Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen2⃣) ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘ TRUE LIFE STORY ABIN LURA Yana da kyau mu kula mu gane cewa munufar yin rubutu ko karatun kanshi ba wai don nishadi bane kawai ko rage lokaci, a'a, muna yine don fahimtarwa da wa'azantarwa ta hanyar nishadantawa don muyi gyara kan kurakiran da muke aikatawa. Misalin a lokutan da yawa mukan dauki aure wani abin da ake yin shine don a samu dadi a cikin shi, in dai ba kuskuren fahimta nayi ba wannan shine burin yawancin mata har ma da wasu mazan akan aurarrakinsu, har ma auren da yawa kan kasa kai kabari a dalilin an kasa samun abin da za'ayi zaton samu tun farko. Don haka naga bari mu tunatar da juna don mu kara fahimtar menene AURE? Farko dai dukanmu mun sani mu kuma yarda cewa, shi aure IBADA NE, haka nan mun yarda shi aure raya sunna ne na manzo rahma ( S.A.W.) daga yin shine kuma zamu mallaki rabin addininmu, ma'ana duk kokarinka akan aiyukan ibada matukar baka da aure, to ladanka rabin na mai aure ne. Ina gani daga wannan kawai ya'isa mu fahimci cewar, akwai wani babban al'amari mai wahala gaske a cikin shi. Kamar misali biyayya mai karfi da aka sanya tsakanin mu da mazajenmu, mafi yawancin mazajen namu bass mu'amala damu irin mu'amalar da za ta sanya muji saukin yi musu wannan biyayyar, domin basa bamu 'yancin da shari'a ta bamu, basa yi mana adalci da manzon rahma yayi musu wasiyya da suyi mana SBA tsabar son zuciya irin tasu da sonkai. Muna mata munada namu komisino din Allah ya ganar damu amin. JINJINA Ga dukkan wani wanda Allah ya jarabta ya kuma yi hakuri da jarabawar da Allah yayi masa, hakuri kyau. SADAUKARWA Sadaukarwa wannan littafi ta tabbata ga dukkan matan da suke aure suke kuma hakuri da abinda Allah ya kaddara musu a gidajen mazansu, Allah ya kara mana hakuri da kuma jin tsoronsa Amin. GAISUWA MAI TARIN YAWA GAREKI HJY ZABBA'U BUKUR PARCK JOS PLATAEA STATE Bazan mance dake ba uwar daki ta gari Allah ya kara girma da daukaka yaiwa dukiya albarka amin 0⃣1⃣ "Zauna take cikin dankararriyar parlour wanda yasha kayan alatu a jin dadin rayuwa' tasha kyau har tagaji cikin foguwar rigar shadda wanda yasha aikin sama mai ruwan kore. "Bini saeta kalli window dan ta kagu taga mijinta ya shigo' da taji shiru mikewa tai taje gidin window ta yaye labulaiyar da yake jikin bango ta tsaya shiru batafi mintuna da tsayuwa ba saega shigowar sa da sauri taje ta yanayin parking ta bude masa mirfin mota. "Yana fita da rungumesa hade da yi masa sannu da xuwa. "Murmushi yai hade da cewa yauwa Aisha ta'ya gida?". "Tace alhamdllh. "Suna tafe tana gaba yana biye da'ita suka shiga ciki kai tsaye dakinta suka shiga tana ije handbag dinsa ta shige toilet ta hada masa ruwan wanka snn tafito bedroom ta sameshi zaune a bakin gado. "Dukawa tai ta tana tayashi cire takalmin kafarsa shima hannu yasa yana cire botir din wiyar riganshi. "Mikewa tai ta dauko masa towel ta mike masa ya yana daurawa yashiga wanka kafin yafito taje kitchen ta kwanso abinci takai masa dinning ta jere masa. "Yana fitowa jallabiyarsa yasa yafito parlour gani bata gun dinning ya nufa kai tsaye daga ido da zatayi taga yana xuwa da sauri ta saki abinda takeyi taje ta gyara masa kujera ya zauna hade da cewa har ka fito. "Murmushi yai hade da cewa nafito Aisha ta sannu da aiki' kedae baki gajiya da yimin hidima. "Murmushi kawai tai masa plate ta dauko tafara xuba masa abinci' gani hannunta na rawa sbd nawin plate din da sauri ya tanlafo hade da yimata dariya yana fadin kinga abinda nake fadi ko? "Tace na mefa Yallabai?" Yace na rashin cikin abinci mana. "Murmushi Aisha tai hade da cewa to ai bacin abinci be kesa kiba ba' gaba daya hannayesa ya hada ya tablafo habansa dashi ya xuba mata ido ko kibtawa ba yayi yace to menene?". "Tace nifa haka Allah yayini... Da sauri ya tareta da cewa ai banace ba haka Allah yayi kiba nima kaina nafi sonki a haka kodan naji dadin sarrafaki yadda nakeso. "Da sauri tasa hannu ta rufe fuskanta sbd kunya. "Jawo plate din abinci yayi ya fara ci hade da cewa xubamin ruwa. "Daukar jug din ruwan tai ta xuba masa yanaci suna hira har yagama snn ya mike hade da cewa biyoni inada mgn dake. "To kawai tace tamike ta bishi tana gaba yana baya suka shige dakin ta. "Bakin gado ya zauna' gani ta tsaya a tsaye jingine da bango yasashi cewa ki zauna mana. "Snn ta samu gu ta zauna a kasa hade da nade kafa tana fuskantarsa saeda yasake kallonta snn yace Aisha. "Tace na'am. "Yace da farko dae nasan ke me hakuri ne kuma mai biyayya wanda bata bujirewa umarni maigidanta ko ba haka ne ba?". "Yana mgnr ne hade da dago fuskanta. "Murmushi kawai tai masa. "Snn yaci gaba da cewa shiyasa duk cikin matana nake alfahari dake' sbd kedin ta dabance. "Aisha dake zaune taji kanta yakara girma sbd yadda maigidanta yake yabonta. "Yaci daga da cewa Hauwa ce ta kirani tace tana hanya dawowa daga tafiya kuma kinga be kamata ta dawo bata sameni a gidan ta bako?". "Shiru Aisha tai bata tanka ba. "Yace kinga daganan idan na fita gidan ta zan wuce sbd na riga na sallami Fatima kece kawai be sanarwa ba shiyasa nazo na sanar dake' sbd gudun musake irin wancen karo. "Wasu kwallane suka cika mata ido kafin ta ankara sun xubo. "Da sauri Nasir yace subbuhanallah Aisha menene kuma haka meye abin kuka kuma?" Hannu yasa ya dagota ya dorata akan cinyarsa yana share mata hawaye snn yace dan Allah banaso na sake gani hawaye sun xubo akan kyankyawar fuskanki kina jina ko. "Kai kawai ta daga masa. "Snn yaci gaba da cewa wlh Aisha ba lalla bane kisan irin sonda nake maki bazan mance farkon ganina dake ba' tun daga lokacin Allah ya jarabcemi da sonki. "Idan zan zauna ina jero maki irin sonda nake maki da kuma yadda nakeji a cikin zuciyata idan naganki cikin bacin rai ba lallane ki amince ba daga karkema zakice karya nake maki ko kuma kice dadin ba amma wlh Aisha ina matukar sonki. "Murmushi tai hade da cewa nagode. "Nasir yace kukan yakare ko yan'mata na?". "Murmushi tai hade da boye fuska cikin jikinshi. "Mikewa alhji Nasir yai hade da daukarta cak kamar jinjira ya juya ya shinfidata a gado snn ya cire jallabiyarsa hayewa kan gadon yai hade da cewa bari naiwa yan'mata na tausa. "Tsanle Aisha tai tana fadin nashiga uku' da sauri Nasir ya cabkota ya maidata karkashinsa Aisha tace dan Allah Yallabai kabari. "Da haka yaci gaba da janta da wasa har yasamu ya biya bukatar sa snn suka tashi yana rike da'ita suka shiga toilet sukai wanka yaxo ya shirya yatafi gidan Hauwa sbd kada ta iso baya gida. "Duk da tana shakkansa amma kuma yafi kowa sani halinta batada mutunci' mafi yawancin har gara yaiwa Aisha da Fatima zasu dauke amma ba Hauwa ba. "Nasir yana fita Aisha taje ta kwashe kayan abinci dayaci takai kitchen. "Ko kafin alhji Nasir ya'isa har Hauwa tarigashi iya gidan yana parking yashiga daga cikin gidan' wani irin kallo tai masa snn tace sae yanxu kaga damar xuwa ka taroni?". "Murmushi yai hade da cewa sannu da zuwa malam Hauwa. "Karisawa yai gun da take zaune ya rungumeta yana fadin kinsha hanya. 📖🖊 🍀🍀 🍀 AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.🍀 MMN USWAN 0⃣2⃣ "Murmushi itama tai masa hade da cewa haba alhji sbd Allah ka kyauta kenan?" Tun kafin na isa na kiraka na sanar dakai ina hanya a tunanin kafin na'iso zakazo nan kajirani ne ashe ba haka bane. "Yanx sbd Allah ka kyauta kenan? murmushi alhji yai snn yace amma kinsan kafin nazo sae naje na sallami yan'uwanki ko?". "Hauwa tace ina xuwana dasu wann matsalar kace ba tawa bace idan ni babu ruwana dasu' amma kasan tunda ba dadewa zanyi ba anan har nakoma ko?" Tunda kaga ba dade zanyi ba nan da jibi zantafi. "Alhji yace Hauwa kenan dadina dake son kai babu ruwanki da damuwar wani taki kawai kika sani. "Murmushi ita tai kasa snn suka gaisa hade da hiran yaushe gamo. "Hauwa ita matar alhji Nasir ta biyu a da' gun cikinsu daya kafin ya aureta amma bayan sunyi aure tabar aikin ta koma international business xuwa kasashen larabawa dana turawa tana saro kaya shiyasa ita kanta batada lokacin kanta banle na wani. "Ita da maigidanta sae sukai wata 2-4 basu hadu ba tun alhji yana korafi har yagaji ya hakuri sbd babu yadda zaiyi da'ita. "Bayan sunyi sallar isha'i yafita yaje family kitchen ya siyo masu abinda zasuci sbd yasan koda yai mata mgn cewa zatayi tagaji baxata iya shiga kitchen ba'maje fada banxa banle sarki yai sako ba daga tafiya take ba bata shiga kitchen sae tayi ra'ayi banle yau da ta dibo gajiyar hanya. "Shikuma alhji Nasir a rayuwarsa babu abinda ya tsana a rayuwarsa kamar yaje siyo abinci a kanti a cewarsa da girman sa da mutuncinsa bayan haka gashi da mata har uku amma ace yana siyan abinci a waje?". "Wancan karo da taxo Aisha yasa tai masu girki akabawa draver ya kawo masu gidan Hauwa' Hauwa batasan daga ina ne abinci yake ba saeda takare ci snn take tambayar Nasir. "Nasir yace daga gidan Aisha ne'Hauwa tace wata Aisha kuma?". "Yace Aisha amaryata a take ta haushi da fadi inda take shiga banan take fita ba'tsayawa yai yai shiru yana kallonta mmki ita kanta Aisha bataso girka wanga abincin ba sanadiyar takura mata da yai akan girkin harda kuka saeda ta amma besa taki yiba sbd son da take masa da kuma shakkansa. "Amma a wanga karo na kanti kawai ya siyo sukaci bayan sun gama cine sukai wanka suka kwanta duk yadda Nasir yakai ga sha'awar Hauwa amma haka ya hakura da haka har saeda yai kwana biyu a gidan ta kwananta biyu snn ta shirya kayanta xatabar gari ta koma gun harkokinta. "Tunda Nasir yabar gidan Aisha batada lfy a tunaninta da safe zaizo gani kwanansu ne kamar yadda yasaba idan har ba gidanka ya kwana ba da safe kafin yatafi aiki sae yaxo gani kwananka snn yakarisa gun aiki. "Amma idan Hauwa na gari baya iya yin hakan sbd Hauwa gogaigiyar yar'barikine wanda tasan duniya duniya ya santa duk wata hanya ta kisisina ta dade da saninsu dan ma Allah yasa tana shakkan Nasir ne yasa take rage wani abu. "Sbd idan tabari ransa ya baci abin baya masu kyau. "Dan Nasir mutum ne mai taurin kai da fushi ga kuma nuna isa' shiyasa baya daukar rainin wayo duk matanshi susan da haka. "Duk da zazzabin dake damuji haka lallaba da shiga makwabtanta gidan mmn juwairiya ta aiketa siyo mata danyan kubowa sbd tun da Nasir yabar gidanta takejin cin miyar kubuwa danya. "Taso inda Nasir yaxo da safe ne sae ta sanar dashi idan yaxo koda balyaminu ne yaron aikinsa sae yabashi ya siyo mata sbd ya hanata fita ko'ina gashi kwanarsa biyu be leko ba hakan yasa taje ta nimi yar'aike. "Kafin ta dawo daga makwabta Nasir ya shigo gani bata parlour yasashi shiga har bedroom nimanta ninma be ganta ba sae yaleka toilet ko tana ciki nan ma batanan parlour ya koma ya zauna yana tunanin ina taje sbd a iya sanisa yasan bata da kowa a garin kuma batasan wani ba toma yaya za'ayi tasan wasu sbd tunda aka kawota garin babu inda ta taba zuwa kuma babu wanda yake shiga mata sbd Nasir yariga ya hanata hulda da kowa. "Suma kansu yan'uguwa gani suke tafi karfinsu sbd babu mai kudin mijinta a uguwarsu shiyasa suke tsoro shiga gidan. "Haka ya zauna yana faman tunani ire-iren haka yasa juyi da key din motar dake yatsarsa kamar daga sama yaji sallamarta tana shigowa parlour suka hada ido da sauri ta sunkuyar da kanta kasa hade da komawa da baya tai shiru. "Mikewa yai yaxo inda take tsaye ya xuba masa ido batare da yai mata mgn ba'gani irin kallon da yake mata ne yasa tafara hawaye. "Da sauri ya daka mata tsawa yana cewa wlh idan baki daena min kuka ba saena yimaki abinda baki taba zato ba. "Aisha najin haka da sauri ta goge hawayen'Snn yace ina kikaje?". "Nan tafara inda inda' Nasir yace badake nakeyi ba?". "Wasu hawayen ne suka sake zubowa tace gidan su mmn juwairiya naje. "Yana me kikaje yi a gidan?" Dama kinsaba fita kenan idan bani... "Da sauri tace a'a yau ne kawai shidinma sbd juwairiya naje na aika ta siyomin kubewa danya. "Nasir yace ina Bilyaminu? Tana tunda katafi be shigo gidan ba dama idan bakanan becika xuwa ba sae in kana nan. "Yace to meyasa baki kirashi a waya ba'yazo ya siye maki?". "Shiru tai taci gaba da kwalla. "Nasir yace banace bana son gani wanga hawayen na rashin dalili ba. "Da sauri tasake kamo bakin hijab dinta ta goge hawayen. "Snn yacigaba da cewa amma kinsan hukunci matar da tafita bada izinin mijinta ko aisha tunda lokacin da kika fita har dawowarki kinsan ubangiji yana tsine maki kuwa?". "Shiru tai. "Idan yanxu ban yafe maki ba haka ubangiji zaici gaba da tsine maki tunda bada izinina kika fita ba. "Dukawa tai har kasa tace dan Allah kayi hakuri in Allah ya yarda hakan bazai sake faruwa ba. "Yace na yafe maki tashi kije ki dauko min abinci. "Shiru tai takasa ce masa komai. "Yace da kefa nakeyi. "Snn tace ban dafa komai ba. "Matsawa yai dab da'ita hade da rike mata hijabin dake biye da'ita yace yaushe rabonki da girki. "Tana hawaye tace yau ne kawai'shidinma sbd banajin cin komai ne sae tuwo kuma bansamu mai siyomin kubewa ba shiyasa.... "Cikin tsawa ya dakatar da'ita hada da haushi ya yaye mata hijab din dake wiyarta. "Fisgota yai xuwa bedroom gaban miroow ya tsaidata yasa hannu ya cire mata rigar dake wiyarta hade da cewa nasha gaya maki banaso ganiki da wanga zulubbuwar riganga. "Tanage da'ita sae pan gashi ko bra bata dashi yaka kanta yai dab da mirror din yace dubeki fa dan Allah aisha' Aisha meyasa kikeson jawomin zagi ne?". "Sbd Allah yanxu idan yan'uwanki sukazo suka ganki haka me kike gani zasuce?" Ba sae suga kamar ina cutar dakece ba. "Ita dae tana tsaye kanta na kasa babu abinda takeyi sae kuka. "Nasir yaci gaba da cewa idan bakici dan kanki ba ai kyaci dan d'an dake cikinki sbd Allah waye zaiganki yace kinada ciki har na wata uku' dubi yanda kika koma fa. "Wlh Aisha duk irin son da nake maki idan har kikeyi sanadiyar cikinga ya samu matsala daga har ke ina me tabbatar maki ranmu zai baci a gidan nan. "Sake fashewa tai da wani kuka snn taci gaba da cewa tun ranar da kabar gidan nan banida lfy ko bcc banayi kuma bana iya cin komai koda naci baya zama. "Gani irin kukan da takeyi ne yasashi kamota ya rungume yana fadin ya'isa haka daena kuka haka Aisha towel din dake gefen gado ya jawo ya daura mata snn ya kamata ta kwanta sallamar juwairiya ne ya katseshi mikewa yai yaje ya amso kubewar ya'ije mata a kitchen. 📚✍🏻 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES☘ MMN USWAN 0⃣3⃣ "Yana eje kubewar komawa yai dakin ya samu bakin gado ya zauna snn yace ni dae aisha zantafi. "Aisha dake kwance ta tashi zaune snn tace katafi ina?". "Nasir yace g'idan Fatima mana. "Aisha tace g'idan Fatima komawa? 'Haba Yallabai meyasa kakemin h'aka sbd Allah' Idan ba mantuwa nai ba ranar da Hauwa tazo nice fa da girki amma h'aka ka tsanleke kaje g'idan ta ban nuna damuwata ba sbd nasan ba'a tare kukeba na barka katafi g'idan ta har kwana biyu yanxu da yakamata ace ka nan shine zakaje g'idan Fatima kuma bayan nan yakamata ka dawo. "Gaskiya Yallabai bazan boye maka zan'iya hakuri akan komai amma banda irin wanga abubuwan' sbd Allah kodan kaga ni banida kowa ne a garin nan sae kai yasa kakemin h'aka Aisha tana mgnr ne da fashewa da kuka 😭. "murmushi kawai Nasir yai ha'de da jawota jikinshi yana lallashinta yana cewa to ya'isa h'aka Aisha ta Idan banda abinki ni banga abin kuka ba 'k'uma mgnr kice bakida kowa a garin nan sae ni' naji dadin h'aka amma k'uma kada ki mance kinada Allah da manzonsa ga k'uma to ai kece mai gata gaki da Allah da manzonsa ga k'uma ni mijinki da h'aka ke kikafi kowa gata dan h'aka ki dai na damu kanki "Shiru Aisha tai tana sauraransa har ya kare' snn yace dan h'aka banaso ki sake irin wanga tunanin kina jina ko? " " ni zanfita zanje na duba kwana su Fatima da yara na dawo'dan Allah kada ki shiga ciki sbd bilyaminu zai kawo sako kada yanxu yai ta sallama kina ciki. "Aisha tace amma dan Allah kada ka dake ' Nasir in sha Allah. "mikewa tai h''ade da cewa me kakeso ci na dafa maka kafin ka dawo? "murmushi yai h'ade da jawota yace yan'mata na duk abinda kika dafa inaso. "murmushi tai snn tace Yallabai kenan. "Yan'mata fa kace. "Yace Eh mana amma tawa ba! Ba tani Ba. "murmushi cikin shagwaba tace da!'kenan. "kallanta yai snn yace yanxu fa?". "sai da ta kwalkwale da dariya snn gave na girma. "murmushi yai h'ade da cewa Aisha ta kenan ni zantafi sai na dawo. "Aisha tace to sai ka dawo. "alh Nasir yace bako rakiya? " "murmushi tai snn suka jera tare'har bakin kofar parlour ta rakashi ya tafi. '"Kai tsaye kitcher ta shiga ta fara aikin abinci' tana cikin aikin kenan ta jiyo sallamr bilyaminu a parlour da sauri ta saki aikin da takeyi taje gun bilyaminu. "Bayan sun gaisa bilyaminu yace alh ne yace na kawo sako. "gun Aisha ta nuna masa ya'ije kayan' har yajuya zaifita sai Aisha tace bilyaminu katsaya kaci abinci mana. "Yace wlh Aisha sauri nakeyi' Aisha tace to bari na zuba maka katafi dashi. "Da sauri ta shiga kitcher ta zuba masa a foodplast ta kawo masa. "amsa yai h'ade da godiya ya tafi' Bayan fitarsa ne Aisha tayi kokarin daukar kwalayen da bilyaminu ya shigo dashi amma ta kasa sbd sunyi nawi da yawa. "H'aka ta barsu a gun ta koma kitcher taci gaba da aikin ta' tana karewa ta kwashi abincin ta kai dinning ta jere masa snn ta shiga wanka. "Tana fitowa daga wanka ta dindisa kwalliyarta cikin riga da sket ta koma parlour ta zauna zaman jiran alh ya dawo. "Shiru Shiru tun tana kokarin dinne bacin rai har sai da ya kamata' ita kadae take zaune kallon TV ma ya gagara kashewa tai ta shige dakinta kan gado ta fadi tana koka. "Gani har magrib yayi Yallabai be dawo ba yasa Aisha ta mike ta shiga toilet tai alwala tazo ta fara sallah' sai da tai magrib da isha'i snn ta dauki wayarta ta kira alh'Yai ringing har three miss call amma be daga ba h'akan yasa ta hakura da kiran taje ta rufe kofar parlour snn ta dawo ta tube tasa rigan bcc ta kwanta. "har bcc ya fara daukarta sai taji wayarta yana ringing, koda ta duba number Nasir tagani tana dagawa yace xo ki b'ude min kofa. "Sauka tai daga kan gadon taje ta b'ude masa h'ade da amsar ledan daya shigo dashi snn tace sannu da zuwa shige wayarta tai batare da ta tsaya jiran sa ba. "Shiko tsayawa yai ya rufe g'idan snn ya kariso parlour' ko kafin yazo ta'ije masa ledarsa ta shige dakinta ta kwanta. "kai kawai ya kada snn ya bita cikin dakin' koda ya shiga ganinta yai kwance ta kama bakin aiki wato kuka. "Karisawa yai bakin gadon ya zauna snn yace Aisha. "banxa tai dashi taci gaba da kukanta. "Nasir yace da kefa nakeyi k'uma nasan kina jina. "Snn tace na'am. "Yace tashi inaso muyi mgn dake. "A hankali taja ta zauna kamar bazata tashi ba' Bayan ta zauna ne ya kalleta snn yace inaso kisa hannu ki goge hawayen nan da suke xubowa na rashin dalili ko k'uma yanxu kiyi me dalili. "Aisha najin h'aka da sauri tasa hannu ta goge hawayen tass' Snn yace tashi ki mayar da kayan da kika cire' A sanyaye ta sauka ta dauko kayan har zatasa sai yace a'a kananu nakeso kisa min ba wanga Ba. "Meda kayan tai ta dauko english wear tasa riga ce wanda bata wuce iya cinyaba sai karamar wandonta itama bata kai cinyaba ba. "Bayan ta gama sawane ya juyo sai da ya kare mata kallon snn yace saura kwalliya. "H'aka ta dauki kayan tai' duk tana yine tana hawaye har tagama. "Nasir yace banace banason gani kwalla suna xubowa daga idan ki ba. "Hannu tasa ta share h'ade da cewa ba kuka nakeyi ba. "Sai da ya kare mata kallon snn yace yauwa ko kefa' tsayawa tai kanta na kasa 'yace jeki ki dauko min abinci na. "fita tai taje parlour ta kwaso masa abincin sa yanaci yana hira yace ta dauko ledan daya shigo dashi. "mikewa tai taje ta dauko ta kawo masa' yace ta zauna ta b'ude ledan tana budewa kayane ta gani kananu masu kyaun da tsada kala kala. "gani yadda take kallon kayan yasashi dariya snn yace wata matace ta kawo office dinmu shine ba siye maki. "Cikin murna da doki Aisha tace nagode Yallabai Allah ya kara budi yasa kafi h'aka. "Dariya sbd jin dadi addau'arta yace nima nagode Allah ya barni da yan'mata na' kashe ido daya yai h'ade da yimata gwado 😜 sbd yasan bataso. "Mikewa tai tana bubuga kafa alamar shagwaba' da sauri ya mike ya rungumeta yana cewa to kiyi hakuri na tuba bazan kara ba' Yan'mata na yanxu ta gaima. "Gani irin hararan da ta kai masa yasashi cewa au na kuma ko? Mari ta kai masa a kirji amma da wasa. "Daukarta yai tsaf ya dorata akan gado shikuma ya shiga wanka ' kafin ya dawo ta kwashe kayan dayaci abinci ta kai kitcher snn ta dawo daki. "Tana shiga ya fito wanka sanye da kayan bcc a jiki' shigewa yai bargo suka kwanta. "A wann dare Aisha taso birge alh amma ina!!!! Ta kasa sai faman kuka takeyi da juyi' gani taki tsaya masa da kyau hannu yasa ya b'ude ta da karfi yaci gaba da aiwatar da nufinsa itako Aisha sai faman lankwaye masa takeyi kamar maciji. "kafin safe duk Nasir ya galabaitar da'ita' Bayan sallar asuba komawa tai ta kwana'shima zuwa yai kasa da'ita ya kwanta h'ade da kiran sunanta. "Can karkashin makoshi ta amsa masa' Yace dan Allah kiyi hakuri kirji? " kai kawai ta daga masa. " Nasir yaci gaba da cewa wlh Aisha nima kaina bana sani inada karfin sha'awa h'aka sai nazo kanki' na kanyi iya kokarina naga nayi cintrolling kaina amma sai na kasa bansan abinda yasa ba. "K'uma h'aka baya kamani sai a kanki amma in Allah ya yarda zanyi kokarin h'akan bazai sake faruwa ba kinji Aisha ta. "Aisha tace naji. "mikewa yai ya shiga wanka yana shiga toilet a hankali ta lallaba ta mike taje kitcher ta h'ada masa abin karyawa. "kafin ya fito ta gama ta kai masa dinning table' yana fitowa ya shirya cikin bakaken suit yaje yai breasfast yanayi suna hira har ya kare snn sukai sallama ya tafi. "Bayan ya fitane ta kwashe kayan ta kai kitcher snn ta koma daki 'Zama tai a bakin gado rike da wayarta a hannu shiru tai tana faman tunani kala kala. "A zuciyarta tana f'adin dama h'aka duk wanda yai aure yakeji? Dama h'aka mu' amala tsakani mata da miji yake da wiya? Kai anya koma?! Kodai ni kadai ce nakejin h'aka? Ko k'uma banida lfy ne? "Nasan idan h'aka ne babu yadda za'ayi zamansu ya dare har yakai ga haihuwa'kuma babu yadda za'ayi budurwa tabar g'idan iyayenta tabi wani katon banxa. "Ko kodai na kira karima ne na tambayata yadda abin yake tunda ita ta rigani aure harma da yara biyu 'nayi h'aka kuwa idan nai h'aka batonawa kaina asiri nai ba da mijina? Sbd tunda nake da ummata bantabaji koda wasa suna irin wanga hiran da kawaye ko makwabta ba. "k'uma kullum sai Yallabai yace duk wiya duk rintsi kada na fadiwa wata sirina banle ma irin wanga 'To kodai zan kira ummata ne na fadi mata? Kai bazan iya ba' inama xanfara. "Duk Aisha ta wanga mgnr ne a cikin zuciyarta' a hankali ta lallaba taje ta dauko wani karami mirro ta dawo kan gadon tubewa tai ta h'ade da raba kafafuwarta ta bude sosai snn ta dauko mirro din ta duba gabanta gani yadda gaba daya ya canxa harda wasu kananu kuraje suka feso mata a gefen cinyoyinta kamar yan'yan zafi wani irin ijiyar zuciya tai snn ta ije mirro din ta dauko powder zafi ya yayyafa agun h'aka ta kwanta ko pan babu banle zani kafa a bubude kamar yar'shayi a take bcc ya dauketa. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F..O. W. ☘ MMN USWAN 0⃣4⃣ "Aisha bata falka ba sai bayan azahar'tana tashi taje tai wanka h'ade da alwala tazo tai sallah' bayan ta'idar ne ta tashi kitcher tasa sanwa. "duk da ba wani cin abinci take jiba amma h'aka ta lallaba tai masa tuwon shinkafa da vegetable soup bayan ta gama ta kai masa dinning ta danke masa su snn taje tai wanka tasha kwalliyarta cikin englsh wear takoma parlour ta zauna tana jiransa ya dawo. "Gani tara yayi be dawo ba yasa ta canxa channer daga zeeworld xuwa nigeria news tana kallon abinda ke tafiya a duniya duk abinda Aisha keyi tanayi tana duba agogo har aka kare labaran Nasir be dawo ba' Wayar ta ta dauka tai dilling nmbe sa har sau uku yana ringing amma be dauka ba sai a na hudu snn ya daga. "Cikin natsuwa tai masa sallama' Nasir amsawa yai da fara'arsa snn Aisha ta gaidashi da aiki' yace aiki alhamdllh snn tace gani nai har goma yakusa baka dawo ba shine nace bari na kira naji ko lfy? ". "murmushi yai snn yace Aisha ta kenan wlh aiki ne yimin yawa shiyasa kikaga bandawo ba amma yanzu h'aka zantaso kenan na dawo g'ida kinji Aisha ta. " Aisha dake zaune tace naji Yallabai. "Nasir yace Aisha ya! Najiki wani irin h'aka?". "murmushi tai snn tace kewarkane kawai ya dameni. "Dariya yai snn yace Aisha kenan'idan banda abinki tare fa muka kwana ko duk kin mance ne? Shiru tai' Shiru da tai ne yace Aisha. "tace na'am. "Yace me kikaso na siyo maki? Kinsan me ciki da kwadayi. "murmushi tai h'ade da cewa babu komai kai kawai nake bukata. "Wani irin d'adi ne ya ziyarci zuciyar alh Nasir' amma ya matse yace kamar da gaske... "Aisha tace wlh kuwa Yallabai. "Nasir yace na yarda amma inaso kimin alkawari. "Aisha tace na mefa? ". "Nasir yace yau baza'aimin kamar na jiya ba. " Aisha tace kamar yaya? ". "Nasir yace kin mance abinda kikai jiya ne? Lankwayewafa kikai tayi kamar wanda babu kashi a jikinta kina cewa kashi! Waish! Aish! Yallabai ka tausayamin wlh akwai zafi' Ko duk kin mance ne?". "Hannu tasa ta rufe fuskarta kamar yana ganita. Jin shirun da tai yasashi kwalkacewa da dariya h'ade da kashe wayar. "mikewa tai ta sake wani wanka daya daga cikin rigunar da ya siyo mata daga office d'insa tasa kafin ta tafi parlour taji knocking d'insa' Da sauri taje ta b'ude masa ya shigo h'ade da yimasa snn da zuwa. "d'adi ta rakashi h'ade da tayashi tubewa ta h'ada masa ruwan wanka ya shiga wanka kafin ya fito ta fidda masa da kayan bcc sa bakin gado ta zauna tana jiran fitowarsa 'yana fita ta mike ta dauko masa lotino d'insa ya shafa ta tai maka masa yasa kaya snn suka nufi dinning d'an cin abinci. "Plate ta dauko ta xuba masa yanaci suna hira har yakare ta kwashe kayan ta medasu kitcher snn ta dawo' Tana dawowa yace suje su kwanta sbd dare yayi' Koda sukaje kwanciya gani Nasir ya fara shafeta da sauri ta janye jikinta daga nasa. "Da mmki Nasir yace Aisha menene h'aka? Kizo mu kwanta mana. "Aisha tai shiru duk idanuta suka cika da kwalla. "Sbd duhun dake d'akin yasa bega kwalla ba' jawota yai jikanshi yaci gaba da aiwatar da nufinsa' duk da juye juyen da takeyi amma be hanashi ba h'akan yasa tashi wiya sosae. "Da safe be tsaya bata lokaci gun bresfast ba a tsantsaye yasha ya fita' yana fita taja a hankali tashiga wanka' tana cikin wankan ne i'dan ruwan zafi ya tabi gun wani irin zafi takeji da taga h'aka watsa ruwan kawai tai a jiki ta mike. "Ruwan lipton kawai tasha ta kwanta' dama tunda Aisha ta samu ciki bata da wani abincin da yawoci lipton sbd koda taci wani abu baya zama duk dadin sa'Sai lipton din shiyasa duk ranar da Nasir baya g'idan ta bata girki' I'dan ma tayi kadan ne na bilyaminu d'an aikenta. "Shiyasa yau tai kwanciyarta sbd ko bilyaminu ma da take girkin d'anshi yau bayanan ruwan zafi ne k'uma akwai a plast' Bayan Nasir ya tashi daga aiki sai da yazo g'idan Aisha sbd suyi sallama yau g'idan Fatima zai koma. "Dama kwana bibbiyu sukeyi' Aisha na kwance sukai sallama ya fita h'ade da janyo mata kofa ya rufe'bayan fitarsa ne Aisha ta fashe da kuka sai da tai kuka sosae snn ta mike taje toilet tai alwala tazo ta zauna tafara nafila snn tai sallah. "Bayan ta'idar ne ta zauna tana tunanin baya a zuciyar tana cewa Ashe mgnr KARIMA gaskiya ne lokaacin da zan auri Yallabai KARIMA take cewa ke Aisha da kuruciyarki zakije ki shiga cikin mata biyu kece ta uku Aisha' Aisha ki daure ki auri yazed yaro kema yarinya koba komai zaku more kuruciyarku ga k'uma kwanciyar hankali. "Wlh Aisha bantaba koye maki komai ba a tsakanina da bbnsu su AMIR lokaacin da zaikara AURE Wlh har cikin ziciyata ji nake kamar idan yafita g'idan karya dawo' har addu'a nakeyi i'dan yafita mota ta bugeshi a dawomin da gawarsa sbd kowa ya raya' amma nasan yanxu Aisha ba lallane ki fahimci abinda nake nufi ba ko kisan halin da nake ciki amma tunda yanxu me mata zaki aura watarana ko bani tare dake sai kintuna da mgn ta Aisha. "Wani irin ajiyar zuciya Aisha tai h'ade da cewa lalla KARIMA Ashe akwai ranar da zan zauna ina tuna wanga mgn' Yau inda ace saurayi na aure wanda beda mata nasan da nunanan tare yana tayani raino ciki da nan-nan dani amma da yake wanga me iyaline ko'ajikinsa gashi yasan banda lfy k'uma duk wanta laluran dana shiga sanadiyar auransane dani sbd kafin nayi aure bansan irin wanga laluran ba sai yanxu k'uma na rasa meke kawomin irin wanga yawan cututuka h'aka ko asibitine zanje naga likita? ' K'uma naje batare da sani Yallabai ba?'. "Duk Aisha na mgnr ne a cikin zuciyar ta' can k'uma tace ba nabari xuwa gobe gani yanxu kuraje zasuyi' idan yaro in Yallabai yazo da fase saena sanar dashi. "Washe gari da safe Aisha nasa idon Yallabai har tara yai amma bezo ba gani h'aka yasa ta dauki waya ta kirashi ringing din farko ya daga h'ade da sallama be tsaya sun gaisa ba yace Aisha ta dan Allah kiyi hakuri nasan nayi lafi amma kiyafe min kinji. "Aisha tace babu komai ya wuce. "Snn yace kin tashi lfy? ". " tace klau'kaima katashi lfy?. "yace klau ya jikin naki? Aisha tace dama nabuga ne na bambayeka inaso naje asibiti.. "Nasir yace jikin ne har yanxu? "Tace eh amma zazzabine kawai. "Nasir yace zazzabin har yanxu kina jinshi sosae ne ko yane? Tace a'a yanxu dai nasamu sauki ba kamar dare ba. "Nasir yace to ganinan zuwa mutafi asibiti kawai doctor ya dubaki ko? Aisha tace a'a da kabari kawai bilyaminu ya kaini basai kabaro office ba. "Nasir yace zamana kikeyi ko zaman bilyaminu?Shiru Aisha tai. "Kashe wayar yai h'ade da mikewa ya baro office zuwa g'ida' yana shiga kai tsare d'akin ta ya nufa da sallama ya sameta zaune a bakin gado. "Tana ganisa ta saki fuska h'ade da murmushi tai masa snn da zuwa'ya amsa da tambayar kijinta. Tace da sauki. "Yace shirya mutafi' mikewa tai ta dogowar riga da hijab suka nufi asibiti' suna isa kai tsaye d'akin doctor suka shiga Nasir ne ya mika masa hannu suka gaisa snn itama Aisha ta gama shinkafa. "Doctor Kamal yace Yallabai yai! dae? Nasir yace yan'mata nace batajin dadi' Aisha najin h'aka ta sunkuyar da kai kasa Doctor Kamal yace hjy Aisha ya kikejin jikin? "kan Aisha na kasa takasa daga kai banle ta basai amsa' da doctor Kamal yaga h'aka kashewa alh Nasir ido yai alama yafita. "mikewa yai yafita yana murmushi'bayan ya fita ne doctor Kamal yace Aisha meke daminki? Aisha tace wani kurajene suka fitomi matse matsina. "Doctor yace yaya kuraje suke? "Aisha tace kananune masu Zaria da kankayi. "Doctor yace tun kina budurwa ne suke maki h'aka ko yaya? "Aisha tace a'a bayan aure nane. "Doctor yace h'aka kawai suka fito ko yaya? Kan Aisha na kasa tace eh amma basa tashi kankayi da zafi sai ranar da take g'ida na' doctor yace kayar yaya? Banga ne ba? Shiru Aisha tai. "Doctor yace ko dai kina nufin idan ya sadu dake?(sex) Aisha tace eh. "Doctor yace ok. "Alh Nasir ya shigo'Dama duk mgnr da sukeyi yana jinsu' maguguna ya rubuta masu snn yace ba komai ke kawo irin wanga ciwon sai idan kuna sharing toilet ana iya dauka.... "Da sauri Aisha tace a'a toilet d'inmu mukadai muke amfani dashi kuna tun ina g'ida bana h'ada toilet da wasu. "Doctor yace eh basai h'ada toilet kawai yakesa a dauka ba miji yana iya bawa matarsa misali idan ya kwanta da wata matar tanashi to anan ne zai dauka ya bawa wanda bata dashi. "Shiru Aisha tai h'ade da kurawa alh Nasir ido'duk idanuta suka cika da kwalla' Duk da Nasir ya lura da h'aka amma be nuna mata yaci gaba da sauraran doctor har yakare bayanin sa' snn sukai sallama h'ade da gidiya. "jikin Aisha a sanwa take tafiya sukaje gun saeda magani suka siye' bayan su siye ne sukeje mota ya bude mata gaba ta tashi shima ya zaga ya shiga ya jasu zuwa gida. "Bayan su isa g'ida ne da kansa ya dauketa ya kaita d'akin ta ya shinfidata ta kwanta ' bude frg din dake d'akin ta yai ya dibo ruwa yace ta tashi tasha magani' amsar kofin ruwan tai ta eje a gefe. "Da alh Nasir yaga h'aka hannu yasa ya dagata ta zauna' shima dukawa yai a gabanta yace Aisha 'Aisha' Aisha. "tace na'am. "yace sau nawa na kiraki? "Tana kwalla tace sau uku. "Snn yace wlh Aisha ko kur'ani kika bani zan'iya yimaki rantsuwa' wlh tunda nake a duniya bantaba yin wani aiki makamancin zina ba banle har na aikata zina da kaina. "Tun bansan ciwon kaina ba lokacin inada kuruciyata naiwa ubangiji alkawari idan har Allah ya cikami burina ni k'uma nai masa alkawari bazan taba saba masa ba. "Sai dai d'an Adam ajixina amma bata hanyar zina ba. "Idan h'aka kimin wani zargi amma banda zina. "Shiru Aisha tai tana kwallonsa' Nasir ya mike yace ni zantafi Allah ya kara sauki' fita yai h'ade da janyo mata kofa ya koma office. ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES. F. O. W. ☘ MMN USWAN 0⃣5⃣ YA ALLAH, ACCEPT OUR PRAYERS AND FORGIVE OUR SINS BEFORE WE RETURN TO YOU AMEEN TAKAITANCEN BAYANI. MAGANI TOILET INFECTION 1 SASSAKEN BAURE KANUMFARI ZUMA MAZARKWAILA CITTA ZAKI ZUBA SASSAKEN BAURE A CIKIN TUKUYA KI ZUBA RUWA DA YAWA SAI RUWAN SUN KUSA SHANYEWA SAI KI SAUKE' KI CIRE SASSAKEN BAURE ' SAI KI TACE BAYAN KIN TACE SAI ZUBA ZUMA MAZARKWAILA CITTA KANUMFARI. ANASO A ZUBA KANUMFARIN DA YAWA A MAYAR A CIKIN TUKUYAR YA KARA TAFASAWA SANN KIJUYE KI RINKA SHA KOFI BIYU A RANA. WANAN HADIN HADINE NA MUSAMMAN WANDA MACE TANA AMFANI DASHI' ZATA KARA SAMUN WADATACCIYAR NI'IMA SNN DUK YANA KASHE KWAYOYIN CUTAR GABAN MACE. KUMA YANA MOTSA SHA'AWA DA KARAWA MACE NI'IMA DA KUMA KASHE KWAYOYIN CHUTA. YANA KUMA MAGANI FITOWAR FARIN RUWA DAGA GABAN MACE. ALLAH YASA MUDACE. 2 GABAN YANSUN GARIN TAFASAWA ZUMA COKALI 10 A HADA SU GURI GUDA ANA SHA KARAMIN COKALI SAU BIYU A RANA HAR KWANA GOMA ZA'ADACE INSHA ALLAH. 3 GARIN SI'ITIR NANAR SHAYI RUWAN KHAL ANA HADA MAGANIN COKALI DAYA DA KHAL ZA'A DACE INSHA ALLAH. DAN ALLAH YAN'UWA GA DUK ME LALURA IRIN WANNAN KARA YAJI KUNYA SBD BA'A KUNYA DA CUTA TAYI KARAMIN NIMAN WANGA MAGUGUNAR TA HADA INSHA ALLAHU ZA'A DACE. ALLAH YA DATAR DAMU AMEEN. **** ***** **** "Shiru Aisha tai tana kallonsa har yafita' wani sabon kuka sai da tai me'isanta snn tai Shiru ledar magugunarta ta dauko tafara cirewa sai da ta gama snn ta k'ada tasha. "Tana gama sha bcc ya dauketa bata tashi ba sai gab da la'asar snn ta tashi' tana tashi toilet ta shiga tai alwala tazo sallah bayan ta'idar ne taje tashiga kitcher ta h'ada ruwan lipton tashi snn ta koma dakin da yamma kafin Nasir yaje g'ida sai da ya biyo ya dubata da jiki snn ya karisa g'idan Fatima. "washe gari snn ya dawo g'idan Aisha tunda Hauwa ba gari take ba sai tazo shiyasa ya raya kwana bibbiyu amma duk ranar da Hauwa tazo ko g'idan wayo yake zaije gun Hauwa a nan ne zai zauna har sai ta koma. "Shiyasa yau ya dawo g'idan Aisha bayan yagama cin abincin yamma yana zaune a tsakiyar gado yana jingine da allon gado' ita k'uma Aisha tana kwance a gefen gado kusa dashi ta jiya masa baya shiru tai kamar bata gun. "Gani h'aka yasa alh Nasir daukanta ya dorata akan cinyarsa yana mata murmushi Aisha ta kokarin yin mgn hannu Nasir yasa ya rufe mata baki h'ade da shafeta kamar mai tausa. "Itama shiru tai tana masa murmushi Nasir yace yan'mata na yah! naga kin kwanta shiru ko dai jikin ne?. "murmushi Aisha tai h'ade da cewa yayi sauki ai. "Aisha ta fadi hakane kawai bawai dan ta samu saukin ciwon da take jiba. "Nasir yace da gaske yan'mata na. "Kai Aisha ta daga masa tana murmushi. "Nasir yace to bari naga gun' hannu yasa zai b'ude mata zani' da sauri Aisha ta rike zani tana cewa a'a Yallabai' shima dariya yai ya h'ade da janye hannunsa a gun. "Daga kai Aisha tai tana kallon cikin Alh Nasir' daya lura da kallon da take masa yace yah! dai yan'mata na? Aisha tace kaga yadda tunbinka ya kara girma kuwa? Dariya yai h'ade da cewa nima h'aka nake gani amma inda na godewa Allah duk girman da tunbina zaiyi kina iya daukanta ko?. "Da sauri Aisha tasa hannu ta rufe fuskanta' shima dariya yai snn yace ni dae wanga kunyar taki bansan abinda zaiyi maki na cire taba' amma naasan ta'inda zan bulo maki. "Da sauri tace kamar yaya? Gira ya daga mata' ido 😳 Aisha ta bude tana kallonsa' cikin wasa yace to menene a ciki wani dare baki gani ba? Me zai baki tsoro a ciki? Da ido Aisha ta nuna masa kirjinsa' shima dariya yasake yi masa snn yace kyau kenan kinga koba komai zanrufeki lip babu me ganiki saini' Yunkurawa tai zanta tashi da sauri ya rikota h'ade da kashe light. "Duk magugunar da doctor yabawa Aisha tana kokarin amfani dasu amma duk da h'aka be'hana kurajen fitowa ba' Gaba daya ya fetso mata' tun daga kasar cibiyanta har gaban ta kurajan suka fetso mata' gashi Nasir ba g'idan ta yake ba. "A wanga lokacin zama ya gagari Aisha sai dai kwanciya ' ko rintsawa batayi ga azabar kaikayi da suke mata' cikin dare da kurajen suka hanata bcc mikewa tai ta lallaba tashiga toilet ta kunna ruwan zafi saeda ya kusan cika bath snn tashiga cikin ta zauna h'ade da daukar sabulun dettol protection anty bacterial soap dashi take wanke kurajen duk da zafin da takeji amma h'aka ta hakura ta d'anne'bayan ta gama ne tai wanka daga ta daura towel ta dawo bedroom magani da doctor ya bata na shafawa tube shine ta dauka h'ade da auduga' bude audugan tai yai falefale sai da ta shafe tube din snn ta dauko audugan ta lulube gun dashi snn ta kwanta kafa a bubude ko zani bata iya rufe jikinta dashi ba' tana kwanciya bcc ya dauketa. "Aisha bata tashiba sai bayan shadda na safe' tashi tai taje tai alwala tazo tai sallah bayan ta'idar kwanciya tai tana jiran xuwan Yallabai shiru2 har goma bezoba h'aka ta sake lallabawa taje kitcher ta h'ada tea tasha da magani'bayan ta gama ne takoma d'akinta ta dauki waya tai dilling nmbr Nasir sai da tai kira biyu ana uku snn ya daga. "Cikin natsowa Aisha tai sallama' Shima da fara'arsa ya amsa' snn ta gaidashi'bayan sun gaisa ne Aisha tace gani nai baka shigo dubani bane da safe yadda kasaba shiyasa nace bari na kiraka naji ko lfy? Allah yasa dai lfy ne. "Nasir yace wlh Aisha aikine yimin yawa shiyasa bansamu biyowa ba'amma kiyi hakuri dan Allah' murmushin karfin hali tai tace babu komai' Nasir yace nagode wa Allah daya banike k'uma yasa kinada fahimta Allah yai maki albarka kuma ina Allah ya yarda yau dawori zan dawo kinji yan'mata na. "Murmushi tai h'ade da cewa naji Yallabai Allah ya kawo dakai lfy'. "yace amin nagode' amma jikin yayi sauki sosae ko? "Aisha tace ai nawarke' Nasir yace alhamdullh Allah ya kara lfy' saena dawo. "daga nan sukai sallama' Da yamma kafin Nasir ya dawo shiga kitcher tai ta h'ada masa tuwon semo da miyar kubewa busassa tana gamawa ta kwashe ta kai dinning snn taje tai wanka bayan ta fito doguwar riga kawai tasa batare da ta tsaya wani kwalliya ba ko pan babu a jikinta parlour ta koma da kwanta tana jiransa. "Bata dade da kwanciya ba alh Nasir yai sallama cikin dabara ta mike taje ta amshi jakar hannunsa h'ade da yimasa sannu da xuwa' Yace yauwa Aisha ta' ya jiki? "Tace naji sauki' "yace Allah ya kara sauki". "Kamo hannunsa tai xuwa cikin d'akinta'Bayan ta'ije jakar hannunta shima ya zauna a b'abin gado' dukawa tai tana cije masa igiyar takalmin dake kafarsa. "Dankwalin dake kanta ya f'adi ido alh na kaiwa kanta hannu yasa yana fashe masa kitson dake kanta h'ade da cewa gaskiya yan'mata na kina shagwabani da yawa' wanga irin kitso duk sbd ni akayita gaskiya naji d'adi sosae Allah yai maki albarka. "Murmushi Aisha tai h'ade da cewa Amin' Bayan ta gama cire masa takalmin dagowa tai tana kwance masa igiyar rigarsa da yake suit ne yasa sai da tagama snn ya mike ya tube' itama mike tai ta shiga toilet ta h'ada masa ruwan wanka bayan ta fitone yashiga. "Kafin yafito taje ta kara gyara dinning ta zuba masa abincin sa a plate h'ade da juice d'in da tai masa ta zuba a cup da ruwan sanyi snn ta koma parlour ta kwanta' koda yafito sanye yake da farar jallabiya a jikinsa dinning ya nufa gani tai masa arraging komai zama kawai yai yaci gaba da cin abincin sa. "Itako Aisha tana parlour tana kallon tashar zeeworld wani films da dukeyi mai suna my lost home' Gani tara yayi ta canxa channel d'in zuwa Nigera news sbd kallon labarai. "Jin za'ara labarai yasa alh Nasir cire hannu daga abincin da yakeci dama lokacin ya riga ya koshi' xuwa yai ya zauna kusa da'ita sukaci gaba da kallon labarai tare sunayi suna yana janta da hira har aka gama. "Aka koma nuno rahotanni gani goma ya wuce ya kashe TV yace tashi muje mu kwanta sbd gobe idan Allah ya kaimu inaso na fita da wuri' TO kawai Aisha tace h'ade da mikewa suka shige cikin bedroom' suna shiga Nasir ya tube ya rage daga sai short nike ya kwanta' Itako Aisha da rigarta ta kwanta can gefen gado taje ta rakube sbd bataso tai kusa dashi banle harya yajawo wani abu ya shiga tsakaninsu. "juyawar da zaiyi yaga bata kusa dashi' hannu yasa ya jawota jikinsa ya rungume ta' yace cewa Aisha yau k'uma wani sabon salon wasane kika samu h'aka? Na lura kedai baki rabuwa da wasa' shiru Aisha tai tana jinsa. "Nasir yace yan'mata na' Aisha ta dago kai tana kallonsa' yace tashi ki tube wanga rigan nasha f''idan maki babu kyau mutum ya kwanta da suturunsa masu kyau' karkiga kamar f'ade nane annabi Muhammed ( S. A. W) ya f'adi h'akan' idan h'aka kada ki sake kinjiko. "Aisha tace to. "Gani ta tsaya nawa kamar bazata iya tashi dagowa yai ya zauna akan gado snn yasa hannu ya yaye mata rigan daga kasa zai cire mata jan da zaiyi yaga batada komai a jiki inba rigan ba' da sauri ya saki rigan snn yace h'aba Aisha wani irin d'abi'a ne wanga ke ko tsoro bakiji kada wani shedani aljani yazo ya shigeki. "Shiru Aisha tai. "Nasir yace wlh koda wani idan nasake shigowa g'idan nan na sameki h'aka sainayi maki abinda baki taba tsanmani ba' wani rainin wayo ka wala kanci kirinka zama kina wala kantarmin da jiki sarai-sarin wani katon banza yashigo a kuskure ya gane min jikinki ko? To wlh bazan dauki irin wanga abin ba idan kika sake sai kinyi mmkin abinda zaiyi maki. "Aisha na hawaye tace dan Allah kayi hakuri. "Alhj yace ba zance nayi hakuri bane Aisha gani nayi dame na rageki nasan duk wani abinda zaki bukata na tanada makisu enough a g'idan nan ko sun karene bansani ba' Kai Aisha ta daga masa. "Yace to menene dalilin walakantamin jiki h'aka? "Shiru Aisha tai. "Snn yace bayan h'aka banace kada na sake dawowa g'idan nan na sameki da wanga rigan ba? Koda badake nakeyi bane Aisha. "Shiru Aisha tai tana shaeishekan kuka' Nasir yace wlh idan baki rufemin baki ba k'uma ki goge hawayen nan ba sai na maki duka idan yaso sai kiyi kuka me dalili' jan h'aka da sauri Aisha ta goge hawayen snn ta daina kuka' tsareta yai da ido. "gani bata tashi ba banle ta cire rigan' sauka yai daga gadon snn ya jawota da karfi ya cire mata rigan jikinta' hannu Aisha tasa tana rufe gabanta snn ta matse kafafuwarta' da alh ya lura da h'aka yace menene a gun da bakiso na gani? Da sauri Aisha tace babu komai. "Nasir yace banyarda ba. "gani ta kara matse cinyoyinta k'uma tana matse fuskanta alamar tana jan zafi' yawota yai dakin gadon snn yasa hannu da karfi ya bude mata kafafuwan' gani gun yai damage mmki ya kamashi yana f'adin me zangani h'aka Aisha? Tun yaushe wanga ciwon yasameki Aisha?. "Fashewa da kuka Aisha tai takasa bashi amsar tambayarsa. "Nasir be tsaya jiran amsar ta ba' toilet ya shiga ya h'ada ruwan zafi mai zafin gaske snn yazo ya dauketa xuwa baht room d'in cikin bawon wanka ya yasa snn ya dauko dettol da soso xuba dettol d'in yayi a ruwan zafin snn ya dauko medicatet soap ya goge a cikin soso h'aka ya dunga dibo ruwan zafin yana gurje kurajen. "Aisha inba ihu ba babu abinda takeyi duk da h'aka besa Nasir ya daina dirje kurajen ba' duk sai da suka farfashe suna jini snn ya kyaleta h'aka ya dauki ragiwar ruwan yai mata wanka dashi' bayan ya gama mata wankan ya dauketa xuba bedroom tube d'in da take shafawa ya shafa mata a gun snn ya rufeta da bargo shima ya kwana. "Aisha batasan lokacin da bcc ya dauketa ba. