifiyarki dake k'asa sannan kin cuci kanki.........✍🏿 *domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️...........*73 & 74* Kin cucemu Zarah kin b'ata yardar da mukayi miki"ta k'arasa fad'a hawayen bak'inciki na sauka daga idonta Dan Duk cikin Yayan y'an uwanta ba Wanda tafiso kamar Zahra"Kuka Zahra take kamar ranta zai fita tama kasa magana Baba ne da hankalinshi yayi mugun tashi yana dafe da saitin zuciyarsa ya ce "me yake faruwa Habiba kiyimun bayani me zahrar tayi " Cike da takaici ta Kalleshi ta ce "Saidai kayi hakuri Malam abunda na kiyayar ne Ya faru Yaron nan yaudararta ya yi yayi mata ciki shiyasa yazo lokaci guda yace ya fasa" A matuk'ar tashin hankali Baba ya furta "Ci ki" a rarrabe "Mama Zainabu ce " Cikin b'acin rai Ta ce "Meye haka kike Habiba wai kasancewar itace gaba da ita ta ce " wannan Abun da kika fada kai tsaye ai sai kija kuma zuciyarsa ta tarwatse shida daman ba kosashshiyar lafiya ba tun mutuwar mahaifiyarta ba lafiyar kirki ta ishesa ba "To idan ban fad'a masa ba an nemu mafita shiru zanyi dole yayi hakuri muzo mu nemu mafita tunda Mai faruwa ta Riga ta faru Wlh Zarah kin kunyatamu bantaba tunanin haka daga gareki ba " Kasa magana Baba yayi sai Dafe saitin zuciyarsa da yayi cikin k'arfin hali ya ce "Habiba Nasan halin Zahra sarai na san irin tarbiyar da na yi mata ba zata aikata wannan Abun ba kodai likitan ya gwada ba daidai ba kafin ya kalli zahra data durkushe kasan kujera tana kuka ya ce " Zahra taso ki fad'a mana Ba Gaskiya bane bazakiyimun haka ba nafi kowa sanin halinki da irin tarbiyark...kasa k'arasa maganar yayi sakamakon wani irin daci da yake ji a a makogaransa na tashin hankali "Cikin muryar kuka zahra ta d'ago ta ce " Ba Ba "Saikuma kuka yaci karfinta " Cikin b'acin rai Mama Habi ta nufi Inda take ta ce "Fad'a mana ubanda yayi miki wannan abun" Kasa Dagowa tayi saici gaba da kukan da tayi tana tsinewa Musty a ranta ta ce "Ka cuce ni ,ka zalince ni,ka tozartani ,ka sanya mutanen da suka yarda dani yanzu bazasu tab'a aminta dani ba ,bani da bakin da zan k'are kaina Allah ya isa tsakani na dakai" cikin Zafin rai Mama Habi ta nufi Inda take tare da shakota ta ce "Zaki fad'a mana ubanda yayi miki ko saina illataki yau d'innan" dukda zahra taji shak'ar sosai kasa magana tayi sai kuka"Kasancewar D'akin tsakar gidan yake gashi da karfi suke magana ya sanya mutanen dake tsakar gidan suka Fahimci halin da ake ciki kowa Salati kawai yake Asmy ko tashin hankalin data shiga baya musaltuwa har Chuchu da taji abun tamkar almara saida tayi kuka ta ce "Asmy ban yarda ba Momcy zata aikata haka Dan Allah kije kiyi musu bayani kila Dr dinne ya rubuta ba daidai ba " tagumi Asmy tayi hawaye na sauka daga idanunsu Cikin tsananin b'acin rai Mama Habi ta ce "Magana ta ta tabbata amma yaron nan anyi Dan iska ba kama ,ya cucemu aiko wlh bai isa ba yanzunnan bazan zarce ko ina ba sai gidan uwarsa da ubansa suji abunda dansu yayi yasa ya ce ya fasa Auren ta fad'a tana yin hanyar waje kamar wacce aka tsunkula haka Zarah ta zabura tare da saurin Kamo K'afar Mama Habi " mama Ba shi ba ne "Ta fad'a a rarrabe duk juyowa sukayi suka Kalleta yanda ta rik'e kafarta tana wani irin kuka mai cin rai sai sannan Mama Rabi da shigo d'akin Bayan ta gama shewarta da hamdala a d'aki d'auke ta da Mari Mama Habi tayi ta ce " To Dan Ubanki idan ba shi ba uban wa yayi miki ko fyad'e aka miki"Nan ma shiru Zarah tayi saici gaba da kuka da take "Daidai lokacin da Baba ya fara tari dukansu cikin tashin hankali Suka nufi Inda yake sosai ya shiga tari ba kakkautawa yana dafe da saitin zuciyarsa" Salati duk mutane suka fara "Mama Rabi ta ce " Shikenan kin kashe sa kin kashemun miji bakincikin ki ya kashe ubanki Munafuka duk sanya hijab din da zarya Islamiya ba fashi Ashe na banza ne na kariyar iskanci ne ni daman Nasan An Rina jami'ar nan da ta tafi nasan da bura'ubar da take yo yarinya ce Daga shiga Jami,'a ta waye tana ganin kowa a daddage sai wani kyau da take Da kiba kamar ba karatu take ba Ai yanzu ga ranar tonuwan asirinki nan muna fuka algulguma "Kannen Baba sunajin abunda Mama Rabi take cewa Amma hankalinsu yana ga Dan uwansu dake tari hankali tashe sai sannan zahra ta lura da Baba da gudu taje Inda yake tare da Rungumesa da fashe da wani irin kuka ta ce " Dan Allah Baba karka tafi ka barni kai kad'ai ka ragemun a duniyar nan kai kad'ai ne mai sona kuma nasan kai kad'ai zaka fahimceni Dan Allah Baba karka mutu kodan ni ka tausaya mun "Mama Rabi Ce cikin zafin nama Ta fardo ta dagaa kan Baba ta ce " Dan Ubanki k'arasa kashe shine zakiyi y'ar iska karuwa cike da muganci ta hau Bugunta Karan da Zarah tayi ne ya sanya su Asmy da chuchu dake daki Sauri fitowa ba shiri suka shiga d'akin ganin irin dukan da Mama Rabi ke mata ya sanya suka isa wurin da Sauri tare da fardar Zarah Cikin b'acin rai asmy ta ce "Ke kuma ina ruwanki da ita Munafuka har zakiyi mata irin wannan Dukan Muguwa" Nuna kanta Mama Rabi tayi ta ce "Dan Ubanki ni kike fad'awa haka ohhh kungama yawon iskancinku tare shine Asirin d'aya ya tonu zaki Fara borin kunya to saura ke " Cikin Tsawa Chuchu ta ce "Shut up Malama Annabi MUHAMMAD (s a w) ya ce falyakul khairan auli yasmut " ka fad'i alkhairi ko kayi shiru amma daga ganinki bakinki baya fadar alkhairi wannan dukan da kika hauta dashi kasheta zakiyi Dan muganci "Salati Mama Rabi tayi ta ce " watau tsabagen yanda zahra keyi dani har kawayenta ta sanya zasu Zage ni lallai Ta haihu duk ruk'on da nayi mata tun yarinta"Mama Habi ce Dake kokarin tada Baba a kaishi Asibiti ta juyo ta ce "Da Allah Malama fita kiba mutane waje waya sakoki ma d'akin nan muna ta lafiyar Dan uwanmu kin zauna kina wasu banzayen maganganu marar tushe da ma ana ke in kina da kunya har kince kin Riki zahra wlh idan baki bar d'akin nan ba zanyi miki rashin mutuncin da bakiyi zato ba " Tsaki Mama Rabi taja kasa kasa ta ce '"yo ina zani mijina na wani hali yanda yake Dan uwanku nima haka yake mijina kuma uban y'ay'a na Dan haka ba Inda zani kuma ta kashe mun miji kotu Ce zata rabamu da ita "Ohhh haka kike ce kenan to bari nazo mu fidda Raini " Mama Habi ta fad'a tana tunkarar Inda take cikin Sauri Mama Rabi tabar d'akin tana tsine mata kasa kasa "tsaki taja tace k'aramar y'ar iska kafin ta kalli Asmy ta ce " Dan Allah jeki taro mana mai napep"Asmy dake Kuka Rungume da Zarah da ta sume ta ce "To Mama Chuchu ma hawaye take ganin kawar tata sume kamar ba rai " Sai sannan su Mama Habi suka lura da zahra ta suma "Ruwa suka kawo suka yayyafa mata amma taki tashi Sosai hankalinsu ya k'ara tashi ga zahra sume ga Baba dake tari ba kakkautawa yana fara fita hayyacinsa koda mai napep suka zo da taimakon Baban Asmy aka saka Baba Inda sai sannan suka samu labari sosai maman Asmy ta shiga tashin hankali jin wannan Abun tamkar almara wata napep din aka taro Inda aka saka zahra da Chuchu Da Asmy na gefenta Asibitin da aka kai Baba Chan aka kai zahra sosai likitoci suka fara iya kokarinsu wajen ganin sun ceto rayuwar Baba wajen ganin hawan jinin nasa da yahau sosai ya sauka Allurar bacci suka masa kafin su daura masa drip Wanda aka zuba magunguna a ciki" Zarah ko cewa sukayi ba wata matsala tashin hankali ne Yayi mata yawa sannan suka horesu da yadaina shiga irin wannan tashin hankalin zai iya Sanadiyar zubewar D'an cikin ta "A zuciyar Mama Habi ta ce " Ai dama zubewa yayi me za ayi da shege Allah yasa ya zube ma "Chuchu da Asmy ko har lokacin hawaye suke musamman Chuchu da takejin zafin irin abunda Mama Rabi da dinga aibantawa kawartata da take jinta har ranta " Su kadai aka bari a d'akin da zahra take hawaye cike da idonta ta kalli Asmy ta ce "Sis nasan bata boye maki komai a baya ban gaskata cikin nan gaske bane sai yanzu da Dr yayi bayani na k'ara tabbatarwa Nasan halin zahra Bazata iya aikata wannan mummunan abun ba Dan Allah Ko Fyade wani yayi mata Dan Allah ki fad'amun wlh bazan iya jurar ganinta cikin wannan halin ba ki fad'amun kowaye yayi mata fyaden wlh sai Inda karfinmu ya k'are " Asmy bata iya bata Amsa ba saici gaba da Kuka da take "Ganin ba amsa ya sanya Chuchu yin shiru sai wajen Bayan magriba Zahra ta farka koda ga farka da bakin cikin abun ta tashi sosai taci gaba da rera kuka abun ban tausayi Cikin su ukkun bamai Lallashin wani cikin Muryar kuka Zarah ta ce " Asmy ya cuce ni ya zalince ni Allah ya isa tsakani na dashi ban tab'a tunanin Abubuwa zasuzo da haka ba a yau ji nake daman Allah ya karbi rayuwata babu abunda nake da Buk'ata sama da mutuwa na sanya Mahaifina mafi soyuwa raina Wanda yafi kowa kaunata cikin wani hali ina Baba Asmy yana cikin wani hali da wani ido zan Kallesa,,,kuka ne ya k'ara cin karfinta Inda ta shiga rerasa ba kakkautawa "Rungumeta Asmy tayi tana kuka ta ce " Duk ni na janyo wannan din zahra ni na cuce ki na zalunceki"Chuchu da duk hankalinta ya tafi akan fyad'e akayiwa zahra cikin Sauri ta mik'e ta ce "Wlh ko waye yayiwa Momcy wannan Abun bai isa yaci lilis ba wannan ai zalinci ne babba wai garinyama haka ta faru" Cikinsu ba Wanda ya iya bata Amsa sai kuka Banko k'ofar da akayi da karfi ne ya maida hankalinsu gamai shigowa d'akin Mama Rabi Ce ta shigo daga ganinta kasan ba mutunci Kai tsaye gadon da Zarah ta nufa ta shakota iya karfinta ta ce "Wlh baki isa ba kika kashemun miji nima saina kasheki kingama yawon karuwancin naki shine kika dawo ki kashemun miji rufin asiri na uban ya ya na ,," sosai ta fara bugun Zarah iya k'arfin ta Cikin wani irin b'acin rai da Chuchu tajima bataji irinshi ba ta daga hannu da wanke Mama Rabi da mari"kafin ta d'ago ta k'ara kifa mata wani "Dagowa Mama Rabi tayi rik'e da kumcinta ta ce " kutumar uban nan ni kika Mara"An mareki d'in wlh kika kara yunkurin tab'ata abunda yafi mari ma zan miki ki fita kibar d'akin nan tunda ba Haihuwarta kikayi ba da zakizo kina jibgarta "Kururuwa Mama Rabi tayi cikin b'acin rai Ta nufi Chuchu da niyyar shakota Waigawa Chuchu tayi cikin Sauri K'arfen da ake sanyawa majinyata kafin ruwa ta janyo tare da Buga Mata shi da karfi aka ji kake tasss Ai Mama Rabi azabar da tajice batasan sanda ta k'walla Kara ba tare da Zamewa a wajen tuni goshinta ya fashe ya fara zubar da jini Chuchu na ganin haka hankalinta ya tashi Asmy ma dake gefen Zarah tana Rungume da ita saida ta zaro ido ta ce " Chuchu me.kikayi mata haka"Cikin rudu Chuchu ta ce "Kina gani yunkurin Kaimun Duka fa tayi kinsan dai karfi na da nata ba d'aya ba shiyasan ya na Buga mata " Innalillahi Zarah da Asmy suka shiga nanatawa ganin yanda Mama Rabi ta sume Zarah ta ce "Shikenan Chuchu kinjamun na shiga ukku"ta fada cikin muryar kuka Cikin Sauri Chuchu ta ce "Ki maza mu bar asibitin nan"ganin Mama Rabi na k'ok'arin farfadowa Dan sumar ma ta azaba ce ya sanya Chuchu saurin zuwa gadon da Zarah take ta kamo hannunta ta ce " ki maza mu tafi karta farka kinsan bazata kyaleni ba nikuma bazan juri ganin kin sake fad'awa cikin wani halin ba please ki taho mu tafi gidanmu Dan girman Allah "Zarah na kuka ta ce " Bazan biki ba Chuchu a halin yanzu mutuwa ita nafi buk'ata fiye da wannan bak'ar rayuwa meyasa baki barta ta kasheni ba ku tafi kawai na shirya amsar kowani irin hukunci koda kuwa hakan zaiyi sanadiyar mutuwa ta...rufe mata baki Asmy tayi tana kuka Itama kukan Chuchu take duk ta rude ta rasa yanda zatayi janyo Zarah tayi ta ce "Ki taho momcy karki zauna su illataki " daida nan sukaji muryar Mama Rabi tana cewa "wayyo Goshina zai balle Allah tsinewa yarinyar nan ta illatani wlh saikinsan kin tabo Rabi y'ar dangi a garin funtua yau d'innan ko baki mutu ba keda tsinanniya kawar taki saikunzama Abun tsoro Dan wlh kartin mazan gidanmu bazasu barku ba saina sanya sun sauya muku halittu ta fad'a tana Kokarin Mikewa amma azabar zafin da takeji yasa ta kasa" Cikin kuka Chuchu ta ce "Kinji abunda take fada ko Momcy Dan Allah ki taho mu tafi" Asmy ce itama data tsorata tace "ki tashi Mubar asibitin nan zahra kinsan sarai matar nan ta aika y'an dabar gidansu Sunkai biyar wlh zata iya sawa a illataki " Zahra na kuka ta ce "Baba Dan Allah ku bari ko ganinsa nayi" Janta sukayi dole suka tayar da ita cikin Sauri Suka nufi barin d'akin "Mama Rabi na ganin haka ta fara ihu tana cewa " Wlh baku isa ba zaku dawo saina illataku tsinannun asarar haihuwa "Basu saurareta ba in banda saurin da suke Allah ya taimakesu basu gamu da na gida ba a wajen asibitin kai tsaye bakin get d'in suka nufa saida suka fita hankalin Chuchu ya d'an kwanta Ajiyar zuciya ta sauke Tare da zaunar da zahra da takejin layi akan wani dakali har lokacin kuka take " itada Asmy "matsawa kusa dasu Chuchu tayi cikin Sauri ta bud'e wayarta kai tsaye contact din Yayanta ta kira tanajin ta fara ringing ta fara zirga zirga har ta katse bai d'auka ba oh my god ta fad'a kafin ta k'ara kira cikin Sauri ta ce " yaya d'auka yaya d'auka kai kad'ai ne zaka iya fuskanta ta kai tsaye ka taimakemu saida ta kusa katsewa kafin ya d'auka tana jin ya d'auka ta fashe masa da kuka "Cikin tsananin tashin hankali ya ce " Innalillahi what happened Chuchu me akayi kike kuka waye ya mutu"Cikin kuka ta ce "Yaya ba mutuwa bace Zadai a kashemu Dan Allah kazo ko katuro a taimaka mana Allah muna cikin wani hali" Cikin tashin hankali ya ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un shiyasa banason barinki barin gida daidai da second fad'amun me yake faruwa karki tarwatsarmun zuciya "cikin kuka ta ce " yaya nasan kai mai fahimta ne zaka fahimcemu momcy ce ta shiga wani hali yanzu haka muna cikin tsananin tashin hankali Dan Matar ubanta ke son kasheta yanzu ma dak'yal muka samu muka kubuta yaya ka taimakemu ka turo mota azo a d'auke mu kartayi mana illah"ta k'arasa fad'a tana kuka"Ai MD daga zaunen da yake baisan lokacin d'aya zabura ya Mike ba ya ce "what takeson kasheta Innalillahi wa inna ilaihiraji'un wani tashin hankaline ya ziyarci zuciyarsa jin ana son kashe Zarah a matuk'ar d'imauce ya ce " Yanzu kuna ina "Kallon Sunan Asibitin tayi ta ce " Muna general hospital funtua"Okay to gani nan kusamu waje ku b'uya Karku bar wajen "to yaya Dan Allah ka turo a taimakemu" katse wayar yayi batare da ya saurari abunda take cewa ba Dan hankalinshi a matuk'ar dage yake jin ana farautar rayuwar Zahra waje yayi daga palourn shi cikin Sauri Duk ya rud'e d'aya daga cikin driver d'inshi da bai tafi ba ya kwalawa kira yana zuwa ya ce "yi maza ka dauko mota yanzu wacce ba Suna na jiki kuma wacce ba asanni da ita ba yanzunnan " Driver najin haka cikin Sauri yaje ya d'auko motar MD na shiga yace "Yi gudu sosai kayi gudun da baka tabayi ba ina son kafin nan kafin 30 minutes ka kaini Funtua " Angama ranka ya dad'e ya fad'a yana karawa motar gudu "Duk kanshi ya kulle Jabir ya kira yana d'auka ya ce " kana ina yanzu"Ina gida "Idan baka komai ka fito da Mota yanzu na kama hanyar funtua mu hadu a Chan" Funtua da Daren nan Jabir ya fad'a cikin mamaki "eh yanzu Chuchu ta kirani cikin tashin hankali wai ana harin rayuwar Mai Sunan Ammy Yanzuma dak'yal suka sha" Cikin tsananin tashin hankali Jabir ya ce "Subhanallahi gani nan yanzunnan" anyi gudu ma awa guda ya kamata ya kaisu shine cikin minti 35 suka isa garin funtua Wanda kai tsaye general hospital din suka nufa Saida sukaje gab kafin Suyi parking ta nesa MD.ya hangosu su Ukku sai sannan hankalinsa ya tuno masa Tabbas ya tunkaresu kai tsaye asmy da Zahra zasu ganesa su tona masa asiri gaban Kanwarsa "dafe kanshi dake tsananin sara masa yayi kiran jaber yayi ya ce " kana ina "na kusa yanzu " naga Inda suke amma Kasan Bazaiyu na tunkaresu ba su Ukku Chuchu zata gane halin da ake ciki"Daga bangaren jabir ya ce"yanda za ayi ka.kira Chuchu Kad'an ja hankalinta da kwatancen gaba Kad'an Inda kake data bar wajen saika shammaceta kaje kawai ka daukota amma karka saki kabarta "Ajiyar zuciya MD ya sauke ya ce " To ita kawar tata fa"Karka damu da ita kota ganka ba matsala hankalinta ma zaifi kwanciya akan tayi tunanin ko Sace ta akayi "yanda Jabir ya basa shawara haka yayi ya kira Chuchu ya d'auke hankalinta tayi wani wajen yana ganin ta danyi nesa dasu ya sauka daga motar Inda suke ya nufa har lokacin kuka zahra take tanajin takaici da bak'inciki a cikin zuciyarta Asmy ma tayi tagumi hawaye kawai take " kamar daga sama zahra taji an ruko hannunta Duka biyun tare da daukarta gaba d'aya tana shirin fasa ihu Yayi saurin rufe bakinta da hannunsa Asmy dake shirin itama kwala ihun ya Kalla tare haska mata kansa da hasken screen din wayarsa"ya mata nuni da tayi shiru da hannu" gwalo idanu tayi ganin Wanda Bata tab'a tsammani ba ta ce "me ya kawoka nan " Karki damu ina tare da ita bazata cutu ba "Asmy duk ta rude waige ta fara ta ce " To to to "Saurin barin Wajen yayi bai dire Zarah ko ina ba sai mota Ya bi Shima ya shiga ya rufe yacewa " Driver ka juya damu"Zahra Najin muryarsa ta gene cikin tsananin tashin hankali ta bud'e idonta ta sauke a kansa cikin tsananin b'acin rai da bakin ciki ta ce "Ubanme kazo kamun ka sauke ni Na rantse da Allah kafin na Tara maka mutane Bayan Lalatamun rayuwa da kayi da ruguzamun rayuwa dakayi bai isheka shine har saika biyo Inda nake zuwane kayi ka k'arasa kasheni Allah ya isa tsakani na dakai mugu azzalumi macuci ka cuceni ka yaudareni kaci Amanata daman Kasan da cikinka jikina shiyasa kaki Sanar dani kak'i Sakina ka barni na taho da kadarraren cikinka gidan iyayena ka lalata Aure na da Wanda yayimun halicci ya soni tsakani da Allah yayi dakon soyayyata shekara da shekaru sannan ka ruguza mu'amula ta da mahaifina da y'an uwa na ka cuceni Ka zalunceni Allah ya isa tsakani na dakai" ta k'arasa fad'a cikin wani irin kuka mai tab'a zuciyar mai sauraro rumtse idonsa MD yayi yanajin kalaman nata na dakar masa zuciya jin ta ambaci ciki ya sanyashi Sauri Dagowa cike da mamaki ya ce "Ciki ?Kina nufin Kina da ciki " Hawaye cike da fuskarta ta ce "Bansaniba mugu azzalumi wlh saina zubar da kadaddararan cikin nan kamar yanda na tsaneka haka na tsani cikin ta fad'a tana Kokarin bud'e kofa ta fita dukda Gudun da motar take MD na ganin haka yayi Saurin ruk'ota tana fusgewa dak'yal ya samu ya rungumota jikinsa " Bugunshi ta fara da hannu iya karfinta ta ce "Ka sakeni nace Wlh baka isa ba ka gudu dani Ka maidani Inda Ka daukoni ko kuma kayi Dana sanin tab'a sani na ma da kayi a rayuwa"ta fad'a tana kokarin fusgewa daga jikinsa" Meye haka Mamy ki nutsu "Bazan nutsu dinba ku saukeni na rantse da Allah ko na yi muku ihun y'an kidnapping"Innalillahi" MD ya fad'a "Hankalinsa a matuk'ar tashe yake baima lura da Kiran Jabir da Chuchu suke masa ba Sosai zahra ta chaza masa kai ganin tana Kokarin fusgewa daga ruk'on da yayi mata ya sanyashi kallon driver ya ce " Kayiwa ko ina na motar lock sannan Ka wuce Abuja damu"Angama ranka ya dad'e drivern ya fad'a yana cigaba da tukunshi"Sai sannan MD ya tuna da maganganun da zahra tayi gaban driver kwata kwata Yama manta da wani a motar "Kuka zahra take sosai Kamar ranta zai fita ,Wanda MD jin kukan nata yake har cikin ransa Yana rike da ita tana kuka Dak'yal har suka zo Kaduna yana sassauta ruk'on da yayi mata ta fusge tare da Fara kokarin bud'e motar ta kasa buga glass din motar ta fara a haukace kamar mahaukaciya " Dafe kanshi MD yayi dake masa tsananin ciwo ya ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Allahumma ajirni fi masifatihi" Ganin tana shirin fasa glass din motar ya sanyasa Saurin ruk'ota Da k'arfin tare da matseta jikinta Ya ce "Ki nutsu Mamy Dan Allah kibari" Bazan nutsu ba din mugu macuci wlh ka maidani garinmu ko nayi addu'ar da motar nan zata kama da wuta Duka mu mut....bata k'arasa fad'a abunda take son fad'a MD ya Sanya bakinshi cikin nata Dan ya lura wannan hanyar ce kad'ai zata taimaka masa ta kasa magana"Zahra najin bakinshi cikin nata ta fara yunkurin ta kwace amma ta kasa samu tayi ta gantsarawa harshensa cizo iya karfinta..............✍🏿 😅 *karma Kuyi tambayar page biyu wolla dan bazai samu ba* *Domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️ .........*75 & 76* Cikin Sauri MD ya zame bakinsa dukda yaji zafin cizon da tayi masa amma bai nuna ba har suka isa Abuja zahra a hauka ce take lokacin da suka isa 11pm harta gota kin fita tayi daga motar bayan isarsu gidansa dake Buzu quarters sosai take kuka tana ja masa Allah ya isa Wanda sosai yakejin zafin hakan a cikin ransa Saida ya ciccibeta tukwana ya samu ya fito da ita zullewa take amma ya ki sakinta ya Rungumeta jikinsa sosai yayi Hanyar part din da ita shidai driver kanshi gaba d'aya kulle yake Dan yayi mamakin abubuwan da suka faru yasan dai uban gidan nasa mutumin kirki ne to me zai hadasa da wannan yarinyar har tana ikirarin yayi mata ciki"Sauri barin wannan tunanin yayi ya ce "Ba abunda ya shafeni bane inje inyi ta aiki na " MD bai dire ta ko ina ba sai tafkeken bedroom dinsa dake gidan zahra na ganin haka ta zabura ta mik'e kamar mahaukaciya ta ce "me kake nufi da satoni da kayi Bayan tozartani din da kayi bai isheka ba wlh wannan Karin baka isa ba Saidai duk abunda zai faru ya faru Ka cuce ni Allah ya isa tsakani na dakai Daman kasan da cikinka jikina ka bari na koma gidanmu dashi Dan na wulakanta a idon iyaye na da jama'a sannan kak'i saki na kawai d'anka wulakanta ni nasan Duka da gangan kayi wannan din Allah ya isa tsakani na dakai kuma wlh saina zubar da tsinannan cikin....MD baisan lokacin dayayi saurin rufe mata baki ba cikin muryar tashin hankali ya ce " Karki tsinewa Cikina Mamy look ki tsaya mu fahimci Juna "fusgewa tayi da karfi tace " wace fahimtar juna,ai ba wata sauran fahimta ni dakai Wlh tallahi kaji na rantse saina zubar da kaddararran cikin nan mugu azzalumi macuci Alla ya isa tsakani na dakai"Innalillahi wa inna ilaihiraji'un MD ya shiga maimaitawa Dan a halin yanzu ji yake babu abunda yake so yake k'auna kuma yasa guri akansa kamar cikin nan dake jikinta da ya tabbatar yanzu sosai yaji k'aunar cikin na musamman Wanda yakejin bazai tab'a iya jure rashinsa ba ga zafin irin yanda take ja masa Allah ya isa "Toshe kunnuwanshu yayi tare da rumtse ido Dan bayajin zai iya jure kalaman da take danganashi dasu " Zarah wata tsanar MD takeji wacce bata tabajin irinta ba A matuk'ar haukace ta mik'e tare da kalle kallen Inda zataga mabugi Dan zuciyarta wata irin tafarfasa take "gaba mirror ta ruga kamar mahaukaciya ta fara warwatsa abubuwan da ta gani a kai tare fara tillawa MD Sosai yakeyi mata kallon mamakin abunda take" Mikewa yayi yana shirin nufar Inda take ta tilla masa.kwalbar turare a kafa ji kake tassss "Auchhh ya fad'a yana kallon kafarsa da ta fara fitar da jini Kallonta yayi yaga yanda take kuka ganin tana shirin Bugawa cikinta wata kwalbar baisan lokacin d'aya take kwalbar ba ya chafke ta hannunta Tare da janyota jikinsa cikin b'acin rai ya ce " Baki da hankali ne.wai Mamy me kike haka illata kanki zakiyi"ka sakeni ina ruwanka da rayuwata ina ruwanka da koma meye zanyi wlh na tsaneka na tsani cikin nan "ta fad'a tana bugar cikinta da k'arfin gaske " a d'imauce MD ya rik'e hannayenta sosai baimajin zafin yankan da yayi yana gani ido biyu tana shirin yi masa asarar ciki"Gado ya nufa da ita ta karfi tana fusgewa ya kwantar da ita fusgewa take sosai Kamar mai iska tana kai masa Duka da Allah ya isa "har 3:PM MD da zahra ba Wanda ya rintsa sosai ta haukace masa da tayi nan ta tallabosa dak'yal ya samu ya matseta jikinshi sosai ya rasa yanda zaiyi da ita addu'ar ko yayi ta ba adadi yana tofa mata matseta yayi sosai a jikinsa yanda Bazata iya motsi ba tun tana Kokarin kwacewa harta kasa jikinta ya mutu muryarta ta dishe da kuka a haka ya samu bacci ya kwasheta MD na ganin tayi bacci Ajiyar zuciya ya sauke dukda farincikin cikin dake jikinta bai hana zuciyarsa shiga damuwa ba Ganin irin tsanarsa a idon yarinyar k'iri k'iri kallonta ya dingayi yanda take baccin kasan baccin wahala na kallon cikinta yayi da yaso fitowa Wanda ba kowa zai fahimta ba a hankali ya shafa Cikin ya ce " Allah ya fito mun da ke Ko kai lafiya"Kwata kwata ji yayi bacci ya kauracewa idonsa ranar a zaune MD ya kwana rik'e da zahra da har lokacin take jikinsa duk yanda yaji ta motsa sai yaji har cikin ransa.....bangaren Asmy tunda taga tafiyar zahra ta zaune wajen ta fashe da wani irin kuka Nan Chuchu ta dawo ta isketa ta ce "Ina momcy din "" Ganin yanda take kukan ne ya tsoratata da Chuchu ta ce "Ki fad'a mun Inda take karkice mun sunzo sunkoma da ita" ta fad'a cikin daga murya sai sannan Asmy ta d'ago cikin dakiya ta ce "Wanda yayi mata ne yazo ya tafi da ita " What ya tafi da ita kuma kika zauna a nan kina ganin ina ya tafi da ita"ruko hannunta Asmy tayi ta ce "Na yarda ya tafi da ita d'in ne badan komai ba saidan hakan zaifi mata sassauci iyayenmu bazasu tab'a fahimtar mu ba Chuchu duk nice silar shigar zahra halin nan da take ciki Nina cuceta na zalince ta " ta fad'a tana fashewa da kuka "Sosai kwalwar Chuchu ta chushe ta ce " me kike nufi Asmy Dan Allah ku fiddani cikin duhu kuna rud'ar dani Na kasa fahimtar komai"Ruko hannunta Asmy tayi tana zaunar da ita gefenta ta ce "Chuchu cikin dake jikin zahra ba cikin shege bane cikin sunna ne kamar kowani d'a Saidai nasan ba kowa zai fahimci hakan ba " ta fad'a kukan nadama nacin karfinta karfinta "Da mamaki fuskar Chuchu ta ce " me kike nufi Asmy bangane ba taya zakice haka Bayan ba Aure tayi ba kin sanyani cikin duhu"Goge hawayenta Asmy tayi ta ce "Zanfada maki sirrin da muka jima muna boye miki badan komai ba Saidai bamuyi tsammanin zuwan wannan ranar ba Chuchu zan fad'a maki labarin nan saboda na yarda dake kuma zamu iya magance matsalar nan mu Ukku tunda dukanmu mun yarda da juna kuma munzama tsintsiya madaurinta d'aya amma kafin nan kiyimun Alk'awarin bazaki fitar da maganar nan ba tsakaninmu zaki barta a cikinki kamar yanda muma muka barta cikinmu batare da sanin kowaba" kama hannun Asmy tayi ta ce "karkiyi shakkar fad'amun koma meye Asmy wlh nayi maki alk'awarin bamaiji hatta mahaifiyar da ta haifeni bare wani ki daukeni tamkar yanda kuke da zahra " numfashi Asmy ta ja kafin ta fara labartawa chuchu komai daya faru bata boye mata komai ba har alakarta da zahra Sosai Chuchu ta girgiza dajin wannan al'amarin tamkar almara bata tab'a tsammanin hakan ba Sosai zuciyarta ta girgiza dajin wannan bak'ar chakwakiyar da suka shiga "a Gaskiya Asmy kinyi wauta kawai dai mutanen nan yaudararku sukayi Amma wlh akan wai ciwon cikin perioud karyane Ace anyi aikin million's har Talatin a tunani na kawai suna da wata manufar tasu na Auren a Gaskiya a lokacin da kinyi shawara dani wlh da hakan bata faru ba mai faruwa ta Riga ta faru Saidai a kokonci gaba yanzu ina mafita?,Goge hawayen da suka zubo mata Asmy tayi ya ce " ba wace mafita data wuce mu roki Allah ya warware mana wannan sarkarkiyar "numfashi Chuchu taja wayarta Ce tayi ringing dubawa tayi taga ya jaber ne " Cikin Sauri ta d'auka Daga bangarensa ya ce "Kina ina nazo daukarki ina daidai gaban general din ?waidaman Kaine zakazo shine dazu yaya Ya kirani yace yazo harna tafi nemansa bangansaba daman Nasan da wasa yake bazaizo garin nan da Daren nan ba ka jira ni gefen asibitin Kad'an gani nan" tana gama fad'ar hakan ta katse kiran Tare da Kallon Asmy ta ce "Sis muje na d'auki kayana gida zantafi" Haba Chuchu da Daren nan saikace wacce aka kora ai Ammy ma taganki bazataji dadi ba ki barwa Safiya"Girgiza mata kai tayi ta ce "Bazan iya kai gobe garin nanba sis wlh a tsorace nake Matar nan kinajin tana zata hadamu da y'an daban gidansu Gwara na tafi gida, banso kika bari macucin mutumin nan ba ya tafi da momcy naso mutafi gida tare Ammy bazata tab'a kasa fahimtarmu ba amma dai kome kenan zamuyi waya ki taso muje" Goge hawayenta Asmy tayi tare suka jera Chuchu sai leke take Dan har lokacin a tsorace take Hango Motar jaber da tayi yasa hankalinta ya kwanta Jabir na ganin Asmy saida hankalinsa ya tashi tsoronshi d'aya karta ganesa dayake Chuchu ta shiga gaba Asmy ta shiga baya kwata kwata hankalinta ma baya jikinta Hakan yasa bata gane Jabir ba gashi daman dare ne jakar kayanta kawai Chuchu ta d'auko daga gidan su Asmy tayi musu bankwana suka juya Kd ita da jaber da Daren nan Asmy ko Daren ranar kuka ta kwana tanayi bangaren Chuchu sosai Ammy tayi mamakin dawowar tata cikin dare ga yanda ta dawo duk a firgice ba walwala koda Ammy ta tambayeta meke faruwa ce mata tayi ba komai yin duniyar nan Ammy tayi ta fad'a mata abunda ke damunta ta ce Bakomai "To ya akayi kika dawo yanzu bacin ko d'aurin Auren ba ayi ba " Amfasa "ta bata amsa kai tsaye " subhanalla garinya"a Shagwabe Chuchu ta ce "Dan Allah Ammy mubar maganar nan " Hmmm Allah kyauta "kawai Ammy ta fad'a ta rabu da Chuchu Daren ranar da abun Chuchu ta kwana a ranta sosai labarin da Asmy ta bata ya tsaye mata a rai Juyi kawai ta dingayi amma bacci kam Saidai barawo ya d'auketa...bangaren Zahra koda ta farka ta ganta a hannun MD sosai taji takaici da bak'inciki kamar taga kashi haka ta tashi daga kanshi Tana Danasanin saninsa da tayi a rayuwa Toilet ta nufa MD na ganin haka ya sauke ajiyar zuciya Tare da fita Bayan ya rufeta Dan karma ta gudu ta sanyashi cikin wani hali itama ta saka kanta Sai sannan ya samu damar shiga bedroom dinsa yayi alwala Zahra ko a toilet dinma saida Tasha kuka ba wanda take tausayi take tunawa kamar Baba" yana wani hali?ta tambayi kanta"Sosai ta dinga kuka har ciwon kanta ya dawo sabo kafin ta daure tayi alwala akan lallausan carpet din d'akin tayi salla jingina tayi da Gado tana rusa sabon kuka mai tab'a zuciya MD koda ya shiga ya ganta cikin wannan halin sosai ta daga masa hankali "Cikin tausassar murya Wanda kana jinta kasan Shima a tashin hankali yake ya ce " Dan girman Allah Mamy ina begging d'inki Dan Allah kiyi hakuri ki nutsu karki sanya kanki cikin wani hali ki sanya yaron dake cikinki "D'ago da idanunta da sukayi ja tayi tare da banka masa wata irin harara ta ce " kai har kana da bakin da zakayi mun magana akan Abunda ya shafi rayuwata wani hali kuma zanshiga Wanda yafi Wanda ka sanyani cikinsa Sannan cikin da kake magana kama daina sashi a lissafi Dan wlh kaji na rantse bazan haifesa ba bazan haihu da mutumin da ya ruguzamun farincikin rayuwataba bazan haihu da mutumin da yayi sanadiyar shigar mahaifina cikin wani hali ba ka cuce ni ka zalunceni......"kuka ne yaci karfinta ta kasa fad'ar abunda tayi niyyar fad'a rumtse idonsa MD yayi yanajin zuciyarsa na wani irin zafi da rad'ad'in maganganun nata a fahimtar sa kenan dalilin bayyanuwar cikin nan ya sanya mahaifinta shiga wani hali Tabbas dole ne yayi bincike sosai yakejin zafi idan tace zata zubar masa da ciki "Shiru yayi na d'an lokacin yana sauraran kukan nata da yake jinshi kamar ana d'iga masa darmar wuta kafarsa ya Kalla da tayi kumburi ga rad'ad'i da take na yankan glass din da ya shige masa danma kwalbar ta fita amma wannan bai dameshi ba hankalinshi yana kan yanda zai samu ta fahimcesa sosai MD ya shiga yi mata magiya da ban hakuri akan ta nutsu suyi magana amma takiya sai kuka da take tana ja masa Allah ya isa 'Ganin ta tsagaita kukan ne ya sanyashi cewa" Dan soyayyarki da fiyayyen halitta Annabi muhammad (s a w ) Wanda akayi duniya dominsa mukecin darajarsa kiyi hakuri ki nutsu muyi magana na had'aki da girman Allah da manzon sa Mamy badan ni ba girman da darajar Wanda na had'aki dasu zaki duba "Shi kanshi MD baisan ya iya magiya haka ba Dan baitabayi ba baitab'a rokon wani Abu ba a wajen wani tunda yake idan ba a gurin mahaliccinsa ba Amma yau shine yake magiya yana rokon yarinya k'arama tana batsewa gaba d'aya ta since masa notin kansa " Zahra batayi niyyar sauraransa ba Amma darajar Wanda ya had'ata dasu yasanyata tsagaita kukan ta d'ago kanta daga hade kai da gwuiwar da tayi tana Goge hawayen ta kauda kai Alamun tana sauraronsa "Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce " Me kikeso kike da Buk'ata da zakibar kukan nan Banason ganinki cikin halin nan ki fad'amun me.kikeso"cikin muryarta data fara dishshewa ta ce "Abunda nake so mai sauki ne na farko ka sakeni ka fita daga rayuwata har abada ko a hanya ka ganni.karka nuna ka tab'a sanin mai suna na ma ka rabu dani Na har abada na biyu Kuma ka kaini a zubar mun da Cikin nan...ta k'arasa fad'a cikin kuka" Tirk'ashi ai abunda ta lissafo MD baijin zai iya d'aya daga cikinsu musamman cikin d'aya kwallafa ransa a kanshi"fuskarsa ba walwala ya ce"ki daina maganar zubar da cikin nan Mamy ina son kaya na Ina kaunarsa Fiye da komai nawa da na mallaka ki taimakeni ki haifamun shi please Dan girman Allah "wani irin kallo na baka da hankali zahra ta bishi kafin ta ce " ohhhh wai a tunaninka ni zahra zan Haifa maka cikin nan to tun wuri Inma mafarki kake ka maza ka farka Dan wallahi tallahi kaji na rantse bazan haifi cikin nan ba ko ka kaini a zubar mun dashi ko kuma wlh na zubar dashi ta karfi da yaji"dafe kansa MD yayi dake matuk'ar sara masa yanajin wani irin daci idan yaji tace zata zubar masa da ciki "cikin dauriya da k'arfin hali Dan kansa wani irin ciwo yake masa ga tension ga kwanan zaune da yayi ya ce " Na shirya mallaka maki komai nawa dana mallaka kudi,kadara,componynnika na ,gidajena nako ina wallahi tallahi kinji na rantse na shirya sadaukarwa miki da komai nawa hatta gidajena bazan bar kaina da komai ba indai kin yarda zaki Haifa mun cikin nan wlh a shirye nake da baki Duka dukiya ta akan cikinnan yafiye mun komai Dana mallaka Abunda najima ina burin samune tsawon rayuwata shine yanzu na samu Mamy ki dubi girman Allah karki zubar mun da ciki a shirye nake da mallaka maki dukkan abubuwan nan Dana lissafa maki madamar zaki Haifa mun cikinnan saboda ina masa tsananin soyayyar da bantaba yiwa wani mahaluki irinta ba ,"wani banzan Kallon zahra take binsa dashi na tsana kafin ta ce"a tunaninka dukiya ita zata iya baka komai,a tunannika duk wannan abubuwan daka lissafo zanyi kwadayinsu ne yasa harnaji ina sha'awarsu na Haifa maka cikin nan to tun wuri ka sauya tunani k'aramar kwakwalwarka ta fad'a maka da daidai ba Ina son ka sani ba komai kudi ke iya saya ba ,baka da kud'in da zaka sayeni dasu ,Kai har kana da kud'in da zaka saye ni dasu to idan baka sani ba ka sani ni zahra bana sha'awar dukiyarka,bana kaunarta,kuma babu abunda zanyi da ita ,bakada kudin da zaka ribe ni da su wlh ,baka da wannan ikon koda kudinka Sunkai tundaga sama har k'asa "ta k'arasa fad'a tanajin wani irin dacin takaici a cikin zuciyarta " Sosai MD yayi mamakin yanda yarinyar ke fad'a masa magana son ranta kwata kwata gani yake ta sauya kamar ba zahrar da ya sani bace a baya mai saukin kai da saurin Sauka ,rasa ma abunda zaice mata yayi sai kallo d'aya dinga binta dashi Mikewa yayi batare da ya sake kallonta ba yayi palourn Yajima yana sake sake a ransa Ya zaiyi da rayuwarsa ne Wai "tunowa da bata ci komai ba ya sanyashi saurin zabura Tare da mik'ewa yafita compound din gidan ma'aikatan dake gadin gidan ya kira Tare da umartarsu su da suyo masa take away na abinci kala biyar " kafin ya juya Dan a cikin biyar d'in ta zab'a Wanda takeso yana palourn har aka kawo abincin A plate ya juye d'aya Bayan daya kafin ya d'auka ya fara d'aukar biyu yayi bedroom d'inta dashi yanda tabarya haka ya sameta ta hade kai da gwuiwa tana kuka shi yanzu baimasan da wasu kalamai zaiyi amfani wajen Lallashinta ba "zaunawa yayi tare da Aje Plate din Abincin Duka biyun a sanyaye ya ce " Ki taso kiyi break fast "Zahra kamar jira take tana gadowa ta kalli abincin da Kallesa D'aukar plate din Duka biyun tayi tare da watsa masa tundaga saman rigasa har kasa ga zafin abincim" MD baitab'a expecting haka daga Wajenta ba Kallon kanshi yayi da kalleta tare da Kallon abincin data bata masa kaya dasu Miyar soyayyan dankalin dukta bata masa farar shadda "Baice mata uffan ba sai barin dakin da yayi tare da komawa Bedroom dinsa shi kanshi yayi mamakin da bai iya cemata komai ba Yasan dai duk duniya Bayan Ammy babu wacce ta isa tayi masa haka a duk fadin duniyar nan ya rabu da ita shi kanshi har mamakin kanshi akan yarinyar yanda harta iya d'aga baki ta dinga gaya masa maganganu son ranta saida ya sake wanka ya sauya wasu kayan kafin ya fito hankalinshi gaba d'aya yana kanta bataci komai ba wani Abu zai iya affecting cikin dake jikin ta " amma yasan ko yaje da wani abincin bazata sauraresa ba "Wayarsa ya janyo tare da dannawa jaber kira Jabir yanajin muryarsa yasan cikin damuwa ya ce " Yadai bloody meke faruwa?Numfashi yaja kafin ya ce "Jabir ina son kayi mani wani taimako? Inaji Jabir ya fad'a daga wayar" Akwai mahaifin yarinyar nan da nake tunanin bashi da lafiya ina son ka binciki Chuchu ta fad'a maka asibitin da yake duk wani taimako daya kamata da ni zanyi kayisa kome ake ciki ka kirani sannan a sauya masa Asibiti duk yanda likitocin sukace idanma waje ta kama a fitar dashi kome kenan na bar maka ragamar kula dashi a hannunka"daga bangaren jabir ya ce "Insha Allahu baka da matsala Aboki amma Bazan tambayi Chuchu ba saboda kartai zargin wani Abu tunani na general hospital d'innan da na gansu a nan ne asibitin da yake yanzu zanje garin na bincika tunda nasan gidansu kaga komai mai sauki ne karka samu damuwa" numfashi MD yaja yanajin yarage y'ar Kad'an daga cikin abunda ke damunsa ya ce "sainajika idan ansamu yanda akeso ka kirani" yinin ranar ba abunda zahra taci a cikinta dukda irin yunwar da takeji har juya ke daukarta amma batajin zata iya cin abunda ya fito daga hannun mutumin nan da takejin tsanarsa a ranta bangaren MD ma hankalinsa tashe yake bai iya sanya komai a cikinsa ba sai fresh milk yinin ranar daga ita harshi Cikin tashin hankali Suka yishi Dan sosai ta d'agawa MD hankali washegari ma haka zahra harta fara fita daga hayyacinta da komai bibbiyu take ganinsa kwana biyu kenan ba abinci cikinta sai ruwa da Takesha yanzu babu abunda take da muradin sama da tasamu hanyar da zata zubar da kadararren cikin nan Kallon cikin tayi Wanda da a haukanta kiba ce ta fara taga harya so ya fara fitowa batasan lokacin da ta fara bugun cikinta da hannu bibbiyu ba iya karfinta sosai take bugun cikin dukda azabar zafin da takeji tana cikin Bugawa taji wata irin azaba batasan lokacin data k'walla wani uban k'ara ba Wanda daga nan bata Kara sanin Inda kanta yake ba ta zube a wajen summammiya MD daga palour ya jiyo Karan da tayi ba shiri ya Ruga d'akin yanda ya sameta ne ya yi tsananin tayar masa da hankali kwance k'asar tiles ga jini da ya ga ya fara fitowa daga kasanta a matuk'ar tashin hankali ya nufi Inda take tare da Fara jijjigata yana kiran sunanta shiru Ba shiri ya sungumeta a guje yayi waje da ita makullin motarsa dake kan centre table ya d'auka cikin tashin hankali yayi waje yana bud'e motar ya sanyata a baya tare da Juyawa gidan Gaba a 360 ya figi motar tare da dannawa mai gadi wani Mahaukacin horn kafin ya isa da motar get dinma an wangale masa gudu yake sosai Cikin tashin hankali yana driving yana waigawa yana kallonta ikon Allah ne kawai ya kaisa Asibiti....