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W ☘. MMN USWAN 0⃣6⃣ "Cikin dare koda Aisha ta falka taji saukin radadin da takeji' lokacin ido Nasir biyu gani ta b'ude ido yasashi cewa Aisha yaya jikin? Aisha tace naji sauki. "Nasir yace ya kikejin radadin dake maki? Tace yai sauki. "yace alhamdullh' Allah ya kara sauki. "Tace amin. "Da safe bayan yai wanka ya shirya juyowa yai gun Aisha yace tashi muje asibiti' Aisha tace kabari kawai nasamu sauki' Nasir yace wani sauki ne h'aka kina gani yadda kika koma kuwa. "hawaye ne suka xubo mata h'ade da cewa bazan iya zama bane shiyasa' Kai kawai alhj ya kada h'ade da cewa ayya sorry insha Allahu nan bada dadewa ba zaki samu sauki kinji. "kuka Aisha tasa tana f'adin dan Allah kakiramin ummata naji muryarta dan Allah. "Gani kukan da takeyi ne yasashi cewa ya'isa h'aka zankira maki ita amma ba yanxu da sassafen gaba' kabari anjima' Aisha najin h'aka tasa kuka tana f'adin dan Allah ka taimakeni ummata. "Matsowa Nasir yai kusa da'ita ya duka a gabanta snn yace h'aba Aisha kiyi hakuri mana xuwa rana' idan muka kirata a irin wann lokacin me kike zaifaru? H'aka kawai bamu kirata ba sai da kike ciwon' Aisha tace eh nidai kakiramin ita naji muryarta. "Nasir yace to Aisha amma dan Allah koda na kirata bazakiyi kuka ba? Aisha tace eh na yarda' wayarsa ya ciro daga aljihunsa yai dilling nmber mmn Aisha' yanajin ya fara ringing ya mika mata wayar. "Aisha najin ummata tai picking call d'an ta fashe da kuka tana kiran umma' umma tace na'am Aisha' jin kukan da takeyi yasa umma cewa Aisha kiyi hakuri ita rayuwar aure dan hakuri ne' sbd ita AURE IBADA NE zaki hadu da jarabawa kala kala amma idan kikai hakuri wataran sai labari' Aisha tace Umma!!!! Umma tace Aisha banaso naji komai daga gareki sbd Allah subbuhanahu wata'ala yana fushi da macce da take tona asirin mijinta. "dan h'aka kiyi hakuri banaso ki kasance kina daya daga cikin wanda Allah zaiyi fushi dasu' nagode da gaisuwa k'uma ki gaida maigidanki sai anjima' ta kashe wayar. "Kuka Aisha tasa h'ade da hurgi da wayar' duk abinda umma ke f'adi a kunnin alhj Nasir' hannu yasa ya dauki wayar snn yace kigani ko da kinbari da rana idan na kirata nai mata bayani kinga sai ku gaisa amma kin matsa saena kirata maybe ko tashi daga bcc batai ba. "Aisha bata ko kallesa ba kuka kawai takeyi sosae' Nasir yace tunda bazaki iya zama ba bari naje na taho da doctor kamal yazo ya dubaki' idan yagama sai nai maki wanka snn naje aiki. "Aisha bata tanka masa ba' key d'in motarsa ya dauka ya fita' yana hanyane ya kira doctor kamal yake tambayarsa yana offince? Doctor kamal yace a'a amma yanxu zai fata. "Nasir yace ok' ganinan na dauke ka' doctor yace lfy? Nasir yace wlh jikin madam ne k'uma ko zama batayi da muzo asibitin kawai' doctor kamal yace ayya' tunda hakane to kabari kawai ga ninan xuwa' Nasir yace ok sai kazo. "juya kan mota yai ya koma g'ida' be d'ade da dawowa ba doctor yai sallam' Nasir ne yaje yai masa iso xuwa parlour bayan sun gaisa ne h'ade da tambayar mai jiki' Nasir yace jiki da sauki. "Mikewa yai yaje cikin bedroom gyara wa Aisha kwanciya yai h'ade da rufeta da bargo snn ya leko yace bismillh' doctor kamal ya kariso cikin bedroom d'in kujeran dake gefe ya jawo ya zauna' shikuma Nasir yana zaune a bakin gado doctor kamal yafara duddubata h'ade da yimata tambayoyi' Nasir ne kebada amsa be bari tayi mgn da kantaba' da doctor ya lura akwai lauje cikin nadi shiyasa bece zai bude bargon yaga yadda gabata yai ba. "dube dubensa yai cikin dabara snn ya sake rubuta masu magani' duk dai iri dayane da wanda ya taba rubuta mata take amfani dashi snn sukai sallama. "Bayan doctor kamal ya fitane sai Aisha tace Yallabai meyasa baka bari nayi masa bayanin abinda ke damuna da kaina ba? Nasir yace Aisha kenan h'akan ma daurewa nayi na bari har yatabamin jikinki' kodan bakisan yadda nake kishinki bane yasa kike f'adin h'aka? "Shiru Aisha tace tana kallonsa har yakare mgn snn tace to nidai kiramin ummata' Nasir yace Aisha kibari har nadawo aiki snn na kira maki ita' kinji. "Aisha tace nidai dan Allah nace' Nasir yace to ba dazu na kira maki ita ba' idan dan muryarta ne kike son ji to'ai kinji. "Cikin bacin rai Aisha tace na lura dakai Yallabai so kakeyi ka rabani da ya'uwa na'sbd tunda nazo garin nan ko da wasa baka taba tambayata ya nakejin labarin ya'uwa na ko iyayena' banle har kace na shirya naje na gansu. "Nasir yace haba Aisha wlh ba h'aka bane ' dan baki fahimceni bane yasa kike gani h'aka' amma wlh a tawa zuciyar ba haka bane. "Aisha tace h'aka ne mana sbd Allah watana biyar kenan fa a garin nan amma koda wasa bakaso nai maka mgnr d'angi na' banle har kace naje naga iya yana. "Dawowa Nasir yai ya zauna kusa da'ita snn yace dan Allah Aisha inaso ki fahimceni wlh ba nufi na kenan ba' abinda yasa kikaga banaso kikira wani daga garinsu ko nakira maki iyayenki ku gaisa sbd lokacin da aka kakemin ke bayan tafiyar ya'kawo amarya Aisha kinki kwantar da hankalinki kullum cikin kuka kike' k'uma a iya sanina dake ba tilassa maki nayiba kika aureni' da amincewarki ne mukayi aure amma kinki kwantar da hankalinki. "nayi iya kokarina wajan naga kin kwantar da hankalinki amma abu ya gagara' h'akan yasa na yanke shawarar sanarwa iyayenki ko zansamu saukin abu amma duk a banza ' shiyasa duk kikaga nake maki h'aka sbd a lokacin da baki waya dasu bakijin muryarsu nafi gane kanki k'uma hankalinki yafi kwanciya. "Shiru Aisha tai tana kallonsa har yakare. "snn yace to tunda hakane bari na kira maki ummanki d'in ku gaisa. "Wayar Aisha ya dauko ya kira umma yai ringing har ya yanke bata daga ba' gani yakira har sau uku bata daga meda mata wayarta yai ya ciro nasa daga aljihu ya kira' kiran farko umma ta daga da sallama bayan Nasir ya amsa cikin girmamawa ya gaidata snn yace Aisha ce takeso ku gaisa. "mikawa Aisha wayar yai bayan ta amsa sallama h'ade da cewa umma'Aisha tana f'adin umma tasa kuka' murmushi umma tai snn tace Aisha kenan har yanxu kinanan da halinki ko' idan har kinaso na saurareki to kidai na kuka. "har umma zata kashe wayar sbd Aisha bata daina kukan ba' cikin kuka Aisha tace umma banida lfy ko zama banayi' da sauri Nasir ya fisge wayar. "babu abinda umma keyi sai salati ta sanarwa ubangiji' jin wayar ta katse wayarta ta dauko ta nimi nmber Aisha sai kash!!!! Koda tai dinning nmber taji customer care sukace babu kudi a wayar dole yasa ta meda wayar ta eje sbd gida babu kowa abdul ne kuma yaje school. "mikawa tai taci gaba da nafilarta ta walha tana h'ade da addu'ar nimawa ya'ta sauki a gun ubangiji. "shiko Nasir yana can yana yiwa Aisha f'ada wai sbd me ta f'adiwa ummata' kuka Aisha taci gaba dayi tana cewa meyasa bazan f'adi mata ba? Ummata ne fa' a duniya banida wanda yafita. "Nasir yace ok hakane fa nima mancewa nai' mikewa yai yafice yabar g'idan. "bayan su abdul sun dawo daga school umma ta aikesu suka siye mata rechange card tasa ta kira Aisha ' Aisha na gani "muryar ummata tasa kuka tana f'adin umma! Umma tace na'am Aisha ya kike? Aisha tasa kuka tana f'adin umma banida lfy' ko zama banayi. " Cikin natsawa umm tace subbuha'lillahi Aisha meya sameki h'aka? Cikin kuka Aisha tai mata bayani abinda ke damuta' umma bata nuna damuwa ba' a matsayinta ta uwa tagari' umma tace Aisha. "Aisha tace na'am umm. "umm tace Aisha inaso kisan da cewa ita rayuwa d'an hakuri ne banle zaman AURE ki gode ma mijinki yana sonki kuma yana baki kulawa daidai gwargwado koda mune da muka haifeki iya kacin abinda zamuyi maki kenan' dan haka ki kwantar da hankalinki kinjiko. "Aisha tace naji umm. "umm taci gaba da cewa kuma dan Allah Aisha kiwa mijinki biyayya sbd aljannarki tana karkashin kafar mijinki kinjiko Aisha. "Aisha tace naji umm kuma nagode. "umm tace Allah ya kara sauki Aisha' k'uma dan Allah Aisha ciki da adda'a kamar yadda kika saba' kada kiyi wasa da addu'oin dana koya maki' idan kika rike wng addu'oin insha Allah kina tare da rinjaye a rayuwa. "k'uma dan Allah inaso na tunatar dake dan Allah Aisha koda wasa kada wata kawarki tasan sirrinki na tsakanin keda maigidanki' ko ni dana haifeki banaso nasani banle wata kawa' sirrinki sirrinki ne kiwa mijinki biyayya k'uma ki zauna lfy da abokan zamanki. "Aisha tace to umm. "umm tace Allah ya kara sauki kuma dan Allah kizama jaruma ga duk wani abu da zai bijiro maki' banda yawan kuka. "Aisha tace to. "umm tace Allah ya kara sauki saina sake bugowa' ki gaida maigidanki. "Aisha tace zaiji. "snn sukai sallama. "tun daga lokacin safe da yamma sai Nasir ya wanke wa Aisha kurajan' koda ba'ita keda girki ba sai ya tsaya ya wanka mata snn ya tafi g'idan Fatima. "Cikin hukuncin ubangiji Aisha tasamu sauki sosae kamar ba'ita ba' ummata kuwa tun daga narar da tasan Aisha batada lfy kullum sai takirata dan jin yadda jikin yake. "bayan Nasir yazo ya duba Aisha da yake yau ba'a g'idan ta yake ba' bayan ya dubata ne yatafi aiki sai ga bilyaminu da sako rigi-rigi kayane iri-iri ya dunga shigowa dasu' bayan ya gamane yace maigidane yace nakawo maki. "Aisha tace to nagode. "bayan bilyaminu ya fita Aisha ta kwashe kayan ta kai dakinta' da yamma lokacin Nasir yataso daga aiki yabiyo g'idan Aisha ' da sallamarsa yashigo rike da yar' karamar kit a hannunsa. "Da sauri Aisha taje ta amsa h'ade da yimasa snn da zuwa' Nasir yace yauwa yan'mata na' lalla kam yau na tabbatar da kinji sauri wanga irin kwalliya h'aka. "Aisha ta kyalkyale da dariya kamo hannunta yai zuwa Cikin bedroom suna shiga bakin gado ya zauna snn yace ta miko masa kit din daya shigo dashi. "bayan ta mika masa har ta mike' yace zo kiga wani abu' dawowa tai ta zauna kusa dashi snn ya bude kit din sarkokine kala2 kamar su DIAMOND DUBAI SAUDI' da mmki Aisha tace Yallabai ina kasamo gwalagwalai haka? "dariya Nasir yai snn yace office din mu aka kawo na siyarwa shine na siye maki' ido 😳 Aisha ta b'ude sbd mmki ita kanta batasan lokacin da tai masa tsanle a jiki ba tana godiya. "shima dariya yai snn yace akwai kaya nabawa bilyaminu yakawo' Aisha tace ai yakawo' Nasir yace suna duk nakine' zansamo tela da zai dinka makisu. "Aisha tace haba Yallabai ai sumin yawa yaya zanyi dasu h'aka? Sun fifa ishirin. "Nasir yace ina sane da yawansu ai. "sbd murna Aisha har da kukanta. "Nasir ya jawo ledar dake gefensa kayane kala2 English wears ne a cikin ledar h'ade da su jallabiyoyi' yace idan zaki dinka kayan ban hanakiba amma inda zakibi tawa nafiso kananun shiga' shiyasa ma nasiyo maki su. "Nasir tace babu damuwa yadda kace haka za'a. "Nasir ya mike yace ni zantafi kada tace nazo nai wani abune anan kinsan halinku mata da zargi. "dariya Aisha tai masa snn sukai sallama yatafi' bayan fitarsa tai masa rakiya ta dawo daki zamane tai dirshan a gaban kayan tafara budewa daya bayan daya tana kallo zannuwane masu rai da motsi kamar su super wax holan english swess lace E. T. C.. "Snn ta dauko kit din sarkokin tafara dubawa shima daya bayan daya mai kasamin kudin a ciki shine ta five hudren thousand a ciki' haka ta dunga dubawa tanawa ubangiji godiya. "a zuwaiyarta tace Allah sarki ummata inama da gari daya muke' ko kuma inada dan aike' himmm kawai tace a fili. HUMM' HIMM WASA FARIN GIRKI 🤔 ALLAH YA KYAUTA. MUJE ZUWA' GARIN BABU NISA IN DA RAI KASHA KALLO. TAKU HAR KULLUM MOM USWAN CE 😅🤝 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W☘ MMN USWAN 0⃣7⃣ "Kwashe kayan Aisha tai ta zuba a cikin wadrp ta rufe'. "washe gari dayake alhj yau a g'idan ta yake' duk da besamu zuwa da safe ya dubata ba bata nuna damuwar hakan ba tunda tasan a g'idan ta zai kwana. "tun azahar tafara aikin abinci lafiyayyar tuwon shinkafa da vegetable soup snn ta hada masa juice din sobo tasa a cikin frg dan yai sanyi kafin Yallabai ya dawo daga aiki. "kayan abinci kuwa kwashesu tai ta jere a dinning snn ta shiga wanka' tana gama wanka tai alwala daga nan tazo tai sallah snn tai kwalliyarta sbd tasan sai Yallabai yaje g'idan Fatima ya sallameta kafin yazo g'idan ta. "Duk ranar da bakai ne da girki ba yana tashi a aiki saiya biya ya sallameka snn ya wuce g'idan da yake' hakan yabawa Aisha daman samu lokaci bayan ta'idar da sallah daga parlour har cikin dakunan da suke g'idan tafeshesu da room freshinal snn ta kunna turaren wuta. "Shiko jikinta haka tabi kowani gabobi ta shafeshi da humra ta dindisa kwalliyarta daya daga cikin kayan da jiya ya kawo mata tasa snn ta koma parlour zaman jiransa ya shigo. "Batafi mintoci da zama ba taji gateman yana bude gate' da sauri ta mike da leka ta window gani alhj ne a guje taje ta b'ude kofar parlour ta tsaya jiransa ya kariso dan bazata iya fita farfajiyar gida haka ba. "Nasir yana parking yafito zuwa parlour yana shiga Aisha tai masa tsanle a jiki tana f'adin oyoyo Nasir. "Da mmki alhj ya rike baki 🤔 yace Nasir fa kikace? ". "Aisha tace au afuwan dan Allah subutan bakine. " Nasir yace a'a bakida laifi' girman da kikayine yakawo haka. "Aisha tace ba haka bane. "Nasir yace haka ne mana' ba shiyasa bakiso na kiraki da yan'mata ba. "harara snn tace kasake ko. "yace Eh mana kinga fa duk tsayina amma saida kika kamoni. " Da sauri Aisha tace lahhh!!!! Takalmine fa. "Saida ya leka snn yace ok' to zomuje yan'mata na' Ashe dai baki gama girma ba tunda baki kamoni ba. "Hannu yasa ya jawota jikinshi ya rungumeta suka karisa cikin daki' bayan ta taimaka masa ya tube ya shiga wanka bayan ta cire masa jallabiyarsa ta'ije masa akan gado parlour ta komawa ta zauna zaman jiransa. "Yana gama wanka yafito parlour ya zauna snn yace yan'mata daukomin abinci na' Aisha tace ga dinning' yace a'a yau a nan zanci. "Mikewa tai taje ta dauko masa takawo ta eje a gabansa'itama zama tai tana zuba masa a plate h'ade da sobo a cup. "Nasir yana ci suna hira a cewarsa wai tatsuniya yake mata' itako Aisha sai faman dariya takeyi' har yakusa karewa sai Aisha taji wayarta na ringing da sauri ta mike zuba duba mai kiran. "Tana mikewa Yallabai yana binta da kallo' har tayi nisa can Yallabai ya hango kamar jini a bayan riganta' da sauri yace Aisha. "juyowa tai h'ade da cewa na'am. "yace zo nan. "Dawowa tai gun sa. "Cire hannu yai daga cikin abincin yasa a cikin roban da yake gefe ta wanke snn ya kamota ya juyata h'ade da kamo riganta yana dubawa' da sauri Aisha tace lfy? "Nasir yace kamar jini na gani. "Aisha tace jini kuma? "Koda Nasir ya duba jini ne abinsa' da yaga h'aka janta yai zuwa bedroom' Shinfidata yai akan gado' gani h'aka Aisha tace lfy? Me zakaimin? "Nasir be tanka mata ba' cire mata gajeran wandon dake jikinta yai snn ya dibo tissue ya tura a gabansa'itama koda ya ciro jini ya gani sosae a cikin tissue din. "Yana gani h'aka dagota yai h'ade da dauko mata zani da hijab yace tashi muje asibiti da sauri' Aisha naso tai mgn amma Nasir be saurareta ba. "Dole h'aka ta bishi sukaje' koda doctor ya dubeta yace cikin yariga ya lallace' yanxu da h'aka taimako daya za'ai mata shine wanki cikin' in ba h'aka ba zai'iya zamo mata matsala. "Nasir yace ok babu damuwa a shirye muke. "Aisha najin h'aka tsanle tai ta sauko daga kan gadon h'ade da sa masu kuka' da sauri Nasir yace Aisha lfy? Cikin kuka Aisha tace wlh babu wani wankin cikin da za'aimin' ni wlh bazan yarda ba. "daga kawai kaga jini sai kace ciki ya lalace ni wlh bazan yarda ba' Aisha kuka take tsakaninta da Allah. "Nasir yana gani h'aka mikewa yai daga kujeran da yake zaune ya kamota yace Aisha dan Allah kibari ayi maki wanga wankin ciki' tunda har kinji doctor yariga ya f'adi haka shikadai yasan abinda ya hango. "Aisha najin haka tasake rushewa da wani sabon kuka tana cewa ni wlh bazan yarda ba' tunda nake a rayuwata bantaba kwanciyar asibiti ba' shine yau zakace wai za'ai min wani wankin ciki ni wlh bazan yarda ba' f'adi tai a kasa h'ade da sa masu ihu tana f'adin waiyoooo ummata na shiga uku na lalace ummata kizo ki taimakeni. "Gani tanada niyar tara masu juma'a da sauri Nasir yace tashi muje g'ida. "hannu yasa ya dagota suka fita' suna fita doctor kamal ya Kwashe da dariya yana f'adin garin kwashe Kwashe bana kakwasowa kanka irin wanga yarinya h'aka. "Tunda suka fara tafiya Nasir be tanka mata ba har suka isa g'ida' a bakin gado ya zauna' ita k'uma kwanciya tai' Nasir yace Aisha nidai har ga Allah hankalina be kwanta ba' wlh da kin daure kibari a cire wanga ragowar cikin' Aisha tserona dare ko k'uma lokacin da bana gida' Aisha koda ina gida dagani har ke babu wanda yasan kan barin nan. "dan Allah Aisha ki daure muje a cire cikinga' Aisha kuka tasake sawa tana f'adin nidai wlh babu inda zani ko kasheni zakai. "Da sauri Nasir yace a'a kwantar da hankalinki wama zai kasheki. "tun daga snn besake mgn ba' kwanciyar sa kawai yai. 'itama kwanciyar ta tai hakan suka kwanta babu wanda ya tanka ma d'an uwa sa. "Can cikin dare kamar a mafarki Aisha taji cikinta yana juyawa ko kafin ta falka jini ya riga ya bata gado da ihu Aisha ta tashi tashige toilet. "shiga Nasir a guje ya bita' koda ya shiga ganita yai cikin jini kace -kace sai faman xuba yakeyi kamar fanfo' gani haka yasa Nasir daukarta cak ya sata cikin bawon wanka ruwa ya dibo ya wanketa snn ya dauko wani babban towel ya cusa mata a gaba ya dauketa sai asibiti. "ko kafin su'isa Aisha ta riga ta suma' shiyasa har aka kwashe cikin bata sani ba' ko kafin ta falka doctor ya kare. "Doctor yana gamawa yace suje gida' haka Nasir ya dauko ta suka koma g'ida' da safe alhj da kansa ya sanarwa iyayen Aisha umma tai masa Allah ya kyauta ya kuma maida sabon arziki. "yace amin. "tunda daga lokacin kullum umma sai ta bugo su gaisa h'ade da yimata fadan ta rinka sha ruwan zafi. "Da haka Aisha tai ta jinyar jikinta' lokacin kuwa daga g'idan Fatima ake kawu mata' bayan sati daya cikin dare wani jini yasake banlewa kamar da bakin kwarya' haka Nasir yasake medata asibiti koda doctor ya dubata ashe akwai wani gudan jini da befita ba haka yasake kwashe ragowar jini. "gani yadda tai ta suma yasa aka bata gado Nasir shike kwana da'ita asibiti da safe bilyaminu ya kawo masu abin karyawa daga g'idan Fatima' bayan ya'ije ya fita mikewa Nasir yai ya shiga toilet ya dauko kwanu silve yazo ta tare a bakin ta yai mata brosh snn yaje ya xubar yazo ya hada mata tea yace tasha. "Aisha tace bazata iya shaba' babu yadda Nasir beyiba amma Aisha taki sha' haka ya gaji ya kyaleta. "Da rana kuwa Fatima takawo masu abinci ita da yara sukazo gaida ta' suna shiga Nasir da fara'arsa ya amshesu h'ade da bata kujera ta zauna' shikuma yakoma bakin gado ya zauna. "khadijat da jabeer suka duka har kasa suka gaida bbnsu. "Nasir ya amsa' snn suka juya gun Aisha suka gaidata h'ade da tambayar jikinta. "Aisha ta amsa da cewa jiki yai sauki. "sukace Allah ya kara sauki. "Tace amin ngd. "snn suka gaisa da Fatima h'ade da tambayar jikinta. "Tun daga snn Fatima bata sake cewa komai ba ido kawai ta zuba masu sai faman cin cingam takeyi tana kashe kwai Kararas-kas kamar tawa karuwa. "can kuma ko mai ta gani ta mike tacewa yaranta suzo suje gida. "ko sauraran Nasir batayi taja yaranta banle tasan abinda yake fadi tai tafiyarta. "kwanan Aisha biyu suka koma gida' abinka da mara jiki sai takara ramewa sosae sai tsayin. "kafin sati biyu Aisha taji sauki sosae kamar ba'ita ba sai dai ramar da tayi' yau Nasir a g'idan ta yake da safe ya shirya yatafi office sbd har yanxu E. F. C. C. suna bincike a kansa. "Hakan yasashi fita da sassafe' bayan ya fitane Aisha ta kwashe kayan daya bata ta kai kitcher taje ta gyara parlour snn takoma bedroom ta gyara sai da ta gama gyara ko'ina snn tashiga wanka. "kafin ta fito taji motsin anyi parking din mota da alama kuma Nasir ne yadawo' amma kuma lokacin Dawowarsa beyiba sbd yanxu karfe gomane. "hakan yasa tai saurin wanke sabulum dake jikinta towel kawai ta daura h'ade da sa hijab tafito parlour dan gani ko waya. "tana isa parlour motar Nasir ta hango a gefe kuma bashi a parlour a take taji gabanta yai mummunar fadi. '"juyawa tai tanufi dakinsa' koda taje tana knocking Nasir yana jinta amma yaki bude kofar' Aisha tai knocking har tagaji amma Nasir be bude ba' gani haka yasa ta fasa da kuka h'ade da kiran sunansa. "jin kukanta ne yasa Nasir bude kofar tashiga cikin dakin' suna hada ido taga gaba daya ido sa yai jazir kamar garwashin wuta. "Sake fashewa tai da kuka' shima Nasir kuka yakeyi' Aisha tana fadin dan Allah Nasir ka fadimin menene ke faruwa. "shima zama yai dirshin a gabanta yaci gaba da kuka' gani bashida niyar fadi mata yasa Aisha kwanciya akan carpet tana birgima. "Hannu Nasir yasa ya dagota ta zauna a gabansa snn yace Aisha' kinaso kisan abinda ke faruwane? Yace to zan fadi maki amma sai kimin alkairi nasan zanrasa komai a rayuwata amma inaso ki zamomi daya daga cikin abinda bazan rasaba. "Cikin kuka tace insha Allahu nayi maka alkairin hakan. "Snn yace Aisha E. F. C. C. sunyi bincike a ministry namu ana zargina da haddame kudi ta biliyoyin naira wanda nima kaina bansan iya adadinsu ba' yanxu da haka Aisha nimana sukeyi su kamani. "babu abinda yake fitowa daga bakin Aisha sai innalailahi'wainna'ilaihim'raju'un. "Nasir yace Aisha ba taba lokaci zamuyiba ki tashi nasa bilyaminu ya medaki garin kuma nima barin garin zanyi. "Cikin kuka Aisha tace babu inda zani sai dai mutafi tare dakai. "Nasir yace a'a Aisha. "ihu Aisha tasa ta fada masa a jiki tana fadin Nasir wlh bazan iya rabuwa dakai ba sai dai mutuwa. "Nasir yace a'a Aisha. "Itama Aisha tace a'a Nasir TOFA KUBIYONI KUJI YADDA ZATA KAYA TSAKANI NASIR DA AISHA 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W ☘ MMN USWAN I'm wait 4 ur cmm 👆 Hafsat Hausa Novel H2 fcbk A Gaskiya bani da bakin godiya a gareku sai dai Allah ya bar kauna sbd nvl din na idan bakuzo na daya ba to ko zakuzo ba biyu dan haka Allah yabar kauna da zumunci amin. 0⃣8⃣ "Nasir yace Aisha inaso ki saurareni d'kyau wlh Aisha bazan iya barinki a garin nan ba. "Aisha baki da kowa saini' ni k'uma yanxu da h'aka da kike gani barin garin zanyi Aisha k'uma kinga be kamata natafi na barki a garin da bakisan kowa ba' shiyasa nace kibi bilyaminu ya medaki gun yar'uwanki. "Insha Allahu idan komai ya lafa zanzo da kaina na daukoki mudawo' kinji Aisha. "Aisha dake kwance jikinsa tasake fasawa da kuka tana fadin wlh babu inda zani. "Nasir yace a'a Aisha katafi kawai. "Aisha tace nifa na fadi maka. "yace wlh Aisha nima na sukeyi ido rufe sutafi dani' idan har sukasan ina nan g'idan wlh zuwa zasuyi su tafi dani' shiyasa nakeso kibar nan kafin suzo kamani. "kuka Aisha tasa tana cewa wlh sai dai su kamamu tare dakai amma bazan iya tafiya na barka cikin irin wanga halinba. "Cikin fushi Nasir ya egijeta gefe ya mike h'ade da cewa ke wacce yarinya ce me shegen nacin tsoya' meyasa abinda nake duba maki baki dubawa kanki ne. "Ana guje maki wahala baki guje wa kanki. "Idan har suka kamani kikasan iya adadin shekarun da zanyi a prision tunda ni dai a yanxu da haka har ga Allah banida kudin da zanbiyasu' ba kudi bama ko duk abinda na mallaka a duniyar nan ne zasu kwashe wlh bazai biya kudin da suke tuhumana ba. "Amma tunda kince nacine dake' k'uma ban'isa dake ba ni kinga tafiyata. "Da sauri Aisha ta mike tana kallon Nasir' gani yasa kai be saurareta ba yai tafiyarsa babu ko waige. "ihu Aisha tasa tana kiran ummata a guje tabi Nasir tasha gabansa h'ade da kankameshi taci gaba da kiran umma' hannu daya Nasir yasa ya fisgota daga jukinshi ya hurgata a tsakar parlour yaci gaba da tafiyarsa. "Buguwar da Aisha tai da cushion yasa takasa kuka sai faman shure-shure takeyi da kafa. "Har Nasir yakai bakin gate ko me yatuno kuma oho yasashi komawa da baya yashiga cikin parlour yadda yabarta haka yadawo ya sameta a gun kwance' hannu Nasir yasa ya dagota snn yace Aisha' Aisha daga ido tai tana kallonsa. "Nasir yace kin amince zaki zauna dani a h'aka? Kai kawai Aisha ta daga masa' Nasir yace banida komai da kika sani a dah' Aisha da h'aka zaki zauna dani? "Aisha tace eh' zan zauna. "Nasir yace a'a fa Aisha ' kinga kinada ragowar kuruciyarki' be kamata na tauye maki hakkinki ba' a matsayinki ta yarinya mai kuruciya da jini a jika' ina tabbatar maki idan har kika rabu dani zaki iya samu wanda yafini Aisha. "Cikin kuka Aisha tace a'a ni ina sonka a haka' k'uma zan'iya zama dakai koda kafi haka ne talaucewa. "ido kawai Nasir ya zuba mata yana kallonta har takare' Bayan ta karene Nasir yasa hannu ya jawota jikinsa snn yace Aisha nagode da Allah ya azirtani da mace tagari irinki Allah yai maki albarka' yanxu kinga babu lokaci zomuje ciki duk wani acceses da kikasan nakine kikwaso mutafi. "Aisha tace ina zamu? Nasir yace g'idan Fatima ne zankaiki ku zauna tare' ni kuma zan kauce zuwa wani lokaci' ko bazaki zauna da'ita ba. "Aisha tace zan zauna amma dan Allah koda cikin dare ne kadan rinka lekowa kana dubamu kaji". "Nasir yace naji Aisha ai dama bazan barku haka kawai ba ' idan banzo dan kuba ai zanzo dan yarana. "Aisha tace to shikenan' tare suka kwashe kayan' gaba daya zibarenta ya kwashe mata da kayan sawarta ya zuba cikin wata karamar kit snn kaya kuma cikin karamar jaka ya zuba mata yaja zip ya rufe' hijab kawai ta dauka shikuma yana rike da jakar sukabar g'idan. "Lungu Nasir ya dunga bida Aisha har sukabar cikin gari snn ya yanka ta daji' sakamako tsakani g'idan Fatima da Aisha akwai tazara sosae' hakan yasa Aisha tai tafiya har tagari amma da haka sukai ta tafiya har sukakai g'idan Fatima. "Gani sun shigo Nasir na gaba Aisha na baya yasata cewa har abu yazo amma dai anji kunya' Nasir najinta amma be tanka mata ba' kai tsaye dakinshi ya kaita' bayan su shigane Nasir yace Aisha ga dakin da zaki zauna. "Aisha tace to' snn yace zomuje na nuna maki lungu da sakon g'idan ko' to kawai Aisha tace' Nasir na gaba Aisha na baya ya nuna mata ko'ina snn suka koma daki' gani lokacin sallah yayi yasa Aisha cewa bari nayi sallah. "Nasir yace Aisha nima zantafi akwai kayan abinci a kitcher' Aisha ta fasa da kuka h'ade da cewa yanxu ina zaka? Nasir yace nima bansan inda zanje ba Aisha' amma ina Allah ya yarda koda sau dayane a sati zansan yadda zanyi naxo na ganku. "Ni inda ma zasu kwashe duk wata abinda na mallaka su barni cikin iyalina wlh Aisha yafimin kwanciya hankali. "Aisha naji haka ta fadi kasa taci gaba da kuka. "Fita Nasir yai h'ade da daga mata hannu yana mata bye bye' a guje Aisha ta bishi' gani haka yasashi fita da sauri h'ade da jan kofar ya rufeta a ciki. "Fadi a kasa Aisha tai taci gaba da kuka. "Nasir na fita daga dakin Aisha sukai karo da Fatima tace an dai ji kunya wlh' Nasir najin haka ya daure fuska snn yace Allah yasa dai kinsan ko ni waye' idan na kara jin bakinki wlh saina kwantar dake a nan. "Fatima najin haka bata sake cewa komai ba' Nasir ya shige gaba h'ade da cewa zaki biyoni daki muyi mgn ko yaya? "Batare da ta tanka masa ta bishi' sun kusan minti talatin a ciki snn yafito yai tafiyarsa. "Itako Aisha da tai kukanta ta gaji tashi tai taje tai alwala tazo tafara sallah. "Da yamma Aisha ta fito zata shiga kitcher dan girki' da sauri Fatima tace me zakiyi? Aisha tace abinci ne nakeso na dora. "Fatima tace ba haka mukai da maigidanba' cewa yai idan nadafa na rinka sa maki iya bakinki' tunda ba dan kowa ne dake ba. "Aisha tace shine yace maki haka? "Bazan Fatima tai da'ita. "har Aisha ta juya zata koma d'aki sai Fatima tace akwai abinci ki a kalla yana kitcher' k'uma idan kika cinye ke kika sani sbd harda na dare nayi' sbd ke bazansa wani sanwa a g'idan nan ba. "batare da ta tanka mata ba shiga kitcher din tai taje ta dauko abincin tana tafe tana hawaye ta shige d'akinta. "Tana shiga eje abincin tai a gabanta ta dauko wayarta d'an kiran Nasir' sai dai kasa!!! Koda tai trying sai tajishi swech off. "medawa tai ta eje shi a gefe taci gaba da kukanta. "washe gari da safe Fatima ta aiki yara sukai wa Aisha abin karyawa' na rana kuwa cewa tai harda na yamma ta hada' dan haka idan ta cinye to harda na darenta kenan. "Aisha tace to. "Da haka Aisha taci gaba da rayuwa a g'idan Nasir bata kula Fatima sbd damuwar rashin mijinta ma kawai ya'isheta' kuka kuwa dashi take kwana take tashi' shiyasa tabi tai rama sosae sbd yadda tasa damuwa a ranta' ba kamar Fatima ba' duk da yaran dake tsakani su amma ko'a jikinta. "Bayan sati biyu cikin dare misalin karfe biyu saiga Nasir yashigo kai tsaye dakin Fatima ya shiga duk da tana gani dhigowarsa amma tai banza dashi kamar bata ganshiba. "Nasir yai mgn har yagaji amma Fatima bata tanka masa ba' gani haka yasashi fita daga dakin ya koma d'akin Aisha' sallamar da Nasir zaiyi sai kunni Aisha' a birkice ta tashi' gani Nasir ne a guje taje ta rungumeshi h'ade da fashewa da kuka. "Gani irin kukan da takeyi yasa Nasir daukarta kamar karamar yarinya har kan gado ya kaita snn yafara lallashinta. "Cikin kuka Aisha tace ina ka shigane nake nimarka a waya amma baya shiga? Nasir yace eh ga wayar nan' hannu yasa a aljihu ya fito mata dashi ya nuna mata snn yace na kashene sbd kada su nimeni ta waya su sameni. "Shiru Aisha tai tana jikinsa. "Nasir yace Aisha ba komai ne ya kawoni cikin dare ga illa na sheda maku naji labarin gobe zasuzo bincike a g'idan nan' sbd duk abinda kika sani na wancan g'idan sun kwashe. "Aisha tace Innalillahi'wainna'ilaihim'rahu'un' Allah umma ajirni fi musibati wa akhlifni khairan. "Yanxu yaya zamuyi? Nasir yace wlh nima Aisha bansan yadda zaiyi ba' shiyasa ma naxo na sanar daku duk wasu abubu naku masu mahimmaci ku boye. "Aisha tace toni ina ne zankai sarkokin da kasiyemi? Nasir yace kefa macece kiyi dabaran nan naku na mata mana. "Aisha tace a'a bari na baka katafi dasu ka boyemin kawai a inda kake idan komai ya lafa saika kawomi. "Nasir yace a'a Aisha. "Aisha tace katafi dasu kawai. "Sai da yai shiru na dan mintoci snn yace to Aisha. "Aisha na makale jikin Nasir har karfe bayan asuba' gani biyar tayi da sauri ya mike yaje yai wanka yadawo ya meda kayan jikinsa Aisha ta mike ta dauko sarkokin ta bashi' har Nasir yakai bakin kofa sai Aisha tabiyoshi snn take sanar dashi yadda sukai da Fatima akan mgnr girki. "Nasir yace eh shine yace kada tai abinci da kanta sai dai ayi a bata sbd aikin g'idan da yawa ba lallane ta'iya ba' shikuma bayaso ta wahala. "Shiru Aisha tai. "Nasir yace ni zantafi saina sake dawowa. "Aisha tace to shikenan' komawa tai ta shiga toilet tai wanka h'ade da alwala tazo ta fara sallah. "Nasir yana fita dakin Fatima ya shiga ya sameta zaune akan sallaya tana lazumi' duk da shigowar da taga yayi besa ta yanke ba cin gaba da lazuminta tai. "gani h'aka Nasir yace ni dai zantafi Fatima' a lokacin ne ta shafe addu'a snn tace yanxu dan Allah alhj abinda kakeyi ya dace kenan? girma fa kakeyi ba komawa baya ba' k'uma abinda kake aikatawa baka tsoron wataran a aikatawa yar'uwa? "Nasir yace Fatima kenan yanxu sbd Allah me k'uma na aikata? ke kullum baki rabuwa da zargi' idan kina tunanin wani abu na kawo mata wlh ina shiga g'idan nan d'akin kine na fara shiga snn naje d'akin ta.... "shigawar yarane yasa takasa meda masa mgn' rungumeshi sukeyi suna baba oyoyo baba' baba ina katafi bamu ganka ba bb? "murmushi Nasir yai snn yace doughter kenan wani aiyukane suka shami kai amma in Allah ya yarda nakusa kammalawa ina kammalawa zandawo mu zauna tare kinji ko... "kafin ta b'ude baki tai mgn Fatima tace ke fita kinaba gun. "Nasir yace nima tafiya ne zanyi saena sake dawowa. "Banza dashi Fatima ta mike h'ade da tada kabbarar sallah taci gaba da sallarta' shima dayaga h'aka fita yai yai tafiyarsa. "Itako Aisha tana idar da sallah alkur'ani ta dauko tafara karantawa' saida ta dade tana karantawa snn ta'eje tafara kwararowa mijinta addu'a h'ade da iyayenta snn ta shafe addu'a komawa tai gado ta kwanta amma ba bcc takeyi ba. "Tunanin iyayenta ne ya f'ado mata a zuciya'ita kanta batasan lokacin da tasaki wani kuka ba' cikin kukan ta dauko wayarta ta duba ko akwai kudi a ciki' tana duba gani tai babu ko sisi' medawa tai ta eje kai da gwiwa ta h'aka taci gaba da kuka. "Misalin 10AM Fatima na zaune a parlour taji shigowar mutani g'idan' da sauri ta mike d'an mekawa taga ko su waye. "Tana lekawa wasu mutani ta gani turkaka duk mazaje ne su biyar' salati tai ta sanarwa ubangiji' kafin tarufe baki har su shigo cikin g'idan. "Titsiye Fatima sukai a parlour h'ade da tambayar ina maigidanki? Cikin rawar jiki Fatima tace bayanan. "Daya daga cikin su yace ina d'akin sa yake? Da hannu Fatima ta nuna masu' sukace da'ita muje' suna gaba tana baya suka shiga d'akin' suyi bincike iya bincikensu amma basuga komai ba' sukace muje naki d'akin a nan ne sukaga sarkokin zinare da sauran kaddarorin da baza'a rasa ba. "bayan sun gama kwashewa suka koma d'akin Aisha' Aisha na gani sun shigo tace innalallahi'wainna'ilaihim'rahu'un' snn tace daga ina k'uma? ID Card d'an E. F. C. C. Suka nuna mata daga snn bata sake cewa komai ba. "Suma suka fara seaching d'akin a d'akin ta kam basu sami komai ba' sbd tariga tabawa Nasir ya wuce dasu' sunyi bincike iya bincikensu amma basuga komai ba' ita ko Aisha tana gefe inba kuka ba babu abinda takeyi' Gani basuga abinda suke bukata ba yasasu fita subar g'idan. "Suna fita Aisha ta fashe da kuka sbd yadda suka walakanta mata d'aki' itako Fatima bala'i tasa tana f'adin wlh sisi bazaiyi ciwon kai ba' idan sai anbiyani. "Su iyayen sai faman nimanta sukeyi amma basu samuta k'uma koda sun kira wayar maigidanta shima baya shiga h'akan yasa hankalinsu ya tashi sosae' amma sai bbnta yace tunda anji shiru lfy ne' sbd lfy ne ke buya inda ba lfy da tuni anji. "umma tace h'aka ne alhj' Allah ya tsare ita a duk inda take' alhj yace amin' komai menene tunda AURE NE insha Allahu bazata tagaiyara ba ' himm kawai umma tace. "Bayan zuwan E. F. C. C. g'idan Nasir da sati daya misalin 12AM dai dai sai gashi ya shigo kamar daga sama' komada ya tabi kofa yaji a kulle yake gam da key'gani h'aka sai ya zaga ta dai dai window Fatima yana kwada mata kira' a gigice ta falka' jin muryar Nasir yasa taja dogon tsuki ta koma ta kwata taci gaba da bccn ta. "Gani h'aka yasashi komawa gun window Aisha kira daya ta mike Nasir yace nine Aisha da sauri ta mike taje ta b'ude masa kofa ya shigo cikin d'aki' bayan ya zauna ne ta b'ude frg ta dauko ruwa ta bashi h'ade da cup' koda ta xuba masa ruwan a cup k'adin kawai yasha snn ya'ije cup din. "Har kasa Aisha ta duka ta gaidashi' amsawa yai babu yabo babu fallasa snn ta zauna' karewa d'akin kallo yai snn yace ya naga d'akin kamar a birkice. "A lokacin ne Aisha ta sanar dashi mutani da sukazo bincike' Nasir yace nasan za'ayi h'aka amma ni dai banida abinda zance sai Allah ya kyauta. "Aisha tace amin' ni inda zasu kwashe komai su barmin kai wlh zanfi kowa murnar h'aka amma sbd Allah wanga wacce irin rayuwane h'aka' mutum da g'idan sa da iyalinsa amma ya gagaresa zama. "murmushin yake yai h'ade da cewa Aisha har yanxu ke yarinya ce' ko zan kwana ina maki bayani ba lallane ki gani ba' amma Allah ya naganki wani iri kodai bakijin dadin zama da Fatima ne? Ko k'uma wani abu take maki. "Aisha na hawaye tace babu komai'kewarka kawai ke damuna'da k'uma kewar su yar'uwa na. "Nasir yace shiyasa nace bilyaminu ya medaki garinku idan komai ya lafa ni da kaina zanzo na daukeki. "Da sauri Aisha tace a'a ni babu inda zani na barka' ni nafiso na zauna dakai' Nasir yace to ai yanxu ba tare muke ba' sai lokacin dana samu hanya nake zuwa inda kike' Aisha tace eh na yarda a h'aka inda har zaka rinka zuwa lokaci - lokaci ina ganika. "Shiru Nasir yai na dan wani lokaci snn yace Aisha kina sona? "Kai kawai ta daga masa alamar eh. "Nasir yace gobe duk yadda zanyi sai nayi na nimi kudin mota da zai kaiki garinku' ki shirya kayanki da safe cikin dare daidai wanga lokacin zanzo na daukeki mutafi na saki a mota kafin safe insha Allahu nasan kin isa garinku. "A sbd yasa zansaki a motar haya sbd duk wasu yaran aikina da kika sani yanxu da h'aka babu kowa' kowa ya kama kansa sbd nima yanxu da haka ta kaina nake dan mafaka nake nima. "shiyasa zan saki a motar haya ki tafi gida..... "Cikin kuka Aisha tace ni babu inda zani' zan zauna a h'aka idan har zaka rinka lekowa ina ganika. "Gani irin kukan da takeyi yasa Nasir dagota yai ta zauna akan cinyarsa snn yace waya kukan ya'isa h'aka banaso na sake gani wanga hawayen' hannu yasa ya share mata tass snn yaci gaba da cewa yanxu Aisha kin zabi ki zauna h'aka? Aisha baki tausayamin kada hakki yai min yawa Aisha. "Aisha manna kai tai a kirjunsa tana ejiyar zuciya' shima rungumeta yai a jikinsa kamar yaramar yarinya' snn yaci gaba da cewa ni dama ba wani abu nake dubawa ba illa zamanki ke kadai gani nai kamar baki saki jiki a g'idan nan bane shiyasa' duk da nasan ko waye Fatima bazata cutar dake ba' amma kinsan halinku mata banlema ace kishiya dole wataran sai a hankali' k'uma kinga ba zaune nake a cikin ku ba banle idan naga wani abu zai shiga tsakaninku na kwaba yanxu duk da haka kin amince zaki zauna? "Aisha tace eh. "Nasir yace to shikenan' da haka ya lallaba yai ta bayan bukatarsa. "itako Fatima gani 2AM yayi mikewa tai taje tai alwala tazo tafara jera nafiffilinta kamar yadda tasaba. "Nasir yana tare da Aisha gani 4AM ya mike h'ade da dauko towel ya daura yashige wanka' bayan ya fitone yana meda wandosa ya mika mata towel din ta daura snn tashiga wanka. "bayan ta fitone daga wanka ne tasa kayanta Nasir yace Aisha ni zantafi' shiru Aisha tai kanta na kasa' sbd tanaso ta tambayesa amma kuma takasa' Nasir yace yan'mata na yah! dai? "A sanyaye Aisha tace dan Allah kanada dari biyu kabani? Nasir yace Aisha me zakiyi dashi? Aisha tace ummata nakeso na kira sbd munyi kwana biyu bamuyi waya dasu ba. "Nasir yace Ayya wlh gashi dagani sai naira dari k'uma idan nabar nan bayanki dashine zanyi amfani na hau napep na karisa' Aisha tace dan Allah Yallabai ina kasamu gun fakewa? Murmushi kawai Nasir snn yace kada kisamu yan'mata na kimin ko. "yanxu ga darin idan yaso ni saina hakura' da sauri Aisha tace a'a katafi dashi kawai ni na hakura. "Nasir yace Allah kuwa ki karba' sbd bansan mgnr da kikeso kuyi dasu ba. "Tace a'a ba komai bane dama gaisawane kawai zamuyi dasu' tunda hakane babu damuwa wani lokaci sai muyi. "Nasir yace to shikenan Aisha nagode Allah yai maki albarka yasa kici gaba da wanga hali naki ta gari. "Murmushi kawai Aisha tai masa' Nasir yace ni zantafi saina sake dawowa. "Aisha tace Allah ya tsareka ya kareka aduk inda kake. "Nasir yace amin mugode snn yafita d'akin Fatima yaje koda yashiga ganita yai tana sallah ' hakan yasa betsaya bata lokaci ba yai tafi yarda' har yakai bakin kofar parlour zai fita saiga Fatima tasha gaba na h'ade da hankadeshi ya koma da baya. "Nasir yace Fatima menene h'aka k'uma? Fatima tace ina sarkokina da katuro aka amsawa? Da mmki Nasir yace sarkoki k'uma Fatima wasu sarkoki kike mgn akai? Fatima tace kafi kowa sani' kuma wlh bari kaji sisina bazaiyi ciwon kai ba' tunda ba kai kasiyemin ba ubana ne yasiyemin' idan haka kafitomi dasu kawai. "Nasir yace Fatima kanki daya kowa? "cikin tsawa Fatima tace kaina biyu ne ba daya ba. "Nasir yace ubanwa kike ma tsawa? Wlh idan kikai wasa saina maki dukan masifa kafin nabar g'idan nan. "Fatima tace bance bazan dukuba amma wlh in har kadukeni saina rama' Nasir yace ok ba kinada karfi ba? "Fatima tace kada ban'iya ramawa da kaina ba wlh sai kudina ya ciremin ta kaici' domin wlh biya zanyi a ramami. "Nasir yace ok bari na dukekidin k'uma kafin nabar g'idan nan inaso naga wanda zasu rama maki. " Fatima tace bismillah... "kafin ta karisa Nasir ya dauketa da mari wanda yasa ta f'adi' kafin ta dago yasake kai mata wani' ihu Fatima tasa h'ade da kukan kura ta shakeshi. "Gani h'aka yasa yaci gaba da dukanta harda tokari' jin hayaniya yaki karewa yasa Aisha fitowa daga dakinta' gani halin da suke ciki yasa Aisha fashewa da kuka. "Duk uban dukan da Nasir kewa Aisha besa ta karaya ba' Yana kai mata kafin ya sauke take ramawa' da Nasir yaga haka wani irin nushi ya kaimata h'ade da shaketa a bango. "Ihu Aisha tasa h'ade da tafiya ta shiga tsakiyatsu tana kokarin cire masa hannu ya wiyar Fatima' cikin fushi Nasir yace Aisha ta tashi a gun Aisha taki. "Hannu daya Nasir yasa ya fisgo Aisha yai hurgi da'ita akan cushion din dake parlour. "A guje Aisha ta tashi tasake zuwa gusa taci gaba da kokarin cire masa hannu a wiyar Fatima' sbd shakar da yaiwa Fatima zata iya suma koma tarasa ranta. "Gani haka yasa yai hurgi da Fatima yakoma kan Aisha' itama ya hauta da duka kamar mahaukaci' Aisha sai faman ihu takeyi' amma besa Nasir ya kyaleta ba' gudu kada ya cutar da yar ' mutani da yawa yasa Fatima ta rarrafo tazo ta haye jikin Aisha dukan yakoma sauka a kanta. "Aisha zare jikinta tai a guje tashige dakinta h'ade da rufe kofar da key' kan gado ta fada tasa kuka. "Gani yara sun fito gada dakinsu ne suna kuka sukayo kan mmsu yasa Nasir egijeta h'ade da tokari snn yafita. "Fatima na nishi tace Allah ya'isa ban yafe ba' mugu kawai. "suma yara zuba sukai a jikin mmsu suna kuka. GA TAMBAYA KUMA A GUNKU NAKE BUKATAR AMSAR READERS 1 Duk wanda yasan doka kuma yasan me ake kira gamnati kuma yasan menene E. F. C. C ta yaya za'ace suna nimanka har kazo gida ka kwana ka kuma biya bukatarka da matarka hankalinka kwance? 2 Duk mutani da akace ana nimansa ina yakeda lokacin tsayuwa fada da matarka???? Amsa tana gareku saina jiku READERS TAKU HAR KULLUM MOM USWAN 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W. ☘. MMN USWAN 0⃣9⃣ "Gani irin kukan da sukeyi yasa Fatima tsaida nata kuka ta koma lallashinsu. "mikewa tai ta rike masu hannu sukai d'akainta. "Itako Aisha gani irin dukan da Nasir yaiwa Fatima da sabadiyar haka itama ta sami nata' yasata tsorata tai data sani rashin tafiya garinsu da batai ba' kamar yadda ya umarceta da taje. "Zama tai taci kukanta har ta gode Allah' dan kanta tai shiru sbd babu me lallashinta. "Gani har gama yayi Fatima bataji motsin Aisha ba yasa Fatima bin Aisha har d'akainta' da sallama tashi d'akin' Aisha na zaune a bakin gado ta amsa da shigo anty. "Fatima na shiga a bakin gado ta zauna' Aisha tace ina kwana anty' Fatima tace lfy klau Aisha ' Fatima taci gaba da cewa dama dana zuwa nai na baki hakuri akan abinda ya faru dazu da asuba' Aisha tace babu komai anty' snn tace dan Allah anty na tambayeki mana. "Fatima tace Allah yasa nasani. "Aisha tace dama h'aka alhj yake dukan matarsa h'aka? "murmushi Fatima tai snn tace a'a wanga ma bacin ranane' amma ba h'aka yake ba. "himm kawai Aisha tace. "Gani h'aka yasa Fatima dafa kafadan Aisha snn tace Aisha ki yarda dani duk abinda zanyi bazan cutar dake ba' sbd na daukeki tamkar yar'dana haifane. "Aisha kinga yarinya nan ko bayan rai nane bazanso ta auri namijin da zai cutar da'ita ba' shiyasa na daukar wa kaina alkairin duk matar da Nasir zai kawo g'idan nan insha Allahu bazan cutar da'ita sbd nima inaso yarinyata Allah ya bata sbokin zama na gari. "Cikin kuka Aisha tace nagode' amma dan Allah ku daina irin wanga fadan h'aka dan Allah. "murmushi Fatima tai snn tace menene Aisha? "Aisha tace wlh har kunsa tsoro ya kamani' dariya ne Fatima tai sosae snn tace Aisha ke yarinyace shiyasa. "mikewa tai h'ade da cewa zomuje ki karya' tare suka fita zuwa kitcher Fatima da kanta ta dibawa Aisha abin karyawa tabata' hannu bibbiyu Aisha tasa hannu ta amsa h'ade da godiya. "D'akainta ta koma ta zauna zubawa abincin ido tai tana kallon abincin tunani kala2 takeyi a zuciyarta. "Tunda Nasir yabar gida yau tsawon satinsa biyu kenan amma be likitan Aisha tai nimansa ta waya har tagaji wayar a kashe yake' h'akan yasa Aisha kuka kullum dashi take kwana take tashi. "Wani tunani yazo mata tace kodai naje na tambayi anty ne ko ita tana samunsa a waya' wani zuciya tace me zaisa kije ki tambayeta bayan kina gani irin rabuwar da sukai... "Tana cikin irin wanga tunani - tunani kenan taji ana knocking da sauri ta mike taje ta b'ude kofar yarinya ta gani tace Aisha tace ubaida lfy? "Ubaida tace mamy ne tace kizo kici abinci. "Tare suka tafi zuwa dinning' Fatima tace Aisha ta zuba masu' Aisha tace to anty. "Mikewa tai ta zuba masu snn ta zauna suka fara ci' suna ci suna hira' khadijat tace mamy' Fatima tace na'am ubaida' khadijat tace wanga ma anty mune? "Fatima tace eh' itama anty kune' k'uma daga yau sunanta anty. "Khadijat tace to shikenan mamy' kani khadijat dake gefe yace yaya kullum kullum sai dady ya kawo mana sabuwar anty ko? "Jabeer ya karisa mgnr ne da kallon khadijat. "khadijat tace kai dan Allah kai wawane wayan nan ba dady ya koresu ba. "A gigice Aisha ta yarda spoon din dake hannu ta. "Gani h'aka yasa Fatima ta daka masu tsawa. "mikewa Aisha tai da sauri ta koma d'aki' gani h'aka yasa Fatima mikewa ta bata d'akin' tana shiga gani Aisha tai ta zabga uban tagumi. "Fatima tace Aisha lfy? Aisha tace anty dama alhj yana auri sakine? Da sauri Fatima tace me kika gani? Aisha tace mgnr dasu khadijat ne sukai yasa nai zargin h'aka. "Fatima tace a'a duk mgnr yarane' idan ma yanayi ina ruwanki' shifa na mijine yanada ikon auren mata hudu idan h'aka ni banga abin damuwa ba. "uhm kawai Aisha tace. "Fatima tace dan Allah Aisha kada ki damu kinji' wlh duk mgnr yarane. "Aisha tace babu komai anty nagode. "mikewa Fatima tai ta koma ta sami su khadijat da Jabeer f'ada ne tai masu sosae' h'ade da jan kunni akan surutu. "Da yamma Aisha tazo ta sami Fatima a kitcher tana aikin abinci' Aisha tace anty wani aikine zantayaki? Fatima tace ki barshi kawai. "Aisha tace Allah kuwa anty. "Fatima tace Allah kije na yafe maki. "Aisha tace to shikenan' komawa daki tai. "Nasir watarsa biyu kenan da barin g'ida ko lekowa bayayi' Aisha tai nimarsa har tagaji' kuka kuwa kusan shine abincinta babu dare babu safe' rama kuwa ba'a mgn koda wanda ya kwanta jinya sai h'aka. "Tabi ta rame ta kara baki' duk wanda ya santa ada ba lalla bane idan ka ganta ka ganeta ba' dama ba kiba ne da'ita ba sai tsayi h'akan yasa takara fitowa doguwarta sabbal. "Can ko gun iyayenta hankalin ummata a tashe yake' sbd munanar mafarkai da takeyi akan Aisha' mafi yawancin idan ta kwanta bcc da dare cikin mafarki take gani Aisha a zaune tana faman kuka' wani lokaci k'uma ganita takeyi cikin duhu mai tsananin baki tana fama ihu' A gigice umma ke tashi h'ade da salati "Tana mikewa toilet take shiga tai alwala tazo ta fara nafila h'ade da addu'ar nima wa ya'ta sauki a duk halin da take cikin. "Gani duk irin nafiffili da sadaka da takeyi besa ta daina gani Aisha a cikin irin wnn halin matsawa alhj bbn Aisha tai akan zataje ta dubo ya'na sbd jikinta yana bata Aisha tana cikin wani hali. "Alhj ya kara ya tsare yace babu inda zata' sbd Aisha ba karamar yarinya bace' k'uma inda babu lfy da maigidanta ya sanarwa ya'uwa' bayan h'aka inda ita Aisha har yanxu tana tare da kuruciya aishi maigidan nata ba yaro bane' dan h'aka babu wanda zaije banlema insha Allahu tananan cikin koshin lfy. "Tunda alhj yace h'aka umma bata sake cew komai ba' mikewa tai taje taci gaba da aikinta. "Alhj yaci gaba da cewa kawai dan anji shiru sai afara wasu irin tunani na banza' to inda daukarta yai sukabar kasan fa yaya zakiyi?banlema kuna kasa daya da ita' kawai dai kila dan wasu uzuzukane sukasha gabansu banlema shi namiji mai iyalai ga k'uma lokaci da Allah ya kawomu. "Duk maganganun da yakeyi umma na jinshi amma bata tanka masa ba har yakare mgnr sa yai shiru. "Gani goma saura yasa umma shigewa d'akainta tai alwala tazo ta fara nafila ta walha. "Sai da Nasir yakai wata hudu currr da rana bayan sallar azahar sai Nasir yai sallama lokacin Aisha tana d'akainta kwance' shima yana shiga g'idan d'akin Fatima ya nufa' itama tana toilet shiyasa batasan shigowarsa ba. "Bakin gado ya samu ya zauna yana jiranta' Fatima na fitowa ta ganshi yadan shingida akan gadon' kamar bazata tanka masa ba' sai dai tace sannu da zuwa. "Nasir ya mike da cewa yauwa uwar g'ida rai g'ida har kin fito? Gani yadda yake mata mgn tasan da bayani' h'akan ya sata daure masa fuska. "Nasir yana gani h'aka ya mike yazo inda take tsaye' hannu ya mika yana kokarin rikota' da sauri taja da baya' gani taja da baya yasashi binta itama bata daina komawa da baya ba har saida takai bango. "Gani takai bango ne yasa Nasir kwashewa da dariya h'ade da sa hannu ya riketa' Fatima tai kokarin tureshi amma takasa' cikin dariya Nasir yace tureni mana idan zaki iya. "Shiru Fatima tai tana kare masa kallo' baki Nasir yakai yana kokarin yimata kiss' da sauri Fatima ta kauda fuskanta' duk da kauda fuskan da tai behana Nasir abinda yai niyaba. "bari tai sai da yai nisa snn ta tureshi zata gudu' hannu yasa ya riketa da karfi yana f'adin h'aka Fatima yau k'uma rowa ne za'aimin h'aba matata ta kaina uwar ya'ya'na abin alfaharina kace jiya k'uma kace yau a kullum jinki nake tamkar buduwa' ke ko budurwanma bazata gwada maki komai ba a guna' daya kike tamkar da duhu. "Murmushi Fatima tai h'ade da cewa a d'adin baki irin taka ba. Nasir yace wlh kuwa Fatima' Fatima kada ki mance irin soyayyar da mukewa juna tun muna yara h'akan ne yasa koda mukayi aure' muka samu matsalar rashin haihuwa babu yadda iyayena basuyi dani ba akan saina kara aure sbd ke baki haihuwa' ni k'uma nakeyi sbd wlh Fatima har gobe bantaba so wata mace a duniya irinki ba. "Fatima ba lallane kisan irin son da nake maki ba' soyayyar da nake makine yasa nabar iyayena nabar yar'uwana na nimi transfer na aiki na dawo nan garin sbd lokacin da muke garinmu gaba daya ya'uwana sukai miti akan idan na fita aiki zasuzo sui maki duka su koreki a cewarsu wai kin mallakeni ni k'uma basusan cewa ba haka bane. "wlh Fatima ba haka bane tsatstsar soyayyar da nake mikine yasa suke gani haka' jumai kanwata itace tabini har gun aiki ta sanar dani abinda aka shirya maki' kinji dalilin dayasa mukabar g'ida kenan. "Cikin shagwaba Fatima tace to meyasa tunda mukazo nan kaketa aure-aure? Dariya Nasir yai h'ade da shafe mata fuska yace Fatima kenan' kinfi kowa sani tun kafin muyi aure na sha sanar dake alkawari na daukawa ubangijina bazan tanayin zina ba. "Fatima tace to hakki fa? Tunda idan ka auresu ko shekara basuyi a gunka kake koransu. "Dariya Nasir yai h'ade da jawota jikinsa yana cewa Fatima ta manta da wann mgnr' Fatima tace baza'a manta ba Nasir' Nasir yace menene abin damuwarki tunda kina tare dani' kefa mutu karaba ne' kinriga kinsha gaba su. "Dariya Fatima tai h'ade da cewa Nasir kenan' shima dariya yai h'ade da kara mannata a jikinsa' da haka Nasir ya samu ya biya bukatarsa' bayan ya gama ne ya wanka ya meda kayan kijinsa yadawo bakin gado ya zauna' Itama Fatima zaune take a bakin gado daure da towel Nasir ya jawota kijinsa snn yace Fatima. "Fatima tace na'am Nasir. "Nasir yace inaso ki fahimceni dan Allah. "Fatima tace ina sauraranka. "ido ta zuba masa tana so taji abinda zaice. "Nasir yace wlh Fatima duk auren da kikaga inada ba dan naci maki fuska bane yasa nakeyi' kawai kinsan ance matar mutum kabarinsa ko. "wani irin kallon banza Fatima tai masa h'ade da cewa hakane. "Snn yace wata yarinya na gani kuma wlh yarinya tayi saima kinganta.... "Da katar dashi Fatima tai tana cewa bashi na tambayeka ba' karisa zancenka. "Nasir yace wlh Fatima yarinya tayine shiyasa naji ta biyamin rai' wata muguwar tsaki Fatima tai masa. "Nasir yace nakarike maki zance dai har nakai kudin aurenta har iyayenta sun sa mana rana. "Fatima tace yayi kyau' ita kuma wanga da ka'ije ta fa? Nasir yace wafa? Fatima tace Aisha mana ko ka mance da'ita ne. "Nasir yace ok' Aisha ai ba wata matsala bace a guna' Fatima tace sbd me kace haka Nasir? Nasir yace kinga takardanta a nan. "Fatima tace mugani' hannu Nasir yasa a aljihu ya ciro takardan ya mika mata ' Fatima tana amsa ta yage takardan h'ade da cewa wlh baka isa ba dan kayi kadan. "Cikin wasa da dariya Nasir yace Fatima idan kika hanani aure so kike ace ga maigidanki nan yana zina ne' kinfi kowa sani yadda nake. "Fatima tace bagani ba' tunda nake dakai kataba zuwa da bukatarka na hanska ne? Ko k'uma ance duk matar da suke duniyane saika sansu' "hannu Nasir yasa ya jawota jikinsa snn yace haba Fatima ki tausayamin mana' fisge jikinta tai daga nasa snn tace baza'a tosaya dinba' kuma wlh babu inda Aisha zata' kai meyasa bakada tsoron Allah meyasa baka tunanin haduwarka da ubangiji kane Nasir. "Nasir yace Fatima kenan duk abinda nai bafa zina nai ba' aurensu nakeyi. "Fatima tace idan aurensu kakeyi sai me to na tambayeka Nasir. "Nasir yace Allah yasa nasani. "Fatima tace kai Nasir baka gajine? Nasir yace dame? Fatima tace da kwanciya da mace' Nasir bayan aureni dakai yar ' matan da ka aure kasaka sukai goma kai Nasir meyasa bakada tsoron Allah ne? Meyasa kake meda ya' ya' mutani zawarawane Nasir' meyasa bakada tausayine Nasir? Wlh Nasir da badan so ba babu abinda zanyi dakai' bakai bama duk me hali irin naka. "hannu Nasir yasa yana toshe mata baki. "tsawan da Fatima tai ne wajan cewa sakanmin bakina yasa Aisha ji. "Da sauri tazo tana knocking. "tura Nasir gefe Fatima tai snn tazo tasa hijab snn taje ta b'ude kofar h'ade da cewa Aisha yaya akai ne? Aisha tace a'a ji nai kamar kuna hayaniya. "sai da tai murmushi snn tace a'a babu komai maybe karar TV ne da kikaji. "rufe kofar tai da key snn takoma taci gaba da cewa yanxu dan Allah bakaji kunya ba ace kana yaudarar yar ' cikin ka Nasir. "daure fuska Nasir yai h'ade da cewa menene abin yaudara k'uma Fatima? Fatima kinfi kowa sani inba keda wlh babu matar da itasa ta tsaya a gabana tana fadimin mgn h'aka kawai dan kace. "Fatima tace oho kai kasani ' yanxu sbd Allah menene Aisha tai maka da har zaka saketa? Nasir yace wlh batai min komai ba' nidai kawai gajiya ne nai da'ita sabo nakeso. "Fatima tace to wlh baka isa ba' bari kaji Aisha babu inda zata zama daram. "Nasir yace idan zamanki takeyi basai nagani ba'ai ko ba zamana takeyi ba ' tunda kai kaje garinsu ka daukota ka rabata da iyayenta ka kawota nan to wlh tazo kenan sai dai mutuwa' mgnr aure k'uma kayi na karke kenan. "Dariya Nasir yai h'ade da cewa kace Allah kenan. "Fatima tace ba nice Allah ba amma in har ina raye kayi na karke kenan. "Dariya Nasir yai snn yace Fatima kenan shiyasa kike birgeni' ni zantafi. "Fatima tace na mance ban sanar dakai ba abincin mu ya kare. "Nasir yace kedawa da naji kike cewa abincin ku' Nasir wlh tsorona daya ne kada idan Allah in yasashi sakawa yaran mutani ya saka masu ta hanyar yaranka.... "wani irin tsawa Nasir ya dakawa Fatima h'ade da cewa wlh Fatima duk irin bakaken maganganu da zaki f'adi a kaina zan amince amma banda yarana idan kike sake sainayi mumunar saba maki. "K'uma na fadi na saki Aisha taci gaba da zama a g'idan tunda g'idan ubanta ne' mgnr abinci k'uma tunda kin iya eje Aisha a g'idan na tabbata kinada kudin ciyar da'ita ai. "Fatima tace idan bazaka bawa Aisha ba' to nida yara fa. "Nasir yace ni tabbata kudin da aka sallameki aiki Sunnan basu kareba. "Fatima tace idan kudin sallamana aiki yananan fa sai me? Kai ni wlh bazan yarda ba. "Gani tana kokarin rikesa da sauri yafice yabar g'idan. "Itako Aisha tana can cikin dakinta batasan abinda ake ciki ba. "itama Fatima tana dakinta ta rasa ta yaya zata fita ta sanarwa Aisha sakin da Nasir yai mata' gashi k'uma tana bata tausayi' shiru tai tana tunani ta ina zata fara' wani zuciya yace kyaleta kawai har ranar da Gaskiya zaiyi halinsa' sbd idan kika sanar da'ita sai tafi ganiki da baki akan wanda yai saki. "A nan tabar mgnr sukaci gaba da zamansu Fatima bata taba nunawa Aisha wani abuba koda wasa. "Yau kam umman Aisha da kuka ta tashi tatasa bbnsu Aisha a gaba da kuka a dole zataje gun Aisha taga halin da take ciki. "Gani tashiga damuwa sosae hakan yasashi cewa tanari gobe zai tura kannita suje su dubata. DAN Allah FANS KUYI HAKURI NA RASHAN JINA DA ZAKUYI KWANA BIYU SBD EXAM NAKEYI MAYNE NO MONDAY MUHADU NAGODE ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W. MMN USWAN 1⃣0⃣ "Washe gari da safe alhj bbn Aisha da kansa yakai abdul tashar mota' din union yana hango su da kaya da sauri yaje ya amshi abdul dake rike da jakan snn suka kariso gun motar. "din union yace bb ina zaku? Alhj yace motar birni kebbi mukeso. "din union yace gashi nan sai dai gun mutum dayane ya rage. "alhj yace ba damuwa dama dhikadai ne zaije. "abdul yana shiga mota alhj ya biya kudi din union ya kwashi kayan da umman Aisha ta siye mata na tsaraba aka xuba a but abba bebar tasha ba saida yaga tashin su abdul. "abba shima ya juya ya koma g'ida. ☘☘ ☘☘ ☘☘ ASALIN AISHA "Aisha yar'asalin garin bauchi ne' itace babba a gun iyayenta sai kaninta abdul basek sai kanwarsu nafeesat wadda Allah yai mata rasuwa shekaru hudu da suka wuce. "Aisha ta taso tun tana yar'karamarta yarinuace mai ilimi na addini dana zamani' tun tana yar'shekara goma da watanni a duniya tai saukan slkur'ani mai girma' a lokacin daidai da takare primary' bayan walimar saukan alkur'ani ne abbbata ya kaita secondry school' duk da ba mai kudi bane amma yana iya kokarinsa akan yaransa' hakan yasa daga ita har kannita prvt school sukeyi. Alhj muhammed da matarsa mai suna Hafsatu duk yar'asalin garin bauchi ne a cikin karamar hukumar ningi' hakar budiness din sa ne ya dawo dashi cikin birni bauchi. "Alhj muhammed din kasuwa ne' ta fannin kayan masarufi'k'uma ya kware sosae a harkan ta hanyan ne ya siye g'idan sa da motarsa' bana karya bane amma bazaka raina masa wayoba. "Da Allah ya kara buda masa duk su biyun suka sauke farillah shida matarsa' sakamako Allah yaiwa iyayensu rasuwa. "lokacin da Aisha tafara secondry school a snn ne abdul yake primary 5 sakamakon prvt school aji 5 biyar aka tsayawa' ita k'uma Nafeesat na primary 3' sbd tsakani Aisha da abdul be wuce shekara biyu ba' Itako nafeesat shekara uku abdul yabata. "Aisha da iyayenta suna rayuwarsu ne cikin rufin asiri dan baza'a sasu cikin jerin masu kudi ba k'uma bazaka ce dasu talakawa ba' sbd duk wani abin ma da mai kudi bazai iya yiwa ya'ya ' sa ba bbn su Aisha yana masu' ga k'uma kyautatawa makwabtansa masu laluran rashin lfy ko halin yau da gode daidai gwargwado da befi karfinsa ba. "H'akan yasa duk makwabtansa suke gani girmasa. "lokacin da Aisha ta fara JSS1 lokacin zahradee yana SS2 goying to 3 k'uma shine head boy a school din' dayake boys and girls ne' mafi yawancin lokuta Aisha tana makara sbd jiran kaninta da takeyi' sai ta rakasu nasu makarantan su shige snn takarisa nata. Zahradee yasha kama Aisha late tun yana dukanta har yagaji ya daina dukanta' a bangaren g'ida kuwa ummansu tana kokari wajan gani sun bar g'ida akan lokacin sbd koda su makara' amma abinka da yara da yara tsayawa takeyi tai ta biyewa su abdul da nafeesat' gashi k'uma rules din school din su duk kansu su biyu before 7-30 anaso aga kowani student a class sbd eight dult uncle yake fara leason. "ita kuma Aisha bata shiga school sai koter after eight. "tun zahradee na dukan ta har yagaji ya kyaleta' suma kansu teachers din uzuri daya sukewa Aisha sbd yarinya ce mai kokari abune mai matukar wahala uncle or anty suyi tambayar bata amsa masu ba' koda ko ba'ita aka tambaya ba. "Tun daga lokacin zahradee yafara son Aisha' duk da a lokacin ba girma ne da'ita ba' sbd natafi 11 years ba dan ma Allah ya yita doguwace shiyasa ake gani kamar tafi h'aka. "h'aka zahradee yaci gaba da raino soyayyar Aisha a zuciyarsa babu wanda yasani dagashi sai abokinsa mai suna Rsslayni' zahradee yana zani weac din sa resutl dinsu yana fita mahaifinsa yaje kaduna ya samummasa addmno na H.N.D. dake kaduna' babu yadda alhj Kaelani beyi da zahradee ba akan yaje kaduna karatu amma zahradee yaki. "A cewarsa koda diploma ya samu yai wanda ke cikin garin bauchi ma kawai ta ishesa' gani yadda zahradee ya kasa ya tsare yasa mahaifinsa yabiye masa da k'uma sonda yake masa' sbd zahradee shine na uku a gun mahaifinsa yana da yayyi a gabansa' babbnsu shine Nurundee sai na biyu shimsundee zahradee sai kanninsa biyu mata dake binsa Amatunrahman da Amatunkaree dayake haihuwar kunikane tsakanisu shiyasa komai tare ake masu' yanxu da h'aka suna JSS3 goying to SS1. "H'akan alhj Kailani ya samanwa zahradee diploma dake cikin garin bauchi ya karanta ACCOUTING' dayake bamai dadewa bane karatun nan danan zahradee ya kammala' duk a lokacin Aisha bata kare secondry ba yasa zahradee shiga univesty( Sr AHMADU TABAWA BALEWA) dake bauchi nan ma yaci gaba da karanta ACCOUTING d'in sa. "tun lokacin da Aisha ta shiga secondry suka h'adu da wata yarinya mai suna ubaida komai tare sukeyi sbd ita ubaida yarinya ce mai kokari kusan ince GG suke da Aisha' akwana a tashi Aisha tafara girma a mamomin balaga sun fara baiyana a gun ta' ma wankin yan'mata yafara wanketa". "Tana SS1 samari suka fara kawo mata hari' amma mahaifinta yahanata sauraran kowa sbd a cewarsa karatu yakeso tayi' k'uma mafi yawancin samarin babu wadda zakace dashi yafito ayi AURE sbd suma kansu basu gama rike kansuba balle su rike mata. "gudun kada su batawa yar'sa rayuwa k'uma su hure mata kunni yasashi dakatar dasu gaba dayansu' itama ya hanata sauraran su. "Duk da h'aka basu kyaleta ba ' idan zata school ko na islamiya sai sun tareta' Duk da ba area d'aya suke da zahradee ba amma yanajin labarin komai a gun Rsslayni'g'ani H'akan yasa zahradee xuwa g'idan su Aisha kai tsaye yaje tsayawa yai a kofar g'ida yai sallama' Allah yasa lokacin akwai alhj muhammed a g'ida' jin sallamar da yakeyi ne yasashi mikewa yaje ya dubo mai sallamar. "Gani yarone d'an matashi wadda ba zai wuce shekara ashirin da biyu zuwa da uku ba ' yasashi cewa yaro lfy? Murmushi zahradee yai h'ade da susa kansa. "Dukawa yai har kasa ya gaida shi' gani natsowar yaron yasa alhj muhammed ya amsa da fara'arsa' snn yace lfy yaro wa ya aiko ka? "Cikin jin kunya zahradee yace a'a bb aiken kainane. "alhj muhammed yace Allah yasa dai lfy. "Murmushi zahradee yai snn yace dama mgnr Aisha ce. "Da sauri alhj muhammed yace wani abu tai maka ko? "zahradee yace a'a dama naga Aisha ne inasonta shine nace bari na fara sanar dakai. "Murmushi muhammed yai snn yace so fa kace yaro? Toma wani irin so kake mata? "zahradee yace bb sonta nake da aure. "Sae da alhj muhammed yai dariya sosae snn yace yaro kayi Gaskiya amma kai baka gani kayi karami da aure? "Shiru zahradee yai be tanka ba. "alhj yace wai ma ya sunnaka? "zahradee yace su nana zahradee baba. "muhammed yace Allah sarki zahradee nagode sosae da gurmamani da kayi k'uma koba komai ka nunamin kai d'an babban g'ida ne' A Gaskiya bazan boye maka ba zahradee Aisha tayi karama da AURE k'uma koba komai nafiso sae tayi karatu koda diploma ne snn nai mata aure k'uma kaga yanxu da h'aka ko secondry bata kareba... "Da sauri zahradee yace eh bb nima nafiso tayi karatun sbd koba komai zatasan encin kanta' nima yanxu da h'aka karatun nakeyi bb. "bb id'an har zaka bani Aisha aure wlh zan'iya jiranta bb. "Dariya muhammed yai h'ade da cewa Allah me iko' zahradee dan Allah kai daga wani g'ida kake ne? "zahradee yace ni daga almadina queaters suna mahaifina alhj Kailani. "muhammed yace a'a! Kardae ace Kailani me atanfofi? "zahradee yace shifa. "muhammed yace a'a lalla kafito daga babban g'ida ne domin duk zari'ar alhj Kailani sae son barka. "jin h'aka yasa zahradee jin dadi a ransa. "muhmmed yace zahradee yanxu abinda za'ayi kaje tuku' zahradee yace bb bangane ba? Alhj muhmmed yace zahradee ni dae nasan a yanxu da h'aka Aisha bakasan komai akan soyayya ba' k'uma banaso ta sani sbd banaso ta raba hankalinta biyu. "nafiso ta tsaya kawai tayi karatu' sbd shine kawai gatan daya dace na bata a duniy. "zahradee yace h'aka ne baba. "alhj muhmmed yace to kaji dalilina na hanata tsayuwa da samari. "zahradee yace to bb yaushe zandawo? "murmushi muhmmed yai h'ade da cewa yaro kenan' yanxu duk mgnr da nai maka baka Fahimta ba? To kaje ko gobe zaka iya zuwa mu gaisa' aikai d'ane a guna. "zahradee yace nagode bb' mikewa yai h'ade da sallamarsa. "yace to a gaida g'ida' idan ka'isa kace ina gaida alhj' kace masa alhj muhmmed na yan'wake na gaida shi. "zahradee yace zaiji in Allah ya yarda. "zahradee na tafiya alhj muhmmed ya kwashe da dariya h'ade da cewa yaro kenan' idan banda jarabar duniya kamar wanga yaron mai yasani akan aure? ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W.☘ MMN USWAN FANS NAGA ADDU'OINKU NAGODE SOSAE ALLAH YABAR ZUMUNCI YA KUMA AMSA ADDU'ARKU AMEEN. 1⃣1⃣ "Alhj muhmmed yana shiga cikin g'ida gani yadda yake dariya yasa Hafsatu tambayarsa lfy? "Sae da ya zauna snn yake sanar da'ita yadda sukai da zahradee' Hafsatu tace Allah me iko yanxu da kansa yazo da mgnr ga alhj? "Alhj yace wlh kuwa nima kaina abin ya bani mmki. "umma tace to yanxu yaya kukayi dashi? Alhj yace aa kawai dae cewa nai ba yanxu zai aurer da'ita ba. "umma tace to ma alhj koda yanxu ne zaka aurer da Aisha sai a dauketa abawa yaron da besan ciwon kansa ba banle yasa nata. "Alhj yace kema dae kyagani. "zahradee yana isa g'ida parlour ya sami iyayensa zaune suna hira da yayyinsa h'akan yasa shima ya samu gun ya zauna kusa da abbansa. "Gani shi cikin nishadi yasa hjy cewa zahradee yah! dae? "Cikin zumudi zahradee yace himm hjy nibaki labari. "hjy tace bani nasha Allah yasa alkairi ne. "zahradee yace alkairi ne ma hjy' hjy tace to ina sauraranka' cikin doki zahradee yace hjy kinsan daga ina nake da kika gani h'aka? Hjy tace a'a saeka f'adi. "zahradee yace g'idan su yarinyar da zan aure. "duk parlour suka sa masa dariya. "zahradee yace Allah kuwa hjy da gaske nake. "Nan hjy ta haushi da f'ada tana f'adin kai zahradee kanka daya kuwa? Kasan abinka kake f'adi? Zahradee yace Allah hjy da gaske aure nakeso. "hjy tace idan kasake irin wanga mgnr anan saena mareka. "A take zahradee ya canxa fuska. "Gani yadda zahradee ya canxa fuska yasa alhj cewa xonan my son' bani labari nasha' kace dae zanyi sarkuwa. "hjy na gani haka mikewa tai ta shige daga ciki ta barsu a nan. "zahradee yace wlh abba wata yarinyace na dade ina sonta tun ina secondry lokacin batayi girma ba' haka nabar wa zuciyata har Allah yasa tai girma shine yau naje da kaina har g'ida su na sanarwa mahaifinta. "Alhj yace eye kacedae na girma tunda gashi har zankai ga sarkuwa. "zahradee yai dariya h'ade da cewa dan Allah abba kaje g'idan su Aisha kayi mgn da mahaifinta dan Allah abba wlh abba ina son Aisha sosae. "Alhj Kailani yace zahradee kasan mgnr da kakeyi kuwa? Kwata2 shekaruka nawa a duniya da zakayi mgnr aure zahradee? In ma banda abinka baka gani yayyinka ga suna ko mgnr auren basu' shine kai zakace kanaso aure zahradee. "Nurundee da shamsudee suce ato abba kowa ma ya gani' dan Allah kafita har kansa sauraransa da akeyi ma shine yasa yakewa mutani mgnr banza. "Jin h'aka yasa zahradee dukawa a gaban abbansa gwiwa bibbiyu h'ade da rike gwiwar abba yace dan Allah abba dan annabi abba ka taimaka min kaje g'idan su Aisha ka nima min auren ta abba' abba ni koda ba yanxu za'ayi auren ba inaso ta zauna a matsayin nine mijin da zata aure sbd ko secondry bata kareba k'uma abbanta yace sae tayi karatu snn zai mata aure. "Tunda zahradee yafara mgn abbansa ke kallonsa har ya kare' snn yace waima yarinyar da kakeso yar ' g'idan waye? "zahradee yace yar ' g'idan alhj muhmmed ne dake kasuwan yan'hatsi. "Alhj yace wani alhj muhmmed kake mgn akai? "zahradee yace alhj muhmmed dake zaune a doruwa mana abba' shifa ya sanka har cewa yai ma na gaidaka. "nan alhj Kailani yace ohooo ayya yanxu na tuna' Allah sauki aiko mutumin kirkine. "yanxu sbd Allah zahradee bataji kunyar tunkararsa da irin wanga mgnr ba? "murmushi zahradee yai h'ade da shafe kansa snn yace to ai abba mutumin hanata tsayuwa da samari yakeyi wai sbd kada a bata masa tarbiyar yarinyar sa' ni k'uma da gana h'aka shiyasa naje gunsa direct na sanar dashi manufata. "mmki ya kama alhj Kailani sosae' shiru yai yana kallon zahradee har yakare snn yace to da kaje gunsa ya kukai dashi? "zahradee yace cewa yai wai sae tai karatu snn zai aurer da'ita. "Nima kaina abba inaso Aisha tai karatu sbd yarinyar mai hazakace tana da ilimi sosae' amma inda so samune da tana kare secondry sae ai mana aure idan yaso a gidana sae taje gaba.... "amma ya dakatar dashi da cewa haba zahradee wanga irin zance kamar saeda kai haddansa snn kazo guna. "Snn abba yace zahradee lalla hakan ya nunamin ba karamin so kake wa Aisha sha sbd tunda nake dakai baka taba fitowa gaba da gaba ba ka nunamin bukatarka haka sae yau' sae da alhj Kailani yasa hannu ya dafe kafadar zahradee snn yace zahradee. "Nagode da h'akan dakai koba komai nima ka siyemin girma da daraja a idon sa' amma ita yarinyar tasan kana sonta? "zahradee yace a'a bata sani ba abba. "Alhj Kailani yace ina me baka shawara da kaje ka nimin soyayya a gun yarinya idan har ta amince tana sonka nikuma nai maka alkairin nima kama aurenta a gun mahaifinta. "tsanle zahradee yai h'ade da rungume mahaifinsa yana godiya' sae da ya zauna snn yace to abba itana zanfara? "Duk su uku sukasa dariya shamsudee yace shege dama ashe karyan rashin kunya kake mana' ko iya zance da budurwa ma baka iya ba. "Sae da zahradee ya daure fuska snn yace abba kaganshi ko. "kamo hannunsa abba yai h'ade da cewa xonan my son fadimin me kake bukata? "zahradee yace dama kudin da zaiyi mata siyayyane na kai mata shine bandasu. "dariya abba yai snn yace zahradee waye yace maka zuwan farko gun budurwa ana bata kudi? Zahradee yace to abba me zankai mata wanda zataji dadi itama? "Alhj Kailani yace zahradee. "zahradee yace na'am abba. "abba yace tattaro hankalinka ka miko min su nan. "zahradee yace to abba na. "Gani irin abinda sukeyi su kamar abokan juna shamsudee da Nurundee yasa su tashi subar gun. "bayan sun tashi ne abba yace zahradee. "zahradee yace na'am abba. "Alhj yace inaso ka natso da kyau ka saurari abinda zan f'adi maka' nasan yana mstukar son Aisha' sbd yadda ka nuna min' amma inaso kasan da cewa ita mace kamar wahainiya take tana iya chanzawa a ko wani lokaci. "Idan h'aka a matsayina na mahaufunsa ina baka shiyasa kada ka sake Aisha tasan kana sonta h'aka' bance kada ka nuna mata so ba amma kayi da kadada sbd gudun yin dana sani. "kai na mijina k'uma duk namiji ansansa da karfin hali da juriya ba komai ne zaka nuna zakewa akai ba' banle akan mace. "idan har kabari Aisha tasan kana sonta haka tabbas kana tare da wahali' k'uma ita rayuwa da kake gani ba lallane abinda kakeso ka samuba' idan yau Allah yasa Aisha ba matarka bace yaya zakayi? Shiyasa nakeso kabi komai a hankali. "mgnr abinda zaka kai mata k'uma da kake mgn akai' zahradee banaso tun farko ka fara budewa Aisha ido da kudi' bawai banaso kai mata alkairi bane ko dan baka dashi ko k'uma kayi tunanin banaso na baka ne a'a wlh ko daya zahradee kafi kowa sani duk cikinku nafi sonka dan h'aka banga abinda zaka bukata a guna na hanaka ba sae dae idan bandashi ko yafi karfina. "Amma idan tun yanxu kafara b'ude mata ido da kudi in har Allah yayi ita abokiyar rayuwarka ce baka tunanin yadda zamanku zai kasance. "idan h'aka nafiso kaje ka hureta da soyayyarka tuku idan yaso komai sae yabi baya'idan har kanaso ka bata kyau kabari kaje kamar sau biyu kaga irin karban da zatai maka snn in katashi komawa sae kai mata shatara ta arziki ka kai mata. "Amma idan tun yanxu kafara zuwa da mata da kudi ko wasu abin duniya ba lallane ka tantance irin son da take maka ba' dan Allah ne take sonka ko dan abin hannu kane' amma idan kaje babu komai ta nanne zakasan irin son da take maka na Allah ne ko kuwa. "ni kuma nai kama alkairin insha Allahu da kaina zaje na nimo maka auranta. "zahradee yace hakane abba na' tafawa sukai suka sha hannu. "zahradee yace Nagode abba na' shiyasa nake matukar sonka' Allah ya barmin kai. "nan dae sukaci gaba da hiransu' zahradee nabawa abba labarin Aisha suna dariya. "Alhj Kailani duk cikin yaransa yafison zahradee' sbd Zahradee yarone mai biyyaya k'uma baya tsanlaka mgnr mahaifinsa duk cikin yan'uwansa yafisu sa hankali akan kasuwancin abbansu sbd su shamsudee da Nurundee tunda sukai girma suka san dadin kasuwanci kowa kama nasa yai' kasan yasa abbansu daukar yaran shago yana biyansu'amma tunda Zahradee yakawo karfi yashiga har kasuwancin mahaifinsa gadan gadan' koda yaran shago sun so yin cuwa- cuwa amma ganisa yanasa su rage wani abu. "duk da dae bazai hanasu yi kwata2 ba amma zaiyi sauki' shima kansa abba yaga canji sosae' duk da karatunsa amma be hanasa xuwa kasuwa ba' h'akan yasa abbansa yake matukar son sa fiye da sauran yan'uwansa. "duk da nuna masu babbancin da yakeyi be damesu ba sbd sufi kowa sani dalilin da yasa yake masu hakan. "tun daga lokacin Zahradee yake zariya g'idan su Aisha' tun bbn Aisha yana kin kulasa har ya gaji yaci gaba da kulasa' mafi yawancin lokuta batare da abbansa ya sani ba idan Zahradee zaije g'idan su Aisha yakan siyewa su abdul sweet da chocolate da ice cream yakai masu. "su abdul suma har sun saba dashi sosae' amma duk a lokacin be yarda sun fara tsayuwa da Aisha ba' shima beyi fushi yasa ya daina zuwa ba. "A lokacin Aisha na SS2 wata juma'a da zahradee yazo shida abokinsa Russlayni suna tsaye a kofar g'ida ga hadari ya taso gadan gadan haka ruwa yai masu dukan tsiya' shiko Russlayni da yake mai zuciya ne nan yahau masifa inda yake shiga bsnan yake fitaba. "in banda hakurin da yake bashi babu abinda Zahradee yakeyi. "Russlayni yace badae zan rantseba amma ba lalla bane na sake rakoka g'idan ga' sae kace yar'gwal' ko ita kadae ce macen da tarage a duniya da zaka rinka wahala h'aka a kanta. "Wai ma na tambayeka dame suke takama kudi ko mulki? Nidae naga ba yar'kowa ne ba' k'uma ubanta ba finku kudi sukai ba amma sae sa wani uban doka' to wlh idan kai zaka jure ni bazan jure ba ' k'uma bazan sake rakoka ba. "Sae kace wata gwal kai idan gwal ne daga yau ka yage inaso su dauketa su daura a wiya su rinka yawo a gari sbd asan suna da kaya mai tsada da daraja' amma ita ba gwal ba banle ace. "Duk mgnr da Russlayni keyi shiru Zahradee yai yana kallonsa har yakare. "Ashe duk mgnr da Russlayni keyi alhj muhmmed yana jinsu' shiru yai har Russlayni ya kare' shima kansa yasan be kyauta ba' sbd tun kafin ruwa ya dauko suke tsaye a kofar gida shi bace su shigo daga ciki ba kuma bace su tafi ba gashi kenan ruwa yai masu dan banzan duka. "hakan yasa shi matsewa yace Zahradee dan Allah kuyi hakuri wlh kafin na iso gunka ne ruwa ya sauko amma insha Allah idan na shiga cikin g'ida yau d'in nan zansanarwa Aisha komai a kanka k'uma in Allah ya kawoka ko zuwa gobe ne zanbata izini fitowa ta saurareka. "Zahradee yace ba komai bb Allah yasa mukai. "Russlayni da yake yariga ya fusata ko kallo alhj muhmmed be'ishesa ba jan hannu Zahradee yai suka bar gun' ko sallama be bari suyi ba. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W. ☘. MMN USWAN Allahamdulillah masha Allah. It's a great pleasure for me to be able to make the most important decisions in my life and I am very thankful to almighty for the opportunity and the previllage of my life to be in a good health condition. 1⃣2⃣ "Alhj muhmmed yana shiga cikin g'ida umman su Aisha dake kwance a kan gado gani yadda ya shigo a jike sharkam da sauri ta mike h'ade da tambayarsa daga ina h'aka. "Alhj yace gani nai baku da bread ya kare shine ya fita siyowa sbd yara duk sun yi bcc ga k'uma dare da yai shiyasa nsje da kaina. "umma tace shine kabari ruwa ya dukeka h'aka? "Alhj muhmmed yace to yaya za'ayi' mikewa tai ta taimaka masa ya cire kayan snn ta dauko masa bargon da yake rufe jikinsa dashi idan sun zo kwanciya ta bashi ya rufe jikinsa dashi snn suka kwanta. "suna kwance ne alhj muhmmed yake sanarwa umma cewa yanxu su zahradee ya tafi g'ida k'uma gashi ruwa yai masu duka'umma tace Allah sarki Gaskiya alhj yaronga ba kasamin so yakewa Aisha ba' idan ba kana gani zaizama matsala ba' mai zaihana kabara umurnin tsayawa dashi' tunda kaga yanxu ta mallaki hankalin kanta' k'uma shima yaron a iya nazarinsa da nai yanada nasha. "Alhj muhmmed yace himm Hafsatu kenan nan kullum ku mata tunaninku irin daya ne kina gani yaro karami wanda be gama sani ciwon kansa ba banle na wani' ta yaya zanbari Aisha ta tsaya dashi' umma tace sbd me alhj? Kodae baka sonsa da'ita ne? "Dariya alhj yai h'ade da cewa wlh ko daya Hafsatu nidae kawai tsorona daya ne kada nazo na saki jiki dashi yazo ya kaeni ya baroni' in banda rayuwa yariga ya zamo abinda ya zama kamar yarona ina yasan wani kalmar so' himm Hafsatu wlh idan bakine ranar da yafara zuwa guna ni da farko ma na dauka aikensa akai ashe aike kansane. "Babu ko kunya wai yazo niman auren Aisha. "Tsayawa tai ta barshi sae da ya kare snn tace alhj kenan ni k'uma a nawa tunani yanada hankali sbd inda wani yaron ne yadda kake mgnr yayi karami to wlh ba lalla bane yazo ya sameka sai dae kawai kaji a gari ace Aisha tana hira ko k'uma ace tanada samari suna zuwa gunta. "amma tunda har kaga yayi haka ya nuna maka shi dan babba g'ida ne' k'uma in Allah ya yarda abinda kake tunani in Allah ya yarda bazai faruba' k'uma idan banda abuka hanata sauraranro samari bashi ne zai shiryar maka da'ita ba' idan Allah yariga ya shiryar maka da yaro to ka gode Allah. "Alhj yace hakane amma ai Allah da kansa yace tashi na taimaka ko? "Hafsatu tace hakane amma inaso kasan cewa Allah shike shiryarda da wanda yaso ko. "Alhj yace hakane to Allah ya kara shiya mana' musan ba wayanmu bane k'uma ba dabararmu bane. "umma tace abinda nakeso ka gane kenan. "Nan dae sukai ta hiransu. "Tun a hanya zahradee yake tunani kala-kala akan Aisha' anya bbnta yana sosa dashi kuwa? Duk tsawon lokacin daya diba yana zuwa g'idan su amma har yanxu bbnta bebari ya fara tsayuwa da'ita ba' kodae akwai wani abu a zuciyarsa ne? Da yake boyesa k'uma ya kasa fitowa ya sanar dashi. "Sae dae kullum idan yazo yai ta jansa da hira bayan k'uma ba gusa yazo ba' shifa Gaskiya yafara gajiya da irin wanga abu da bbn Aisha yake masa' idan yasan bazai bashi bane kawai gara tun farko yafadi amma ba yaita ja masa rai ba. "Russlayni ne ya katse masa tunaninsa da tabansa yace zahradee. "yace na'am Russlayni' Russlayni yace tunanin me kikeyi? Murmushi kawai zahradee yai h'ade da cewa babu komai. "Suna area d'insu kowa ya shige g'ida da yake dama layinsu daya ne. "zahradee yana shiga g'ida d'akinsu kawai ya nufa' da yake anyi ruwan sama shiyasa parlour babu kowa. "koda zahradee ya kwanta yai kokarin bcc amma abu ya gagara'sae faman juyi yakeyi' zuciyarsa na saka masa abubuwa kala-kala zahradee be samu bcc ba sae asuba. "bari yai sae da yai sallar asuba snn ya kwanta. "washe gari da safe da yake yau weekend ne k'uma dama duk ranar end alhj muhmmed baya su Aisha da kannita suna karyawa bbnta yace Aisha idan kin gama inaso ganiki. "to kawai Aisha tace. "Aisha na gani karyawa taje jin kiran bbnta' da sallama ta tashi dakin har kasa ta duka snn tace abba gani. "sai da alhj muhmmed yai gyaran murya snn yace Aisha dama ba komai bane yasa na kira ki' inaso na sanar dake wata mgn ne ina yaron nan zahradee da yake yawan zuwa? Ba kince kin sanshi kuyi mkrnta daya ba? Aisha tace eh' yace dama niman izini yazo a guna sbd duk ganisa da kikeyi a g'idan nan ba zuwa yakeyi ba' guki yake zuwa abinda yasa kike gani yana zuwa guna sbd naki bashi bakine a kanki. "Amma yau nayi masa alkairin zanbari kifita idan yazo shiyasa nace bari na sanar dake' sbd kada kice baki da masaniya akai... "Aisha tace to abba ni mezan masa da yake zaizo guna? "abba yace nima bansaniba amma idan yazo zai sanar dake da kansa manufarsa. "Aisha tace to shikenan abba. "Alhj muhmmed yaci gaba cewa dan Allah Aisha inaso ki kula sosae kada kiga nabaki izini tsayuwa da samari ki nimin ki zubarmin da mutunci' wlh Aisha idan kikaimin h'aka bazan yafe maki ba. "Aisha ban amincewa zahradee ba sae da naga natsawarsa' amma kasa dan'adam ta yake be cika goma ba' dan Allah Aisha kada kibari shedan ya rinjsyeku ku aikata abinda zaisa mutunci na ya zuwa a uguwa kinjiko Aisha. "Aisha tace naji abba k'uma in Allah ya yarda zankiyaye. "Alhj muhmmed yace Allah yabada iko. "Aisha tace ameen. "Da yamma bayan an idar da sallar isha'i gani garin da hadari yasa zahradee zuwa da motar bbnsa' itama Aisha bayan ta idar da nata sallar duk da abbanta be sanar da'ita ita nufin zahradee a kanta ba amma be hanata rangada kwalliyarta ba' da yake dama ma'abociyar kwalliyace. "kwallliya tai cikin doguwar rigan shadda wanda abba ya dinka mata ita da kanita abdul irin daya green ba kasamin kyau tai ba. "bayan ta gama gun tasamu ta zauna kusa da abdul suna hira' ita k'uma ummansu tana gun alhj tana bashi abinci' dama dabi'ar Hafsatu ne bata barin mijinta ya zauna shikadae dan zaici abinci' koda bazataci ba zama takeyi kusa dashi yanaci suna hira har ya gama. "sallamar yarone ya katsesu da sauri umma ta leka h'ade da tambayar waye? Bayan yaro yai gaisuwa snn yace wani ne ya sikoni wai yana sallama da Aisha. "umma tace jeka kace waye? "komawa yai snn ya dawo yace yace wai zahradee ne. "umma tace jeka kace tana zuwa. "yace to. "komawa cikin dakin tai ta sanarwa alhj' alhj yace kice taje amma minti talatin nabata' kuma tasa hujab idan zata fita. "umma tace to. "kiran Aisha tai dakinta sae da takara gyara ta h'ade da sanya mata hujab snn tace taje ana sallama da'ita. "Cike kunya ta kami hanyar fita sae k'uma ta juyo' umma tace lfy? Aisha tace abdul nakeso ya rakani. "murmushi umma tai snn tacewa abdul yasashi suje. "Aisha na rike da hannu abdul suke fita gun zahradee. "zahradee dake zaune a mota hangosu yasashi fita da sauri ya kariso gunsu h'ade da kiran malama Aisha' murmushi kawai Aisha tai snn tace ina yini. "Cikin doki da murna zahradee yace lfy klau Aisha' ya g'ida dasu umma da abba? "Aisha tace lfyrsu klau. "juyowa yai gun abdul dake tsaye ya tsaresu da ido snn yace abdul bako gaisuwa? "murmushi abdul yai snn yace ina yini. "zahradee yace lfy klau malam abdul. "juya akalar kallonsa yai gun Aisha h'ade da cewa Aisha ina tafan abba ya sanar dake komai ko? "Aisha tace a'a. "juyawa yai gun abdul snn yace dan Allah abdul din bamu gu muyi mgn kaji. "to kawai abdul yace snn ya kauce ya basu gu. "bayan kaucewarsane zahradee yai wani gyaran murya snn yace Aisha nayi tunanin abba yariga ya sanar dake ne' amma tunda kince be sanar dake ba babu damuwa ni da kaina zan sanar dake abinda yake tafe dani Aisha. "zahradee yace kina kayrarona kuwa Aisha? Aisha tace ina sauraronka. "Ba komai bane ke tafe dani Aisha sae so da kauna danake maki Aisha' Aisha ba dade ina sonki shekara da shekaru h'aka naci gaba da rainon soyayyarki har izuwa wanga lkcn Aisha' shiyasa yanxu bace lokaci yayi da yakamata na sanar dake kudurina akanki' gani abba baya barinki tsayuwa da samari yasa nazo gusa direct dan niman izinin zuwa guki. "Shiru tai tana sauraronsa' gani shirun da tai ne yasashi cewa Aisha kina jina kuwa? Murmushi kawai tai masa. "zahradee yace shiru da kikai tabani amsa sae dae kashhh! Bazan iya babbance kalar amsarki ba sbd fasara biyu tabani wakau eh ko a'a' Aisha kina sona kuwa? "murmushi tai h'ade da sa hujab dinta ta rufe fuskanta. "wani irin dariya zahradee yai h'ade da hamdala snn yace Aisha nagode da amsar soyayyata da kikai yi' Allah yasa kinaso kamar yadda nake sonki Aisha' Allah kuma ya barmu dare har karshen rayuwarmu. "Cikin jin kunya Aisha tace zantafi abba yace kada na dade. "zahradee yace Aisha hakan ma nagode' ban sbd tunda nake zuwa g'idan ku ban taba tsabar kaina cikin farin ciki irin yau ba. "Bari na barki ki tafi gida haka kada abba yai maki fada kinga ba zanji dadi ba ko? "Shiru Aisha tai. "zahradee yace Aisha ki gaida abba da umma saeda safe. "juyawa tai h'ade da kama hannu abdul suke shige cikin g'ida. "zuba mata ido yai har saeda yaga ta shige' wani irin tsalle yai yana murna snn yashige mota yaja yabar uguwar. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W. ☘. MMN USWAN ALLAHAMDULILLAH MASHA ALLAH. INA TAYA DAYA DAGA CIKIN MEMBERS DINKU MURNAR AURE. HAPPY MERRIAGE LIFE SIS KHAIRAT UP. Marubuciyar Takaicin d'a namiji Fatima zara Aisha Humaira Kai nake so Da sauransu. Allah ya bada zaman lfy yakawo zuri'a na gari yasa nayi kenan mutu ka raba. 1⃣3⃣ "yau zuciyar zahradee cike yake da farin ciki fal baya musaltuwa. (Ya Allah Ka HADAMU DA MASOYAN MU KO A LAHIRANE AMEEN Ya RABBI). "zahradee yana isa g'ida' bayan yai parking direct parlour ya nufa sbd bare banyi ba banle ance su abbansa su kwanta. "Da sallama ya shiga parlour' su hjy da yayyansa suka amsa' bayan ya duka ya gaida iyayyensa da yayyinsa snn ya mike kusa da alhj Kailani yaje ya zauna' gani yadda yake cikin farin ciki yasa alhj Kailani cewa my son yaya dae? Yau na ganka h'aka? "zahradee yace himm abbana ban baka lbr ba' alhj Kailani yace son bani nasha. "zahradee yace yau bbn Aisha ya bari ta fito ta saurareni na bayyana mata abinda ke raina k'uma ta amince tana sona. "Alhj yace wow son na tayaka murna. "zahradee yace nagode abba. "Gani irin abinda sukeyi yasa hjy tace dan Allah alhj menene kukeyi h'aka? koda auren aka daura nasan iya kacin murnar da zakuyi kenan. "Kailani yace bazaki gani bane shiyasa. "mikewa tai ta bar masu gun. "su shamsudee da Nurudee da suke gun h'ada ido sukeyi snn shamsudee yace a dae yi a hankali. "Nurudee yace kasan JJC( july just come) ne that is why. "duk suka sa dariya. "su Amatulrahman da suke zaune a gefe'Amatullah tace yy anty ne zaka kawo mana? "Tsawa abba ya daka masu yana cewa waye yasa bakinku a mgnr? shiru sukai h'ade da mikewa su bar gun. "abba yace my son yanxu kasan me za'ayi? Zahradee yace a'a abba. "Sae da alhj Kailani ya gyara zama snn ya fara da cewa yanxu tunda har ta amince tana sonka to ba kullum zaka rika zuwa g'idan su ba? Da sauri zahradee yace meyasa abba? Alhj yace zuwa tadi kullum yakansa mace taji ta tsaneka' k'uma koda ba h'aka ba idan kuna bawa juna iska duk lokacin da kuka h'adu zakuji kunfi marmarin juna. "amma idan kana zuwa gunta kullum tun kana f'adi mata Gaskiya wataran karya zakayi kaga daganan ma zaisa raini ya shiga tsakaniku. "idan k'uma kabari raini ya shiga tsakanika da mace ko wlh koda aurenta kai bazakaji dadin zama da'ita ba. "ni k'uma son bazanso ka auri matar da zata rainaka ba banle harmu da muka haifeka taga girmanmu. "zahradee yace h'akane abba. "alhj Kailani yaci gaba da cewa abu na biyu k'uma dan Allah zahradee kada kabari shedan ya rinjayeka ku aikata abinda zaizubar mana da mutunci da k'uma darajar g'idan nan' duk da nasan ba aikinku bane daga kai har yayyanka amma tuni yanada kyau ko? "murmushi zahradee yai. "Alhj Kailani yace koma menene son kayi kahuri idan akai auren zakuyi. "Da sauri zahradee yace ehhhh abba' ya karisa mgnr ne h'ade da bude ido😳 sbd mmkin mgnr. "Alhj yace son da alama har yanxu kuruciya na tare dakai' sbd gani nayi kanka na rawa' gara na dungayi ina yimaka girgadi sbd kada kaje ka jawomin na barin gari. "murmushi zahradee yai h'ade da susa kai. "mikewa abba yai h'ade da cewa son ni zani na kwanta. "Aisha na shiga cikin g'ida dakinsu kawai ta nufa taje ta tube snn ta kwanta' amma ba bcc takeyi ba' mgnr zahradee ne yake mata yawo a kwakwalwarta' tana f'adin ashe dama duk zuwan da yakeyi gun abbana sona yakeyi shine abba be taba sanar dani ba sai yanxu? "meyasa abba yake h'aka? Meyasa abba yake hanani tsayuwa da samari? ga kawayena wanda na girma da wanda suka girmeni abba su iyayyansu basu hanasu tsayuwa da samari sae ni? "kodae auren dolene yakeso yai min? Kodae yariga ya bawa wani nine bansaniba? "kai ina' inda h'akane da bazai bari na fita gun zahradee ba' sbd kafin yasan waye zahradee na rigashi sani zahradee sbd muyi school daya dashi' To dama shi zahradee tun ina yar'karamata yake sona komai? "ba tare da tabawa kanta amsa ba bcc ya dauketa. "washe gari kuwa gun yadda zahradee yaso zuwa gun Aisha dole ya hakura sbd mgnr da abbansa yai masa' washe gari kuwa a masallacin kofar g'idan su Aisha yai sallar isha. "koda aka idar saeda yadan tsaya saeda yaga takwas yayi dobt snn yai sallama cikin dauren g'idan' abdul ne ya amsa umma tace kamar muryar zahradee amma jeka ka leka kaga waye. "kada abdul ya leka zahradee ne ya gani bayan sun gaisa ne ya dawo ciki ya sanarw umma' umma tace tashi kije.... "Da sauri abba yace taje ina? Idan zamanki take a g'idan to taje' jin hakan yasa umma mikewa ta shiga d'akin' kusa dashi ta zauna h'ade da sa hannu ta dafe masa kafada snn tace maigidana dan Allah kayi hakuri' abinda yasa nace h'aka gani nai anriga an zama daya shiyasa. "yace kekika daura masu aure? "a'a. "To kince anzama daya? "dan Allah kayi hakuri nayi kuskure amma insha Allahu bazan karaba' Allah ya huci zuciyar angon Hafsatu. "shima kansa besan lokacin da dariya ta subto masa ba' snn yace jeki kice taje amma koda ta dade dan inaso na rufe g'ida na kwanta. "To tace h'ade da mikewa. "hujab kawai ta sanya batare data tsaya kwallyaba da nufi kofar g'ida abdul na biye da'ita suka tafi gun zahradee. "Da sallama suka isa gun ita da handbag d'inta' shima zahradee dake tsaya da fara'arsa ya amsa h'ade da karisowa gun data tsaya ita da abdul. "rike wa abdul hannu yai snn yake my little bro da kake? Abdul yace lfy klau' zahradee yace yah school kana kokari kuwa? Abdul yace sosae ma' zahradee yace okey yanxu fadi min yau me aka koya maku a school din? "abdul yace umh"uhm" uhm" yauwa' kasan yau wenesday ne ko? Zahradee yace eh! Snn abdul yace to dama duk ranar wenesday Englash language mukeyi. "zahradee yace a Englash din wani topic aka koya maku? Abdul yace Diff b/w news paper and magazine. "zahradee yace fisrt tell da meaning of news paper before we tolk abourt the diff. Abdul ya fara da cewa The news paper it's unboud printed publicatino issued at regular which prints information in unboud words and after supplemented with pictures.... "zahradee dake tsaya yace ya'isa h'aka kanina ashe dae kana da kokari. "dariya Abdul yai' Aisha dake tsaye ta daure fuska sbd tasan halin Abdul sarai da bakar surutu' idan aka biye tashi sae ya kwana yana zubawa ba damuwarsa bane. "Gani Aisha ta danke fuska ne yasa zahradee cewa Abdul shiga mota ka zauna ugo wayata kayi game. "bude masa motar yai ya shiga snn ya mika masa wayar' gani yadda ta daure fuska yasa zahradee cewa kiyi hakuri Aisha na bata maki rai ko? "Aisha tace to ba kaine ka kama jan yaro da surutu ba. "zahradee yace a'a Aisha bazaki gani bane nima kaima mmki Abdul ya bani sbd yadda akai masu explanation ba kowani yarone zai fahimta ba' sbd yadda akai masu bayani ba method din secondry level bane' wanga method din na yan' hghth intitut ne' maybe qua teacher ne. "Aisha tace ni zantafi sbd abba yace kada na dade' zahradee yace tun yanxu Aisha? Aisha tace abba ne yace kada na dade shiyasa. "zahradee yace to shikenan gobe ko jibi nadawo' juyawa yai gun Abdul yace fito katafi g'ida. "Abdul yana fita zahradee sa hannu yai cikin mota ya dauko wata yar'karamar jaka ya mikawa Abdul snn sukai sallama. "tashige cikin g'ida' shima yashiga mota yai na g'ida. "tun daga lokacin soyayya mai karfi ya shiga tsakaninsu kullum cikin msrarin juna suke da dakin gani juna dan ma duk su biyun iyayyansu na take masu birki. "komai zahradee ya samu na Aisha ne tun mafaifinta yana hanata amsa idan ta kawo abu tace zahradee ne ya bata sae abbanta ya hauta da fada' idan zahradee din yazo da kansa yake daukar kayan ya meda masa dasu' duk irin fsdar da zaiyi bazaisa zahradee ya amshi kayan ba. "zannuwa kuwa adon nida abuna akeyi duk wasu sabbabin yayi idan bbn zahradee ya kawo saeya cirewa Aisha a ciki' gani aiyuka suna masa yawa baya samu zuwa gun Aisha sosae yasashi siye mata waya ya bata a cewarsa idan besamu zuwa ba zai kirata ta wayar surinka hira. "boye wayar tai basu bari abbnta yasa tanada waya ba' daga ita sae mmnta suka sani' idan har zahradee zai kira sae dae lokacin da abbnta baya g'ida ko k'uma lokacin suna dadinsa shida umma suna hira snn zahradee zai kira suyi hira'gudun kada abba yaji ringing din wayarne yasa tasashi a silet wani lokaci sae yaita kira har ysgaji bata daga ba sbd ba'ajin ringing din wayar. "duk lokacin da zahradee ya kira Aisha bata daga ba zahradee yana shiga cikin damuwa sosae amma daya samu lokaci yazo hira shine yake tambayarta dalilin h'akan' Aisha tai masa bayani tun daga lokacin ya daina damuwa k'uma ya rage yawan kiran da yakeyi mata' a cewarsa idan tananan lfy shikenan. "kwanci tashi babu wiya a gun ubangiji su Aisha ana shirin zana weac duk yawancin student su biyu amma banda Aisha' sbd tunda ta sanarwa abbnta besake cemata komai akai ba' itama bata sake tutubarsa da mgnr ba' shiyasa yau da taje school aka koreta ta dawo g'ida. "sbd takaici ko shiga napep batayi ba haka tai ta cin kafa tana tafiya' dan kwata2 basufi su biyar ba da'akewa mgnr kudin duk yawancin student su biya. "Tana cikin tafiya kamar daga sama taji ana jawo mata school bag ta baya' da sauri ta juya dan gani ko waye' juyawar da zatayi zahradee ta gani yana mata murmushi' wasu hawaye ne suka zubo mata. "Da sauri ya hadiye dariyansa h'ade da tambayar lfy Aisha? Hawaye da suke zubo mata ya hanata yi masa bayani. "Gani a bakin titi suke yasa zahradee rike mata hannu zuwa gefe snn yace lfy Aisha ta waye ya bata maki rai? Aisha tace babu komai' zahradee yace banyarda ba' babu komai shine kike kuka? Aisha kodae matsayina bakai na kisanar dani damuwarki bane?. "a'a ba haka bane. "In ba haka bane to menene? "Shiru tai kanta a kasa. "tsareta yai da ido yana sauraran abinda zatace' gani tai shiri batada niyar fadi yasashi cewa shikenan Aisha tunda banida matsayi da kima a gunki da har zanga kina cikin damuwa na tambayeki' ni natafi. "sa kai yai zaitafi da sauri Aisha tace dan Allah katsaya' idan na tsaya me zanmaki tunda ban'iso naga kina cikin damuwa na tambayrki ba. "Shiru Aisha tai har yakare snn ta fara da ida-ida h'ade da wasa da yatsun hannunta. "daga nan ne tazare komai ta fadi mata' zahradee yace shine yasaki shiga damuwa? To yanxu abinda nakeso dake shine kishare hawayenki snn sae muje school din naku. "Sae da ta share hawayenta tsaf snn ya tare masu napep yace a kaishi school din su Aisha' suna tafe suna hira' amma a nasa zuciyar cewa yake wlh yau duk yadda abba zaiyi dani Sae dae yayi'idan wlh da kudinsa zanbiyawa Aisha kudin makaranta. "suna isa suka sauka ya baya mai napep snn suka karisa cikin school din' office din principal Aisha ta kaisa' bayan sun gaisa ne zahradee yake tambayar nawane kudin da zaisa a kori Aisha a school. "principal yace ba masu yawa bane 53,750 ne kawai. "jin among din yasashi hadiyar yawo da karfi' shidae har ga Allah yasan bashi da sisi nashi na kanshi sae na abba dake hannunsa akan yaje yasa masa a cikin account dinsa' gani yai shiru yasa principal cew malam yah dae? Faskewa yai h'ade da cewa babu komai nawama kace? Yace 53,750' a zuciyar zahradee yace jarrr uba' wlh yau duk yadda abba zaiyi dani sae dae yai amma wlh saena biyawa Aisha kudin school din nan. "haka ya ciro naira dubu dubu babu ko chaji yabawa principal. "amsa principal yai h'ade da godiya. "shima zahradee godiya yai h'ade da mikewa suka fita' sae da Aisha ta rakashi har bakin gate din school din tai masa godiya snn ta koma ciki'. "shima daga nan kasuwa ya nufa sbd babu mgnr zuwa wani bank kuma tunda ba kudin. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W. ☘. MMN USWAN 1⃣4⃣ "zahradee yana hawa napep be tsaya ko'ina ba sai kasuwa gun bbnsa. "yana isa ya biya me napep kudinsa snn yakarisa cikin shagon' yana shiga bbnsa yace har kasa kudin? halan yau bank babu queue ne? "Eh" kawai zahradee yace h'ade da susa kansa. "yace yanxu kasa ko tun dazu? "Shiru zahradee yai. "zahradee da kai fa nakeyi. "Nan zahradee yafara inda inda. Cikin dimaita yace tun dazu. "okay kawai alhj Kailani yace' daga sann yace gaba da uzurinsa. "Itako Aisha ba karami dadi tajiba' duk da tasan kudin ba yafi karfin mahaifinta bane amma taji dadin h'akan da zahradee yai mata' sbd ya taimaketa a lokacin da take bukatar taimakon. "duk irin bayani da uncle keyi masu Aisha bata san me yake fadiba sbd ta fada duniyar tunani' seat mate din tane ta tabeta h'ade da tambayata da Aisha wht 're u think about? "Cikin gigita tace nothing. "okay kawai tace. "Da dare bayan su zahradee sun dawo daga kasuwa' suna cikin hira sae mgnr kudin ya fadowa alhj' nan yasa cewa so har yanxu fa banga alert ba' ace har yanxu matsalar network ne? "Nan zahradee yace dan Allah abba kayi hakuri". "A kan mefa son? "Wlh abba a gaskiya amfani nai dashi. "Cikin rashin nuna damuwa abba yace son me kai dasu? "zahradee yace wlh abba lokacin da ka aikeni bank ina kan tafiya kenan da yake a kafa nake shine na hadu da Aisha tana tafe tana kuka' ni kuma gani halin da take ciki yasani tsayuwa na tambayi ko lafiya' shine take sanar dani cewa koranta akai kudin weac kuma cikin week dinga za'a rufe idan bata buyaba shikenan' ni kuma gani haka yasa nai amfani da kudin da ka aikeni na biya mata. "kafin abba yace komai su yya shamsudee da Nurudee suka haushi da fada' h'ade da cewa bazan kawai mara wayo waya sanima ko ba rabonka bace ita' kaje kana faman wahalar da kanka a kanta' b'ude baki yai zaiyi ngd da amma!. "shamsudee yace amma me wlh idan kai wani mgn saena mareka' in kuma kana gani kamar karyane to ka gwada. "Gani duk sun taso masa yasa abba dake zaune dakatar dasu' hannu kawai ya nuna masu alama su bashi gu. "duk mikewa sukai sukabar masa gun. "bayan sutarsane abba yace zahradee. "na'am abba. "wlh zahradee wannan inaso yazama shine farko k'uma shine karke' wlh zahradee inda wani daga cikin yan'uwanka ne sukai min h'aka na wlh da sae sun bayani kuduna' amma sae yazamanto kaine' kae waya cemaka ana h'aka ma? "itace tace kama iyayenta basuda kudin biya mata school feel ko mai? "A'a abba' nine dae kawai. "to kada kakara' idan k'uma kakara wlh saena hukuntaka. "nagode abba in Allah ya yarda bazan karabama. "to shikenan. "Da yamma bayan bbn Aisha badawo daga kasuwa suna cikin hira da ummanta shine umma take sheda masa da cewa zahradee ya biyawa Aisha kudin weac. "Nan alhj muhmmed ya hau fada inda yake shiga ba nan ne yake fita ba daga karke yace takira masa Aisha tazo. "mikewa umma tai taje dakinsu ta kirata sukazo tare har kasa Aisha ta duka snn tace gani' alhj yace wato Aisha irin sakayyar da zakinmi kenan ko? Yanxu sbd Allah abinda kikai yadace kenan? "Cikin sanyin murya Aisha tace abba wani laifine nai maka? "Aisha ba laifi kikai min ba amma sbd Allah har abin yakai ga kije ki roki zahradee yabiya maki kudin weac?. "Cikin kuka Aisha tace roko k'uma abba? Wayace maka rokonsa nai? Wlh abba ni ban rokeshi ba' shine dae yai niya ya bayamin kudin' idan ma kana gani kamar karyane wlh abba ka kirashi ka tambayeshi kaji. "Alhj muhmmed yace Aisha ni bance kina karyaba ba sbd tun farko bansanki da karya ba ' amma abinda nakeso ki fahimta idan har yar' uwansa sukaji labarin h'akan gani zasuji kamar nakasane' Aisha kifi kowa sani idan a kankune abinda ya kama daga 1 naira zuwa million idan akan school ne ni me kashe makune' k'uma kifi kowa sani banaso rainin wayo' idan har sukace zasu rainamin wayo akan h'akan wlh bazan dauki walakanci ba. "Shiru Aisha tai har yakare mgnr sa snn tamike batare da tace masa komai ba. "AFTER 5 MONTH "Su Aisha suzana weac dinsu cikin sa'a k'uma paper su yai kyau' gani sun samu sakamako mai kyau k'akan yasa abba ya nima mata diploma dake cikin garin bauchi' da yake yanxu wani irin lokaci ne da muke ciki wanda idan kanada abin hannu komai zakayi a doran kasa' karma ace kasarmu NIGERIA. "hakan yasa besamu matsala ba wajan nima mata addmi' yana zaune a gida aka gama masu komai' attanding lecture kawai tafara batare da tasan wahalar komai ba. "tana karatune a bangaren business' koda Aisha ta sanar masa da mgnr samu school dinta yai murna sosae sbd a yadda yai lisafi mgnr bikinsu zaizo masa daedae da lokacin da yake so. "dinkuna yai mata sosae da siyayya a cewarsa yanxu zata fara harkan big girl dole saeda manyan shiga sbd gudun rainin wayo. "Aisha tai murna sosae da zahradee ya kaimata kayan gidansu. "Ranar monday Aisha tafara attanding lecture. FANS KUYI HAKURI NA RASHIN JINA KWANA BIYU WLH EXAM NE YA BOYENI AMMA YANXU NA GAMA SAE JIRAN SAKAMAKON. ZAKU RINKA JINA KULLUM KODA BAMAI YAWABA. NAGODE SOSAE ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W. ☘. MMN USWAN ZANYI AMFANI DA WANNAN DAMAR WAJAN TAYA YAR'UWATA ZAINAB SHU'IABU MARUBUCIYAR YARAN MIJUNA MUNAR KAMMALA LITTAFINTA HAKIKA KIN WA'AZARTAR KUMA KIN NASHADANTAR KIN BAJE KOLINKI WAJAN NUNA FASAHARKI. KUKA KURAN DA KIKA SAMU ACIKI ALLAH YA YAFE DARANSAN DA AKA DAUKA A CIKI ALLAH YABADA IKON AMFANI DA SHI. 1⃣5⃣ "Cikin sa'a Aisha tafara karatunta k'uma alhamdullh sbd duk yawancin lecture din da ake masu tana fahimta sosae' idan ma bata fahimta ba idan zahradee yazo hira in har ta sanar dashi zama suke sosae yaita yimata bayani har sae ta fahimta snn zantafi g'ida. "Itama Aisha dayake tanada brain shiyasa da zaran yai mata bayani take dauka. "zahradee ya taka rawar gani sosae wajan karatun Aisha' duk da shima mahaifinta ba baya ba amma da h'aka zahradee yaci gaba da yimata hidima wani lokaci shiyake kaita school' idan h'akan besamu ba suna tashi lecture zaije ya daukota da motar abbanshi. "Alhj Kailani yai f'ada har yagaji amma duk a banza' gani h'aka yasa alhj sakarwa zahradee motar' shikuma ya siye wata. "shima zahradee yana kammala project din sa aka turashi service a kasar kudu IMO state amma abinda dan NIGERIA idan kanada hanya h'aka alhj Kailani yashiga ya fita aka barshi a nan bauchin yai service dinsa. "Da h'aka zahradee yake raba kansa biyu sbd yana tashi daga aiki yake zuwa kasuwa gun bbnsa' sbd zahradee yanada wani abu daya duk yadda zaiga harkan kasuwanci abbansa sae yayi h'akan yasa abba ke matukar sonsa. "Gani Aisha tayi nisa da karatun yasa zahradee birgewa abbnsa a dole shifa sae dae aje g'idan su Aisha a nemo masa aurenta tunda tayi nisa da karatun kusan aiya cewa ma kadin yarage mata. "Duk yadda alhj yai dan yashawo kan zahradee akan yabari har takare amma zahradee yaki. "Sbd zahradee gani yake kamar bazaikai lokacin ba' ko k'uma idan lokacin yai Aisha tace bata sosa. "Da yaga kamar alhj bashi da niyar tafiya nimo tasa auren Aisha yasa damuwa idan ko kasuwar da yake zuwa ya dae na' idan yafita aiki tun safe baya dawowa g'ida sae dare yana shiga kai tsaye dadinsa yake shiga ya rufe kofa batare da ya tsaya parlour hira da yan'uwa ba. "Ba komai bane yasa alhj yaki tafiya nimawa zahradee aure ba so yake saeya kare gini da yake masu shida yayyinsa sbd bayaso su zauna gun daya da sirikansa yafiso suyi nisa da juna' shiyasa beje nimawa zahradee auren Aisha ba' yafiso idan ya kammala a lokacin ne da kanshi zai daukesu ya kaisu gun sugagi snn sae yatada mgnr bakin. "Amma rashin sani da yafi dare duhu yasa zahradee yakewa mahaufinsa h'aka sbd duk a ganisa ba nima masa aure Aisha ne za'ayi ba. "Gani yadda zahradee yashiga damuwa sosae yasa abba da kansa yabi zahradee har dakinsa' lokacin zahradee yana zaune ya tasa wayarsa a gaba yana kallon pict din Aisha' har alhj ya shigo zahradee besani ba. "gun yasamu ya zauna h'ade da sa hannu ya tabo kafadar zahradee snn ne zahradee ya dago kansa' gani abbnsa ne yasashi cewa abba yaushe ka shigo?. "murmushi abba yai h'ade da cewa son kenan pict din sirikan tawa ake kallo h'aka? To nima abani naga sirikansa tawa. "murmushi zahradee yai h'ade da susa kansa' batare daya tanka ba. "hannu yasa ya amshi wayar saeda ya karewa wayar snn yace sirikan tawace h'aka? Lalla kam dole dana ya rikikice ya rinka fushi dani sbd naki tafiya nima masa auren ta. "jin h'aka yasa zahradee daure fuska. "murmushi alhj yai snn yace zahradee. "Cikin karkashin murya yace na'am abba. "Alhj yace ba naki tafiya nima maka auren Aisha bane kawai h'aka akwai wasu aiyuka da nakeyi ne nafiso idan nagama snn na sanar daku snn k'uma na nima maka auren. "juyowa yai snn yace abba wani irin aikine zai hanaka nimami aure? Aikin da kikeyi ya shafi mgnr aurena da Aisha ne kome? "himmm abba ni tun ba yanxu ba tuni nariga na gano kawai dae baka sona da Aisha ne. "Subbuhanalillah son kada kaimi mumunar fahimta wlh har ga Allah ba nufina ba kenan son. "abba inba nufinka ba kenan abba to menene a zuciyarka? Abba kana gani tunda Aisha tafara doploma din nan samari suke ta kawo mata hari' idan ma Allah yasa tana sona' wlh da ba dan son da takemin ba nasan da bazata kuni ba sbd ba kananun mutum bane suke zuwa gun ta' harda manyan attajirai. "murmushi kawai alhj yai. "Gani irin murmushin da abba yai yasa zahradee cewa Allah kuwa abba. "Alhj yace son kenan' ba komai ne bane nakeyi illa gani ne nake yimaku kaida yan'uwanka wanda idan kunyi aure zaku zauna a ciki sbd banaso mu zauna gu daya daku a cikin g'idan nan... " abba idan akan inda zamu zauna ne abba ni inada kudin da zai'ishemu nakama haya har kakare mana gini. "mikewa zahradee yai yazo gaban alhj ya duka har kasa snn yace abba dan Allah dan annabi idan soyyayar da kakewa shugabanmu annabi muhmmedu (S. A. W.) abba ka taimakeni ka taimaki rayuwata kaje ka nemamin auren Aisha' wlh Allah abba ni kaina bansan irin sonda nakewa Aisha ba' idan har narasa Aisha a rayuwata abba zanshiga wani hali abba. "Shiru alhj yai yana me jijina mgnr zahradee. "can yasa hannu ya dagosa ya zauna snn yace son karka damu insha Allahu gode da yamma zantura kawunka da bbnka habu suje nima maka auren Aisha... "wani irin tsanle zahradee yai h'ade da rungume abbnsa yana murna. "abba yace saurareni d'kyau kaji abinda zanfadi maka' zahradee. "na'am abba. "zantura a nimo maka auren Aisha amma da sharadi' kudi da kake mgnr kama haya dasu zaka bani na karisa maka gini bangarenka dashi. "abba na amince bari yanxu nai maka transfer dinsu zuwa account dinka. "murmushi kawai alhj yai ya fita. "washe gari da yamma bayan sallar la'asar dayake ranar saturday koda sukaje bbn Aisha yana g'ida beje ko'ina ba' koda sukasa akai masu sallama dashi tare suka fito da dan'sakon' gani manyan mutunine yasashi karisawa da sauri gusu suka gaisa. "bayan su gaine alhj muhmmed yace gashi be sheda kusa ' daya daga cikin su yace alhj Kailani me zannuwa ne ya turomu. "jin h'aka yasa alhj yasasu sake gaisawa snn yai masu iso zuwa parlour sa' a take yasa aka kawo masu abinci dasu juice da ruwa. "hada hannu sukai sukaci bayan su gamane snn sukace dama alhj Kailani ne ya turomu nimawa dan'sa auren yar'ka. "Alhj muhmmed yace kai madalla abu yai kyau kaga dama kadan yarage mata ta kammala karatun da takeyi. "nan dae suka daedae ta alhj muhmmed yace dama DEC ne zata kare tana karewa JANUARY sae ayi bikin kawai a huta. "suma suyi marna sosae dajin h'aka. "Sae da suka dan jima suna tattaunawa snn sukai sallama. "koda labari ya'iske zahradee ba kasamin murna yai ba' h'ade da hamdalla yana mika godiyar sa gun ubangiji. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA WRITERS F.O.W.☘. MMN USWAN 1⃣6⃣ "Yana gama murnarsa ya dauki wayarsa ya kira Aisha' wayar yai ringing har saubiyu bata daga ba sbd bata kusa DA wayar sae a na uku snn taji ringing din wayar a guje tazo ta daga h'ade da sallama. "Zahradee yace hello my Aisha ta'kina inane nake ta kira baki daga ba? Aisha tace Ina kitchen ne nida umma muna aiki shiyasa ban daga ba. "Ayya yaya umman take?tana lfy? "Klau. "Aisha ta. "Na'am. "Nasan kisan komai basae na f'adi maki ba ko? Na fa? Mgnr aurenmu mana Aisha. "Himm zahradee kenan kaedae wlh kacika gaggawa. "Gaggawa fa kikace Aisha' eh ma naji idan a kankine'kenan bari ma kiji wlh a yadda nakeji banki ace yau an daura mana auren ba' idan yaso sae ki karisa karatun a gida na. "Uhm" nidae banyarda ba' h'aka kawai sae anzo anyi kahanani karisawa' nidae nafiso na kammala snn koma menene sae ayi. "Himm'aisha kenan dan bakisan yadda nake jinki a zuciyata bane yasa' wlh Aisha nafi kowa son naga kinyi karatu'koda bakiyi aiki ba. "Eh" dae naji' nidae saena kare snn. "Aisha ki kwatar da hankalinki nima mgn kawai nakeyi' ko tsaida watan bikin ma da akayi shima abin farin cikine aguna'fatana kawai Allah ya nuna mana lokaci darai da lfy. "Shiru tai tana murmushi. "Kiran umma ne yasata kashe wayar taje a guje. "Tun daga lokacin g'idan su zahradee suke ta shirye2 shima Alhj Kailani gani yanada wasu kudi a hannunsa yasashi tada gini gaba daya kawai' a cewarya gara ayi a huta gaba daya. "Ranar wata asabar su Aisha batada lecture tun safe umma tace zata aiki Aisha G.R.A. g'idan wata kawarta Hjy madina amso wasu kaya da tasata siyo mata idan taje DUBAI' Hjy madina tare suka tashi da hafsatu tun suna yara'shidama rayuwa ta gaji h'aka fini ubane na fiki miji' amma duk da h'aka akwai kyakykyawar alaka a tsakanisu. "Aisha ta amso sakon da ummanta tai mata' tafito kenan daga g'idan tana tafe sakamakon ba kasafai ake samu napep a street d'inba' h'akan yasata tafiya a kafa' har takusa fita daga street din kawai ji tai kamar daga sama aka janyo mata kyalen da tarufe kanta dashi. "A gigice ta juya dan gani waye yai mata irin wanga aikin. "Wani kyakykyawar mutune tagani tsaye a gabanta sanye cikin English wear blue jeans da white T.shirt yana yimata mirmushi' a sanyaye tace malam lfy? Me nai maka da zaka rikemin kyaleta. "Murmshi yai h'ade da cewa allahamdullh Allah Kaine abin godiya'gaskiya inada sa'a a rayuwata sbd duk inda naje cikin sa'a nake' yau gani a garin bauchi kuma da abin kaunata. "Yan'mata ya sunaki? K'uma wacce uguwa kike? "Shiru Aisha tai takasa mgn. "Au yan'mata tsorona kikeji? Kinga daga fuskanki kiga wani abu. "Kin dagawa tai. "Wlh idan baki daga na f'adi maki abinda zanfadiba da kaina zansa hannu na daga maki fuska da kaina. "Jin h'aka yasa Aisha tsorata' gashi area babu kowa daga ita saeshi na uku su shine Allah' k'uma yadda take ganisa tasan komai zai'iya. "Gani jikinta ya fara rawa'yashi kara daure fuskansa. "A hankali Aisha take dago fuskanta' shikuma dake tears zuba mata kwala kwalan idanusa yai' yana jira ta dago fuskanta. "Tana dagowa gani zasu h'ada ido da sauri ta dauke fuskanta daga nasa. "Wani irin dariya yai h'ade da tsalle yana kiran yan'mata ran gari' gaskiya kinada abin birgewa fa' wlh nayi sa'ar mata. "Idanu Aisha suka ciko da kwalla'a sanyaye tace Dan Allah kabarni natafi kada ummata taga na dade taimin f'ada. "Kai alhamdullh naji dadi da samo uwa ta gari irin ummata Allah ya kara mata tsawonrai da lfy mai amfani. "Shiru Aisha tai. "Bazakice amin ba. "Can karkashin murya tace amin. "Yace banji ba. "A lokacin ne tace amin a pili. "Yawwa ko kefa' h'aka kawai naiwa ummata addu'a k'uma kiki cewa amin? Yanzu f'adimin sunanki'kinji yan'mata. "Bakin Aisha na rawa tace ni banida da suna. "Juyawa tai zata tafi'da sauri ya fisgo jakar dake hannunta h'ade da cewa wlh idan baki f'adimin sunaki ba wlh babu inda zaki. "Aisha tajin h'aka tace ni sunana Amina. "Dariya yai snn yace daga gani wanga kyakykyawar bakin naki besaba da karya ba' shiyasa a yanxu ma da zakiyi karyan yake rawa. "Bazan tilassamaki ki f'adimin gaskiya ba' amma inaso kisan cewa nasan ba gaskiya kika f'adi ba. "Shiru Aisha tai tana mgn kasa kasa. "Gani yadda bakinta ke motsi yasashi cewa lahhhh! Zagina kikeyi ko? "DA sauri Aisha tace ni wlh ban zagekaba ko sa'ata bana zagi banle kai da girmanka'ni tun ina yar'karamata ummata ta hanani wasan zagi banle yanzu da nai girma. "Good kawai yace' gani yamma yayi yace bari nabarki kitafi g'idan kodan taya immata aikin abinci. "Amma kafin nabarki kitafi sae kin f'adimin uguwarku. "Gani idan ba karyan tasake yimasa ba ba zaibari ta tafi gida ba' matsewa tai tace gun central mosque g'idan mu na kallon masallacin ne. "Okay yace da saekin gani' k'uma ki gaidamin ummata. "To kawai tace a guje ta bar gun. "Gani yadda tasa gudu tabar gun yasashi dariya. "Kwanci tashi babu wiya su Aisha har ta kammala karatunta' yanzu da h'aka gun g'ida biyun shirye shirye kawai sukeyi an tsaeda rana 23 March sbd murna zahradee rasama yadda zaiyi yai. "Alhj Kailani ya gyarawa zahradee g'ida tsaf abin sae son barka komai na g'idan irin dayane da fyantin g'idan hatta furniture da labulaiyan g'idan iri daya ne. "Gun kawarta ubaida taji labari result dinsu ya fito yasata cewa itama zataje duba nata'bayan takare aiki tai wanka ta shirya zuwa school dinsu' Batare da bata lokaci ba taje ta duba'gani yadda G.P.dinta yai low yasa ranta baci. "H'aka tafito daga school din tana share kwalla'ji kawai tai ance ke yan'mata yau Allah yakaminke cikin sauki. "DA sauri Aisha ta juya'gani mutunmin ran nan ne yasata tsaki. "Durowa yai daga kan motar da yake zaune yasha gabanta. "Gani kwallane cike da idonta yace subbuhana lillahi lfy? Cikin muryan kuka Aisha tace yanzu sbd Allah duk irin kokarin danai wajan hana idona bcc nai karatu k'uma bama hakaba saeda nazo karke shine zasumin h'aka? "Mutumin yace me k'uma akai maki? "Aisha tace tunda nafara karatu bantaba samun carry over ba k'uma G.P. dina 3.1ne bayan ace yafi h'aka sbd Allah saeda nazo karewa shine zasuce yadawo 2.99 statement of result dina. "Wow! yau mean at shis your age kice kin gama diploma? Congrats" gaskiya nasarawa abbana. "Yan'mata be happy about your result, it's a good attempt. "A lokacin ne Aisha tad'anji dadi a zuciyarta' juyawa tai zata wuce batare da tace masa komai ba. "Ji kawai taji yace' Can I have few of your time pls. "Okay kawai itama tace. "Snn yaci gaba da cewa duk da nasan ba sunan ki ta gaskiya bane amma tunda ke kika bani bari nakiraki dashi h'aka. "Kunyane yakama Aisha'mayafin dake kanta ta rufe fuskanta dashi. "Yace Amina nagode sosae da wahalar da kika bani' amma abinda nakeso dake shine dan Allah kidaena karya sbd be kamaceki ba' k'uma nasan ba tarbiyar dasu abbana suka baki ba kenan. "Dan Allah kidaena sbd kada ki zubar masu da mutunci' kinsan idan yaro yai abu mara kyau akance daga g'ida yakoyo'nikuma nayi imani wann ba koyarwan su Abba da umma bane. "Jikin Aisha yai sanyi tace to kayi hakuri'in Allah ya yarda bazan karaba. "Murmushi yai snn yace to yanzu f'adimin inane uguwarku? Doruwa kana shiga uguwar hannu dama g'ida ta uku nan ne g'idan mu. "Allah yasa yau d'inma ba wata karyan aka zuba min ba. "Batare daya yatsaya tambayarta ba' ji kawai tai ya fisgo wayar dake hannunta yasa number sa anata yai plashing nasa' snn yai seving number sa a nata yasa Nasir Mai guduma' snn yamika mata wayar h'ade da cewa sae nazo. "To kawai tace snn tafara tafiya' tana tafe tana juyi tana kallonsa. "Gani zata f'adi yasashi cewa sarkin gudu yau ba gudun k'uma sae yayge yayge. "Jin mgnr da yaine yasa bata sake juyiba. "DA yamma bayan 5 PM saega Nasir a kofar gidan su Aisha ta waya yai kiranta' gani zata fita yasa umma tace Aisha Ina zaki? "Wlh umma wani mutum ne yake kirana' daga ina kuma yake Aisha? "Wlh umma nima bansanshi ba' kuma daga ganisa ba yaro bane. "To Allah ya kyauta jeki ki ganshi. To umma. "Tana fita kai tsaye gunsa ta nufa da sallama. "Cikin girmamawa ta gaidashi' shima da fara'arsa ya amsa. "Snn yace da farko dae sunana Nasir guduma Ina zaune a cikin garin argugune nida iyalina'matana biyu amma ban dade da kara na biyunba idan kin yarda inaso na kara dake ana uku'yan'mata idan har kika amince kika aureni'ni Nasir nayi maki alkaewari da tanajin jin dadi da kwanciyar hankali a gidana. "Kiyi hakuri sbd nasan a ciki zuciyarki zakice nacika dadin baki ko? Ko kuma kice natara mata bazaki samu kulawar daya dace ba a g'ida na ko? "Shiru Aisha tai takasa hada ido dashi. "Nasir yaci gaba da cewa wlh idan har kika yarda kika aureni wlh zanbaki kulawar da bazaki samu agun yaro ba' yan'mata kada kiganni h'aka kiyi tunani na girma wlh girman jikine kawai. "Amma bari banari naji ta bakinki ko. "Kan Aisha na kasa tace to naji amma Dan Allah kabani nan da jibi zanyi shawara. "To yanzu f'adimi sunanaki. "Murmushi tai snn tace Aisha. "Nice name' suna me dadi'. "Ni zantafi umma tace kada na dade. "Okay Dan Allah ki gaidamin dasu umma da Abba. "To zasuji ni nashige sae anjima. "Ngd Aisha'nan sukai sallama tashige gida'shima yatafi. ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F. O.W.☘. MMN USWAN 1⃣7⃣ "Aisha na shiga cikin g'ada'umma tace Aisha har kindawo? Eh umma nadawo' umma tace wayene yazo gunki d'in? Wani mutum ne umma' amma dae lfy ko? "Eh' kawai tace' da sauri takarisa cikin d'akinsu. "Itama umma gani yamma yayi idan tatsaya mgn zata iya makara' h'akan yasa taci gaba da aikin g'abanta bata sake bi takai Aisha ba. "Aisha na shiga d'akinsu daega kiran Nasir yashigo' koda ta daga wayar gani number Nasir yasa bata ta meda wayar ta'ije a gefe. "Duk da h'aka Nasir bedae na kiranba'gani yana niman tona mata asiri yasata sa wayar a silet yai ringing har yagaji bata daga ba. "Tana shirin mikewa kenan sbd kiraye kirayen sallar magrib da akeyi sae ga text message yashigo. "B'udewar da zatayi sako tagani kamar h'aka. "Allah ya huci ran gimbiyar tawa' da fatan ba nine na bata maki rai bako? To idan ma nine ga gwiwata bibbiyu a kasa ina niman tuba' a yafemin. "Duk da ba ganita yake ba'wani irin murmushi ta sakan ma wayar dake rike a hannunta. "Snn ta rubuta masa reply da cewa a'a babu wani kawai dan bana kusane yasa. "Snn tai sending text d'in. "Yana b'udewa'bayan yagama karantawa' alhamdullh kawai ya rubuta h'ade da saenazo jibi' snn ya tura mata. "Koda tai receiving text d'in tana gama karantawa ta'eje shi gefe. "DA yamma bayan sallar isha'i Aisha na zaune ita da Abdul kaninta suna hira saega kiran zahradee yashigo' gani number sane yasa Abdul sauri sa hannu zaidaga wayar. "Daure fuska Aisha tai snn tace kada ka dagamin waya. "Anty zahradee nefa. "Dan zahradee ne sae me? "Anty kenan' halan yau wanine ya bata maki rai? "Bazan dashi tai bata tanka masa ba. "DA h'aka zahradee sae da yai 5 miss call amma Aisha bata daga ba. "Har zahradee zai'ije wayar gani dare yayi banle yaje g'idan su aisha k'uma gashi bayajin bcc kawai sae ya h'au online d'an rage lokaci' yana h'au Aisha yagani k'uma da'alama tp takeyi. "Shima tura mata da hello. "Koda tagansa kin tanka masa tai. "Duk da h'aka besa zahradee yai fushi ba' h'aka yasake tura mata da sallama. "Karab hannunta ya d'anna gun sako daya tura mata. "Gani hello h'ade da sallama yasata hyyyy. "Zahradee yace my aisha Dan Allah kiyi hakuri na rashin zuwane kwana biyu wlh wasu aiyukane sukasha kaina shiyasa amma dan Allah kiyi hakuri'sbd nasan kiyi fushi dani na rashin zuwa kwana biyu ko. "A'a ba h'aka bane. "To menene my dear?. "Kawai dae banji dadi b'ane that is why. "Ayya my dear' I wish you quick recovery may Allah see you through, on ur healthy. "Ameen ngd tace. "tomorrow I'II cme nd check you to see hw you feel. "Aisha ta meda masa da reply da' known need of your coming I'm getting better. "Alhamdullh yace but still I'II come'bekamata ace bakida lfy banzo na dubaki ba' gobe in Allah yasa mukai zanzo. "Aisha na gani h'akan rufe data tan tai h'ade da kashe wayar gaba daya. "Koda zahradee yaji shiru bekawo komai a zuciyarsa ba sae tunanin ko caji ne ya'kare' h'akan yasashi s'auka ya kwanta. "Da safe misalin goma zahradee yaje g'idan su Aisha har ciki yashiga da sallamarsa' ummace ta amsa'h'ade da cewa waye? Zahradee yace nine zahradee' umma tace bimillah. "Snn zahradee ya karisa cikin g'idan' cikin girmamawa ya gaidata h'ade da tambayar me jibi. "Da mmki umma tace me jiki k'uma? Aina? "Zahradee yace Aisha mana. "Umma tace Aisha k'uma? Eh umma' itace tace maka batada lfy?" Shiru zahradee yai yai yana murmushi. "Kwadawa Aisha kira tai da cewa fito nan' dama itama a makale take a bayan kofa tana jin duk abinda sukeyi. "Sae tasa hijab snn tafito tace gani ni umma. "Umma tace dama bakida lfy ne shine bansani ba? Shiru tai h'ade da daure fuska' umma tace dakefa nakeyi Aisha. "Zahradee dake duke yace a'a umma kilan jikin be matsa mata bane shiyasa bata sanar dakuba' mikewa yai h'ade da cewa umma ni natafi. "Umma tace ka gaida iyayen naka. To kawai yace. "Yana gaba Aisha na baya suka fita waje' bayan sun fitane zahradee yace h'aba aisha meyasa kikeso dauko wasu dabi'u wadda bansanki dasu ba? Aisha tunda nake dake sama da shekara nawa bansanki da karyaba' amma gashi yanzu kinfara yi. "Aisha kodae akwai wani abune a zuciyarki? A'a' to f'adimin menene ke damuki? Idan yaso sae mutafi asibiti. "A'a kabari kawai nasamu sauki. "Aisha kodae wanine ya bata maki rai. "A'a". "Nine nai maki laifi? "A'a" "Su umma ne? "A'a" "To dan Allah idan ma nine kiyi hakuri' kinsan idan aiki yazo g'aban goshi yafi zafi' k'uma kinsan mundu zata aikata abin alkairi sae ka daure'sbd shedan zaiyi ta kawo nakasu akai. "Banlema kwana nawa yarage mu kasance tare na har abada. "Shiru kawai Aisha tai h'ade da daure fuska. "Gani yadda ta daure fuska yasa zahradee cewa h'aba duk cikin fushine h'aka da daure fuska? Gaskiya nidae a sakarmi fuska ko zanji dadi. "Yadda yake yimata yasata dariya. "Daedae kunnita yazo snn yace kokefa har kinyi kyau. "Murmushi kawai yakarayi masa. "Snn yace ina zuwa. "Mota yakoma yaje ya dauko wata karamar jaka yadawo snn ya mika mata h'ade da cewa gashi kiyi hakuri babu yawa. "To kawai tace. "Snn yasa hannu cikin aljihun rigarsa ya ciro kudi yace gashi wann na katine sbd nasan yanzu wanda nasa maki yakare ko? "Eh basu kare ba. "To babu damuwa ki rike ko zaki bukaci wani abu. "Shiru tai batare da tace nagode ba. "Zahradee yace ni zantafi Abba yana jirana mutafi kasuwa. "To tace'snn tace sae anjima' shigewa tai batare da tatsaya sunyi sallama ba. "Ido kawai zahradee ya zuba mata har tashige ko kibtawa beyiba. "Jikin zahradee yai sanyi sosae sbd ziciyarsa tana raya masa abubuwa kala-kala akan Aisha' can yaji gabansa yai mummunar faduwa. "Innalallahi'wainna'ilaihi'raju'un kawai yake ambata a bakin sa.. "Da kar ya'iya jan mota zuwa g'ida. "Yana isa Alhj Kailani yace son tuntuni nake jiranka k'uma kaje kai zamanka' ido kawai zahradee ya zuba masa' Alhj yace son lfy k'uwa na ganka h'aka? "Kai kawai ya kada h'ade da cewa banji dadi ne shiyasa. "Amma bayan fitarka ne ciwon ya sameka ka ko? Son kodae mutafi asibitine? Murmushin karfin h'ali zahradee yai h'ade da cewa a'a Abba nasamu sauki ai. "Shiga motar Alhj yai h'ade da cewa son jamu muje. "Zahradee yace Abba bazan iya ba' subhanallah Alhj yace snn yace son muje hospital kawai. "A'a" Abba kabari kawai idan muka isa kasuwa zankwanta' maybe idan nasamu hutu jikin zaisakeni. "Alhj yace to shikenan son Allah ya saukake. "Ameen Abba. "Koda sukaje kasuwa babu abinda zahradee yai a kwance yake. "Duk a lokacin gabansa be daena bugawa ba. "Aisha na shiga g'ida umma ta kirata zuwa tai inda umma take ta duka har kasa h'ade da cewa gani umma. "Umma tace Aisha inaso kisan da cewa idan kinji ana cewa babban mutum ba sae lalla wanda yakeda kudi ba' ko mai matsayi ko d'an siyasa ba'a'a babban mutum yana nufi mai mgn daya' nidae bance lalla inaso naji tsakaniki da zahradee ba'amma inaso kisan cewa in har kika bari wata matsala tafara kunno kai daga gunki ba kekadae abin zaishafafa harda mu' sbd mafi yawanci kafin afara zaginki mune za'a fara zaki. "Dan h'aka Aisha duk abinda zakiyi kada kibari mutuncinmu da darajanmu ya zuba. "Tunda umma tafara mgn babu abinda Aisha keyi sae kuka. "Umma taci gaba da cewa yanzu sbd Allah Aisha ace bakida lfy shine bazaki iya sanar manaba sae zahradee? Ba mmki shidinma karya kikai masa' amma k'uma Aisha bansanki da karyaba'Aisha ina kika koyo dabi'ar da bansanki da'ita? Yanzu sbd Allah h'aka zakije g'idan miji kina masa karya ko Aisha? "Kai kawai takada. "Nan umma tai ta mata f'ada h'ade da nasiha. "Da yamma Aisha taje g'idan ubaida kawarta wanda tarigata aure harda yaranta biyu' bayan sun gaisa ubaida tace amarsu ta ango wlh Aisha ba karami dace kikaiba. "Aisha tace na mefa? "Ubaida tace Aisha kenan kifi kowa sani irin soyayyar da Bbn su Abba ya nunamin amma bekai irin naki da zahradee ba' ki dubafa komai yasamu kece. "Uhm" kawai Aisha tace. "Ubaida tace yahh! Dae Aisha? Kodae akwai matsalane. "Aisha tace wlh ubaida kwata kwata naji banason zahradee ko ganisa ma banasonyi. "Dariya ubaida tai h'ade da cewa kawata kenan dadina dake akwai son tsokana. "Aisha tace wlh kuwa ubaida ba wasa nakeyi ba. "Ubaida tace Aisha kina h'auka ne? Kodae gamo kikayi?kinsan idan kikaiwa zahradee h'aka baki masa adalciba ko? Fasawa da kuka Aisha tai tana f'adin wlh ubaida bana sonsa kwata kwata. "Ubaida tace h'aba Aisha Allah yakusan rufa maki asiri shine kike niman tonawa kanki' idan kince baki sonsa ke a ganiki akwai wanda zai'iya biyan zahradee abinda yai maki? K'uma kinada wani da zaki fitarne?. "Aisha tace eh. A gigice ubaida tace lfyrki k'uwa kodae h'aukane kika fara. "Banza da'ita tai. "Gani babu wasa a idon Aisha yasa ubaida canxawa daga wasan da takeyi nan tafara tambayar Aisha" itako Aisha babu abinda ta boyewa ubaida. "A gigice ubaida tace Aisha kanki daya kuwa? Wani lokaci ma ka auri saurayi ya kakare dashi banle mai mata har biyu kije ana uku. "To wlh Aisha bari kiji kibar gani duk irin sonda nakewa Bbn su Abba lokacin da yazomin da mgnr zaikara aure har addu'a nakeyi idan nazo sallah Allah yasa yana fita mota tai ajallinsa akawomin gawarsa yafimi da nagansa da wata mace' shine zakije ki h'auko wa kanki dala ba gammu. "Aisha tace kekika sawa ranki shiyasa nidae babu abinda yadameni dasu tunda Ina sonsa. "Ni barima natafi sbd banga zansamu mafita a gunki ba. "Ubaida tace lalla kam. "Fita Aisha tai babu ko sallama. "Mmkin Aisha yakama ubaida sosae. "Da yamma saega Nasir yakirata ta wayarta' lokacin umma na parlour Abba h'aka yasa Aisha samu hanyar fita. "Da sallama ta'isa gusa' shima yana ganita da fara'arsa ya tareta cikin girmamawa ta gaidashi' shima ya amsa. "Bayan sun gama gaisawane yace Aisha nazo jin sakamako nane'ina fatan Allah ya amsami addu'ata. "Cikin jin kunya Aisha tace babu komai na amince. "Nasir yace alhamdullh Allah na gode maka. "To yanzu yaushe zanzo naga Abba? Idan gaskiya a shirye nake. "Shiru Aisha tai snn tace kabani kwana biyu. "Nasir yace to shikenan. "Aisha tace zanshige sae anjima. "Batare daya tankataba hannu yasa cikin aljihu ya dauko bandir d'in five five hundred naira note yamika mata. "Aisha tace a'a kabarshi kawai. "Nasir yace idan ba rainawa kikai ba to ki amsa. "Hannu biyu tasa ta amsa hade da godiya' snn sukai sallama. "Aisha na shiga daga lungu tsayawa tai ta boye boye kudin snn ta karisa daga ciki'kai tsaye d'akinsu ta shiga da sauri sbd umma batasan da fitataba dama. "Tana shiga d'akinsu kyakykyawar buya taima kudin snn tafito. "Da dare zahradee yaso zuwa gun Aisha amma yanayin yadda yakeji ya hanasa zuwa'sbd ji yake kamar kirjinsa zai b'ude sbd azaba. "D'akinsu ya shiga ya kwanta snn ya dauko wayarsa dama number Aisha yana dialled call ne kawai d'an nawa yai' a lokacin na kwance tana f'aman tunani ta'ina zata fara? Kawai taji wayarta yana ringing. "Koda ta duba taga number zahradee ne tsaki kawai tai h'ade da juyawa wayar baya. "Zahradee yai kira yakai sau'biyu amma Aisha bata daga ba. "Gani bata daga ba yasa ransa sake baci' zubawa wayar ido kawai yai yana kallonsa' can wata zuciya yace me zaihana karubuta mata text message ka tambayeta ko akwai wani laifin da kai mata k'uma tanajin kunyarka bazata iya f'adi maka ba. "Amma ta text tunda ba ganika takeyiba maybe ta'iya f'adi kama. "Mikewa zaune yai ya jingina da bango snn yafara da. **** ***** ***** Dear Aisha, The reason I write this letter to you I don't known what I did to you, If I call you, you did use to pick my cell, that is the reason I write this letter to ask you what I did to you? Pls tell me. **** ***** ***** "Snn yai sending d'insa. "Aisha najin shigowa text da sauri tadaga wayar' tana dagawa taga suna zahradee budewa tai ta karanta bayan ta kare tsaki tasakeyi snn tai hurgi da wayar. "Shiru shiru zahradee zaiga reply yaji shiru. "Sake rubuta mata yai yace Aisha I'm waiting for your reply. "Koda tasake karantawa kamar jiya'dan batada niyar meda masa da reply d'in' kawai bude data tai taci gaba da chat d'inta. "Shima da yaga tunani yana nima yimasa yawa hawa online yai' nan suka h'adu da Aisha. "Yace Aisha"shiru' Aisha'shiru. Bata tanka masa ba. "U don't want to telk to me ba? Himm Allah ya kyau. "A lokacin ne ta bude'gani sakonsa ta meda masa da cewa ba h'aka bane. "To menene?. "Kawai dae. "Kawai dae me?. "Look nifa ba yaro bane kada kinimi rainami hankali. "Idan kinsan da wani abu a zuciyar gara ki sanar dani. Aisha U don't care about me. "Haba zahradee' wani irin tunani kakeyi h'aka? "Aisha idan damuki nakeyi' Is better I should stop disturbing you. "H'aba zahradee meyasa kai a rayuwa bakayiwa mutum uzirine. "Babu wani uziri da zanmaki Aisha wlh akwai abinda kike kunlawa Aisha. "H'aba zahradee meyasa kace bandamu dakai ba zahradee... "Hakane mana Aisha' If you care about me let me see. Zahradee banida lokacin ka. "Iya kacin amsar da Aisha ta turawa zahradee kenan ta sauka' tana kashe data Nasir yana kira. "Sbd bugun da zcyr zahradee yakeyi mikewa yai yashiga toilet yai alwala yazo yafara nafila yanakai kukasan gun ubangiji. "Dan shine mekowa me komai me ikon yida hanawa. Allah yasa mudace' mufi karfin zcyr mu. "Zahradee yana sallah hawaye kawai suke kara kaina a fuskansa. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. MMN USWAN Zanyi amfani wann damar wajan mika godiya ta ga masu backing din na nagode sosae Allah yabar kauna da zuminci. Kada kudamu ba komai bane gazawane kesa ka ka dauki fasaha wani ka juya' idan har kasan kai perfect basai kayi amfani da hikimar wani. Dan haka ina rokon dan Allah duk meyi yabari pls👏 1⃣8⃣ "Bayan zahradee ya'idar da sallah yai tahhiya h'ade da sallama' snn ya dauko carbonsa yai subhanallalahi wabihamdihi, adadi khalkihi, wa rida nafsihi, wa maidada kalimatihi, wa zinati arshihi, guda 100. "Snn yai Subhanallai, walhahamdul lilla Allahu Akbar. sai salatin Annabi manzon (S.A.W.) guda 100. Snn ya karanta fatiha, Ayatul kursiyu, Amanar rasulu, Lakadja'akum. Snn ya daga hannayensa sama yana mai kaskantar da kansa da k'uma tawali'u ga Ubangijin rahma maijin kan bayijsa. "Duk a likacin hawaye basu daena zuwa daga i'donsa ba. "Yace Ya Allah ina mai tawassali da salatin manzon ka fiyayyen halitta Annabin rahma sallallahu alaihi wa sallam, tsira da aminci sukara tabbaba ga shugabanmu Annaba Muhammad (S.A.W.) da k'uma kyawawan sunayenka guda cassa'in da tara". H'aka zahradee yaita jero su tun daga Allahu har Assaburu. Snn yace " Ya Allah ubangijin sammai bakwai, ubangijin kowa da komai mamallaki mulki ga wanda yaso, kai ne kashen annabawa wanda bawani bayanka. "Allah kai ka halitceni ka halitfi Aisha, k'uma kai ka jarabceni da sonta ya Allah, Allah kafini sani abinda yake cikin zuciyarta Allah idan wani abu take shirin kunlawa a kaina ya Allah kada kabari ta cutar dani Allah, "Idan Aisha alkairine a gareni Allah ka mallakamin ita a matsayin matata, idan k'uma ba alkairi bace Allah kaimin zabi mafi alkari. "Ya Allah Kaine masani sirin dake boye' bansan abinda Aisha take nufi dani na' Allah kafi kowa sani yadda nakeji da Aisha a zcyta Allah, idan Aisha ba rabona bace Allah kada kabari sonta ya halakar dani har yakai ga sabamaka, Allah ka sanyamin sanyi a zcyta kamar yadda kasanyawa Annabi Ibrahim sanyi a lokacin da yake cikin wuta. "Allah kai nabarwa zabi kaimin zabi mafi alkairi a tsakanina da Aisha. "Bayan ya shafane ya dauki alkur'ani mai girma' ya b'ude Suratul Yasin ya karanta snn ya b'ude Suratul Rayman, da Waki'a snn ya rufe da Suratul Mulki. "Snn ya bude Suratul Ali- imran (Sura 3 Aya ta 59) INNA MATHALA "ISAA "INDALLAAAHI KA MATHALI ADAM (A') KHALAQAHU MIN TURAABIN THUMMA QAALA LAHU KUN FA YAKUUN(U). "Lalle ne misalin Isa a wurin Allah kamar misalin Adam ne, (Allah) ya halitta shi daga turbaya sa'annan kuma yace masa"Kasance" Sai ya kasance. "Yana da'kyau kowani musulmi yazama yasan wayanga SURORIN' badan komai ba kodan biyan bukatarka a gun ubangijinka. "Surorin suna cikin ( Suratul Ali-imran sura ta 3 aya ta 59) "( suratul mu'min' sura 40 aya ta 68) "Suratul yasin' sura ta 36 aya ta 82) Allah yasa mudace. "Yana shafewa wani irin sanyi yaji a zcyrsa' amm duk da h'aka bedae na ambato Allah a bakin sa ba' haka yaita tasbihi da f'adin Alhadumllah har 100' snn ya shafa yasamu gun ya kwanta. "Tun daga lokacin zahradee yaji sauki a zcyrsa' duk da saukin da yaji a zcyrsa amma da zaran zai kira Aisha sae yaji abin yadawo masa sabo a zcyrsa. "Duk kiran da zahradee zaiwa Aisha tana gani amma bazata daga ba har ya tsinke sai dae idan yagaji da kira dan kansa ya hakuri' h'aka k'uma koda sun h'adu a whApp zaiyi mgn har yagaji tana gani amma bazata tanka masa ba. "Shima tunda yaga walakancin yana niman yai yawa yasashi hakura da kiranta'kodan bacin ran da yake kamashi idan yakirata shiyasa ya hakura. "Duk da halin da yake ciki h'aka ya boye besanarwa iyayensa ba' yabarwa zcyrsa shikadae' gani baya zuwa yasa Aisha tai amfani da wann damar tabawa Nasir damar zuwa' daedae lokacin da zahradee yake zuwa ta medawa Nasir lokacin. "H'akan yasa iyayenta basu luraba' mafi yawanci lokuta umma ce take tambayar zahradee'sae Aisha tace aikine yai masa yawa shiyasa becika zuwa ba. "Umma tace dama hakane Ai idan aski yazo baki goshi yafi zafi' mudae fatanmu Allah ya tabbabar mana da alkairi yasa ayi a sa'a. Nidae a matsayina na mahaifiyarki Aisha bazan gaji da yimaki nasiha ba' Dan Allah Aisha kiwa mijinki biyayya kibar gani yana mutuwa maki babu yadda Allah baya juya al'amarinsa' biyayya da kwantar dakae nasa mijinki ya kara sonki fiye da yadda kike tsammani. "K'uma ki rike iyayen mijinki tamkar sune suka haifeki. "Hakan zaisa mijinki yaji ya kara sonki SBD kina wa iyayensa biyayya. "Aisha kizamo mace ta gari mai koyi da shugsban matan aljanna' Aisha inaso a lokacin da aka kaiki dakin ki' inaso ki natsu da'kyau ki lura da abinda mijinki yakeso kuma ki lura da abinda mijinki bayaso' kirinka kwantar masa da hankali a lkcn da yake cikin damuwa' hakan yakesa kiji ance mace ta mallake mijinta' wlh aisha babu boka babu Malam ladabi da biyayya ma kawai sun isheki Aisha' kinjiko. "Naji umma k'uma ngd. "Umma tace Allah yai maki albarka yabaku zaman lfy. "Shiru Aisha tai bata tanka ba. "Yau sauran seven week biki duk g'ida biyu shirye shirye sukeyi' da safe kafin su Alhj da zahradee sufita kasuwa Hjy mmn zahradee tabi Alhj har d'akinsa lkcn yafito wanka yana yana Shafa mai' b'akin g'ado ta zauna' cikin raha Alhj yace gimbiyata yaya akaine? "Murmushi hjy tai alamar nuna jin dadin mgnr da yai mata' snn tace dama mgnr kai kaya g'idan su iyayen yarinyar gane' shine nace bari nazo na tambayeka SBD naga mako daya ne yarage. "Murmushi Alhj yai h'ade da cewa h'aka ne' amma kiramin son tuku. "Babu musu tamike zuwa part d'in zahradee taje ta sanar dashi abbansa na kiransa. "Batare da bata lkc ba ya biyota sukaje tare' da sallama suka shiga d'akin' bakin gado ta zauna kusa da maigidanta'shikuma zahradee dukawa yayi a gefe yace Abba gani. "Alhj yace dama mgnr kai kayane g'idan su Aisha' kamar yau she kake gani yafi dacewa akai kaya?. "Nan Hjy ta h'au f'ada inda take shiga banan take fita ba' h'aba Alhj ni da kae be'isa muyi shawara ba sae da zahradee? "Murmushi Alhj yai snn yace son ina sauraranka. "Zahradee yace Abba abar mgnr kai kayan nan tuku' a gigice Hjy tace mekace zahradee? "Shiru zahradee yai. "Alhj yace son kasan abinda kake f'adi kuwa? Murmushi karfin hali yai amma duk wanda yasan me ake kira damuwa fuskan zahradee ya baiyana. "Karewa zahradee kallo Alhj yai snn yasa hannu ya dagosa ya zuba masa ido cikin ido ya kare masa kallo snn yace son any prbms?. "Kai kawai yakada sbd a yadda yakeji a zcyrsa bazai iya masu bayani ba' gani ransa yafara baci da sauri yafita yabar d'akin. "Jikin haifiyarsa yai sanyi sosae'dukkansu su biyu sun kasa mgn. "Da sauri Alhj yasa jallabiyarsa yafita zuwa part d'in su zahradee. "Koda yashiga gani zahradee yai zaune a bakin gado ya zabga uban tagumi hannu bibbiyu' dukaww Alhj yai a g'aban zahradee h'ade da dafe kafadar sa yace son wani abune yake faruwa wanda ka kasa sanar dani? "Shiru yai sae dae ido kawai. "Son pls talk. "Nothing'k kawai yace. "Lock son inaso kasan da cewa ni fa mahaifinka ne' wanda a duniya bakada kamarsa' idan har kasan nine na haifeka inaso jin abinda yake faruwa. "Zahradee naji h'aka fashewa da kuka yai' hade da kifewa a gado yana f'adin Allah Abba kafita kawai Abba.... "Kukan da yakeyi ya sashi kasa mgn. "Gani irin kukan da yakeyi har jikinsa na rawa yasa Abba dagashi ya rungume yana f'adin is okay son. " mgn Abba yai ta bashi har sae da ya numfasa yaga ya dae na kuka snn Abba yafita a dakin. "Yana fita sukai karo da Hjy har zata shiga dakin Abba yace kada ta shiga ta rabu dashi. "Hakan yasata komawa da baya. "Batare da bata lkc ba Abba ya shirya ya fita zuwa g'idan su Ruslayni a kofar g'ida ya tsaya yasa yaro dake wucewa yai masa sallama da Ruslayni. "Dayake shima yashirya zuwa kasuwa inda yake harkokin kasiwancinsa yasashi fitowa tare da d'an aiken. "Gani motar Abba ne yasashi karisawa da sauri yaje inda Abba yai parking har kasa ya duka ya gaidashi' bayan sun gama gaisawa ne Abba yace nasan zakayi mmkin ganina a kofar g'idan ku' k'uma da safiya h'aka ko. "Murmushi Ruslayni yai h'ade da cewa wlh kuwa Abba' amma Allah yasa dae lfy. "Abba yace babu komai dama akan mgn abokin kane... "Da sauri Ruslayni yace wani abune yafaru dashi?. "A'a". "Akan mgn aurensa ne ko kasan abinda ke faruwa a tsakanisa da yarinyar da yake so? "Gaskiya abba banida lbr komai. "Batare kuke zuwa g'idan su yarinyar dashi bane?. "A'a" abba ni tun farkon zuwwnsa g'idan su Aisha yadda suke masa yasa naga kamar abin da rainin hankli shiya na dae na binsa. "Amma wani abune ya hadasu da aisha?. "Daga nan abba ya kwashe iya abinda yasani ya f'adiwa Ruslayni. "Himm wlh nidae dama tun farko wlh Allah Abba Aisha kwata-kwata bata min ba'SBD daga gani idonta batada da mutunci' amma yanzu ina yake?. "Abba yace to fa' Allah ya'kyau ta. "Yana g'ida". "Okay daga nan can kawai zanwuce. "Nan sukai sallama. "Tun daga lkcn Aisha tahana Alhj Nasir zuwa kofar g'idan su' Alhj Nasir babu yadda beyiba akan Aisha ta sanar dashi dalilin h'aka amma taki' cewa tai yai hkr tanaso koda zaizo yazama mgnr aure ne yakawosa amma yanzu idan yazo zai'iya bata mata shiri. "Shima dayake akwai abinda yake shiryawa zcyrsa yasa hakan be damesa ba. "Washe gani da yadda abba yatara duk yan'g'idan snn yasa aka kira zahradee dake kwace a daki yazo parlour' abba yace son gani da yan'uwanka' idan ni bazaka iya f'adimi ba to ga yayyinka sae kasanar dasu abinda ke faruwa. "Shiru zahradee yai kansa a kasa. "Shamsudee yace ba dakae akeyi bane. "Zahradee yace Abba nafasa auren... "Zahradee ya karisa mgnr ne h'ade da mikewa yabar gun. "Gun yayyin hada ido suka duk sunkasa mgn SBD mmki. "Salati kawai Hjy tai ta sanarwa ubangiji. "Shamsudee da Nurudee mikewa sukai suka bishi daki' koda suka shiga babu irin tambayar da basu masa ba amma zahradee yace shidae fasawa ne kawai yai. "Gani sauran kwana hudu biki babu wani abuda yashigo daga g'idan su zahradee' yasa umma tasami Alhj Muhammad da mgnr' shima yace abinda yana damusa amma idan yakira beyi laifiba? "Umma tace laifi me? Kaidae kira muji abinda yake ciki. "Wayarsa ya daga ya kira Alhj Kailani bayan su gaisa ne Alhj yace dama bugowa nai na tambaya sbd saura kwana hudu baku zoba baku turo wani daga bangarenku yazoba banle muji ina muka tsaya. "Alhj yace eh hakan da kai yayi ko dama baka kiraba ni da kaina zanzo nasar dakai cewa mgnr aure dae babu idan yarodae yace yafasa. "Yana fadin mgnr ya kashe wayarsa. "Salati Alhj Muhammad yasa' cikin gigita umma tace lfy? Alhj yace mgnr aurene babu sunce su fasa. "Fashewa da kuka umma tai hade da salati tana fadin yanzu SBD Allah irin cin mutunci da zasu mana kenan. "Jin kukan umma ne yasa Aisha fitowa a guje daga dakinsu tana fadin umma lfy. "Cikin kuka umma tace idan su zahradee ne wai sun fasa auren. "Wani irin doguwar tsaki Aisha tai hade da cewa dan suce su fasa sae me sae kace shikadae ne autan maza'ni wlh na dauka ma mutuwa ai. "Dan Allah umma ki daena kuka haka. "Haba Aisha kinsan abinda kike fadi kuwa? Yaya kike mgn kamar wanda batasan ciwon kantaba. "A lokacin ne Aisha tai dan guntun kwalla tana fadi to umma ya kikeso nace umma. "Abbansu dake zaune kasa mgn yai. "Umma taci gaba da cewa yanzu yaya zamuyi? "Abba yace nima kaina tunani da yakeyi kenan' wlh hafsatu inda inada wani da zanbashi Aisha kodan na tura masu bakin cikin da suka cusami da jibi zan daurawa Aisha aure. "Aisha najin haka wani irin dadi ne yakamata. "Umma tace gaskiya kam' gashi babu wani dake zuwa gun ta banle ace yafito' to koda ma yafito ba lalla bane ya'amince a kwanaki hudu ga da suka rage. "Aisha naji haka tace idan haka ne Abba ka kwatar da hnklinka insha Allahu bazakaji kunyaba duniya da lahira' idan har ka'amince akwai wani dake zuwa guna zan gwada nagani kodan naga na share maku hawaye. "Shiru umma tai. "Abba yace a'a aisha bazanso na takura makiba dan wata biyan bukatarmu' tunda abu yazama haka nabarwa Allah komai Allah yabaki wanda yafishi. "Umma tace amin alhj. "Aisha dake duke tace abba kada kadamu zan gwada nagani. "Abba yace a'a aisha bazanso kiyi auren kiyayyaba nafiso ki auri wanda kikeso. "Aisha tace karka damu abba. "Mikewa tai tabar dakin' tana komawa dakinsu ta kira alhj nasir ta sanar dashi gobe yashigo gida. "Nasir yai murna sosae dajin haka. "Washe gari yazo gidan su Aisha' bayan sun gaisa da Bbn aisha ya gabatar da kansa kuma yace shi ko yaune idan sun shirya shima a shirye yake. "Jin hakan abba yai murna sosae hakan yasa sukabar shi a ranar da akasa ita da zahradee. "Zahradee wasa wasa ko fita baya iya yi' anyi anyi akaisa asibiti amma yaki. "Ranar asabar aka daura auren aisha da nasir' zahradee najin labari fashewa da kuka yai' hade da yanke jiki yafadi sumanme. "A gigice abba ya daukesa zuwa asibiti. "Ana daura aure da safe da yake yan'uwan nasir sunzo' anayi azahar aka basu amarya sbd gari ba daya ba' kuma akwai tazara a tsakaninsu. "Gani zatabar gida da yan'uwa da iyaye yasa Aisha kuka har ana riketa. "Kwata kwata mutu 3 kawai Abba yabari suka bita SBD nisan guri. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. MMN USWAN 1⃣9⃣ "Rushing d'insa zuwa hospital' Abba dake rungume dashi a mota in ba addu'a babu abinda yakeyi' idan yai wann baya karisaea yake sakewa ya kamo wani' Shamsudee shike driving gudu yake kamar zaitashi sama. "Da h'aka har suka isa hospital ko parking kirki basuyi ba Abba ya b'ude mota h'ade da fitowa da zahradee emergency room aka kaisa doctors dasukan duty to sukai can a kansa' kowa na nasa bakin kokarin'abba da Shamsudee da suke waje sae faman leke sukeyi. " Da taimakon Allah yasa zahradee ya farfado' but still sama sama yake numfashi gani yabude ido yasa doctors d'in juna masa drip gani ya koma wani bcc yasasu fita daga d'akin' suna fita Abba da Shamsudee sukasa kai zasu shiga d'akin' da sauri doctors d'in suka dakatar dasu' h'ade da cewa dan Allah yana cikin critical condition dan h'aka yana bukatar hutu. "Ido cikin ido suke kallon juna snn Abba ya kamo hannu Shamsudee suka zauna kan kujeran dake gefe d'akin' basu dade da zama ba saega su Hjy da Nurudee sun shigo hospital d'in ganisu da tai zaune a gefen d'akin yasata tambaya lfy?. " shiru Abba yai mgn ta gagaresa' Shasedee yai masu bayani abinda ake ciki' salati Hjy tasa da salallami. "Zahradee be falkaba sae gam da magrib snn ya falka Abba kawai yake ambato a bakinsa' da sauri Abba ya mike shida Shamsudee suka shiga d'akin' suma su Hjy suka bisu ciki gani hawayen dake gangaro masa ta gefen ido yasa Abba matsawa gun gadon tissue ya diba yana goge masa haeayen. " zahradee yace Abba Aisha' Abba Aisha ta cuceni Abba. "Abba yace son kabar mgnr Aisha d'in nan kaji da kanka son. " wani muguwar tsaki Hjy tai h'ade da cewa Aisha me? Aishan banza. "Shamsudee dake gefe yace to kai zahradee idan banda abinka wayasan abinda ya h'ada ku? Banle har a tayaka. " zahradee yaci gaba da cewa Abba bansan abinda naiwa Aisha ba Abba Aisha ta gujeni Aisha ta daena sona Abba' dan Allah Abba kaje ka dawomin da Aisha wlh Abba inason Aisha Dan Allah Abba. "Abba dake tsaya kusa dashi tsayawa yai shiru yana kallon zahradee dake kwance' gani shiru da yai yasa zahradee yunkurin mikeww zai tashi' da sari su Shamsudee suka rikeshi suna kokarin medashi ya kwanta' zahradee yace a'a ku barni kawai ni masamu sauki. " duk zahradee yana mgnr ne amma bedae na kuka ba. "Gani zasu gwada masa karfi yasashi rike Abba' a lokcin ne Abba ya dawo daga tunanin da yake' hannu kawai ya daga masu alama su bari. "Abba da kansa ya jinginar da zahradee a jikin gado' snn shima ya h'au gefen gado ya zauna' cikin kuka zahradee ya kwashe duk abinda Aisha tai masa ya sanarwa iyayensa' yanayi yana kuka' har ya kare' yana karewa yasake fasawa da wani kukan h'ade da rungume Abba sa. " Hjy dake gefe a take tace kan'buhun uba! Ni zata kawo rainin hankali to wlh bata isaba' ni da tuntuni ma ka sanar dani wlh har gida zanje naci ubanta' wai tsayama tukun waye ubanta a garin nan? Da zcy ya dibeta fisgo hannu Nurudee tai dake tsaye kusa da'ita h'ade da cewa kai zomuje har gidan naci ubansu marasa mutunci. "Har sukai bakin kofar fita Abba yace ina zani? " babu ko tsaoro bale shakka tace g'idan su Aisha. "Abba yace in har kikabar nan ba gida kika jeba to bada izinina ba. " Hjy laila macece me zafi sosae amma kuma me biyayya bata tsallake mgnr mijinta' h'akan yasa ta dawo tasamu gu ta zauna duk da h'aka inda take shiga ba nan take fita ba. "Alhj yace kiyi hakuri h'aka nafiso naje da kaina' sbd idan har nabari kikaje nasan komai zaki iya aikata masu" kuma banaso ki aikata abinda zamu dawo muna danasani SBD bamusan abinda gaba zaiyi ba. "Cikin goats one tace yayi dawa Allah ya saukake. " zahradee dake manne jikin Abba cire drip d'in yai h'ade da cewa Abba muje gida ni na warke. "Abba yace a'a son kabari kakara samu sauki. " suna cikin h'aka doctor ya shiga koda yasake dubashi yace yasamu sauki dama damuwace tai masa yawa shiyasa amma Dan Allah arinka kulawa dashi da kuma gujewa abinda zaisa yasake shiga irin wani yanayi. "Abba yace insha Allahu. " daga nan aka rubuta masu magunguna h'ade da sallama' suka koma gida. "Tunda suka dawo guidance Hjy mmnsa da yayyinsa kae har ma da Abba suke bawa zahradee kyakykyawar kulawa h'ade da kwatar masa da hankali dan gani yadawo normal kamar da' kusan kullum sae Abba yai masa addu'a a ruwa yabashi yasha sbd ko Allah zaisa a cire mgnr Aisha a ransa. " d'an koda suka dawo g'ida kullum mgnr kenan Aisha'aisha ta tafi ta barni Abba da Hjy suyi fada har sugaji' amma zahradee bedaena ambaton su Aisha ba' idan ka gansa kamar mahaukaci sbd yadda ya koma' shiyasa har bada kudi Abba yai arinka yimasa addu'a ana bashi yana sha' shima kuma yana yimasa da kansa. "Cikin hukucin Ubangiji komai yafara daedae ta har fita kasuwa yakeyi shida Abba' amma ko da wasa bayaso a kawo masa mgnr budurwa' h'aka yaci gaba da rike kansa' amma idan har ya dauki wayarsa yafara duba pict d'in sae kawai kaji yana nisawa' da Abba yaga h'aka canza masa wayar yai wanca k'uma ya goge komai dake cikinta snn ya kai d'akin sa ya boye. " tunda daga lkcn zahradee ya dawo normal life kamar kowa' duk wanda yasan zahradee k'uma yasan bayason mgnr budurwa bayayi masa' shima yaci gaba da harkikin kasuwancinsa gani suna samun Improvement yasa Abba ya sakan masa komai Dan yanzu kusan duk dukiyar Abba a hannu zahradee yake sbd zahradee irin mutaninan ne wanda duk abinda zasu taba sae yayi albarka' shiyasa Abba yake matukar son zahradee akan sauran yaransa. ☘☘☘ ☘☘☘ CI GABAN LABARI Abdul be'isa garin binni kebbi ba sae gam da magrib ana saukeshi a tasha yai amfani da address d'in da umma tabashi dashi ya'isa har g'idan su Fatima a bakin gate ya tsaya sae da yasake tambayan gateman snn yace dan Allah shi kani matar maigidan ne Aisha ko zai taimaka masa ya sanar da'ita? "Gateman yace ba matsala ga gu ya zauna ya jirashi yaje ya sanar dasu snn yashiga daga ciki' wani d'an karami bechi dake gefe ya nuna masa ya zauna' snn shikuma ya shiga daga cikin g'idan lkcn Fatima na zaune a parlour ita da yara gateman yai sallama Fatima tai masa izini daya shigo. "Yana shigowa bayan ya gaisheta snn yace dama wani bakon saurayine yazo yace wai shi kani madam ne daga garinsu yake sunasa Abdul shine nace ya tsaya na sanar maki snn. " Fatima tace okay bari a kirata tuku' juyawa tai gun Khadijat dake zaune kusa da'ita tace jeki ki kira antynku. "Khadijat tace to' mikewa tai taje da sallama tashiga d'akin lkcn Aisha na zaune bakin gado ta zabga uban tagumi' gani Khadijat ta shigone yasata dagowa da sauri tace Khadijat ya akai ne? " Khadijat tace Anty momy ne tace kizo kinyi bako. "Aisha tace bako k'uma? Daga ina?. " mikewa tai suka fita tare' suna tafita parlour Aisha tace Anty gani' Fatima tace gateman yashigo yake sanar dani kinyi bako' Aisha tace bako k'uma Anty toni wama nasani a garin nan da zaizo guna. "Murmushi kawai Fatima tai sbd yadda Aisha take mgn' snn tacewa Aisha jeki kiga ko waye. " komawa tai ta dauko hijab tasa snn tafito h'ade da kiran Khadijat ta rakata' Aisha na fita gani bataga kowa kusa a gun ba tajuya zasu koma ciki da sauri gateman yace Hjy ga bakon nan snn Aisha ta tsaya fita yai yakira Abdul suka shigo tare' Aisha na ganisa a guje taje ta rungumesa h'ade da fasawa da kuka tana kiran Abdul dama Ashe zansake ganika?. "Abdul yai matukar mmkin gani Aisha sbd gaba daya ta lalace ta fita a haiyacinta kamar ba Aisha daya sani ba' dan ma jinisane inda badan jini ba da ba lalla bane ya shedata. "Shirun da Fatima taji yasata lekawa gani Aisha na rungume da Abdul yasata fita taje gunsa kallo daya taiwa Abdul taga kamanni Aisha a fuskansa' tace a'a Abdul yau bakone h'aka mukai to kukariso ciki mana. " snn suka karisa ciki' tana gaba suna baya suka shiga a parlour suka zauna Fatima ta kira Khadija sukaje kitchen ruwa da juice tabawa Khadijat tace takaiwa su Abdul parlour' Khadijat na gaba Fatima na baya suka koma parlour a gaban Abdul ta'eje try d'in' bayan ya sha ruwan ne suka gaisa h'ade da tambayarsa su ummansu. "Abdul yace duk suna lfy' sun cema a gaida ku. " Fatima tace muna amsawa. "Mikewa tai da Khadijat snn ta dauki Jabeer dake bcc suka basu gun' bayan tashiga dakine yasake aikan Khadijat ta kira Aisha' tare suka tafi da Aisha kitchen Fatima taje ta d'au abincnsu na dare wanda zasuci da yara ta raba biyu tace Aisha ta dauka h'ade da bata hakuri sbd abinci babu yawa k'uma abincin gida kadan yarage banle ace za'a sake dafa wani. '" Aisha tace ba komai ngd sosae Anty. "Itama Fatima tace babu damuwa. " kai tsaye d'akinta takai masa abincin snn ta d'ibi nata da zataci na dare ta kara masa a nasa snn takoma parlour ta kirashi daki yazo yaci abinci. "Zama yai dirshan akan carpet yanaci suna hira yana bata lbrin su Abba da umma' suna cikin hira ta dauko nata zataci gani abincn kadin ne yasa Abdul cewa Anty kije ki kara mana amma wann abinci kamar zakibawa yaro. "Yage Aisha tai h'ade da cewa a'a h'aka ma ya'isheni. " ragowar abincin da Fatima da eje tabawa yara sukaci ita k'uma tasha ruwan Lipton' lkcn kwanciya da yayi extra d'akin da babu kowa Fatima tace Aisha ta bude wa Abdul ya meant a a ciki. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘. MMN USWAN 2⃣0⃣ "Da safe cikin abinda Fatima ta h'ada wa yara na breakfast ta d'ibawa Abdul tea ne da arish ko madaran kirki babu a ciki' da Aisha tashigo gaidata ne tace taje kitchen ta dauki abin breakfast takaiwa Abdul, Aisha tace to ngd Anty. " har tajuya sai Fatima tace amma ke hkr zakiyi sbd bekai damu ba' koni bansamu wanda wajan nawa ne nabawa Abdul tunda shi bakone be kamata a barsa da yunwa ba. "Aisha tace hakane Anty babu damuwa nagode. " kai tsaye d'akin ta takai abincin ta'ije duk da yau ta tashi da yunwa sbd ragowar abincin tane wanda zataci da dare ta karawa Abdul yaci ita k'uma ta hkr, shiyasa ta tashi da yunwa amma yaya zatayi dole yanzu d'inma ta hakura tunda bashida inda zaije yaci inba nan ba. "table d'in dake gefen gadonta tadora akai ta eje masa' Abdul be tashi ba sai around nine snn ya tashi bcc yana fitowa daga daki parlour yazo ya zauna snn ya kira Aisha ta waya' Aisha na fitowa tace yazo suje d'akin ta. " mikewa yai suka shige bayan su gaisa ne Aisha ta d'au abin breakfast ta mika masa' Abdul yaci suna hira' duk hiran da sukeyi ba shigar Aisha yake yiba kawai amsashi takeyi amma bekai ciki ba' idonta su cika da kwallo k'adan yarage su xubo da sauri tasa hannu ta goge. "Da Abdul ya lura da h'aka yace Aisha lfy? murmushin yake tai masa wanda bekai zuci ba' h'ade da cewa babu komai tun dare ne wani abu ya f'ada min a ido shiyasa kaga duk idanu suyi ja. " Abdul yace sorry' idan kinga zai dameki ki sanarwa maigidanki ya kaiki hospital sbd ba'a wasa da ido fa. "To kawai tace. " Snn Abdul wayya ni tunda nazo banga maigidan nakuba kodai baya gari ne? Aisha tace yana nan wasu aiyukane sukasha kansa shiyasa baya samu isaishen lokcin da har zaka gansa. "okay kina nufin baya kwanan g'ida kenan?. "shiru Aisha tai bata sake tankasa ba. "Abdul yace yauwa Aisha. "na'am. "nidae tun jiya da nazo wani iri na ganki kamar mara lfy kodae tun cuwon da umma tace kinji shine har yanzu baki dawoba. " Eh"kawai tace. "Amma ai kinkai wata uku da rashin lfy ko?. " Eh" "To kina amfani da magugunar da aka baki kuwa?. '" ina amfani dasu mana. "amma gaskiya yakamata ace kin canza' dubi yadda kika koma kashi kashi fa' kamar wanda batacin abinda' Aisha kodae kina zama da yunwane? ko k'uma bakijin dadin zaman g'idan ne?. " shiru Aisha tai kanta na kasa. "Abdul yace Aisha kiyi mgn mana. " hawayene kawai suka zubo mata. "lalla Aisha Akwai matsala dama shine dalilin zuwana kenan sbd su umma koda su kira number baya shiga h'aka ma na maigidanki k'uma ga munanar mafarkai da umma keyi a kanki. " Aisha naji h'aka fashewa da kuka tai. "gani kukan da takeyi yasashi kasa cin abincin dake gaban sa' jikinsa yai sanyi sosae. " mikewa yai ya fita waje can gefe ya samu ya kira umma bayan sun gaisa h'ade da tambayar ya yasami aishan' Abdul yace gskya umma akwai matsala sbd ni kaina banji dadin ganita da nai ba. "nan yazare komai ya sanarwa umma'umma harda kukanta take cewa idan mijin aishan yadawo yace tanaso mgn dashi. " Abdul yace to umma. "bayan fitar Abdul ne Aisha ta d'au abincin daya barshi yafita taci' dama kukanta da biyu sbd yunwar daya addabeta. " itako Fatima ruwan Lipton tasha' gani eleven yayi yasata shiga kitchen taduba taga abinda yarage masu' shinkafa ya kare h'aka semovitar sae kuskus da taliya wanda basufi three three bag ba' tsayawa tai tai shiru tana tunanin ta'ina zata fara? ita k'uma a yadda takeji a yanzu a zcyrta bazata iya siyo kayan abinc ta ciyar da wata ba' sbd ma inda zata duba irin abinda Nasir keyi mata wlh koda ruwan g'idan bazata bari wata tasha ba. "amma abu daya take dubawa sbd itama ta haihu k'uma bazataso yau ace yar'ta tai aure ta f'ada irin wnn yanayin ba' shine kawai dalilin dayasa duk yaran da Nasir zai aure bayan ya gama ci moriyarsu snn k'uma ya koresu suke bata tausayi. " Amma suna Allah ya kara masu da kwadayinsu daga gani mutum bakasan daga inda yakeba kabashi aure' Ai ga irinta nan. "wani d'an karamin tsaki tai h'ade da kuna gas tasa sanwar taliya jallop gaba daya dafa harda na dare tana gamawa tasawa Aisha da Abdul a kula daya sauran k'uma tazuba a kula ita da yara. " koda ta kira Aisha tazo ta dauka da aishi tazo Fatima tace gashi keda Abdul k'uma harda na dare nayi d'an g'idan babu wani abu da yai saura komai ya kare. "Aisha tace to' snn ta dauka takai daki. " itama Fatima d'akin' ta tashaga wayarta ta dauko bugu daya taiwa number Nasir yashiga sbd ita kadae ce takeda wann number' daga ita sae shi kawai suke amfani dashi' ko Aisha batasan yanada wann number ba. "Nasir yana gani kiran Fatima da sauri ya daga h'ade da cewa hello gimbiyata' Fatima najin h'aka sae tai marerece tace batada lfy tun ranar daya fita dake fama da ciwo. "Da sauri Nasir yace kifito kice drive yakawoki hospital d'in doctor kamal nima ganinan tafe. " to kawai tace. "yana kashe wayar toilet tashiga ta watsa ruwa snn tafito riga kawai tasa batare da kwalliya ba ta d'au key d'in motarta ko sallamar Aisha batai ba tafita. "dama kwance yake a hotal d'in daya kama yake hutawarsa mikewa yai ya d'au key yafita' koda Fatima ta'isa hospital d'in can gefe tai parking motar ta inda ba lallane ya ganta ba' tana gani shigowarsa tai saurin fita daga motar taje jikin wata itaciya ta rabe. " Nasir yana parking har ya bude mota zai fita da sauri tashige juyawar da zaiyi ita yagani yace Fatima yaya jiki dae' wani Orin mugun kallo tai masa snn tace lfyta klau. "dawowa cikin motar yai Fatima taci gaba da cewa h'aba Nasir waikai meyasa bakada imanine da tsoron Allah tun yaushe nace maka abincin mu yakare amma baka tankaniba' to wlh yau ko sanwa bamu dora ba' h'aka yara suka tafi schl. " b'ude makin Nasir yace kinsone. "kamar yaya Nasir?. "bakinada kudi ba? bangane ba?. "wlh Fatima idan Aisha tana g'idan nan bazan sisina na siye abinci ba' kinfi kowa sani ina nimana sbd iyayena nan da kuma yarana sae kuma ke... '" haba Nasir wani irin mgn kakeyine h'aka sbd Allah' to wlh bazan yarda ba' idan har baka siyo mana abinci ba saena buga g'ida na f'adi duk irin abinda kakeyi anan' k'uma wlh har abbana saena f'adi mawa na gwammaci idan auren zai mutu nema ya mutu.. "kina mgnr banzargi ne idan akwai uban da ya'isa ya kashemin aurena dake inaso na gansa'ke bakisan aurena dake mutu karaba bane. " cikin masifa Fatima tace toni wlh bazan zauna ba sae dae ko nakoma g'ida. "A isgilance yace ga hanya. "Ni dae abu daya nasani kudina nasa na auro yarinyarga a lkcn da nake sonta yanzu k'uma nace banayi dolene?. "haba Nasir sbd Allah me baiwar Allah ga tai maka? "bataimin komai ba gajiya ne kawai nai da'ita wlh Fatima wani aure nakeso naji shiyasa' ni k'uma banida ra'ayin tara mata dayawa' ko Hauwa ma da kikaga mun dade da'ita dan bazama takeyi ba shiyasa' kinga da'ita da babu duk daya ne.. "cikin fushi tace kai wlh baka isa ba' k'uma wlh kai da auren saedae idan anayi a lahira' amma a duniya kagama kenan. " dariya yai h'ade da cewa wlh shiyasa nake kara sonki Fatima ta. "Amma yanzu abinda za'ayi ga wasu kudi sae dae babu yawa Dan basufi ten thousand ba kisiyewa yarana sweet sbd nasan dae wanda na siyo yakare' amma idan kinaso nasiyo abinci a g'idan nan to ki tabbata Aisha tabar g'idan. " dole yasa Fatima amsar kudin d'an batada yadda zatayi. "Washe gari Abdul na idar da sallar asuba ya d'au jakarsa zuwa bauchi' Aisha tai kuka kamar me' d'an a zcyrta ji take kamar tabisa.... 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. MMN USWAN ALHAMDULLILAH FANS INA MIKA GODIYATA GAREMU A GSKYA INAJIN DADIN CONMM D'INKU D'AN SHIKE KARAMI KARFIN GWINWA WAJAN TP. NAGODE NAGODE SOSAE FANS ALLAH YABAR ZUMUCI. BABY ZULAIHAT BEST FRIEND GRP MAIMUNA MUHAMMED MMN USWAN GRP AISHA MAGAJI KD LONG LIVE HOME OF NVL JIJJINAR BANGIRMA GAREKI MMN MEEMA MARUBUCIR RAIHANA AND YARAN MIJINA NAGODE ALLAH YABAR ZUMUCI. DUK INA MIKA GODIYATA A GAREKU, CMM DINKU BA KARAMIN KARAMI KARFIN GWIWA YAKEYI BA TNX SO MUCH ALLAH YABAR KAUNA DA ZUMUCI. READERS GA QUESTION PLS MISALI ACE KECE KISHIYA TA D'AU TAKARDAN SAKI TA BAKI, BAFA MIJIN DA KIKE ZAMANSABA KISHIYA DAN ALLAH YAYA ZAJI??? AMSATA TANA GAREKU. INA SAURARO👂. 2⃣1⃣ "Abdul be'isa ba sai bayan sallar magrib snn ya'isa g'ida' lokacin umma na zaune akan sallaya tana lazumi h'ade da jiran isha'i yayi tai Abdul yai sallama. " jin salamarsa ne yasa umma shafe addu'a snn tai masa barka da zuwa Abdul' yana murmushi yace yawwa umma sannu da g'ida' umma tace yawwa sannu da hanya. "bayan sun gaisa ne umma ta mike ta kawo masa abinci' Abdul yaci suna hira har Abba yashigo'shima zama yai sukaci gaba da hira' sae dae duk irin hiran da sukeyi be yarda ya f'adi halin da Aisha take ciki ba har suka kare hira. "Da asuba lokacin Abdul ya dawo daga masallaci kai tsaye d'akin Abba yashiga gaida shi' bayan su gaisa ne Abdul yake bayyanawa Abba halin da Aisha take ciki' wuf umma tai ta antayo d'akin ashe dama tana gada b'akin kofa zata shigo jin suna mgn ne yasata dakatawa ta tsaya daga b'akin kofan. "Cikin gigita umma tace mekace!!! Abdul Ashe dama halin da 'yar'uwanka take ciki kenan shine ka boyemi Abdul' umma tana karisa mgnr da fashe da kuka h'ade da cewa ni dama tunda naketa mafarke munana nasan ba lfy. "shiru Abdul yai yana sauraran maganganu da umma keyi' Abba dake zaune akan cushion yace h'aba Hafsatu wani irin mgn kikeyi h'aka ta yaya za'ace mutum zaiyi rayuwa batare da jarabtaba banlema rayuwar aure. "Ita rayuwa ta gaji h'aka dole sai da jarabta wani yazo maka a farko wani k'uma a tsakiya wani k'uma a karke' idan Allah ya jarabceta a farko ta gode masa ma wata kila jin dadin ta na gaba' d'an h'aka a guna ba wani abu bane Allah ya fidda dasu lfy. " Nace dae duk suna lfy ita da maigidan nasu? Abdul yace ni wlh Abba tunda naje garin har nabari banga maigidan ta ba'wani abu mmki koda na tambayeta takasa bani amsa guda daya kwankwara sae faman kame kame takeyi. "umma tace kaga abinda nake f'adi h'aka ko Alhj to nidai wlh bazan yarda nayi asarar yan'daya da Allah yabani ba wayasani ma ko d'an yankai kaine.... "A take Alhj ya daka mata wani irin tsawa h'ade da cewa h'aba hafsatu wani irin mgn kikeyi h'aka sbd Allah' to wlh idan bcc kikeyi ki falka k'uma ina mai tabbabatar maki da kiyi gaggawar rokonsa gafara sbd mummunar zato da kikai masa. "Umma tace nifa ba zarginsa nakeyi ba. " Abba yace idan ba zarginsa kikeyi ba to menene amfani irin wnn mgnr? ni dae abinda nakeso dake shine nafi bukatar da kitayata da addu'a Allah yabata zaman lfy ita da mijinta' idan ma wani hali take ciki Allah ya fidda'ita. "jinsa kawai umma keyi amma duk mgnr da Abba keyi bekai zacin ta ba. "shiru da tai tana share kwalla yasa Abba cewa hafsatu kina jina ko' umma tace nidae gskya Alhj hnklina be kwanta ba sbd Allah kadae yasan halin da Aisha take ciki' in da zaka amince ne da sae naje na ganta... " kije ina hafsatu? "gun Aisha mana. "Tab d'in jam wlh bantaba sani bakida hankali ba sae yau'Ashe h'aka kike? dama ance ku mata habkalinku daya yake dana yaro' idan banda rashin hankali daga yaro yazo da zance sae kice zaki' to wlh bari kiji ko da wasa kada ki sake tunanin h'aka' ba keba wani ka daga cikin g'idan nan babu wanda zaisake zuwa tunda abin yazama h'aka. "Umma tace amma Alhj.... "Amma me? banaso nasake jin b'akin wani daga cikin ku' d'an h'aka kutashi kubani gu. "H'aka duk suka mike jiki a sanyaje. ~~~ ~~~~ ~~~ Tun bayan tafiyar Abdul Aisha kullum cikin kuka take' ko fitowa parlour batayi' idan har kinga ta fito to abinci tazo dauka bayan h'aka zama takeyi a daki tai ta faman tunani kala kala. "S'au kinta daya yanzu sbd lokaci lokaci umma tana bugowa suyi hira amma ba kullum ba sae k'uma Abdul' duk da Abdul yana kokari wajan sa mata recharge car k'uma yace idan tana bukatar wani abu tai mgn amma nawi takeji sbd tunda tai aure dae dae da rana daya bata taba aikawa iyayenta da komai ba' bayan ka auran da yaro ka huta amma sae yazama har yanzu ana wahala da'ita. "shiyasa duk yadda takai ga bukatar wani abu take hkr' impact ma koda za'a bata' itana zasu aika mata dashi? tunda ba wani tasani a garin ba' k'uma ba account ta b'ude ba banle tace kota account zasu iya turo mata. "ita dae Fatima tananan sae faman tunani takeyi kala kala ta'ina zata bulowa Nasir kodae takira g'ida gu iyayensa ne ta f'adi irin abinda yake aikatawa anan. " Can k'uma tace kae a'a idan nai h'aka bedace ba sbd mahaifiyarsa be kamata a daga mata hankali ba' idan k'uma mahaifinsane ba lallane ya damuba tunda bayason yaji ance ga laifin Nasir tun yanada kuruciyarsa banle yanzu da girma ya kamashi' idan k'uma idan iyayenta ne tarida da tasan halin Abba ta cewa zaiyi ta h'ada kayanta da yara yadawo g'ida' tasan idan har tasake tabar g'idan Nasir to ba lalla bane abbanta ya bari tadawo g'idan Nasir' koda zata dawo tasan sae ta wahala kafin abari. "Sbd a rayuwar Alhj Sunusi duk cikin'ya'yansa yafiso Fatima sbd suna mahaifiyarsa ne da'ita. "" Can wani zcy yace kodae na tambayesa kudi ne nace zanyi wasu uzurorine dasu' to k'uma idan nai h'aka zaice aikin da nakeyi fa? tunda besan nabar aiki ba. "kai bama zanyi h'akan ba' baridae kagani' mikewa tai ta dauko wayarta cikin bedroom tashige snn tai rangadawa Nasir kira' lkcn yana kwance kamar bazai daga ba gani kira yaki karewa h'aka dagawa h'ade da sallama. " ko amsawa Fatima batai ba' ta h'au shi da masifa tana f'adi wlh idan bakazo g'idan nan yanzu ba na rantse da Allah a yau bazan kwana garin nan ba sae kano k'uma g'idan mu zantafi direct' idan har ma na sanarwa Abba ya nabiyo jirgi nazo. "Nasir yace what? Fatima kanki daya kuwa? to wlh idan kika sake kikabar g'idan nan nida kene' k'uma kada kifita ko nan da b'akin gate dan ganinan zuwa. "Batare daya kashe wayar ba yasata cikin aljihu yafice daga d'akin kai tsaye motar a'a ya shige yakama zuba gudu kamar zaitashi sama. "Kafin yashigo g'idan tuni ta h'ada kaya a cikin jaka h'ade da yafa kyalenta' ko minti goma ba aiba Nasir yashigo da motarsa. "jin tafiyarsa yasata daukar jaka tafara tafiya kamar da gaske yana shiga fisge jakar yai yai hurgi dashi h'ade da jawota yasama kofar key yarufe ta ciki. "Yana dadin Fatima kina haukane ko? ke da daske kikeyi tafiya zakiyi ki barni? to wlh karyanki tasha karya babu inda zaki kibarni. " tsawa Fatima ta dake masa tana f'adin wlh baka isa ba Nasir'. "A fusace Nasir ya dauketa da mari Wanda yasata saeda ta f'adi kasa. "Ihu tasa tana kiran wayyo Allah na. " yace wlh Fatima kibar gani irin son da nake maki idan har ina mgn dake kina cemin ban'iya ba wlh saena maki dukan masifa a g'idan nan k'uma na gwada maki isata d'in. "Ita k'uma Aisha yau zatabarmi g'ida tunda bada ubanta muka h'ada kudi muka gina ba' a fusace yajuya zai fita. " Da sauri Fatima tasha gabansa h'ade da cewa a'a Nasir Dan Allah kada kai mata h'aka' idan kai mata h'aka bakai mata adalciba. "garama kafito da wata hanyar zaifi' ko kace tashirya taje gani g'ida' kaga daganan ma zaka iya aika mata da takardanta saifi. "H'aka yafita batare daya tanka taba' yana fita sukai karo a parlour Aisha ta duka ta gaidashi' fuska daure ya amsa da cewa jeki ki hadu bayan ki yau d'in nan zaki gani g'ida. "Kamar a mafarki Aisha taji wani irin tsanle tai ta rungumesa tana fadin nagode sosae Alhj Allah ya kara girma da daukaka. " batare daya ce amin ba yace jeki ki h'ada kaya kizo ina jiranki. "Idan banda rashin wayo da batan basira irin na Aisha ba'ai ta tambayi dalili'amma ina jiki na rawa taje ta h'ada kaya tafito' tana fitowa ya mike har zasu fita a guje taje sallamar Fatima. " Rungumar juna sukai Fatima harda kukanta Aisha tace h'aba Anty wani irin kukane kikeyi h'aka tafiya ai ba mutuwa bane inanan dawowa nan bada dadewa ba.... "Nasir ne ya daka mata tsawa da Dan Allah kizo muje kinbarni a tsaye kamar wani d'an'iska. " Da sauri Aisha ta saki Fatima tazo ta d'au jakarta suka fita. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W. ☘. MMN USWA fans gskya banida b'akin gode maku sae dae nace Allah yabar kauna da zumuci a gskya comm d'in ku yana karami karfin gwiwar sosae nagode nagode sosai wnn pg kafatalinsa sadaukarwane gareku masoya aure ibada ne.