✍🏾 *Domin magana da marubuciyar 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss hajo ce*_🤙🏿 🅿️..........*77 & 78* Da isarsu asibiti ma emergency aka wuce da ita idan hankalin MD yayi dubu a tashe yake zirga zirga kawai yake yana cikin wannan tashin hankalin wayarsa tayi ringing baima duba mai kiran ba ya daga daga dayan bangaren amera ta ce"Hello honey ykk daman zan fad'a maka ne gobe zanyi tafiya Dubai dan wlh jina nake kamar a k'aya k'asar nan dan karkaji na tafi"md ji yayi kamar ya shakota ta cikin wayar ya wanke ta da mari ba karamun haushi ta basa ba cikin bacin rai ya ce "Ba london ba kitafi bangon duniya stupid mahaukaciya kawai kije gaba da bangon duniya " baijira amsarta ba ya katse kiran yanajan tsaki shi yana cikin wannan babban tashin hankalin wanda duk silarta hakan ya faru ita tana ma masa zancen tafiya wata kasa baimasan ya zage ta ba ,babban Dr d'in mai asibitin kanshi kasancewar da kansa ya shiga duba ta tare da taimakon nurse saida yayi awa Ukku a ciki kafin ya fito yana shafce zufa da Sauri MD ya taresa ya ce "ya ake ciki dr tana lafiya Kardai kace mun abunda ke cikin ta ya zube" Calm down ranka ya dad'e Babu abunda ya samu abin cikin ta Gaskiya kayi Namijin kokari da kukazo da wuri asibiti Dan da aka kai wani lokaci Abinda ke cikin ta zai fita ita kanta zata wahala sosai Dan dak'yal da taimakon Allah yasa Muka ceci cikin daga zubewa Amma yanzu alhmdllh cikin iko na ubangiji Munyi aiki da kwarewa har muka tsaidar da jinin sannan muka yi control d'in matsalar dake shirin faruwa Amma Gaskiya next ka kula sosai Dan Abu Kad'an ba fata ba Zai iya Affecting cikin ayi asararsa sannan ta dinga cin abinci please "nauyayyar Ajiyar zuciya MD ya sauke Jin cikin bai zube ya ce " Thank you so much Dr itafa ya jikin nata"Alhmdllh da sauki amma zata kwana biyu kafin a sallameta saboda ta k'ara warwarewa yanzu munsanya mata Karin ruwa tana bacci ne "Okay Zan iya samu na ganta" ba matsala ranka ya dad'e "Dr din ya fad'a yana masa nuni Dan kallo d'aya yayi masa ya ganesa saboda suna cin karo da hotonsa a Internet sannan MD ba boyayyan mutum bane dukda yayi mamakin Kawo yarinyar da yayi Saiya d'auka matarsa ce tunda bakowa yasanta ba " Bayan shigar md d'akin da zahra take kan kujer dake gaban gadon ya zauna kallonta ya shigayi ba kakkautawa kwance take tana bacci hankali kwance Fuskarnan tata tayi fayau yanayin yanda take baccin sosai ya basa sha'awa a hankali ya kamo hannunta mai d'auke da bakin lalle da ratsin ja sosai lallen yayi masa.kyau Kallon lallen ya shigayi ba kakkautawa yana Dan shafa lallausan hannunta a hankali A rayuwar MD yanason yaga matarsa na masa lalle wayarsa ce tayi ringing ganin jaber ne yasanyashi saurin picking Daga bangaren jaber ya ce "Yadai najiki kamar baka cikin yanayi mai dadi"da sauki ya fad'a yana matsawa daga Inda take ya ce " ya ake ciki kaje asibitin?Eh naje komai ya tafi yanda akeso kuma sun bada Had'in kai Sunji dadi sosai da taimakon sannan munyi magana da Dr d'in a jiya ma ina Chan yace Zuciyarsa ke ke shirin kamuwa da ciwo amma idan aka tallabi abun da wuri bazai kamu ba "Innalillahi MD ya maimaita a ransa duk shi yayi sanadin shigar mahaifinta wannan halin kafin ya ce " Dan Allah Jabir kamun kokari duk yanda za ayi ayi kar wani Abu ya samu mahaifinta muddin wani Abu ya samesa bazan tab'a yafewa kaina ba duk yanda za ayi ayi chuku_chukun da za ayi kafin gobe a fitar dashi daga kasarnan na shirya kashe ko nawa ne wajen nema masa lafiya"insha Allahu babu abunda zai samesa amma ga shawara mezai hana a jaraba akwai wata Dr Najmat Kwararrar likitan zuciya ce har daga kasashe kawo masa patient ake Inma anfitar dashi wajen tofa abunda zatayi zai iyafin ma na Chan din saboda itama gwanace har Asibiti gareta a India a Gaskiya indai muka sameta tofa insha Allahu za a dace "cikin Sauri MD yace " To yaza ayi a sameta cikin Sauri kar wani Abu ya kuma samunsa sannan wani gari ne take "a nan kaduna itama take gidansu shima cikin GRA yake babu matsala insha Allahu saboda akwai abokin mijinta Habib to Abokina ne kuma matarsa Amera Y'ar uwar ita Dr najmat d'ince yanzu insha Allah zankira Habib din zanje har gidansa ta hanyar amerar zata hadamu da Najmat d'in Insha Allahu" (Only najmat abiy fans can related😝masu buk'atar cmplt book din *Najmat Abiy* su tuntub'eni akan wannan number 07026166536 Na Batin ne😝)Ajiyar zuciya MD ya sauke ya ce "Nagode Jabir komai Kenan ka sameni a waya zan maka transfer kudi kome ya kamata ayi sannan Dan Allah ka sayi kayan abinci da komai na Buk'ata ka kai gidansu ka d'ora musu da isassun kudi kayi abunda koda ina nan haka zanyi Dan Allah" Bayan sun gama wayar kujerar da yake ya koma ya kafeta da idanu kamar zai cinyeta yana jiran farkawarta da akayi Sallar Azahar yaje yayi salla d'aya daga cikin restaurant dinsa ya kira drivern sa akan yaje ya amso abinci Bayan ya fad'a masa asibitin d'akin da take ya koma kafin 1hour drivern ya kira number d'akin ya fad'a masa Akan idan yazo yayu knoking karya shigo haka ko akayi yana zuwa yayi knoking MD yafita ya amso warmers din yazo ya Aje sai wajen la'asr zahra ta farka dak'yal ta iya bud'e idanunta saboda wani irin nauyi da sukayi mata Ga jikinta da duk yayi tsami takejin ko tashi bazata iya ba MD yana lura da tashinta Ajiyar zuciya ya sauke suna hada ido hud'u zahra ji tayi kamar ta kashesa saboda a halin yanzu ba Wanda ta tsana sama da mutumin nan da yayi silar rugujewar farincikinta Dana mahaifinta "MD na shirin tab'ata cikin b'acin rai Ta ce " karka sake hannunka ya tabani"Kamar Wanda aka tsaida haka MD yayi dukda yaji ciwon abunda tayi masa Telephone din dake d'akin ya d'auka tare da kiran Dr din akan yazo ya duba ta ta tashi ba dau lokaci ba likitan yazo Nan yashiga tambayarta irin yanda takeji tana basa amsa a takaice Dan duk haushin kowa takeji "y'an rubuce rubuce dr yayi a paper tare da mik'awa MD ya ce " gashi a saya wannan magungunan ta fara sha daga yanzu amma kafin nan a tabbatar taci abinci "kin amsar paper MD yayi ya ce "a saya a pharmacy din asibitin bani acco no dinka zanmaka transfer kudin"take MD yayiwa dr din transfer kudi masu yawa dukda Dr baiyi mamakin hakan ba Dan MD zaiyi fiye da haka ba dukda asibitin mai mugun tsadane dan kwana daya ma kudin gado kaji kudin saikayi mamaki amma saida ya ninka kudin sau hud'u dr din na shirin taba hannun zahra dan ya cire mata karin ruwan da ya kare md ya daga masa hannu yace " kaje zancire mata"okay dr din ya fada tare da yin hanyar fita zahra ta ce " Dan Allah Dr cikin ya fita"Murmushi yayi mata ya ce "Ki kwantar da hankalinki madam ba abunda ya samu cikinki ya na nan Saidai ki k'ara kula wajen rainonsa " Wani irin bak'inciki ne ya tokare zuciyar Zahra batasan sanda ta fashe da kuka ba Ta ce "wannan wani irin jarababben makwawacin ciki ne Ba irin bugun da banmasa ba Dan ya zube Amma ya like to duk jarabarsa wlh saiya fita Dan Allah dr ka fitarmun da Cikin...bata k'arasa fad'ar abunda take son fadaba sakamakon kwabe mata baki da karfi MD yayi Kallon Dr yayi yace " ka wuce kawai"Dr na fita cikin b'acin rai MD ya Kalleta ya ce "Wlh kika kara aibantamun ko yunkurin yimun asarar ciki zakiyi mugun mamaki na waike wace iri ce da bakisan lallashi ba ba irin Lallashin da ban maki ba cikin nan ko shege ne iya wulakancin da zaki masa bare cikin halak mai matsayi da gata kamar kowani d'an sunna " wani irin banzan kallo zahra ta bishi dashi kafin ta ce "kai harka samu bakin magana an aibanta cikin kayimun abunda zakamun macuci kawai" Kafin ta hade kai da gwuiwa ta fara rera kuka "Tsaki MD yaja yana dafe ka kansa yace matsala " Mikewa yayi Tare da kama hannunta yana kokarin cire mata Karin ruwan Ta fusge a murtuke ya ce "Ki tsaya na cire maki karya ja miki jini" a hankali ya samu ya cire mata Wanda har lokacin jin kukan nata yake na dakar masa zuciya komawa yayi kujerar da yake tare da bude warmers din d'aya Lafiyayyan sakwarace da tasha Miyar ja sai d'ayar kuma pepper chicken ne sakwarar ya zuba a plate tare da d'ora naman a kai sama yayi da plate din tare da Ajewa gabanta yace tashi kici "Cikin kuka ta ce " Bazanci ba Ka maidani gidanmu naga halin da mahaifina yake ciki "Ba irin Lallashin da MD bai mata ba Wanda shi kanshi baisan ya iya lallashi haka ba akan taci amma taki " Omg ya fad'a yana buga kansa da hannu ya ce "Ya kike so dani ne Wai Mamy kwana nawa bakici komai ba Zai iya shafar abunda ke cikin ki?Tsaki taja cikin Masifa ta ce " ina ruwanka Yama shafi kome zai shafa cine bazanyi ba saika kaini naga halin da mahaifina ke ciki"kwantar da murya yayi ya ce "Indai kikaci zan kaiki wajen mahaifin naki" lokaci guda ta d'ago ta ce "Ka rantse " Yanda ta fad'ar ne yaso bashi dariya ya fusge ya ce "saina rantse zaki yarda " Eh saboda kaid'in ba abun yarda bane"dukda MD yaji zafin abunda ta fad'a Hakanan ya sasa daurewa Dan yanzu ya zama dole ya lallab'ata kodan cikinsa dake jikinta da take shirin yi masa asara "kwantar da murya yayi ya ce " indai kina cin abinci da magunguna har aka sallameki wlh zan kaiki ki gansa"Sai lokacin zahra ta d'an yarda amma da sharadin yau a sallameta cemata yayi ba yanzu ba saikinji sauki sosai kafin ya d'auko sakwarar a spoon ya fara kokarin bata da farko kin amsa tayi saida ya k'ara rantse mata akan Zaikaita data warke taga Baba tukwana ta yarda dukda tace zataci da kanta ya kiya shi zaiyi feeding d'inta shi kanshi yayi mamakin akan yarinyar yakeyin abubuwan da bai tab'a yinsu ba a rayuwa wannan ne karo na farko daya tab'a feeding d'in mace sosai ya samu taci abincin Sai sannan hankalinsa ya kwanta magungunan da Nurse din ta kawo ya b'alla mata Tasha sai sannan ya iya Mikewa Dan yaje ya gabatar da salla da harara zahra ta bishi kafin taja tsaki ta ce "mugu macuci azzalumi wlh na tsaneka " Dak'yal ta yunkura tashiga toilet ta dauro alwala ta gabatar da salla dukda batasan tana da tsarkin yin sallarba Dan bataga komai ba yanzu sab'anin idan bata manta ba kafin hankalinta ya gushe...bangaren Jabir sosai yayi kokari akan Baba kamar yanda MD ya umarcesa haka akayi ya samu yarda sosai daga wajen dangin Baba bisa ga taimakon da yayi musu baisha wahala ba ya samu appointment da Najmat a ranar aka maida Baba asibitin dr Najmat Wanda d'aya daga cikin y'an uwanshi ne kad'ai zaiyi jinyarsa bisa ga Dokar asibitin ko dubiya ba a barin mutane shiga saboda masu irin ciwon basasan hayaniya....bangaren Mama Rabi saida akayi mata dinki.kwana tayi tana tsinewa zahra da kawayenta Asmy ko har gida taje ta samu mamanta Tayi mata tas Wanda Bata biye ta ba nanfa mutane aka shiga binciken ina Zahra tayi tsegumi saiya dawo sabo wasu na cewa guduwa tayi Mama Rabi ko itace uwar zazzakewa wajen bada labarin abunda ya faru dukda wasu daga cikin mutane basu yarda zahra ta aikata hakan ba Sosai Mama Rabi ta dinga mamaki lokacin da aka fara shigowa da libgin kayan abinci kamar za a bud'e wani store tsakar gidan saida ta kusa cika da kaya Bayan anyiwa Jabir Iso ya shigo Mama Rabi har kakkarwa take wajen shimfida masa tabarma a takaice suka gaisa kafinma ya fara mata bayani ta ce "yaron nan wannan kayan fa ko b'atan hanya kukayi" Murmushi d'auke da fuskar Jabir ya ce"a a a nan aka kawo Oga na ne ya sanya na kawo muku ga wannan anyi cefane ya fad'a yana mik'a mata y'an Rafar dubu"ai irin godiyar da Mama Rabi tayi kamar tayiwa Jabir sujjada kira take "Kinji Allah Mai iko tsuntsu daga sama gasashshe amma Allah ya sakawa ogan nan naka da alkhairi ya bashi abunda yake nema duniya da lafiya Allahsa ya gama da iyaye lafiya sai kuma kuka ta ce " Allahsrk wai yau nice Rabi da rik'e irin wannan kudin Wanda tunda nake bantab'a rik'e ko rabinsu ba ga kayan abinci Wanda ko buhun shinkafa ba a tab'a Aje mana ba Sosai Mama Rabi Tasha sabbatu daga baya kuma Bayan fitar Jabir tahau rawa da guda yanda.kasan anyi mata albishir da gidan Aljanna..bangaren Asmy kullum cikin kuka take ta rame Ba irin tambayar da Mamanta batayi mata ba akan ta fad'a mata abunda ke damunta ta ce "Bakomai" Dukda ta fahimci akwai abunda ke damunta Ganin ba fad'a ba zatayi yasanyata rabuwa da ita ta sanya mata ido....bangaren Chuchu ma tunda ta dawo bata da walwala sosai labarin da Asmy ta bata ya burkita mata kwalwa sosai takejin tausayin zahra har cikin ranta Dan Asmy ta bata labarin irin bak'ar wuyar da tasha wajen Mama Rabi itamadin wani time d'in kukan tausayin zahra take yanzu bata da burin da ya wuce na Tasan Inda take Ammy itama tayi tambayar duniyar nan akan tafada mata abunda ke damunta Saidai ta ce Bakomai amma daka Kalleta kasan tana tare da damuwa....kwanan zahra hud'u a asbiti aka sallamesu Wanda MD shi yayi jinnyarta harta warke dukda wuyar da take basa na gardama da fad'a masa bakaken maganganu tun a mota zahra ta tubure ta ce "Wlh saiya kaita taga mahaifinta " ba irin yanda MD baiyi da ita ba akan ta Bari idan ta huta saitaje ganin tana shirin Tara masa mutane ya sanya bama su koma gida ba ya d'auki hanyar kd sai sannan hankalinta ya Dan kwanta suna isa kd ya kira Jabir ya turo masa address din asibitin da room d'in Suna isa asibitin MD ya sanya facemask Dan kar a ganesa cike da mamaki zahra ta ce "Yaya zaka kawo ni nan asibitin Bayan yana funtua" A takaice ya ce "ya na nan asibitin ki biyoni " binshi ta dingayi suna zuwa daidai Wani waje aka Hanasu shiga Dukda Dan basu gane MD bane da zasu iya mai alfarma dukda Dokar asibitin ce haka dak'yal fashewa da mai gadin wajen kuka zahra tayi ta ce "Dan Allah ka taimakeni ko ganinsa ne nayi" Hakan yasa ya tausaya mata ya ce "Zan iya muku wani taimako mu zagaya ta k'ofar baya akwai tagar da zaku hangesa ta nan amma karkuyi magana" Cikin Sauri zahra tace "bazanyi ba ngd" Kofar dake baya ya zagaya da su Tare da bude musu Kad'an nan zahra ta Hango Baba kwance Bisa makeken gadon da baiyi kama da na sauran asibitoci ba ga AC har biyu data sama data k'asa banda fanka ga k'atuwar plasma a d'akin kamar wani hotel batasan sanda wasu hawaye masu d'umi suka zubo mata ba ta ce "Dukni nayi sanadiyar shigar ka cikin wannan halin Baba na cuceka bansan da wani ido zan Kalleba ka yafemun Baba ...kuka ne yaci karfinta sosai Kamar daga sama tajiyo tarin Baba yana kokarin farkawa zara idanu tayi ta murza ganin yana bud'e ido Kasancewar ko ina na asibitin ctv camera ce ya sanya daga Chan office d'inta take gane wadanda ke buk'atar taimako ba ayi minti biyar ba saiga Najmat Ta shiga d'akin Sanye cikin farin glass dayayi mugun amsar kyakyawar fuskarta sosai naga ta k'ara kyau da wayewa fiye da wacce take da ita a baya tana sanye da labcoat kai tsaye Inda Baba yake ta nufa Fuskarta dauke da Fara a ta ce " Alhmdllh "Kujerar dake gefen Baba ta zauna Ganin ya farka nan ta fara aikinta Ta tambayesa me yakeji a jikinsa Girgiza mata kai kawai yayi kafin a hankali ya ce " Ina Zahra "Zahra najin da sunanta Baba ya farka batasan sanda kuka Ya Kubce nafa ba rufe mata baki MD yayi tare da girgiza mata kai sosai taji tausayinta da na mahaifinta Yasan akwai shakuwa da k'auna tsakaninsu cikin hikima irin ta kwarewar aiki Najmat Ta kwantar masa daa hankali dukda batasan dalilin shigarsa cikin wannan halin ba ta ce " y'arka ce Baba?gyada mata kai yayi"murmushi tayi masa ta ce "ta na nan jiyama tazo ganinka Yanzu haka tana gida na idan ka warke zatazo ganinka" Ajiyar zuciya Baba ya sauke yanajin damuwarsa ta ragu Saikuma yayi shiru tunowa da abunda Akace zahra ta aikata wanda har yanzu bai gama gaskata hakan ba Najmat na ganin ya fara tunani tayi saurin katsesa Ta fara masa labarai na sanya Dariya da zai hanasa tunani kafin ta kunna masa kallo Na abunda zai basa nishad'i Likita guda takira akan ya zauna dashi pull time kar a sake A barsa yayi tunani ko na minti d'aya ne kafin tabar room d'in ta koma duba wasu Duk akan idonau MD hakan ya faru Ajiyar zuciya zahra ta sauke tana jin k'aunar Dr d'in ganin yanda ta kula da mahaifinta Sosai ta tsaya Kallon Baba ji take kamar ta fasa kofa tashiga taje ta Rungume mahaifin nata dukda tayi mamakin waya sauya masa asibitin daga wancen zuwa wannan Babban asibitin da daga gani za a chashi kudi masu yawa Wanda yayi musu jagora ne yace "Ya isa Haka su tafi kar wani ya gansu a ja masa ta aikinsa "hawaye d'auke da fuskar zahra ta ce " nagode "kudin da suka rage a aljihunsa MD ya basa masu yawa kafin Su koma mota sosai jikinsa ya mutu gaba d'aya kamar Wanda aka zarewa lakka Har suka isa motarsa nanfa zahra ta tubure tace batasan wannan ba ba Inda zata koma hankalin MD nanfa ya k'ara tashi yahau Lallashinta amma ta tubure ganin tana shirin guduwane baisan lokacin da karfi yazo masa ba ya fardota tare da sanyata mota yayi Sauri ya zagaya yayiwa motar lock kai tsaya ma bai tsaya saurarar komai ba ya juya Abuja sosai zahra ta dinga fasa masa kuka kamar ranta zai fita har suka isa Abuja tana kuka tana tsine masa Daren ranar sunsha dabu da ita Dan burkucewa tayi ya ce Wlh saiya maida ita gida kota jaza masa bala i dak'yal ya samu baccin gajiya ya kwasheta ....sosai Baba yake samun sauki a asibitin Dr Najmat kulawa.sosai Jabir yake basa bisa ga umarnin MD Bayan sati biyu jikin Baba ya warware Ranar da aka sallamesa y'an uwansa sukayi shawarar awuce dashi Batsari ya karajin sauki saboda sunsan halin Mama Rabi sarai zata Kara tayar masa da hankali ne akan zahra ta gudu Bayan sun boye masa sunce tana gida zuciyar Baba chunkushe da tunanin zahrarsa .....Cikin satin nan ba k'aramun dabi zahra da MD suke sha ba Sosai zahra ta birkitawa MD tunani ne yau inya tallabota nan gobe ya tallabota Chan sosai yake hakuri da jure irin abunda take masa shi kanshi baisan yana da hakuri har haka ba abinci ko Sai yayi kamar zai mata d'ure tukwana yake samu taci da bala'i da masifar saiya maida ita gida sannan ancire mata cikin nan har sukayi wata guda a gidan Wanda MD ko kd baisamu yaje ko gaishe da Ammy yayi ba Saidai ya kirata a waya ya ce uzuri ne yayi masa yawa .yauma yana zaune a palour around 9pm yana waya da Ammy tana masa complain Chuchu ta kasa gane kanta indai bashi ba yazo babu Wanda zata fad'awa damuwarsa"numfashi yaja Dan yasan damuwar Chuchu bata wuce ta abunda ya samu kawarta ba ya ce "Badamuwa Ammy Zankirata waya Naji meke damunta insha Allah zansamu nazo " Daga bangaren Ammy ta ce "Hmmm haka dai kake cewa Na rasa wani irin aiki ne wannan da zakayi wata guda kana k'asar bakaga ammynka ba " Shafa lallausan sumar gashin kansa yayi yana murmushi ya ce "Ba haka bane Ammy insha Allahu.muryarsa ce ta sartse ganin fitowar zahra daga ita sai rigar bacci cikin kayayyakin da ya sayo mata Wanda Hakanan take sanyawa d'an bata da wasu Cikinta ya fito yayi das a jikinta Cikin b'acin rai da hawaye ta ce " Waikai d'aukar me kayimun marar galihu ko.kuma me mi.kake nufi da ajeni a gidan nan da kayi kamar wace y'ar iska ....saurin katse.kiran md yayi gabansa na fad'uwa tsoransa Allah kada Ammy taji abunda zahra ta fad'a kallonta yayi fuska ba wasa ya ce "Zaman Aure kike?Tana binsa da wani banzan kallo ta ce " lallai kai baka da kunya ma.wlh har kana da bakin da zaka iya furta wannan Kalmar Wacece zatayi zaman Aure da mugu azzalumi Wanda baisan damuwar wani ba damuwar kansa kawai ya sani mayaudar....bata k'arasa fad'a abunda takeson Fad'a ba MD yayi sama da ita bai direta ko ina ba sai kan Bed yana shirin danneta ta k'walla Kara ta ce "Wlh tallahi ka sake kayimun wani Abu zanyi maka abunda ba a tab'a yi maka shi a rayuwa ba " banza MD yayi mata ya rungumota jikinta sosai tare da Fara Aika mata K'ananan sakwanni ganin zai birkitawa kansa lissafi gashi yayi alk'awarin bazan k'ara wani Abu da ita ba saboda cikin dake jikinta daidai kunnanta ya rada mata a hankali "ki kwanta kiyi bacci yanzu indai bakyaso wani Abu ya faru" Zahra najin haka ta Had'iye kukanta Batasan lokacin da wahalallen bacci yayi awon gaba da ita ba saida yaji saukar numfashinta tukwana ya sauke ajiyar zuciya ya zame a hankali saida ya sha ruwan liptop da lemon tsami tukwana ya samu bacci ya daukesa washegari zahra ta tashi bayan asuba dan ta makara salla shiko md koda yayi salla ya fita daga dakin ya koma nasa Bayan tayi alwala ta gabatar da salla Sosai ta rokawa mahaifinta samun lafiya dukda MD ya fad'a mata ansallamesa yaji sauk'i amma bata yarda ba Tana gama salla yunwa ta ciyota tsaki taja Dan yanzu wata irin jin yunwa takeji da taci kamar bataci ba hakan yasa yanzu ta daina masa zuciya da abinci Dan ita ke illatuwa kofa ta nufa tana turawa taji a rufe tsaki taja Dan sosai takejin haushin kulleta din da yake ko yaushe kamar a gidan yari tsaki taja tare da komawa ta zauna tana lazumi tana addu'ar Allah zubar da cikin nan dake jikinta ba ayi 30 minutes ba MD ya shigo d'auke da plate din wainar kwai kusan guda biyar sai cup din tea da bread a hannunsa kai tsaye gabanta ya nufa dasu a hankali ya ce "Good morning mummyn baby" Tsaki taja tare da kauda kai Dan murmushi yayi Dan ya saba da abun nata ya Aje kafinma ya ce ta ci tuni ta fara ci Dan yunwar data ciwo ta saida abun yaso basa Dariya ganin yanda ta murtuke takeci kamar an mata dole cewa yayi "ki gama ki shirya muje Asibiti ayi miki scanning sannan ya kamata mu fara zuwa awo" wani banzan kallo tayi masa cike da takaici ta ce "Allah kiyaye Allah tsari gatari da saran shuka a tunaninka ni zanje Asibiti saboda lafiyar cikin nan Dana tsana Aiko Inma kana wannan tunanin tun wuri ka bari Dan wlh ba haihuwar....saurin kwabe mata baki yayi cikin bacin rai ya ce" Da Allah yiwa mutane shiru "Dogon tsaki Taja Wanda MD Inda sabo harya saba da tsakin nata wanda duk duniya bayan ammy babu wanda ya isa ya masa su wanje lafiya ta ce" Satoni dinma da kayi Allah saiya sakamun wlh Dan laifinka d'aya da y'an kidnapping"tsaki MD yaja tare da mik'ewa ya ce "Idan kina buk'atar wani Abu ina palour" Da harara ta bisa har yaban palourn wajen Azahar zahra ta karajin wata yunwar koda ta fita palour zaune ta samesa yana aiki a laptop Wuri ta samu ta zauna tana shashan magani so take tace masa yunwa takeji ta kasa ganin baiyi mata magana ba ya sanyata cewa "yunwa nakeji fa Malam" Kamar bazai tanka mata ba ya ce "Me kike son ci a kawo miki" Bana son Cin abincin restaurant Dan ban yarda da tsabtarsu ba bazan sake ci ba"Yana mata kallon mamaki ya ce "To shiga ki girka?Harara ta banka masa ta ce " Wlh kaji na rantse ko hanyar kitchen bazanyi ba"Aje laptop d'in MD yayi yana kallonta ya ce "To wa kike tunanin zai girka maki" Kai da kayi cikin da ke sakani jin yunwar kai zaka dinga girkamun harya zube.........🤙🏿 *Ohni wai yaushe zahra ta zama y'ar Rashin kunya haka*🙆🙆😆 *Domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE* 1, *MU GANI A ƘASA..🔥* _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚* _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5_ *AUREN WATA TARA👩‍❤️‍👨* _Miss Hajo_ Guda ɗaya N300 Guda biyu N500 Guda uku N600 Guda huɗu N700 Guda biyar 1k *ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇* Fatima Rabiu Sunusi 0037219728 StanbicIBTC Bank. Shaidar biya tanan 👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 ...........🥚👩‍❤️‍👨💥🌎.... *ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number 08141799224 *MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO* *_Miss Hajo ce_*✍🏽 🅿️...........*79 & 80* Nuna kanshi da hannu MD yayi ce "Kina nufin ni zan shiga kitchen na girka maki abunda zakici" Tana binsa da harara ta ce "To kaid'in waye" Sosai Abun nata ya fara isar MD tsaki yaja yana maida hankalinshi ga aikin da yake ya ce "Baki da aikinyi shiyasa kike maganar nan ga abinci Chan a dining danayi order kala Ukku ne ciki ki zab'i Wanda zaiyi maki," Harara zahra ta banka masa tana kauda kai dajan tsaki ta ce "Bazanci ba Kuma wlh ka maidani gidan iyaye na na fad'a maka tun kafin nayi abunda baka tunani" Banza MD yayi mata kamar badashi take ba Sosai hakan ya bakanta mata dukda yunwar da take ji amma ta rantse bazataci na restaurant ba ciki ta koma Tare da hayewa Gado ta fashe da kuka MD ganin kusan har awa biyu da komawarta daki a tunaninshi ta fito taci abincin amma yaji shiru tunani yayi yarinyarfa yanzu ta tarki kafiya da zuciyar bala'i karfa wani abun ya samu cikinsa Dan yasan illace mace mai ciki na zama da yunwa Mikewa yayi Koda ya shiga daki kwance ya sameta tana hawaye yana ganinta yasan taci kuka gefenta ya zauna cikin sigar lallashi ya ce "Please Mamy ki daure kici abincin kar wani Abu ya sameki kinsan ban iya girki ba Sarai fa neman rigima ne" banza zahra tayi masa "Mamy ya k'ara kiranta Nanma shiru" Omg " ya fad'a a cikin ransa Kafin ya sake dauriyar cewa "Ko na kawo maki kici anan" Bazanci ba na k'oshi ta basa amsa kai tsaye"shiru MD yayi yana mamakin taurin kai irin nata Wanda da kwata kwata baiyi tunanin tana dashi ba shi damuwarshi bai wuce abunda ke cikinta ba da yakejin sonsa na daban yakejin zai iyayin komai indai zata Haifa masa cikin nan bashi da wani girman kai dole ya Aje ya ce "To ki fad'amun please me kike son ci " Na fasa bazanci komai ba "Cikin lallashi ya ce " na yarda zan girka maki din indai zakici "Sosai zahra tayi mamakin jin wai zai girka " shiru tayi masa "Kifadamun me kike so please" Saida taja mintuna kafin ta ce "jolloup d'in taliya da wake " Ajiyar zuciya MD ya sauke a boye ganin bata tsiro mai wahala ba Mikewa yayi ya ce "give me 30 minutes please kibar kukan nan" Shiru tayi harya fita kafin ta bisa da harara A waya MD yayi browsing Dan ko simple indomie bai iya girkawa ba tsawon rayuwarsa bai tab'a girki ba baima San ya ake ba dan ko school baiyi girki ba Saidai yaci na restaurant Saida ya kwabe manyan kayan jikinsa kafin ya shiga kitchen din waya na rik'e hannunsa daman video ne nan ya shiga Kalla ba laifi MD yayi trying sosai dukda yasha wahala Dan ji yake kamar an sanyashi aikin gini haka dai ya samu ya gama girkin Inda ya juye a plate sai shafce Zufa yake yana fitowa ma kai tsaye d'akin da take ya nufa Inda ya sameta tayi bacci Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Allah mai iko yau nine MD da shiga kitchen akan Aiken wannan y'ar kankanuwar yarinyar saikuma ya tuno da ai kome yayi saboda cikinsa yayi hakan ya sanyasa Aje warmers din tare da Fara kiran sunan da yake kiranta dashi watau Mamy saida ya kira sau Ukku kafin ta tashi Tana murza ido " ta ce "Meye " Abunda kika buk'ata"ya fad'a yana hade fuska "Tura baki gaba tayi tare da mik'ewa taje toilet tayi brush tana dawowa ta iske harya zuba mata d'aukar plate din tayi ta na yatsine fuska kamar taga kashi ta nuna Alamun baiyi mata dadi ba nanko ba laifi saidai magi da yayi yawa kauda kai tayi ta ce "na koshi"murtuke fuska ,yayi ya ce "wlh kinji na rantse saikinci aini ba bawanki bane ki sani bakar wahala kuuma kiki ci abunda bazaiyu bane"bata tanka masa ba sai jujjuya spoon din take kafin ta dauka ta faraci MD na ganin ta fara ci har tayi rabi ya sanyashi sauke ajiyar zuciya Tare da ficewa daga d'akin da harara ta bisa sosai taci abincin Daren ranar zahra karfe d'aya ta tashi ta hau salla Sosai ta daga hannu tana rokon Allah ya kawo mata mafita hawaye na sauka daga idanunta ta ce '" ya Allah kaika jarabceni da duk wannan Abun kuma kana sane dani ya Allah ya kawomun mafita Ya Allah kasan banyi abunda zai tab'a mutuncina da na iyayena ba ya Allah ka fitar dani daga zargin da mutane ke yimun ya Allah ka wanke ni,ya Allah ina kamun kafa da masoyinka fiyayyan halitta Wanda babu kamarsa a duk duniya ya Allah ka bawa mahaifina lafiya Allah ka sanya cikin nan ya zube ta k'arasa fad'a cikin kuka gwanin ban tausayi sai wajen 2 ta ji bacci ya fara daukarta Kallon MD dake bacci kan gadon hankali kwance tayi Dan baya yarda ko daki daya Suki kwana Saboda baisan abunda zata kuma yiwa cikin ba Sosai takejin haushinsa kamar ta kashesa gefen gadon Chan karshe ta ja ta kwanta ba b'ata lokaci bacci yayi awon gaba da ita Cikin baccin ne tayi mafarki Gasu a wani tafkeken lambu Wanda ya cika da kayan marmari da alatu iya rayuwar zahra bata tab'a ganin irin wannan lambun ba waigawa ta dingayi taga ba kowa ba Tana cikin waigawa ta Hango wata mata na kusantowa Inda take fuskarta cike da murmushi da annuri tana sanye da fararan kaya kallonta zahra take har ta karaso Inda take sak Matar taga kamarsu d'aya rai da rai Kallon kanta tayi ta kalli Matar taga sak komai nasu iri daya Karasowa tayi tare da kama hannunta tanayi mata murmushi ta ce "bakisanni ba ko Zahra?Gyada mata kai tayi ta ce " Eh"Kama hannunta ta kumayi suka zauna kan wani lausassan waje da bata Tantance menene ba Matar ta ce "Ni ce Mahaifiyarki Zahra shine suna na nima" sosai zahra ta tsorata saikuma ta Rungumeta ta fashe da kuka ta ce "Ina kika shiga Mama kika barni ina ta shan wahala gashi yanzu ma bata rabu da ni ba Dan Allah Mama Karki k'ara tafiya ki barni ina matuk'ar buk'atar ki a rayuwata ina shan wahala a sanadin rashinki Mama Dan Allah ki daina tafiyar nan Mai nisa karki sake komawa ki zauna tare dani"sai taga hawaye na zuba daga Idanun mahaifiyartata tare da murmushi a fuskarta ta ce "Nasiha nake son nayi miki zahra rayuwa cike take da k'alubale da jarabawowi iri_iri a duk halin da kika tsinci kanki kiyi hakuri sannan ki k'ara kusanta kanki Da ubangijinki shine kawai Wanda zai yaye maki dukkanin damuwarki kiyi hakuri da jarabawa Allah yana jaraba bayinsa ne Dan yaga iya imaninsu karki karaya y'ata ki zama mai tawakkali da godewa Allah a duk halin da kika tsinci kanki sannan ina son ki nemu yarda a wajen Allah ko Duka mutanen duniya basu yarda dake ba indai Allah ya yarda dake kingama samum komai a wajen Allah ake neman yarda ba d'an Adam baa sannan ba mutumin banza Allah yake jarabta ba ni kaina bada son raina nayi doguwar tafiyar nan Ba batare da na rayu dake ba kiyi hakuri da rayuwa kiyi hakuri da rayuwa y'ata ki sani ked'in Haske ce a cikin duhu Ked'in alkhairi ce a rayuwar duk wanda kika rayu dasu zahra ina matuk'ar alfahari da kasancewar ki y'a gareni ina matuk'ar kaunarki kedin yace ta gari " Rungumeta sosai tayi tana kuka ta ce "Mama Dan Allah karki sake tafiya ki barni" murmushi tayi tana Hawaye ta ce "taso nayi miki Albishir" tasowa tayi ta ce "Kalli Chan ta fad'a tana nuna mata wani waje" wajen zahra ta Kalla bata fahimci komai ba saboda wani haske daga gani guda biyu hannunsu rike da juna ta juya ta kalli maman tata ta ce "Mama Haske ne na gani" Murmushi ta kuma ta ce "Kinsan meye hasken can" a a a "" To hasken Chan kece Tare da abokin rayuwarki kudin haskene mai maganin duhu "Da mamaki ta ce " bangane ba Mama"Zaki gane nan gaba kawo hannunki"Mik'a mata hannun tayi "Wasu irin kwandalolin kudi ne taga ta fiddo sai Haske suke guda Ukku kamar zinare har wani Wal_Wal suke ta damk'a mata a hannunta Tare da rufewa ta ce " Ki bawa jikokina kowa d'aya idan sunzo kice ina gaishesu kuma ina sonsu sannan ta bata fuska ta ce "Bazanji dadi ba muddin kika asarar da alkhairi nan dake cikinki zahra ina son kiyi rayuwa Me kyau ki Tara zuri'a mai albarka da zakiyi alfahari da ita ko Bayan ranki sudinga maki addua y'ay'a da kike gani dukiya ce mai daraja Wacce ya kamata mu darajasu mu martaba su sannan inayi miki murna da samun abokin rayuwa na gari kuma Haske a cikin rayuwarki dama ta all'umma Zan Tafi Y'ata sai wata Rana " Cikin kuka Zahra ta ce "Dan Allah Mama karki k'ara tafiya ki dawo ina sonki ina tsananin bukatarki cikin rayuwata " Hawaye na zuba daga Idanun Matar ta na murmushi ta ce "Kalli Chan hasken chan dake rike da hannunki shine mamayina a wajenki zaibaki farinciki insha Allahu tamkar Wanda zan baki " zahra na kallar wajen ta kuma ganin hasken dazu kafin ta juya taga babu Matar babu alamar ta a wajen "Kara sosai ta fashe dashi cikin kuka ta ce " Mama Mama Mama "A matuk'ar firgice da gigicewa ta farka tana Kiran " Mama Mama Mama da karfi"A rude md ya farka yana kallon yanda ta firgice tana ihu tana Mama "Rik'eta MD yayi sosai tare da Fara tofa mata adduo'i a Amma bata fasa kuka ba Tana kiran Mama Wanda MD dukya shiga kogin tunani Har aka kira asuba yana tofa mata adduo'i karatun qur'ani ya shiga rera mata cikin zazzak'ar muryarsa A haka ya samu tana sauke ajiyar zuciya a hankali a hankali ta fara dawowa hankalinta har tagama nutsuwa tana shirin barin jikinsa ya ce Ina kuma zaki" a sanyaye ta ce "Salla zanyi" Ajiyar zuciya ya sauke tare suka Mike Bayan tashiga toilet tayo alwala Shima sai sannan ya samu damar zuwa yayi shiya jasu salla suna gamawa zahra ta hade kai da gwuiwa ta shiga rera kuka sosai mafarkinma dayazo mata a abun al'ajabi ya tsaye mata a rai tsawon rayuwarta koda wasa bata tab'a mafarkin mahaifiyarta ba sai wannan Karin sosai tashiga kuka tana tunwoa da Abubuwan da suka faru a mafarkin gani take kamar gaske ji take kamar gaske ne gata ga mahaifiyarta ji tayi inama bata farka ba Sosai take kuka tanajin wata irin soyayyar mahaifiyarta na ratsa kowani sassa na jikinta MD lure yake da ita yasan kukan take kuma yasan irin yanda ta tashi Tabbas tayi wani mafarki ne ganin kukan nata yayi yawa ne ya sanyashi cewa"Me ya sanyaki firgita lokacin tashinki a bacci da kuma wannan kukan da kike ko kinyi wani mugun mafarkin ne"fuskartat jab'e jab'e da hawaye ta ce "Nayi mafarkin Mama na ne bantab'ayi ba Sai yau ina son na sake mata magana saita tafi" ta k'arasa fad'a cikin kuka sosai"Lokaci guda Jikin MD yayi sanyi a sanyaye ya ce"Bata raye ne?kanta sadde ta daga masa kai"Sosai MD yaji wani irin tausayinta ya kara tsarguwa a ransa Tabbas yasan Rashin uwa Babban gibi ne su kansu mahaifine suka rasa suna damuwa duk sanda suka tunashi bare ita data rasa Mahaifiya Sosai yakejin tausayin yarinyar na ratsa duk wani sassa na jikinsa "Shi mamaci har kullum Addua yake buk'ata ba kuka ba Addua da Sadaka itace kawai take buk'ata wajenki a halin yanzu shine Babban gatan da zaki mata tayi alfahari dake Na Haihuwarki da tayi kuma taji dad'in barin baya da tayi ki daina zubar mata da hawaye har kullum mamaci baya son kuka addua kawai yake bukata " Kasa tsaida kukan zahra tayi ta ce "wannan shine karo na farko dana tab'a ganinta Shima kuma a mafarki ba zahiri ba zanso kullum ta dinga zuwamun koda a mafarkin ne" ta k'arasa fad'a cikin kuka"Janyota jikinsa MD yayi ya fara Lallashinta a hankali ya ce"Kina nufin bakisan mahaifiyarki ba?Gyada masa kai tayi tana Hawaye "Ko baki da wayau ta mutu" muryarta na rawa ta ce "a haihuwa ta ta mutu wai" Allahsrk Allah ya jikanta yasa ta huta yasanya tana cikin Rahama ki daina mata kuka please Addua take buk'ata "Gyada masa kai tayi har lokacin hawaye take lokaci guda kuma Ta firgita tare da mik'ewa " ta wara hannunta ta ce "Ina Kudin da ta bani " ta fad'a tana dube dube Zanin gadon ta zazzaga amma bataga komai ba nanfa tahau sabon kuka ta ce "Dan Allah bakaga wasu kudade ba Masu kamar zinare A fa hannuna ta damk'a mun banyarda na sakesu ba kaga kuma yanzu babu su" Ganin Tana neman zaucewa ya sanya MD Zuwa Inda take ya zaunar da ita ya ce "Ki nutsu Mamy mafarki fa ba Gaskiya bane Dan Kinga Abu ko anbaki Abu a mafarki bashi ke nuna cewa zaki tashi kiga abunba a a wani mafarkin yana mana nuni ne da wani alkhairin ko kuma akasin haka Dan haka bazakiga abunda ta bakiba ki daukesa matsayin Alkhairi" Tana Goge hawayenta ta ce "Kuma fa cewa tayi na bawa jikokinta kowa d'aya guda Ukku ne ta bani Amma banga ko d'aya ba" Nazari MD ya fara Tabbas akwai isharar da mahaifiyar ta takeson yi mata a mafarkin nan amma Kuma dole ne ya samu ya nutsar da ita kar mafarkin ya gigitata yinin ranar haka dai zahra tayini sukuku MD shi yayi kokari wajen ganin ta cire mafarkin nan a ranta Tundaga ranar zahra bata Kara yunkurin Zubar da Cikin ba sannan duk lokacin data tuna da mafarkin da tayi saitayi hawaye sosai ta k'ara duk'ufa wajen yiwa mamanta Addua MD ko gidan marayu dake Abuja da yake tainakawa da kayan abinci yakai da niyyar Allah ya kaiwa mahaifiyar zahra ladar sosai tausayinta ya nunku a cikin zuciyarsa sanin cewar marainiyace da yayi kulawa ta musamman yake bata ita da abunda ke cikinta hankalinsa ya kwanta sosai Ganin bata Kara masa yunkurin Zubar da Cikin ba Bangaren zahra koda ta warware daga mafarkin nanfa ta k'ara tuburewa akan ta gaji da zaman gidan ya maida ita gaban iyayenta ta shirya yi musu bayanin koma meye MD ji yake bazai iya barinta ta tafi ba matukar ba haihuwa tayi ba Bangaren Ammy sosai ta shiga kogin tunani jin muryar mace da tayi a wayar MD Wanda ta tabbatar da ba Amira bace sosai hankalinta ya tashi karfa Dan nata ya halaka ya fara neman mata tunda tasan daman Chan hakuri yake da Amera sunan suna da Aure ne hankalin Ammy inyayi dubu ya tashi Tsoranta kar MD mace ya Aje a abujar ta d'auke masa hankali har baya zuwa kd Duka ina kd ina Abuja kullum adduarta akan Allah ya tsare mata d'an nata daga sharrin zina Bayan wata biyu Wanda cikin watanninan zahra kamar a k'aya tayisu dukda kulawar da MD ke bata duk kwana biyu likita yakan zuwa har gida ya duba ta saboda taki yarda suje asibitin a haka dai MD yana Daurewa yanzu cikin watansa Bakwai ba yan kwanaki amma zakuyi mamakin irin girman da yayi kamar yanzu ne.Lokacin haihuwar sosai zahra ta fara tsorata da irin nauyin da Cikin yayi mata da kuma irin motsin da takeji Bangaren Asmy kullum cikin fargaba da tashin hankali take na Rashin zahra wata Ukku sai yanzu taga Rashin kyautawarta na barin MD ya tafi da zahra da tayi a halin yanzu tanason fad'ar abunda ya faru Dan tagaji da boye boye amma tana tsoron halin da Baba zai shiga baigama warkewa ba Kuma yaji wannan sabon labarin na Auren zahra bada masaniyarsu ba Yau suna waya da Chuchu daga bangaren Chuchu ta ce"a Gaskiya Asmy baikamata mu zuba ido akan al'amarin nan ba sai daga baya nayi tunanin kwata_kwata kinyi hauka na barin mutumin nan d'aya tafi da zahra Bakisan mutum ba,bakisan garinsu ba ,bakisan sana'arsa ba wata kila d'an yankan Kaine ma ko d'an sayar da mutane Ki barshi ya tafi ita Wanda ke kanki bakisan Inda zai kaita ba haba asmy Haba ya kamata mu bincika al'amarin nan mu gano Inda y'ar uwarmuce take karta kuma shiga wani halin data shiga a baya "Asmy na hawaye ta ce " Wlh Chuchu duk banyi wannan tunanin ba sai yanzu da kika fada hankalina ya k'ara tashi innalillahi wa inna ilaihiraji'un wlh chuchu ki yarda kwalwata bata aiki yanda ya kamata wani gamin innayi Abu kamar mahaukaciya Bayan Babban kuskuren da muka tafka a baya yanzu ma na sake wani a Gaskiya banyiwa zahra adalci ba wlh Chuchu saboda banason ta shiga wani hali yakesanya nake aikata irin wannan abubuwan yanzu Dan Allah meye mafita ta ina zamu ganosu"Numfashi Chuchu taja ta ce "hanyar farko na wajenki ina shi abokin nasa da kuka had'a abun tare kuna waya dashi"? bama waya yayi bloack Dina tun lokacin da muka nemu saki"turkashi Chuchu ta fad'a kafin ta ce 'Kina da number sa to har yanzu"Cikin Sauri ta ce "Eh Eh" Ayawwa to yanzu kinsan yanda za ayi ke kika kirasa ganewa zaiyi zamu shirya masa plane idan yasan wata ai basu san wata ba turoman number tasa a message yanzu zanyi masa plane d'in dazan gano address dinsa Kinga daga nan munkamasa shi zai fad'a mana dole inda abokin nasa yakai zahra"cikin farinciki Asmy ta mik'e ta ce "Alhmdllh Gaskiya Chuchu kina da kwalwa me kyau wlh bantaba tunanin wannan ba bari namaza na turo maki" tana katsewa Chuchu taji shigowar message Number ta d'auka ta fara kwafewa a wayarta harta gama kwafa zaro idanu tayi ganin Fitowar number jaber baro b'aro a jiki kara sanyawa tayi taga again number tasa ce gabanta na fad'uwa ta kira Asmy ta ce "Sis inaga fa wrong number kika turo mun ki duba please" A a a banturo maki whrong ba daidaice wlh saboda copy dinta nayi na sender maki Kinga Ko ai daidaice kuma saida na duba sosai "Cikin tsananin firgice Asmy ta ce " ya sunansa"Jabir"Asmy ta bata amsa kai tsaye"jabir"Chuchu ta maimaita da karfi"Eh sis Jabir lafiya?Cikin Sauri ta ce "Ya sunan abokin nasa da ya auri zahra?Mustapha sunansa na mance sunan Baban nasa amma akwai a videon d'aurin Auren" Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Chuchu ta shiga nanatawa cikin zuciyarta kardai ace Yayanta ne ya auri zahra?danson tabbatarwa ta ce "Ki turoman da video din d'aurin Auren yanzunnan a what's app Dan Allah" Sosai Asmy tayi mamaki rudewar na Chuchu dukda a waya ne Ta ce "to bari na tura maki" Tuni zufa harta karyowa Chuchu What's apo tahau tashiga Asmy tayi ta jiran taji shigowar sako VA ayi minti biyu ba taga shigowar video hannunta har karkarwa yake tayi saurin budewa ta fara Duba d'aurin Auren Ga MD a zaune har zuwa Inda Liman ya daura Auren zahra yusuf da Mustapha dikkko" abun saiyazowa Chuchu tamkar almara Tabbas Yayanta ne Daman Yaya shine Wanda ya auri zahra kenan?Shine uban cikin dake jikinta,Shine ya gudu da ita kenan"Innalillahi wa inna ilaihiraji'un ta shiga furtawa da karfi lokaci guda ta firgice batasan lokacin da kuka yaci karfinta na ta ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un shikenan Dara taci gida Kamar wacce aka zabura haka ta mik'e tare da rugawa da gudu bata zarce ko ina ba sai d'akin Ammy Inda ta sameta kan prayer mat tana lazumi cikin kuka da rud'u Chuchu ta mik'awa Ammy wayar tace " Ammy amsa ki Kalla abun Al'ajabi da mamakin Dana gani Ammy "Lafiya Auta meye zangani karki dagamun hankali" Ammy ta fad'a"Ammy ki fara Kalla ki gani kafin nayi miki bayani "Hankalin Ammy dukba kwance ba haka ga amsa ta fara Kallon videon har takai karshe zuciyarta chunkushe kanta gaba daya ya kulle Da ganin wannan rikitaccen al'amarin Kallon Chuchu tayi hankali tashe ta ce " me hakan ke nufi Chuchu yaushe babana yayi Aure bamu sani ba "cikin kuka Chuchu ta kwashe labarin komai da Asmy ta fad'a mata da abunda ya faru gidansu zahra na zargin cikin da komai bata boye wa Ammy ba " Innalillahi wa inna ilaihiraji'un kawai Ammy ke maimaitawa sosai Abun yazo mata tamkar saukar aradu a ka Jin abun take tamkar almara batasan lokacin data fara hawaye ba ta ce "Babana yabani mamaki bantaba tsammanin haka daga garesa ba dukda Aure ne amma baikamata suyi Aure ta wannan hanyar ba a Gaskiya ba a kyautawa Yarinyar nan ba kawarta da Babana da Jabir sun cuceta " Cikin kuka Chuchu ta ce"Ammy ita Asmy ba laifin ta bane Allah duk laifin su yaya ne Kinga su Suka tsoratata akan zata rasa ta shysa tayi haka"Goge hawayenta Ammy tayi ta ce "Hakane Maza kiramun Jabir kice duk Inda Yake inason ganinsa saiyayimun bayanin dalilinsu na na yin haka wlh zasu fuskanci b'acin raina da basu tab'a gani ba Dan iskanci idan aure yake so ba har lokaci Hajiya ta basa yayi ba Dan Raini da wulakanci Shine zaije yayi Aure a b'oye su wulakanta yarinya maza kiramunshi" Chuchu na laluben number Jabir harta samesa ta kira yana d'auka Ammy ta amshe wayar cikin fushin da baisanta dashi ba ta ce "Na baka nan da minti Talatin kome.kake ka sameni a gida" hankali tashe ya ce "Lafiya Ammy?Inkazo zakaji koma.meye minti Talatin na baka" tana gama fad'ar haka ta katse wayar tana huci minti Talatin bai cika ba Jabir ya iso gidan yakira Chuchu ya shaida mata yana palour baki daya suka fita palourn Wanda kallo d'aya zakayiwa Ammy kasan ranta a matuk'ar b'ace yake "har kasa Jabir ya gaisheta ya ce " Ammy Lafiya wannan kiran gaggawar"tana binsa da harara ta ce "ba lafiya ba munafukai watau daman da munafurci da kuka k'ulla k0 to asirinku ya tonu munji komai Abu d'aya nakeso ka fad'amun gaskiyar magana yanda take kuma wlh ka sake kamun karya zaku fuskanci Karin wulakancin da zan muku daga kai har babana fad'amun Gaskiya Had'in baki kukayi da Dr wajen Auren zahra sannan dalilinku nayin hakan wannan amsar biyu kawai nake buk'ata" Hankali tashe Jabir ya d'ago yana Kallon Ammy tuni harya fara zufa cikin muryar Rashin Gaskiya ya ce "Ammy wa ya fad'a maki maganar nan" ya fad'a a rarrabe "Ammy nabinsa da harara ta ce " a tunaninki bazamuji ba ko To asirinku ya tonu Daman ance rana d'aya ta barawo rana d'aya tame kaya ba bani amsar tambayar da nayi maka fak'ad"Ammy ta fad'a cikin d'aga murya"Innalillahi Jabir ya shiga nanatawa a ranshi Tabbas dole ne ya fad'awa ammy Gaskiya Dagowa yayi kallo d'aya zakayi masa kasan ba Gaskiya ya ce "Ammy zanyi miki bayanin komai Amma Dan Allah kiyi hakuri sannan karkiyi fushi" Inajinka oya ka fad'amun karka dinga b'atamun lokaci"numfashi yaja kafin ya labartawa Ammy komai d'aya faru bai boye mata komai ba saboda daman yasan da irin wannan ranar dukda yayi mamakin yanda akai Ammy tasan da maganar Salati Ammy tayi ta tafa hannu ta ce "Naga ta kaina ni Fatima daman a saboda Amera ne kuka aikata wannan Abun kunji kunya kun rako maza wlh Babana yaban mamaki bantaba tunanin zaiyi irin wannan Rashin imaninba Ya sanya yarinya a cikin wani hali kawai saboda shegiyar amera kayan bannza kawai a saboda banzar biyan bukatarku kuje ku auri yarinya ba sanin iyayenta Kuyi mata wayau ku tsoratasu kuga mugaye azzalumai wlh babana sai yayi nadamar abunnan d'aya aikata zaisan mu yayiwa haka zaisan zahra ba a banza take ba wlh tallahi saina kwatar mata hakkinta zan mance cewa ni na haifeshi na kwatawa zahra hakkinta tamkar Nina haifeta bana zalinci sannan bana goyon zalinci Kenan so kukayi ku cuceta ta haihu ku kaiwa waccen y'ar Iskar d'an da ita kanta tarbiya bata isheta ba bare harta tarbiyar da wani mu kuma ayi mana lullubi ko to ai dayake a cikin abun ba Allah gashinan asirinku ya tonu hada had'o karyar Amera ta samu ciki toni bansan wannan wani irin so da tsoro ne babana yake yiwa amerarnan ba Abu saikace an asircesa A baka damar kayi Aure kawai saboda gudun b'acin ranta kaje ka yi Aure a b'oye ka zalinci yarinyar mutane wlh Duka a cikin abunnan banga laifin Zahra da Kawarta ba ko Kad'an kune manyan mugayen da kuka tilastasu suka amince muku macuta mayaudara Tsaffin munafukai Ka tashi kaban wuri wlh saikunyi mamaki na Akan Lamarin nan daga kai har shi Babban munafikin sannan Ka fad'amun gidan da yake idan ka fita saika kirasa ka fad'a masa ga yanda mukayi kace ya gudu da ita kaga abunda zai faru"Jabir dukya tsure ya ce "Dan girman Allah Ammy kiyi hakuri wlh nikaina nayi Nadama tsaki Ammy taja tace" ai nadama baku fara ba ma ka fad'amun gidan da yake da ita " kasa yayi da kansa yace "buzu quarters "Mikewa Ammy tayi ta ce " Saura kakirasa ka fad'a masa munyi haka tunda kunsaba munafurci tare "Kasa yayi Jabir da kansa yana muzurai saurin barin palourn Ammy tayi Chuchu dake tsaye duk tayi shock kafafuntama ji tayi sun kasa daukarta sosai Abun yazo mata yanda bata tab'a tunani ba wai Yayanta ne Mijin zahra kuma shine uban cikinta Shine sukayi *Auren wata tara* da ita idan ta tuna saitaji kamar almara Kallon screern din wayarta tayi ganin kiran da Asmy ke mata mema zata ce mata " Muryar Jabir ce ta dawo ita daga dogon tunanin data Lula ya ce "Chuchu please waya fad'awa Ammy zancen nan taya tasan wannan din" Turo baki gaba tayi Dan duk haushinshi takeji har yayan nata ta ce "Saika bi Ammyn ka tambayeta" tana gama fad'ar haka ta juya "Mikewa Jabir yayi zuciyarshi chunkushe da tunannika ta wani bangaren kuma yaji dadin da Ammyn sukasan da maganar ko ya fita daga sarkarkiyar d'aya shiga tsaka Baiyi yunkurin kiran MD ba Koda wasa Dan yasan yana fad'a masa guduwa zaiyi da ita koma subar k'asar Wanda bazaiso hakan ba Tunda asiri ya tonu gwara kawai ta fanjama " Ammy sosai ranta ya b'aci Hijab kawai ta sanya da takalmi ta fito Chuchu ta biyota ta ce "Ammy ina zaki kuma Yamma tayi fa" daga mata hannu tayi ta ce "Ki koma yanzu zandawo zanje na taho da yarinyar nan tun yanzu kafin abokin munafurcin nasa ya kirasa " Ajiyar zuciya Chuchu ta sauke Ammy na fita ta kwalawa driver kira Ta ce ya kaita Abuja cikin Sauri "Ba bata lokaci motarsu ta dauki hanyar Abuja ana gab da magriba Suka isa Kai tsaye buzu quarters suka nufa......MD na zaune a Palour ya na dafe da kansa Saboda yau ba k'aramun kuka zahra tayi masa ba akan ya maida ita gidan iyayenta ga Allah ya isa da ta dinga ja masa yau ko.abincin kin ci tayi duk ta chaza masa kai yajiyo knking Kamar bazai Mike ba saikuma yaje ya bud'e gabansane ya bada daram cin karo da Ammy tsaye fuska ba wasa lokaci guda Alamun Rashin Gaskiya suka bayyana k'arara a fuskarsa a rarrabe ya ce " Am my "ka bani hanya na wuce " Ammy ta fad'a a tsawace 'sosai yayi mamakin abunda baitab'a gani daga Ammyn nasa ba Hankalinsa sosai ya tashi waigawa yake Kar zahra ta fito Ammy ta ganta asirinsa ya tunu"tsawar da Ammy ta daka masa ce ta sanyashi matsawa ba shiri daidai sanda zahra ta fito daga daki cikin doguwar Hijab Fuskarta jab'e jab'e da hawaye Tsaye Ammy tana kallonsa tana kallon zahra sosai zahra tayi mamakin Ganin Ammy a gidan Gabanta banda fad'uwa ba abunda Yake Sosai ran Ammy ya k'ara b'aci tunkarar wajen zahra Ammy tayi tare da kama hannunta tajata itadai zahra binta kawai take har suka isa Inda motar take ammy ta ce "shiga " ba musu zahra ta shiga motar Kallon Ammy MD d'aya biyosu yayi cikin tashin hankali ya ce "Ammy" Daga masa hannu tayi cikin Tsawa ta ce ..............✍ *Domin magana da marubuciyar 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙 🅿️.......*81 & 82* "karka Cemun komai baka da bakin da zaka fad'amun wata magana "Sannan ta kalli driver tace jamu" Bayan Inda Zahra take Ammy ta zaga ta shiga "Motarsu ta tashi sosai zahra tayi mamakin Ganin Ammyn Chuchu me ya kawota gidan meye alakarta da Musty" Ganin ba amsa ya sanyata hade kai da gwuiwa tana hawaye "A sanyaye Ammy ta ce " Kidaina kukan nan kar kanki yayi ciwo"Duk yanda zahra taso shiru kasawa tayi Ammy na ganin haka ta janyota jikinta tare da Fara Lallashinta ta ce "Kiyi hakuri insha Allahu komai yazo karshe " Shiru zahra tayi tunani chunkushe a kwalwarta kafin bacci ya kwasheta a jikin Ammy tayi baccinta kallonta kawai Ammy take tana jin tausayinta na ratsa ta yarinyar abar tausaya wa ce Kamar yanda Chuchu ta bata labari ga maraici ga kuma halin da MD ya jefata Har mahaifinta ya shiga wani hali banda zargin mutane Har suka isa gida zahra batasani ba saida Ammy ta tasheta ta ce "Tashi Daughter munzo" a sanyaye zahra ta fito daga motar sosai tayi mamakin Ganin saukarsu gidan su Chuchu dan bazata mance gidan ba kama hannunta Ammy tayi a hankali take binta saboda cikinta da taga yayi girma har suka isa Babban palourn ita dai zahra na biye da ita Suna shiga palourn zahra tayi ido hud'u da chuhu Da gudu chuhcu ta Ruga tare da Rungumeta Da karfi saikuma ta sanya kuka Ammy ce ta ce "Ki bita a hankali Maryam bakiga yanda take " tsagaita kukan sukayi suka zauna Kan sopa Chuchu na dubar zahra dake hawaye Goge mata hawayen tayi ta ce "Kina.Lafiya sis?Gyada mata kai tayi har lokacin hawaye zahra take " Ajiyar zuciya Chuchu ta sauke ta ce "Kiyi hakuri momcy insha Allah komai yazo karshe Mikewa Chuchu sukayi tare da zahra Kallon Ammy da har lokacin ranta b'ace yake tayi ta ce " Ammy zamuje ciki"Okay tafada maki abunda take so a girka mata sannan ta huta sosai "To Ammy " Chuchu ta fad'a tana kama hannun zahra "Ki bita a hankali fa wajen hawa stairs " To Ammy Chuchu ta fada "koda suka isa d'akin Chuchu kasayin shiru zahra tayi Dan tun d'azu zuciyarta cike take da Tambayoyi Kallon Chuchu tayi ta ce " Sis Dan Allah na.tambayeki"Murmushi Chuchu tayi mata ta ce *bama saikin tambaya ba zanyi maki bayanin komai yanzu dai kiyi salla ki fad'a abunda kike so kici "numfashi zahra taja ta ce " Banason cin komai "wara idanu Chuchu tayi ta ce " taya zakice bakisoncin komai inke bakya so Unborn d'inmu yana so"Hararar wasa zahra tayi mata ita kunyar cikin nan ma take ta kauda kai Chuchu ta Kalleta ta sake cewa "please me kike son ci Dan Allah kinsan Na fad'awa Ammy Bazakici abinci ba fad'a zata maki " nafa koshi "ta bata amsa " okay bari naje na fad'awa ammy"Chuchu ta fad'a tana Mikewa saurin Rikota Zahra tayi ta ce "Ki bari mana karkije ki fada mata naji zanci koma meye " a a a ki fad'a a girka maki"girgiza mata kai tayi ta ce "Duk abunda kukayi zanci" Shikenan Chuchu ta fad'a ta ce "Bari naje na had'o maki ruwan wanka" gyada mata kai zahra tayi har lokacin mamaki take "Bayan Chuchu ta fito daga bathroom d'in Kallon zahra tayi ta ce " na hada kishiga kiyi bari naje na dawo"Okay "ta fad'a tana Mikewa a hankali Ta shiga toilet din sosai taji dad'in Wankan saboda ruwan dumin da Chuchu ta had'a mata Bayan ta gama ta d'aura towel a bakin gadon taga kaya marassa nauyi da Chuchu ta Aje mata d'auka tayi ta sanya tare da sanya Hijab tayi magrib da isha'i tana lazumi Chuchu ta shigo da plate din Farfesun naman rago d'ayan kuma lafiyayyan shinkafa da miya ce Samanta anyi yanke yanken kayan lambu da itama Tasha naman kaji a sama y'ar aikinsu da suka shigo Tare tazo gabanta ta Aje jug din dake d'auke da kunun Gyada da yasha madara cikin girmamawa ta ce " Ina yini Hajiya"Ina yini Zahra ta mayar mata Bayan barin mai aikin d'akin nan Chuchu ta tisata gaba saida ta kusa cinye naman shinkafarce ma ta kasa ci saboda kunun gyadar da ya cika mata cikin Dan sosai taji dad'inshi wajen 10 harsun kwanta ganin Chuchu bata da shirin mata wani bayani ya sanyata cewa "Baki fad'amun komai ba Chuchu" Shiru Chuchu tayi tanajin nauyin ta fad'awa zahra Yayanta ne yayi mata haka dak'yal ta iya tattaro jarumta ta ce "Tun ranar da yatafi dake Asmy tafadamun komai na *Auren wata taran* da kukayi wlh sis bantaba sanin yayana bane yayi miki haka sai dazu" mamaki cike da Cikin zahra ta ce "Kamarya Yayanki" Shiru Chuchu tayi kafin ta labartawa zahra komai d'aya faru har suka gane Yayanta shine ya aureta shiyasa har Ammy taje ta d'auketa sannan Chuchu ta Goge hawayen da suka zubo mata tana kama hannun zahra ta ce "Dan Allah sis kar dalilin wannan yayi sanadiyar shafar zumuncin mu nasan a halin yanzu ba Wanda Kika tsana sama da yaya na Dan Allah kiyi hakuri kar abunnan ya tab'a zumuncinmu" Sosai zahra tayi mamakin jin cewa Yayan Chuchu da take yawan musu zancenshi shine Mustaphan wannan shiru tayi mamaki duk ya gama cikata kenan d'an Ammy ne "Kinyi shiru sis bakice komai ba " Chuchu ta fad'a"Sai sannan zahra ta d'ago ta kalli Chuchu ta ce "Nayi mamaki ne sis Inajin bacci mu kwanta " Shiru Chuchu tayi duk tayi sanyi ganin yanda zahra tayi ta ce "Dan Allah sis kiyi hakuri ki daukeni tamkar y'ar uwa kar laifin yayana ya shafeni" Kirkirar murmushi Zahra tayi ta ce "Kibar maganar nan Chuchu babu abunda kikayimun mubar maganar kawai" Chuchu najin haka ga sauke ajiyar zuciya kwanciya zahra tayi kan makeken bed din Chuchu ta lumshe ido bacci take so ya d'auketa amma tunani ya hana....bangaren MD tashin hankalin daya shiga bana wasa bane cikin Sauri ya kira Jabir a waya bai samesa ba Innalillahi wa inna ilaihiraji'un kawai yake maimaitawa kafin yayi Sauri ya fito ya kwalawa driver dinsa kira kai tsaye Airport ya nufa ya wuce Kaduna koda isarsa gidansa dake nan din g r a ya nufa Yana son zuwa gidan Ammy amma baisan me zata masa ba saboda yasan tsananin fushi Ammy take dashi sosai yayi mamakin ya akayi Ammy tasan da maganar nan d'ayar number Jabir ya kira nan yaci sa. a ya d'auka baima jira komai ba ya ce "Kana ina Jabir ka maza kazo gidana dake gra ina kd akwai matsala babba" Daga bangaren jabir yasan daman da haka Koda Jabir yazo gidan Cikin tashin hankali MD ya ce "ya akayi Ammy tasan da maganar nan Jabir Bayan kasan dagani saikai sai Dr Aliyu sai ALLAH daga bangarena suka san da maganar nan taya akayi ta fita" Nan Jabir ya bawa MD labarin yanda sukayi da Ammy Shima yayi mamakin yanda sukasan maganar"Sosai MD ya shiga tsananin damuwa Daren ranar da idonsa bacci gagararsa yayi....washegari Around 9:am Ammy ta sanya Chuchu ta kira mata zahra tare suka isa palourn da Ammy take Wanda zahra kasa yarda ta had'a ido da Ammy tayi saboda wani irin nauyinta da take ji "A sanyaye kanta a k'asa ta ce " Ina kwana Ammy"Lafiya qalu takwara ya bakunta"Ammy tafada fuskarta d'auke da murmushi"alhmdllh "Zarah ta fad'a a hankali" shiru Ammy tayi kafin ta ce "D'ago ki kalleni zahra zamuyi magana" Sai sannan zahra ta iya d'agowa amma bata yarda sun had'a ido da Ammy ba tana wasa da yatsun hannunta ta ce "Tohm Ammy"saida Ammy taja numfashi kafin ta fara magana da cewa" Nasan Chuchu tayi maki bayanin komai Ba saina Kara maimaitawa ba ina mai baki hakuri akan dukkan abunda Babana yayi miki Dan banga laifinki ko Kad'an ba Kiyi Hakuri ki d'auki hakan a matsayi jarabawa ce kuma insha Allahu kinkusa cinyeta abunda nake so dake ki kwantar da hankalinki waje Daya ki nutsu kiyi hakuri Nasan anyi miki ba daidai ba ki daukeni tamkar mahaifiyar da ta haifeki karkiyi d'ari_d'ari dani ina son ki zauna a wajena ne Har ki haihu kafin muga yanda Allah zaiyi na bincika na samu labarin mahaifinki yanzu yaji sauk'i yana garin danginsa kiyi hakuri ki zauna damu har zuwa lokacin da zaki haihu saimuje tare ayiwa iyayenki bayani sannan a basu hakuri Sannan Abu na gaba da nakeson fad'a maki Ko babana yazo gidannan kar wani Abu ya k'ara hadaki dashi ko ganinsa kikayi kibar wajen kada wata alaka kota magana ta kara hadaki dashi karki sake ki sake masa fuska koda wasa kinji na fad'a maki " gyadawa Ammy kai tayi Alamun taji"Ajiyar zuciya Ammy ta sauke ta ce "Yawwa to Allah yayi miki albarka ya Rabaki da abunda ke cikinki lafiya " Shiru tayi Chuchu ta amsa da ameeen "ga Dr nan zaizo ya duba ki yanzu ki tabbatar kin karacin abinci sannan ta kalli Chuchu ta ce " ki kulamun da ita sosai Kuje Kuyi break fast an shirya muku a dining dake sama "Daman zahra so take Ammy tace Su tashi saboda jinta take kamar a k'aya tare sukayi break fast da Chuchu kafin Su fara hira sosai Chuchu ta dinga Jan zahra da Hira Wanda har saida ta samu da wartsake wayarta Chuchu ta jawo ta ce " Bari na kira Asmy nayi mata albishir"Lokacin da Chuchu ta kira Asmy tana kwance zazzabi ya rufeta daga bangaren Asmy ta ce "Tun jiya nake jiranki bakya d'auka nakagara Naji yanda kukayi dashi" murmushi Chuchu tayi ta ce"AI Albishir na kira na miki gama momcyn nan a kusa dani"Asmy batasan sanda ta mik'e ba ta ce "Da gaske ko wasa" Dariya Chuchu tayi ta ce "Ga kat ki gani" ta fad'a tana bawa zahra wayar murmushi tayi ta k'ara wayar a kunne a hankali ta ce "Hello sis" Ai Asmy batasan sanda ta buga ihu ba ta ce "wayyo Allah Alhmdll Alhmdllh Zahra kece kuwa" Murmushi zahra tayi ta ce "Karki batamun dodon kunne da Allah Malama " Dariya Asmy tayi ta ce "ba dole nayi murna ba karkiga yanda nayi kewarki Kina ina" chuchu ta mik'awa wayar Chuchu ta ce "tana gidannanmu" Gidanku kuma ina kika sameta "Dariya Chuchu tayi ta ce " akwai labari baya fad'uwa a waya"Aiko gani nan zuwa yanzu"duk daukarsu wasa take basu yarda ba da zatazo sai Bayan two hours data kira Chuchu ta ce "Na Iso kizo ki tafi dani security sun hanani shiga" Da mamaki Chuchu tace "waida da gaske kike gani nan" Tana fita suka shigo Tare da chuchu Asmy na ganin Zahra batasan lokacin da taje ta Rungumeta ba ta ce "I really miss you so much My Dear nayi kewarki over kafin kuma ta Goge hawayen da suka zubo mata ta ce " kina ina tsawon watannin nan zahra"Shiru zahra tayi mata saikuma ta sauya hirar da cewa "Yagida yasu Mama Ya jikin Baba" murmushi d'auke da fuskar Asmy ta ce "kowa lafiya qalau Baba yanaji sauki yana Batsari jiya ma su Mama sunje duba sa sunce ya warke sosai Dukda yana tambayarki " Goge hawayen da suka zubo mata zahra tayi sosai takeson ganin Baban Nata ko taji sanyi a ranta Sosai suka sha Hira da Asmy Sosai sukaji dad'in ganin juna dukda Zahra bata da wata sakewa sosai da fara'a fuskar asmy ta kalli cikin zahra ta ce"tubarakalla sis ji yanda cikinki yayi girma saikace yanzu ne lokacin haihuwar"Harararta Zahra tayi tare Jan tsaki ta kauda kai "Dariya Asmy tayi ta ce " Daga magana Sorrry Harna k'agara naga Unborn d'innan Na *Auren wata Tara* sosai zahra ta k'ara shakuwa tsaki taja tare da mik'ewa ta shige ciki Dariya Asmy tayi ta ce "Wlh Chuchu zahra duk ta sauya hali dukta zama wata jarababbiyar karfi da yaji" inaga fa Cikin nan ne ya sanyata haka"Uhm kuma hakane Allah dai sauketa lafiya "Ameen Chuchu ta fad'a Asmy ce ta ce " bakiban labarin yanda akayi kuka sameta ba "A sanyaye Chuchu ta labartawa Asmy cewar yayantane " Sosai Asmy tayi mamaki jin cewar da Yayan Chuchu akayi haka no wonder kamarsu da Ammy daman ta baci Dan tun sanda sukaga Ammy suka San tana tsananin kama dashi ta wani bangaren Asmy taji dad'i da abun yazo da sauki tasan Ammy mutuniyar kirki ce Zata kula da Zahra sannan zata fahimtar dasu Baba Ita yanzu chuchu Tsoranta bai wuce Zahra ta gane Yayanta shine MD d'innan data tsana tasan tsanarsa ninkuwa zatayi a ranta "Sai yamma Asmy tayi musu bankwana zata wuce bayan taje ta gaishe da ammy Inda Chuchu ta sanya driver ya kaita har gida sosai Asmy taji Kashi tamanin na damuwarta ya ragu zahra ko saitaji ba dadi da asmy ta tafi koda taje gida ta yanke shawarar fad'awa iyayenta Maganar Gaskiya dukda tasan zasuyi mata fad'a mamanta ta samu a tsorace ta labartawa mata komai " salati mamansu tayi ta salamce "sosai ta shiga yiwa Asmy fad'a kamar ta doketa ta ce " daman ashe kece kikayi silar shigar zahra wannan halin kece silar komai Dan Ubanki ita kuma ta biyeki to ai gashinan kinja mata "fad'a sosai maman su Asmy take Inda asmy ke bata hakuri daga karshe kuma ta godewa Allah da Cikin zahra ya kasance ta hanyar aure aka samesa ba hanyar banza ba dukda dai tasan mutane ba kowa zai fahimta ba har videon d'aurin Auren saida Asmy ta nuna mata Dan ta tabbatar.....Shiru MD yayi gaban Ammy yama rasa abunda zaice mata saboda tun gaisheta da yayi ta amsa a takaice bata Kara ce masa komai ba " Dak'yal yayi jarumtar cewa "Ammy Dan Allah kiyi hakuri" Me kayimun da zaka bani hakuri "Ammy ta fada'"Shiru ya sake kafin ya ce " Ammy nasan fushi kike dani Dan Allah kiyi hakuri Bazan iya jurar fushinki ba "murmushin da yafi kuka ciwo Ammy tayi ta ce " Ah ah ni ai baka tsoron fushi na ga Amira uwarka data haifeka ta kawoka duniya ita kake shakka kake tsoron fushin ta baniba "Omg MD ya fad'a ya ce " Ammy ba haka bane nasan ban kyauta ba ki tsaya nayi maki bayani"Daga masa hannu tayi ta ce "ba bayanin da zakayimun " duk yanda yaso Ammy ta sauraresa kin sauraransa tayi kullum.MD saiyayi zarya gidan Dan son shawo kan Ammy amma bata kulawa wani lokacin ma tashi take ta basa wajen Dan ba abunda yafi mata ciwo kamar idan ta tuna wai Dan Matar d'aya aura a boye ta haihu suce mata Dan ko d'iyar ya mutu ya kaiwa Amera ace ita ta haihu idan ta tuna wannan Abun sosai takejin zafi a ranta tana tunanin yaushe MD ya zama marar imani haka a saboda da matarsa ya saka wata cikin wani hali hakan yasa ko tayi shirin sassauta masa take fasawa sosai MD ya shiga damuwar da bai tab'a shiga irinta ba ga sosai yakeson ganin Zahra saboda ya ganta kullum yana gidan Amma ko giccinta baya gani mamaki yake to ina Ammy ta kaita yauma yana zaune a palour shida Ammy dake kallo tayi banza ta kyalesa cikin dauriya ya ce"Ammy bazan gaji da baki hakuri ba Dan Allah ki yafemun"Kallonsa ta k'asar glass Ammy tayi taga harya rame.sosai yaso bata tausayi amma ta fusge ta ce "Na fad'a maka ka daina bani hakuri me kayimun " Shiru yayi yana sauke numfashi kafin ya d'ago ya ce "To Ammy Ina Mamyn ina kika kaita" wacece haka?Ammy ta tambayesa dukda tasan da wacce yake Dan baya fad'ar mai irin sunanta "Saida tadanyi shiru kafin ya ce " Takwarar taki"Wani irin kallo Tayi masa ta ce "Ina ruwanka da ina take ai babu wani abu tsakaninka da ita Illa iyakar ta Haifa maka abunda ke cikinta a ranar ta mik'a maka Ka kaiwa Matar gold Matar so da tafi duka mata kyau da Asali "Innalillahi " MD ya fad'a a ransa Kafin ya ce "Ammy ba haka bane Dan Allah"Tsaki Ammy taja ta mik'e ta ce " idan kagama zaman ka rufemun