😍🤝❤ 2⃣2⃣ "Aisha suna fita zama Fatima tai tai shiru tana tunanin irin wann hali na Nasir' yanzu sbd kwata kwata a rayuwar Nasir be dauki saki wata aba bace a kalla bayan aurenta dashi Nasir yai aure da zaikai shabiyar a cikin yaran da yake aurowa Aisha itace ta shabiyu banda zawarawa' a cikin zawarawanasa Hauwa zuwaira sai ni'eema duk su uku nan gogangune sosae' sae k'uma kash!!!!! duk da gogewarsu Nasir yawuce wa tunaninsu' h'akan yasa zuwaira da ni'eema basu dade da shiba. "kwata kwata sati ni'eema biyu da Nasir ya koreta sbd tanimi taka masa Fatima' ita kanta ni'eema batasan Fatima ke takawa Nasir birki ba a kanta sakamakon tun daren farkonsa da'ita a cewarsa besameta yadda take sons shiyasa tun washe garin bikin ya nimi bata takardanta amma Fatima ta hanasa. "itako ni'eema batasan wacce wainar ake toyawaba kullum da Fatima take kuka shiyasa idan ta tashi is kan in ta tace zatawa Fatima duka" Nasir ne ke shigarwa Fatima' gani h'aka yasata bari narar daba Nasir a g'ida ya gun aikinsa tabi Fatima har d'akin ta acewarta wai zaneta zatayi. "Itama dayake Allah yasa Fatima a tsaye take ga tsayi da jiki' tace bismillh idan bakayi kabani gu. "DA Allah yabawa Fatima Sa'a ta kwace igiyar hannu ni'eema tafara zuba mata da taji wiya da kanta ta gudu. "Da yamma bayan Nasir yadawo a zcyr Fatima bataso sanarwa Nasir ba' shiyasa koda yashiga d'akin ta yaganta wani iri ya tambayeta lfy cewa kawai tai babu komai' amma yana shiga d'akin' ni'eema ko zama bata bari yayi ba ta d'au igiyar radio ta mika masa. " Nasi yace me za'ayi dashi k'uma ni'eema? "ni'eema tace idan har kanason zamana dakai a cikin g'idan nan to ka amshi wnn wayar yanzu basae anjuma ma inaso ka zanemin Fatima a cikin g'idan nan. "murmushi Nasir yai h'ade da cewa kai h'aba dae wani abune tai maki? " ni'eema tace banida amsar baka a yanzu idan har kuwa kana bukatar amsa kabari sai bayan ka aikata abinda nasaka. "batare da musuba Nasir ya amshi wire d'in yanufi d'akin Fatima' yana fita ni'eema tai wani irin girgiza h'ade da tsalle ta f'ada akan gado tana murna. "Fatima na kwance a gefen gado Nasir ya shigo h'ade da cewa Fatima dama f'ada ne kukayi da ni'eema? "Fatima tace me tace maka. " Nasir yace ke nake tambaya ko ban'isa ki sanarmi bane? "Daga nan Fatima ta kwashe duk yadda sukai da ni'eema ta f'adi masa har tana kwalla. "A fusace Nasir yafita' yana shiga d'akin ni'eema ya h'au ta da duka saeda wire ya tsantsanke' yasake dauko balt d'in sa yaci gaba da Durante' duk ihu da ni'eema keyi a kunni Fatima amma besa ta fito cetontaba. "da ni'eema taga ba sarki sae Allah a guje tafice daga d'akin waje tanufa direct babu ko mayafi banle takalmi sae g'idan su. " Bayan ta fitane Nasir yaje yana bawa Fatima hakuri. "da yamma iyayen ni'eema suka dawo da'ita lkcn Nasir da Fatima suna parlour suna kallon lbrai' iyayen ni'eema sukai sallama suka shigo'suna shigowa bayan sun gaisane Fatima ta mike tabasu gu. "Nasir yace lfy kunzo ku tsattsareni da ido wani abune yafaru? kishiyar mmn ni'eema saeda ta d'an gyara zama kafin tace komai. "batare daya kalleta ba yace Dan Allah kiyi hkr kada ki yagamin rigan cushion nasan koda'yarki nasa akasuwa bazatai farajan cushion d'in na ba. "A fusace ni'eema tace h'aba Nasir mmntace fa kake f'adi mata irin wann mgr... "Tsawa Nasir ya daka mata h'ade da cewa kimin shiru ko nasake masa d'an bansan duka' d'an uwarkice sae me kotane tai abin duka bazan duketa bane? ko kina da uban da zai rama makine?. "kae Nasir ya'isheka h'aka banza kawai mara mutunci.. "kafin ta karisa tuni Nasir ya dauketa da mari. "kishiyar mmn ni'eema na gani h'aka ta kamo hannu ni'eema tace zomuje daga gani wnn mutumi ba mutucine dashi ba.. "B'ude b'akin Nasir yace kuma mutuncine daku? banzaye kawai masu kwadanyi kawai. "Ni'eema tace kaene banza ba dae ni ba. " kanta Nasir yai zai kae mata duka. "da sauri kishiyar mmnta ta janyeta' h'ade da cewa rabu dashi muje. " Nasir yace ina zaki? tsaya to nabaki abinda ya kamaceki' be kamata kije g'ida ba tareda tsaraba ba' jeki na sakeki saki uku.. "matan dake rike da hannu ni'eema tasa kuka h'ade da salati.. "Nasir yace Dan Allah gyatuma kinmin shiru kada ki taramin jama'a a g'ida aga kamar mutuwa akayi. "fusge hannunta tai daga hannu matan dake rike da'ita tajuya zata shiga ciki... "da sauri Nasir yace ina zaki?. " kayana zankwaso. "kayan ubanwa?da uban me kikazo g'ida. "Shiru ni'eema tai ta tsareshi da ido sbd tssan dae babu abinda tazo dashi komai na d'akin' ta shine ya zuba. " Nasir yace wlh idan baki bacemi da gani a gaba ba saena babbalaki a kwasheki a baro. "matan najin h'aka da sauri ta jawo hannu ni'eema suka fita. " Nasir yace shegiya kawai. "nasan duk wacce zata aureni sbd kudi nane inda badan kudi ba nasan ko kallon banza ban ishekuba. "bayan rabuwa da ni'eema da sati biyu yasake auro zuwaira' zuwaira ce suka dade da Nasir sbd bame baki bace' k'uma da ta lura yana matukar son Fatima d'an h'aka ta kwantar da kanta kasa' dukkansu su biyun idan sukai mgn bata musu. " da h'aka tai cikin kissa da kisisina tasamu ta h'ada Nasir da Fatima f'ada har yakai ga Nasir ya kori Fatima takoma g'ida kano' bayan tafiyar Fatima kano da wata daya shiru shiru Nasir beje biko ba amma mahaifin Nasir yaje bbn Fatima yace yaji but sae Nasir yazo da kansa snn Fatima ta koma. "gani shiru Nasir bezoba yasa Bbn Fatima ya turata kasar waje taje h'ada doctoring degree d'in ta. "itama zuwaira bayan tafiyar Fatima Nasir ya kamata taje fasa masa kofa zata diba masa kudi saeda yai mata duka snn yasa police suka rufeta satinta guda snn aka sakota shima ya rubuta mata takardan saki yabata snn yarufe g'idan sa tanufi kano. " koda Nasir yaje bega Fatima ba k'uma mahaifinta yaki fadin kasar datake. "h'akan yasa Nasir kamar zaiyi hauka' da yaga bazai iya jure rashin taba h'ada kayansa yai yabita duk kasar da yasan tana zuwa kafin suyi aure da inda bbnta ke turata harkan bnz d'in sa' da k'uma inda tai karatu saeda Nasir yaje amma duk abanza d'an beganta ba. "h'akan yasa Fatima tasamu tai karatu hankalinta kwance tana gamawa tadawo g'ida najeriya' bbnta da kanshi yaje tarota a airport' yana isa nasar yana isa. " H'akan yasa tana saukowa bbnta yace tabi mijinta sutafi. "itama bata Musa na sbd tayi kewar masoyinta. " Nasir baki har kuni yake godiya' biyawa yai g'idan su ya dauki yaransa suka koma binni kebbi. "tun daga lkcn Nasir yake taka tsatstssan da Fatima' amma duk da h'akan be hanashi aurensa ba sae k'uma yadaena auren bazawara saedae'yanmata wacce bata wuce secondary wata ma bata karewa yake aure' amma kuma baya hadasu gu daya kowa da g'idan sa. "Da zaran yaji ta sake zaisaketa yasake auro wata' duk cikin yaran da yake aura aishan ce kadae me diploma k'uma itace ta dade dashi sakamakon soyayyar da take masa yafi wanda shi yake mata. " ba komai ya jawowa Aisha h'aka ba sbd Nasir mutum ne me dadin baki da k'uma duk yadda zaiyi yaga yacimma burinsa akan abinda ya kudura sae yayi sbd iya baeti' dayake Aisha JJC ( Joly just come) ne sae ta tsunduma. "H'akan yasa tasha wuya dashi' d'an ma tagode Fatima batada keta. "Nasir yana kai Aisha tssha drop ya daukan mata har bauchi snn ya d'au dubu dari yabata yace tayi tsaraba dashi. "Batare daya tsaya yaga tashinsuba yajuya yai tafiyarsa ko waige beyi' itako Aisha harda kukanta. "G'ida kai tsaye Nasir yakoma shina gashi d'akin' Fatima yaje gainta yai kwance shima tubewa yai ya kwanta kusa da'ita h'ade da cewa kae yau narabu da ala kakae nahuta zanyi bcc har nazidda miyau. "gani duk mgnr da yakeyi Fatima bata tanka masa ba yasashi cewa baby kinyi bcc ne? "banza dashi Fatima gani h'aka yasa Nasir jawota jikinsa ya rungume ta yana f'adin h'aba Fatima dina kardae ace fushi kikeyi dani? karamar tsaki Fatima tai masa. " Nasir yace amma kinsan nasha f'adi maki banason tsaki ko? Fatima dake fa nakeyi amma kika kyaleni ko? da yaga batada niyar mgn mikewa yai ya haye kanta h'ade da fara yimata kiss' a dole yasa Fatima ta tanka masa. ~~~~ ~~~~ ~~~ "Aisha bata isa bauchi ba sae around eleven PM har kofar g'ida drive yakai ta sae da ya tayata kwashe jakar zuwa cikin g'ida snn yafito yai tafiyarsa' a guje Aisha taje ta rungume umma tana h'ade da fashewa da kuka. "umma tace aishan kece h'aka a irin wnn lkcn? sannu da zuwa Aisha' riketa umma tai suka shiga daki' bayan su gaisa ne umma tace ina maigidan naki? " Aisha tace yana lfy duk suce suna gaida ku' Aisha na mgn ne kawai amma hankalin umma baya gun ta mmki kawai takeyi sbd gani yadda Aisha ta rame' dama ba me kiba bace sae takara ramewa sosae. "sallamar Abba ne ya katse tunanin umma tadawo da tunaninta gun su. " Abba yace wanake gani kamar Aisha? cikin murna Aisha tace nice Abba mikewa tai taje inda yake tsaye ta duka har kasa ta gaida shi' Abdul ma yashigo shima yai murnar gani 'year"uwansa kusan kwana sukai suna hira ita da ummata' da safe tace Abdul ya rakata kasuwa siyayya sukai sosae taiwa Abba da umma sae k'uma Abdul ya"uwa kuwa sabulai da klin tasiye masu sbd kudin daya rage bazaiji tasiye masu zannuwa ba. "Umma da Abba sukai ta samata Albarka' Ita da Abdul sukai ta zaga ya"uwa da abokan arziki tai ta raba masu abinda ya sauwaka a gareta' sukai ta samata Albarka. "Sati Aisha daya Ashe umma tana lura da'ita tunda tazo gari Nasir be kirata yaji ssaukanta ba h'aka k'uma gashi yau tsawon sati daya kenan da zuwanta amma Nasir koda wasa bekira Aisha ba' ko irin d'in gaisuwar safen nan babu. "Da safe lkcn suna karyawa umma tace niko aishan gani nake kamar tunda kiiazo maigidanki baya kiranki ko' sae da Aisha ta sukuyar dakai snn tace eh amma ina gani kamar aikine suka sha masa kai shiyasa. " umma tace wani irin aiki da zaihanashi kiranki Aisha tunda kikazo fa koda da wasa banji kince yau maigidana yakirani ba. "Aisha ta maske da lahhhh' yana kirana sae dae kika lkcn da yake kirana bakya kusane shiyasa kike gani kamar baya kira. " umma tace anya kuwa Aisha?. "Aisha tace da gske umma. "gani yadda Aisha ta zakalkale yasa umma bari zance. ~~~ ~~~~ ~~~ " Fatima suna zaune a parlour ita da Nasir yace Fatima,. "Fatima tace na'am. " Dan Allah inaso ki fahimceni k'uma kimi kyakykyawar fahimta kinjiko. "Fatima tace naji' ta amsa masane kawai amma tasan lbrin gizo baya wuce na koki. "Nasir yace Dan Allah Fatima ni Nasir nayi maki alkawari daga wnn bazan sake wani auren ba. " maskewa Fatima tai snn tace ban fahimci me kake nufi ba. "Mgnr aure mana Fatima. "Nasir kenan wani aure k'uma kake mgn akai' Ai kakare aure kenan sae dae in anayi a lahira k'uma sae kayi amma a duniya kayi na karshe. " Fatima kenan karfa ki mance ke bafa uwata bane banle kice zakimi baki. "nasan ni ba uwarka bace amma wani sashine daga bangaren rayuwarka. "Fatima!!!!!!. " Nasir!!!. "Fatima banaso musake samu matsala dake' bafa niman iziniki nakeyi ba sbd bani ke zamanki ba'kece kike zamana dan h'aka baki isa ki hanani jin dadin rayuwa taba,. " kae Nasir idan har kanada kunya ma ka dubi tsabar idona kazomi da mgnr aure Nasir' na rantse da Allah idan har kasake min irin wani mgnr wlh saena kira g'ida na sanarwa abbanka da nawa Abba na gwammaci sanadiyar h'akan yazama karken zamana dakai' domin duk hukunci da Abba ya yanke bazan musa masa ba' bakace ka'iya zirya g'idan mu ba' to wlh bakae ba kowa zaka tura na hakura dakae na har abada Nasir. "h'aba Fatima kinsan abinda kike f'adi kuwa? Fatima kifi kowa sani banaso naje na aikata zina ko kinfi son H'aka ne Fatima. " babu abinda ya dameni Nasir nidae aurene bazakayi saba. "to naji shikenan amma wlh Fatima baki isa ki hanani holewata ba. " Nasir kaje ka aikata duk abinda kai niya' nikuma wlh subma tallahi daga lkcn da kafara na haramta maka kaena har abada bakace kae ka'iya jaraba kamar bakin bunsurune ba. "Fatima ni kike fadiwa haka? " na f'adi Nasir' Nasir me narageka dashi Nasir?. "Shikenan Fatima naji na amince amma da sharadi. " f'adi naji. "daga yau a koda yau'she idan nazo da bukatata zaki biyami' idan har nasamu h'aka daga gareki ni Nasir nayi maki alkawarin wlh wlh wlh bani ba sake aure k'uma kema a matsayinki na matata ina bukatar addu'arki Allah yabani ikon jurewa h'aka. " wlh Fatima nima na gaji da barnan kudin da nakeyi wajan aurarakin da nakeyi. "naji zantayaka amma kaima saeka taimaki kanka kafin Allah ya taimakeka. " himm Fatima kenan' yanzu dae abani kayana na dana ko. "duk dariya sukai. ~~~ ~~~ ~~~~ " yau tsawo sati uku kenan da zuwa Aisha g'ida a yanzu da h'aka hankali Abbanta da ummanta yafara tashi' sbd duk wani karyan da Aisha ke masa dan kare Nasir yanzu dae yakae karke sbd kowa yasan dae akwai lauje cikin nadi. "h'aka yasa da dare Abba ya tsare Aisha akan saedae tafadi masu gskya abinda ya hadata da Nasir da har ya kotota g'ida k'uma yaki zuwa. " Aisha tai rantsuwa har da kukanta amma Abba yaki yarda' gani kukan da takeyi yasashi kiran Nasir. "lkc Nasir yana kwance jikin fatimarsa suna wasa gani kiran bbn Aisha zai takira masa yasashi kashe wayar gaba daya. " Fatima na gani h'aka tace waye? kafin ta karisa tuni Nasir ya toshe mata baki da nasa. "abban Aisha yace lalla akwai matsala. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES. F. O. W.☘. MMN USWAN 2⃣3⃣ "tun daga lkcn abban Aisha yake kiran Nasir' Nasir na gani amma bazai daga ba' har saeya gaji d'an kansa ya hkr. "itama Aisha tai iya lokarinta wajan kiran Nasir amma duk a banza, umma tace a gskya Alhj Akwai matsala sbd idan lfy klau babu yadda za'ayi yaturo Aisha har na tsawon mako uku tana niman shiga na hudu amma bece tadawo ba' ni dama wlh tunda Aisha tazo nake lura Nasir betaba kiranta amma a lkc kodae nai mata mgn cewa tai yana kira amma yanzu da gskya tai halinta bagashi kowa ya gani ba. "Alhj yace gskya ne amma yanzu menene abinyi?. " abinyi kenan akirashi aji wani irin leifine tai masa da har zaiturota g'ida batare da ya biyota ko yakira yasanar damu ba abinda tai masa ba' idan ma yana gudun ya dauki mataki da kansa kenan. "h'aba Hafsatu wani irin mgn kikeyi h'aka kwata kwata guda nawa Aisha take da har zaiji tsoron ya hukutata, idan tun yanzu yana tsoron yai mata hukunci to gaba fa?. " Aisha na jin h'aka tasa kuka tana f'adi banlema ni babu abinda nai masa kawai ina zaune yashigo yace na h'ada kayana zaikaini tasha yasani a mota nazo g'ida. "salati umma tasa tana cewa kajiko Alhj. " shiru Abba yai sbd ya kasa mgn, gaba daya kansa ya daure. "Allah ya'kyauta kawai ya ambata. ~~~~ ~~~~ ~~~ " Alhj Kailani mahaifin zahradee ba karami alfahari yake da yiwa ubangiji godiya da azirtashi da zahradee ba sbd a yanzu da h'aka arziki yaci uban na dah! duk yadda yasan zahradee adah ba lalla bane yanzu idan ya gansa ya ganesa ba sbd canzawar da yai ga fari ga'kyau da k'uma raina gashi yaro d'an kwalisa' duk wanda yasan me ake kira raina akaga zahradee tofa anga raina. "h'akan yasa Abba ya siya masa fankareriyar mota ta alfarma h'ade da kujeran hajji da umra. " h'akan yasa yan'mata suke ta kawo masa hari' text message yan'mata kuwa ba'a mgn wani ya karanta yai dariya wani k'uma baya karantawa sae dae idan su ishesa a waya sae yagoge' h'aka mafi yawanci lkt idan suna zaune da Abba dauko wayar yakeyi ya nunawa Abba hotunan harda karanta masa text d'in shida Abba sui ta dariya. "cikin wasa Abba yace to son wacece sarkuwar tawa a ciki?.. " zahradee yace wa🤔 d'an Allah Abba karufami asiri d'an baso kake su kashe maka son d'in kaba. "Abba yace a'a Allah ma ya kare. ~~~ ~~~ ~~~~~ "Nasir na zaune shida Fatima a d'akin' ta bayan yara sun tafi school' idan tunda aisha tabar g'idan Nasir becika zuwa aiki ba' Fatima tace Nasir. "na'am matata. "dan Allah na tambaye ka?. "tambayeni Allah yasa nasani. "ina fatan ka sanarwa Aisha mgnr sakin da tsakaniku ko' kodae kanada ra'ayin ci gaba da zama da'ita ne? kae koma kanada ra'ayin ci gaba da zama da'ita amma kasan yana d'kyau tasani ko.. " himmm!' Fatima kenan tunda nake dake kintaba gani narabu da mace k'uma nadawo da'ita aini bana kome' idan ma zandawo da'ita ne to gara nayi wani auren zaifimi. "amma Aisha ai tatafi kenan. "Tunda h'aka ne gskya yakamata ka sanar da'ita dan tasan matsayinta. "Eh" zansanar da'ita ko ba yanzu ba. "har tsawo wani lkcne zaka sanar da'ita Nasir? gara tunda wuri kasanar da'ita Dan tasan matsayinta. " ko k'uma fa h'aka ne gskya kinkawo shawara mai'kyau. "Nasir kenan kai dae Allah ya'kyauta ma halinka. "Ai ya kyauta min tunda ya barni dake. ~~~ ~~~ ~~~~ "kwanaki sae tafiya sukeyi tun Abba yana hana umma mgn har yakai abinda yafara damusa yan' uguwa har sufara rade radin kodae sakota akayi? itama kanta Aisha abinda duniya duk yabi ya dameta. " idan tafita uguwa har zunde ake mata' masu cewa maganin masu kwandayi kenan shidama a rayuwa idan mutum be gogewa rahamar da Allah yai masa zai godewa azabarsa. "gashi kenan aure ko shekara be h'ada ba ya mutu. "duk mgnr da akeyi a gari yana zuwa kunni umma' hakama da akai rasuwa kwabtansu umma tace Aisha ta tashi suje gaisuwa' babu musu Aisha tasanya hijab d'in ta suka tafi' zamansu kenan aka fidda gawa zuwa gun sallah duk mutani dake gu suka mike h'ade da salati can wata matar dake gefe ta hango Aisha suna tsayen take tabo yar'uwarta h'ade da cewa dubi Aisha Ashe dama da gske ne auren nata ya mutum? " kedae bari kawai h'aka nima naji lbr' amma fa basu sanarwa kowa ba. "Allah sarki wlh har taban tausayi' dubi yarinya salbebiya akirata da suna bazawara' gskya maigidanta be'kyauta ba'idan ma wani abu tai masa ai sae yai dubi da kuruciya amma ba ya sakotaba. "Ohooo koma menene ai su suka sani' ba sunce yar' mai kudi bazata auri d'an talaka ba' sai yar' mai kudi irin sa' ai gashi auren maikudin yayi kyau. "Nifa tsiyana dake kenan Hulera ke a rayuwarki abu betaba samu mutum ba ki tausaya masa' banle ni banga aibu Alhj Muhammed ba sbd a layinga idan bezo na daya ba zaizo na biyu wajan dukiya' ga k'uma sani hakkin talakawarsa kema shedane sbd koda rabo yakeyi kafin yazo guna sae yazo gunki' idan ma lkcn fidda zakkansa beyiba ni da kaina nasha gananki kinfito maula.... " Too talatuwa kada kimin tonan silili maulanna dae kowa na zuwa. "duk mgnr da sukeyi umma da Aisha suna jinsu' Aisha dake gefen umma batasan lkcn da tafashe da kuka ba' gani h'aka da sauri taja hannu Aisha suka koma g'ida. "washe gari da safe around eleven saega ubaida tai sallama Aisha da fara'arta ta tareta' bayan ta gaida umma suka shiga d'akin' ta. " Ubaida tace Dan Allah Aisha kiyi hakuri wlh naji abinda ya faru' naso zuwa Allah Bbn Abba yahana' kinsan tunda suka samu matsala da amaryarsa ya koreta g'ida ya shiga min wani sabon kunle ko g'idan mu bayaso yaji nace zanje sae ya muna bacin ransa' kinji dalilin rashin zuwana amma Dan Allah kiyi hkr. "murmushi Aisha tai h'ade da cewa babu komai ubaida. " Ke Aisha garin yaya h'akan yafaru?. "wasu kwallane masu zafi suka zubowa Aisha snn tace kenan ubaida bari kawai' daganan ta kwashe tun daga lkcn da take amarya har izuwa wann lkc ta fadiwa ubaida tana kuka. "Ubaida tace Allah sarki Aisha to ya'isa h'aka kodae na kuka' kefa musulmace k'uma me imani Dan h'aka ki dauki wnn a matsatin jarabta. " nan dae tai ta bawa Aisha mgn har ta dae na kuka ta saki jiki sukae hira sosae. "Ubaida tace wlh Aisha tun ranar saurin aurenki da Nasir da suka shigo godiya bayan daurin aure a lkcn ne naga Nasir ni kadae a zcyta nace tab di jam ina Aisha zata kai wnn mutumi' a cire jikinsa ko tsayinsa aka barki dashi aikuwa anbarki da aiki banle ga tsayi da jiki' lalla Aisha kinshi fama inama da gari daya muke washe gari nazo naga yadda kika koma. "Dariya Aisha tai snn tace ubaida kenan koma menene kafin nasan shi kin rigani. "Eh nasan da h'aka amma kinfi kowa sani Bbn Abba guda nawa yake da har zanji jiki. " amma yanzu Aisha aina kuka tsaya dashi? "himm wlh ubaida nima kaina bansan makomata ba' bansan abinda Nasir yake nufi dani ba' Abbana da kansa yasha kiran sa amma baya dagawa' nima da umma musha kiransa duk da h'aka baya dagawa. " ni k'uma har ga Allah nasan ba f'ada mukai dashi ba banle nace ko dan h'akan ne ya turoni g'ida h'aka kawai nefa ubaida. "kwallane suka zubowa Aisha. " da sauri ubaida tasa hannu ta sharewa Aisha hawayen snn tace to yanzu kinsan abinda zakiyi? "a'a". " Ina wayarki?. "gashi. "Amsa ubaida tai snn ta shiga gun text tafara da ( Assalamualaikum Barka da warhaka da fatan kana lfy Allah yasa h'aka amen, abban Khadijat nayi ta kiran wayarka baka daga amma nai tunani ko baka kusane shiyasa, Gani nayi yau tsawon watana uku kenan da zuwa g'ida bakazo ka daukeni ba k'uma baka turoba Allah dae yasa lfyne.). " snn tai sending d'in text d'in. "yana shiga daedae lkcn wayar tana hannu Nasir' gani text yashigo ya b'ude bayan ya gama karantawa har ya'eje wayar a gefe sae k'uma ya dauko ya rubuta kamar h'aka. " ( Karkiji komai lfyta klau ki kwantar da hankalinki ko banzoba zakiga sako) snn ya tura mata. "yana shigowa suka b'ude ubaida ne ta karanta wani irin ajiyar zcyne Aisha tai. "Ubaida tace kingako Aisha Dan Allah kikara hakuri har Allah ya kawosa kikoma dakinki. " amin ubaida ngd sosae. "ni zantafi Aisha saena sake dawowa. " nan sukai sallama Aisha ta rakata har b'akin kofa. "tun daga lkcn idon Aisha kullum a kan hanya yake ko zataji Nasir yai sallama' gashi koda ta kirasa baya dagawa idan tai masa text baya biyota' h'akan yasa tasake shiga damuwa sosae kullum cikin kuka take. "Sbd kuka zazzabi ya kamata ga zafin da takeji a gabanta batare da tasan dalili ba' wasa wasa kuragen da tatabayi a g'idan Nasir ne suka dawo mata' tun tabasha amfikulos a boye har yakai ga saeda umma tasani' bayan ta sanine da sanarwa Abba' Abba da kansa yake siyo mata amma duk a banza. "Tun Aisha na daurewa tana tafiya har abu ya gagara takoma a kwance komai saedae ayi mata kusan kullum umma ke wanke mata ta shafa mata mgn' duk lkcn da umma zata wake mata sae ta daure sbd ihun da Aisha keyi. "Gani abu yaki ci yaki cinyewa yasa Abba d'aukarta zuwa hospital suna zuwa da doctor ya duba h'ade da yimata tambayoyi gado yabata' ko riga bata sawa sbd kullum s'au biyu ake wanke mata. "Gani wayarta babu caji k'uma hospital basu kuna generator ba yasa Abba daukar wayar Aisha zuwa g'ida yaje daga nan yai mata caji. " suna cikin tafiya Abdul ke drive saega shigowar text wayar Aisha. "Abba kamar bazai b'ude ba amma gani number Nasir NE yasashi budewa. "Gani yai kamar h'aka. ( Assalam Aisha kiyi hkr wlh mancewa nai kamar nace zakiga sako' to ba komai bane sakon dama takardankine gashine nan kamar h'aka, Ni Nasir guduma na sakeki saki uku sae anjima) INNALAILAHI'WAINNAILAIHIM'RAJU'UN KAWAI ABBA YAKE AMBATA. tofa jama'a Allah ya'kyauta 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE F.O.W.☘. MMN USWAN KAE KAE KAE WANI KAYA SAI AMALE BABBAN GORO SAI MAGOGIN KARFE MURUCIN KAN DUTSE BAKI FITOBA SAIDA KIKA SHIRYA INA MIKA SAKON GAISUWATA GAREKI Mrs G'IDADO MOM ABDUL JALAL KINA GABA MUNA BIYE DAKE JA GABA MANYANMU ALLAH YAJA DA NISAN KWANA YA KARA LAFIYA. 2⃣4⃣ "Abdul dake driving yace Abba lfy? wlh Abdul Mijin Aisha ne ta aiko mata da takardan saki. "Innalallahi'wainnailaihim'raju'un. "sakifa Abba kace?. "wlh kuwa Abdul. '"wlh Abba ni dama tun farkon da yazo niman aurenta hankalina be'kwanta dashi' kawai Dan babu yadda zaiyi ne. "hakane Abdul kasan ance matar mutum kabarinsa' babu damuwa Allah yasa haka yafi alkairi. "amma dan Abdul inaso kabar mgnr ga anan yatsaya gani sae kae. "Abba ko zansan dakikin biye mata?. "Eh" ba komai ne yasa sbd yadda take cikin irin wnn halin kaga be kamata a sanar da'ita irin wnn zancen ba. "Eh" k'uma mgnr ka gskya ne Abba'to shikenan fatanmu dae shine Allah yabata lfy. "Ameen' Abdul. "Kwanan Aisha bakwas a hospital safe da yamma sae an wanke mata kurajan' duk lkcn da za'a wanke mata idan har su umma da Abba suna gun' tashi sukeyi suyi nisa da gun sbd ihun da takeyi su k'uma hankalinsu tashi yakeyi. "gani ciwo yaki ci yaki cinyewa yasa Abba zuwa office d'in doctor bayan sun gaisa ne Abba yace a gskya doctor be'raina da yinkaba amma dan Allah inason zanyiwa Aisha canji hospital sbd banga wani progress da ake samu anan ba. "mirmushi doctor yai snn yace Alhj kenan laluran Aisha be d'anganci rashin kwarewar aikin mu' tunda kana gani kamar laifinmune to bari na f'adi maka gskya laluran Aisha ba karamin lalura bane' dama inason kashigo nai maka bayani sae gashi Allah ya kawoka. "a gskya Aisha tana bukatar kyakykyawar kulawa sbd wani cutar ba'iya waje ya tsaya ba can cikin jikinta yake shiyasa sae ammata gwaje gwaje sosae snn musan irin magani da zamu dorata akai. "to doctor yanzu me kake gani za'iya?. "abinyi yana gunka. "kamar yaya?. "to a gskya irin wnn lalura ba karamin kudi yake ciba' ba nan ba duk hospital da zaka kaita mgnr dae kenan. "yanzu kamar nawa kake gani zataci?. "A yanzu kam bazan iya f'adi ba sae yadda muka gani' abin nufi sae mufara mugano wacce irin lalurane snn k'uma mu abinda magani daya dace tai amfani dashi'zamuyi kokarin bata kyakykyawar kulawa wajan gani cutar besake dawowa ba. "to doct babu damuwa nidae fatana Allah yabata lfy. "Amin Alhj'. AFTER 2 DAYS "dict ya h'ada takardun duk wata gwaje gwajen da yaiwa Aisha da k'uma results d'in da yabayar' da Abba yazo kai tsaye office d'in doct ya nufa baya su gaisa sae da dotc ya gyara zama snn yace to Alhj gskya a iya binciken da mukai akan Aisha result na farko da yafara bamu shine a gskya dae Aisha tasamu matsala a mahaifarta wanda ba lalla bane ta mahaihu. "na biyu k'uma shine tana bukatar kyakykyawar treatment sbd cutar da take dauke dashi.. "A gigice Abba yace badae HIV bane doct?. "murmushi doct yai snn yace a'a Alhj. "ba HIV bane' wnn wani irin cutane wanda k'uma ina kyautata zaton tasamune a gun maigidanta sbd a iyan tambayoyin da nai mata da k'uma gwajin da mukai ya nuna mana cewa adah batadashi sae bayan auren ta. "to ni k'uma a Iya sanina da Aisha ba maza takebi ba banle nace daukowa tai gun biyebiyen maza. "ita k'uma irin wnn cuta daukarta akeyi. "maybe yana niman matan banza ko k'uma auri sakine sanadiyar h'aka ya dauki wnn cutar wanda har itama tasamu. "da alama shima kansa besan yana dauke dashi ba' sbd duk wanda yake dauke da irin wann cutar dole ya samu nakasu a harkokin lfyrsa' ma'ana ta hanyarne yake iya harbawa wani. "Amma zamuyi iya kokarinmu akan Aisha mgnr haihuwa k'uma maybe maybe zata iya samu nan gaba' amma dae anya kuwa" himmm!!. "to nidae doct abinda yafi damuna shine naga Aisha tasamu lfy' shine babban matsala ta. "karka damu Alhj insha Allahu zata samu lfy nan bada dadewa ba' tunda yanzu mugano cutar da take dauke dashi. "to nagode doct. "nima nagode". "tun daga lkcn aka canzawa Aisha maguguna' mgnr kaikayi da zafi da suke hanata bcc duk tafara samu saukinsu shiyasa yanzu h'aka koda doct yazo wanke mata gun batajin zafi kamar yadda da takeji' sbd doct yana shigowa da kanta take b'ude masa gababta ya wanke snn ya shafa mata magani'. "In day!! ne kuwa sae yazo da masu riketa' duk da h'aka be hana Aisha ihu da shure shure' hatta makwabtanta sae sun san ana wanke mata ciwo sbd ihu. "tuni zahradee yaji labarin Aisha tadawo g'ida' tun kafin Nasir ya aiko mata da saki tun anriga ansanarwa zahradee da cewa Aisha batada aure' da k'uma sanar masa halin da take ciki na rashin lfy. "Zahradee yai matukar tosaya masa amma a yadda yakeji a zcyrsa ba zai'iya zuwa gaidata ba. "sae dae a matsayinsa na masiyinta zaitayata da addu'ar samu sauki. "Cikin hukunci ubangiji a hnkli Aisha tafara samu sauki' yanzu har zama tanayi k'uma tana iya tashi ta d'an zaga d'akin. "Abba da umma suji dadi gani 'year"su tafara samu sauki. "Yau ma da ubaida tazo dubata har waje suka fita can wajan wani gidin bishiya suka zauna' ubaida tace niko Aisha kinsanarwa Nasir kamar bakida lfy? "a'a ubaida bansanar masa ba' niso na nasar masa amma wayar bata hanuna' tun ranar da Abba ya amshi wayar yace zaije g'ida yasamu caji shine besake dawomin dashi' koda na tambayesa cewa yai ina ta kainane ko inata waya. "ni k'uma tun daga lkcn besake tambayarsa ba. "To Allah ya kyauta' amma ai yakamata ki sanar dashi koda bazaizo ba' tunda zamansa kikeyi yanada'kyau yasani. "Eh" nima nayi tunani h'akan ubaida amma babu yadda zanyine. "Abinda yafi damunama shine besan halin da yake ciki ba' sbd nasan inda lfy klau ne Nasir bazai barni na zauna a g'ida har tsawon wnn lkcn ba. "kowani haline yake ciki oho Allah ne masani. "Aisha na mgnr ne tana kwalla. "To Aisha Allah ne masanin komai' duk ma halin da yake ciki dae addu'a ne naki insha Allahu Allah zaikawo masa mafita. "Amin ubaida ngd. "sun jima suna hira ubaida natabawa Aisha hkr da cewa Nasir yananan zuwa gateta insha Allahu' da h'aka har yamma yai snn ubaida ta tafi g'ida. "Sae da Aisha ta shafe wata daya da kwanaki snn suka koma g'ida mgnr sauki kam ba'a mgn sae dae ramar datai. "da h'aka Aisha taci gaba da kula da kanta'shima Abba kusan kullum idan yana dawowa daga kasuwa saeya siye mata kayan marmari h'ade dasu frue a hankali Aisha tafara maida jikinta. "mgnr waya kuwa kusan kullum sae tayi amma Abba yaki bata k'uma yacewa umma kada tabari Aisha tai amfani da wayarta wajan kiran Nasir. '"mmki ya kama umma'umma tayi tayi da Abba akan ya sanar da'ita dalilin h'akan yaki. "shiyasa tun tana mgn har tagaji ta hakura' da mgnr' h'akna yasa tai tunanin zuwa g'idan ubaida sbd tai amfani da wayarta takira Nasir idan a yanzu da h'aka kewar Nasir takeji. "tana matukar son gsnisa koda bazai mata komai ba' amma k'uma kash!!!. sae tai rashin sa'a koda ta tambayi umma' umma kin yarda tai a cewarta wai abbansu yace kada abari tarinka fita ko nan da kofar gida ne. "babu yadda Aisha zatayi dole yasa ta hkr. "Tunda Aisha taji tasamu sauki tasawa iyayenta kuka ita zata koma g'idan mijinta' duk yadda umma takai ga lallashinta amma Aisha taki hkr h'akan yasa da yamma bayan Abba yadawo daga kasuwa umma ta sanar masa. "Abba yace ta kira masa aishan' mikewa tai taje dakinta ta kirata sukazo tare. "Da sallama Aisha ta shigo dakin bayan sun gaisa snn tace Abba gani' Abba yace Aisha. "na'am Abba". "naji sakonki a gun ummanku' h'akane?. "jiki a sanyaye tace eh'Abba. "Amma ke Aisha meyasa kikason komawa g'idan Nasir baki gani akwai tutarwa a zamanku? yanzu sbd Allah me sonka tsakani da Allah kenan zai turoki g'ida tsawon wata hudu babu ko waiwaiye? yadda sbd Allah kina gani yai maki adalci kenan?. " h'akace nima nasan be kyauta ba amma Dan Allah Abba kuyi hkr' babu mmki wasu uziririkane suka shamasa kai da yazo amma Dan Allah kayi masa hkr Abba. "Aisha kenan bafa ba mgnr hkr nakeyi ba. "eh"to Abba inaso na koma. "ina Aisha?". "Aisha kiyi hkr babu inda zaki.. "kuka Aisha tasa tana f'adin Dan Allah Abba kayi hkr. "Aisha kiyi hkr Nasir baya sonki' ni k'uma bazanso 'yanta taje inda ba'a sonta ba'. "a'a Abba wlh baka fahimcesa bane yasa. "himm" Aisha kenan". "Aisha kinfi kowa sani kukalai keda kaniki Allah yabani a rayuwata Dan h'aka bazanso naga abinda zai tabamin Ku na kyaleba. "ko aurenki da maigidanki Allah ne kawai yai da k'uma namu gudumuwar na rashin bincike sbd a lkcn dukkanmu idanumu ya rufe' Aisha a gskya kinban mmki sbd a rayuwata da k'uma irin tarbiyan dana baki banta tunanin zakimin h'aka ba. "bayan aurenki da Nasir labari yazomi duk irin rashin mutunci da rashin adalci irin naki dan Allah ma shedane banmaki irin wnn tarbiya ba' shine bika juyawa zahradee baya' ke a ganiki kinmasa adalci kenan?. "Allah ya gani bankasa da komai a g'ida naba banle ace rashine yasa yai maki duk irin hidimomin da yai maki' amma ni nasan so da kauna ne yajashi ga h'aka. "Aisha nasan ba rokonsa kikai ba' amma kodan darajar soyayyar da yake maki wlh be kamata ki masa haka ba. "tunda Abba yafara mgn jikin sisha yai sanyi" kukanma da takeyi ya gagara. "Abba yaci gaba da cewa bazan boye maki ba Aisha tun bayan tafiyar wlh kasa h'ada ido da Alhj Kailani nayi sbd bansan da wani ido zan kallesa ba. "duk da shima bezo yaimin bayani ba amma banyi blimey nashiba sbd tun bayan tafiyarki zahradee yashiga matsanaciyar hali na rashin lfy wanda dakar mahaifinsa yasamu gano kan d'an sa. "duk halin da suke ciki lbr yana zuwamin naso naje amma matsalar shine bansan da wani ido zan kallesu ba. "yanzu dae koma menene Aisha gashi nan kin gilbi kayanki' rashin hakkinkine da bandashi shiyasa' sbd kin nimi kibani kujya a idon duniya ki zubarmi da mutunci k'uma ki hakani f'ada da jama'a to ta Allah bataki ba' sbd yanzu da h'aka ina me tabbatar maki Nasir ya aika maki da sako tun ba yau ba'ga salon nan. "mika mata wayarta yai snn yace b'ude ki karanta sakon. "jikin Aisha har rawa yakeyi wajan budewa. "koda Aisha ta bude bata karisa karantawaba ta sulale ta sume. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘. MMN USWAN 2⃣5⃣ "Umma na gani Aisha ta sume tasa ihu h'ade da kuka' Abdul dake zaune a gefensu a guje yaje ya d'ibo ruwa' yana dawowa jikin umma na rawa ta amsa ta yayyafa mata. "duk abinda sukeyi Abba na kallonsu amma be tanka masu ba" duk da shima d'in ya razana amma ya matse yanuna ko a jikinsa. "umma ta kuka h'ade da kiran suna Aisha. "Aisha na farfadowa h'ade da sauke wani irin ajiyar zcy. "daga umma har Abdul sae faman sannu suke cewa Aisha. "Aisha na dawowa normal tasake fasawa da wani kuka. "tsawa Abba ya daka mata h'ade da cewa rufemin baki" yarinyar banza kawai. "a'a" Alhji"... "rufemi baki' ko kema nadawo kanki. "dama duk wani irin abinda yaranga zasuyi ba a gunku suke gani ba.. "h'aba Alhj... "Au bazakimi shiru ba?". "tun daga snn umma bata sake mgn ba. "Aisha dake zaune sae faman nufarfaki takeyi h'ade da ijiyar zcy. "Aisha". "na'am" Abba. "inaso ki saurareni da'kyau. "to'Abba". "Aisha kinsan duk cikaiken musulmi ansanshi da yarda da kaddara me'kyau ko'mummuna ko Aisha?". "h'aka ne'Abba". "Aisha inaso kisan cewa duk abinda ubangiji aiwatar akan d'an"Adam yaga h'akan yafi dacewa da shine yasa yai masa h'akan. "h'aka ne"Abba'. 'yawwa Aisha ta"shiyasa tun kina yarinya nake alfahari dake. "murmushin karfin h'aka tai. "Aisha inaso duk mgnr da zansana dake bazaki nuna damu ko bacin rai ba. "babu komai Abba". "sba ita rayuwa da kike gani babu yadda za'ayi kayi rayuwa batare da Allah ya jaramceka ba. "h'akane'Abba". "k'uma dama ba komai kakeso k'uma ka samuba" idan har kikaga mutum yana samu yadda yakeso tabbas akwai matsala nan gaba. "Dan h'aka Aisha kiyi imani' ki yarda da cewa Allah shine me kashewa k'uma me rayawa' babu wanda yafi karfin jarabata a rayuwa. "shiyasa ake cewa idan baka mutuba Allah begama canza maka halinta ba. "gskya Abba". "babu komai Abba" kafadi kawai na maka alkawarin dan'newa koma menene shi. "alhandullh". "dama ba komai bane Aisha lkcn da muke asibiti dake bayan binciken da docts sukayi shine suka gano cewa kinkamu da wata irin lalura wanda kika dauka a gun mijinki sanadiyar h'aka ya kashe maki mahaifa' bazaki sake haihuwa ba... "A take taji kirjinta yabuga dim dim dimm" har sae uku' wani irin mummunar ajiyar zcy tai" kwalla suka ciko idanta' jikinta har rawa yakeyi. "Idan niman sassauci a zcyrta tafara karanta" ALLAHUMMA AJIRNI FI MUSIBATI".( BATARE DA TA KAREBA TA DAUKO" ALLAHUMMA LA SAHLA ILLA MA JA'ALTAHU SAHLA FA ANTA TAJ'ALUL IHAZNA IZA SHI'ITA SAHAL.) BAYAN DA KAMMALA TA SAKE DAUKO (RABBANAA INNAKA TA'ALAMU MA NUKHFII WA MAA NU'ULINU WA MAA YAKHFAA 'ALAL-LAAHI MIN SHAY'IN FIL- ARDI WA LAA FIS-SAMAA') "H'aka Aisha tai ta jeresu a cikin zcyrta. "a take tasamu natsuwa. "Abba yaci gaba da cewa kinsan babu yadda Allah baya juya lamarinsa' ba lalla dan su f'adi h'aka yazamanto da gske h'akan zai kasance ba. "h'akane Abba". "sbd h'aka inaso kita addau'a Allah ya kawo mana sassauci ciki lamarin. "Ameen". "k'uma muma Dan Allah ki yafe mana sbd muma muyi kuskure a matsayinmu na manya da muka biye maki' da k'uma rashin bincike akan Nasir. "Aisha a gskya naso nayi bincike a lkcn amma yadda ya nuna mana da k'uma irin mutani daya kawosu a matsayinsa na babba' banzaci h'aka daga garesa ba. "Aisha kiduba irin dattijan daya kawo kae harda ma shi kansa babu Wanda zai zaci h'aka daga garesa. "h'akan yasa naji karfin gwiwar amincewa na bashi ke'Ashe kallo kirse nakewa rogo. "kema Aisha harda naki contributions d'in nayi inama a lkcn inda kinfito kice bakison zahradee wlh bazan tilassa maki ba. "banle ma ba shine ya kikiba kece kika kisa' wlh Aisha bayan tafiyar da gskya ta bayyana naji kunya matuka h'ade da jimaki takaicin rashi samu surikai na gari' da bakarami gata zaki samuba Aisha. "sbd halin mahaifin yaronga ni me tafiya nimo masa aure ne' banle yace kece yakeso. "amma babu damuwa' h'aka Allah ya tsara maki. "Allah k'uma yasa h'aka yazama izina da aya. "Abdul dake zaune yace amin Abba". "shiru Aisha tai hawayene kawai ke kai kawo a fuskanta. "Aisha kina jina kuwa?". "ina jinka Abba Allah ya yafe mana baki daya". "amin Aisha." "mikewa tai tanufi d'akinta' tana shiga fadawa tai a kan gado taci gaba da kuka. "tun daga lkcn Aisha ta goge number Nasir na wayarta' duk wani Abu da tasan yana sa tarinka tunawa da Nasir ta dae na. "bayan kwana biyu taje g'idan ubaida' bayan su gaisa Aisha ta kwashe komai ta sanarwa ubaida da mgnr sakin da Nasir yai mata. *"ubaida tai salati ta sanarwa Ubangiji h'ade da tambayar tun yaushe h'akan yafaru? "Aisha tace tun lkcn ina hospital" Ashe kenan koda muke mgn yarida da yai sakin. "wlh kuwa" "amma gskya banji dadi ba" Allah yasa h'aka yafi alkairi". "amin ubaida". "kice ma har kin kusa gama iddah kenan?". "Eh kwanaki yarage min". "kawata kodae rabon zah ne?". "himm ubaida kenan" kina gani irin butuncin da nai masa zahra zaidawo gareni kuwa?". "ubaida kinsan ita so yadda take". "Eh" nasan da h'aka' amma ba lalla bane h'akan ya faru' shiyasa ma bana kawo h'aka a zcyta. "Aisha ki kwantar da hnklinki k'uma ki dade da addu'a Allah yai maki zabin alkairi". "amin ngd". "ni zantafi sbd Abba ya hanani fita ko ina"fitar ma da nai yanzu besani ba". "to Aisha nima ngd"k'uma in Allah ya yarda zanzo". "ni ko ina sun Abba tunda nazo bangansu ba?". "suna g'idan kakansu" kinsanta da kulafaci". "him ubaida kenan kinanan dae da halinki". "Aisha meza"a fasa". "to sae anjima". "to ngd". AFTAE 1 MONTH "Bayan fita iddan Aisha wata asabar Aisha taje kasuwa siyo kayan kwalliya' wata dankareriyar shago tashiga wanda ya h'ada komai babu abinda babu a ciki. "duk tai ta juye juyenta tana kallon sababbin kayan kwalliya da suka fito' duk da jikinta be bata ba da shagon sbd tunda tashiga taji tsigar jikinta yake tashi h'ade da jin sanyi" amma h'aka ta matse sbd kada ta bada kanta ciki yan'matan dake shagon suma suzo siyar kayan kwalliyarne. "duk da wani abu batasan yadda zatayi amfani dashi amma h'aka ta dauka' sbd taga yan'matan da suka shigo suma duk sun d'au irin su. "h'aka ta zabi wanda taga zata iya anfani dasu da k'uma wanda bazasu bata wiya wajan koya ba. "bayan ta gama zabane takai gun da za'a f'adi mata kudin' Ashe zahradee yana ciki shida Ruslayni suna kallonta". "zahradee yaso yai mata mgn amma Ruslayni ya hanasa. "a cewarsa me zaiyi da'ita yanzu bayan tazama bazawara. "tun lkcn tauraruwarta na haskawa be samu ya aure ta ba sae yanzu da aka gama kwashe albarkatun jikinta. "murmushi zahradee yai snn yace abinda nakeso ka gane ita so babu ruwanta da wann. "so" d'in me?". "so d'in bazan". "Ruslayni bazaka gane bane wlh". "amma"... "gani Aisha zata fita' a guje zahradee ya fice daga d'akin da suke zaune shida Ruslayni yabi Aisha. "har tafita daga shagon tana kokari tsanllaka titi ji kawai tai anrike mata hannu. "a gigice ta juyo" gani zahradee ne yasata sakin ledar dake hannunta. "Da sauri tasa kae zata tsallaka titi batare da ta dubi titin ba. "gani mota yashigo a guje yasa zahradee yawota ta f'ada jikinsa. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. MMN USWAN INA TAYA YAR'UWATA MARUBUCIYAR DIJEEMA NUMAR KAMMALA LITTAFINKI HAKIKA KIN WA'AZARTA K'UMA KIN NISHADARTAR ALLAH UBANGIJI YA BAKI LADA ABINDA KIKAI NA KUSKURE ALLAH YA YAFE NAMA BAKI DAYA. 2⃣6⃣ "duk su biyun zubawa juna ido sukai' babu Wanda ya tanka a cikinsu' shiko zahradee tsurawa Aisha ido yai babu ko kobtawa. "A take Aisha taji tsigar jikinta yana tashi' da sauri ta fisge jikinta daga nasa' a lkcn ne zahradee ya dawo daga kogin da ya f'ada" h'ade da cewa ohhh! srry baby. "batare da ta saurari me zaice ba sa kai kawai tai ta tsallaka titi' ta barsa da ledan kayan make-up d'an a hannunsa. "da sauri shima yabita h'ade da kwada mata kira. "amma besa Aisha ta juya ba'banle ta tsaya. "gani ya dage da binta da sauri ta shige ta wani lungu. "ko kafin Zahra yace zaibita lungu ta riga ta shige' har da h'ade da gudu. "tsayawa yai yai shiru yana kallon ledan da tabarsa dashi a hannu' amma babu yadda zaiyi h'aka ya koma dashi. "Aisha na fita daga lungu ta samu napep ta h'au zuwa g'ida. " tana zaune a napep tana faman sake-sake kala-kala' suka isa'tana sauka ta bashi kudinsa snn ta shige g'ida. "tana shiga da sallama sukai karo da umma a bakin kofa umma tace kindawo Aisha. "nadawo umma. "baki samu kayan bane?". "Eh" a'a' bansamu irin wanda nakeso bane yasa ban siye ba. "him Aisha kenan" to yanzu wanne ne zankama daga cikin?". "Eh". ko a'a?". "au mantuwa nayi". " mantuwar me k'uma Aisha?". "Ina zuwa umma". "da sauri Aisha ta shige d'akinta. "murmushi kawai umma tai' sbd tasan ba kawai ba. "Aisha ta shiga d'akinta bakin katifa ta zauna tunani kala2 takeyi' a zcyrta k'uma tana tambayar kanta badai zahradee yanaso ya dawo guna bane?". "to mema zaiyi dani?". "kodae yanaso ya rama abinda nai masa ne?". "kae duk da dae baka shedan mutum amma zahradee da ban ne" sbd zahradee beda mugun nufi da kowa. "to amma idan ba zaice yana sona ba me zai kawoshi guna?". "kai anya zahradee zai iya dawowa gareni?" idan ya duba irin butunce masa da nayi". "bama wnn ba" ta yaya Zahra zaidawo gareni a matsayinsa na saurayi ni k'uma bazawara?' budu da kari k'uma ga mgnr rashan haihuwar dana samu. "duk da dae so bata duba da h'aka amma nasan idan har zahradee yaji wnn labari ba lalla bane ya aure ni' duk irin son da yakemi. "nima idan har zahradee yadawo gareni ba karami dadi zanji ba' sbd a gskya zahradee ya caccaci asoshi. "k'uma nima zanyi alfahari idan na samu zahradee a matsayin mijina. "kai amma Nasir ya cuceni" ko daya Nasir beda laifi dan ni nafisa laifi amma babu komai. "jin kiraye kirayen sallar azahar yasata mikewa taje ta dauki buta tai alwala tazo tafara sallah. "kai tsaye zahradee shagibsa ya nufa' be koma shagon Ruslayni ba'sbd yasan idan ma ya kai masa mgnr Aisha ba shiryawa zasuyi ba. "da yamma bayan sallar isha'i zahradee ya shirya cikin captai lkcn su Abba suna parlour yazo fita' Abba yace son ina zuwa kasha irin wnn kwalliya h'aka?". "murmushi zahradee yai kawai batare daya f'adi inda zaije ba' da sauri yabar gun yai tafiyarsa. "zahradee yana fita be karisa g'idan su Aisha ba sai da yabiya yaje yakara mata wasu siyayyar sosae snn ya karisa. "koda Zahra ya'isa kofar g'idan ciro wayar dake aljihunsa yai dialing number Aisha wanda ya santa dashi amma sai yaji shi switch off!" a dole yatsaya niman yaro Dan aikensa cikin g'idan. "zahradee yai kusan thirty minutes before yasamu yaron aike. "koda ya tura yaron ciki g'idan da sallama yashiga Abba ya amsa snn yara yace wai ana sallama da Aisha. "Abba yace waye ke sallama da'ita?". "yace nice zahradee". "Aisha dake dakinta tana jin taji kirjinta ya buga'innalallahi'wainnailaihiraju'un" kawai tace. "murmushi Abba yai snn yace zahradee fa kace yaro?" kodae mance suna wanda ya aikoka kai ne?". "a'a" shidin dai ne. "to shikenan jeka kace tana zuwa. "to". "yaro yana komawa ya sanarwa Zahra. "yace to ngd yaro"zo ugon wnn kasiya minti ko?". "amsa yai h'ade da gdy. "abba da kansa ya karisa bakin kofar Aisha snn yace kije Aisha". "na'am Abba". "kin jifa wai zahradee ne yazo gunki'kinga ikon Allah. "a gskya nayi murnar h'akan". "shiru Aisha tai kanta na kasa sbd duk idanunta sun ciko da kwalla. "Aisha kina jina kuwa". "ina jinka Abba". "to tashi kije Dan Allah kada yaga kamar walakanci ne. "to Abba". "mikewa tai batare da tatsaya kwalliya ba'hijab kawai tasa snn tafita. "tana fita umma tace ina zuwa Aisha?". "shiru tai kanta na kas!. "Abba ne yace zahradee ne yazo gunta. "zahradee fa kace Alhj?". "wlh kuwa Hafsatu. "ikon Allah kenan". "koda Aisha ta fita can gefe ta tsaya takasa karisawa gunsa. "Aisha ki kariso mana' kodae nine na kariso?". "shiru tai'kanta na kasa". "murmushi kawai zahradee yai snn ya kariso inda take tsaye yace Aisha kenan. "da sauri Aisha ta juya masa baya. "h'aba Aisha menene k'uma h'aka'kamar wata yaranya' har da juya baya". "Dan Allah kijuyo mana". "Aisha dake tsaye bata tankasa ba". "Aisha dake fa nakeyi". "kukan da takeyi a zcine ya fito fili". "Subhana'lillahi ya ambata h'ade da zagayowa gabanta' yana f'adin Aisha!" me zangani h'aka?" laifine akai maki? ko nine nai maiki laifi?". "kai kawai ta k'ada masa". "to menene?". "kai tasake kadawa". "ba zakiyi mgn ba?". "to shikenan ni natafi tunda bazaki mgn ba". "da sauri Aisha tace Dan Allah kayi hkr". "to kukan me kikeyi?". "babu komai". ki f'adin min Aisha". "a'a kabari kawai". "to shikenan babu komai'dama kinsan rayuwa yadda take komai yana iya juyawa k'uma a kowani lkc' bazaiyi mmki dan kimin h'aka ba' alamune da nunamin cewa yanzu kinfi karfina tunda kintaba aure... "a'a wlh ba h'aka bane". idan ba h'aka bane to menene?" nidai Aisha ta dana sani babu abinda take rufemi' amma yanzu kiga kenan alamune tamin nuni da cewa kintashi daga tawa da nasani kinkoma ta wani. "a'a bah... "ba h'aka bane me nene?" idan ba h'aka bane to inaso ki komami real Aisha ta dana sani. "yanzu kinsan me za'aiy?". "kai tadaga". "kinga matsonan". "tsayawa tai tsab a inda take sai dai shida yabita. "Aisha dago fuskanki kiga wani abu' hannu yasa ya ciro handkerchief daga aljihunsa ya goge mata hawaye tas snn yace yawwa ko kefa. "murmushi tai masa. "snn yace dama kayanki da kika gudu kika bar shine na kawo maki gashi". "hannu tasa ta amsa h'ade da cewa ngd. "sbd ita kanta tasan ba iya kayanta bane a ledar dan ba h'aka ledar kayanta suke ba. "snn yace ni natafi Aisha saina sake dawowa". "to ngd". "nima ngd" ki gaidami umma da Abba'snn ki kulami da kanki". "idanu kawai ta zuba masa". "sahibata ya!!!dae?" zo kishige snn natafi. "batare da musuba tabi umarnasa tashige snn shima yatafi. "koda Aisha ta shiga ciki snn umma tana d'akin Abba suna mgn' duk dai akan Zahra ne da Aisha ne da fatan Allah yasa yazo da mgnr yadawone. "shiyasa Aisha ta shige dakinta daya bayan daya take dago kayan take kallo h'ade da mmkin irin kudin daya kashe mata. "duk da dae ko da datasanshi h'aka yake amma daalamu yas amu budi fiye da da. "bayan ta gama kallon kaya ta medasu cikin ledar ta kwanta' cikin dare bcc ya gagareta sai faman juyi takeyi akan gado' gani tunani bazai kaimata mikewa tai taje ta doro alwala tazo tafara sallah' saida tai raka'a hudu snn tai sallama addu'a sosae tai h'ade da mikawa ubangiji zabinsa. "Zahra shima kusan hakane'koda safe daya tashi gaba daya yar'gidan suga canji a fuskansa har mmki sukeyi. "Aisha suna karyawa da umma lkcn Abba da Abdul sutafi kasuwa' umma ke tambayar Aisha yadda sukai da zahradee. "nidai becemi komai ba kaya nane kawai ya kawomi. "to shikenan Allah ya rufa asiri. "amin umma". ~~~~ ~~~ ~~~~ "tun bayan tafiyar Aisha Nasir da Fatima suka bude wani sabon babin soyayya ko fita yanzu becika yiba tare suke shirya su Khadijat da Jabeer zuwa schl suna tafiya kuwa shikenan kakarsu ta yanke saka sai abinda suka mance. "mafi yawanci lkt Bilyaminu ne kaya katsesu sbd aiyukan da Nasir kesashi' shiyasa wasu lkt idan yazo lkcn Nasir na daki cewa takeyi bayanan tunda ita kanta batasan abinda suke kullawa ba. "k'uma koda ta tambayi Nasir bazai f'adi mata ba. "yau ma da rana bayan sallar azahar suna zaune a parlour suna cikin wasa saiga kiran Hauwa ya shigo. Nasir yana gani kamar bazai daga ba ko mai yagani k'uma sae dae ya daga da sallama' Hauwa tace ranka ya dade ango Fatima. "Dariya nasir yai h'ade da cewa yau k'uma da sabon salo da kika bugo kenan madam Hauwa?". "To ranka ya dade menene duniyar?". "hakane Hauwa shiyasa kike birgeni". "duk mgnr da Nasir keyi Fatima na gefensa". "Dama ba komai yasa na bugo maka ba da lili kuwa shine na sanar dakai cewa a gskya Alhj ni nagaji da zama dakai' shiyasa ma naki dawowa garin. "kaji manyan mata" to yanzu me kikeso ayi?". "kafi kowa sani". "a'a"Hauwa a gskya abinda kikeso ba lallane ki samu ba". "H'aba dae Nasir" f'ade dae kakeyi ko?". "da gske". "to nidae a gskya nariga dana gama yanke hukunci". "bangane ba". "eh ina nufin na gaji da zama dakae". "kamar yya?". "kae nasir tunda nake a rayuwata tun bayan mutuwar uban'yar'yarna duk irin aure auren danayi bantaba shikara biyu dana miji daya kai a kanka Dan h'aka yanzu ni nagaji dakai canji nake nima". "to niko zan'iya". "me fa?" "rabuwar mana". "yanzu Hauwa me kike bukata?". "takarda". "shi'kawai kike bukata?". "Eh" "to shikenan' nima Indi kin kwantar da hnklinki inada niyar turo mana' sae gashi kinkasa hkr kin tambaye';amma duk be baciba sbd kin tunatar dani ne. "yanzu dai kije na sakeki saki uku. "Innalallahiwainnaillahim raju'un. "Nasir way me kadauki sakine?". "shiiiiinm🤫". "himm Allah dae ya shirya". "ina fatan kinsan dokata ko?". "daga lkcn dana saki mace cokali bata fita dashi daga g'idana" amma duk abinda kikasan nabawa yara' tunda marayune kizo ki kwashe masu nabasu duniya da lahira. "kai ne wann yadama nasir". "kema ya dameki Hauwa". "kashe wayarsa yai batare da sallama ba". "yanzu Nasir sbd Allah mekuma Hauwa tai da'ita ma ka saketa?". "Fatima bazaki gane bane" shegiya ta dauka da gske ne nake bata hkr?" dama duk gwadata nakeyi naji me zatace' angaya mata a rayuwa ina aikin banzane?". "yaushe zan zauna da mata bata biyami bukatata k'uma tace tanaso tasamu yadda takeso. "humm nidae wlh banji dadi ba". "kada Allah yasa kiji dadi'tunda ina tare dake ai niko nakeda jin dadi. "him nasir kenan". "Fatima kenan" ~~~~ ~~~ ~~~~ "bayan kwana biyu zahradee yasake dawowa g'idan su Aisha wnn karo har cikin g'ida yashiga suka gaisa da umma da Abba snn yafita. "sae da Aisha ta d'an gyara snn tafita" bayan su gaisa' Aisha kinsan ance da sassafe ake kama fara ko?" a gskya Aisha tunda lkcn da kika dawo gida naji lbr har izuwa lkcn da kuka rabu Allah ya kiyaye na gaba. "amin ngd" "Aisha bada bata lkc ba nazo da kokon baratane a karo na biyu ko yaya kika gani?" "uhm" "Aisha idan har kika amince min ina me tabbar maki cikin satin nan zanturo a nimamin aurenki ke inda da halima zanso a daura kawai' sbd bazanyi sanya irin wacce lkcn na. "aure k'uma". "Eh" aure". "a farko na daukeshi kaddara amma wlh a wnn karo idan har kika sake na rasaki wlh Aisha bazan yafe makiba Aisha. "Aisha ina sonki'Aisha kodan bakisan halin dana shiga bane bayan tafiyarki' to wlh a wnn karo bazan yarda ba. "him zahradee amm.. "amma" me?" eh" kawai nakeso naji kince' sbd nayi imani da kina sona Aisha". "hannu bibbiyu yasa ya dafe kafadarta h'ade da zuba mata ido yace Aisha har yanzu kina sona kamar yadda nake soki ko kindaena so?" "a'a" "kina sona?". "Eh" "wani irin runguma ya kai mata h'ade da cewa alhamdullh. "jin ya matseta a jikinsa k'uma ga mutani suna wucewa yasa Aisha kwace jikinta ta ruga g'ida. "dadi ne kawai ya kashe Zahra. bayan Zahradee ya koma g'ida kae tsaye dakin Abba yanufa da sallama ya shiga Abba yana ganisa yace son lfy?". "klau Abba". "bayan ya zauna ne snn yace Abba wani abu nake bukata a gunka sae dae bansani ko zansamu. "h'aba son me zaihana?" sae idan yafi karfina son. "banlema Abba bazan tambayeka abinda yafi karfinka ba. "h'aka son" "tun ina yaro Abba kasha sanar dani cewa duk abinda nakeso na tambayeka kai k'uma zakai minshi ko menene idan be sabawa addini ba. "h'aka ne" Dan Allah Dan annabi Abba ka taimakeni kamar yadda Allah ya taimake ka Abba wlh Abba idan har narasa wnn Abu ina me tabbatar maka wlh zan'iya rasa raina Abba.. "subhana lallahi' son shiko wani irin abune h'aka son?" "Abba wnn ne damata ta karshe idan na rasashi shikenan nasan banida rabo a duniya. "wa'iyazu billa" "Dan Allah kafadi kawai niko nayi maka alkawari zanyi maka shi koma menene kuwa". "Allah yasa Abba" "amin" Abba auren Aisha nakeso ka nimomi dan har muriga da mugama mgn da'ita. "son kasan abinda kake fadi kuwa?" "Abba nasani" "Abba inaso Aisha bansan yadda zanyi da soyayyar Aisha a raina ba Abba Dan Allah ka taimake ni Abba. "yanzu son ka'amince zaka aureta bazawara a matsayinka na saurayi?". "na'amince" "son banason abinda zanje ya dawo". "babu abinda zaije ya dawo sai alkairi". "to shikenan son" "amma Abba banaso yawuce wnn satin sbd kada nazo nasake rasata irin wacce karo. "kai son kenan babu damuwa insha Allahu. "ngd Abba". "Aisha ma tana shiga gida ta sanarwa umma mgnr da sukai da zahradee. "da umma da Abba suyi murna sosae dajin h'aka. "bayan fitar zahradee Alhj ta shigo kwanciya shine Abba yake sanar mata. "haba Alhj wani irin mgn kakeyi h'aka?' sai kace ita kadaice autar mata' auren fari shine zaifara da bazawara' bazawararma Aisha da tanimi kashemin shi. "to wlh tana isa ba" "ko k'uma kece baki isa ba' idan har na'isa dake banaso kikara cewa kala' tunda bazaki sawa lamarin albarka ba. "shikenan k'uma Dan Allah kayi hkr. "babu komai ya wuce" "amma Dan Allah ina rokon arzikin abarsu mu zauna tare sbd idan kutafi kasuwa nasamu a bokiyar hira. "babu damuwa Alhj gida ga dakuna burjik nan' kiduba inda yafi dacewa sae a gyara masu. "to ngd" "a nata zcyr tana f'adin Aisha zakici ubanki Dan wlh saina ramawa dana abinda kikai masa. "washe gari Abba da kansa yaje g'idan su Aisha'Bbn Aisha yana fitowa cikin girmamawa suka gaisa h'ade da bawa juna hakuri snn Abba yafadi abinda yakawosa. "abban Aisha yai murna sosae snn yace babu damuwa. "nan suka daedae ta mgn juma'a me zuwa daura auren Aisha da zahradee. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. MMN USWAN KAI,KAI,KAI, AMINCI 1 AND 2 FOLLOW BY MMN USWAN GRP GSKYA INAJI DADIN COMMENT DIN KU SBD COMMENT DINKU KE KARAMIN KARFIN GWIWA GSKYA NGD NGD SOSAI ALLAH YA BAR KAUNA. HOME OF HAUSA NVL WTSPP AND HAFSAT HAUSA NVL H2 FCBOOK DUK INA GODIYA FANS ALLAH YA BAR KAUNA. 2⃣7⃣ "washe gari da safe Aisha taje g'idan ubaida bayan su gaisa take sanar da'ita mgnr zahrd. "ubaida tai murna sosae da fatan Allah yasa ayi a sa'a". "amin ngd ubaida" "amma Dan Allah na tambayeki mana Aisha". "Allah yasa nasani". "Dan Allah Aisha yaya kikaji a lkcn da zahrd yazo a matsayin yadawo gareki?". "him ubaida kenan". "a rayuwata ubaida babtaba tsammani zahradee zai dawo gareni amma wani hukunci na ubangiji yau way nine zahradee zai aura. "him" Aisha kenan" "wlh dama tun farko banso aurenki da Nasir ba' kawai dae dan naga yaddau kika zake kika nuna kinfi sonsane akan zahradee shiyasa' k'uma kinsan ance matar mutum kabarinsa koda na yini daya Allah yariga ya rubuta zaki zauna da Nasir. "h'aka be ubaida' wlh bantaba tsammani Nasir zaimi h'aka a rayuwa ba' shiyasa har yanzu nake kwankwanto Nasir din dana sanine kuwa" "a'a" Aisha ba shibane wanisa ne". "Aisha idan zaki kwantar da hankalinki ki rungumi masoyi dae da yafi maki". "Nasir d'in me Nasir din bazan' idan yana soki da bazai turoki g'ida ya mance dake h'aka ba'daga mgn sae ya'aiko da takardan saki. "Ni wlh idan banda ina gani girmansa dako gaisawa bazamuyi ba. "ba mmki dama tun farko ba sonki yakeyi ba' sha'awace tasa ya aureki' yanzu k'uma da kika daina bashi sha'awar ya koroki. "wlh Aisha duk da kinki f'adiwa kowa irin zaman da kikai da Nasir amma duk wanda yasan menene jin dadi Aisha baki tare dashi sbd jikinki ya nuna. "ke idan bandama abin ubangiji da yake dauke mana nawin mazajanmu kawata ina zakikai Nasir' mutum ga girma ga tsayi kamar basamude. "amma ke dubeki kamar akama a karya". "dariya Aisha tai". "Aisha idan zaki kwantar da hankalinki ki kwantar kibada kai biri ya h'au. "a rayuwa idan ka auri me sonka wlh kagama komai koba komai ke kuruciya shima h'aka kinga sae kumore kuruciyarku banlema ke da kika taba aure kinga kenan sae yadda kika juyashi sbd yanzu kinfishi sani kan duniya. "amma kinsan yakamata kiyi gyara ko". "gyaran me k'uma?". "keko kigane mana". "shewa sukai h'ade da tafi". ~~~ ~~~ ~~~ Gskya Nasir ya kamata muje g'ida kano' sbd mudade bamuje ba". "h'aka ne Fatima amma kinsan na f'adi maki banida lfy ko?" baki gani ko fita banayi?". "h'aka ne' Allah ya baka lfy". "amin Fatima". "Nasir kodai hospital ne zamu?". "a'a" kibari mugani tuku kin dict kamal yana zuwa har g'ida ya dubani idan muka tafi hospital zaice banyaba da kokarin da yakemi bane. "h'aka ne kam" "amma kibari mugani zuwa gobe". "gobe k'uma?" "Eh" "to' Allah ya kaimu". "amin" "amma yanzu ya kakeji jikin naka?" "wlh Fatima ni kadae nasan abinda nakeji' cikin jikina kamar wuta ake huramin". "a'ahhhh!" "kashi magani rana?" "a'a" ban shaba" "bari to na dauko maka kasha". "a'a" dibomi ruwa nayi addu'a kawai sbd nafi jin dadinsa". "to tace h'ade da mikewa". "daga nan ki kirami su Jabeer da Khadijat. "Fatima na dibo ruwan tare suka dawo dasu Jabeer. "amsar ruwan yai yafara addu'a' saeda yadade yanayi snn yasha ragowar k'uma Fatima ta amsa ta shafa masa a jiki. "bayan ta gama bayansa taje ta zauna gab dashi h'ade da dora hannayenta a kafadarsa tana masa tausa" musmushi yai alamu nuna jin dadin abinda take masa". "gani su Khadijat da Jabeer suna kallonsa bude masu hannu yai alama suzo. "a guje sukaje jikinsa". "h'aba Khadijat meyene kukeyi h'aka?" baku gani beda lfy ne". "a'a kyalesu kawai' basuda inda yanan. "amma gani nayi bakada lfy ne ai". "kamar ki damu". "Nasir nace kodae a sanarwa g'ida ne?'. "me fa". "a'a barsu kawai". "himm Nasir kenan". "tun daga lkcn Fatima bata sake mgn ba. "cikin dare around 12AM jikin Nasir ya tsanata'gani yadda yake hasa-hasa Fatima ta kira gateman ya taimaka mata suka dauki zuwa mota. "Da sauri tai rushing dinsa zuwa hospital din doct kamal' suna isa emergency room aka kaisa doct kamal ya bashi taimakon gaggawa h'ade da samasa drip da allurai snn yasamu bcc. "Tunda Nasir ya sa bcc be falkaba sai bayan allar asuba snn ya falka' yana falkawa daidai lkcn Fatima na zauna a gefen kasan' gani ya bude ido yasata dagowa da sauri tana f'adin sannu Nasir yaya jikin?". "kai ya daga mata alama da sauki". " a hankali yake kiranta amma batajiba sai dai kawai gani bakinsa tai yana motsi' hakan yasa ta kara kunnita a bakinsa snn taji abinda yake cewa. "Ashe yara yake tambaya. '"Fatima tace suna gida. "da hannu ya nuna mata alama taje gunsu. "Fatima tace aa Nasir babu damuwa kaidae kaji da kanka kawai. "duk da h'aka Nasir yaki yarda gani ya nace yasa Fatima taje ta dauko su. "anan su Khadijat suke yini da yamma Fatima ta medasu gida ita k'uma ta dawo hospital. "a hankali Nasir ya fara samu sauki dan har mgnrsa yafara fita ba kamar da ba. "da Bilyaminu yazo bayan sun gaisa da Fatima Nasir yace Fatima tafita ta basu gu zasuyi mgn. "h'aka ta fita dan babu yadda zatayi' bayan ta fitane suka sake gaisawa da Nasir snn yai masa mgnr da yakawoshi. "Nasir yace babu damuwa bari yanzu nai kama transfer a account dinka idan yaso sae kaci gaba da aikinka. "Okay kawai yace". "bayan ya fitane Fatima ta tare Bilyaminu tace Dan Allah Bilyaminu inaso nai maka wani tambaya?". "Allah yasa nasani". "Dan Allah bilyaminu waini me kuke kullawane kaida Alhj Nasir?". "haba Hjy me kike tunanin zamu kulla kuwa". "humm bilyaminu kenan' kasan dae ni matan Alhj ne k'uma bazan so ace yau ya aikata abinda zaije ya dawo ba ko?" "haka ne but Dan Allah kiyi hkr sbd alkawari naiwa Alhj akan koda wasan bazan bari wani yasani ba.. "haba bilyaminu wani irin abu kuke aikatawa ne da bakuso wani ya sani. "babu komai sai alkairi'amma tunda kin matso kiji zaki iya tambayar Alhj idan yafadi maki da kansa fanilabihamduli. "to shikena ngd". "Allah ya kara sauki" "amin ngd". "bayan Fatima ta koma daki gu tasamu kusa da Nasir ta zauna hade da dora hannayeta akan kirjisa' snn tace Nasir Dan Allah na tambayeka mana?" "Allah yasa nasani'. "Dan Allah Nasir mekuke kullawane kaida bilyaminu?" "na mefa?" "kusan lkt da dama idan yazo zakuyi mgn bakason yi a gabana". "Eh" h'aka ne'be shafeki bane yasa". "yanzu sbd Allah Akwai abinda zakayi kace be shafeni ba?" "amma kinsan a rayuwa babu abinda nake boye maki idan zanyi me'kyau ko akasin hakan ko?" "h'aka ne". "to kiyarda mi beshafeki bane". "himmm" "Fatima abinda nakeso kigane wnn Abu inayine dan ni dake da k'uma yaranmu fa" "to shi abin beda suna?". "yanada suna amma kibari idan lkc yayi zaki sani. "Allah yasa a aikata alkairi". "alkairi nema Fati na". ~~~ ~~~~ ~~~~ Allah ya kawomu yau daurin aure Aisha da zahradee' gidan su Aisha kam babu wasu mutani sbd ummata tace bazatayi taroba sbd ba'a dade da taron farko ba yanzu k'uma ace ana wani taro' ita gskya bazatayi ba. "hakan yasa babu wasu mutuni sosai' saidai wanda baza'a rasaba. "goga zahradee kuwa yaiwa Aisha dike dike na ban mmki' h'aka shima kanshi. "gidan su suma Alhj bata sanarwa abokanar arziki ba'sai dangi kawai suna yakama dole ne yasa. "karfe goma daedae aka daura aure. "zahradee najin anshafe wani irin kabbara yai wanda shima kansa besan lkcn da yai ba. "bayan sallar magrib aka kai amarya gidan mijinta. "ya kumbo ita ta kai Aisha dakin uwar miji bayan sun gaisa matan dake dakin kowa ya tofa albarkacin bakinsa da fatan zaman lfy. "fuska Aisha a rufe da kyale ta mike kenan zasu fita kyalen yai santsi fuskanta ya bude. "da sauri taja ta rufe. "a lkcne daya daga cikin matan dake zaune a dakin ta karewa Aisha kallo. "mikewa tai h'ade da kiran Hjy su shiga daga cikin bedroom' duk matan dake zaune su baza kunni suji abinda zatace. "suna shiga matan tace ke Hjy dama wnn aishan ne zahradee ya aura?" "Eh ita ce". "amma kika yarda". "kamar yaya menene da'ita?" "hmm" Hjy kenan". "lfy?" "yanzu sbd Allah zakice bakisan komai a kanta ba". "kamar yaya?". "kodan tabata aure?" "aure me?" idan sbd aurene Ai me sauki ne". "to menene?". "na tabbatar maki Aisha dai HIV ne da'ita k'uma ance ba'a gun kowa tasamuba sai gun tsoho mijinta. "HIV fa kikace" "kwarai da gske". "kan ubantan uban nan' Ashe da kasa. "yau za'a yita". 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W.☘. MMN USWAN 2⃣8⃣ "me za'ayi Hjy?" "Dan Allah duk sbinda zakiyi bazan hanaki tunda d'anki ne' k'uma lfyrsa tafiye maki komai amma kibari idan jama'a saragu duk abinda za'ayi sai a yisa. "yanzu dae d'anne zcyrki mukoma gun jama'a tuku. "batare da ta saurari abinda Hjy zata ceba ta jata zuwa parlour. "bayan su Aisha sun shiga daki' kanni Hjy dana Alhj sukakai masu abinci' masu ci sukaci bayan su gama drive daya dauko amarya ya medasu g'ida. "around 11-30 duk yan'biki su tafi masu kwana kuma suyi bcc' yarage Hjy da kannita a d'akinta suna ta hirarsu. "abokan zahradee suka kawoshi' Aisha na zaune a bakin gado' jin sallamarsu yasata rufe fuskata. "duk suka shigo Ruslayni ne yafara b'ude taro da addu'a snn kowa yafadi abinda baza'a rasa ba. "zahradee baki har kunni yana godiya. "snn sukai sallama' bayan ya rakasu ya dawone ya matso kusa da Aisha' duk a lkcn kanta rufe yake hannu yasa ya yaye mata mayafin dake kanta. "gani tai face-face da hawaye yasashi cewa subhanalillahi Aisha me zangani h'aka? kuka k'uma a rana irin ta yau' wanda idan a f'ade ne banida kalmomin ko lafazin da zanyi anfani dasu wajan furtasu ba' to dan Allah kiyi hkr ki dae na kukan nan kinji Aisha ta. "jawota jikinshi yai ya rungume ta'yasa hannu yana share mata hawaye' ita k'uma manna kai tai a kirjinsa. "saida yaga ta daina kuka snn yace to yanzu tashi muje muyi alwala muzo muyi sallah mugodewa ubangiji ko?". "mikewa yai h'ade da kamo hannunta suka shiga toilet saeda tafarayi bayan ta gama ne shima yai nasa suka fito. "zahradee ya jasu sallah raka'a biyu suna idarwa zahradee ya dora hannu a kanta yai addu'ar da ibangiji ya umarci ango da yayishi. "yana idarwa duk da dai ba wnn ne na farko a gunta ba amma koda zahradee yai mata tambayoyi h'aka ta amsa masa tsaf snn yace alhamdullh. "mikewa yai ya dauko ledar daya shigo dashi ya dawo bayan yau zauna ne ya bude ledar snn yace bismillh. "musmushi kawai tai". "har zahradee yakai na biyu Aisha batasa hannu ba' gani taki sa hannu yasa zahradee dibawa da kansa yake bata' Aisha taso taki amma gani yadda ya nace mata yasa ta amsa. "suna gamawa yace suje suyi brush' bayan sun gama brush suka fito sbd kunya zahradee kasa cire riga yai saida ya kashe light snn ya tube' jin yazo ya rungume ta yasa ta kankame jikinta duk abinda yake mata' kasa meda masa tai. "shiko zahradee be dameshi ba' h'aka yaci gaba da aiwatar da nufinsa. "da h'aka yasamu ya rabata da kayan jikinta zahradee yana gab da zai aiwatar da nufinsa kenan yaji knocking kamar bazai tashiba amma jin knocking d'in yaki karewa yasashi mikewa saida ya meda dogowar wandonsa snn yaje ya bude kofar. "gani Hjy ne yasashi komawa ya dauko rigansa yasa snn yafito' yana fitowa Hjy ta jamasa hannu sukai nisa da d'akin snn tace kaje d'akin su Shamsudee ka kwanta. "cikin rawar murya yace lfy Hjy?" "bana bukatar tambayarka dalilin h'akan' kawuce kawai. "jikin zahradee yai sanyi' tsayawa yai ya zubawa Hjy ido. "bazaka wuce ba?" "wlh zahradee idan kaje ka kwana a dakin ban yafe maka ba'sa kai kawai tai tabarsa tsaye a gun. "babu yadda zaiyi' h'aka yaje d'akin su Shamsudee ya buga masu sbd suma sunriga suyi bcc. "Nurudee ne yaji knocking d'in da akeyi' da sauri yace waye?" nine yaya" kai wa? zahradee. "da sauri yaje ya b'ude kofar h'ade da tambayar lfy?" ba tare daya tamkaba yashige d'akin' dakai fa nake". "Hjy ce tace nazo nan na kwanta". "ka kwanta?" me yafaru?" "wlh yya nima bansani". "kai Shamsudee tashi dan Allah". "cikin magagi yace lfy me yafaru?' "Dan Allah katashi" "b'ude ido da zaiyi yaga zahradee da sauri yace lfy kazonan?" "shiru yai be tamka ba". "Shamsudee ne yace Hjy ce tace yazo nan ya kwanta. "ya kwanta k'uma?" "to Allah ya kyauta" koma menene da safe maji". "matsa masa sikai ya kwanta". "shiru shiru Aisha bataga zahradee ya dawoba mikewa tai taje ta leka bataga kowa ba' dawowa tai ta zauna a bakin gado mmki ya'isheta can ta tuna da waya da sauri ta d'au wayarta tai dialling number yana shiga taji ringing kusa da'ita dole yasa ta hakura da kiran. "mikewa tai ta dauki kayanta ta mayar snn ta kwanta. "da asuba lkcn Abba yafito zuwa masallaci yaje tadasu Shamsudee sutafi'dama dabi'arsane duk asuba tare suke zuwa masallaci yana knocking duk suka fita sbd dama duk sun riga su tashi. "gani sufito harda zahradee yasa Abba cewa son meya kawoka nan k'uma?" "murmushi yai h'ade da cewa Abba muje masallaci tuku kada mu rasa sallah. "to kawai yace amma mmki ne ya isheshi. "bayan su idar da sallan ne suka fito sallamaci Abba ya jasu gefe yake tambayar yadda aikai. "Shamsudee ne ya f'adiwa Abba h'ade da cewa amma muma bamusan dalili. "to shikenan kuzo muje. "kai tsaye d'akinsa ya nufa'yana shiga ya dauki wayarsa ya kira Hjy" da sauri Hjy tazo a ladabce gaidashi' bayan su gama gaisawane yace Hjy meyasa kika hana son kwana a d'akin matarsa?"sbd wasu dalilaine da nakeso naji bancike akai. "bincike k'uma?" "Eh" bincike". "ko zan'iya sani?" "Eh" zansanar dakai koda ba yanzu ba amma Dan Allah kayi hkr a matsayinka na maigidana kadan ban lkc har na kammala. "to shikenan babu damuwa' amma duk abinda zakiyi banaso ya dauki lkc Dan gudun kada mushiga hakkinsu. "babu damuwa ko yau ne na kammala bincikena zai'iya shiga d'akin matar. "shikenan amma Dan Allah banason yawan bincike sbd banason abinda zaije ya dawo. "za'a kiyaye insha Allahu. "k'uma Dan Allah ina niman izini". "na mefa?" "inaso zanje hospital nida Aisha. "asibiti k'uma?" "Eh" "himm" Hjy manyan gari kenan" "Allah ya tsaye". "amin ngd". "zahradee yana gama wanka ya shirya cikin captan orange colour yayi kyau matuka bayan ya gama shiryawa ne yashiga cikin g'ida'kai tsaye d'akin Abba yashiga da sallama cikin girmamawa ya gaidashi. "my son kenan ango kaga yadda kai kyau kuwa". "himm Abba na kenan". "amma dae kashiga kaganemin kwana sarkuwata ko?". "a'a" banje ba Abba". "a'ahhh! mazan tashi kaje". "to yace h'ade da mikewa" "saida yabiya d'akin Hjy yabiya suka gaisa bayan su gaisa ne yautar su Hjy wacee bata wuce 25 years ba tace ango ango ina zuwa h'aka?" "karaf yace Abba ne yace naje naga kwanta Aisha. "wani irin dariya tai masa'' hade da cewa lalla zahradee har yanzu Akwai kuruciya a tare dakai. "yayar Hjy dake gefe tace aike kinfishi kuruciya' a matsayinki na uwa kitsaya kina tsokanar d'anki. "murmushi yai kawai ya fita' yana fita da sauri Hjy ta bishi h'ade da kiran sunasa. "zahradee na tsayawa Hjy tace ban hanaka zuwa gun matarka ba amma wlh kada ka kuskura wani abu ya shiga tsakaninku. "shiru yai be tanka ba" "kana jina ko baka jina?" "naji Hjy" "to" k'uma idan kashiga kace tashirya zamu fita. "to kawai yace". "da sallama yashiga daedae lkcn tana fitowa daga wanka daga ita sae towel daure a kirjinta wanda bewuce gwiwa ba. "tsayawa yai sakaka kamar dolo yana kallonta' da sauri ta d'au wani zani ta kara a jikinta' snn tace kariso mana' dan murmushi yai h'ade da shafe kansa alamar kunya. "snn yazo ya zauna a bakin gado. "Aisha tace ina kwana". "lfy klau kintashi lfy" "klau" "dama na shigo na sanar dake ne Hjy tace kishrya zaku fita". *"fita k'uma?" "Eh*". "to shikenan". "mikewa yai ya dauki wayarsa da sauri yabar d'akin. "Aisha nason mgn dashi amma gani yadda yakeyine kamar yana tsironta yasata kyaleshi kawai. "Hjy na gamawa ta aiki Amatulraman ta kira Aisha ta fito su tafi. 'to tace hade da mikewa taje da sallama tashiga bayan sun gaisa tace Hjy tace kifito kutafi tana jiranki. "batare da ta tankaba mayafi kawai ta dauka suka fita tare. "tana fita ta hadu da Hjy dukawa tai har kasa ta gaida ta' da fara'arta ta amsa'bayan sun gama gaisawa ne Hjy tace muje. "suna shiga Shamsudee ne ke drive suna cikin tafiya yace Hjy ina zamu? "hospital". "hospital k'uma?". "Eh". "A take gaban Aisha yai mummunar fadi' innalillahiwainnailaihiraju'un' kawai take fadi a zcyrta. "shima kansa Shamsudee dake drive yashiga kokoto a zcyrsa. "general hospital suka fara zuwa' suna shiga doct yace Hjy meke tafe daku?" "doct yarinyata ce nakawo inaso ka gwadami ita kaf idan da wani lalura da take dauke dashi inaso nasani. "Hjy zarginta kikeyi ne?" "a'a ba zarginta nake ba". "idan ba zargiba to menene' buduwarce ko tanada miji?" "tanada miji amma sun rabu' k'uma zarginsa ake yana dauke da cutar HIV shiyasa na kawota a gwadata sbd nasan ta inda zanbulowa lamarin. "Aisha dake zaune idanuta suka ciko da kwalla' a zcyrta tana cewa dama Ashe kallon da akemin kenan. "doct yace gskya kinji dabara' bari a hadata da masu gwajin. "tunda akaje da Aisha dakin gwajin habanta ke fadiwa' babu abinda takeyi sai salati a zcy. "duk gwaje-gwajen da zasuyi suyi amma basuga komai ba' dauko result din sukai suka kawowa doct. "yana budewa ya karanta snn ya sanarwa Hjy. "Hjy bata nuna damuwa ba amsan result din tai hade da godiya. 'itako Aisha alhamdullh tai. "a zcyr Hjy ko bata yarda ba. "suna fina wani hospital suka tafi' nan ma duk dai result din iri dayane. "a hospital na uku da suka jene garin bincike doct yagano Aisha nada matsala a mahaifa k'uma sanadiyar h'aka bazata haihuba. "kuram baka kawai tai ta amshi result suka koma gida' suna isa dakin Aisha suka shiga tsayawa Hjy tai akan Aisha' ita k'uma Aisha ba duke gwiwa bibbiyu a gaban Hjy. "mika mata result din tai tace karanta da kanki. "jikin Aisha na rawa ta amsa ta bude tana karantawa tana kuka. "dama kinsan da wani laluran ko baki sani ba?" "nasani" "harda shi zahradee?" 'a'a" "meyasa kika boye masa?" "kiyi hkr Hjy". "kibani amsata". "Dan Allah kiyi hkr". "a fusace ta fisge result din hade da cewa almura mana fuka wlh nidake ne a gidan nan. "Hjy na fita Aisha ta fadi a kasa ta fashe da kuka. "da yamma bayan Alhj ya dawo daga kasuwa Hjy ta shiga suka gaisa'bayan su gaisa na ta dauki wayarta takira zahradee yazo dakin Alhj ya sameta. '"tana kashe wayar tamikawa Abba result din' Abba yace na menene wann k'uma?. "kaidai karanta gaka abinda yake ciki' budewa yai ya karanta' mmki ya kama alhj sosae" ke dama Hjy ta yaya akayi kikasan da wnn matsalar?" "Hjy ta kwashe komai ta sanar masa' kan Alhj ya daure sbd betaba zaton h'aka ba. "suna cikin mgn saega zahradee yai sallama ya shigo % ganisu da yai h'aka yasashi cewa lfy Abba?" "Abba be'iya cewa komai ba mika masa result din yai. "wnn na menene k'uma Abba?" "shiru Abba yai". "budewa yai ya fara karantawa' batare daya kareba yake what?????? "Aisha fa" "kwarai da gske" "zahradee" "na'am" umma". "bazan boye maka ba wlh banji dadin h'akan ba'amma yanzu ni bazance komai ba sai abinda kayanke". "kamar yaya Hjy". "ina nufi har yanzu kana sonta?" "Eh"ina sonta". "kana sonta fa kace". "Eh"inaso" "to shikenan' amma da sharadi. "na mefa?" "zaka kara aure... "aure"k'uma?" "Eh" aure". "Abba!!!!! "a'a son ni banidana cewa' mgnrta gskya ne. "Dan bazan boye makaba son har ga Allah inason gani jikokina' idan k'uma kaga shekarunka bekai na ije mata biyu ba to fa saedae ka saki Aisha.. "haba Abba meyakawo mgnr saki?" "zabi yarage gareka son dan ni nagama shawara". "to shikenan Abba na amince". 📖 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F. O.W.☘. MMN USWAN INAMA DAUKAKIN'YAR UWANA MISULMAN DUNIYA BARKA DA SALLAH ALLAH UBANGIJI YA MEMETA MANA AMEEN. 2⃣9⃣ "shikenan son Allah ya baku zaman lfy". "amin"amma Abba... "amma me?" banason ji komai tashi kaje kawai". "mikewa yai batare daya sake cewa komai. "bayan fitarsane Abba yace amma wlh Hjy Alhj Muhammad yaban mmki". "name fa Alhj?". *"Hjy kenan a iya sanina da Alhj Muhammad ban taba zaton zai buyemi wani Abu ba. "Eh" abinda yasa bazai f'adi makaba kada ya sanar dakai kazo ka hana zahradee auren Aisha... "haba Hjy kamar ba musulmi ba". "h'aka ne mana". "himm Allah ya'kyauta. "amin" koma menene gashi musani Ai. "da sallama zahradee ya shiga d'akin Aisha' duk da sallamar da yai besa ta amsa ba, sbd kikan da takeyi. "a sanyaye ya karisa inda take zaune ya duka a gabanta h'ade da cewa h'aba Aisha kukan me kikeyi h'aka kamar wanda akaiwa mutuwa?". "Dan Allah ki daena kukan nan h'aka". "tamkar ba da'ita yakeyi ba". "gani h'aka yasa zahradee mikewa h'ade da sa hannu ya dagota tsaye' dakar yasamu ta mike snn ya kamota zuwa bakin gado ta zauna' hannu yasa yana goge mata kwallar dake gangarowa a fuskanta. "da zaran ya goge sai wasu su sake gangarowa gani batada niyar daina kukan yasashi jawota jikinshi ya rungumeta akan kirjishi. "Aisha najin h'akan kwanciya tai a kirjin zahradee ko motsi batayi. "a take zahradee yaji yanayinsa ya canza sbd sabon yanayin da yaji jikinsa. "da sauri ya mike zuwa toilet yai wanka a nan cikin toilet din ya tsaya ya meda kayan jikinsa snn ya fito batare daya h'ada ido da Aisha ba wayarsa ya dauka da sauri yabar dakin. ""itako Aisha tana kwance kallonsa kawai takeyi h'ade da mmkin zahradee'a zcyrta tana cewa dama ashe h'aka ma'aurata sukejin fadi bansani sai yanzu kodai zahradee ne kawai yakeda irin wann ni'imar h'aka?". "zahradee yana fita d'akin su Shamsudee yanufa yana shiga daidai lkcn Nurudee zaifita kasuwa sbd yau befita da wuri ba' gani zahradee a hanzarce yace lfy kuwa zahradee?". "murmushi yai hade da cewa klau. "kai kawai yasa yashige cikin dakin ya kwanta. "juyi yakeyi kawai a kan katifa a zcyrsa k'uma yarasa yadda zai kwatanta irin dadin da yakeji a zcyrsa' wani bangare k'uma yana cewa ashe dama h'aka aure yakeda dadi bansaniba? ko dai Aisha ce kawai takeda dadi h'aka? kai idan ko Aisha ne gskya nayi dace. "mikewa Aisha tai taje toilet ta tsaftace h'ade da alwala sakamakon kiraye-kirayen sallar da'akeyi. "tana fitowa daga toilet Amatullah tashigo da abinci tace iji Hjy". "to ngd" "bayan ta'idar da sallah zama tai ta dibi abinci iya wanda zai'isheta ta barwa zahradee nasa. "shiru2 Aisha bataga zahradee ya dawowa har akai la'asar gani h'aka ne yasata daukar waya ta kira number sa. "duk kiran da Aisha takeyi zahradee na kallo amma be daga ba' wani irin dadi kawai yakeji' gani be daga ba yasata yimasa text da kazo kaci abinci. "yana gani da sauri ya b'ude text d'in' yana gama karabtawa yai mata reply da ganina zuwa. "dama yana cikin g'ida mikewa yai ya kami hanyar cikin g'ida har zahradee yakai kofar d'akin Aisha ko me yatuna k'uma oho komawa yai da baya yana fita ya kira Amatulrahaman yace taje dakin Aisha ta amso masa abinci. "to kawai tace. "tun daga lkcn zahradee besake shiga cikin g'ida ba sbd yanajin kunyar yadda zaihada ido da Aisha'da yamma koda Hjy ta aika masu da abinci h'aka Aisha tasake ije masa' tana idar da sallar isha'i tasake wani wanka ta zauna zaman jiran zahradee nan ma bedawo ba' Aisha ta zauna har dagaji da zama goma yayi gashi bcc takeji cire kayan tai ta sanya na bcc snn ta kwanta. "shiko zahradee yana can da yayyinsa tare sukaci abinci sbd duk a tananinsu har yanzu Hjy bata basa izini shiga dakin matarsa bane. "bayan su gama ci zama sukai sunata hira har 11PM gani h'aka gashi dama su Shamsudee sufara bcc mikewa yai yafita zuwa bangarensa' lkcn Aisha na zaune tana tunanin abinda ya hana zahradee shigowa' tana cikin h'aka sai gashi yai sallama ya shigo. "Aisha dake zaune bakin gado ta amsa snn ya kariso ciki'sannu da zuwa tace masa h'ade da mikewa abinci ta dauko masa' zahradee dake zauna a kan cushion one ster a gabansa ta'ije masa abincin hade da ruwa. "murmushi kawai yai cikin jin kunya yace nakoshi sbd nariga naci dasu yaya. "to" shikenan". "kwashewa tai ta ije a gefe snn tashiga toilet ta h'ada masa ruwan wanka tana fitowa ta sanar dashi. "ngd kawai ya ambata snn ya shige. "shiru-shiru zahradee befito ba' yasa Aisha kwanciya' tana kwanciya bcc ya dauketa. "shima zahradee din lekawa yai yana gani tai bcc shine yafito yazo suka kwanta. ~~~ ~~~ ~~~~ "baba"! "yawwa sannu Khadijat". "Fatima". "na'am Nasir". "wlh Fatima inajin jiki". "h'aba Nasir Dan Allah kadai na f'adin h'aka. "himm Fatima kenan jinake a jikina kamar bazan tashiba. "Fatima najin h'aka fashewa da kuka tai h'ade da rungume Nasir dake kwance akan gadon asibiti snn taci gaba da cewa Dan Allah Nasir kadaina f'adin h'aka ita cuta ba mutuwa bace' insha Allahu zaka tashi Nasir. "hannu Nasir yasa yana lallashinta' haba Fatima kidai na kuka duk wanda kikaga ya mutu to fa ki tabbata lkcn sane yai' h'aka k'uma wani baya rayuwa da rayuwar wani Fatima' amma a yadda nakejin jikina him". "kae Nasir insha Allah babu inda zaka munanan tare' Nasir idan kamutu kabarni yaya kakeso nayi Nasir?" Nasir tunda nake a duniya bantaba son wani d'a namiji ba sai kai Nasir' Nasir kasancewarka gareni tabkar wata tsokace a cikin jikina wanda idan babu inda ba lalla bane na rayu. "Dan Allah Nasir kada kamutu katsaya mu zauna tare har tsawon rayuwarmu. "Fatima kenan' wani abu da bantaba sanar dake ba shine tunda nake a rayuwata a lkcn banfi 20 years old ba nakan tashi cikin dare na roki ubangijina abubuwa da yawa amma duk cikin rokon da nake masa bantaba rokonsa da yasa nayi tsawon rai ba sai bayan haduwana dake' na karkata akalar rokona da ubangiji yaban tarin dukiya mai yawa da kuma ya mallakamin ke sbd nabaki kyakykyawar kulawa koda bamuyi tsawon zama tare ba. "nasha f'adi idan ubangiji ya cikamin burina duk wata hanya ta sabon ubangiji zankiyaye' saidai kinsan d'an"Adam tara yake becika goma ba Fatima. "ba mmki aure-auren da nakeyi shine kalar tawa jarabtar da Allah yai min. "Fatima ngd da Allah ya hadani dake me sonane' inda watace da yanzu ta tafi tabarni. "Dan Allah Fatima koda bayan rai nane ki rikemi Khadijat da Jabeer tabkar ina raye' zanyi alfahari dake a duk inda nake sbd nasan kasa zairinka kaimin lbrin kabarina Fatima. "Fatima najin h'aka tasake kankame Nasir tana kuka". "gani h'aka yasa su Khadijat da Jabeer zuwa su rike mmnsu suna kuka. "Nasir dake kwance shima hawayene kawai yake gangare masa. "bayan kwana biyu jikin Nasir ya tsananta duk abinciken da doct kamal zaiyi yayi amma a cewarsa bega komai ba k'uma gashi jikin babu sauki. "h'akan yasa Fatima yanke shawarar sanarwa Alhj Rabi'u guduma wato mahaifin Nasir halin da suke ciki. "washe gari kafin azahar saiga Alhj Rabi'u a binnin kebbi gani halin da Nasir ke ciki yasa Alhj daukar Nasir zuwa gida kano' Nasir na motar bbnsa da yyasa ke tuki' Fatima k'uma dasu Khadijat suna motar Nasir din wanda bilyaminu ke tukasu. "kai tsaye gidan su Nasir suka nufa. "duk'yar uwa su hadu' kani da yayyi kowa yana kawo kalar nasa shawarar' Bbn yayansuAlhj Tasi'u dake zaune a abuja shida matarsa Allah yasa lkcn suma suje gani gida yacewa abbansu Alhj Rabi'u idan har ya amince me zaihana baza'a fita dashi kasar waje ba kawai. "alhj rabi'u yace eh" kam h'akan zaifi amma wani harzari ba guduba nidai yanzu kufi kowa sani bazan iya doguwar zama ba' saidai acire wasu daga cikinku hade da matarsa kutafi tare. "Alhj tasi'u dake zaune yace Abba kada kadamu zamusan yadda za'ayi. "kwana biyu da mgnr aka fita dashi kasar Cairo Egypt Fatima ne da yayyinsa biyu suka tafi. "alhamdullh yanzu kan anfara samu canji akan da' idan shima kansa yafarajin canji a jikinsa. "watan su Fatima daya bbnta Alhj Sunusi yaje dubasu' Fatima taji dadi sosae gani abbanta yazo gani su. "kwanarsa uku da tafiya ya dawo gida Nigeria. ~~~ ~~~ ~~~ "bayan kwana bakwai da bikin zahradee Hjy ta daina samasu abinda suka farayin nasu' saidai idan suyi zahradee yacewa Aisha tarinka tasa Hjy. "Aisha tace to. "tun daga lkcn idan har Aisha tai girki takesawa Hjy' h'aka ma yau tuwan shinkafa tai da miyar vegetable duk da ba mai yawa bane amma h'aka tasawa hjyn da kanta ta dauka da sallama tashiga d'akin Hjy gani babu kowa a d'akin yasata ije kular tafita. "lkcn Hjy na kitchen tana abincin yamma'Aisha na ijewa ta koma bangarenta' hjy bata shigo d'akin ba saeda tagama abinci tsaf snn tashigo dan yi wanka h'ade da sallah. "can gefe ta hango kular Aisha' batai ta kansaba sbd dama ba cin abincinta takeyi ba' su Amatullah ne da Amatulrahaman sukeci. "sumadin ba kullum ba sbd gaba dayansu ba yara bane'dan a yanzu da h'aka Amatullah tana three hudreen ne ita k'uma Amatulrahaman tana two hudreen ne a tabawa balewa university dake bauchi. "toilet Hjy tashiga tai wanka hade da alwala bayan ta idar da sallane ta bude abincin da Aisha takawo mata' gani leda dayane yasata meda murfin ta rufe bata sake bi takansa ba k'uma. "zahradee yana dawowa daga kasuwa kai tsaye bangare su Hjy yanufa shida Abba' dama dabi'ar zahradee ne duk lkcn daya dawo kasuwa saiya fara zuwa gun Hjy su gaisa sann zaije bangarenshi. "da sallama ya shiga Hjy na zaune kan sallaya tana lazumi a ladabce zahradee ya gaidata. "da fara'arta ta amsa hade da tambayar kasuwa". "alhamdllh". "hannu yasa ya ciro bandir din two hudreen naira note yabata h'ade da cewa Hjy ga wnn kyasiye goro. "Hjy tai murna hade da samasa Albarka. "zahradee na duke sai faman cewa amin yakeyi. "mikewa da zaiyi hannu tasa ta jawo kular Aisha tace gashi kakaiwa matarka. "to kawai yace snn ya amsa. "yana amsa ya fita' bagarensa yanufa' yana shiga Aisha ta taresa da murna tana f'adin sannu da dawowa. "yawwa sannu. "mike mata kular yai yace Hjy ce tace na kawo maki. "kakawo k'uma?" dazufa na kaimata abincin a ciki' kodai har sugama dashi ne?". "kibude ki gani mana. "to" "koda Aisha ta b'ude yadda takai ko taba ba'ayi ba aka dawo dashi. "shirutai tazubawa kular ido. "yah dai Aisha?". "kagafa yadda nakai abincin h'aka aka dawo dashi". "kamar yya?". "gashi kagani fa". "dama iya kacin abinda kika zuwa kenan ko yafi h'aka?". "a'a" iya kacinsa kenan". "sbd Allah Aisha wani irin abinci kenan kamar za'abawa mage' dubafa kigani' fushi kenan tai k'uma ko nine h'akan zanyi. "idan banda rainin wayo wani irin abincine wnn sbd Allah' yau koda bakisanta ba kya dauki wann figigin abincin kibata. "amma".. "amma me?". "gani nayi ranar da nayi da yawa fada tai sosae wai albazaranci ne. "eh kema kanki ranar kinsan baki kyauta ba. "sbd h'aka idan har kinaso mu shirya kije kibata hkr kawai. "hkr k'uma?". "Eh" kifita kawai kije tun kafin tabiyomu nan ta hadamu gaba daya. "to kawai Aisha tace duk idanuta sun cika da kwalla' hijab tasa tafita. "haka kawai kizo ki jamin wani mgn agun Hjy bayan kisan ba kyalemu zatayi ba dagani har ke. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F. O.W.