palour "Dafe kansa dake Sara masa MD yayi Yasan tsananin fushi Ammy take dashi kafin ya ce " Allah yasa basu fad'a mata haka ba ta k'ara kullatuwa dani"Tunani yake ina take,sosai yakeson ganin ta yanda shi kanshi baiyi tunanin zaiso ganin wani Abu da yayi kewa kamar yanda yake son ganinta ba wayarsa ya janyo tare da kiran Chuchu yace "Kizo ina son ganinki palourn k'asa" koda Chuchu tazo sosai tayi mamakin Ganin ramar da Yayan nata yayi Daka Kalleshi kasan baya cikin yanayi mai dadi dukda yaji haushin abunda yayi kusa dashi ta zauna ta ce "Ina yini Yaya" Lafiya qlau "ya bata amsa a takaice tana ganin yanda ya had'e fuska tamau" Ina Mamy"ya tambayeta"Shiru tayi tana nazarin. Wa yake nufi da haka Kallonshi tayi ta ce "Yaya ko Momcy kake nufi " a takaice ya ce "Eh " Ohh tana sama Bacci ma take"Nauyayyar Ajiyar zuciya taga ya sauke kafin ya Mike ya nufi hanyar sama "binshi da gudu Chuchu tayi ta ce " Dan Allah karkaje Ammy ta hana fad'a zatayi mun"Hararar d'aya watsa mata ce ya sanyata Jan bakinta tayi shiru yana haurawa sama kai tsaye d'akin Chuchu ya nufa Yana shiga ya sameta kwance tana bacci hankali kwance daga ita sai wata doguwar rigar Chuchu kasancewar rigar bata da nauyi yaba cikinta damar bayyanuwa a hankali MD ya zaune gefen gadon saitin da take kafeta yayi da Kallo bako k'iftawa beauty face d'inta kawai yake kallo Ajiyar zuciya ya sauke koba komai ya rage damuwar dake cinsa a hankali ya shafa cikinta tare da sumbatar cikin ya ce "I love you more my unborn Allah ya fito mun da kai/ke Lafiya Ganin tayi motsi kamar zata tashi ne ya sanyasa saurin matsawa ganin ta koma bacci ne ya sanyasa sauke ajiyar zuciya saida MD ya shafe 20 minutes a d'akin yana kallonta kafin ya Mike ya fito a palour ya samu Chuchu na chart hanyar fita yayi " Zey na gida"Yafada kamar bashi yayi maganar ba"Eh yaya tana gida Sundawo "bai amsa mata ba yabar gidan kai tsaye MD gidan Zey ya nufa Wanda harya mance rabonshi da gidan Palourn ya zauna yaranta duk sun baibayeshi suna murnar ganinsa sai tsalle suke mai yana musu murmushi da wasa jin suna oyoyo uncle ya sanya Zey ganewa yaya md ne da Fara a tashigo d'akin ta ce " Yaya yau Kaine a gidan namu kamar kayi Batan kai"b'atan kan nayi Shiyasa kika ganni"ya fad'a yana sanyawa Mimi da Daddy sweet a baki "Dariya Zey tayi tana zaunawa ta ce " ina yini Babban yaya"Bayan sun gaisa Ana shirin gabatar masa da abinci ya ce "Ki barshi ina Sauri magana nazo muyi" Kallon su Mimi tayi ta ce "My Daughter My son ku wuce waje mai lesson dinku yazo" Suna barin d'akin MD ya sauke ajiyar zuciya kallonta yayi ya ce "Nasan kunyi magana da Ammy kinji duk abunda ya faru" Jim tayi kafin ta d'ago ta ce "Eh Tun a waya ta kirani ta sanar mani to kasan bama k'asar Duka sai shekaranjiya muka dawo ina ma son zuwa gidan to dadyn su Mimi na gida pull time sai yanzu ya fita ina shirin injema gidan kazo"Okay kinsan da Ammy fushi take dani taki saurarata shine nazo wajenki nasan zaki iya taimakamun wajen shawo kanta" numfashi zey taja kafin ta d'ago ta ce "Insha Allahu Yaya Amma kaima yaya sai nakega baka kyauta ba lokacin da ammy ta labartamun ba karamun mamaki nayi ba wlh Naji yarinyar ancema kawar Chuchu ce " Numfashi yaja ya ce "maganar kyautawa da Rashin kyautawa Duka wannan ya wuce tunda Mai faruwa ta Riga ta faru " Hakane.kam yaya Allah ya kyauta insha Allah zamuyi magana da Ammy"yawwa Zey Thnks ya fad'a tare da mik'ewa yayi mata bankwana ya wuce Abuja wani meeting da aka kirasa a ranar Zey tazo gidan koda ta fara bawa Ammy hakuri Akan ta janye fushin da take akansa ce mata tayi "Zainab ba fushi nake dashi ba ina kwatarwa yarinyar nan hakkintane yasan darajarta tafi yanda yake Tunani" numfashi zey taja ta ce "Kuma fa hakane Ammy Tabbas ciwon y'a mace na y'a mace ne Amma a sassauta masa " Shiru Ammy tayi ta kyaleta "Mikewa Zey tayi ta ce " bari naje mu gaisa"lokacin da ta isa palourn Sama Zahra na saman sallaya tana karatun qur'ani Chuchu na gani Zey ta guda da gudu ta Rungumeta ta ce "oyoyoy My Aunty nayi missing naki sosai ya Paris din " Murmushi Zey tayi tace Alhmdllh Auta "ina su Mimi" Ta tambayeta"Suna gida Ana musu lesson shiyasa bantaho dasu ba dayake ba jimawa zanyi ba "ayya naso ganinsu Ina Tsarabata" Tana Chan kije ki amsa da kanki kinsan dai ba kawo maki zanyi ba y'ar rainin hankali ina yayarki a gari amma saikiyi watanni bakije Inda nake ba ni bama wajenki nazo ba wajen Auntynmu nazo"Dariya Chuchu tayi sai sannan ta kalli Chuchu da ta Aje qur'anin ta ce "momcy ga fa Aunty Zey yayatace daga yaya sai ita saini" Murmushi d'auke da fuskar zahra ta ce "Ina yini" Cikin fara'a zey ta ce "Lafiya qlau momcyn mu ya jiki" Alhmdllh "ta fad'a kasa_kasa" masha Allah Allah ya k'ara sauki bari na wuce saina dawo ina Sauri"Murmushi Zarah tayi ta ce "A gaida gida Kallon zahra Chuchu tayi ta ce " ina zuwa momcy bari na raka aunty"gyada mata kai tayi"Suna fitowa Zey ta kalli Chuchu ta ce "Wlh yarinyar tayimun ji nutsuwa da hankali gata da kyau masha Allah jifa duk yanda ciki kesa ayi muni Amma ita kyanta na nan " Dariya Chuchu tayi ta ce "Ai da tafima haka kyau wlh Aunty bari ta haihu kiga ta koma asalinta " Har suka Iso palour Zey na yaba zahra Zaunawa tayi gefen Ammy ta ce "Wlh Ammy Yaya ya rasa wannan ya yi Babban rashi da asara Dan wlh bazai samu kamarta ba Dan Allah Ammy karki yarda Su rabu Tunda gashi hada rabo tsakaninsu" Harararta Ammy tayi ta ce "Ke daman ai Chan bakinku d'aya babu ruwanki da duk hukuncin da zan yanke dole ya rabu da ita tunda ba kaunarta yake ba jira nake.kawai ta haihu na amayar da duk abunda ke cikina a kansa " Jan bakinta Zey tayi shiru ta ce "Amma Ammy sainakega kamar ba yaro d'ayane cikinta ba jifa girman cikin yakamata ayi scanning asan meye cikin Dan mufara sayayya kar wuri ya K'ure Dan daga gani ta kusa" Nasa Dr yayi mata scaning Nasan komeye ciki harma na sanya ayo order kayan daga Dubai jibi ma zasu iso "Ammy nawane?basaikinji ba ta haihu kingani" Marairaicewa Chuchu tayi ta ce "Dan Allah fad'a mana nima inason na fara sayayyar kayan baby" Jin haka ya sanya Ammy cewa "Triplet ne amma Karku fad'awa kowa koshi ko ita kada Wanda Naji kun fad'awa" Sosai suka Zarah ido a tare sukace y'an Ukku Ammy"Dariya Ammy tayi ganin yanda sukayi Chuchu ta buga tsalle ta ce "Wayyo Allah dadi wlh Ammy karkiji yanda na k'agara Momcy ta haihu naga jinin yaya wayyo Allah y'an Ukku a gidannan" Zey ko hamdala tayi ta ce "Allahsrk yaya Double Allah yayi masa Ammy Banmasan wani irin farinciki nake cikiba" murmushi d'auke da fuskar Ammy tace "baku kaini farinciki ba Zey ranar da aka fad'amun kwana nayi ina Godiya da Allah Dan al'amarin nan gaba d'aya ikon Allah ne Amma Karku fad'a musu Kuyi sayayyarku kawai" Insha Allah Ammy bazasuji ba "Tundaga ranar Zey tahau uwar sayayyya komai Ukku takanas ma kawarta takira dake Paris tatura mata kudi akan tayi mata sayayyar kayan jarirai na triplet yawan kudin ma data tura mata saida nayi mamaki yanda kasan ita ce Zata haihu cikin sati uban kayan suka iso akwai kusan goma banda abun goyon jarirai na ciki irin na turawan nan shima komai ukku Chuchu ma Sosai take jibgarta sayyya itadai zahra nata ido bata tab'a tanka mata akan sayayyar dataga tana lubgowa ba Ammy ko ba amagana Dan har kekunan wasa yara saida ta sayo daki guda ta ware ta cika kayan jarirai dashi da gadon kwanciyarsu keken koyon zama kai komai Wanda wani ma baka tab'a ganinshi ba saida Ammy ta had'o mai gayya kwa mai aiki kwata kwata hankalinshi baya jikinshi baimayi tunanin fara wata sayayya ba duk yanda yaso koda ganin Zahra Ammy ta kasa ta tsare bangaren zahra ba laifi zaman gidansu Chuchu yayi mata dadi saboda wata irin kulawa da suke bata a halin yanzu cikin zahra ya shiga watan haihuwa sosai Ammy da Chuchu suka ninka kulawar da suke bata kaffa kaffa suke da ita sosai dan sosai Ammy ke tausaya mata nauyin cikin yara Ukku ba wasa yau zahra tunda ta tashi takejin sauyi tattare da ita Hakanan dai ta daure batare da ta nuna komaiba tun safe tun tanajin Abu Kad'an har yazo yayi yawa Sosai take zufa a d'akin tana yarfe hannu tuni ta fara fita hayyacinta sunan Allah kawai take Ambata a haka Chuchu ta shigo ta sameta tana ganin haka a d'imauce ta ruga wajen Ammy ta ce "Ammy kizo kiga yanda momcy take zai zufa take kamar ta mutu" ba shiri Ammy ta mik'e ta sanya hijab d'inta ta ce"inaga haihuwarce tare suka koma d'akin Inda suka tarar da Zarah na murkashi Sannu Ammy tayi mata tare da kamata ta kalli Chuchu tace "yi Sauri D'auko hijab d'inta Da Sauri Chuchu tasa mata hijab tare da takalmi su biyu suka kamota har wajen motoci Inda Chuchu ta kwalawa driver kira ba shiri yatado mota Tare suka shiga su Ukku Chuchu dukta rude asibitin mafi kusa dasu suka nufa da ita Inda suna isa aka wuce labour room da ita zirga zirga kawai Ammy take da Chuchu Sosai zahra take karb'ar wuta tayi awa guda tana wahaltuwa sosai takejin wata irin azaba da tunda uwar da ta haifeta bata tabajin irinta ba D'aya Daga cikin likitan d'aya duba ta ya fito ya kalli Ammy ya ce " A Gaskiya Hajiya Kuyi hakuri Ayi mata cs bazata iya haihuwa da kanta ba sakamakon Rashin bud'ewa da batayi ba na Auna bata Inda zata iya haihuwa Inma akace dole saita haihu da kanta Gaskiya zata wahala over sannan abunda ke cikinta Shima zai wahala"Innalillahi Ammy ta fad'a ji take kamar ta fashe da kuka ta ce "Dr Kuyi mata Cs din kawai Kar wani abun ya sameta" Chuchu ko kuka ta fashe dashi Okay "Zamu shirya yi mata yanzu amma ana buk'atar ganin mijinta da mahaifinta da Susa hannu" Ba matsala dr ku shiryata yanzu mijin nata zaizo saiya wakilci nbaban nata tunda emergency ne cikin Sauri Ammy ta kira MD Cikin tashin hankali ta ce "Ka sameni a asibiti" Bayan ta fad'a masa sunan asibitin ta kashe ba ayi 20 minutes ba saiga MD yazo afutatan wajen Ammy ya nufa ya ce "Lafiya ammy" Da sauki Zahra ce Zata haihu muka kawota sunce bazata iya haihuwa ba sai anyi mata cs shine muke buk'atar sa hannunka"Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Ammy yanzu tana ina Ina ne za a sa hannun"Sosai MD ya rikice ya rude Shi ya sanya hannu kuma shi ya bada jininsa kasancewar group o garesa suna gani aka shiga Theater room da zahra sosai Chuchu ta fashe da kuka Ganin kamar zata rasa kawartata Ammy ma hawaye take tana addu'ar Allah sa ayi aikin lafiya MD ma addua kawai yake hankalinshi a matuk'ar tashe yake "Ba ayi 30 mminutes ba sukaga fitowar dr D'auke da jariri a hannu fuskarshi d'auke da Fara'a suna ganin haka suka Kallesa Ammy ta ce " An sauka"Alhmdllh Dr ya fad'a yana mik'a mata jaririn"Amsar jaririn Ammy tayi "Allahu akhbar Allahu akhbar" kawai Ammy ke fad'a ganin yau ita ce rik'e da jinin MD a hannunta shiko gogon har yanzu gaba d'aya hankalinshi yana kan ga wani hali zahra ke ciki Nurse biyu suka ga sun Kara fitowa rik'e da wasu jariran a hannu"sai sannan MD ya kusa daskarewa ganin sun nufo su da Yaran Daya daga cikin nurse ta mik'awa MD.jaririyar ta ce "Congratulation Sir Allah ya raya" d'ayar kuma ta mik'awa Chuchu da itama ta daskare a wajen Kallon y'ar MD Yayi ya kalli sauran yaran dake hannun Chuchu da Ammy kamar Wanda bakinshi yayi masa nauyi ya ce "Kuna nufin Duka yaran nan aka ciro kuma Duka nawa ne" Murmushi nurse din tayi ta ce "Triple ta haifa gasunan Allah raya "farincikin da MD ya shiga fadarsa bata baki ne ji yake tamkar a mafarki wai yau shine Allah yaba yara har Ukku baisan lokacin da wasu hawayen farinciki suka zubo masa ba ya goge ya ce " Alhmdll.......✍ *Domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙 🅿️...........*83 & 84* Gaba d'aya MD yana rikice ya rasa wace irin Godiya zaiyiwa Allah s w a da yayi mashi wannan gagarumar kyautar yara Ukku lokaci guda yana Rungume da babyn yayi sujudu shukur sosai yake kwararo yabo da gdy ga Allah s w a Kafin ya bud'e fuskarsa d'auke da murmushi kamar gonar Auduga ya kalli Ammy ta ce "Ammy wai wannan din Duka yara na ne da gaske" murmushi kawai Ammy ke masa Dan farinciki harya mantar da ita wani b'acin rai Ta ce "yaranka ne babana " Daga hannu ya sakeyi ya ce "Allah Alhmdllh Alhmdllh bansan da wasu kalamai zanyi amfani ba wajen gode Maka " murmushi kawai suke Chuchu ma uwar kuka yanzu andawo murmushi cikin d'oki ta ce "Yaya wlh Duka kamarsu d'aya kuma dakai sukayo kama " daidai lokacin da na hannun Ammy ya fara kuka jijjigashi Ammy tayi ta ce "Yi Sauri Babana Kaje gida D'akin nan na kusa da na Chuchu zakaga kayan jarirai kodan ku tafi da chuchun Aje a d'auko duk abunda ya kamata sannan Ka taho da Dabino mai laushi tare da zamzam ka basu " to to Ammy Amma ya jikin nata ita mu bari a fito da ita"Jikinta Alhmdllh Dr ya ce "anwuce d'akin Hutu da ita bazamu samu ganinta yanzu ba allurar bata sake ta ba kuje ku kawo kayan yaran" Mik'a mata Namijin Chuchu tayi shiko MD Kallon yarinyar kawai yake dake tsala kuka yana murmushi wai yau shine rik'e da jininsa sosai yaji k'aunar yaran ta musamman Na ratsa sa wata nurse ta amshi yaran biyu Ammy ta rik'e d'aya Dan Aje a shirya su Kafin a kawo kayan "Cikin doki Ammy ta kira Zey tayi mata albishir Hajiya kaka takeson kira ta mata albishir to bata San taya zatayi musu bayanin zahra ba Hakanan dai Ammy ta lalubo number Hajiya Bayan suun gaisa ta ce " Hajiya Albishir na kira miki addu'ar ki dai ta amsu Matar MD ta sauka yanzu an haifi y'an Ukku"Ammy saida ta kauda wayar daga kunnanta saboda irin. Bud'ar da Hajiya ta rangada kira take "Alhmdllh Alhmdllh Ina kike rukayya maza taho ki kiramun iyayenki muyi musu Babban Albishir Matar Mustapha ta haihu"Ammy lura da Hajiya murna tama mantar da waya ya sanyata katse wayar tana murmushi ta window ta lek'a ta Hango zahra dake baccin wahala sanye da blue din rigar da aka gama mata aiki hannunta biyu Duka sanye da kalula d'aya Karin jinin da aka diba a na MD ne d'aya kuma Karin ruwa ne Goge hawayenta Ammy tayi ta ce "Allah ya baki lafiya zahra ya tashi kafadunki" ba ayi Minti goma ba saiga zey ganin yanda ta fito daga motar kasan ba karamun gudu ta sharara ba cikin farinciki ta ce "Ammy da gaske Ta haihu kuma y'an ukku yayanmu ahima ya zama uba" Murmushi ammy tayi mata ta ce "da gaske zainab kinga ikon Allah ko Yanzu haka Ana ciki ana shirya yaran ana jiran su maryam su kawo kayan da za a sanya musu kinsan a dimauce muka zo " Ajiyar zuciya zey ta sauke tare da goge hawayen farinciki ta ce "Alhmdllh ammy Adduar tsawon shekaru goma ta amsu Ta inda ba ayi tsammani ba ina mamyn take yanzu?tana ciki kinsan cs akayi " wayyo Allah ya bata lfy kaico "ba a dau lokaci ba su Chuchu sunkadawo tana rik'e da kayyayakin MD fara'a ta kasa barin fuskar sa sai nan nan yake Bayan an shirya yaran nanfa Chuchu ta shiga yi musu hoto Kamarsu d'aya har macen dukansu kuma da dimple d'insu irin na zahra dukda jariraine amma saida suka fito Fari da kammani da kyau duka MD suka biyo dimple din zahra kadai suka biyo nan fa aka shiga liliyar yaran d'aya Bayan daya MD ya d'aukesu ya tauna musu Dabino da zamzam rik'e Namijin dayan yayi yana ta kallonsa kamar zai cinyeta sai Murmushi yake yanajin wani irin farinciki na ratsa sa Ammy bata damu da irin rawar k'afar da MD yake ba ko Kara bayayi saboda tasan dole yayi abunda aka ta roka tsawon shekara goma yanzu Allah ya kawo ai dole yayi rawar kafa ganin yaran sun fara kuka ne ya sanya hankalin MD tashi duk ya rud'e Kallon Ammy yayi ya ce " please Ammy me za ayi musu suna kuka fa "Harararsa Ammy tayi ta ce " Waikai baka da ta ido"Sosai k'eya yayi ya ce "Ba haka bane Ammy kar wani abun ya samesu" girgiza kai kawai tayi koda Chuchu ta kira Asmy ta fad'a mata irin ihun murnar da tayi bana wasa bane farincikin data shiga bana wasa bane Koda ta fad'awa mamansu itama tayi farinciki matuka tana Jinjina ikon Allah tare suka shirya a motar babansu ya taho dasu Kaduna Dan suga jikin na zahra tunda ance musu cs ne "Kafin one hour sun Iso sosai Ammy ta karramasu da girmamasu dukda a Asibiti ne akayiwa juna barka Asmy ko tunda ta rik'e macen taki ba kowa saida tayi hawayen farinciki wai wannan din Duka yaran zahra ne nanfa hankali ya koma jiran farkawar Zahra Dan har yanzu saida su lek'a ta window MD ko tsaye yayi a jikin window din sosai yaji tausayinta ya k'ara kamashi ganin halin da take ciki saida yaga y'an gidan su Asmy tukwana yabar jikin Window din sai wajen 4pm zahra ta farka koda ta bud'e idonta Kallon d'akin ta dingayi kafin ta kalli jikinta da hannunta duk drip yunkurawa tasoyi Dan ta tashi amma ta kasa komawa tayi tana lumshe ido wasu hawaye na zubo mata tunowa da wahalar da tasha dazu bata manta da lokacin da za ayi mata cs ba kasancewar bata ido biyu akayi mata ba yasanyata bata tuna ba har yanzu allurar bata saketa ba saboda bibbiyu take ganin komai daidai lokacin da Nurse biyu suka shigo suka duba ta kafin a sauya mata daki aka maida ita wani koda su Ammy suka shiga Sannu kawai suke mata bata iya magana ba sai daga musu kai Goge hawaye Asmy tayi taje gefenta ta ce "Sannu sis" Itama gyada mata kai kawai tayi tana lumshe ido Dan kanta duk Juyawa yake "MD ko daga jikin kofa yake kallonta Ammy ce ta ce Ku Aje mata yaran ta gansu gefenta aka aje mata su Kafin Ammy ta ce " Bud'e ido kiga kyautar da Allah yayi maki daughter "a hankali zahra ta bud'e idanunta har lokacin ba komai take gani ba " Kallon Yaran ta dingayi dukda ba Sosai taga fuskarsu ba Amma har a ranta sosai taji k'auna da soyayyar yaran na ratsa ta kenan y'an Ukku Ta Haifa kallonsu kawai take Ammy na ganin haka saitayi murmushi ta jima tana kallonsu kafin ta daga hannunta d'ayan dake rik'e da drip Da niyyar ta tab'a na kusan nata Daga tsayen da MD yake ya matso ya ce "Ki bari Mamy drip ne hannunki bayason motsawa" Harararsa kasa kasa Ammy tayi ya sanyashi yin shiru amma har lokacin hankalinshi na Wajenta kallonta Ammy tayi ta ce "Zaki iya" gyada mata kai zahra tayi D'aukar shi tayi Ammy ta Aje mata shi a gefenta a hankali zahra tasa hannu ta zagayosa ta matsesa gefenta tana Kallonshi tana kallon sauran Maman Asmy ce ta ce "karfa ki matse sa zahra" Bazan masa komai ba "ta fad'a kasa kasa " Girgiza kai Ammy tayi ta ce 'Allahsrk d'a da uwa kenan sai ALLAH "Dr ne ya shigo Bayan ya duba ta ya tambayeta Saidai ta gyad'a masa kai Dan maganar nauyinta takeji " Ammy ce ta ce "Dr kamarfa har yanzu bata dawo daidai ba " Eh daman bazata dawo daidai yanzu ba ita hakanma da sauki wasu allurar tana dad'ewa tana daukarsu sosai zakiga har suna wasu maganganu kamar marassa kai da ta ido biyu ce akayi mata zata tashi normal amma itama zuwa gobe zata dawo normal please a barta ita da mutum d'aya Ta samu Hutu sosai "Ammy tace zata zauna da zahra sauran duk su koma gida dukda maman Asmy taso zama Wajenta MD ma yaso ace shiya zauna Wajenta Dan hankalinshi yanzu yana ga samun Lafiyarta Ga damuwarshi na abunda za Aba yaran Dan sun fara kuka Sosai Ammy ta kula da Zahra da Yaran tamkar kwai Bayan ta had'a mata Malta da isashshiyar madara Abu mai ruwa ruwa dai ta dinga bata sannan aka bata maganin da tasha dan asamu abincin yaran yazo sai wajen 8pm aka samu ruwan yazo Ammy ta d'ora mata su ta dinga feeding d'insu dukda taji zafi da kunyar ammy haka dai ta daure saboda k'aunar yaran da takeji ta musamman washegari zahra ta dawo normal ta dawo hayyacinta har tana iya zaunawa a danyi Hira da ita dukda nauyin Ammy da maman su Asmy da takeji MD ko ko kallo bai isheta ba Koda yayi mata ya jiki a takaice ta amsa masa da yawwa Wanda baijin dadin hakan ba Ganin yawan matan a d'akin yasanya suka fita shida Jabir shi kanshi Jabir ya girgiza da jin zahra tripplet ta Haifa Sai sannan MD hankalinshi yadan kwanta ganin jikin zahra da sauki sai sannan ya fara tashi sayayyarsa Wanda ba iya yaran yakeyiwa ba hada Momynsu Hajiya ma ranar tazo zo kuga murna da doki Da farinciki Saidai tayi mamakin da ba Amera ta gani ba Koda ta tambayi Ammy ya haka ce Mata tayi kiyi hakuri Hajiya idan muka koma gida za ayi miki bayani su Asmy da mamansu kullum sai sunzo sai yamma suke tafiya Funtua sosai aikin na zahra yayi kyau a kwana na hud'u aka sallamesu suka koma gida Inda Ammy ta ninka kulawar da take mata kafin kace me labarin haihuwar Tripple. D'in MD ya baza gari har internet sosai abokan arziki suke kiransa abokanan kasuwansa dama manya suna kiransa suna masa Barka har gajiya yake da d'aukar wayar wasu daga cikin y'an uwan Ammy ma.dake.india duk sunzo banda y'an uwan Abban su MD na Maiduguri suma sosai suka taho kwansu da kwalkwatarsu ranar daga Ammy sai Hajiya ta labartawa mata abunda MD yayi Dan shaida har videon d'aurin Auren ta nuna mata "Maimakon Ammy taga Hajiya ta daga hankalinta saitaga ta sauke ajiyar zuciya ta ce " na godewa Allah da ba a hanyar banza akayi cikin ba daura Aure sukayi dukda ba Abi shara'a ba Amma Naji dad'in ma da Ba wacce y'ar iskar ya haihu da ita ba yarinyar mutunci mai tarbiya da nutsuwa ta haifa masa kuma insha Allahu zahra saita zama tauraruwar mustapha saita kwacesa daga hannun waccen yar iskar yar marassa tarbiya da izinin ubangiji saiya so zahra ya kaunaceta tamkar ransa"Girgiza kai kawai Ammy tayi a ranta ta ce " hakan ta faru da nafi kowa farimciki "kafin ta ce " Ni yanzu damuwata Hajiya bansan me zancewa mutane ba"Barni dasu ni nasan me zance musu zance matarsa ce Zuwan da nayi na aura masa jikar Aminiya ta akwai ubanda ya isa ya ce Ba haka ba "Ajiyar zuciya Ammy ta sauke ta ce Hakane " Haka ko suka fad'awa mutane wanda ba Wanda bai yarda da hakan ba Saidai suce ba a gayyacesu bikin ba Nanfa aka fara shirin yin suna Wanda sosai MD yake rawar kafa ganin mutane sun fara yawa gashi baya samun damar ganin Zahra saboda d'akinta Ammy ta sauketa take kula da ita saboda d'inkin ta Saida ya kira Chuchu ta d'auko masa yaran idan ya gama liliyarsu ya bata ta koma dasu sosai yakeson ganin ,Zahra amma ba dama dinkuna masu kyau Chuchu da Zey suka kaiwa zahra kala"_kala tamkar Lefe kowa dai sai yaba amayar ta MD yake a yanda Ammy tayi musu bayani Asmy ko nan ta dawo take kwana Saboda kula da aminiyarta mamansu ma kullum sai sunzo Dukda sanyin da zahra tayi ana jibi suna Bayan MD yazo part dinsa na gidan yake sauka daman saboda mutane Chuchu Ya kira lokacin tana gefen Ammy dake bawa Babyn ruwa Ya ce "Ki kawo mun triple yanzu " To yaya gani nan"Ammy dake jinsu ta ce "Kice masa Bazaiyi musu hud'u ba " Daga bangaren MD yanajinta ya ce "Kice Hudubar ce zanyi musu" Kallon Ammy tayi ta ce "Yace hud'ubar ce zaiyi musu" Mika mata shi Ammy tayi ta ce "Saiki kai masa su" Zahra ko tanaji tasan da Wanda ake waya daga kwanciyar da tayi ta rumtse ido Tanajin wani iri a ranta rukayya ta dauki d'aya Chuchu ta rik'e biyu koda suka isa part dinsa Gaisheshi sukayi Tare da mik'a masa su "Kamar ko yaushe saida yayi musu addua Sannan yadanyi musu wasa kamar wasu manya Kallon su Chuchu dake shirin fita yayi ya ce " Ku jira ku koma dasu "Dawowa sukayi suka zaune sunzaci y'an mintuna ne amma saida suka kusan shafar awa suna jiransa ga ba damar su tafi saida ya gama liliyar yaranshi ji yake kamar kar atafi dasu Bayan yayi musu Huduba sai sannan ya ce " Zoku tafi da su "Cikin Sauri Chuchu taje ta amshe Su tana Dariya ta ce " Yaya me ka sanya Musu "Namijin d'aya fara mik'a mata ya ce " Yusuf"Sannan ya mik'a mata dayan ya ce "Shi kuma sunan Abba" Macen ya mik'awa Ruqayya ya ce "ita kuma Ammy" Wow Chuchu ta fad'a ta ce "Aiko yaya Harnayi musu nickname " Akhbar,Amar,Ammy kuma little zahra"Murmushi yayi mata ya ce "sunan yayi chuchun yaya Amma takwarar Ammy a sauya bazanso a dinga kiranta da sunan haka ba " hakane yaya Amma ai kaga Ammy ba zahra ake ce mata ba Fatima ake Ce mata"baice komai ba sai lalubo wayarsa da yayi ya ce "Zan miki transfer 10 millions "Kafin jibi ki shirya kayan da za a bawa bak'i jakunkuna, calendar, Turamen atamfofi super Holland da duk abunda kikaga za a raba karki sake ayi harkar karanta kafin gobe komai yazo sannan Jabir yayi wasu jakunkunan anjima zai kawo miki tare da wayoyin da nayi order daga compony duka a sanya a jakar rabon ki tabbatar komai ya tafi successful idan kudinma basu isaba kiyimun waya zanmuku transfer wasu " insha Allah yaya komai zaitafi yanda ake.so"Ajiyar zuciya ya sauke tare da Danna mata transfer Take suka shigo wayar Chuchu koda suka koma Ammy ta tambayesu ta ce "Me.Ya sanya musu" Cikin doki Chuchu ta ce "Ammy baby girl din takwararki ce kuma takwarar momcy Baby boys din kuma wannan Yusuf (Akhbar) wannan kuma Takwaran Abba (Amar)Murmushi Ammy tayi ta ce " masha Allah Ubangiji ya raya "Zahra tana daga kwance kamar tana bacci sosai tayi mamakin karar da yayi mata na sanya sunan mahaifinta tunowa da Baba da tayi ko yana wani hali yanzu ya sanyata Goge hawaye Wurinta Chuchu tayi ta ce " Tashi momcy kinji sunan yaran yayi ko "Bud'e ido tayi a hankali tare da sakar mata murmushi Dan bazata iya magana akan yaran gaban Ammy ba Sai gyada mata kai tayi alamar sunan yayi Ranar suna tunda safe aka yanka gardama gardaman shanaye Guda goma.reras raguna shidda Wanda naman shanayen.duk sadaka aka babbada gidajen marayu da gajiyayyu Sosai MD.ya taka rawar gani a wannan sunan y'an uwan Shima haka uwa uba Ammy data k'asa zaune ta kasa tsaye zahra ko duk yanda bataso tayi kwalliya ba saida Chuchu ta sanyata tun safe take sauyin.latsa latsan kaya hoto ne dai dak'yal ta yarda akayi mata tare da Yaran sannan akayi mata da Ammy da kuma Chuchu da Asmy dukda a sanyaye take saboda sosai taron mutanen ya bata mamaki Sosaifa aka shiga shagali da fidda abinci da baza Naira a bikin triplet gidan Ammy duk Inda ka hanga cike yake da mutane Wasu ma basu sansu ba haka suke zuwa Dan aci banza" Kaji ko yanda kasan Tuwo haka aka maidashi a gidan duk Wanda yaje sunan nanfa tofa ya shaida Sunzo gidan kudi sunzo Inda ba a tausayin naira Duba ga irin Abubuwan da aka rarrabama kansu ya isa mutum girgiza K'atuwar jika mai d'auke da hotunan yaran da sunansu cikinta galleliya Atamfa Holland banda Callender sai Tab d'in yara a ciki Kirar Iphone wacce kudinta ma saiya girgiza mai karatu mutane ganin amfara basu wannan Abun duniyar nanfa aka rude Wasu Dasun fito suke kiran y'an uwansu akan suzo kar ayi basu Babu alamar karewar kayan rabo saboda daman masu uban yawa akayi Chuchu itace gaba gaba kan rabo ita da Asmy duk anshiga busy ga ba ruwansu da wai sai Wanda suka sani Kowa bashi ake saboda ranar farinciki ce acewarsu duk Wanda yazo murna yazo tayasu hakan yasama suka sanya security barin kowa ya shiga amma fa sai anyiwa mutane bincike kafin Su shiga saboda karsu shiga da mugun Abu Chan na Hango *Auren wata tara*Fans Gungunsu guda Ni kaina nayi mamakin Ganin irin yawan sunfi a kirga Wanda ba ma zan iya kiran sunan su ba chan na hango khadyn sp ana yagar cinyar kaza Rachel ko ina kallonta tana zuba wasu kajin a ledar da tataho da ita su ummu suhaif sai washe baki ake banza ta samu,su halimatu ko an sha goggoro yanda kasan itace chuchu su fatima sai zazzakewa ake tana sune kirjin biki sunan ammy da amarya zahra gareta yan uwansu ne ai,chan na hango quen faridat suna fada da wata tana cewa zata sa security su fitar da ita batasan yanda suke da md ba to cousine brother dinta ne nikam hajjo ina rike da takarda da alkalami nace zuķ'i,su tsohuwa maman Siddiqa sai shafce zufa ake,su aisha,zainab oum ibisam ,jikalle ruky ,rahama ,maman nana,su nafisa kai sauran bazasu fadu ba wollah anyi kara Maman Khairat ita ce gaba Wajen yi musu jagora Akan suma suje su Amso nasu kason raba su gida hud'u tayi ta ce"Kunga ku bari mu kasu hud'u karsu ganmu gayya guda suce daman kayan suka kawomun kashi d'aya mu fara shiga kafin Sauran tunda Kunga munyi yawa "Ummu shugaba ce tayi k'araf ta ce " Wlh bazaiyu ba maman khairat kawai mu shiga gaba d'aya sanadin wanda suka fara shiga su su samu kawai mu mu rasa wlh bazaiyu ba "Ganin suna shirin yin sama ya sanya maman khairat cewa to shikenan muje mu Duka din Tunda bakusan ayi Harkar da baza a raina mu ba dukansu suka runkuta suka shiga kowa ya fito zaka kalli fuskarsa cike da farinciki sai wage baki suke kowa sai murna yake banda Sherston ghayu da ta fito hawaye jabe jabe da fuskarta wai bata samu rabo ba sosai na tausaya mata ganin yanda take kuka cikin bila'adadin mutane ita kadai ta rasa Allah sarki maman ummy da tausayi cewa tayi Dan Allah mu hada mata ko wani Dan abun ne a bata ,mutanen namu najin haka aka fara sassanfewa chan na hango lolos ta maida nata cikin hijab ta dukunkuneta ,mom shukurama cewa tayi tofa mu ma'assalam dadyn shukura yayi kira ,ummu suhaif da ummu rafi a sukace jiramu muma sun kira bansan yanda yan auren wata tara fans suka wansheba saboda barin wajen da nayi na kutsa ciki chan na hango zahra tasha tsadadden lace da yayi mata mugun kyau yanda kasan matar president Tripple dinta ko sunsha kyau cikin tsatsadan kayansu zey ta kasa ta tsare akan yaran ba a daukarsu kar a jagular su ganin Zahra a matukar gajiye take ga cs dinta da bata warke ba ga kaya masu nauyi da ta sanya ya sanya Ammy da itama tasha kyau kama hannunta ta kaita wani part din ac ta kunnawa dakin bayan ta sanyata tayi wanka ta sauya kaya kan gado ta kwanta daman gajiye take saida ammy taga bacci ya dauketa tukwana ta fita bayan ta rufe mata dakin taro ya tashi lafiya cikin girma da dattako anyi Abu na bajinta da nuna sa a md ma lunch suka shirya hatta abokanan kasuwancin shi na kasashe saida sukazo wajen lunch dinma haduwar da yayi bata baki ne iya maza kadae akayi anci ansha kafin dare ma labarin sunan triplet din,md sun baza duniya sakamakon yan jarida da suka ziyarci wajen event din da wajen sunan kuma md ba boyayya mutum bane da dare abban amira yaga bikin sunan a news cikin tsananin mamaki yacewa matarsa me nake gani haka hajiya itama tana mamaki ta ce "nima abunda na gani md yana da wata matar ne daman bayan amira"cikin tsananin tashin hankali ya dannawa amira kira a layin ta na chan kasar lokacin amira na bacci ringing din wayar ya tasheta cikin muryar bacci ta ce"hello dad cikin tashin hankali ya ce "Kina ina daughter labarin Me nake gani wai an haifawa mijinki triple yaushe kika haihu mu bamu sani ba"a rude amera ta mike ta ce "what daddy daman jita-jitar nan gaskiya ce tun last week friends dina ke kirana sunamun barka daga karshe har kashe wayata nayi nama dauki abun a rainin wayau Innalillahi wa inna ilaihiraji'un wai meke faruwa shima honey din nayi ta kiransa baya dagawa"kome kike ki maza ki dawo kasar nan akwai gagarumar matsala "cikin tashin hankali ta ce "To dad ganinam"a take ta ,Mike ko bag dinta bata tsaya dauka na passpord da wayarta kawai ta dauka ta fito kai tsaye Airport ta nufa hankali tashe zuciyarta chunkushe da tunani kala^kala ba bata lokaci tayi clearing din komai a daren jirginsu ya d'aga daga London zuwa Nigeria......... ✍ *domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Misa Hajo ce*_🤙 🅿️.........*85 & 86* Amera koda isarta jikin dadynta ta fad'a ta fashe da kuka ta ce "Dan Allah dad ku fad'amun me yake faruwa bansan abunda ya faru ba hankali na bai kwanta ba " Lallashinta ya dingayi akan ta nutsu ba komai bane ta Bari ayi bincikike tukwana washegari dak'yal ta Bari gari ya waye ba yanda Mamanta batayi.da ita ba akan ta Bari a bincika aji gaskiyar Lamarin ta kiya ta ce "saitaje gidan Ammy tunda shi tayi ta kiransa kusan 1 week baya dagawa abunda baitab'a yi mata ba " girgiza kai mamanta tayi ta ce 'Ai daman Amera na fad'a maki tun ba yanzu ba akan ki tsaya kiyi zaman Aure kwata kwata rayuwar da kika zab'awa kanki ba rayuwar y'a mace mai mutunci bace"da Allah mom Ni kibarni Naji da abunda ke damu na fisabilillahi"ta fad'a tana yin gaba tana gunguni "Girgiza kai Hajiya Farida tayi ta ce "Allah ya kyauta"Dadynta ko zirga zirga kawai yake...k'arfe 7:am zaune suke a palourn Dagashi sai Ammy Bayan kiran gaggawa da tayi masa shiru yayi ya maida hankalinshi ga sauraron abunda take son fad'a masa fuska ba wasa Ammy ta ce " d'ago ka.kalleni babana"ba shiri ya d'ago yana fuskantar mahaifiyar tasa "Hannu Ammy ta mik'a masa ta ce " bani takardar Saki ukkun zahra "Lokaci guda MD yaji wani irin tashin hankali ya ziyarce sa a matuk'ar rude ya ce"Ammy saki kuma" Eh saki ko kana da wata maganar ne daman ba Dan ka saketa ka aureta ba,ba Dan ta Haifa maka d'a ko y'a ka aureta ba to ai burinka ya cika ta Haifa maka yara har Ukku kaga ko amfaninta a wajenka ya k'are dan haka ka saketa ta kama gabanta itama taje tayi Aurenta cikin kwanciyar hankali da nutsuwa "Cikin tsananin tashin hankali ya ce "Ammy kiyi hakuri kibar maganar nan please ni har yanzu Mamy matsayin mata ta take kuma haka zataci gaba da zama insha Allah please Ammy kiyi hakuri kawai ki barmun matata kodan yaran nan Ammy kinsan d'an sai uwa please Ammy ina begging d'inki kidaina maganar sakin nan ba Ni Gaskiya bazan iya sakin Uwar y'ay'a na ba" ya fad'a kai tsaye "Sakato Ammy tayi tana kallon ikon Allah kafin ta tab'a hannu ta ce " ikon Allah daman Kasan da ruk'on d'a sai uwa ka shirya rabata da Y'ay'anta ka kaiwa Matarka Matar so da.kafi sonta da kowa inbanda asirinku ya tonu to wlh baka isa ba saika saketa"Hankali tashe ya d'ago ya ce "Ammy Dan girman Allah ki daina maganar sakin nan nifa bazan saketa ba period magana Zan zauna da ita na bata kulawa kodan yaranta Dan Allah Ammy naci darajan yaran nan"baka isa ba wlh watau nufinka Zama ka zauna da ita zaman Y'ay'anta lallai Babana kai harka isa ka zauna da zahra zaman Y'ay'anta zahra harta isa tayi zaman ,y'ay'a to bazata zauna dakai ba sannan zata baka Y'ay'anka kaje ka kaiwa duk ubanda zaka kaiwa ka kaiwa Amera uwarka ko iyayenta su rik'e maka y'ay'an amma.koni bazan rik'e maka su ba Tunda baka da mutunci sannan zahrar ma bazata rik'e maka su ba bari naje na D'auko maka su sannan na k'ara ganin k'afarka a gidannan Zakaga mamakin irin Rashin mutuncin dazan maka tunda Haihuwarka nayi bakai ka haifeni ba " ta fad'a a fusace tana Mikewa"Cikin sauri ya yi Sauri ya riko k'afar zanen Ammy Ya ce "Baki fahimce ni bane.Ammy Dan...bai k'arasa abunda yake son fad'a ba ta fusge zanenta cikin Sauri ta haura sama " Innalillahi wa inna ilaihiraji'un ya fad'a yana dafe goshinshi Daidai shigowar Amera d'akin a matuk'ar rikice "kallonta yayi yanda tashigo da itama d'in shi take kallo kafin ta karaso palourn cikin tsananin tashin hankali ta fashe da kuka tare da kama.hannunshi ta ce " Ka fad'amun Gaskiya MD me yake.faruwa Wasu Yara ne ake zancen an Haifa maka Bayan Banida masaniya ka fad'amun gaskiyar cewar bakai bane wasune kawai suke.karya da yaranka ne"Ba karya bace Yaransa ne halak malak Shiya haifesu da Matarsa da ya aura kina Chan kina yawon tambadewa a jirgi harta haihu baki saniba ta Haifa masa Yara Ukku reras lokaci guda ko kina da abun cewa ne zakizo kiwa mutane hauka da ba abunda kika iya sai bakin kishin jaraba to alkadarinki dai ya karye Duka Asirin da kika masa ya sakesa yayi aurensa ya rabu dake saiki koma Chan k'asar tambadewar taki kici gaba da tambadewa a sararin samaniya "Hajiya kaka ta fad'a tana shigowa palour" a matuk'ar rude Amera ta juya ta Kalleta kafin ta saki Hannun MD tanajin zuciyarta tamkar zata tarwatse ta ce "What sai kuma ta fashe da kuka ta ce " wlh Allah karya ne bazaiyu ba ,bazaiyu ba MD yayi Aure ya haihu da wata,karyane ,ihu ta k'walla iya karfinta tana girgiza kai kamar zata hau bori "tab'a hannu Hajiya tayi ta ce " ikon Allah to ko aljanu zata tada kihau bori Kece bishiyar kuka karewar iskokai mahaukaciya y'ar mahaukata Kaikuma Solon hofi tsayawa ma kayi kana kallonta"MD Yama rasa Inda zai tsoma ransa fitowa Ammy tayi tare da little zahra a hannunta Chuchu na biye da ita tare da biyun tana hawaye ta ce "Dan Allah Ammy kiyi hakuri karki basa yaran nan Momcy zata shiga wani hali Kinga koda kika amsosu kuka take Dan Allah Ammy kar fushi yasa kiyi aikin Dana sani" Daidai shigowarsu palourn Duk Kallon Amera suka tsayayi dake kwala ihu kafin ta chukumi MD iya karfinta ta shakesa ta ce "Daman kai Bakin Munafuki ne bansaniba,Mayaudari ne kai daman ,ashe duk kalaman da kake fad'amun na bazaka iyamun kishiya ba na karya ne to wallahi tallahi ka sani Mustapha baka isa ba kayi Kad'an ka yaudareni kaci bulus wlh baka isa ba ka hada matsayi na Dana wata ba karya ne Wlh zan kasheka zan kasheta zan kashe kaina Bayan na kashe shaggun yaran Dan wlh badai aure ba Saidai in y'an zina ne kuka haifa.Marin da taji an wanka mata ne ya sanyata Had'iye maganar da ta fito daga bakinta Dagowa tayi da kalli wacce ta maretar Ammy ta gani tsaye kanta tana huci rike da baby cikin b'acin rai Ammy ta ce " Duk iskancin da zakiyi ki tsaya iya mijinki shine Wanda zakiwa kici bulus amma ba zahra da yaranta da sukafiki matsayi da daraja a wajena ba baki isa ki shegantar mata yara ba sannan anfada Yayi Aure matarsa ta Haifa masa Yara ba karya akayi ba ko haramun ne Dan yayi Aure tunda ke kin kasa basa farincikin da kowace mata take bawa mijinta hakan yasa yayi Aure kuma da masaniyarmu yayi kece baki sani ba yanzu kuma ai kinsani"Wani irin kallo Amera Kebin Ammy dashi tana rik'e da kumcinta ta ce "Ni kika mara " An mareki Dan Ubanki ko ramawa zakiyi" "Kutumar uban nan to Inma na rama din ke uwata ce ko haihuwa ta kikayi munafukai ke mijinki har ya mutu ya taba miki kishiya ne da zaki sanya nawa mijin yayimun kishiya daman Nasan ba kaunata kuke ba shine har Kuka sanya yayi mun kishiya to wlh kusani ni Amera nafi k'arfin kishiya nafi k'arfin hada miji....d'auke da Mari har sau Ukku da taji anyi ne ya sanya ta kasa fadar abunda tayi niyyar fad'a cikin huci MD ya ce" baki da hankali ne Amera mahaifiyar tawa kike fad'awa hakan Dan iskanci ko ubanki ya isa ya fad'awa mahaifiyata haka bareke kodan Kinga Duk abunda kike ina kyaleki kina cin Darajar Abu biyu ne Inbanda haka da baki isa kiyi wani abun na kyaleki ba"kuka sosai Amera ta fashe dashi tare da k'walla Ihu duk saida suka toshe kunnuwansu Kafin ta bud'e ido Jaririyar dake hannun Ammy idonta yakai kukan kura tayi tare da nufar Ammy ta amshe Jaririyar Tana shirin timata da K'asa Zahra ta rugo A guje batasan sanda wani k'arfi yazo mata ba ta amshe y'ar daga fad'uwar da Amira taso kadata Huci kawai zahra take tana kuka Dan yau ita kadai tasan tashin hankalin data shiga da Amera ta kada mata yarnan da batasan yanda zatayi ba jijjiga yarinyar ta fad'a data fara tsala wani irin kuka kowa Ajiyar zuciya ya sauke ganin irin kokarin da zahra tayi saboda ba k'aramar shammatarsu amira tayi ba Cikin Hargagi Hajiya ta ce "Ka fitar mana da mahaukaciya Matar nan gidan nan Dan ubanka tunda ta shanyeka Ibanda sakarai ta zagi uwarka Ka tsaya kana kallonta baka sauke mata saki Ukku ba " cikin ihu Amera ta ce " da Allah iwa mutane shiru ke asuwa Ke ki sakeni d'in tsohuwar banza kawai" Ai MD baisan sanda ya k'ara d'auke Amera da wani Marin ba ya ce "Dan baki da hankali iyayen nawa da kakata kika zaga?Anzagesu din kaima wuce a zageka kayi banza d'an iska Mayaudari tana kallon zahra dake jijjiga y'arta tana kuka ta ce " Daman Y'ar Iskar karuwarka ka aura Macuci Mayaudari"waige waige ta fara tana neman mabugi Chan ta Hango Fankar K'asa cikin Sauri ta nufi wajen iya karfinta ta Karya Fankar ta d'auko K'asar da gudu ta nufi wajen zahra zata maka mata MD yayi Sauri Yarike cikin tsananin b'acin rai ya ce "Wannan wani irin hauka ne kike Amira" Kallon Chuchu da zahra Ammy tayi ta ce "Ku wuce ciki" Zahra hada gudu_gudu suka wuce Dan sosai ta tsorata da Amira Dan bata mance karansu na farko ba Cikin b'acin rai Hajiya ta ce "Bazaka saketa ba Sai kallonmu ka tsayayi ta zageni ta zageka,ta zagi uwarka ta shirya kashe maka y'ar da ka shekara goma Kana fatan samu ka tsaya kana kallonta Dan Kana Asararre"MD rasa Inda zai tsoma ransa yayi cikin bacin rai Ammy ta ce " ku barmun gida daga kai har ita inba so kake na yi muku abunda bakuyi tsammani ba "Cikin tashin hankali ya ce " Dan Allah Ammy kiyi hakuri idan sakinta kike so nayi sainayi"Daga masa hannu Ammy tayi ta ce "Bance ka saki Matarka ba ya rage ruwanku amma Abunda nakeso ta barmun palour sannan a maida mun duk abunda ta lalatamun na palour " tana gama fad'ar haka ta haye sama da Kallo Hajiya ta bita kafin taja tsaki ta ce "Kaji d'ayar mahaukaciyar a tunani na zakice ya saketa ne ko ki tsine masa amma ke ta kayan Da aka lalata miki ma.kike Allah mai iko zaman gidannan ko kayan takaici Aiko zuwa zanyi na tattara kayana na bar garin haihuwa yau har tajamun Zagi" Hajiya ta fad'a tana goge hawayen takaici kafin tayi fuuuu itama tabar palour "Cikin b'acin rai MD.ya kalli Amira ya ce " Hakan da kikayi burgewa ce to hankalinki ya kwanta kin had'ani da iyayena sannan zakisan iyayena Suna da martaba da daraja sunfi k'arfin zagi a wajenki ki biyo ni"ya fad'a yana fita sai sannan tsoro da fargaba suka kama Amira ta tuno da abunda tayiwa Ammy da Hajiya kaka sai sannan hankalinta ya fara dawowa jikinta tasan karya take ta zagi mahaifiyarshi da kakarshi ta kwana Lafiya karfa ya saketa "Cikin tashin hankali ta bishi Inda ta sameshi cikin mota ya had'e kai da sitiyarin mota Cikin tashin hankali ta fashe da kuka ta ce " Dan Girman Allah MD.karka sakeni wlh tallahi bansan na zagesu ba zuciya ce kasan bata da kashi"Wani irin kallo ha dinga binta dashi cikin Tsawa ya ce "shigo nace" Cikin Sauri ta shiga da Sauri ya figi motar bai tsaya ko ina ba sai gidansu suna isa bakin get ya tsaya ya ce "Fita ki tafi gidanku " Kuka ta fashe dashi ta ce "Dan Allah honey karkace ka sakeni" Cikin Tsawa ya ce "Bakiji abunda nace ba " Ba shirin ta fita tana fita Ya rufe motarsa ya jata da gudu da gudu Amira ta shiga gidansu tana wani irin kuka ta fad'a jikin dad d'inta ta ce "Na shiga Ukku Dad shikenan md ya rabu dani daddy yayi Aure bansaniba Matar harta haihu naje gidansu na zagi mamansa da kakarsa yayi fushi ya maidoni gida shikenan dad nasan sakina zaiyi na shiga ukku wlh dad inason mijina ina kaunarsa bazan iya rabuwa dashi ba wata bata isa ta rabani dashi ba Dady zuciyata ji nake kamar zata tarwatse dad tana cikin wannan sai ganinta sukayi ta sulale a wajen summammiya hankalin iyayenta idan yayi dubu ya tashi a guje aka wuce Asibiti da ita hankali tashi Kafin likitoci su fara kokarin ceto rayuwarta.....MD ya rasa yanda zaiyi da ransa yasan Ammy ba k'aramun fushi ta k'ara dashi ba nakin sakin Amera Jabir ya kira a waya ya sanar masa halin da ake cikin hankali tashe Jabir ya ce " Innalillahi Abu dai baiyi dadi ba bloody me yasa kak'i sakinta Ammy fa da Hajiya ta zaga kishi hauka ne "Jabir bazaka gane bane ni kadai nasan yanda Naji zafin hakan a cikin raina Nafi su Ammy jin zafi naki sakinta ne saboda Duniya zata zageni babu Wanda zai duba abunda tayi za ace na saketa ne saboda Na auri wata harta haifamun yara nayiwa Matar data zauna dani tsawon shekaru goma ko shad'aya butulci" numfashi Jabir yaja yace "Tabbas hakane kayi tunani bloody amma dai abunda yafi kamata kaje kaba Ammy hakuri yanzu kayi mata bayanin nan zata fahimce ka" Kamar yanda Jabir ya fad'a masa haka yaje ya samu Ammy da dare ko gaisuwar da yayi mata kin amsawa tayi cike da damuwa ya ce "Dan Allah Ammy kiyi hakuri wlh bawai Dan banji ciwon abunda Amera tayi ba yasa ban saketa ba nayi hakan ne saboda gujewa surutun mutane za ace na saketa ne kawai saboda wata Matar ta haifamun yara na rabu da ita tsawon shekararmu goma ban rabu da ita ba sai yanzu za aga Rashin kyautawata Wanda kome tayi baza a ga nata ba Amma Ammy kiyi hakuri indai zaki janye fushin nan naki wlh zan saketa yanzu daman na Turata gidansu Saina aika mata takardarta indai hakan zaisa hankalinki ya kwanta" Tunani Ammy tayi tace tabbas hakane dagowa tayi ta Kallesa har saida yaso bata tausayi ta ce "Bance ka saki Matarka ba Inama umartarka da kaje ka D'auketa ku koma gidanku Kamar yanda bazanso a saki nawa y'ay'an ba haka bazanso a saki nawasu ba ka mayar da Matarka gidanku sannan Ka lallasheta harka samu ka shawo kanta Tabbas kishiya da ciwo musamman baka San da ita ba har sai da y'ay'a dukda dai batasan dalilin Auren ba saboda soyayyarta ne ni na yafe maka ba abunda kayimun amma dai ka sani ina kan bakana saika saki zahra "cikin wani sabon tashin hankalin ya d'ago ya ce " Dan Allah Ammy kidaina maganar sakin Mamy na yarda zan saki Amira amma Bazan iya sakin Mamy ba please ammy ki barmun mata ta"nazarinshi Ammy ta dingayi kenan yayarda zai iya sakin Amera Amma Bazai iya sakin zahra ba Tunaninta takeso tabbatarwa na gane irin son da MD yakeyiwa zahra da matsayinta a zuciyarsa Dan tun ba yanzu ba ta Riga da gano irin son da yakeyiwa zahra kenan yanzu zahra harta samu matsayin da yafi na Amira a cikin zuciyarsa a zuciyarta ta ce "Alhmdllh" a fili kuwa murtukewa tayi ta ce "Bazan barmaka ita ba Bazatayi zaman y'ay'a ba sannan na baka daga nan zuwa awa 24 ka kawomun takardar zahra kaji na fad'a maka" Mikewa yayi cike da damuwa ya ce "Gaskiya ni bazan saki matata ba Ammy saboda ina sonta kuma ina muradin zama da ita Dan haka ni bazan sake ta ba " Yana gama fad'ar haka yabar palourn kamar zai tashi sama"Saboda ina sonta "Ammy ta maimaita kafin ta saki wani kasaitaccen murmushi ta ce " Alhmdllh Allah na gode Maka Addu'a ta ta tsawon shekaru ta amsu"Daren ranar MD bai iya bacci ba idan ya tuno da yanda Mamy take tilastashi akan saiya saki Zahra bai tab'a fahimtar irin tsananin so da k'aunar da yakeyiwa Zahra ba sai ranar da Ammy ta rabota dashi shi kadai yasan irin halin d'aya shiga na rashinta ba Tunanin irin rayuwar da sukayi tun a Zaria ya dingayi Tabbas baisani ba ya jima da Fad'awa kogin soyayyar yarinyar sani ne kawai baiyi ba Amma yasan ba k'aramun so yakeyiwa Zahra ba tunba yanzu ba Wanda yakejin duk ruwa duk iska bazai tab'a yarda ya rabu da ita ba ....Bangaren zahra sosai ta tsorata da ganin yanda Amira taso halaka mata ya dak'yal suka samu little zahra tabar kuka Bayan Chuchu ta goyata tana jijjigata ta samu tayi bacci sai sannan hankalinsu ya d'an kwanta...bangaren Amera ko itace bata farka ba sai washegari Kamar mahaukaciya haka ta tashi dak'yal iyayenta suka dinga Lallashinta harsuka samu tadan sauko amma har lokacin kuka take kamar ranta zai fita idan ta tuno da wai MD yayi Aure harda yara ji take kamar zuciyarta zata tarwatse babanta ko shi kadai yasan tashin hankalin daya shiga watau duk harin dukiyar MD da yake na Amira ta Haifa masa y'a y'a Wanda ko ya mutu ko ya kashesa Amera da yaranta Kadai sai mahaifiyarsa zasuyi gadonshi Duka plane d'inshi ya tafi a banza wata banza tazo ta Haifa masa Har yara Ukku Tabbas dole ne Yaran su mutu Sannan dole ya kashe MD.....Kwana biyu Amira tayi a Asibiti aka sallamesu Lallashinta kawai dadynta yake akan tayi hakuri ta nuna musu ta hakura karta sake tayi haukan da MD zai saketa tabi komai a Sannu shi zai sama mata manufa dak'yal ya samu ta yarda da hakan amma ita kadai tasan yanda takeji a cikin zuciyarta wannan matsiyaciyar MD ya had'a matsayi d'aya da ita harta Haifa masa Yara intana Tuna abunnan ji take zuciyarta na shirin tarwatsewa saida tayi sati Tana jinya kafin a sallameta a cigaba da kula da ita a gida Dan yazama wata mahaukaciyar karfi da yaji...MD dakatawa yayi da zuwa gidan Ammy saboda kullum yaje zance d'aya ne akan saiya saki Zahra shi kuma ya kafe Akan bazai saki matarsa ba a haka dai Ammy na kula da Zahra da yaranta Bayan gyarata din da take Dan kayayyakin gyara na musamman ta sanya aka hadoma surukar tata gyarata take tsab a haka har sati biyu Wanda nanfa hankalin MD ya tashi akan son ganin zahrarsa Yau tunda ya shigo Ammy tayi banza ta kyalesa dukda ta k'asar ido ta Kallesa ganin ya rame saida ya bata tausayi amma Kuma Tabbas ko tana basa zahra saita gwalasa shiru yayi yana hangen Inda zai ga bullowar zahra ko Chuchu amma shiru Chan yaga tashin Ammy a wajen Ajiyar zuciya ya sauke kai tsaye stairs yahau ya nufi bangaren Chuchu Koda ya shiga tsaye ya samu Chuchu na goye da little zahra na zaune tana feeding d'in Akhbar daga kofar MD ya dinga mata wani irin mayen kallo ganin yanda take Shayar da d'an cikin nutsuwa suna Hira da Chuchu Gyaran muryar da yayi ya fargar dasu da Kallon mamaki suka bishi kafin Chuchu tayi Dariya ta ce "Yaushe ka shigo yaya daka tsoratani " banjima da shigowa ba Ganin yara na nazo""ya fad'a yana karasowa d'akin Tare da Zama gefen Gado Sosai gaban zahra ya tsananta fad'uwa kallo d'aya tayi masa bata sakeba saboda wani irin kwarjini da yayi mata rabonta dashi tun washegarin Suna gabanta na fad'uwa tayi Sauri ta cirewa Akhbar Mama dukda ba koshi tayi ba "Sauko little Chuchu tayi daga bayanta ta ce " Gata yaya yau saikayi mana raino tunda Allah ya kawoka"amsarta yayi yana murmushi ya ce "Oyoyo my Ammy" yana amsarta ta tashi daga bacci Da Hannu ya dinga mata wasa yana murmushi fita Chuchu tayi tabar d'akin zahra na ganin haka ta Aje Akhbar kusa da amar da duka sunyi bacci ta mike zata fita Tana yin hanyar fita Ya fardota da hannu d'aya Tare da matsota gefenshi"wara idanu tayi saikuma ta hade rai Ta ce "Meye haka wai malam " Har mommy's d'insu nazo gani ai Kuma ya zaki fita"ya fad'a yana kissing Little zahra Turo baki tayi ta ce"Ni Dan Allah ka sakeni bansan wannan Abun sanadin Ammy tazo tagani ko Chuchu su zargemu "murmushin gefen baki yayi ya ce " So what Dan sun gani ai kowa dai yasan da matata nake tare"Wani banzan kallo tayi masa tana shirin kwatar kanta daga matsar da yayi mata ta ce "Dan Allah ni ka sakeni kajedai Chan wajen Matarka ni ba matarka bace" ta fad'a tana Kokarin kwace kanta A hankali ya Aje little wajen y'an uwanta tare da juyar da zahra ya kwantar ta ita yabi ta kan kirjinta ya hayeta Dan yana sane da dinkinta Tana shirin kurma ihu ya had'e bakinsu waje Daya ya d'auki lokaci sosai yana kissing d'inta Kamar zai cinyeta lokaci guda yaji ya fara fita daga hayyacinsa baisan lokacin d'aya sanya hannunsa cikin rigarta ba ya fara wasa da ...... kamar zai cinyeta zahra gabak'i d'aya bata yanda zata kwaci kanta ga ya had'e bakinsu waje Daya Sarautar Allah kawai tasawa ido Dan bata da damar kurma masa ihu gaba d'aya MD ya rikice har baiji kukan da Amar ya fara ba Alamun ya tashi zahra ko Naji ta fara kokarin ya saketa amma ta kasa chuchu daga palourn da take ta dinga jiyo kukan Amar shataf ta manta da MD.na d'akin da gudu ta Ruga d'akin abunda ta gani ne ya sanyata yin Sauri tayi baya ba shiri tana dafe k'irji tace"na shiga ukku ni maryam me.na ganoma.idona"Zaune tayi tana tagumin tunanin yanda zahra ta biyewa Yayan nata murmushi tayi Ita d'aya ta ce "Allah sarki babu yanda banso zahra da yaya na ba ashe Allah ya Riga da ya tsara itace matarsa hadda y'ay'a ita kanta ta tuna abun nan al'ajabi take sai ta tuna lokacin da take cewa su Asmy.kilama ita d'in rabon yaya ce Ashe dai rabonshi d'ince...saida Little itama ta tsala nata kukan kasancewar na yara biyu ya dawo da MD hankalinshi cikin Sauri ya tashi a kanta Ajiyar zuciya zahra ta sauke tare da sauke numfashi Cikin Sauri MD ya d'auki little ta dauki amar jijjigashi ta fara shima MD na jijjigashi ganin bata da shirin feeding dinsa ya sanya MD cewa " ki basa abincinsa bakijin irin kukan da yake"Kauda kai tayi tana turo baki gaba tayi ta ce "Dan Allah Malam ka fita Haba" murmushi yayi ya ce "Ko kunyata kike Bayan yanzu na gama liliy...batajira abunda zaice ba tayi Sauri ta bar dakin cike da jin kunya da haushin Rashin junyarsa palourn ta koma gefen Chuchu ta zauna tana turo baki Chuchu na kallon yanda ta fito a murtuke saida tasoyin Dariya ta Had'iye MD ko murmushi yayi tare da jijjigar y'arsa kafin ya d'auki akhbar dake bacci Duka ya sanyasu a kafada ya fito Chuchu ya mik'awa shi ya ce " ku daina barmun yara su kadai a d'aki ko nan da nan ne"Murmushi Chuchu tayi tace "Daman bama barinsu yaya " satar kallon Zahra yayi da ta wani had'e rai yayi murmushi ya wuce da little kasa...tundaga lokacin nan MD ya samu damar zuwa ya rage zafi da zahra Chuchu ko tuni ta ganesa Dan d'aya shigo d'akin yake cewa ta basu waje ganin haka ya sanya data gansa take ficewama ta basu waje Zahra ko Dan dole yake mata Dan ba irin yanda batayi dashi akan ya daina zuwa Wajenta ita bataso idan yaranshine Ya dinga kiran Chuchu tana Kai masa su A haka dai har zahra ta kusa yin arba'in Yau ma MD yazo Chuchu ta fice tana palour ita da Amar da Alkhbar da suke kan gadonsu na kwanciya tana yi musu wasa suna mata dariyar koda Ammy ta shigo d'akin rik'e da little dake Tsala kuka Chuchu na ganinta ta ce "Ammy kuka take" Eh kuka take ai tamayi hakuri rabonta da mamanta tun safe fa "bari na kai mata ita" ta fad'a tana nufar kofar chuhu na ganin haka tayi Sauri ta shige gaban Ammy Dukta rude ta ce "Am my bari na kai mata ita" Harararta Ammy tayi ta ce "Da Allah bani waje bansan shiririta D'akin naku bako na ne " ta fad'a tana tura kofar kusan daskarewa tayi ganin MD kan zahra sai kissing d'inta yake Saurin rumtse ido tayi kafin Ta daka masa wata irin Tsawa wadda ba shiri MD Ya tashi a kanta Sosai ya rud'e ganin Ammy baiyi tsammaniba zahra ko wace irin kunya ce ta lullubeta tasan Ammy bazata fahimceta Ba ason ranta yake mata haka ba Dan ba yanda zatayi"Cikin Tsawa Ammy ta ce "Wuce ka bar dakin nan munafiki" sim sim MD yabar dakin cike da jin kunya Zahra ko kunya ta isheta saita fashe da kuka "Cikin fad'a Ammy ta ce " Watau ni ina Chan ina kwata miki hakkinki ke.kina nan kinbiye masa Ina tibka kina warwarewa kin mayarmun da aiki baya zahra me.yasa kika saki jiki dashi haka bakison yasan darajarki da martabarki yagane matsayi da muhimmancinki zahra "Cikin kuka zahra ta ce " Dan Allah Ammy kiyi hakuri nima banason yana zuwa kuma ki tambayi Chuchu kiji "tab'a hannu Ammy tayi ta ce " kenanma wannan bashine karo na farko ba kafin ta dallawa Chuchu harara ta ce "Ke kuma Munafuka watau duk hudubar da nayi maki akan karki sake ki barsa yana zuwa Wajenta bakiji ba to ai shikenan gaba d'aya yau zata koma part Dina sai Inga in d'akin nau zai dinga binta " Dariya Chuchu tayi ta ce "Ammy ni karkiga Laifina Miji da matarsa kuma saina hanasa shigowa" Dundu a baya Ammy takai mata ta ce "ja'ira" Dariya Chuchu tayi tana kaucewa ..tundaga ranar Ammy ta mayar da zahra part d'inta ta kasa ta tsare sosai akan MD ko Yaransa Saidai taba Chuchu takai masa sosai MD ya damu da hakan hankalinshi ya k'ara tashi Dan koba komai yana da buk'atar ganin matarshi sosai Ammy ta burkuta masa lissafi gabak'i d'aya ...yana kwance a makeken Royal bed dinsa kamar koyaushe indai ya kwanta shi d'aya to ba tunanin da yake idan ba nata ba yaji wayarsa tayi ringing kamar bazai daga ba saikuma ya d'auka ganin Baba na gombe ne Cikin girmamawa MD ya gaishesa ya amsa masa ya ce "jikana ashe haihuwa akayi maka baka fadamunba Abun farinciki ya samu ashe har anyi wata guda bani da labari sai dazu Jabir Daya kirani muka gaisa yake fad'amun gsky banji dadi da baka fadamunba kasan ai nazo naga y'ay'an nawa amma dukda haka insha Allah na shirya gobe gani nan zuwa kadunar zanzo nayi maka barka naga yaran kaga harmun gaisa da Hajiya sannan nayi mata Godiya"Cikin girmamawa MD ya ce " ba haka bane Baba lokacin wani uzurine ya mantar dani fad'a maka ai Baba dama ka barsa karka wahalar da jikinka idan sukayi kwari a kawoma maka su kaga jikin naka bai gama warwarewa ba"murmushi yayi ya ce "a a jikana jiki kuma ai ya warware gobe insha Allah Zanzo naga y'ay'an tunda tafadamun haihuwar Naji ina son ganin Yaran " cike da murmushi MD.ya ce "To shikenan Baba gobe da safe driver zaizo ya tafi dakai saika biyoshi zai kawoka har gida " haka ko akayi washegari tunda safe driver yaje ya taho da Baba na gombe da Yakejin gabanshi na fad'uwa tunda suka taho suna isowa garin Kaduna Baba ya dinga bin garin da Kallo yana murmushi Har suka isa tafkeken gidan su MD Daman tun jiyan MD.ya sanar da Ammy da zuwan Baba anshirya masa komai na tarba a Babban palourn bak'i aka saukesa Bayan an cika masa gabansa da abubuwan makuleshe sosai MD ya nuna jin dadinsa na zuwan Baba Bayan Ammy ta shigo tana rik'e da Amar Hannunta da fara'a tayi welcoming din Baba cikin girmamawa tamkar mahaifinta haka ta dinga girmamasa Bayan sun gaisa Baba ya k'ara yiwa Ammy Godiya akan irin taimakon da MD yayi masa murmushi Ammy tayi ta ce "Bakomai Baba Ai anzama daya kaid'in ai tamkar uba kake a gareni shiko jika ne a gareka" fara'a cike da fuskar Baba ya ce "na jima banga mutanen kirki mutane na kwarai ba irinku ba Allah dai yasa a gama da duniya lafiya ya kareku daga sharrin makiya ya raya zuri'a Ameen Ammy ta fad'a tana mik'awa Baba Amar ta ce " Ga d'iyan naka Baba Biyun yanzu za a kawo maka ana shiryasu"Murmushi Baba yayi yana amsar yaron Ya ce "kai kai masha Allah Tubarakalla Allah ubangiji ya raya ya karesu daga sharrin makiya " shidai MD yana mamakin Baba tsoho da duk addu'ar da zaiyi ko waya suke saiya ambaci makiya da mahassada "Kallon yaron kawai Baba yake yanajin k'aunar yaron haka kawai yakeganin yaron tamkar ya rik'e jininsa Chuchu ce tare da zahra suka shigo tana sanye cikin zullubebiyar hijab har kasa ita na rik'e da Akhbar Chuchu kuma little gefen Ammy Zahra ta zauna Hakanan yau ta tashi a sanyaye kallon ta kawai MD yake tunda ta shigo sosai yaga ta k'ara yi masa kyau da kwarjini baisan lokacin d'aya saki kasaitaccen murmushi ba tare da sauke ajiyar zuciya Dagowar da Baba zaiyi daga Kallon Amar idonsa ya sauka akan zahra dake mik'awa Ammy akhbar Ammy ta ce " To Baba ga sauran an kawo maka kaga maman yaran"ta fad'a tana nuna masa Zahra"A matuk'ar firgice Baba ya Mike Hankali tashe yake kallon zahra yana rik'e da Amar ya fara nunata da yatsa kasa magana yayi sai nuna ta da yatsa da yadingayi muryarsa gaba d'aya ta sartsa ya kasa furta abunda yakeson fad'a duk Kallon mamaki suke binshi dashi har zahra da ita yauma ta fara ganinsa Rumtse idonsa yayi da karfi kafin ya bud'e yana nunata da yatsa a rarrabe ya ce "Ma my y'a ta Zahra'u da man kina raye ba ki mutu ba Zahra'u kece nake gani ko ko mafarki ne nake........✍🏽 *Domin magana da marubuciyar kai tsaye 07026166536* *GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇* 1, *MU GANI A ƘASA...*🔥 _Ummu Affan_ 2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚 _Ummu Maher_ 3, *GUNTUN GORO..*💥 _Mom Islam_ 4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎 _Mrs Bukhari_ 5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨 _Miss Hajo_ Guda biyar 1k Guda huɗu N700 Guda uku N600 Guda biyu N500 Guda ɗaya N300 *DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇 0037219728 Fatima Rabiu Sunusi StanbicIBTC Bank. Domin tura shaidar biya👇 0810 433 5144 Masu tura katin MTN👇 0814 179 9224 Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇 0817 952 3215 Guda biyar 1000f Guda huɗu 700f Guda uku 600f Guda biyu 500f Guda ɗaya 300f *TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 🅿️.............*87 & 88* & 🅿️.............*89 & 90* Duk Kallon mamaki suke bin Baba dashi shiko nuna zahra kawai yake "MD ne yayi k'arfin halin cewa " Dan Allah Baba kayi mana bayani ina kasan wannan "hawaye na fita daga idon Baba ya ce " y'ata ce d'aya tilo dana mallaka Nina haifeta a tare Nida ita akayi mana harin da har kuka tsinceni tsawon shekaru bansan Inda take ba a tunani ma ta rasu saboda Bansan Inda sukayi da ita ba "cike da mamaki Ammy ta ce Ka nutsu dai Baba wannan ba y'arka bace Mahaifinta Yana Chan Funtua kuma wannan yarinya ce ma bata kai shekarun da kake Tunani ba kadai duba Baba" mik'awa MD yaron Baba yayi ya nufo Inda Zahra take da duk a tsorace ta ke kama hannunta dake d'auke da zoben da awarwaran da tunda Baba ya bata yake hannunta yayi Kallon zoben da awarwaran yake Yana murmushi yana hawaye ya ce "Kece Mamy ashe daman idona zai sake nunamun ke ina raye Mamy na nine Mahaifinki Mai kaunarki ko kin manta ni zahra'u ko kema sun juye miki kwalwar ne Dan karki tona musu asiri kamar yanda suka juyemun tawa Mamy ki tuna mahaifinki Malam Abdussalam sai kuma ya Rungumeta tsam a jikinsa ya ce " Alhmdllh Alhmdllh Allah na gode Maka da ka nuna mun wannan yara y'ata da na shekara da shekaru ina begenta yau gashi Allah ya had'amu ta yanda banyi tsammani ba "ido ido kawai ake tsakanin Ammy da MD har Chuchu zahra ko Itama kuka ta fashe dashi Tabbas wannan din shine kakanta shine mahaifin Mamanta dukta k'are MD ne ya taso yayi kokarin raba su ya ce " ka nutsu Baba kayi mana bayani wannan ba wacce kake tunani bace "Sassauce ruk'on da Baba yayiwa zahra yayi ya juya ya kalli MD ya ce " Haba yaro ya zakamun gardama na haifi y'ata na kasa ganeta"Juyawa yayi yana kallon zahra dake Kuka ya tallabo Fuskarta kallonta ya dingayi yana son yaga banbanci tsakanin ta da mahaifiyar Ta" motsa bakinki "ya fad'a a hankali zahra ta motsa mamaki ya kama Baba ya ce "To ya haka da sanin da nayi mata tun yarinta abun nan d'aya gareta amma yanzu naga biyu " Cikin muryar kuka zahra ta ce "Ba waccen Da kake magana bace y'arta ce " ta fad'a tana hawaye"duk mamaki yagama. Cikasu Ammy ce ta ce "Kamarya y'arta ce kunsanyani cikin duhu fa Dan Allah ku warware mana " Zaunawa Baba yayi jibis yana mamakin jin Abunda ya fito daga bakinta MD ne yaja numfashi ya ce "da Alamun akwai wani Abu a kasa please ku nutsu ku warware mana muna cikin duhu " cikin muryar kuka zahra ta ce "Babana ya bani labarin mahaifiyata yana aikin noma.ya tsinceta a lokacin Bata cikin hayyacinta har aka samu akayi mata magani Dan da ko magana batayi sai daga baya da aka dage da rokon Allah kasancewar gidansu babana duk malamai ne koda ta farka bata iya tuna komai ba sai sunanta ta ce Musu sunanta " Zahra"a haka har Allah ya sasinta kansu da babana sukayi Aure Wanda suka zauna a funtua wajen sana'arsa yace bata tab'a tuna wani nata ba ko ita kanta wacece Sai lokacin da ta haife ni Wanda a nan ta ciro zoben wannan da awarwaro dake hannu na ta basa ta ce idan na girma ta bani zasu taimaka mani wajen gano danginta daga nan bata Kara ce dasu Komai ba game da asalinta Har Allah yayi mata cikawa"Ta k'arasa fad'a cikin kuka "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Ashe karshen saduwata da Zahra'u kenan a rayuwa ,ashe bazan sake ganin y'ata ba d'aya Dana mallaka Allahu akhbar Su mudan basu samu damar kasheta ba kenan Allah mai iko zahra Har saida ta haihu ashe Allah sarki zahra'u Allah ya jikanki yayi miki rahama yasa kina cikin rahama hakika mamy baki mutu da hakkin iyaye ba Kinyimun biyayyar da bakowani d'a zaiyiwa mahaifansa haka ba allah ya jikanki Ashe bazamu kara saduwa ba sai a darussalam Zahra'u ke kika rigani tafiya ashe ba rabon mu sake ganawa yana hawaye ya kamo hannun zahra ya ce " Tabbas ni nan nine kakanki Nina Haifi mahaifiyarki Wannan awarwaron da zoben Tabbas nata ne ko babu su kamanninki da mahaifiyarki kadai sun isa duk wani ahalinmu ya ganki ya shaidaki Allah ya taimaka Mudan bai ganki ba na tabbata da ya ganki tofa da ya zama dole ya kasheki "Mudan " Ammy ta maimaita zahra ko jin abun take tamkar almara wai yau itace gata ga kakanta,yau itace taga jinin mahaifiyarta ,Allah sarki wasu hawayen farinciki ne suka zubo mata tana murmushi ta ce"Kana nufin kaid'in kaka na ne kai ka haifi mahaifiyata daman da rabon zanga dangin Mama a duniya "ta fad'a hawaye na zubo mata saikuma ta Rungume Baba ta ce " Alhmdllh Allah na gode Maka da ka nunamun wannan ranar tamkar almara Baba najima da bakincikin Rashin sanin dangin mahaifiyata bantaba kawowa a raina ba zan hadu dasu Cikin Sauki haka meya kawoka gidan nan har yayi silar haduwata dakai Baba"ta k'arasa fad'a tana hawaye "Rungumeta sosai Baba yayi yanajin kaunarta kamar yanda yakejin k'aunar y'arsa data rasu " sosai su Ammy suka girgiza dajin al'amarin nan Chuchu da Ammy da Hajiya kaka da bata jima da shigowa ba hada hawaye MD ko mamaki ya gama cikasu cewa yayi "mezai hana Baba ka bamu labarin abunda ya raboka da garinku da wadanda sukayi harin rayuwarka da ta iyalanka " Saida suka saki juna daga rungumar da sukayi da zahra kafin ya goge hawayen bak'inciki da takaici ya ce "Yau zan baku labarin asalin waye ni da kuma silar shigarmu cikin wani hali ta dalilin d'an uwa Nida y'ata asalinmu haifaffun Jihar jigawa ne ina da mata d'aya Hajiya Saratu ina da kanne Shida Wanda muka fito ciki d'aya uwa d'aya uba d'aya sai Wanda muke uba d'aya Mudan Wanda shine autanmu shi kadai mahaifiyarsa ta Haifa har Allah yayiwa iyayenmu gaba d'aya a hankali a hankali rasuwa dalilin wannan ya sanya muke matuk'ar sonsa muke jansa a jiki bamu tab'a nuna masa y'an ubanci soyayyar da nake nuna masa ko Wanda muke uwa d'aya uba d'aya bana nuna musu tun ina yaro daman ni natashi mutum ne mai neman na kansa na kasance Dan kasuwa tun ina K'ananan kasuwanci da noma har Allah ya habaka na zama Babban attajiri a garinmu Wanda daidai ne zaka fad'a suna na Alhaji abdussalam Mai fata na samu sunan nan da dalilin Kasuwancinsu fatocin da nayi Mata ta d'aya Hajiya Saratu wadda tsawon shekaru bamu tab'a haihuwa ba sai Bayan shekaru har manyantaka ta fara kamani Allah ya bamu haihuwar y'armu Fatima wacce taci sunan kakarta ne ta wajen uwa hakan yasa Muka fiyan kiranta da "Mamy " Gata da soyayya ba irin Wanda bamawa Zahra'u kasancewarta y'a daya tilo a wajenmu amma dukda gatan da muke bata baihanamu bata ilimin boko da na arabi ba Gabak'i daya Na d'auki yarda na bawa Mudan Wanda Duka huldar kasuwanci na Shi na sanya a ragamar abun kasancewar girma ya fara kamani shi kuma lokacin yana tashen yarinta duk wasu garuruwa da nake huld'a dasu shi yake zuwa ya wakilceni sosai na dorasa akan dukiya ta saboda yarda Wanda a ido ya nunamun yafi kowa kaunata tare da iyalina ina son mudan har cikin raina Wanda har sauran y'an uwana sukance Nafi kaunarsa akansu Nayiwa mudan duk wani gata na Gina masa Gida Tafkeke na saya masa mota sannan koda ya tashi neman Aure Nina tsaye masa Akan hidimar komai duk wani gata da Dan uwa ke yiwa Dan uwa nayiwa mudan da gangan nake sakar masa kofar dazai samu alheri ina sane saboda ina son Shima yazama wani Abu ko Bayan raina ya zama shine zai kula da iyalina da dukiya ta hakan yasa bana boye masa komai yasan duk wani sirrina yana kanena amma bani da abokin shawara sama dashi ashe bansaniba soyayyar ido mudan yakemun bansani ba ashe mudan Makasar rayuwata yake nema k'watsam wata rana da bazan tab'a mantawaba ranar bak'inciki,ranar da ta kasa goguwa a cikin tarihin rayuwata muna kwance tare da iyalina a lokacin Zahra'u ta zama budurwa Har anfara shirye_Shiryen Aurenta Dan mutane da dama bama jigawa kadaiba har sauran jahohi sukan fito su nuna.suna son zahra Saboda yarinyace mai matuk'ar nutsuwa da hankali Ga kyau uwa uba tarbiya Dan zahra bata tab'a b'atamun raiba ita da mahaifiyar ta mariganyiya Muna cikin bacci mukaji barayi sun duro mana sosai hankalinmu yayi tsananin tashi ba wacce muka tunano sai y'armu Duk mun rikice mun dunkule waje guda a haka mukaga Shigowar garda_gardan samari Wanda bazan iya cewa ga yawansu ba saboda tashin hankalin da muka shiga gabak'i d'ayansu suka zagayemu da bindiga gaba d'aya fuskokinsu a rufe Na tsakiyarsu ne ya bud'e fuskar Wanda saida na kusanyi sumar tsaye ganin Mudan ne tsaye da bindinga ya saitani dak'yal na iya D'aga baki cikin tashin hankali na ce "Mudan ,mudan" Kecewa yayi da wata mahaukaciyar Dariya ya ce "Kana mamakin gani na a nan ko to ka daina mamaki nidinnan da kake gani makashinka ne da hannuna zan kasheka yau na kashe iyalanka gabak'i d'aya zan mallaka gabak'i daga dukiyarka Tun Asali daman ni ba Kaunarka nake ba dukiyarka kawai nake So kuma Alhmdllh lokacin amsarta yayi saboda Nasan Duka gaba d'aya ilahirin adadin dukiyarka da kadarorinka ina son Ka daukomun duk wasu takkadun kadarorinka da baka bani ajiyarsu ba ka mik'omun da hannunka kafin na kasheka" sosai hankalina yayi tsananin tashi Dan uwana Ace akan dukiya zai iya kasheni nashiga tashin hankali da rudun da bantaba shiga ba ranar ina hawaye na ce "Mudan zan mallaka maka Duka dukiyar daka buk'ata amma ka sani Amana Bazata barka ba mudan ka mance cewar ni jininka ne ka zab'i da ka kasheni Akan dukiya daudar duniya Tabbas yau na yarda da cewar d'an Adam bashi da Tabbas" wata irin Tsawa ya dakamun ya ce "Bana buk'atar jin wani Wa'azi daga gareka ka bani abunda na fad'a" Suna tisamun bindiga aka naje na D'auko masa gabak'i d'aya takaddun kadarorina sannan nasa masa hannu a wasu takaddun da tashin hankali baisa na tuna takaddun menene Matata cikin tashin hankali da bak'inciki ta ce "Amma kaidai mudan anyi butulu mugu azzalumi macuci insha Allahu karshenka bazaiyi kyau ba saikayi mutuwar wulakanci makaskanci " Harbin da yayiwa Matata ne A kirji ya k'ara rud'ar dani da shigar dani cikin tashin hankali daidai lokacin da naga shigowar zahra D'akin tana shirin shigowa Na ce "Ki gudu zahra karki shigo ki gudu karki yarda mugayen nan su kamaki zahra ina son ki tsira juyawar da zasuyi Su bita tana ji tana gani ta Ruga a guje inaga lokacin da wasu daga cikinsu suka mara mata baya kafin kuma Naji Jiniyar y'an sanda cikin tashin hankali Suka rude mudan yace mu maza mu tafi Harbin nan da nayi ne ya janyo hankalin jami" an tsaro d'aya daga cikinsu ya ce "To shikuma wannan yazamuyi dashi" mu tafi dashi mun kasesa a.hanya suka fad,a suna sungumata kamar wani yaro Cikin boot din mota suka jefani sosai nasha azaba kamar zan rasa rayuwata Kafin bansan Inda suka tsaya ba saigani nayi sun fiddo ni sun jefani cikin daji suna saita ni da bindiga daga lokacin bankara sanin abunda ke faruwa ba duk halin da na shiga na shige shi ne sanadiyar d'an uwa ya kashe mun mata a kan ido na yaso hallaka rayuwata inbanda Allah yasa ina da sauran kwana a gaba "ya k'arasa fad'a cikin hawaye " Kowa dake palourn saida ya girgiza dajin wannan labarin wai Dan uwanka ne yayi maka haka musamman zahra da yau ta had'u da kakanta sannan taji Tarihin mahaifiyarta sosai su Ammy da MD suka jajintawa Baba sannan sukayi Allah wadarai da wannan D'an uwan nasa ranar Baba jinshi yayi cikin wani irin farinciki ganin jinin y'artasa harda jikokinta md ko yasha alwashin saiya kwatowa baba hakkinshi a wajen Dan uwanshi duk inda yake bayan komai ya lafa Baba ta kalli ammy ya ce "Hajiya naji kince Zahra ce maman yaran Nan ko kina nufin ki cemun matar jikana ce "Murmushi dauke da fuskar ammy ta ce "Eh baba matarsa ce Allah ya kawoka a daidai lokacin da muke da bukatarka Kallonsu Zahra tayi har md ta ce "ku bamu waje zamuyi magana"A tare suka tashi Zahra jinta take cikin farinciki marar musaltuwa bayan ammy tayiwa baba tsoho bayanin yanda asalin aurensu Zahra ya kasance saidai ta boye musu na dalilin auren akan matarsa saboda batason Zahra ko danginta suji abunnan abun kunyarta ne Sosai baba yayi mamakin al'amarin ta wani bangaren Kuma yaji Dadi Sosai da ammy ta fada Masa yanzu md yanason Zahra Sosai itace dai take tunanin ko Bata sonshi bazata amince da koma Masa ba sannan batasan ta yanda zasu tunkari iyayenta ba sun tattauna Sosai tsakanin Ammy da Baba har Kaka kafin su tsaida magana akan jibi idan Allah ya kaisu za a tafi garinsu baba ayi masu bayani sannan a Basu hakuri haka ko akayi ranar suka shirya gabaki dayansu Ammy,kakan Zahra,Chuchu,Zahra,da triple dinta sai Hajiya Kaka ,md ne kadai ba a je dashi ba bayan isarsu batsari Kai tsaye gidan bappa suka wuce Wanda Zahra itace ta gwada musu hanya Banda faduwa babu abundan gabanta yake Sosai Aka karramasu Dukda zarha Bata yarda ta had a Ido da kowaba gabanta kawai ke faduwa A sace take Kallon baba da Shima tunda ya shigo ita yake kallo fuskarshi ba alamar walwala ganin da Zahra a tafiyar bappa yasan maganace Mai mahimmanci hakan yasa ya Kira Yan uwa baba su mama habi kowa duk ya hallara a dakin bayan an gaggaisa cikin mutunci Nan ammy tayi musu bayanin komai game da auren Zahra da sukayi da d'anta a boye har ciki ya Samu har zuwa haihuwarta suma dai Bata fada musu dalilin auren na md ba ta ce dai shirme ne irin na Yara sannan ta Kara kafa musu hujja da nuna musu video din daurin Auren sunyi mamaki matuka da gaske Jin wanna chakwakiyar su mama habi kuwa ajiyar zuciya suka sauke dukda sunji zafin aurar da kanta da Zahra tayi Amma Kuma sunji Dadi da diyan suka kasance y'an halak baba ko cikin bacin Rai ya ce"Kin bani mamaki Zahra ina tarbiyarki,ina iliminki,har ki aurar da kanki ba tare da izinin iyayenki ba kenanma bani da wani amfani a wajenki Dan haka. Ki tashi kibani guri tunda bani da wata daraja a wajenki har Kika iya aurar da kanki ba izininmu ki tashi ki tafi bana bukatar ganinki"Baba ya fada cike da takaici,"Kuka sosai Zahra ta fashe dashi ta ce "Dan Allah Baba kayi hakuri ka yafemun.."Saikuma ta Kara fashewa da wani sabon kukan sosai baba ya nuna bacin ransa matuka.inda su ammy dasu baba har Hajiya Kaka hakuri kawai suke bashi kowa yayi mamakin irin yanda baba ya nuna bacin ranshi kasancewarsa mutum.mai hakuri dakyal da jibin goshi aka samu aka shawo kan baba Amma Kuma saiya gindaya sharadi akan Zahra bazata koma ba zata zauna a wajenshi har lokacin da zata yaye yaran ta mayar musu da Su "Nanfa hankali ya Kara tashi musamman na ammy da Chuchu "Hakuri ammy ta dinga bashi ta ce "Dan Allah malam kayi hakuri munsan mu masu laifi ne a gareka Amma ka sassauta a dauki abunnan matsayin kaddara Dan Allah malam kuyi hakuri a sasinta wlh yaron yayi matukar nadama kuma.yanzu haka Yana son Zahra Yana son idan kun amince ta koma a matsayin matarsa tahar abada Dan Allah malam kuyi hakuri kodan arzikin yaran Nan har ukku dake tsakaninsu"Ammy ta fada hankali tashe "Nanfa baba yace baisan wanna zancen ba Indai Zai yafawa Zahra abunda tayi mashi to zata zauna ne a wajenshi sannan ya Aiko mata takardarta tunda ba aure ne akayi na mutunci ba idan ba haka ba ta tashi ta bisu ya bar musu ita har abada"Sosai hankalinsu ya Kara tashi Banda Zahra ta taji sassauci gwara ta zauna a Nan din kawai "Baba tsoho ne ya saka Baki yacewa "Ammy 'kiyi hakuri Hajiya a barmata sudin Yana cikin fushi ne a Bari su huce kawai"Badan Ammy taso ba dole ta amince musu chuchu ko hada kukan Dan batason tayi kewar Zahra daidai da second yanda takejin zey a ranta haka takejin Zahra tamkar ciki daya suka fito Nan Hajiya Kaka ta gabatar musu da Baba matsayin kakan Zahra Sosai kowa yayi al'ajabi dajin wanna al'amarin baba ko yayi farinciki matuka na ganin mahaifin tsohuwar matar tasa Kuma kakan y'arsa Sosai yaji dadin bayyanuwar ahalin na Zahra dukda sunyi al'ajabi dajin wannan labarin na baba Mai rikitarwa Bayan sunci abinci an karramasu Wajen la'asr suka fito domin tafiya an cika musu ledoji da kindirmo Sosai Ammy da chuchu sukayi sanyi na barin Zahra mama habi da matar bappa suka rike triple chuchu ko ta garkame little Sosai sai kuka take ganin haka ya Sanya Zahra kasa da kanta Tana hawaye sai yanzu takejin kewar su da zatayo ga Kuma baba tsoho da ko sabawa basuyiba Shima tare zasu koma har mota suka rakosu Wanda chuchu dakyal ta Mika little ta ruga da gudu mota Tana kuka Ammy ko dauriya kawai tayi Tana rike da hannun Zahra ta ce "To takwara mun wuce saimun dawo ganinku"Zahra batasan lokacin da ta fashe da kuka jikin Ammy ba duk kallonta suke Sosai ta dinga kuka Ammy da itama zuciyarta ta kusa karyewa dakyal ta lallasheta ta shige mota da gudu Zahra ta koma ciki Tana kuka girgiza Kai kawai baba tsoho yayi Bayan sun Kara bankwana suka wuce cike da kewa da jimamin barin Zahra chuchu ko har suka Isa gida Tana kuka Dan ba Zahra kadai zatayi kuka ba hada triple da tayi muguwar shakuwa dasu kwana tare tashi tare kullum suna hannunta Ammy ma hakan ta kasance baba tsoho ko Shi kadai yake sake sake a ransa bazaiso abunda mahaifin Zahra ya fada ya faru ba watau na rabuwar Zahra da md yasan muddin Zahra ta rasa yaron Nan to fa tayi babban Rashin miji na gari Dan Shi kanshi yasan yaron mutumin kirki ne tashin hankalin da md ya shiga Najin labarin baro Zahra da da yaran baya musaltuwa Sosai ya burkucewa Ammy kamar Zai musu hauka su kansu mamakinshi suka dingayi yanda yake magana kasan Yana cikin tashin hankali ya ce "Ammy me yasa zaku baromun mata meyasa Ammy na fada maki ina son matata meyasa Zaki maida ita Gashinan kin lalata komai Ammy Ana neman rabani da matata wallahi bazan saketa ba kome zakuyi kuyi haba Ammy saikace Ba d'anki ba kinsan Sarai ina cikin tashin hankali shine saida kikayi yanda kikayi Kika rabani da mamy na Baki hakuri ba iyaka Ammy nayi regrade duk abunda nayi Ammy Amma kikaki hakura saida Kika rabani da matata why Ammy me nayi maki"Ya fada kamar Zai fashe da kuka"Ba Ammy ba hattababa tsoho saida ya tausaya Masa "Cikin kwantar da murya Ammy ta ce "Babu Wanda yafini sonka da Zahra babana nafi kowa kaunarka da Zahra saboda bazanso rabuwarka da itaba duk abunda nayi make nayine saboda tayi daraja da martaba wajenka ka gane amfaninta Amma bawai Dan karabu da ita ba ni zanfi kowa shiga bakin ciki ace ka rabu da Zahra In son Zahra tamkar yanda nakeson su chuchu "To Ammy meyasa Zaki Baro musu ita meyasa Zaki kaita wajensu Ammy yanzu kina gani sun amshe mun mata Ammy duk laifinki ne meyasa tun farko Baki sasintani da matata ta ba Kika dinga jamun Rai ni mamy tun ranar Dana fara haduwa da ita nasan darajarta da mahimmanci ta da amfaninta a cikin rayuwata.."Kasa karasa magana yayi saboda wani daci dayakeji a cikin zuciyarsa "Ammy ce ta ce "ka nutsu baba na dole ne a kaita Wajen iyayenta ayi musu bayani Susan halin da ake ciki saboda su sukafi kowa hakki a kanta kaga ko Baba da kagani shiya haifi mahaifiyarta to baikai dangin mahaifinta da mahaifinta hakki a kanta ba kayi hakuri harsu huce " bai tankawa Ammy ba saboda baima San abunda zaice mata ba Kuma, fuuuu yabar dakin kamar Zai tashi sama cikin tsananin bacin Rai "Chuchu ma Tana kuka ta Mike ta ce "Daman Ammy duk laifinki ne tun lokacin da yace yanason momcy kikakiya yanzu Gashinan kinja iyayenta sun amshe Mana ita"ta fada Tana tashi da gudu ta Ruga"Tagumi Ammy tayi ta ce "Oh ni !Fatima yanzu Kuma laifin Nan duka sun maidoshi kaina.........✍️⁩ *07026166536 domin magana da marubuciyar* 🅿️...........*91 & 92* & 🅿️..........*93 & 94* "Ki kwantar da hankalinki Hajiya insha Allah zai huce idanma bai huce ba ni da kaina zankoma na basa hakuri"Baba tsoho ya fada kafin yayiwa Ammy bankwana ya koma masaukinsa Da aka saukesa a gidan"Sosai Md ya burkuce ya shiga tsananin tashin hankali na rashin Zahra da yaransa gaba daya baya cikin nutsuwa cikin kwana biyu harya zabge ya rame saboda tashin hankali da rashin bacci Ga ko abinci baya iyaci saidai ruwan Lipton idan ya zauna ba Wanda yake tunanin irin Zahra Shi kanshi baisan Yana mata so har irin haka ba sai yanzu da tayi nesa dashi Gaba daya yashiga tashin hankali rasa Wanda zaiyi shawara dashi yayi sai jabir ya bude wayarsa ya Kira Dan tun Kiran da iyayen amira suke mashi ya dameshi ya sanyashi kashe wayarsa .....bangaren Zahra Itama Bata da wata walwala Sosai dukda kannen babanta na kokari a kanta Sosai baba ma Yana nuna mata ya hakura Dan har yaran saiya daukesu su yini wajenshi Amma Kuma har yanzu batajin Tana da walwala Sosai takejin kewar su Ammy ga Kuma tunanin Md da tarasa dalilin da Indai ta zauna ba Wanda take tunawa da irin rayuwar da sukayi a baya irinshi yauma Tana kwance Tana tunani batasan lokacin da wasu hawaye masu dumi suka zubo mata ba Haka kawai data zauna saita dinga tunaninsa ta rasa fahimtar abundanda ke damunta game dashi lura da rashin walwalar na Zahra ya sanya Mama habi tafiya da ita gidanta katsina Dan taci gaba da Kula da ita Komawarta katsina Zahra ta danji sassauci saboda koba komai akwai yaran mama habi Sa'anninta da Wanda suka fita sun zauna su danyi hira ta rage kawaici triple ko Daman idan ba yunwa sukaji ba tofa ba a kawosu wajenta suna hannun mama habi da yaranta haka dai rayuwa taci gaba mama habi naci gaba da yiwa Zahra gyara Sosai dukda damuwar da tasa a ranta ta rame yaranta ko sunyi b'ul b'ul abunsu gwanin sha'awa kamanninsu da mahaifinsu na Kara fitowa....a halin yanzu md kullum cikin zazzabi da ciwon Kai yake ya rame Sosai gashi yaki yaje asibiti Ammy ko itama duk hankalinta ya tashi ganin yanda beloved son din nata ya koma ita kanta batasan md Yana yiwa Zahra har irin wannan son ba sai yanzu lallashi ba irin Wanda batayi Masa ba Amma yakiji Baba tsoho ko Yana daya daga cikin gidajen Baki na md inda Ammy ta saukesa kafin Shima su waiwayi jigawa wajen ahalinsa sun Bari dai a gama da matsalar Zahra Ranar da Zahra ta cika sati ukku da tafiya idan ka kallesa saikayi Masa kuka saboda yanda ya firgice kamar ba mr MD billonia ba matashi da kudi Ranar ji yayi bazai iya jure rashin Zahra ba saboda yanda yakejin zuciyarsa kamar zata tarwatse a daddafe ya Kira chuchu a waya Koda tazo saida tayi hawaye ganin yanda Yayan nata ya zabge Address din garin da suka Kai Zahra ta basa tare da fada mashi drivern da ya kaisu baiyi wata wata ba ya Kira drivern a tare da jabir suka tafi garinsu batsari Wanda tafiyar sirri sukayi Allah yasa Drivern ya gane Gidan Koda sukayi sallama da bappa ya fito ganin Baki ne ya sanyashi masu iso har cikin gida Md kanshi Kasa ya gaishesu Har baba da yake zaune baba ya Gane jabir cikin girmamawa suka gaisa Yana tambayar jabir ya mutanen gidan sannan yayi mashi godiya akan Abunda yayi mashi Lura da shine baban Zahra ya sanya mD Kasa had'a ido biyu dashi dakyal jabir ya iya bude Baki ya ce "Baba Daman magane ce tafe damu akan Zahra"Inajinku wace magana kenan"Baba ya fad'a"saida jabir yayi Jim kafin ya. Dago ya ce "Daman hakuri ne muka zo mu Kara Baku akan Abunda ya faru Dan Allah Baba kuyi Hakuri wannan abokina ne Kuma shine mijin Zahra baban yaran shine mukazo mu Kara Baku hakuri "Kallon md baba da bappa sukayi kafin Bappa ya ce "Allahsrk shine yaron kenan To Ai komai ya wuce Hakuri an Riga anyi d'an Adam ai baya wuce rubutun Allah duka abunda ya faru ya faru ne a bisa kaddara da Kuma rabon yaran Nan dan haka daga bangarenmu ya wuce yaro tunda dai ba Zina sukayi ba Aure sukayi har aka haifi yaran ta hanyar sunna kaga ai komai yazo da sauki "saida ya md ya sauke boyayyar ajiyar zuciya "Baba Shima cewa yayi "Ya wuce Allah yafe Mana Tare "Ameen baba mungode jabir ya fada shiru sukayi kafin Jabir ya ce "Sai magana ta gaba baba yace kuyi hakuri Dan Allah ku mayar Masa da Zahra saboda Yana sonta Kuma ba rabuwa sukayi ba "nannefa baba ya murje ido ya ce "baisan wannan Zancen ba "Magiya Jabir ya dingayi Shima md ji yake kamar zai fashewa baba da kuka cike da magiya ya ce"Dan Allah baba kuyi hakuri ku yafemun wlh tallahi in son matata Dan Allah baba kuyi hakuri ku maidomun ita karku rabamu "Saida MD ya bawa bappa tausayi Kallon baba bappa yayi ya ce "Meyasa zakayi haka Yusufu kaida bansanka Da tsauri ba Kayi hakuri a barwa Allah lamarin Nan Karka shiga lamarin aure tunda kaga Allah shine ya hadasu tun farko dukda Bata shara'a a ba akayi abun to me zai Hana abar Masa sauran yayi ikonsa Dan Allah kayi hakuri ka janye fushin Nan Karka shiga ka zak'e cikin lamarin tunda ba a asan Abunda Allah zaiyi gaba ba"Numfashi baba yaja kafin yayi shiru saikuma ya dago ya ce"Na janye fushi na ka nemu yarda a wajenta idan ta amince ba matsala saiku sasinta Allah ya zab'a Abunda yafi Zama alkhairi"wata irin ajiyar zuciya mD ya sauke kafin ya dago ya dinga jerawa baba addu'oi Sosai ya shiga yiwa baba godiya yanda kasan yayi Masa albishir da gidan Aljanna"Jabir ne ya ce"Tana ciki ne bappa"a a a kanwar mahaifinta ta tafi da ita katsina yanzu Tana katsina ita da yaran"Cikin sauri MD ya dago ya ce "Bappa Dan Allah bamu address din gidan da take Dan Allah"Murmushi bappa yayi ya ce "Kai jikannan nawa ka cika azarbabi to bari Nak'i fad'a maka tunda dai Daman kwacen amaryace zakamun "Dan Murmushi MD yayi Yana Kasa dakai Yana Sosa keya"Shidai baba shiru yayi Jabir ne yayi dariya ya ce "A a a bappa ai kayi mata tsufa"Saida suka danyi barkwanci kafin Baffa ya Basu address din gidan Ba yanda baiyi dasu ba Su tsaya ko fura a Dama musu Amma suka kiya saboda saurin da MD yake su wuce katsina kudade bandir biyu md ya bawa su bappa Amma sukaki amsa ba irin yanda baiyi dasu ba Amma suka ki amsa suka kafe ba yanda ya iya sai maida su yayi a yammar driver ya wuce dasu katsina sai Bayan magrib suka Isa garin katsina salla kawai sukayi suka wuce Unguwar su mama habi dake Bayan high court Basu wani Sha wahala ba Wajen gane gidan almajiri suka tura suka ce ana sallama'bayan fitowar Almajirin ya ce "ance wai wa ake nema"Mamy"MD ya fada jabir yayi sauri ya ce "Kace Zahra ake nema"Kallon md yayi ya ce "waya santa da Mamy in Banda Abunka "Dukna riikicene shysa wlh jabir bakasan irin son da nakeyiwa yarinyar Nan ba shiyasa"Dariyar mugunta jabir yayi ya ce "Au Haba yaushe ka Fara son matar Wata tara Kuma tsaki md yaja yace"Kaga matsalata dakai kenan to wannan dai matar ta Har Abada ce Babu rabuwa "Dariya Jabir yayi fitowa Almajirin yayi ya ce "Ancewai Bazata fito ba "OMG"MD ya fada"Jabir ne ya ce "zasuyi tunanin wasune ko samari kaga Tana da aure bazasu Bari ta fito ba fa"Eh Kuma hakane "MD ya fada kafin ya kalli yaron ya ce "ka ce "Baban su Y'an ukku ne yazo"To Almarin ya fada Yana komawa"Ajiyar zuciya mD ya sauke Dan yaji Dadi koba komai ana tsare Masa igiyar aurensa Fitowa Almajirin yayi ya ce "ance wai ku shiga"Ajiyar zuciya mD ya sauke jabir ya bawa Almajirin 2k kafin su shiga Cikin gidan da a palourn Mai gidan aka saukesu Kafin mama habi ta shigo da hijab dinta dafara'a ta tarbesu suka gaisheta Cikin girmamawa Bayan ta zauna ta ce "Kuyi hakuri an tsaidaku waje bamuganeku ba saidaga baya"Murmushi jabir yayi ya ce "Ba komai mama"Madalla Diyarta ce to shigo ta aje musu ruwa da lemo Bayan ta gaishesu ta juya mama habi ta ce "Ku Sha Mana"Jabir ne yasha MD baisha ba "Shiru sukayi kafin mama rabi ta ce "koba a fada ba nasan ga Baban yaran nan ganin Kama karara Masha Allah"ta fada Tana Kallon md "Murmushi Jabir yayi ya ce "e shine mama. Daman zuwa mukayi mu Kara Baku hakuri"A Haba yaron Nan hakuri Kuma na me ai komai ya wuce anzama d'aya tunda harda zuri'a Allah dai ya Raya Ameen MD ya fada Kasa Kasa kafin jabir ya ce "Mungode Daman daga Chan batsari muke munje mun karaba su Baba hakuri Kuma sun hakura harma sun amince da maganar Komawar Tata suma suka fada Mana Nan inda take.akan muzo Kuma mu nemu amincewarku. Da Tata shine mukazo Mama Dan Allah ayi hakuri ta koma dakinta wlh Yana sonta Kuma insha Allah zai riketa da Amana"shiru mama tayi kafin ta dago ta ce "Ai ba matsala tunda Sun amince muma mun amince Allah zaba Abunda yafi alkhairi saiku nemu yarda a wajenta Bari na shiga na turo muku ita "ta fada Tana mikewa ta shige ciki"MD jinshi yayi Cikin wani irin farinciki Jin abun ya Fara zuwa dasauki Koda mama taje ta fadawa Zahra wadanda ke tafe Saida tayi mamaki mama ce ta ce "tashi ki Mike kuje da yaran ku gaisa ko"Zahra kamar zatayi kuka ta ce "Dan Allah akai mashi yaran ni ba sainaje ba"Dukda Tana da bukatar ganin nasa"Tsaki mama habi taja ta ce "Da Allah tashi kibani waje bansan shiririta kije ku gaisa mutanen su taho tundaga kaduna saboda ke Dan iskanci Kiki zuwa ku gaisa maxa tashi kije kafin ranki ya b'aci"ganin ran mama ya b'aci ya sanyata mikewa da Akhbar a hannunta Ta fito MD suna zaune Yar mama habi ta kawo mishi yaran su biyu Amar da Little Sosai ya yaba yaran sun Kara kyau da wayo har Dariya sunayi sunyi bul_bul gwanin ban sha'awa Duka biyun ya dauka Yana musu Dariya ya ce "oyoyo my kids I really miss you so much please karku sake nesa da daddynku zai shiga wani Hali"Daidai shigowar Zahra Cikin hijab sab'e da Alkhbar tunda ta shigo palourn MD ya kafeta da kallo Bako kiftawa yanajin wata irin kauna da soyayyarta na Kara fusgarsa ji yake kamar yaje ya rungumeta Harta zauna Yana kallonta a sace Zahra ta kellesa idonsa suka sartse Cikin na juna sauri tayi ta kauda Kai gabanta na faduwa nauyayyar Ajiyar zuciya mD ya sauke yanajin wani irin sanyi na ratsa sa shiru Zahra tayi Bata tanka ba jabir ne ya ce "Hajiyarmu ina yini Kodai har yanzu fushin ake damu nidai ina bada hakuri Kuma ina wanke laifi na "Dan Murmushi Zahra tayi ta ce "Ina yini Yaya jabir anzo lfy"lafiya qalau ya triple dinmu "Alhmdulillahi"ta fada Kasa Kasa Tana wasa da zoben hannunta"MD bai daina kallonta ba kamar zai cinye ta Biyun ya aje kan sopa kafin ya koma kujerar da take kamar zai shige jikinta saurin matsawa tayi tare da satar kallonsa suna hada ido ta Galla Masa harara"Mika hannu yayi ya amshi little dake Zillo a hannunta Ajiyar zuciya ya sauke tare da kissing din little ya ce "i Really miss you my All above I love you so much my beloved daughter ina sonki Sosai takwarar Ammy na Kuma Favorite wife d'ina gaki Kuma daughter ta "ya fada Yana mata Dariya kamar tasan me yake cewa tahau Masa Dariya hada Zillo "Tabe Baki Zahra tayi Tana Shirin mikewa ya ruko hannunta juyowa tayi tare da tsatsaresa da Dara daran idanunta tare da juyasu ta ce "ka sakeni meye haka gaban mutane da Allah"ajiyar zuciya ya sauke Yana kallonta ya ce "Please ki dawo ki zauna Dan Allah muyi magana wajenki nazo"Kamar bazatace komai ba saikuma ta ce"Inajinka Amma ka.sakeni"Ai na sakeki nasan tafiya zakiyi Dan Allah ki dawo ki zauna" to ka sakeni Mana ha a saikace wata yarinyar nace ba inda zanifa "sakinta MD yayi ganin Bata tafi ba ya sanyasa sauke ajiyar zuciya Bayan ta zauna Dan nesa dashi Tana wani hade fuska Cikin kakkausar murya ya Fara magana Cikin sigar lallashi da kwantar da Kai ya ce"Dan Allah Dan girman Allah Mamy kiyi hakuri ki janye fushin da kike Dani wlh nayi regrade duk Abunda nayi maki bana daidai ba Ina sonki Mamy son da bazan iya kwatantashi da komai ba son da bantaba yiwa wani mahaluki irinshi ba Mamy shigowarki rayuwata nasan abubuwa da Dama Wanda a chan da ban sanshiba Mamy shigowarki rayuwata nasan meye so inasonki son da ni kaina bazance ga adadinshi ba Ina sonki fiye da yanda nake son kaina Mamy Dan Allah kiyi hakuri ko bazaki Soni ba yanzu Ina neman alfarmar da kidawo gareni mu shimfida sabuwar rayuwa irin ta kowasu ma'aurata mu gyara kuskuren da mukayi a baya mu tarbiyantar da yaranmu sannan mu Basu Kula irin wacce kowasu iyaye ke bawa yaransu Dan Allah Mamy Ina kaskantar da kaina akan kiyi hakuri ki dawo gareni insha Allahu zan koya Miki Sona da kaunata Zan Kula dake Zan soki na kaunaceki na baki duk wace kulawa Dan Allah ki ceci rayuwata please Mamy"Sosai Zahra tayi mamakin Jin furuccin nashi a gareta wai yana sonta tunani tayi bafa ita yake so ba kawai saboda yaranshine da yake mugun so shekara goma bai samu haihuwa ba shine zaiyi mata wayau yace Yana sonta ta koma gareshi Ya wulakantata shida matarshi karshema Kila ya saketa ya kwace Mata yaran tunanin wanannne ya dira tsam a cikin zuciyarta Sosai taji ranta ya b'aci lokaci guda ،mikewa tayi tare da kallonsa ta ce "zamana da Kai ya Kare babushi bazan koma gareka ba ka koma chan Wajen matarka Amma ni Nan da ka gani karka Kara tunanin wai zan koma maka inma mafarki kake. Ka farka kagama tafiyata"Tana game fadar haka tabar palourn Cikin sauri tanajin wani daci da zafi a cikin zuciyarta Jin yaudarar da suka shirya Mata a cewarta"Tashi MD yayi Cikin tsananin tashin hankali ya bita, tuni tabar palourn dafe kanshi da yayi matukar Sara Masa yayi ya ce "Innalillahi wa Inna ilahiraji'un "Ganin Yana Shirin faduwa ya sanya jabir yayi sauri ya tallabeshi ya zaunar dashi Shi kanshi jabir baiji dadin Abunda Zahra tayi ba yarasa wata irin bakar zuciya ce da ita shi har yanzu baiga wani laifin zo a ganin da MD yayi Mata ba take wahalar dashi Haka idan taimakonema ita MD ya Fara taimaka bataji laifin kawarta ba saishi mamakin MD yake Akan wani irin so ne wannan yake yiwa Zahra da har take Masa irin wanna wulakancin Yana shanyewa Wanda tunda yake bai Tana tunanin akwai macen da MD zaizo tayi Masa haka ba matanda rububinshi sure Amma ya like yarinyar karama na Shirin nakasashi "MD. Wani irin zafi yakeji a cikin zuciyarsa kamar zai fashe da kuka ya kalli jabir ya ce...........✍️ *Domin magana da marubuciyar 07026166536* 🇳🇬 *Happy Independence day* 🇳🇬 _*Miss Hajo ce*_🤙 ⁦🇳🇬⁩*Happy Independence*⁦🇳🇬⁩ *_Miss Hajo ce*_ 🤙 🅿️............*95 & 96* & 🅿️............*97 & 98* _*SEMI FINAL*_ ⁩💃💃💃 "Why jabir me nayi Mata da zata nunamun irin wannan tsanar wlh jabir Ina son matata bazan iya rabuwa da ita ba please me yasa ta Kasa fahimtata "Kayi hakuri bloody Dan Allah komai yayi farko Yana da karshe kamar Wanda aka zabura haka MD ya aje little yabar palourn ya fita daga gidan y'ar mama Habi tazo ta dauki yaran jabir ya fita ya bishi MD dafe kanshi yayi da yakejin kamar zai rabe biyu ranar hotel suka kwana Dan MD ya dauki alwashin bazai koma Kaduna ba harsai Zahra ta amince Masa Tundaga ranar MD.basu koma kd ba hotel suke kwana kullum saisunje gidan mama habi Saida Yaga yaran Amma Zahra taki bashi hadin Kai ta fitoma su gaisa kiyawa take mama habi ko Sosai ta dinga Mata fada akan wulakancin da take yiwa bawan Allahn Nan yayi yawa Yauma Bayan sun tafi Bata yarda ta fita ba kwance tayi Tana hawaye ita. Kanta yanzu karya take ta ce "Batason Musty Saidai Kuma batajin zata koma Masa ya wulakantata"MD Saida sukayi sati biyu a katsina suna zarya jabir harya Fara gajiya a lakacin ne Kuma MD ya Fara wani irin ciwo Zazzabi da azababban Ciwon kai yau tunda safe Jabir Yana lekawa dakin ya samesa durkushe Yana Numfashi sama.sama hankali tashe Jabir ya dinga kiransa Amma baya iya mayar Masa sai Numfashi yakeja Cikin kidimewa da taimakon ma'aikatan Wajen aka Kai MD asibiti Kai tsaye medical center aka wuce dashi da isarsuma emergency akayi dashi Ammy jabir ya Kira ya fada Mata suna katsina MD ba lafiya "Cikin tsananin tashin hankali Ammy ta ce "Katsina Kuma jabir Me ya kaiku katsina meya samesa"Hankali tashe ya labarta Mata akan Zahra ne satinsu biyu garin"Salati Ammy tayi ta salamce ta ce gamunan yanzu"Hankali tashe Ammy da chuchu suka Wuto katsina kasancewar ta fly suka hau yasa sukayi saurin zuwa Sosai hankalinsu yayi matukar tashi ganin halin da md ke ciki Cikin kuka chuchu ta ce "Ya Jabir Ina Take fadamun wani gida ne take "Ki Bari chuchu a Fara sanin halin da yake ciki tukwana ayi wata magana daga baya "Cikin kuka ta ce "Yaya jabir Dan Allah ka fadamun please ka kaini gidan da take Dan Allah "Ganin irin yanda chuchu ke kuka Ya Sanya jabir daukarta a mota ya dinga lallashinta har suka iso gidan da Zahra take Cikin kuka ta shige Gidan a palourn ta samu Zahra itama dukta rame Tana bawa Amar Madara Cikin tashin hankali da kuka chuchu ta ce "Shikenan momcy Kin kashe Yaya Kin sakashi Cikin wani Hali saboda soyayyarta da yake maki meye laifinshi Dan yace kawai Yana sonki Momcy Yaya Yana halin mutuwa ko rayuwa saboda ke.."ta karasa fada Cikin wani irin kuka Mai cin rai"Hankali tashe Zahra ta Mike kadan ya Hana Bata saki Amar ba cikin tsananin tashin tashin hankali ta Dora hannu aka saikuma ta fashe da kuka ta ce "Na shiga ukku chuchu Yana wani asibitin "Medical center ta fada cikin kuka ai Zahra Bata kuma sauraransu ba hijab dinta kawai dake kusa da ita ta sanya ba Shiri tayi waje a guje kamar wata mahaukaciya Tana fita ta tsaida napep ta fada Masa asibitin dazai kaita hankalinta matukar tashe suna Isa asibitin bama ta saurari Mai napep dinba Dan bama ta fito da kudi ba hango Ammy da tayi jikin wani ward ya sanyata rugawa a guje ba Abunda take in Banda kuka Tana zuwa ta fashe da kuka ta fada jikin Ammy Tana kuka ta ce Dan Allah Ammy karya mutu Ammy wlh Ina son mijina dan Allah Ammy ki taimakamun"ta fada Tana fashewa da wani irin kuka saikuma ta zabura ta ce "Ina ne inda yake Ammy Dan Allah"Ammy na hawaye ta nuna Mata dakin"Ai Bata saurara kowa ba ta Ruga a guje Tana hangoshi doctors biyu akanshi batasan sanda ta Ruga ta fad'a jikinshi ba Tare da fashewa da wani irin sabon kuka ta garkamesa ta ce "Dan Allah ya musty ka tashi karka tafi ka barni wlh Ina sonka please ka tashi Dan Allah"sosai ta rumgumesa doctors din duk kallonta suka tsayayi MD kamar cikin bacci yakejin kamar Zahra daukarsa mafarkine Saida ya bude idanunsa da sukayi Masa nauyi ya sauke a kanta data Haye kirjinsa Tana kuka"numfashin da taking yayi ne ya sanyata sauri tashi tare da saurin Kama hannunshi ta cikin Ido suke kallon juna yunkurawa MD yay ya tashi zaune kamar ba shine aka kawoshi Rai hannun Allah baisan Wanda wasu irin hawaye masu d'umi suka zubo Masa ba tare da gark'ame hannunta yayi sosai Yana hawaye ya ce"Dan Allah Mamy kiyi hakuri karki rabu Dani wlh Ina sonki har cikin zuciyata banajin Zan it's rabuwa dake Kuma na rayu please ki tausayamun"ya karasa fada Yana kuka kamar ba namiji ba "Komawa kirjinshi Zahra tayi Tana shashskar kuka ta ce"Kayi hakuri duk Abunda nayi maka Dan Allah Abban triple na shirya rayuwa dakai na har abada Ina sonki Nima Kuma zankoma maka please ka warke banason ganinka cikin wannan halin "a matukar zabure MD ya rukota ya juyota Yana kallon fuskarta ya ce"Ke kike fad'ar maganar Nan da bakinki Mamy da gaske kike kina Sona ko ko kunnuwanane suka jiyemun ba daidai ba "Zahra na hawaye ta gyada Masa Kai "Ai MD baisan lokacin days sake rungumota jikinshi ba cike da farinciki da tun haihuwar triple bai Taba shiga irinshi ba ya ce "Thanks you thanks you so much my all above ngd Mamy da amincemun da kikayi Zaki koma gareni nagode "Lafewa jikinshi Zahra tayi Tana Murmushi Tana Jin wata nutsuwa na Kara ratsa ta tanajin Kamar ta sauke want gagarumin nauyi a kanta it's kanta sai yau ta fahimci irin son.da take Masa batare da ta sani ba mamaki take har yaushe ta Fara sonshi haka Bata sani ba "Gyaran muryar da Ammy tayi ne ya dawo da su daga duniyar shaukin kaunar junan da suka lumtiya a hankali Zahra ta zame jikinshi daga nashi Tana dagowa ganin Ammy da Baba(kakanta) da tayi ne yasanyata Jin wata irin kunya tamkar ta nutse a Wajen Ammy ko da baba hamdala kawai suke Kallonta days zakayi musu kasan suna cikin tsananin farinciki haka chuchu da it's da jabir da suke bayansu da gudu chuchu ta ruga ta rungume Zahra cikin farinciki ta ce "Thnks you so much momcy kin ceci rayuwar Dan uwana ngd "Murmushi kawai Zahra tayi Tana kasa da kanta karasowa dakin sukayi inda MD yake baba ya zauna ya ce "Ashe jikinshi da sauki jikana hankali na duk a tashe da jabir ya fadamun zuwana kenan Masha Allah "Murmushi MD.yayi Wanda Ammy harsun mance yaushe rabon da yayi irinsa ya ce"Alhmdllh"Jaber ne Yana harararsa ya ce"Yana ganka ka Mike Haka kamar ba Kaine muka kawo Rai hannun Allah ba"Yana Murmushi ya ce "To bakaso kaganni haka ba na warke kaga silar ciwon Daman Kuma tayi magani"ya fada yanayiwa Zahra want shuumin kallo"Ammy na Murmushi ta ce"Babana baka ma karar muna Wajen ko"Sosa keya yayi Yana y'ar dariya"Bayan dr ya shigo ya ce To ya patient Kuma har ana dariya jiki yayi sauki kenan"Mikewa Md yayi tsaye kamar ba shine marar lafiyar ba ya ce "Ku taho mu wuce na warke"Dr ne Yana driya ya ce "To ranka ya Dade baka jira a sallameka ba"Na sallami kaina "ya fada Yana Sanya takalmi"duk dariya sukayi gaba daya gidan mama Habi suka koma Tunda suka shiga suka Fara jiyo kukan triple da gudu Zahra taje ta amshesu shataf ita Tama Manta da zasuyi kuka Dakyal ita da chuchu suka lallashesu har sukayi shiru tukwana tayi feeding dinsu chuchu sai tsiya take Mata Tana ciccijewa"Sosai mama habi taji dad'i da su Zahra suka sasinta kansu Nan aka Fara maganar yaushe zata koma number wayar Baba ta Kira Bayan sun gaisa take mashi bayanin komai cewa "yayi ba matsala habiba duk yanda kukayi daidai ne Ki barmusu ita su tafi kawai Allah ya bada zaman lfy"bayan tayi musu bayanin Abunda ya faru sosai kowa yaji dadin hukuncin na baba a ranar Suka juya kd Tare da Zahra da yaranta MD jinshi yake cikin wani irin farinciki Koda suka koma ya zaci Ammy bashi ita kawai zatayi su koma gidansu saiyaga sabanin haka ta wuce da ita bangarenta Nanfa MD.ya b'ata fuska Ganin Yana Shirin yin wata rashin kunyar gaban baba tsoho ya Sanya Ammy harararsa hakan yasa yaja bakinshi yayi shiru Koda Ammy ta Kira Hajiya Kaka ta fada Mata a waya An daidaita komai sosai tayi farinciki sannan ta Kara sanyawa aurensu albarka Dan ta koma maiduguri tun last week tundaga Zahra ta dawo Ammy ta shiga gyarata ciki da bai kamar wata sabuwar amarya har dilka da tsumin kamshi ake Mata gashi Ammy ta kasa ta tsare Akan md ta ce sai Y'arta ta Kara nutsuwa ta gyarata tukwana zata bashi Ita yaranta ko sosai suke wayau gasu Basu da kiyiwa Gata da soyayya suke Sha a gurin family din nasu ta musamman kayan wasa kuwa saisun ture idan yaran ka gansu saikace sunyi 7 months Nan ko watansu hudu daka kallesu kasan suna da tsananin lafiya irin zubin turawan Nan garesu"bangaren MD Shima Shirin yake sosai Dan Sabon gida ma ya bada kwangilar Gina Masa na gani na fada dan yace a Sabon gida Amaryar tasa zata zauna Banda lefe da suke shiryawa shida zey Dan makudan kudade na ban mamaki ya Bata Akan ta fita waje ta hadowa y'ar gold din nasa lefen da ba a taba yiwa wata y'a mace irinsu ba,yau Ammy ta Shirya bawa MD matarsa Bayan ta Sanya anzo an yarfa Mata Lalle dayayi mugun amsar fatarta kitso ta Sanya akayi mata shima Mai shegen kyau Tsadadden lace da yasha dinki Ta Sanya da yayi mugun yi Mata bala'in kyau simple make_Up asmy da tazo tayi Mata sai zolayarta suke ita da chuchu suna ce Mata amarya saidai ta hararesu ko ta musu Tsaki"Sosai ta fito tayi kyau kamar wata wacce zata zaben sarauniyar kyau ni kaina Saida na ce"Tubarakallah Masha Allah "saboda wankan ta wanku kallo daya zakayi Mata kasan eh ba karya ta cika Mrs MD a palour Ammy ta zaunar da su ta dinga yi musu nasiha sosai gami da nusarwa cikin hikima Ta dinga Musu nasihohi bayan nan ta ce "Iyayen Zahra shekaranjiya sunzo sunyi Mata jere dukda ba yanda bamuyi da su ba Akan su Bari karsu wahalar da kansu sukakiya jiya sunje sunyi Mata jere a Sabon gidanka daka cemun chan zaku tare sannan Nima nayi Mata nawa Allah yayi muku albarka yasa mutuwa ce zata rabaku"kafin Shima baba data Kira Dan yasa musu Albarka ya Dora Akan nashi Saida suka gama musu wa'azi sannan baba ya Kara Masa da nasiha akan yayi adalci a tsakaninsu duka matansa "Sai sannan ya tuno da Amera "Bayan sungama yi musu Nasiha Zahra kanta na kasa Ammy ta ce "Allah yayi muku Albarka "Kutashi ki tafi"A sanyaye Zahra ta Mike ta Ce "Nagode Ammy " MD ko jinshi yake cikin wani irin farinciki marar musaltuwa ya kasa kyafta Ido da kallon Zahra Masha Allah kawai yake fada a ransa Dan shikanshi yasan sai yanzu yayi Mata d'aya da d'aya rike hannun Zahra Ammy tayi har bakin labceciyar motar MD Zahra Tana tunanin Ammy batayi Mata maganar yaran ba MD ya kasa daurewa ya ce "Ammy Triple fa"Ga sunan su chuchu sunshirya su Marar Kara"Ammy ta fada Tana Kai Masa dankwashin wasa"d"an Kara yayi tare dayin dariya ya kauce "Suna tsaye Chuchu Da Asmy suka fito rike da yaran Sunsha Kayansu Suma masu mugun Kyau iri daya sosai sukayi bala'in Kyau chuchu ce ta ce "Wow Yaya gaskiya sainayi muku hoto irin wanna show haka"Murmushi yayi ya ce"Yi sauri kiyi to Kinsan banason hoto sosai"Hannunshi chuchu ta hada Dana zahra ta ce "Yawwa Ku rike a Fara muku Ku biyu"Nan chuchu ta shiga kyalla musu hotuna masu mugun Kyau a dalleliyar wayarta Kafin a Basu yaran a musu Baki d'aya wa'iya zubillah zo kuga irin kyaun da wanna couples din sukayi da yaransu kamar ka sacesu ka ruga Saida chuchu ta Gama kyallarasu kafin ta barsu sai dokin hotunan take Ganin Ammy tabar Wajen ya Sanya Zahra sakin jiki kallon asmy tayi kasa kasa ta ce "Dan Allah Anjima kuzo"Dariya asmy da chuchu sukayi suna tabawa asmy ta ce "So kike ya koromu da karnika kenan ana Shan amarcin Rana kawai zaimuzo muku ai harya hadomu da Kare"Dariya chuchu tayi ta ce kinsan ko yaya wlh ya aika"harara Zahra ta Galla musu kadin ya tsunkini Asmy ta ce "Saura ki tafi yau"Horn din da MD yayi Mata ne ya sanyata rabuwa dasu chuchu Dan ta lura shegantaka suke Shirin yi Mata kafinma ta bud'e taga ya bude Mata Shiga tayi tare da rufewa kallonshi tayi day rike little a Gabansa a ranta ta ce "Da itazaiyi tukin kenan it's kanta tasan cikin yaran yafison Little saidai ilimi yasa baka taba ganewa "motar yayiwa horn a hanya sai kallon Zahra yake da take d'an yiwa amar da Akhbar wasa dukda ya lura kunyarsa takeji kallonta kawai yake gwanin burgewa Yana Murmushi ji yake abun tamkar almara hannunshi daya ya saki tare da Kamo hannunta daya dake dauke da Lalle Abunda yafiso kenan Yana Murmushi yayi sama da hannun tare da kissing din hannun ya ce "I love this"Ganin Yana Shirin karkace tuk'in ya Sanya Zahra Jujjuya Masa idanu tare da shagwabe fuska ta ce "Karka kadamu fa"ai MD ji yayi kamar zai narke Saida tsikar jikinsa ta tashi irin yanda tayi maganar sosai ta rikita Masa lissafi lura da hakan Saida yasanya Zahra ta kusayin dariya tare da zame hannunta "Shima marairaicewa yayi ya ce "Zaki rikitani da yawa babe kija na kadamu a mota"d'an Murmushi Zahra tayi batace komai ba "Har suka Isa Yana kallonta gwanin burgewa yanda take komai cikin class sosai yake son komai nata musamman class dinta Dan shikanshi yasan ajin Zahra bana kananan Yara bane yana son mace Mai aji Daman Shi a rayuwarshi Koda suka isa Sabon tafkeken gidanshi da Shima anan gra din yake ni kaina Saida nayi kauyanci ganin irin wannan gidan aljannar duniya kenan ai duk yanda nake santin gidan md wancen wannan ya Shanyeshi ya Dame ya gidan yanda kasan kazo wata katafaren compony ko Kuma villa tafkeken gidane daya more da kayan alatu da more rayuwa girman gidanko bazan iya cewa ga kwatankwacinshi ba unguwa guda ita kanta Zahra Saida ta tsorata da ganin kyau da girman gidan yanda kasan wata tafkekiyae estate Yana rike da hannunta har suka nufi parlourn bayan ya umarceta da ta shiga da kafar Dama ai shigowar Zahra parlourn Saida ta raina kanta ganin irin turkey da Korea furnitures din da aka lafta a dakin to ai ko gidan shugaban k'asa kayan Nan da gidannan sai Haka rufin selin din dakinma kanshi abun ayi masa kauyancine tiles din Zahra ta kalla Taga Tana ganin kanta Kamar madubi Murmushi kawai MD keyi bayan isarsu tsakiyar palourn A lausassan carpet din da Saida na kusayin sumar tsaye danaga zai Dora twins kanshi ganin yanda yake sawaya ita kanta Zahra Saida ta kusa tsorata ajesu yayi gabaki daya a wayance ta take carpet Jin laushi ya sanyata sauke ajiyar zuciya itadai a rayuwarta Bata Taba ganin duk Abunda ta gani a palourn ba Bata karasa tunanin Nan ba taji ya janyota ya rungumota ta baya tare da rankwafar da kansa Yana shinshinar wuyanta ya Ce "Alhmdllh thanks you so much my all above kingamayimun komai a rayuwa Babu Abunda zance da ubangiji sai hamdala sannan nace ya barmu tare na har abada "Murmushi kawai Zahra tayi Tana kasa da kanta "Marairaicewa yayi ya Ce "please muje ciki muyi sirri aji Dani"RauRau tayi da idanu tare da juyasu ta shagwabe fuska "Suma Ce kawai md baiyi Ba ai baima tsaya wata wata ba yayi sama da ita bai direta ko Ina ba Sai bedroom ya sauketa a kataferen bedroom dinta...sosai ma'auratan Nan suka jiyar da junansu Dadi Kamar zasu cinye juna kunsan mutanen namu duka gwanayene a fagen Nan mD ko haukane kawai baiyiba Jin yanda Zahra ta Kara nice ta dawo Masa sabuwar budurwa Ai iya rikicewa ya rikicewa Zahra sai Wajen magriba suka samu komai ya lafa, fitowa Zahra tayi daga Wanka kallon MD tayi da har lokacin Yana gado kwance, wardrobe ta d'aga sosai tayi mamakin ganinta cike da Kaya na sawa wata Riga marar nauyi a cikin English wears din da ta gani iya gwuiwa ta Sanya sosai rigar tayi Mata kyau musamman data Dame ta bawa albarkatun jikinta damar bayyanuwa jikin mirror taje handrayer ta jona ta Fara busar da lallausan Gashin kanta cikin nutsuwa Daga kwancen da yake ba Abunda yake in banda kallonta Yana Kara godewa Allah d'aya mallaka Masa ita a matsayin Mata Shi kansahi yasan yanzu yayi aure yanzu yasan menene aure Yana Murmushi ya Ce "Kingamayimun komai Mamy bani da kudi ko bakin dazan iya biyanki da alkhairan da kikayimun shigowarki rayuwata kinsauya komai kedin haskece a cikin rayuwa ta data iyalaina kin bani farinciki da ba a taba bani Shiba a rayuwa kedin Allura ce cikin ruwa Ni Allah ya bawa damar chafka I love you so much my wife Ina sonki sosai Ina sonki son da Ni kaina bazan iya kwatanta adadinshi ba "kalamai masu sanyi da sanyayar zuciyar masoyi MD ya dinga zuba Mata Kuma sosai suke tasiri a zuciyar Zahra Saidai kunyarsa ta hanata mayar Masa saboda wani irin nauyinsa takeji Ganin magriba na Shirin gotawa ya Sanya Zahra Ce wa"Za ayi magriba fa ya musty kana kwance"Murmushi yayi tare da mikewa ya Ce "sorry malamata yaufa sai kinyimun karatun Nan Nak'i Mai narkar da zuciyar Mai sauraro cikin zazzakar muryar Nan Taki har nayi bacci sannan ki chanza sunan Nan kibani wani"Murmushi kawai Zahra tayi ta Ce "Uhm"kafin ya fito daga Wanka Harta tada sallar Magriba ganin Tana salla ya Sanya md Shima Sanya jallabiya lokacin magrib ya gota dan yasan yanzu masallataima sun Gama yasanyashi tada Salla a kusa da ita Zahra ta rigasa gamawa a ranta ta Ce"Insha Allah saina sauyaka daga sallar gidan Nan Dan ta Lura ko da sukayi zamansu a gidanshi na Zaria akwai lokutan da yake salla a gida dukda dai taga Yana da kokarin ibada sai idan ya makara Saida suka Gama salla md ya tuno da yaran mikewa yayi ya Ce "Subhanallah na Manta munbar yaran Nan a palour "a rude Zahra ta Mike ta Ce "Sai yanzu na tuna" ta fada Tana nufarr palour da gudu binta yayi kasancewar akwai tazara tsakanin parlourn da bedroom din ya Sanya basuji irin kukan da yaran sukayi ba wajensu suka karasa inda sukaga fuskar little Zahra zabe zabe da hawaye ita da Amar sun hade waje guda suna baccin wahala daga gani ba karamun kuka suka Sha ba Akhbar ko sai tsala kuka yake har Yana kakkafewa a matukar rude Zahra ta daukesa ta Fara jijjigashi da lallashinshi dakyal ta samu ta lallasheshi harta samu ya karbi mama ajiyar zuciya ta sauke MD ko little da Amar ya dauka a hankali ya Ce "Sorry my kids parent din ku sunbarku a palour sunmanta daku "Daidai lokacin da little ta farka itama ta tsala kuka dakyal suka samu suka lallashi yaran sai Wajen isha'i suka samu sukayi shiru bayan kowa ya koshi su kansu sai sannan suka tuna da yaran sunjima a palourn dole susha kuka su suna chan wata duniyar bama suji kukan ba "Da Dare Ammy ta Aiko driver da cooler abinci MD ya fita ya amso Bayan Zahra tayiwa yaran Wanka Wanda MD ya taimaka Mata da shiryasu Kaya ta Sanya musu Bayan ta feshesu da turarruka na Yara masu santin kamshi itama Daman tunda tayi Wanka ta feshi gashi Daman a gyaran da Ammy tayi Mata hada na kamshi Dan ko wake ta zauna saiyayi akamshi Koda suka samu yaran sukayi bacci wata duniyar suka lumtiya daren ranar dai Zahra ta raina kanta Dan MD ba wasa kishirwarshi ta watanni ya sauke a kanta Washe gari ma a palour suka aje yaran da safe Bayan an shiryasu suka babbaza musu kayan wasa Suma iyayen sunyi breakfast MD ya sungumeta suka koma ciki Suna chan suna zuba love dinsu Kamar zasu cinye junansu. chuchu da asmy da sukazo tun a waje suka Fara jiyo kukan yaran da gudu suka karasa suka daddaukeau sosai suka Sha dabi kafin su samu suyi shiru Shima Saida suka goye biyu tukwana suka samu bacci ya dauke su sunyi minti talatin a polourn Amma Basu fito kallon asmy tayi ta Ce "Jifa Dan girman Allah yanzu mintinmu nawa anan Wama yasan dadewar yaran a palour ga kofa ba rufe da key ba Dan Allah want mugun ma basai a sache yaran suna chan ba wlh saina fadawa ammy "Ta fada Tana lalubar number ammy "Asmy Ce ta Ce "Karki kirata Dan Allah "Allah saina fada Mata ba iya rainonsu zasuyi ba "Ammy na dauka chuchu ta Ce "Kinganmu Nan ammy munzo gidan muka iske Yaran a palour kofa a bude ba key sai kuka suke har yanzu Kuma Basu waiwayesu ba "Subhanallah irin ta'asar da zasu tafka kenan Daman Ina Shirin kawo masu aiki su taimaka.mata da aiki da Kuma nanny din yaran Bari yanzu yanzu nakira Mai samamun y'an aiki ta samo wacce xata dinga kula da Yaran"Ajiyar zuciya chuchu ta sauke ta ce "To Ammy"Saida su chuchu suka kwashe awa guda kafin suga fitowarsu hannunsu sartse cikin na juna MD yasha bak'ar shadda da tayi mugun amsar farar fatarsa har wani shining shaddar take tana walkiya Zahra ko sanye take cikin atamfa super Holland Wanda duk a cikin kayan data gani a wardrobe ne duka size dinta ne tasan aikin Ammy ne Dan Bayan dawowarsu ta taba amsar size dinta Zahra na Ganin su chuchu ta saki hannunshi wajensu ta nufa cikin farinciki ta na murmushi ta Ce"Yanzu kuka zo"Harararta asmy tayi ta Ce "a a a Nan muka kwana"y'ar dariya Zahra tayi ta ce"Sorry maida wukar sauke lillte a bayanta da tayi bacci Asmy tayi ta kwantar da ita chuchu Daman tunda Amar yayi bacci ta saukesa kallon MD sukayi suka gaisheshi ya amsa musu cikin sakin fuska "Kallon Zahra chuchu tayi ta Ce "Ina kwana auntynah"Harararta zarah tayi "y'ar Dariya chuchu tayi "MD dai kallon matar tasa kawai yake Wajen Yaran yaje kowanne ya Basu peck a kumatu kafin ya juya ya kalli chuchu ya ce "Kuyi Mata gyaran komai please Karki Bari tayi aikin komai na baki amanarta"Insha Allah Yaya"Chuchu ta amsa Tana dariya kasa kasa"Zahra ko Kallonshi kawai tayi Ganin ya kashe Mata ido daya ya sanyata kasa da kanta Tana murmushi Saida MD ya fita su chuchu suka samu damar zolayar Zahra Asmy ta ce"Kuntafi Kuna love kunbar Yara sai kuka suke "Dariya chuchu tayi ta Ce "Antafi sama musu kanne dai Dan matar Yaya twins da triple zata dinga Haifa Mana kafin 5 years gidan ya cika da Yara tako Ina "shegantaka sosai suka dinga Mata wani ta biyesu wani ta kyalesu yanda MD ya fada su chuchu sukayi aikin komai Banda Zahra da ta kula da Yaran Bayan sungama Mata sauran gyare gyare sun karaa gyara Mata kitchen dinta da jeren da bai musu ba suka sake Wajen ukku sukaji knoking chuchu ta je ta bude Ganin aunty zey Ce sosai tayi murna Bayan ta shigo parlourn Gaisheta Zahra tai ta amsa cikin girmamawa a Tare da cewa "ya bakunta "Alhmdllh"Ta fada kasa kasa "Masha Allah Ubangiji ya bada zaman lfy Mai dorewata fadad'a Tana daukar Zahra ta Ce "Nayi kewarki Ammynmu"Saida ta danyiwa little wasa kafin ta Ce "ki yafa gyale maza ne zasu shigo da Kaya"to "Zahra ta fada gyale Zahra taje ta dauko ta yafa Fita zey tayi ganinta sukayi da kawai Maza na shigowa da jibga jibgan akwatina na gani na fad'a Saida aka jere akwati hamsin reras a palourn Sosai su kansu su asmy sukayi mamakin kayan lefen zey na murmushi ta Ce "To Amaryarmu ga lefe dai munkawo na Bangaren Ango sai Kuma na Bangaren Ammy da chuchu munji dai su shiru"dariya chuchu tayi ta Ce"Naku wasa ne Aunty Zey kikaga namu saikun Raina Naku"Dariya zey tayi ta ce "Ah to muga nakun Mana"Sosai Zahra tayi mamaki Kamar tayi magana yanzu wanna uban kayan duka lefantane ikon Allah "Asmy Ce ta Ari bakinta ta Ce "Kai Masha Allah Aunty gaskiya Kaya sunyi Allah Ubangiji ya saka da alkhairi ya Kara bud'i"chuchu ma ta Ce "To mungode Dai Allah ya saka da alkhairi Bari mu bude muga ko kunyi Abun kirki"ta fada suna Fara bubbude kayan na gani na fad'a mikewa zey tayi ya Ce "Bari na wuce naji Ammy nayimun waya zantafi da little anjima ya taho da ita saina dawo"TO aunty angode Allah saka da alkhairi"ta fada tare da mikewa tarakata har bakin kofa kafin da dawo ciki sai sannan aka Fara bude kayan da ita dariya chuchu tayi ta Ce "Waida Aunty Zey kikejin kunya shiyasa duk Kika wani daddare Naga Baki sake da ita ba kodan hakane Tana da wuyar sabo miskilancin tsiya gareta Anna ke ai Naga Tana sake Miki Sosai ki saki jiki da ita Bata da matsala wlh sannan ko wasu shawarori kike da bukatar irin Naku na masu aure zata taimaka Miki ba ruwanta "chuchu ta fada Tana dariya "Girgiza Kai kawai Zahra tayi ta ce"Insha Allah Abun bamu Saba Sosai ba shysa Saida suka daddaga kayan kowace akwati shake take da Kaya Banda akwatin zinare ma guda na sarkoki da awarwaro da zobuna Masha Allah anyi Kaya na kece rainin sai magriba su chuchu sukayi mata bankwana suka wuce Ganin dawowar MD Da dare suna manne dajuna ya ce"My princess Kinga kayasunyu maki ko"Murmushi tayi ta Ce "Eh Ya musty Nagode Allah saka da alkhairi ya Kara bud'i "Ameeeenmmn matar aljanna "ya fada Yana juyar da ita washegari Nanny din su Yaran biyu sukazo Wanda Ammy ta daukesu suka Fara kula dasu inda iyayen sure zuba love dinsu ba Kama hannun yaro Dan MD fitama gagararsa takeyi yini yake a gida Sai da suka kwana biyar kafin su fito ya zagaya da ita gidan taga ko ina Wanda wani wajenma a mota yakaita saboda Nisan musamman katoton lambun Gidan Masha Allah gsky Gidan yayi matukar kyau cikin gidanko ko palour ne guda takwaas kowanne shake da kayan waje Banda biyu da suke dauke da irin namu na Nan nja saidai Suma Masha Allah Anan Zahra ta gane sune Wanda su baba sukayi Mata kenan Sosai ta Yaba da irin kokarin da baba yayi bedroom din dakinko 12 kowanne Shima shake da Kaya nasu tiple ma cike da kayansu Banda dakin wasansu Wanda aka Sanya kekuna da abubuwa a compound gidanma had a Bangaren wasan Yara an zuba uban Kaya shakatawa baby banbanci da park ranar Ammy ta turo da nata Lefen akwati Sha biyar mamaki duk ya Gama cika Zahra to su wanna wani irin kudine garesu Kamar basusan darajar kudi ba Cikar Zahra sati a Gidan Tana kallon palour MD ya shigo Tana Ganin yanda take fara'ar tasan akwai magana wajenta ya nufa tare da rungumota ta gefe ya Ce "rufe idonki"Murmushi tayi tare da rufewa "Ba ayi two second ba ya Ce "open your eyes"budewa tayi taga ya Sanya mata kwalin waya kirar iPhone14 a hannu wara idanu Zahra tayi ta Ce "Wow"murmushi yayi ya Ce "Surprised na farko kenan tukuicin budurcinki "Wow Zahra ta Kara fada cikin doki ta Ce "Thanks thank you so much my Love Allah ya saka da alkhairi ya Kara bud'i "ameeen princess"Kafin yamikar da ita yaja hannunta sukayi waje daidai Wajen dalleliyar jar motar da Zahra Saida ta tsorata da Ganin kyau irin na motar ya jata daidai mota ya tsaya Yana murmushi ya Zaro"Key"Din Motar Ya Mika Mata ya ce"Ga motarki my love Tukuicin bani farinciki da bawanda ya bani saike na Haifamun triple da kikayi"sannan Ya k'ara d'auko wani Key d'in ya mik'a Mata ya Ce "Wannan Kuma makullin gidanki ne Dake abuja na sanyani kuka da kikayi na rubuta da shaidu da komai ya Zama naki halak_Malak "Ai Zahra daskarewa a Wajen tayi ta rasa want irin farinciki zatayi kawai sai fad'awa jikinshi tayi batasan sanda ta fashe da wani kukan farinciki ba cikin kuka ta ce............ ✍️ *Domin magana da marubuciyar Kai tsaye neman Karin bayani tambaya ko Kuma sayan complete kardai ku Manta Auren wata Tara littafin kudine zaku samu complete dinshi ne Bayan Kun biya 500 kachal domin neman Karin bayani ku tuntubeni Akan number wayata Kamar haka 07026166536* _*Miss Hajo Ce*_🤙 👩‍❤️‍👨 *AUREN WATA TARA* 👩‍❤️‍👨 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* ( Miss Hajo) *Ga Mai Bukatar sayan complete doc na book dinnan a tuntubeni akan wannan number 07026166536* *FINALLY THE END الحمدلله*💃🏾 🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚 _BONUS PAGE_ 😝 🅿️................*99 & 100* Ta Ce "Bani da bakin da Zan yi amfani dashi Wajen gode make mijina kayimun komai a rayuwa ka bani farinciki Nagode Nagode Allah ya saka alkhairi Allah ya faranta maka fiye da yanda ka farantamun "Ta karasa fada cikin kukan farinciki "murmushi kawai MD yayi nayajin kauna da soyayyar matar tasa na fusgarsa ya Ce "Ameeeeeen my beloved wife ke Kika Fara bani farincikin da bantaba tsammaniba farincikin da dukiya ta suka kasa sayamun kome nayi maki ban Isa na biyaki tukuicin abunda kikayimun na alkhairai"Sosai Zahra tayi dokin motar murna da fainciki ba irin Wanda Bata nunawa mijin Nata ba addua ko ya sashi Kamar me Daren ranar Zahra ta bashi hadin kan da Bata taba bashi irinshi ba ta jiyar dashi dadi Sosai..satinsu biyu da tarewa Wanda irin love din da suke zubawa mutum yaji Saiya girgiza a satinne aka shirya tafiya jigawa gabaki daya suka tafi baba,ammy,Zahra,MD,sai triple kasancewar ta fly sukabi basuyi wata tafiya ba suka Isa Sosai baba yayi mamakin cigaba da sauyin da aka samu a garin ya habaka Sosai Kamar ba garin ba dakyal ya iya gane Unguwarsu Kai tsaye Gidan k'aninshi mai biya mishi suka nufa Ai Ganin baba Saida Alhaji tukur ya tsorata shida matarshi acewarsu fatalwace dakyal suka yarda shidinne Rungume juna sukayi Sosai alh tukur ya Sanya kuka ya Ce "Yaya Kaine Daman Ashe da raban xamu sake ganawa kenan karyace akayi Mana akace an kasheka "Baba na hawaye ya ce"nine da kaina tukur"kafin Kace me Yan uwan baba sun cika Gidan kowa yazo sai yayi kukan farinciki mutumin da daukarsu ya mutu kasa da shekara ashirin da biyar su ganshi yanzu dole suka girgiza Kuma cikin ikon Allah y'an uwan baba duka suna Nan da ransu Basu mutu ba"nanfa Kuma aka Fara yiwa Zahra kallon Mamanta Saida baba yace musu ba ita bace zaiyi musu bayani"A katoton parlourn Gidan aka saukesu Dan ba laifi k'annan baba dukansu a da chanma da halin su bare yanzu da cigaba yazo Shima babban gidane Nan mutane akayi ta kawo gaisuwa mutane duk sun cika Gidan Bayan ankawo musu Abun tarbar Baki daya daga cikin K'annan baba alh Habu ya ce"Yaya muna jinka kayi Mana bayanin Ina ka shige kaida Zahra tsawon Shekaru"Nan baba ya kwashe labarin komai ya Basu ciki har da haduwarshi dajikarshi da Kuma rasuwar y'arsa da irin taimakon da MD yayi masa "Salati kowa keyi masu kuka nayimasu tsinewa mudan nayi Ya"Yan Yan uwa ko Mata da iyaye sai rungumar Zahra suke Sosai kowa yayi mamakin Jin mudan shine ya kashe Hajiya saratu(kakar zaha?)Sannan yayi kokarin kashe Dan uwansa godiya Sosai aka shiga yiwa Ammy da MD Alh tukur ne ya Ce "Haba biri yayi Kama da mutum Amma Abun Nan yazo da mamaki mudan fa dashi akayi suturar Hajiya saratu ya dinga kukan munafurci a fuska yafi kowa shiga tashin hankalin ance Mana y'an fashin da suka kasheka Suka tafi da gawarka da Zahra har adduar ukku da sadakar bakwai data arba'in Saida Akayi muku Ashe dai da sauran kwananku a gaba gaskiya mudan bazai gama da duniya lafiya ba Haba kenan shiyasa da aka tambayesa dukiyarka ya Ce Babu abunda naka Dake hannunshi duka ka amsa sannan barayin sunkwashe komai haka kawai muka kyalesa saboda mu Kai ka fiye Mana komai bamu kuma waiwayarsa Akan dukiyarka ba saboda a ganinmu Fatima maringanyiya itace magajiyarka fiye damu to Bata Nan da Tana Raye ne ma a lokacin zamuce saimun kwatar Mata hakkinta ba ayi shekara biyu da faruwar Haka ba Mudan ya kwashe komai nasa Dake Nan har Gidan daka saya Masa ya sayar tare da matarsa da y'arsa sadiya da tun kana Nan aka haifeta suka tashi ya Ce wai ya samu wani babban aiki a kaduna Babu Wanda ya kawo komai akai mukayi mishi fatan alkhairi Tunda ya komai kaduna mudan mudashi ko a waya Sosai hankalinmu ya tashi kasan d'an uwa da d'an uwa bamu k'ara samun labarin mudan ba sai kwanaki Nanda shekara ba ayi goma ba Alh Habu yaje garin wani taronsu na professional suka hadu dashi dakyal ya barshi ya kaishi gidanshi Yana mishi fada Akan meyasa ya baro Yan uwanshi bai Kara waiwayaba Yana hawayen munafurci ya Ce "wai bazai iya Zama garin bane zuciyarsa ji yake Kamar zata tarwatse saboda rashinka da yayi yasa yaji garin ya fita a ransa haka dai habu yayi Masa fada ya Ce "Zai dinga zuwa"Koda habu yazo ya fada Mana Sosai mukayi hamdala Jin lafiya yake Dan a tunaninmu ma ko wani Abun ya samesa takanas sati na zagayowa mu biyar din muka shirya A mota mukaje domin mu ziyarcesa muyi mashi fada Akan ya dinga ziyartarmu ko hankalinmu ya kwanta saidai me Koda muka je saimuka tarar ya sayar da Gidan Harma wanda suka saya sunshiga Sosai mukayi mamaki da Al"ajabi mun tambaya inda suka koma Amma ba Wanda ya sani Daga lokacin muka Fara zargin mudan Akwai rashin gaskiyar da yake boyewa Ashe dai Haka dinne gaskiya mudan yacika Maci Amana Yayi Mana bazata"MD ya dago sai lokacin yayi magana ya na kallon alh tukur ya ce "Baba Shi Alh Habun Zai iya gane Gidan"Alh habu Dake gefe ya Ce "Kwarai kuwa Har Gidan Zan iya ganewa a Nan ne unguwar dosa saidai fa ya tashi Dan sau biyu muna komawa Amma ya tashi Babu Wanda Kuma yasan inda ya koma"ba matsala baba Indai ka gane Gidan Abun Mai sauki ne bazai wahalar kamuwa ba Indai har Yana garin kaduna Zai kamu "Malam sani ya ce"Tabbas hakane saidai ayi plane din ylda wuri saboda kar labarin bayyanuwarka yasanya ya gudu ko yayi maka wani Abun"Murmushi MD yayi yace "ba abunda Zai faru Insha Allah yanzu kawai yanda za ayi mu koma kd sai muje a nunamun Gidan"Alh tukur ya ce "a a a fa saikun kwana Taya zakusha doguwar tafiya haka Baku kwana ba "tarba ta musamman da girmamawa sunshata a garin Nan Zahra ko Yan uwa sai zuwa ganinta ake Wannan ya dauki Yaran wancen ya dauka cousine din Mamanta da diyansu Sai zuwa suke ana kulla zumunci duk sunyi musayar number da su kwana biyu sukayi a jigawa suka dawo kd Wanda MD duk jinshi yayi Kamar a Kaya saboda baby zahrar sa a tare dashi Koda suka Isa kd kafinma su wuce gida unguwar dosa suka nufa har bakin get din Gidan dukda an Kara sabunta Gidan ya kaisu suna Isa ya ce ayi parking Nan ne Gidan"Mamaki ya gama cika MD ya ce "Baba ka tabbatar kuwa ba batar Kai kayi ba"Comfirm Wannan shine Gidan bazan taba Manta sa ba "Kallon ammy MD yayi ya ce "Ammy wannan Ai Gidan su Amera ne kin Manta lokacin Dana aureta ma Anan Gidan ne kafin Daga baya su koma kawo"Ammy na sake sake a ranta ta ce"Tabbas Nan ne "Baba habu ne ya ce "Wace Amera kake magana yaron Nan"Matata ce baba kilan ko mistake kayi"Sunanta na gaskiya fa "baba habu ya tambaya"Sadiya"Md ya basa amsa gabansa na faduwa"Innallahi Aiko idan ba sa'a ba y'ar mudan ce sunanta sadiya ita daya garesa"Gaban Ammy na tsananta faduwa ta Ce "innalillahi wa inna ilaihiraji'un juyar dakan motar MD yayi "ya ce "Bari muje na kaiku Indai shine kuga fuskarsa idan Kuma bashi bane to"Kai tsaye Gidan su amira suka nufa sunyi mamaki matuka Ganin tundaga farkon layin har karshensa cike da motocin jami'an tsaro Koda suka karasa bakin get din Gidan cike yake da motocin Yan sanda Yan unguwa duk anfito anyone curgo curgo hankali tashe MD ya fito Ganin shine ya Sanya jami'an tsaro basu ce mashi komai ba tambayar days Daga cikinau yayi ya ce "ka shiga dai ciki manyan na ciki ranka ya Dade Daman Abun yashafeka gears da Allah ya kawokama kafin a kiraka"abunda ya shafeni Kuma "Md ya fada Ganin su ammy da baba da baba habu sun fito Dan Zahra k'in fitowa tayi "a tare suka shiga cikin gidan Sosai hankalin MD ya tashi ganin daddyn Amera hannayensa biyu cikin handcuffs sojoji da y'an sanda sun zagayesa amera da Mamanta sun biyosu sai kuka suke amera na Ganin MD ta ruga da gudu wajensa tare da ruko hannunsa a matukar rude ta Ce "Honey kaje Kayi musu magana zasu tafar mun da dad Dan Allah honey karka Bari su tafar mun dashi ba abunda yayi musu"ta fada cikin wani irin kuka Mai tashin Hankali"Kallon kallon aka tsaayayi tsakanin baba da baba habu da Kuma Baban amera da yake hawayen nadama a tare baba habu da kakan Zahra suka ce "Mudan " motsa hannunshi mudan yake Dake rike da handcuffs a matukar rude ya ce "Yaya Daman baka mutu ba "Baba Yana hawaye ya ce "Ban mutu ba mudan kaga ikon Allah a tunaninka ka kasheni saikuma ka Manta da Allah shine Mai iko Akan komai bakayi tunanin Zan rayu ba mudan Me nayi maka da na chanchancin Wannan danyen hukuncin Daga gareka mudan ka Manta cewar Ni jininka ne saboda son Abun duniya yayi maka yawa ka Manta koba hisabin duniya akwai na lahira"Mudan na kuka da idonsa ya ce "Hakika na cutar dakai Dan uwa na hakkinka kadai ya Isa ya Hana Ni zaman lafiya nasan ban chanchanci yafiya Daga gareka ba saboda ban chanchanci a yafemun ba Yaya Ina kunyar hada Ido kadai a yanzu"Ya karasa fada cikin wani irin kuka "salati ammy tayi ta salamce MD kanshi Saida yayi mutuwar tsaye Banda amera da Mamanta da sukaji wata sabuwar maganar ta bullo jami'an tsaronma tsaye sukayi suna sauraron wani case din sabo baba habu ne cikin muryar bacin Rai ya ce "Ai baka ga komai ba mudan na tabbatar bazakayi kyakyawan karshe ba Ina son ka fadamun Kaine Wanda ka kwantar da d'an uwa na tsawon shekaru kwance ka mantar dashi komai "Kauda Kai mudan yayi ya ce "Yau Rana ce ta tonon asiri a gareni Tabbas Nina kwantar dashi tare da y'arsa da tun sanda muka Kai musu Hari ta tsira muka neme ta muka rasa Wanda ba Wanda yasan yanda akayi ta tsira na rufe musu bakine dalilin dodon tsafinmu daye ke nuna Mana Kuna raye dukda ban gaskata kana rayen ba saboda Harbin da nayi maka banyi tunanin zaka Tashi ba "Hankali tashe Baba Habu,da baba ,da maman amera sukace tsafi Kuma Mudan kana nufin har tsafi make bamu sani ba innalillahi wa inna ilaihiraji'un"Banda kuka ba abunda Baban amera yake kukan nadama ya ce "na Fara tsafine tun kafin dawowata kaduna na hadu da wani abokina Wanda sanadiyarsa na fada harkar tsafi Ni mutum ne Mai tsananin son Abun duniya tun Ina yaro hakan yasa nake iya komai Akan Indai Zan samu kudi kisa a wajena ba wani abu bane ,na kashe mutane da Dama.....kasa karasa abunda yakeson fada yayi sakamakon kukan da yaci karfinsa salati kawai kowa yake Jin abunda Baban amera ke fadada bakinsa har Zahra da ta shigo Daga baya Saida ta tsorata you tayi Kamar zata ruga MD Dake kusa da ita ya ruko ta "dukta tsorata ,"tashin hankalinta da MD yake jiki baya musaltuwa dakyal ya iya Daga Baki ya kalli daya Daga cikin jami'an tsaron ya ce "Wan laifin ne yayi Wanda har aka zagaye Gidan. Da jami'an tsaro"Daya Daga cikin dpo din da MD yasa Akan binciken kisan babanshi da Kuma na Alh sammani aminin babanshi ya ce"Case din Akan aikin ka ne MD Kasan tun lokacin kisan mahaifinka Da na Alh sammani bamu bar bincike Akan wadanda sukayi Wannan aikin ba to a jiya ne bincike yagano Mana wasu Daga cikin manyan y'an fashin garin Nan Wanda muka gana musu azaba matuka Daga karshe sai yau da safe daya Daga cikinsu ya fada Mana da Shi aka kashe Alhaji dikko Da Kuma Alhaji Sammani bisa umarnin ogansu Alh Mudan Hakan yasa mukayi mazamuka zagaye unguwar sannan muka shigo muka kamasa Kuma Alhmdllh bamusha wata wahala ba ya amsa Mana laifinsa"innalillahi wa inna ilaihiraji'un kowa ke fada Ammy ji tayi mutuwar ta dawo Mata sabuwa a matukar rude ta fashe da kuka ta Ce "Daman Kaine Wanda ka kashemun miji tsawon shekaru me mukayi maka da muka chanchanci Wannan danyen hukuncin a gareka"MD ko shakesa yayi Cikin wata irin muryar bacin Rai idanunsa sun Rina sunyi jawur ya ce"Me mahaifina yayi maka dazaka kashe Shi me yayi maka me mukayi maka"MD ya fada cikin k'ara Wanda ke wurinma Saida suka tsorata dakyal jami'an tsaro suka kwace Mudan Daga shak'ar da MD yayi Masa wani irin huci MD yake Kamar Zai tashi sama Yanajin Kamar ya kashe Baban Amira Daman shine Wanda yayi silar kashe mahaifinsa"Mudan na kuka ya ce "Ban kashe Alhaji Sammani Dan komai ba sai Dan wata Rana muda abokan tsafinmu munje want kauye muka sato wata yarinya a take muka kwankwale Mata Ido mun dauki wani bangarruka na jikinta da muke bukata juyawar da zamuyi muka hangoshi tsaye ya fito daga mota Yana kallonmu Sosai hankalinmu ya tashi ganin shine saboda ya sanmu muma Kuma mun Sansa a harkar wani kasuwanci muka taba haduwa mun d'auko bindiga muna Shirin harbarsa ya maza ya koma mota tare da janta a guje hakan yasa muka Mara Masa baya har muka shigo garin kaduna Muna binsa Wanda a dabara muka dinga binsa Shi a daukarshi ya bace Mana baisan munaankare dashi ba Saida mukaje har kofar Gidansa ya fito Zai bude get muka harbesa a saitin zuciya kafinma ayi wata_wata mungudu Shi Kuma Alh Sammani aminin mahaifinka ne na kashesane saboda munyi sa'insa dashi akan wani Gidan gonarsa da nake son ya sayarmu ya kiya Wanda har nayi b'arin Baki na ce "sainayi ajalinsa Kamar yanda nayi ajalin abokina Alh dikko"Sosai hankalinshi ya tashi har Yana ikirarin saiya mikani ga hukuma lokacin Dana tuno baran baramar da nayi ya Sanya hankalinta tashi gashi cikin gari muke Indai nayi harbi kamani za ayi saboda duk inda nake Daman da bindiga ka nake yawo hakan yasa bankashesa a Nan ba har Saida ya juya zuwa Komawar Gidansa Wanda Shima irin kisan amininsa nayi masa saidai Shi bani da hannuna na kashesa ba sanyawa nayi aka kashemunshi'"ya karasa fada Yana wani irin kukan nadama"Tashin Hankali ba a gwada maka Rana tashin hankalinta da kowa Dake wajen ya shiga ya baci amira ko zuciyarta kasa daukar tension dinnan tayi ba Wanda ya Lura Da Ta sume ma Saida mudan ya gama tonon asirin kansa Yana kuka Yana yayi nadama Yana Durkusawa akan Kakan Zahra ya yafe Masa kasan Dan uwa da d"an uwa sai Allah Sosai tausayin Mudan ya tsargu a zuciyar baba har za a fita dashi Baba ya juya ya ce "Na yafe maka mudan hakkin kasheni din da kasoyi da hakkin kwantar Dani ko yanzu ka mutu kar a tambayeka hakkin Nan na yafe maka"cikin kuka mudan ya ce "Nagode Yaya Saiwataran sai mun hadu a darussalam Kai baka mutu ba Ashe Ni Zan rigaka mutuwa Yaya nayi tsantsar nadama"Daya Daga cikin sojojin da suka zo kamasa suka Tisa keyarsa akayi waje dashi MD ma ransa a matukar bace Yaja hannun matarsa sukayi waje baima waiwayi Amera da take a sume ba Ammy ma da su baba waje sukayi gabaki daya mD da ammy Jin mutuwar Suke ta dawo musu sabuwa har suka Isa gida ammy na tsine mass Tana ja Masa alkaba'i Zahra ko dukta firgice ga Bata Manta ba Jin MD da aka Kira mijinta dashi sunan da bazata Manta Dashi ba Gidan ammy suka sauka Koda chuchu taji labarin Nan itama Nan tashiga tsinenewa Baban Amira har amirar take hadawa Zahra dai batacewa komai hankalinta duk Yana kan mijinta da taga ya firgice fuskarsa ba fara'a ko Zama baiyi ba ya juya ya koma police station Dan hankalinshi bazai kwanta ba har saiya tsaye an yankewa mudan hukuncin kisa Kamar yanda ya kashe Masa mahaifi ranar da dare Zahra tayi Tagumi Akan bed kallon chuchu Dake waya tayi Ganin yanda take wayar ya tabbatar Mata da Adil ne saurayinta Kuma cousine dinta Saida chuchu ta Gama wayarta kafin Zahra ta kalleta ta ce "Dan Allah chuchu na tambayeki waye MD please",Tirkashi chuchu ta fada kafin ta gyara Zama ta ce "Mijinki shine MD momcy Yaya ne MD din ai"Fuskarsa Zahra dauke da mamaki ta ce "Wai kina nufin shine MD dinnan da yayi harbi a gabanmu Wanda na tsana"Kama hannunta chuchu tayi ta ce "Tun lokacin a school naso maki bayani kikak'i fahimta momcy wanna mutanen da kikaga Yaya ya harba Sune wadanda sukayi kisan abokin mahaifinmu da kikejin labari yanzu ranar sun dawo Daga kisan sun kubucewa Yan sanda yayana yakai wajen Wanda dpo ya kirasa ya fada Masa akan ya harbe su Dan Karsu gudu tofa kinji dalilin daya Sanya har Yaya yayi Harbin Nan Amma ba halin sa bane bai taba harbi ba "Allahsrk shiyasa ba ason saurin yanke hukunci akan abunda baka da masaniya Ashe ma Shi taimakone yayi harna rike hakan a Raina nake Masa mummunan zato ke Kuma kinaji Ina zagin yayanki kikayi shiru kikaki fadamun yayankine"Zahra ta fada Tana sauya fuska"Dan murmushi chuchu tayi ta ce "To Taya zance Ni kanwarsa ce a lokacin tsanar da akayi Masa ta shafeni kintuna momcy yanda muke drama Dake a school Akan ki auri yayana Ashe dai tuni ma Yayan yayi wuf Dake nice bansaniba idan natuna abunnan al'ajabi nakeji"Dan murmushi Zahra tayi ce "Ni kaina wani gamin ina jinjina Abun"Ikon Allah ne kawai momcy wlh al'amarin Nan yakara wa'azantar Dani duk abunda yake rabonka ne Kota wace hanya sai Allah ya kawo dalilin samunsa sannan matar mutum kabarinsa Hafiz mutumin nawa ko ana Ina har yanzu mamaki nake fa dalilin da yasa yace yafasa Auren duk irin son Da ya nuna Yana maki"Sai lokacin Zahra ta tuno Hafiz kwantawa tayi tare da lumshe Ido a ranta ta na tunawa da ai Indai hakane soyayya to ba so takeyiwa Hafiz ba kawai dai zata auresa ne a saboda Halaccin da yayi Mata Amma so na so to MD takeyiwashi akanshi tasan meye so,a kanshi tasan zafi da radad'in so,a sanshiba tasan menene kishi ,taba ta din da chuchu tayi ne ya sanyyata bude Ido ta kalleta chuchu ce ta ce "muna Hira Kuma zakiyi bacci"Ba bacci nake ba fa ai nazata waya zakiyi da Habibyn naki"Murmushi chuchu tayi ta ce "Ai mungama na Manta ban fada maki ba kiyi Mana murna an maido Yaya Adil aiki Abuja kinji murnar da nakeji Dan banason Nesa daku wlh dafa ba ayi Masa transfer ba saidai a kaini maidurin Nan da ko da ziyara banason zuwanta wlh zafi da ranar garin tayi yawa ga Hajiya ta addabeka Amma yanzu Kinga gani gaku ga ammy musamman ma ke da Rabin rayuwar Yaya a Abuja yakeyinta Kinga naji dad'ina "Dariya Zahra tayi ta ce "gaskiya nayi murna wlh Nima da kikacemun an Fara maganar tsaida ranarku da naji maiduguri ce saida hankakina ya tashi Amma yanzu alhmdllh Tunda dai muna tare"Wlhko najima Ammy Tana maganar kafin wanna Case din ya bullo wait zamuje maiduguri Dake y'an uwan abbanmu su ganki Wanda Basu ganki ba sannan tace idan zata India Ganin gida ma tare zaku tafi itama Yan uwanta su ganki "wai kina nufin Ammy y'ar India ce kenan shiyasa Naga ita da abban su Zahra Basu Kama da hausawa najima Ina wannan tunanin Ina musu kallon Indiawa Ashe dai da gaske ne kune bakuyo Kama da y'an chan ba keda Aunty zey"Zahra ta fada "Gyada Mata Kai chuchu tayi ta ce "Eh Mu munyi Kamar Abba ne shiyasa"Allasarki "Bari na Miki wata gulma kinsan Yaya Jabir da Asmy sunjone soyayya suke kuwa to ko rannan da kikaga tazo Shi ya kawota ya maida ita Kinga yanda yake tarairaiyarta saboda dakyal ya samu ya shawo kan y'ar rigimar tasa Suna chan Suna zuba love yanzu Haka da Zaki Kira wayarta waya zakiji tanayi"Chuchu ta fada Tana Dariyar shakiyanci "wow Da gaske kike wai "Zahra ta fada "Wlh da gaske Baku zauna kunyi doguwar hira bane shiyasa Bata fada maki ba "Cike da farinciki Zahra ta ce "Alhmdllh Kai Allah na gode maka wlh karkiji irin dadin da naji Kinga Shikenan dukanmu mu ukkun bamuyi nesa da juna ba"Wlhko Nima karkiji yanda nakeji"a wayar chuchu suka Kira Haka ko akayi suka samu Tana ways Saida ta gama takira Sosai Zahra tayi Mata tsiya ta Rama irin yanda ita take Mata sunjima suna hira cike da kewar juna "Asmy ce to ce"Wai kinsan rad'e_Rad"in da nakeji a gari Wai Su Habiba da Salamatu sunyi cikin shege anje a fidda Abun yaki fita karkiga yanda mama rabi ta rame ta jeme Niko nace Allah ya Kara aniyarta ce ta kome Mata abunda taso ya faru Dake ne ya Kare a kan y'ay'anta har Biyun baba ma ya dawo shekaranjiya "dukda musgunawar da mama rabi tayi Mata Amma Zahra sai bataji dadin abunda ya faru ba kasa kasa ta Ce "Allah ya kyauta to ya kiyaye Dan Allah Asmy gobe kije ki amsomun number baba kituroman ta sabon layina da na kiraki ashi last week"Okay Insha Allah gobe na turo maki"Bayani sunyi bankwana sai sannan Zahra ta Ciro wayarta da ta mutu ta jona chaji gado tazo Harta kwanta saikuma ta kalli chuchu Dake chart ta Ce "Su Akhbar suna wajen ammy fa har 11 yanzu karsu hanata bacci"Naje daukarsu dazu ta Ce Wajenta zasu kwana akwai madararsu da abincinsu wajenta"Ajiyar zuciya Zahra ta sauke ta ce "Kice yau na kwanta sai safe"Gaskiyar Kam Ammy ta fansheki"Zahra Harta kwanta chuchu ta daddabata ta Ce "Momcy na Manta wlh gulmar Nan tun dazu take cina Wai da kukaje ana fadin abun Nan ya Amera tayi shegiyar Ashe duk Takama da gadara da take Akan kudi da duniya ita ta tashi cikin arziki kaza_kaza Ashe ma kudin dukiyar Kakanki ce kai gaskiya dai Baban amirar Nan yaji kunya wlh "Girgiza Kai kawai Zahra tayi ta Ce"Allah shiryeki chuchu Daman akan wannan ne har Kika tasheni bacci yaudai naji gulma kikeji nikuma bacci nakeji wlh"Dariya chuchu tayi ta Ce "Kamarko kin sani Allah yau y'an gulmar ne a Kai"washegari Zahra ta Kira baba a layinta bayan Asmy taturo Mata number Sosai suka Sha waya da mahaifin Nata sai Dadi takeji sunjima suna waya kafin suyi bankwana cike da kewar juna a cikin satin Nan aka yankewa Abban Amera hukuncin kiss ta hanyar rataya bisa ga rashin gardama da baiyi a Court ba yasanya shari'ar tasu tayi sauki Sai sannan hankalinta MD ya Fara dawowa jikinshi Koda yaje ya labartawa ammy Sosai taji Dadi Kuma tayi hamdala koba komai Shima zaije ya girbi abunda ya shuka a ranar suka koma gidansu shida Zahra tare da yaransa ranar dai Zahra taga yadan warware Wanda da taimakonta hakan ya faru da girki ta shimfida Masa Mai dadin gaske bayan ta dau gayu Kuma ta faranta Masa a shimfida washegari Zahra na kwance jikin MD kan kujera Tana zuba Masa shagwaba Yana biyeta Yaran ko suna tsakar polourn suna wasa da wutsil wutsiltu wayar MD tayi ringing yayi mamaki Ganin bakuwar number ta kirasa da special numbersa da makusantata ne kadai ke kiransa da ita kin dauka yayi Saida aka sake Kira Zahra ce ta Ce "Ka Dauka Mana Hubby ana kiranka fa"Dan kar Zahra ta zargi wani Abu ya sanyashi dagawa daga Bangaren Maman Amera ta na kuka ta Ce 'Ga Amira Nan mustapha zata mutu ba sunan da take ambata idan ba naka ba ka daure kazo ko bankwanar karshe ce kuyi Dan Allah"a zabure MD ya Mike ya ce "Subhanallah mama Kuna wani asibitin "BIBA HOSPITAL"ta fada Masa "Cikin sauri ya katse wayar ya ce "gani Nan"Mikewa yayi hankalinta tashe binshi Zahra tayi ta ce"Lafiya dai?Da sauki Amira ce ba lfy ki koma zanje na gano"ya fada Yana fita waje ba shiri komawa Zahra tayi ta zauna Tana tagumin kome ya samun amirar saikuma ta Tabe Baki ta koma wajen yaranta ta dinga yi musu wasa kafin ta Kara kimtsa Gidan da turarruka kamshi saikuma ta shiga kitchen Dan Dora sabon girki"Soaai MD hankalinshi ya tashi ganin halin da Amira ke ciki numfashima dakyal takeyi "hankalinsa tashe ya kalli Mamanta ya ce "mama tun yaushe ta Fara ciwon"Tun ranar da tashin hankalin Nan ya faru take kwance Daman dai duk zaman da tayi gida ba lafiya ta fiya ba yanzu dai yau batama gane wadanda ke zuwa da dawowa sunanka kawai take iya fada kafin Dr yayi Mata allurar bacci"innalillahi wa inna ilaihiraji'un"MD ya dinga maimaitawa kafin ya rike hannun Amira Yana kallonta yanda numdashinta ke fits dakyal Sosai yaji tausayinta Ganin irin ramar da tayi Yana rike da hannunta Yana ta kallonta Yanajin rashin kyautawarshi na kin. Waiwayarta Wanda a nashi salon Dan ya hora ta ne su zauna lafiya Shi yasan idan yace baya kaunar amera yayi karya kodan sabon zaman shekara goma ai ba wasa ba saidai kawai yaji a ranshi yafison Zahra fiye da soyayyar da yakeyi Mata a Cikin ranshi duk abunda mahaifinta yayi baijin Zai rabu da ita saboda Laifin mahaifinta daban ko a lahira Nata daban Laifin wani baya shafar wani ita kanta Mamanta tayi mamakin yanda MD bai nuna komai ba duk wani abunda za a bukata Saida MD ya bada kudi koda amira ta farka da sunanshi a bakinta Yana kusa da ita ya ce"Bude idonki ki ganni honey nine mijinki a tare dake "A hankali amera take kallonsa kafin ta Fara hawaye ta garkame hannunsa ta Ce "Ka yafemun honey duk Laifin da nayi maka Dan Allah honey inajin a jikina mutuwa zanyi honey zuciyata ji nake kamar zata fashe ka yafemun Kace ammy da su Hajiya su yafemun da duk Wanda nayiwa laifi.."ta karasa fada Tana hawaye"Sosai hankalinmu MD ya tashi rukota yayi Sosai ya ce"Kidaina fadar irin maganar Nan My Merah bazaki mutu ba Zaki tashi mu cigaba da rayuwar mu muma zafin ciwo ne Dan Allah kidaina fadar Haka Kina tayar mun da hankalinna"Murmushi yake kawai Amera tayi "Mamanta ce ta karaso ta Ce "Ki daina fadar Haka Amira kinsan ke daya Kika ragemun a fadin duniyar Nan ke daya gareni ba uwa ba uba ba miji bazan rasaki ba amera zamu rayu"Hawaye kawai Amera take Tana kallon maman Tata ta Ce "ki yafemun Dan Allah mama"kuka Sosai Mamanta ta ke tace bakiyimun komai ba amera Baki da hakkina a tare Dake inma akwaishi na jima da yafe Miki banason kina kalama. Nan kina tayar mun da hankalin"MD ji yake kamar Shima yayi kukan mikewa yayi yaje wajen Dr din domin chuku_chukun a fidda ita waje cewa Dr yayi ba matsala sai a shirya fitar da ita din zuwa jibi "yinin ranar mD Shi yayi jinyar Amira Yana rungume da ita duk abunda take so Shi yake Bata Daren ranar shine baikoma gida ba Saida yaga ta samu bacci sai wajen karfe Sha biyu ya koma gida Koda yaje bai samu Zahra a parlour ba Yana shiga bedroom Amma ganta kwance ita da Yaran su duka suna bacci Banda ita daya same ta Tana kallon gefe Tana tunannika Wanda Saida yakira sunanta tukwana tasan da zuwanshi kallo daya tayi Masa da har bazata Masa magana ba saidai ta danne kishin da takeji Tunda yayi Daren Nan tasan Yana tare da matarsa ta Ce "Ya Mai jiki"Numfashi yaja kafin ya ce "Da sauki dai za ace Amma waje Zan fitar da ita gaskiya ban yarda da kwarewar asibitin ba Tana Shan jiki Sosai ciwon Nata ya dagamun hankalinta"ya fad'a fuska ba walwalar"Allah ya bada sauki"ta fada Tana juya baya tare da rumtse Ido tanajin kishin amera Sosai a ranta "Tana jinshi ya dauke Yaran ya mayar dasu gadonsu na iri Wanda ake turawa kowanne Mai net dinsu kafin ya kwanta ya janyota jikinsa Zahra Najin haka ta marairaice Cikin shagwaba ta Ce "nasan ka shawo gajiya kanason ka yi bacci please ka kwanta yanzu danka tashi da wuri Abbansu Amar"d'an murmushi MD yayi Yana jinjina hikima da wayewa irin ta Zahra Bata iya cemasa ita ta gajine bazata iya ba shiyasa ta sauya. Maganar cikin hikima baiyi Mata komai ba sai janyota jikinsa da ya karayi ya ce"Mu kwanta....washegari tun asuba MD ya wuce Asibitin ba yanda Zahra batayi dashi ba Akan Yama tsaya yayi breakfast Amma yakiya Bayan fitarsa Tagumi tayi tana Jin yanda zuciyarta ke nukurkusa akan kishi wata zuciyar tace Mata matarsa ce fa tun kafin ya sanki suke tare shekara goma Sha ,Bata da lafiya dole yayi fiye da Haka ma '"Saurin mikewa tayi ta Ce "Au'zubillah"Kafin ta cire duk wani kishi da tasa a ranta ta aje gefe saima.adduar samun lafiya da tayiwa Amira Bayan sun kimtsa Gidan tare da taimakon Yan aikinta Nanny din yaran Suma sun shiryasu kitchen ta shiga tayi girki Mai d'an yawa Bayan ta gama komai ta Sanya a warmers a lokacin 1:pm Cikin sauri tayi Wanka ta shirya Cikin kayanta masu kyau Bayan ta Sanya katuwar hijab dinta irin ta larabawan Nan har kasa wayarta ta dauka tare da Kiran number MD Bayan ya dauka ta Ce "ya sunan asibitin na shirya ne Ina son nazo na duba ta "Ki Dan jira minti biyar ga driver Nan zanturo ,zaizo ya kawoki Asibitin"ya fada a sanyaye"Okay"ba ayi 10 minute ba Saida driver yazo ya dauketa ita da yaranta sai nannynsu daya data rike Mata biyu koda suka isa har dakin da Amira take Sosai Zahra taji wata irin faduwar gaba Ganin yanda MD ya rungumo Amera jikinsa Yana bare Mata ayaba dakyal ta iya control din zuciyarta da take Jin kamar zata rabe gida biyu ta gaishe da maman Amera ta amsa Mata Cikin mutunci Dan ta gane ta tare da tambayar ya Yan Gidan ta ce "Alhmdllh"Dagowa MD yayi ya kalli Zahra dayaga ta Dan sauya zamewa yasoyi tun dazu Amma amera ta garkamesa Yana Jin nauyin mamantama Dake wajen Amma tun safe da yazo taki barinshi tashi a sanyaye Zahra ta kalli Amera Dake Numfashi dakyal ta ce "Ina yini ya jikin"Kallonta Amera take da idanunta da suka Fara sauyawa tsabar wahala ta gyada Mata Kai ta ce "Alhmdllh"Kallon MD amera tayi ta Ce"Ce ta mikomun yaran na gansu"Ta fada Tana hawaye kallon Zahra MD yayi ya ce "Mamy d'an Miko Mata su "Zahra ji tayi kamar ta ce "a a a Dan Bata mance lokacin da Amira taso halaka yaran ba dakyal tayi shahada ta Mike da little Dake haannunta ta nufi gadon Mika hannunta Amira tayi tana daga kwancen ta amshe ta "Zaki iya daukarta kuwa"Kirkirarren murmushi Amira tayi ta ce"Eh Zan iya yau jikin yafi koyaushe mun sauki"Alhmdllh Daman haka nake sonji Insha Allahu Zaki warke gobe ne tafiyar da za ayi Dake Egypt"Girgiza Kai kawai Amira tayi Zahra ji tayi kamar zuciyarta ta fashe juyawa tayi zata koma amera ta ruko Hannunta juyawar da Zahra tayi sai gani tayi tana hawaye ta ce "Dan Allah y'ar uwata ki yafemun duk rin abunda nayi maki ki yafemun banason na tafi da hakkin kowa ina Neman yafiya a gareki Dan girman Allah"zuciyar Zahra Sosai ta karye batasan lokacin data Fara hawaye ba. Ta ce "Ba abunda kikayimun Aunty Amira idanma kinyimun na yafe Miki Nima kiyafemun insha Zaki warke ki tashi kamar kowa"Suna Jin Amira ta sauke ajiyar zuciya har lokacin Bata saki hannun Zahra ba saikuma ta hada Dana MD ta ce "Honey ga Amanarta Yar uwata Nan ka riketa da Amana kamar yanda ka rikeni Amana nasan kaid'in Adalin mutum ne Kayimun halaccin da ba Wanda yayimun a rayuwa MD ka zauna Dani tsakani da Allah ka kyautatamun dukda irin rashin kyautawar da na dinga maka ka kula Dani ka Soni a lokacin da idan wanine xai gujeni Babu abunda zance a zama na dakai saidai godiya Allah ya hada fuskokinmu a aljanna fiddausi Kema Zahra ki rikesa da Amana Karki Bari MD ya kubuce maki samun irinsa a Cikin maza Abu ne Mai wahala Ina tayaki murnar samun miji na kwarai na gari nagartaccen sannan inayi muku murnar samun zuri'ar da kukayi Allah ya Raya su naso Ganin jini na a duniyar nan Ashe banida rabon Zan gani ,Dan Allah Ina Neman alfarmar da idan Kun haifi wata y'ar ku Sanya Mata suna na MD karka Manta Dani ko bayan Raina ka sani Ni amera na mutu ne da soyayyarka a Raina Kuma da ita zantashi Koda ranar gobe kiyayya Ina sonka mijina ina tsananin kaunarka Kuma Ina alfahari dakai Allah ya hadamu a darussalam"Kuka ne yaci karfinta Sosai Itama Zahra kuka take Sosai taji wani irin tausayin Amera Ganin irin yanda numfashinta ya sauya da tarin da take ya sanya Zahra dauke little Dake kanta MD ko a matukar rude ya Fara girgizata Yana Amira Amira Mamanta ko wani irin kuka ne Mai karaji ta fashe dashi gaba daya hankalinsu ya tashi ganin irin yanda numfashinta ke Neman daukewa suna Ganin yanda bakinta yake motsi Amma Basu San me take cewaba a matukar rude hankalinta tashe MD ya fita ya Kira doctors likita hudu suka shigo bayan sun bada umarnin kowa ya fita MD kin fita yayi Zahra ko wake sukayi suna kuka Duk iya yanda likitoci suka so ceto rayuwar Amera abun ya gagara ba ayi 20 minutes ba komai na jikinta ya daina aiki Ganin likitocin na cire oxygen din da suka da Mata da kayan aikinsu ya sanya MD rikicewa a matukar tashin hankalin ya ce "Me kuke nufi Dr kardai kucemun ta mutu"Daya daga Cikin Dr din ya dafasa ya ce "Am so sorry Allah yayi Mata cikawa dukkan Mai Rai mamaci ne kowa jiran tashi ranar yake ta rigamu Gidan gaskiya saidai muyi addu'ar Allah ya jikanta ya rahamce ta mu Kuma ya bamu guzirin taddasu"Innalillahi wa inna ilaihiraji'un MD ya fada kafin yaje ya rungumeta ya ce "Karkiyimun Haka amera me yasa Zaki tafi ki barni Amera kin mutu innalillahi wa Inna ilaihiraji'un yanzufa kike cewa jikin naki da sauki Dan Allah ki tashi saikuma ya fashe da kuka kamar mace Yana kan gawar Sosai likitocin suka tausaya Masa sunsan ba karamun shigarsa mutuwar tayiba maman Amira ko da aka fada Mata mutuwar Suma tayi Zahra ko Tasha kuka dakyal ta iya daukar waya ta sanar dasu ammy mutuwar Amera Sosai Suma hankalinsu yayi tsananin tashi MD ba karamun tashin hankalin ya shiga ba a mutuwar Amira yayi kukan da bai taba yin irinsa ba tunda yazo duniya A Haka dai aka Kai amera gidanta na aure Wanda Anan akayi Mata. Sutura Sosai wajen jana'izar Tata ta cika da mutane a makabartama MD Saida yasha kuka dashi aka sanyata ya jima Yana Mata addua da Neman Mata rahamar ubangiji Kira yake na yafe Miki Amira Baki mutu da hakkina ba komai kikamun a zamana Dake na yafe Miki Allah Miki rahama Allah yasa mutuwarki ta kasance hutu a gareki Allah yafe Miki mala'ikun rahama su amshi bakuncinki ya Allah Ka jikan Matata ka yafe Mata Sosai MD ya Sanya wasu daga Cikin Yan makabartama kuka kafin dakyal aka samu ya tashi dagakan kabarinta kafin kowa ya watse aka barta daga itasai halinta (😭😭Allahsarki Amera Allah jikanki) Koda Suka koma gida aka Fara zaman makoki MD baya iya cin komai kallo daya zakayi Masa kasan ba karamun shigarsa mutuwar tayi ba ko mahaifiyar Amira Bata Kai MD shiga wani hali ba Zahra ko itama Sosai ta damu idan Tana tuno da maganganun nasu da Amira na karshe dukda ba wani sabo sukayi da itaba Amma mutuwar ta shige ta Kuma ta karyar Mata da zuciya a Nan inda Amira ta yi rayuwar aurenta akayi zaman makoki su ammy da Yan uwa da kowa dasu Zahra da mahaifiyar Amira duk Nan suke kwana Yan uwan Zahra ma na wajen babanta sunzo motarsu guda sunyiwa MD gaisuwa sannan Bangaren Mamanta ma daga jigawa Suma da yawansu sunzo sunyi mashi gaisuwa Saida Akayi sati guda ana zaman makoki kafin ayi sadakar sati taro ya ragu ya rage Saina gida mahaifiyartama ta hakura tayi tawakkali MD ne dai abincima saidai idan ammy ta kirasa Tana Masa wa azi da nasiha Harta samu ya danci Kowa yazo sai yayi Masa nasiha Akan yayi hakuri ya bita da addua Wanda ya tafi baya dawowa a sati na biyu suka koma gidansu saboda Yan gaisuwa yanzu sai daidai tunda suka koma Zahra Bata gane kan MD hira ma basa zaunawa suyi kullum Saidai yayi shiru Yana tunani hirarta dashi saidai ta gaishesa ya amsa ko yanason wani abun tayi Masa yaransama idan ya daukesu baya musu wasa kamar da Sosai Zahra ta shiga damuwar da wannan halin da MD ke nuna Mata hankalinta duk ya tashi yau sati biyu kenan da dawowarsu gida Amma basa Zama suyi wata hira Kullum Cikin tunani yake ga abinci ma idan ta girka ba Ci yake Sosai ba baifi yayi spoon ukku ba ya tashi wani Karin ma bayaci "Zahra saidai taje daki Tasha kukanta Yauma ta na Cikin Shan kukanta taji wayarta tayi ringing Tana Ganin chuchu ce ta Dauka yanda ta amsa Mata sallamar ne ya Sanya chuchu ta gane akwai matsala cewa tayi "Lafiya Momcy naji kamar muryarki kinsha kuka"Kukan da take boyewa ne Zahra ya kubce Mata ta fashe dashi Saida ta tsagaita kukan kafin chuchu Cikin damuwa ta ce "Subhanallah Aunty me yake faruwa ne Wai"Cikin kuka ,Zahra ta Ce "Chuchu bansan me nayi Masa ba tunda akayi mutuwar Nan bayamun magana bayacin abincina Sosai gaba daya na rasa abuna ke mun Dadi zaman Gidan duk ya isheni kwata_kwata bani da walwala bansan me nayi Masa ba"Ta karasa fada Cikin kuka "Ammy Dake Jin Abunda Zahra ta fada kasancewar handsfree aka Sanya wayar Kuma suna kusa da juna amsar wayar tayi a hannun chuchu ta Kara a kunnanta ta ce Hello Zahra"Zahra Najin muryar Ammy gabanta ya fadi Allah yasa bataji ba saboda kartayi tunanin ko kararsa ne takawo saurin katse wayar tayi tare da yin Tagumi ta fashe da sabon kuka MD daga kofa zaishigo dakin yaji komai da irin yanda take kukan take fadawa chuchu batasan me tayi Masa ba Sosai yaji tausayinta ya kamasa Shi kanshi bayama sanin yamata Haka saboda kwata_kwata tunaninshi baya jikinshi Babban tashin hankalinshi da mutuwar Nan irin yanda ya banzatar da ita wata ukku bai taka inda take ba kota kirasa baya Dauka Shi yafi komai tsaye Masa arai na Ganin rashin kyautawar da yayi Mata karasowa dakin yayi tare Kama hannun Zahra ya tallabo fuskarta Dake kuka ya Ce "Kiyi hakuri Mamy bakiyimun komai ba Baki taba yimun laifi ba Dan Allah dalilin mutuwar Nan ne da Bata sakeni ba ya Sanya banason yin magana ko cin abinci Amma ba Wai Dan na musguna Miki ba Dan Allah kiyi hakuri ki yafemun"Lokacin guda Zahra ta dago saikuma ta sadda kanta kasa Tana hawaye rungumota yayi jikinsa ya ce "Baki hakura ba kenan"Girgiza Masa Kai tayi tana goge hawayenta ta ce "Dan Allah kayi hakuri Ka rage damuwar Nan a ranka Tana sakani Cikin wani Hali sainaga kamar ni nayi maka wani Laifin ne ita Kuma Aunty amera addu'ar ka take bukata a halin yanzu fiye da komai Allah ya jikanta"Yana goge Mata hawaye ya ce "Ameen my Mamy Insha Allahu Zan rage daga yau"wayarsa ce tayi ringing Yana Dauka daga Bangaren ammy ta ce "Babana lafiya meya hadaka da Zahra kake Mata gaba"Sorry ammy wlh ba abunda ya hadamu kawai fahimtata ce batayi ba har yanzu Mutuwar Amira ce ke tayarmun da hankali ammy musamman idan na tuna kyaketa din da nayi tsawon watanni fin ukku Ammy abun Nan Shi yafi damuna da tsayemun a Rai"Daga Bangaren ammy ta Ce "Ka daina damuwa da wannan Babana kayiwa Amira gatan da babu namijin da zaiyiwa matarsa Haka sannan ka godewa Allah da saida kayi jinyarta kukayi bankwana kuka yafi juna kafin Allah yayi Mata cikawa inason ka cire damuwar mutuwa a ranka ka dinga binta da addua muma muna Mata Allah yayi Mata rahama nasan kana da ilimi Kuma kasan dukkan Mai Rai mamaci ne kowa jiran nasa lokacin yake"Nasiha Sosai ammy tayi Masa kafin tace ya bawa Zahra wayar itama nasihar tayi Mata ta ce "aikinkine Zahra ke Zaki kula da mijinki har ki mantar dashi wata damuwa ke matarsa ce ke kikasan duk wata hanyar da zakibi wajen basa farinciki Kiyi iya kokarinki nasan Kuma kinayi Allah yayi Miki albarka ga driver Nan zanturo ya kawo mun yaran suyini"To Ammy nagode Insha Allah Zahra ta fada..tun daga ranar Zahra tafara bakin kokarinta wajen Ganin ta dawo da farinciki rayuwar mijin Nata duk wani da hirarraki masu dadi Shi take Masa a hankali a hankali ya dinga sabawa da rashin Amira harya dawo normanl saidai addua da yake Mata da sadakoki har masallaci ya Sanya a Gina Mata kamar yanda ya ginawa mahaifinsa da Kuma mahaifiyartama Zahra Wanda ko ita Zahra Bata sani ba Akan Allah yakai musu ladar rayuwarsu taci gaba da wakana Cikin farinciki da kaunar juna MD ya dawo asalin MD Mai nuna kulawa da soyayyar ga matar tasa itama Zahra Tana Nata bakin kokarin wajen Ganin faranta Masa an Sanya ranar Auren chuchu da Adil Wanda aka had'e Dana Asmy da Jabir wata hudu masu zuwa Yau Zahra na kwance Baba ya kirata bayan sun gaisa yake cewa ta Mika Masa sakon godiya wajen MD Sosai tayi mamakin yanda baba yake kwaraawa me addua tare da gode Masa ita dai Zahra murmushi tayi Bata tambayi baba abunda yayi musu ba baba na katsewa maman Asmy ta kirata itama godiyarce take ta surfawa hada kukan farinciki ta ce 'Allah yayi Miki albarka Zahra sanadinki Zan take kasar da bantaba tunanin zuwa ba sanadinki Zan sauke farali Allah yayi Miki albarka Zahra Yasa a gama lafiya ya Raya muku zuriarku godiya Sosai mama ta dingayi sai sannan Zahra ta fahimta kenan aikin hajji MD ya biyawa su baba Sosai taji Dadi Kuma tayi farinciki Koda ya dawo Tana Fara Masa gdy ya Girgiza Mata Kai ta Ce "Sun chanchanci fiye da haka Mamy kome.nayi akanki ban fad'i ba ke Kika Fara bani farincikin da bazan taba mantawa dashi ba a rayuwa kingako dole wani ma Wanda ya shafeki na basa farinciki kafin ya ce Abunda yasa Baza a tafi Dake ba saboda su Akhbar Dole.saidai next year sannan kin yayesu kin Kuma haifamun wasu triple din"murmushi Zahra tayi tare da rufe fuska "Bayan su baba sundawo daga aikin hajji Wanda hada maman Asmy da babanta da bappa aka biyawa Zahra ta shirya domin taje tayi musu sannu da zuwa Sosai tayi mamakin Ganin yanda aka gyara gidansu da na su Asmy dakyal ta iya gane gidansu Dan har bene aka Dora musu Koda ta shiga ciki ma Saida tayi mamakin irin kayana alatun da aka zuba Baba ko hada kukan farinciki yake Yana godewa Allah na mallaka Masa Zahra a matsayin y'a itadai Zahra saidai tayi murmushi inda yayi Mata addu'a ta amsa da amen MD ko yasha ruwan addua Bayan ta huta gidansu dukda tayi mamakin rashin Ganin mama rabi a Gidan ta wuce gidansu Asmy nanma Tasha godiya da sa albarka Kukan farinciki ko maman su Asmy ta Shashi Bayan sun gama gaisawa Zahra tayi musu sannu da zuwa sai sannan ta samu Daman tambayar maman su Asmy ta ce mama Wai Ina mama rabi tunda nazo banganta ba "Girgiza Kai Mamansu Asmy tayi ta Ce "Ina ko zakiga rabi Ai tuni Malam ya saketa yaran Nan biyun dukansu sukayi ciki lokacin Yana batsari baisan wainar da ake toyawa ba Saida ya dawo Shima saidaga baya Anje cirewa Salamatu Cikin Rai yayi halin sa to kinsan dai maganar garin Nan magana ba boyuwa take ba asirinta ya tonu Wanda Malam ya saketa yace bazai iya Zama da ita ba "Salati Zahra tayi ta Ce "Wayyo Allah Salamatu ta mutu kenan bantaba sani ba Allah ya jikanta to Ina habibar ita ta haihu ne"Eh ta haihu d'an Wai ya mutu waya sani ma ko kashe shege sukayi"Sosai Zahra taji wani iri a ranta ta Ce "yanzu mama Suna wani Gida"Wama ya sane Mata Kullum Tana zarya Tana kuka Tana rokon Malam akan ya yafemata tayi nadama ya mayar da ita ya kiya yo me zaiyi da rabi matar da ta wulakantaki taso taga kin tozarta sai gashi kaikayi ya koma kan mashekiya Abu ya koma kan y'ay'anta shiyasa ba ason bin mutum da mugun nufi Shi shairi kwikuiyo ne Mai Shi yake dawowa"Sosai Zahra tayi sanyi ta ce "Mama Dan Allah tunda tayi nadama kusa Baki baba ya maida ita Dan Allah tunda tayi nadama kodan saboda su khairat Dan Allah mama "wani banzan kallo mama tayi Mata ta Ce "Amma bantaba sanin Baki da hankali ba Zahra sai yau matar da ta wulakantaki itace kike maganar ta dawo taci arzikinki ke wata irin zuciya ce Dake maimaikon kiyi farinciki mahaifin ki ya rabu da muguwar Mata shine kike kokarin ki Kara lakaba Masa"Ba Haka bane mama saboda su khairat za a duba"Barmun maganar Nan Zahra a Kama wata"da dare Zahra tajewa baba da maganar Akan ya mayar da mama rabi furtumarta yayi ya dinga Mata fada Akan Bata da hankali Sosai Zahra ta kafe hada kukanta Tana bawa baba hakuri akan Dan Allah ya dubi su khairat ya maidota idan ta sake wani abun saiya saketa dakyal ta samu ta shawo kan baba ya yarda Zai maidota Amma da sharadin saidai habiba ta koma wajen dangin babanta dan bazata shafawa ya'ayanshi kashin kaji ba ajiyar zuciya Zahra ta sauke ta ce ta yarda Koda baba ya maido mama rabi Bayan yayi Mata kashe sannan ya Dora da cewa arzikin Zahra ne taci harya maidota mama rabi kukan nadama hada durkusawa kamar zatayiwa Zahra sujjada Tana Mata godiya ta ce 'Har kunyar had'a Ido nake Dake Zahra ki yafemun irin zalincin da nadinga maki Shiyasa akace duk yanda ya rike Allah shiya rike Babban bango na tsaneki na tsangwameki naso ki wulakanta ki kaskanta saigashi Allah ya d'aukakaki d'aukakawar da bakowa Zai samu irinta ba Zahra a yanzu kina daya Daga Cikin macen da za ayi alfahari da ita a duniya ki yafemun Zahra nayi nadama har kunyar had'a Ido nake Dake gashinan muna Cikin cin arzikinki Shiyasa akace kaji tsoron mutumin daka wulakanta"Murmushi kawai Zahra tayi ta Ce "Allah yafe Mana tare mama"Kwana biyu Zahra tayi Wanda Cikin kwana Biyun mama rabi kamar ta goyata abinci ma saita tambayeta irin Wanda takeso Dan tunda mama rabi tasan cewar Zahra MD take aure ta sadakas tasan Zahra tayi daukakar da babu mahalukin da ya Isa yayi kasa da ita gwarama tayi hakuri ta dangwali arziki Rayuwar su Zahra na tafiya yanda ya kamata a Haka har lokacin bikinsu Chuchu ya gabato anfara shiryen shirye ta ko Ina Bangaren Zahra da MD ma Sosai suke Shirin bikinnan a Haka har lokacin bikinsu yayi Zahra hankalinta duk ya kasu biyu ga Gidan ammy Bangaren chuchu ga chan funtua Bangaren Asmy tunda aka Fara bikin take Shan gayu da wankan gwala_gwalai Sosai suke Shan masifar kyau ita da yaranta da suka Fara tafiya gwanin sha'awa duk inda suka gitta sai anyi sha'awarsu ana gobe daurin aure ta samu damar zuwa funtuaa Wanda motoci takwas sukayi Mata rakiya tare da security yanda kasan matar shugaban kasa ita kanta Zahra ta kalli wanna daukakar da Allah yayi Mata har hawayen farinciki take Wai itace Zahra da da ba abakin komai take ba yanzu ta daukaku har Haka Koda ta Isa Unguwarsu duk manyan motocin sun cika wajen kowa sai daukin su gaisa da ita ake Saida ta gaishe da tsaffin layinsu Bayan tayi musu alkhairi kafin ta shiga gidansu Asmy dakyal ta samu ta shawo kan mutuniyar Tata Akan tayi fushi sai yanzu take zuwa dakyal ta fahimta bayaninta na cewar hidimar gidansu mijintace ta hanata sakat Yauma dakyal suka barta ta taho Nan aka cigaba da shagali da Zahra da dare gidansu taje Dan ta kwana zo kuga murna wajen mama rabi Kira ta ce "lale marhaban ga y'ar arzikin tazo Yar albarka sannu da zuwa jikokina sannunku ta fada Tana yin sama da little itadai Zahra murmushi kawai take Bayan ta Gaisheta Nan khairat ta ruga da gudu Tana murnar Ganin Yar uwartata Haka safiya da yanzu itama ta Zama budurwa Mama rabi kusan raba dare tayi tana goye da little dakyal Zahra ta samu ta saukota Tana mama zata gajiyar Dake Kira take ba komai Yar Nan barni in Goya abuna washegari aka daura Auren *Jabir & Asmy* tare da *Chuchu & Adil* na Asmy a funtua aka daura na chuchu Kuma a kd kasancewar an hade dinner ya Sanya aka Kai amarya da wuri Gidan ammy aka sauketa karfe goma na dare aka Tafi dinner Wanda Zahra da MD su suka shirya dinner Sosai wajen yayi masifar kyau da tsaruwa amarenma sunyi anko suma angwayen sunsha kyau iyayen gayya kuwa MD da Zahra ba a magana sunyi masifar kyau duk inda suke suna like da juna Excord dinsu na take musu baya tare da yaransu Dake tsalle tsallensu gwanin ban burgewa Sosai cemarori ke yawo Akan Zahra da MD yanda kasan sune amaren Zahra ko an kame girma ana zaune ita ta bada tarihin amaren MD Kuma ya nada na angwayen taro ya tashi Lafiya washegari aka wuce da kowacce gidanta chuchu Abuja Asmy Kuma Nan kd grab Dan gida daya ne tsakanin gidanta da Zahra.. *After 3 years* Fitowarsu kenan daga tafkeken shopping mall din MD Dake Abuja waiwaye ta dingayi inda zataga Akhbar Dan tunda suka fito Bata ganshi ba Sosai Naga ta Kara kyau da wayewa Tana sanye da bak'ar doguwar riga Abaya Mai shegen tsada tayi roalling gyalen Sosai tayi masifar kyau ga fuskarnan Tata kallo daya zakayi Mata kasan Tana samun hutu da Jin Dadi juyawa tayi Tana kallon MD dake rike da karamar y'arsu Wadda taci sunan Amira halimatus sadiya ana kiranta da amera itama watanta biyar da haihuwa kamarta daya da Zahra Rai da Rai ta ce "Sweetheart Wai Ina Akhbar tunfa da muka fito bangansa ba "Cike da damuwa MD ya ce "to ko yayi wani wajen Nan "Kafin ya kalli Amar dake wasa da katuwar bindigar wasa ya ce My boy Ina Dan uwanka ya shiga ba tare kuke ba "Dad Nima bangansa ba "Innalillahi MD ya fada ya ce ki duba sa farfajiyar Nan Ni Kuma Bari nayi maza na duba sa ciki ya fad'a Yana komawa hankali tashe Zahra ta rike Amar ta dinga dubawa duk yaron data gani saita dubasa gaba daya hankalinta duk ya tashi chan ta hangoshi gaban wasu Cikin sauri ta nufi wajen Tana zuwa ta Kama hannunsa ta Ce "Ina kaje Akhbar tundazu muke nemanka ka bamu wahala so kake ka b'ace a wajen Nan"Akhbar na hawaye Cikin shagwaba ya ce "Mom wadannan ne sunki bani babynsu "ya fada Yana nuna Mata wadanda ke tsaye dagowar da Zahra zatayi idonta ya sauka akan Hafiz Dake rike da karamar yarinya da bazata wuce sa'ar amera ba sai karamun yaro da bai wuce shekara biyu da rabi ba waro idanu sukayi a tare Zahra ta Ce "Hafiz"Shima Cikin muryar mamaki ya ce "Zahra Daman Rai kanga Rai"Mamaki dauke da fuskar Zahra ta Ce "wlhko ya Hafiz kwana da yawa"a sanyaye ya ce"Kinyi wuyar gani Zahra saidai muji labarinki"Murmushi kawai Zahra tayi Tana kallon matarsa ta Ce "Ko matarka ce"Eh Matata ce sunanta Aisha wadannan din Kuma Yara na ne Babban sunansa haidar wannan Kuma takwarar Kice Na Sanya Mata "Kai Masha Allah Ubangiji ya Raya Mana su Gsky Ina gdy da takwara Ta fada Tana Mika hannunshi ta amshi y'ar Akhbar na Ganin Haka yayiwa hafiz gwalo ya ce "Yeyeye ka gani mom Dina ta amso Mana babyn Kuma da ita zamu tafi gidanmu tunda Ni ka hanani"Dariya Hafiz yayi ya ce "Ohh itace mom din take kenan "Eh saura dad Dina Shima Yanzu zaizo mu tafi da babyn "Hafiz najin kishi a ransa da yanzu wadannan yaran duka nasa ne in Banda kaddara ta rabasu ya kalli Zahra ya ce "Akhbar yaronki ne kenan "Eh Ya akai kuka hadu"Murmushi hafiz yayi ya ce "Tun dazu yake binmu Wai saimun basa Zahra Yaatafi da ita gidansu Karkiga har kuka ya dinga Mana Allah sarki Ashe rabon mu hadu ne"Yar dariya Zahra tayi ta ce "Alhbar kenan ko har yayi kamu To ai shikenanma tunda ta dawo gurin Mamanta kaga gaka ga babynka ko"ta fada Tana kallonshi tsallen murna yayi ya ce "Yesssss mom "kallon matarsa Hafiz yayi ya ce "Wannan ita ce zahrar da nake ta Baki labarin"Aisha da fara'a a fuskarta ta ce "Allahsarki itace kenan Ina yini"ta fada Tana kallon Zahra "Lafiya qalau momyn takwara ygd "Saida suka Dan gaggaisa da Zahra Hafiz jikinshi gaba daya yayi sanyi yasan duk duniya Babu macen da yaso kamar Zahra Amma yanzu tayi Masa Nisan da har abada shida ita saidai kallo a sanyaye ya ce "Zahra Ina son Daman haduwa Dake domin Baki hakurin abunda ya faru wlh kaddara ce ta raba mu lokaci guda kawai naji an chusa mun tsanarki a Raina Wanda Saida na dawo hayyacina na shiga tashin hankalin da bantaba shiga ba Jin cewar Kinyi aure harkin haihu Wanda har Saida na kwanta ciwo kafin na warke har na auri Matata Aisha cousine sister Dita ce yaranmu biyu da ita Wanda itama Ina yawan Bata labarinki tun Tana kishi har tazo ta daina dalilin kaunar da nake maki ya Sanya har nayi Miki takwara "Sosai jikin Zahra yayi sanyi Bata iya cewa komai ba sai Murmushi da tayi ta ce "yanzu kana wani gari"Ina Nan garin Anan na samu Aiki"Masha Allah Ubangiji ya taimaka "Zahra ta fada daidai isowar MD wajen Zahra na ganinshi taga yanda ya sauya fuska Saida taso tayi dariya tasan ba komai bane sai Ganin Hafiz da yayi Hafiz ko da kanshi yaje sukayi musabaha suka gaisa a wayance Zahra ta gwadawa MD takwarar da MD yayi Mata nannema ya saki fuska harya dauki babyn Wanda Hafiz ya dauki amera Musayar number sukayi tsakanin Aisha da Zahra Akan zasuyi zumunci bandir din 1k MD yabawa takwarar. Matar tasa kuka Akhbar yasa musu da zasu Tafi Shi sai Antafi da babyn duk dariya sukayi Masa dakyal aka samu ya hakura Shima Dan anyi mashi wayau da cewar za'a kawo Masa ita Saida suka biya Gidan chuchu da itama Tana da yaronta guda Sadiq yanzu Kuma Tana da wani Cikin Asmy ko yarinyarta daya itama Zahra aka Sanya Mata gidansu Dake Nan Abuja suka wuce Koda dare yayi Ganin yanda MD ke Shan kamshi Zahra ta gane na ganinta dasu Hafiz ne da yayi Dan a zaman ta da mijin Nata tasan Yana da tsananin kishi Wanka taje tayi na birkitawa Bayan ta feshe jikinta da turrarruka ta baya taje ta rungomosa Cikin muryar shagwaba kamar zatayi kuka ta ce" waya tab'amun Kai Sweetheart yau zaman garin Nan ya gagaresa "Dariyar da bai shirya ba MD yayi tare da janyota jikinsa ya ya rungumeta tsam a jikinsa ya ce "Waya Isa ya tab'a d'an Zahra Mijin Zahra Baban Zahra ya Zahra ukku ya kwana lafiya"kafin ya hade bakinsu waje d'aya su Lula Duniyar ma'auratan......✍️ *TAMMAT BI HAMDULILLAH* Alhmdllh Alhmdllh Alhmdllh I am grateful to God for giving me the ability to finish this book a Nan ne Ni Hajara L Sadeq na kawo karshen wanna littafin Mai dogon zango Kura Kuran da nayi cikinsa Allah ya yafemun Allah ya bawa Al'umma damar fad'akuwa da sakon da nake son isarwa banida bakin magana wajen gode muku masoya bisa ga nunawa book dinnan tsantsar soyayyarku wajen sayansa da Kuma nuna kulawarku a gareshi Nagode ngd ngd bansan da wasu kalmomi zanyi amfani dasu wajen fad'a muku farincikin da kuka sanyani da dalilin book dinnan Kun nunamun tsantsar soyayyar da ba haufi a cikinta ku sani Ni hajara l sadeq taku ce ta har a bada masoyan Asali na gskiya da gaskiya Ina muku son fisabillah wolla inaji daku har Cikin kokon zuciyata zanyi missing dinku over Y'an amana Saimun hade a new book, *NA SADAUKAR GA LITTAFIN NAN GA DUKKAN MASOYANA NA DUNIYA ALKHAIRIN ALLAH YAJE MUKU HAR GADON BACCINKU INA MUKU SON DA BAYA FADUWA A BAKI SAIDAI A ZUCIYA* *ALHMDLLH LITTAFIN AUREN WATA TARA YA KAMMALU CIF INDA YA ZAMA COMPLETE DOCUMENT ZAKU SAMESA NE AKAN 500 KACHAL GA MASU BUKATAR SAYA SU TUNTUBENI AKAN NUMBER WAYATA KAMAR HAKA 07026166536 HAKA ZALIKA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DINA NA WHATS APP SUMA SU TUNTUBENI AKAN NUMBER WAYATA 07026166536* _MA ASSALAM_ _*Miss Hajo Ce*_🤙