☘. MMN USWAN 3⃣0⃣ "sallamu'alaikum" "ami'waalaiki salam'waye?". "nice Aisha. "dama Aisha ce tatsaya tana doka wata uwar sallama kamar bakuwa. "a sanyaye Aisha ta kariso ciki". "lfy?" "lfy klau Hjy" dama rokonki nazoyi' Dan Allah kiyi hkri. "wani abune ya faru?". "a'a" mgnr abinci ne". "zahradee ne yadawo da abincin dana samaki yace kekikace a dawo dashi' sbd kinyi fushi. "shidin yace nayi fushi?". "Eh shiyasa yace nazo na baki hkr". "shidin ko?". "OK tashi kije ki kirashi k'uma kuzo tare. "to Hjy". "mikewa tai yaje kiran zahradee din. "tana fits Hjy tace duk zakuci ubanku dani. "zahradee na zaune a bakin gado yana jiran Aisha' tana shigowa yace kinbata hakurin?". "Eh"Amma tace kaje". "naje k'uma?". "Eh" wai muje tare". "to muje' zahrdeee yana gaba Aisha na baya suka shiga dakin' duk dukawa sukai a gabanta snn yace gani Hjy. "Hjy gani". "basai kacemi gaka ba'naga zuwanka' tunda ba makauniya nake ba. "kacewa matarka tazo tabani hkr sbd nayi fushi ko" kayi shiru kamar ba dakai nakeba. "Eh"h'aka ne". nice nace maka nayi fushi?". "a'a". kaga zahradee banason mananu maganganu daga kai har matarka baku isheni' abincine k'uma ba dole bane sai kunbani' kafi kowa sani bacin sbincinta nakeyi ba'kosu Amatullah dinma su ba kowani lkc sukeciba shiyasa tun farko nace a'a kubar kayanku kace a'a to ga irinta kenan. "Eh" Hjy nine nace arinka sawa koda bazakici". "zahradee Kaine bazan boye maka ba' kane kakeso bani abincinka amma matarka bataso... "da sauri Aisha tace a'a Hjy wlh ba h'aka bane' gani nayi kwanaki da nake sawa da yawa bakwaci shine na rage hannu sbd kada yazama albazaranci. "eh' kinada gskya shugaban'yar tattali tunda daga g'idanku ake kawo abincin ba. "ooo!!!! In Laila abin mmki baya karewa nine yau za'a koyamin yadda ake tatta. "to bari kiji tunda badaga gidan ku ake kawo abincin ba' baki isa kice zaki kawomi wani kauli da ba''adi ba. "dakawa zahradee tsawa tai h'ade da cewa ashe dama duk abinda makeyi da sanika.... "a'a" Hjy wlh bansani ba' kenan kinsan inda na sani bazan kyaleta ba Hjy. "shiru Aisha tai kanta na kasa tana hawaye. "to bari kiji daga yau na kashe kawomi abincinku' k'uma kada kiyi tunanin abinda kikeyine yasa 'a'a ra'ayi nane kawai sbd koda shakeni zakiyi bansan tast din abincinki. "zahradee dake duke inba hkr da yakebawa Hjy ba babu abinda yakeyi. "itako Aisha kuka kawai takeyi. "Hjy taci gaba da cewa yarinya tun kafin kisan zakizo duniya nake girki banle zuwanki jiya-jiya kice abincinki zai tsolemi ido. "suna cikin h'aka ne Abba yai sallama ya shigo da sauri Aisha ta mike tabar dakin' zahradee dake duke Abba yace son yaya akai ne?". "da sauri zahradee ya dago yana me cewa Abba..... "kae tashi kafita. "mikewa yai yafita. "bayan fitarsa ne Abba yace Hjy yaya akaine?". "da fara'arta tace name fa Alhj?". "ganisu nai anan". "babu komai". "washe gari da safe bayan su zahradee da Abba sufita kasuwa' batai aikin komai ba sbd bcc da takeji sakamakon rashin bcc zahradee ya hanatayi da dare. "har bcc ya fara daukarta taji ana knocking da farko batai niyar tashi ta bude kofar ba'amma jin knocking yaki karewa yasata mikewa tazo ta bude. "gani Hjy ne yasata dukawa tace ina kwana Hjy. "ba gaisuwarne damuwata ba' me yasami idon naki sukai jazirrr h'aka?". "babu komai bcc ne kawai nakeji. "bcc?". "Eh". "ke kika sani' wann damuwarki ne' me aikin bece ya gaji ba'saike da kike kwance akeyi maki' tashi muje kimin. "mikewa tai tabita' Hjy na gaba Aisha na baya suka shiga kitchen Hjy ta nununawa Aisha lugu da sake na kitchen din snn tace tana bukatar da goge mata ko'ina harda su gas kuka da electric tace duk ta gogesu tas baya tagama k'uma tai mata wanke-wanke. "to kawai Aisha tace Hjy na fita Aisha na binta da kallo. "tunda Aisha tafara aiki bata gama ba sai bayan azahar snn takare. "zuwa dakin Hjy tai ta sheda mata cewa takare'da fara'arta tace ngd Allah yai maki albarkw". "amin Aisha tace snn takoma bangarenta. "tana shiga bakin gado ta zauna tai shiru h'ade da uban tagumi tana tunanin abubuwa kala-kala' itadai tasan tsakaninta da zahradee batada matsala h'aka yayyinsa da kanninsa h'ade da Abba matsslarta dayane shine Hjy. "me nayi mata da bata sona?" idan akan mgnr haihuwane Ai ba'ita yakamata ta damuba zahradee yakamata ya nuna damuwa amma bedamu ba sai Hjy?" "to kodai kiyayyane?". "wani zcy yace aa Aisha Hjy bata kinki. "tunda mafi yawanci lkc idan Abba yaiwa su Amatullah da Amatulrahman kamar su kayan kwalliya zannuwa turaruka da dai sauransu sai Hjy ta cirewa Aisha tabata batare da zahradee ya sani ba' shima Abba da yaga h'aka idan har zaimasu siyayya saiya hada da Aisha. "shiru tai taci gaba da tunanin dalilin dayasa Hjy take mata h'aka. "gani la'asar yayi ta mike zuwa toilet tai wnka hade da alwala' tana idar da sallah tashige kitchen dan dora sanwa. tanayi tana wanke-wanke da h'aka har tagama tasawa Hjy tana. "bata kaiba daki ta koma taje tasha kwalliyarta cikin doguwar rigan shadda snn taje ta dauki kular abincin takai dakin Hjy. "da sallama ta shiga lkcn Hjy na sallah Amatullahi ne zaune a kan cushion saida suka gaisa snn Aisha ta ije abincin'har ta mike Amatullah tace ina zaki k'uma. "daki zani". "daki? me zakiyi a dakin?. "idan Dan nine akai wnn kwalliyar to kizoki zauna kusa dani. "murmushi kawai Aisha tai tafice batare da ta tanka mata ba. "bayan Hjy ta idar da sallah ne tacewa Amatullah ta dauki ahbincin ta medawa Aisha. "haba Hjy me k'uma tai' Dan Allah kiyi hkr mana. "ni bataimi komai ba' cine kawai bazan yiba. "to mu zamuci' ko sister?". "eh" "to shikenan gaku gashi ai. "bayan zahradee ya gama cin abinci ne yaje dakin Hjy gaisheta' yana shiga su amatullah suka muke hade da cewa sannu yya da dawowa. "yawwa snnuku. dukawa yai ya gaida Hjy' bayan su gama ne Hjy tace zahradee". "na'am Hjy". "yanzu kakai wata nawa da aure?". "lahhh Hjy har kinmance?" biyar kenan fa". "alhamdullh gara da Allah yasa kana sane' yanzu yaya mgnr alkawarinmu?". "alkawari k'uma Hjy?". "eh" alkawari". "gskya Hjy ni babu wani aure da zankara' tunda babu abinda Aisha ta rageni dashi... "kafin zahradee ya kare Hjy ta daukesa da mari' har yaushe kazama h'aka zahradee ashe fitsaran naka yakai h'aka?" wato kai kaji dadi mace to wlh baka isa ba' idan ubanka aure k'uma babu fashi. "wlh Hjy hkr zaki dani wlh babu wani auren da zanyi' da sauri zahradee ya mike yabar daki. "salati kawai Hjy keyi h'ade da mmkin zahradee. "zahradee yana fita dakin Abba ya nufa' yana shiga Abba yace son yaya akai ne na ganka h'aka. "abba kaji Hjy fa wai dole saina kara aure. "aure k'uma?". "Eh" h'aka Hjy tace". "to kai me kagani?". "nidae gskya Abba bazan kara kowani aure ba'sbd duk abinda nakeso Aisha tana nai min. "to son mgnr haihuwa k'uma fa?". "haihuwar me Abba? Dan Allah abar mgnr haihuwarnan h'aka tunda na samu Aisha ta. "lalla son har yanzu kai yarone' to wlh bari kaji mgnr aure ba fashi Dan a gskya inaso naga yaranka kafi ba koma ga ubangiji. "kae Abba harda kae?". "kwarai da gske son. "bayan fitar zahradee ne Hjy ta shigo da sallama Abba yace madam yaya akai. "murmushi Hjy tai sann tace yanzu sbd Allah Alhj h'aka zamu zubawa zahradee ido?". "na me fa?". "mgnr aure mana". "haba dai Hjy nifa tuni nariga na yanke shawara gobe kafin na karisa kasuwa zanje gidan Alhj Musa nagansa da wata yarinya'yar kyakykyawa mai hnkli' dama kwanaki muyi hirar dashi akan Akwai yaron da yake zuwa gunta koda akai masa mgnr yafito sai yace iyayensa sunce basu shirya ba. "to kinga idan ya amince ina nimawa zahradee aurenta' suma su Shamsudee da Nurudee duk mgn zanmasu sufito da yarinyar da sukeso sbd nagaji da zamansu h'aka. "amma shi zahradee inaso ya rigasu' idan har Alhj Musa ya amince koda wani satine a shirye nake. "yawwa Alhj har naji dadi' Allah ya shige nama gaba". "amin". 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F. O. W. ☘. MMN USWAN 3⃣1⃣ "washe kafin Abba yaje kasuwa yabinya g'idan Alhj Musa' bayan sun gaisa ne Alhj Musa yake tambayar Abba lfy ya gansa da safe h'aka?". "murmushi Abba yai sann yace wlh wata mahimmiyar mgn ce take tafe dani. "to Allah yasa dai ba laifi naiwa uban dakina. "duk dariya sukai' snn Abba yace h'aba dai. "saida ya daidaita zamansa snn yace dama roko nazo h'ade da niman iri. "kamar yaya Alhj Kailani? ban fahimtaba. "himm Alhj Musa kenan" ina nufin nazo nemawa d'anka ne auren'yarta. "wacce'yar'taka kenan daga ciki?". "zainab wanda kwanaki mukai mgn akan cewa yaron da yake zuwa gunta kace ya turo magabatarsa amma beturo ba. "Allah sarki wlh har na mance kamar muyi mgnr dakai. "to yaya ake cikine?". "wlh har yanzu shiru". "alhamdullh'dama tsorona kada nayi nima akan nima. "a'a wlh babu damuwa. "aini na fika jin dadin wnn zance'sai wani dani daga ciki? yaran nawa da yawa. "h'aka ne' zahradee ne?". "wanne kenan daga ciki?". "wanda yai aure kwanaki. "Allahu Akbar' shine har zaikara? ikon Allah kenan. "to idan har kasan babu wata matsala shikenan. "insha Allahu babu komai" kasan kowani iyaye yanaso yadda aka mutu aka barsa shima yanaso yabar baya. "kwarai da gske' to Allah ya tabbatar mana da alkairi. "amin" ngd. "amma wani hanzari ba guduba ya kamata yazo su daedaeta tsakaninsu. "Ai dole' bayan su daidai ta mukuma ta rage namu. "h'aka ne amma Dan Allah banaso a dauki lkc me tsayi. "uban daki kenan' a yadda na tsarawa kaina dama koda Allah besa kazo da mgnr ga ba zainab bazata wuce wnn shekara ba batai aure. "sbd koda ace Allah bekawokaba akwai wanda nake saran zanbata sai k'uma ga yadda Allah ya shirya. "h'aka ne' to ngd ngd sosae Allah ya shige mana gaba. "amin nima ngd. "da yamma bayan Abba yadawo kasuwa yasa aka kira masa zahradee ga Hjy agun bayan kowa ya tattara hankalinsa gun daya snn Abba yace zahradee". "na'am Abba". kasan tunda nake dakai a rayuwata bantaba niman wani abu a gareka bako?". "Eh" Abba. "k'uma bantaba dora maka wani abuda nasan bazaka iya bako?". "eh"Abba. "to Dan Allah na tambayeka?". "Allah yasa nasani Abba na". "yanzu a naka tunani yadda nake sonka nake fifitaka da sauran'year uwanka ko zaka fadimi dalilin dayasa nake maka h'aka?". "him' Abba kenan nasan sbd soyayyar da kakemin ne yasa h'aka. "bayan h'aka fa?". "shinedai nasani". "son kenan sbd kyautatamin da kakeyi ne da k'uma tunda nake dakai bantaba saka wani abu ka musantami ba ko ba h'aka bane?". "murmushi kawai zahradee yai. "snn Abba yace a yanzuma umarni ne zanbaka ba niman iziniba son' sbd na duba duk cikinku kaine kafi dacewa dashi... "cikin rawar jiki zahradee yace Abba f'adi koma menene shi insha Allahu zanyi maka shi. "a'a son kafin na f'adi saikami alkawarin babu musu tsakanina dakai. "insha Allahu Abba bazan taba musa makaba' bana fatan Allah yakawo ranar da zaka umar ceni da abu nai maka musu. "allahamdull' ngd son. "dama mgnr aure... "aure Abba?". "Eh" aure". " ne muringa mu gama mgn da iyayen yarinya' yanzu ku muke jira kawai musa rana. "amma Abba"... "a'a"son kada muyi h'aka dakai. "tun daga snn zahradee besake mgn ba". "yanzu koda zuwa gobe ne sai kaje ku daidai ta' k'uma ka tabbatar kasiyewa kanka girma a gun yarinya daraja' kada kaje ka aikata abinda zaisa uban yarinyarnan ya daina gani girmana. "son idan h'aka ya kasance wlh bazaka sake ji dadina ba. 'to Abba zankiyaye. "tashi kaje Allah yai maka albarka. "amin ngd Abba". "bayan fitar zahradee ne Hjy ke tambayar Abba yadda sukai da Alhj Musa' Abba ya zaiyana mata duk yadda sukai Hjy tai murna sosae h'ade da cewa amma Alhj idan sun daidai ta tsakanisu ba lkc me tsayi za'a saba ko?". "Eh" nima h'aka nakeso' shiyasa ma naiwa Alhj Musan mgn' shima yace h'akan yayi. "to alhamdullh' Allah ya shige mana gaba". 'min Hjy". "tunda zahradee yashige daki kwanciya kawai yai batare da mgn ba'Aisha tai tambaya har tagaji amma zahradee be tanka mata ba' da ta gaji da tambayar kwancita tai h'aka suka kwana. "da yamma bayan su dawo kasuwa zahradee na kwance a dakinsa around 8-20 Abba ya tura Hjy ta kirasa sakamakon duk wayayinsa a kashe suke. "koda Hjy taje a bakin kofa ta tsaya snn tai sallama' Aisha dake kwance ne tazo ta bude'gani Hjy yasata dukawa tace snn Hjy. "yawwa snn' ina mijin naki?". "yana ciki". "kice masa abbansa yana kira". "to Hjy". "da sauri tamike ta koma cikin dakin ta sanar dashi Abba na kira" Dan karamin tsaki yai hade da mikewa. "toilet ya shiga ya watsa ruwa snn yafito batare daya shafa mai ba wadrop yaje ya bude ya dauka wata dankareriyar shadda lemon green yasa snn ya dauki turare ya feshe jikinsa dashi hade da kwashe wayoyinsa ya zuba a aljihu. "shiru Aisha tai tana kallonsa kawai sbd mmki irin wnnn kwalliyar. "har yakai bakin kofa' tana zahradee ina zaka a irin wnn lkc ga k'uma wata uban kwalliya da kasha h'aka. "murmushi yai h'ade da dawowa ya rungumeta snn yace I'm srry baby Abba zaya aikeni tun jiya g'idan wani abokinsa bansamu zuwa sai yanzu amma kiyi hkr bazan dade ba zandawo. "to shikenan saika dawo' but pls dear take care of ur self. "OK I'll" tnx. "har zahrdee yakai bakin kofa da sauri Aisha tace au!! zahrdee ga key din mortar ka. "yana amsa ya fita gun Abba yafara zuwa son har kafito?" "Eh" Abba nafito'zantafi kenan". "a dawo lfy k'uma Dan Allah a kiyaye. "to Abba". "zahrdee yana fita supermarket ya nufi yana isa kayane ya diba na tashi hankali kamar su turarika mayuka sabulai sweet chocolate dai sauransu ya hada snn ya karisa gidan su zainab. "a bakin yai parking snn yafita zuwa cikin g'idan lkcn Alhj Musa da matarsa mahaifiyar su zainab da kishiryata duk suna parlour zahrdee yai sallama. "Alhj Musa ne yai masa izini daya kariso cikin parlour' yana shiga dukawa yai cikin girmamawa ya gaidasu kansa na kasa. "dukkansu suka hada baki suka amsa hade da tambayarsa iyayensa. "Alhj Musa yacewa Hjy Hulaira kishiyar mmn zainab taje ta sanarwa zainab tai bako. "batare da bata lkc ba ta mike da zafin namarta ta shige ciki. "gani h'aka zahrdee yace Abba ni zantafi' Alhj Musa yace to zahrdee idan kaje ka gaidamin iyayen naka. "to zasuji". "zahrdee be dade da fitaba Zainab ta fito ita da inna Hulaira' bayan Zainab ta fitane Huaira ke tanbayar Alhj dama wnn shine yaro da kakegaya mana?". "Eh" shine". "Allah sarki' gskya nayaba da hnklinsa Allah yasa ayi damu. "amin Alhj yace". "duk sa Hjy Saratu mmnr Zainab taji dadin abin amma saita matse. "zahrdee yana fita komawa mota yai ya zauna'be dade da zama ba Zainab ta fito'da sallama ta kariso gun. "kusa da motar taja ta tsaya' gani h'aka yasa zahrdee fitowa daga motar ya zagayo. "jikin motar ya jingina suna fuskantar juna' Zainab tace sannu da zuwa". "yawwa'snnu 'yar mata. "kina lfy?" "lfy klau". ya kike ya g'ida da hutu k'uma' tunda angama karatu ko?". "Eh"h'aka ne result kawai muke jira". "to Allah ya taimaka". "amin'ngd". "yah!! sunar malamar nema namance?". "zainab". "OK" srry h'aka fa akace". "to zainab nasan basai nace komai ba' sbd duk wata abinda zanfadi anriga da ansanar dake daga g'ida ko?". "Eh" h'aka ne". "to yah!! kika gani nayi maki?" idan kinsan banyi makiba Dan Allah zafi kowa jin dadi sbd bazanso ayi maki doleba". "ba badamuwa Zainab nayi maki?". "saida Zainab tasa mayafi ta rufe fuska snn tace eh". "wani irin bakin cikine yai kululu ya tokari zcyr zahrdee. "to shikenan tunda kince nayi maki ngd'". "nima ngd". "zantafi amma Dan Allah kiyi hkr sbd bazan samo dawowa cikin satin nan". "to sai yaushe zaka dawo". "uhmmm!!" to maybe nest upper week. "babu damuwa' ubangiji Allah yasa mukai. "amin ngd". "ni zabshige ciki". "to zainab amma Dan Allah minti daya". "komawa yai cikin mota ya memo h'ade da pen yadawo' gashi Dan Allah ki rubutami number wayatane babu caji shiyasa amma idan naje gida nai caji zakiji kirana. "to shikenan". "amsa Zainab tai ta rubuta masa snn ta mika masa. "zainab ngd saikin jini". "shikenan". "ga sako Dan Allah". "tsayawa tai taga wani sakone". "ledar shoping din da yai ya dauko ya mika mata snn sukai sallama. "zainab na shiga ije ledar tai a gaban Hjy hulaira snn tashige dakin su'dama lkcn Alhj Musa baya gun' budewa Hjy Hulaira takeyi tana fito da kayan daya bayan daya tana sambarka. "gani Hjy Mmn Zainab batasa hannu ba yasata dibo kaya ta zuba mata a jiki' murmushi kawai tai batare da mgn ba. "zahrdee yana isa gida dakinsa yashige' har Aisha tafara bcc shigowar shine yasa ta tashi hade da yimasa sannu da zuwa. "bayan kwana biyu Abba yaje gidan su Alhj Musa suka daedaeta aka yanke masa sadaki hade da rana 16 October ranar jumma'a kenan yafito masu. "Alhj Kailani yai murna sosae. "tunda zahrdee yabar gidan su Zainab be kirata ba banle anyi mgnr zuwa. "mmki sosae Yakama Zainab wani lkc sai taji kamar ta sanarwa inna Hulaira' amma dai sae tace bari takara daga masa kafa zuwa kwana biyu tagani. "Abba ya hada Shamsudee da Nurudee yace saedai sufito da matar da zasu aure idan ba h'aka ba da kansa zai samo masu' shidae Shamsudee cewa yai yarinyar da yakeso a wnn shekarane zata zana weac din' ayi masa uzuri har takare. "amma yace kai fa Nurudee shikuma yace habiba yakeso 'yar gidan Alhj sani shima koda yaje da mgnr aure cewa yai bayaso yaita bawa mutani wahala yafiso ayi gaba daya da sauran yaran gidan wata kanin habiba kenan suma wnn shekarane zasu kare karatu idan su kammala sai ayi mgnr auren kawai tunda gidan mazansu ma har sukai komai. "to yanzu muma so suke mukai kenan?". "a'a" Abba kabari dai lkcn yai tuku. "to kenan amma Dan Allah kuyi kokari sbd banaso wann shekara takare batare da munada mata ba' kuna gani kaniku kenan har zaije ga nabiyu amma Ku dakuke manya ace bakuda ko daya. "duk dariya sukasa. "bangare Hjy kuwa sai faman shirye-shirye takeyi babu kama hannu yaro binni da kauye ta aika ba kamar lkcn bikin Aisha ba wanda ma suke binni ba kowane yasani ba banle na kauye. "anko kuwa anyishi yakai kala biyar ko wacce rana da nata. "kan Aisha ya daure sbd mafi yawanci lokuta takan sacijin kamar ana mgnr biki k'uma sunar zahrdee ake ambato. "wani tunani daya zomata tace kodae na tambayesa ne?" can k'uma tace bari kawai na barsa idan yai ra'ayi dan kansa zai sanar dani tunda baya boyemi komai. "zahrdee be kira Aisha ba saida yarage saura sati biyu bayan ta idar da sallar azahar tana zaune kan sallaya saiga kiran zahrdee yashigo' gani bakon number yasa taki dagawa har wayar ta tsinke. "har ta mike saega wani kiran yashigo'gani kiran bame karewa bane yasa ta daga danjin wake damuta da kira h'aka. "tana dagawa da sallama taji duk da bata gane muryaba amma besa taki amsawa ba. "nasan kina mgnr ne batare da kingane dawa kike mgn ba ko?". "wlh kuwa"Dan Allah dawa nake mgn ne?" "zahrdee ne". "eyya Dan Allah kayi hkr wlh bangane muryanka bane?". "Eh" nasan da h'aka Ai". "bayan sun gaisa zahrdee yace dama bugowa nai na tambayeki abinda kike bukata". "murmushi Zainab tai hade da cewa bani bukatar komai". "to shikena tunda baki bukatar komai gani number na idan bukatar yataso saiki kirani'idan k'uma kunya kikeji saiki bawa kawayenki nasan bazaki rasasu ba. "to kawai Zainab tace". "snn sukai sallama'bayan ya kashe wayar ne Zainab ta zauna shiru tana tunanin wann hali irin na zahrdee. ~~~ ~~~~ ~~~~ "Nasir tunda aka kaiaa Egypt dayake Akwai kwararron docts su bashi kyakykyawar kulawa jiki kam alhadumllh yanzu kusan komai da kansa yakeyi batare da yabawa Fatima wahala ba. "sae dae docts din suce yana da'kyau yarinka zagawa yana exercise sbd dadewar da yai a kwance. "Nasir ya samo wnn cutar ne a gun zuwaira daya aure batare daya san tana dauke dashi' ita kanta batasan tana dauke dashi ba sakamakon auren wani mutum da tai shima kusan irinta ne harma zan'iya cewa yafita sbd duk shekara yake zubi' ma'ana kowani shekara yake auren mata hudu kafin wani shekara duk ya sakesu ya dibo wasu. "shine sanadiyar da yasa zuwaira tasamu wnn cutar' bayan rabuwarsu dashi Nasir ya aureta a nan ne shima ya dauki cutar'abinda yasa ma be cutar dashi h'aka ba Nasir mutum ne me kulawa da kansa wajan shan maguguna. "ko'a lkcn da yaji canji a jikinsa yaje dan gani doct' doct kamal yace infection ne amma idan yana kulawa da magani babu abinda zaisameshi. "da h'aka Nasir yaci gaba da kulawa da kansa wajan shan maguguna' inda ya godewa Allah ma jininsa (O) shida Fatima' a nan ne Aisha ta dauki cutar dayake ita jininta bekai nasu karfiba yai affecting dinta har mahaifarta. "amma ita Fatima ma batasan ana yiba sbd bata dashi' shima Nasir yanzu yasamu sauki sosae' a cewar doct zasu iya komawa gida idan yaso yarinka zuwa chickcup' koda Fatima ta sanarwa abbansa sai yace aa sutsaya yakara samu sauki tuku. "shima Nasir din gani yasamu sauki yasashi daukar Fatima suna yawo sauran kasashe suna shan iska.. ~~~ ~~~ ~~~~ gida yashake fal da jama'a na binni dana kauye har babu masaka tsinke. "bagaren maza kuwa duk sun shirya zuwa daurin aure. "jikin Aisha yai sanyi sosae sbd duk halimu ya nuna mata zahrdee ke aure'amma wani abu daya daure mata kai ko jiya tare suka kwana dashi amma bece mata komai ba. "daki takoma ta zauna bakin gado hawaye ne kawai takeyi wani nabin wani. "gidan su Zainab ma duk sun shirya daurin aure gidan su zahrdee kawai ake jira. "zahrdee Shamsudee nurudee duk kaya irin daya sukasa sbd Abba ne ya dinka masu sai dai na zahrdee da malum-malum ne' duk su uku suka shigo cikin gidan abokiyar wasansune mai suna Hajjo ta rangada guda hade da cewa zahrdee ango' kaga ta inda kafi yayyinka kenan har kakaiga mata biyu ga yayyinka marasa zcy dayan ma ya gagaresu. "Aisha dake daki tanajin h'aka tafashe da kuka ashe dama zhrdee zai'iya yaudarata h'aka zai'iya cin amanata h'aka ya boyemi mgnr aurensa. "fadawa tai a gado taci gaba da kukanta. "around ten O'Clock shap aka daura auren zainab da zhrdee. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘. (IMPACTING VALUABLE KNOWLEDGE AND ENTERTAINMENT IS OUR CINCERN) STORY WRITENNG BY MMN USWA SAKON GAISUWATA GAREKI SISTER MARYAM A.I. GITAL WLH INA YINKI SAHEBATA BABU ABINDA YA SAUYA ALLAH YA BARMI KE HAR ABADA TARE DA LAFIYA MAI DOREWA AMEEN INA YINKI TAWA UP UP UP DA YARDAN ALLAH. 3⃣2⃣ "ana gama daurin aure sukayo gida. "ko kafin su dawo anriga an shirya walima'suna isowa aka fara walima. "ango zahrdee yasha wa'azi sosae hade da fatan Allah yabashi ikon adalci a tsakanisu. "bayan la'asar gidan amarya sukakai kaya daya daga cikin gidajen da Abba ya gina ne bangaren da tun farko Abba ya gina masa a nan ne Zainab zata zauna. "tunda bayan dauri aure zahrdee yaso kiran Aisha kodan yai mata bayani amma besan ta inda zaifara ba. "sbd shima kansa yasan be'kyauta ba kamata yai tun kafi lkc yai tasani tunda gaba daya gidan babu wanda ya sanar da'ita' k'uma koba h'aka ba shine ya kamata ya sanar d'aita tunda zamansa takeyi amma be sanar d'aita ba sbd yana gudun bacin ranta. "shiru kawai yai yana tunani sbd besan wani Aisha take ciki ba a wnn lkc' gani duk irin tunane-tunane ga bazai kaisa ba wayarsa ya ciro daga aljihu yai dialling number Aisha zahrdee yayi kira yakai eight miss call Aisha na kallo amma batai picking ba' gani zaidameta takashe wayar daya baya. "jin takashe wayar hnklin zahrdee yakai matuka gurin tashi' kai kawai yasa yashige cikin gida Allah yasa snn babu wasu mutani ta bangarensa hakan yasashi samu damar shigewa dakinsu hade da sa key yarufe dakin. "yana shiga gani Aisha yai kwance sharbe-sharbe a kan gado kamar wanda akaiwa duka' da sauri ya karisa kan gadon h'ade da sa hannu ya dagota jikinshi yana cewa Dan Allah Aisha kiyi hkr ki yafemi' nasan nayi maki laifi amma Dan Allah kiyi hkr wlh ba laifi bane nima kaina bansan mgnr wnn auren ba wlh Aisha. "fisge jikinta tai daga nasa' katashi ka bani gu zahrdee banaso ganika Dan Allah kafita kawai zahrdee' zahrdee banasonka banason ganika zahrdee katafi gun amaryanka kawai. "haba Aisha wacce irin mgn kikeyi h'aka? wlh babu inda zani inanan tare dake Aisha ta.. "zahrdee kafita min a daki". "babu inda zani". "kafita min a dakina". "wlh babu inda zani' sai dai duk abinda zakimi kiyi amma wlh ina tare dake. "hannu zahrdee yakai zai rikota'juyawar da zatayi tasa ta igijeshi ya f'adi ta baya a kasa a guje Aisha ta sauka dan dagoshi. "hannu tasa ta taimaka masa ya mike yana tashi tajada baya' binta yai da karfi ya riketa yana f'adin Dan Allah Aisha ki saurareni kiji mgnr da zanfadi maki Aisha. "cikin galatse tace ina sauraronka. "dukawa yai a gaba rike da hannayenta bibbiyu' snn yace Dan Allah Aisha Dan annabi ki saurari abinda zanfadi maki' wlh Aisha anyi aurenga ne kawai amma wlh kwata-kwata bada amincewa ta bane' su Abba da Hjy ne suka shirya h'aka amma na rantse maki da Allah Aisha bana sonta ko kadan wlh Aisha kece nakeso dake ne zcyta take rayuwa. "nasan ba lalla bane idan na f'adi maki ki yarda ba amma wlh wlh Aisha tunda nake a rayuwata ban taba jin dindinon son wata mace ba bayan ke' Aisha kece rayuwata da sonki nake kwana nake tashi' idan har kika koreni kika rabani dake bansan inda zansa kaina ba' k'uma koba komai kinga kibawa duniya kofar shigowa rayuwarmu kenan su tarwatsa zaman damuke dake. "Dan Allah kiyi hkr ki rungumi wnn aure a matsayin kaddara' ni zahrdee nayi maki alkawarin bazan taba canza makiba ko dede da kwayar zarra. "idan ma banda abinki Aisha wlh bafa sonta nakeyi ba' kece kekadai tawa na mallaka maki kaina halak malak. "murmushi kawai tai. "hannu tasa ta dagosa sama' gani h'aka yasa zhrdee rungumarta. "around 8-30 yyar Hjy da kanwar Abba da sauran da baza'a rasaba suka tafi dauko amarya. "motocine lafiyayyu guda biyar masu bakike glass suna biye da juna' koda suka isa inna Hulairane da sauran jama'a suka taresu cikin girmamawa bayan sun gaisa batare da bata lkc ba aka fito da amarya' Kai tsaye bakin abbanta aka kaita yai mata nasiha sosae snn yabasu ita hade da cewa beyarda kowa ya kwana a gidan ba' ana kaita adawo. "duk suka amsa tare da godiya' snn yace wa Hulaira ta kira masa Hjy umman Zainab tana zuwa yace ko kinada abin cewa?" "a'a" alhjy Allah ubangiji ya basu zaman lfy?'. "amin" kefa Hulaira?". "a'a" Alhj duk abinda zamuce kariga da kafadi' mudai fatanmu Allah ya hada kansu ita da abokiyar zamanta. "amin' tashi kuje". "a lkcn ne Zainab tasa kuka' hade da kiran inna Hulaira. "da sauri Hjy tabar dakin sbd hawayen da suke zabo mata. "ana daukar amarya kai tsaye sai gidan su zhrdee' har dakin Hjy aka kaita snn aka tuwa daya daga cikin bakin da sukazo baki ta kira Aisha. "koda yar'aike taje bakin kofa tanata sallama babu wanda ya amsa mata sakamakon Nisan da sukayi. "Aisha naji tayi kokarin ture zhrdee dan tasamu mikewa amma ina zhrdee ya hanata dole yasa ta hkr. "yar'aike ko da taji shiru komawa tai tace tariga tai bcc' yyan Hjy tace saida aje a tada'ita sbd idan ba'a hadasu yau anmasu fada ba sbd Allah wani lkc ne za'a hadasu. "har tamike da sauri Hjy tace a'a abarta kawai. "Aisha najin shiru tacewa zhrdee kagani ko' da kabarni naje naji kiran da akemi' wata kilama Hjy ne ke kiran. "idan Hjy ne sai me' Dan Allah kizo mu kwanta. "kamo mata hannu yai suka koma. "bayan kowa yai nasa jawabin ne aka dauki amarya zuwa gidan ta". "koda suka isa dakinta aka sauketa kanwar Mmn zainab ce ta dauko wasu maguguna tasake bawa zainab tasha hade dana shafawa a jiki' bayan ta gamane ta dauki bokitin ragowar magugunar ta bata da k'uma nuna mata yadda zatayi anfani dasu' ko wnn da lkcn shansa. "Zainab ta amsa sukuma suka mike h'ade da sallama' drive ya medasu gida' gani za'a watse a bar gida babu kowa gashi har lkcn ango bezoba yasa yyar Hjy ta buga gida ta sanarwa Hjy akan har yanzu zhrdee bezoba ita k'uma gida takeson dawowa sbd bcc takeji. "Hjy najin h'aka taje ta sanarwa Abba abinda ake ciki'murmushi kawai Abba yai hade da daukar wayarsa ya kira zhrdee. "zahradee yana gani number Abba amma be daga ba sbd yariga da yasan kiran da ake masa. "Abba yai kira har yagaji amma zhrdee be daga ba' tun ran Abba be baciba har yakai ga yabaci. "himm Alhj kaga abinda nake fadi maka ko?" tun yanzu kenan yaronga yana niman zuba mana kasa a ido. "mikewa Abba yai batare sa yai mgn ba yana gaba Hjy na baya' bagaren Aisha Abba ya nufa da kansa yake knocking jin muryan Abba ne yasa Aisha mikewa da sauri hade da cewa zhrdee tashi Abba nefa da kansa. "a lkcn har bcc ya fara daukar zhrdee jin ance Abba ne yasashi mikewa da sauri ya dauki wandonsa yasa snn yaje ya bude kofar". "yana budewa Abba yace fito kawuce". "to kawai zhrdee yace hade da komawa cikin d'akin' toilet yashiga yaje yai wanka snn yazo yasa kaya yafita' yana fita Aisha tasa kuka. "zhrdee na fita Abba yasashi a mota da kansa yakejan motar tafiya suke amma babu wanda ya tankawa wani har sukakai gidan. "suna isa zhrdee ya bude kofa ya fita a lkcn ne Abba yace son saida safe' idan ka karisa ciki kakirami yya tafito. "to kawai zhrde yace snn yakarisa ciki. "yana shiga Hjy tai masa sannu da'isowa h'ade da cewa saida safe. "Allah ya bamu alkairi. "tana fita yarufe gida ko'ina kai tsaye wani extra room yanufa koda yashiga dakin babu komai empty ne ko katifa babu dawowa yai parlour ya dauki pilon cushion yaje yai pilo dashi rigarsa k'uma ya shinfida a kasa ya kwanta. "Zainab shiru-shiru ango zaishigo amma shiru' gashi har bcc ya fara daukarta' shiko zhrdee yana can bemasan tanayiba. "Abba yana isa gida Hjy ta taresa da yya dai Alhj?". "murmushi kawai yai batare da yace komai ba. "gani 1C-lock yayi k'uma har yanzu zahrdee be shigoba mikewa tai tanufi parlour a hankali take tafiya sbd tsoron daya kamata a tunaninta ita kadaice a gidan. "koda ta jijina kofar parlour jinshi tai a rufe gam da key' dawowa da baya tai tafara dube-dube gidan' duk inda taduba babu wanda tagani wani Sabon tsoron yasake kamata da sauri ta juya zata koma daki sai nepa suka dauke wuta' gida yasake rufewa da duhu. "hankalin Zainab yayi matukar tashi a hankali take laluba tana niman hanyan zuwa daki dan kunna light din wayarta. "duk juyin da Zainab zatayi saita bige sakamakon rashin light garin lallabawa tana niman hanya yasa duk ta rikito da jeren banga da akai mata glass din suka faffashe. "da sauri Zainab taja da baya' taje ja dabaya ne Glass ya soketa a kafa' a take tasa ihu tana kuka. "duk abinda Zainab keyi a kunni zhrdee amma besa ya fitoba. "da h'aka tai tayi tana karo da bango har ta'isa d'aki' ga bigewar da goshinta yai' da h'aka har tasamu tashiga d'akin. "Zainab najin ta dafe gado ta fashe da kuka tana kokarin daukar waya ta kuna' bayan ta kunnane taje ta rufe kofa a gefen gado ta rakube taci gaba da kukanta. "ga waya a hannunta amma batai tunani kiran zahrdee ba'da h'aka har safe yai. "jin kiran sallar farko zahrder yamike yabar gidan' itama Aisha mikewa tai taje tai alwala tazo sallah' bayan ta'idar da sallah ne taji bcc ya kamata pilo ta jawo ta kwanta akan sallaya taci gaba da bcc. "zahrdee bedawo gidan ba sai around 11AM koda ya dawo parlour ya zauna' bayan ya zauna ne yake gani barnan da Zainab tai. "mikewa yai ya tara kayan gefe glass din da suka fashe k'uma ya sharesu ya zubar snn ya dawo ya hade da kunna TV yana kallo' be dade da zama ba su Amatullah da Amatulrahman sukai sallama dauke da kayan abinci a hannu' zahrdee da fara'arsa ya taresu bayan sun gaisa amatullah tace Hjy ce tace akawo maku abin karyawa. "Allah sarki kice mata mugode. "yya ina amaryan taka?". "tana ciki tana bcc". "jin haka yasa basu sake mgn ba suka mike hade da sallama. "har bakin kofa zahrdee yai masu rakiya sann yadawo. "zama yai dirshan ya dibi abinci yafara ci' yana cikin ci kenan yar'uwan Zainab sukai sallama suka shigo. "da fara'arsa ya karbesu' suka gaisa bayan sun gaisa ne yace dasu tana cikin daki. "gani su tsaya basuda niyar shiga yace bismillh mana. "ido suka sake hadawa suna kallon junasu' da yake duk yar'mata ne mace daya ne me aure a cikin su. "mikewa zhrdee yai ya fita ya bar masu g'idan. "yana fita idon su yakai gun kayan da zainab ta barnatar da sauri har suna h'ada baki suna cewa lahhhh! duk abinda sukai kamar wasu yara". "to mema ya kawosu parlour?". "a'a kekuwa kila garin wasane. "h'aba wani irin wasa?" wasa yabar bedroom sai parlour. "k'uma dai da wani irin tunani wlh' jiya-jiya da daurin aure shine har zasuyi wani abu?". "kekuwa rai da marmari' rai dangin goro". "yanzu dai duk kumubar wnn mgn kuzo muje cikin d'akin muganta. "duk su hudun duguma sukai zuwa cikin bedroom'koda suka shiga ganita sukai kwance kan sallaya tana bcc' shigowarsu ne yasa ta b'ude ido' tana cewa su walida har kunzo sannuku da zuwa. "duk Zainab na mgnr ne a kwance bata tashi ba. nusaiba dake kusa da walida tace Zainab amarya to tashi zaune mana. "to"kawai tace". "da kar zainab ta laluba ta mike zaune' snn tace da wani lkc ne kuka shigo. "bamu dade da shigowa ba' mushigo musamu angonki a parlour yana karyawa amma ganimu yasashi fita. "himm kawai zainab tace' gani gado a mutsutsuke ko gyara shi ba'ai ba yasa walida cewa zainab meyahanaki gyara d'akin tunda safe sbd Allah' yanzu inda bakin kunya ne suka shigo mezakice?" Dan Allah kitashi ki gyara gadonki tun kafin jama'a suyi yawa. "to kawai tace". "saida Zainab ta kamo katakon gado snn ta mike. "h'ada ido suka sakeyi suna murmushi. "gani takasa daga kafa sakakoman ciwon dataji garin yai mata tsami. "nusaiba tace me k'uma ya samu kafar zainab?". "yankewa nayi". "yankewa k'uma?". "Eh" wlh". "garin yaya?" k'uma da me?". "dauke light akaji nikuma naje mikewa ban saniba na bige da katakon friend dake parlour shine glss dinsa ta yanke ni. "to fa' Allah ya sauwake". "amin". "jawo zani gadon da Zainab zatayi taga Ashe shima jini yabata bata saniba' suma suna gani suka sake h'ada ido. "kwashewa Zainab tai ta zuba a gefe har ta daga kafa kenan tanaso taje wadrop ta dauko wani zanin gadon taji kafarta ya rike mata' tsayawa tai tai shiru h'ade da matse baki. "walida tace yah?" dai Zainab?'. "kafa nane yaimin tsami". "to!!! koma ki zauna". "koma gefe tai ta zauna. "nusaiba da walida suka gyara mata gadon tas' zani gadon daya baci da jini suka kai bathroom suka ije sbd a nasu tunanin najasa ne a ciki yasa basu wanke ba. "walida tace Zainab kinyi wanka?". "a'a". "sbd me?". "himm kawai tace". "h'aba Zainab sbd Allah da saniki da komai kike zama da najasa har wnn lkc?". "shiru Zainab tai bata tanka ba". "amma kinyi sallah ko?". "nayi". "to shikenan yanzu tashi kije kiyi wanka daga nan ma saiki gargasa jikinki da ruwan zafi. "to kawai tace". "mikewa Zainab tai gani yadda takejan kafa yasa walida riketa zuwa bathroom bayan ta fitone suke mgn nusaiba ke cewa walida kodai na karfi yai mata?". "me kika gani nusaiba?". "ke baki gani yadda taji jiki' k'uma ga barna da sukai har parlour fa sbd Allah' wann wani irin abune h'aka?". "gskya kam"da alima". "matar aure dake tare da sune mai suna SAMEENRAT tace a'a basai yai mata na karfiba dama dole asamu h'aka tunda ba taba sani namiji taiba'amma idan ta daure kafin nan da sati tasaba. "duk baki suka h'aka suna cewa ko 🤔 ?"!!!. "Eh" mana amma kuce mata tarinka amfani da ruwan zafi wajan tsarki". "duk suka hada baki da cewa to". "fitowar Zainab daga toilet ne ya katsesu. "Su walida da nusaiba yaran yyan Alhj Musa ne Uwa daya uba daya' ita k'uma SAREENRAT matan yayan su walida sai dayan da suka shigo tare mai suna Rahma ita k'uma da bbnta da Alhj Musa uba daya ne duk suna karatu a nan bauchi university ne. "aiki suka taya Zainab sosae harda abinci saida sukai mata suka zubawa zhrdee nasa a kula snn sukai wanke wanke gam da sallar magrib suka tafi gida' bayan fitarsu ne zainab tashiga wanka tana gamawa tai alwala saida tai sallah snn tai kwanlliyarta shikin sket da riga na material light blue tayi matuka dawowa parlour tai ta zauna tana kallo. "koda zahrdee yabar gidan can wata uguwa yaje ya boye inda babu wanda yasan yana gun' saida ya daidaici magrib yayi kowa yatafi masallaci mata k'uma maybe suna daki suna nasu sallar snn ya saci jiki yazo gun Aisha' Aisha na sallah kamar daga sama taji anfado dakinta. "h'akan yasa tai kananu sura sbd ta'idar da sauri' bakin gado zhrdee ya zauna yana jiran ta'idar' tana sallama tace lfy?" me yakawoka kaida kake da amarya?". "gani zata daga masa murya batare daya tanka taba 🤫 yai mata daga snn bata sake mgn ba. "mikewa yai ya tube h'ade da cewa jeki ki hadami ruwan wanka. "Aisha tace wankan me zakaimi anan? inda kaje kai abinka daban inda zakai wanka daban' babu wani ruwan da zanha maka. "ko kallonta beyiba yace ta kanki akeji' snn yashige bathroom yaje yai wankansa h'ade da alwala yazo yai sallah snn ya kwanta. "Aisha dake tsaye tana kallonsa har ta b'ude baki zatai mgn kenan zhrdee ya jawota gado ta fada jikinsa' Aisha na kokarin tureshi da karfi ya danneta yana cewa h'aba Aisha ta Dan Allah meye kikeyi h'aka?" "dama Akwai ranar da zaki iya korata daga gareki?". "sbd Allah zhrdee kai da kake da amarya mezakai dani..... "amarya banza amaryan wufi wayace miki tana gabana?" ko nine na f'adi maki h'aka?". "a'a to amma... "to amma me?". "h'aba Aisha Ashe duk f'adi tashi da nake akanki b'akya gani' sbd da kefa duk nakasa sukuni tun safe nake niman yadda zanshigo na ganki amma shine kike tureni daga jikinki Aisha". "jikin Aisha yai sanyi tace to kayi hkr" amma Ai gani.. "kikaga me?" ni bani gani kowa a kwayar idona saike. "murmushi kawai Aisha tai h'ade da cewa uhmm". "rungumarta yai suka kwanta. "shiru-shiru Hjy bataji motsin Aisha ba tace amatullah taje ta dubota ko lfy?". "to kawai tace mike"?. "koda Amatullah taje tai ta sallama babu wanda ya amsa' sukuma a lkcn duk suyi nisa shiya basu san tana yiba' itama Amatullah tasan zahrdee baya nan h'akan yasata tura kofar ta shiga. "ganisu da tai yasata fita da sauri taja kofar' duk da suna rufe a bargo amma saida taji wani iri' jin motsin kofar yasa Aisha cewa tashi kamar anshigo. "kin tashi yai yana f'adin babu wanda yashigo' a'a zahrdee Dan Allah katashi "gani ta nace ne yasashi tashi yaje yasawa kofar key yadawo. "koda amatullah taje cewa kawai tai tasameta tana bcc. "Hjy tace bcc lfy tun yanzu. "Eh"kawai tace' gani snn bata sake mgn ba". "zainab ta zauna har tagaji ta koma ta kwanta'tana kwanciya bcc ya dauke ta". "zahrdee na rungume da Aisha suna hira har 11PM karaf idon Aisha akan a gogo da sauri ta sanarwa zhrdee' shima mikewa yai tare sukaje wanka bayan sun fitone ya canza kaya sn sukai sallama ya fita a sace zuwa g'idan zainab. "yana shiga ya tarar tayi bcc rufe gida yai snn yazo ya dauki pilo yaje extra room din ya kwanta. "zainab bata falkaba sai 2-30AM. gani ita kadaine a g'idan kamar jiya da sauri ta tashi zuwa bedroom. "da sassafe tazo parlour dan gani wanda yake motsi a g'ida' tana tsaye a tsakiyar parlour zhrdee yadawo daga sallama' yana shiga suka hada ido' yace lfy?". "a'a" dama motsi nakeji cikin dare shine nazo duba waye". 'OK kawai yace har zaishiga dakin daya kwana tace ina kwana". "lfy klau kintashi lfy?". "lfy klau". "shigewarsa yai yaje yaci gaba da kwanciyarsa. "kitchen zainab ta shiga ta hada masu abin karyawa' tana gamawa taje tai wanka da kwalliya snn tazo ta dauki tre din abinci da sallama tashiga d'akin ta ije masa a gaba snn ta tadashi. "sbd ta dauka bcc ne yakeyi batasan idonsa biyu ba". "mikewa yai zaune h'ade da cewa ngd". "murmushi tai har ta zauna zhrdee yace a'a tashi kije kiyi wani aiki' idan ina bukatar wani abu zansanar dake". "to kawai tace snn ta mike ta tice. "da h'aka Zainab take rayuwa a g'idan zhrdee' koda wasa be taba leka dakinta ba banle yasan kalarsa' ita k'uma zainab da rashin wayo irin nata besa ta daina shan maganin matar da aka bata ba' safe rana yamma take sha. "duk yadda zhrdee zaiyi saiyayi idan zuwa gun Aisha' idan beje da asuba ba zaije da rana ko dare. "satin su zainab uku da aure ciwon mara ya kamata tun dare takeyi kamar me nakuda gashi taiwa zahrdee kiran duniyarnan yai banza da'ita' gani h'aka yasa Zainab daukar wayarta ta kira g'ida takira inna Hulaira tana kuka. "kukan da takeyi ne ya hanata mgn' jin h'aka yasa hankalin g'ida ya tashi da sauri inna Hulaira ta d'au hijab sai g'idan zainab' koda tashiga ganita tai kwance tana juyi akan carpet tana kuka. "da sauri tai kanta hade da tambyr lfy zainab meya sameki?". "zainab takasa mgn sai kuka". "gani h'aka yasa inna kiran Hjy Mmn zhrdee ta sanar mata da abinda ake ciki. "nan take Hjy ta kira Abba ta sanar dashi' Abba yace ina son yake?" koba a gidan ne yake ba?". "eh ba'a nan yake ba". "to shikena yanzu abinda za'ayi kije ki dauketa zuwa hospital kafin yazo. '"to kawai Hjy tace' kyale ta dauka gani gida babu kowa da kanta taja mota'tana isa inna ta fito da zainab sukai hospital. "amma yai kira har yagaji amma duk numbers zhrdee a kashe suke gaba daya. "gani h'aka yasa Abba zuwa shagon son da kansa nan ma begansa ba' mmki ya kama Abba sosae. "daga nan hospital ya wuce'ko kafin yaje doct yayi abinciken da zaiyi ya gama' ruwa kawai aka samata hade da alluran bcc. "Abba da kansa yaje office din doct din dayake family doct ne'doct yaiwa Abba bayani komai. "batare da nuna damuwa ko bacin rai ba yace ngd insha Allahu za'a gyara. "bayan Abba yafita a office din doct Abba ya sami Hjy ya sanar da'ita duk abinda ake ciki. "ciko da mmki Hjy tace wlh alhj nifa ban fahimci abinda kake f'di ba". "Abba yace Hjy kenan Ashe tunda akai auren nan son betada tarawa da yarinyarnan ba?" "hade da buga kirji Hjy tace me?" "wlh kuwa Hjy" nima kaina abin yana dauremi kai. "lalla zhrdee yanuna mana yacika dan kansa' amma Dan Allah Alhj kabarni dashi kaga ikon Allah. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘. 🌳Impacting valuable knowledge and Entertainment is our concern🌳. story written by Mmn uswan☘ 3⃣3⃣ "murmushi Alhj yai snn yace Hjy kenan' me zaki?" "kashhhh!!!" nace kabarni dashi kawai". "to naji na yarda amma duk abinda zakiyi banaso ki aikata cikin fushi' ni inda kin barni zanshawo kan al'amarin". "Alhj kenan' nafi kowa sani halinka' shiyasa nace kabarni dashi". "fitowar inna Hulaira ne daga d'akin yasa sukai shiru da mgnr". "Hjy ta tareta da cewa me doct yace ne?". "a'a" ba dani akai mgnr ba da Alhj nima abinda nake tambya kenan kika fito' amma yace result din be fito ba". "Eh" h'aka ne Hjy amma ya jikin nata yanzu?". "Alhj jiki da sauki". "ta tashi ne". "a'a" har yanzu bata falka ba". "to shikenan ni zanje idan yaso ko zuwa yamma ne zamu dawo da maigidan mata". "sbd na aikesa wani kauye be nan shiyasa baku gansa a nan ba". "Allah sarki Allah ya dawo dashi lfy". "amin ngd". "bayan tafiyar Alhj ne duk suka shige cikin d'akin". "Abba be koma kasuwa ba saida yabiya g'ida ko zaiga zhrdee amma be gansa ba' a cewar Aisha tun fitar safe be dawo g'idan ba". "h'aka ya sake komawa kasuwa nan ma bashi' ko da tasake kiran number still a kashe yake". "zama Alhj yai yai shiru yana tunanin yadda akai zhrdee ya lalace h'aka' to ma me yake nima da nine?" kodae so yake ya zubarmi da mutunci a gun uban yarinya nan ne lalla idan ko son be gyara ba wlh saina nuna masa kuskurensa. "Aisha na komawa d'aki zhrdee yace lfy Abba ya kiraki?". "kae fa ya tmbya". "Ni k'uma?". "Eh kae". "to me zanmasa?". "nima bansani ba". "to bari na fita baje kasuwa naji abinda zaice". "to". "mikomin wayata da riga". "Aisha na mika masa yasa snn ya kunna wayar". "bayan ya sanya riga ne yace da Aisha dubami kiga idan babu kowa nazo na fita" Aisha na fita sukai karo da Amatullah'gani yadda Aisha ke juye juye yasa amatullah cewa lfy Aisha?". "me kika gani?". "gani nayi naki juye-juye kamar mara gskya". "rashin gskya k'uma?". "Eh"mana". "a'a" babu komai". "uhmmm"!!. "amatullah tace". "makewa Aisha tai ta dauka amatullah shigewa d'aki tai' batasan itama makewar tai ba". "Aisha na gani shigewar amatullah da sauri taje ta sanarwa zhrdee suka fito tare ya fice snn ta koma d'aki. "duk abinda sukeyi a idon amatullah' kama baki kawai tai tana mmkin yadda zhrdee ya lallace h'aka bayan da ba h'aka yake ba". "Zainab bata falka ba sai bayan la'asar tana falkawa da sauri suka mike zuwa kanta suna tambyar jikinta". "shiru Zainab tai sai hawaye da suke kara kaina a fuskanta' gani h'aka inna hulaira taje daidai inda kanta yake tasa hannu tana shafe mata kai h'ade da tambyarta meke damut". "cikin kuka Zainab tafara mgnr tun kafin ta fasa goran da sauri Hjy ta tareta da cewa ya'isa h'aka' ba'ason mara lafiya da surutu". "inna hulaira tace gskya kam". "gani magrib ya kusa yasa Hjy kiran amatullah' amatullah na dagawa Hjy tace suyo abinci sukawo". "amatullah tace to Hjy". "har zata kashe wayar sai k'uma ta tambya ko zahrdee yazo g'ida". "a'a kawai amatullah tace". "koda zhrdee yaje kasuwa gun Abba'Abba bece dashi komai ba sbd a kasuwa suke". "da yamma lkcn su amatullah da amaturahaman suna hospital saiga Abba da zhrdee sun shigo". "suna shigowa duk suka mike bayan su gaisa da Hulaira Abba ya tambyi mai jiki". "tace da sauri'snn suka fita shida Hjy". "zahrdee dake gefen gado daedae kan zainab yadora hannu pilo da tasa kai batare dayace mata komai ba' gani h'aka yasa Hulaira fita daga d'akin'. suma su amatullah fita sukai yarage subiyu kawai. "bayan su fita ne zhrdee ya jawo kujeran dake gefe ya zauna' saeda ya zauna snn yace yaya jikin?". "banza dashi Zainab tai bata tanka ba". "dakefa nakeyi ko baki jikine". "a lkcn ne tace meya dameka da jikina da har kake tambya ta". "Dan na tambayi jiki sai yazama f'ada k'uma". "ta yaya bazanyi f'ada da kaiba sbd Allah nasan kana jina lkcn da nake kwada maka kira amma baka amsani ba kai tafiyarka". "h'aba zainab ta yaya zanji kiranki na kwaleki' wlh banji bane amma tunda kince h'aka ne to kiyi hkr' yanzu dai yaya jikin naki. "tsaki tai bama h'ade da jiya masa baya. "yanzu Zainab ni kikewa tsaki sbd Allah dan na tambyi jiki kin?" tunda tambya ya zama laifi Allah ya baki hkr ni zantafi ko kina bukatar wani abu?". "banza dashi tai bata tanka ba". "Zainab dakefa nakeyi.... "shigowa inna Hulaira ne ya katse zhrdee' Ashe taji abinda suke f'adi' nan take ta h'au zainab da f'adi". "zainab najin h'aka tasa kuka h'ade da cewa a'a". "shima zhrdee gani h'aka yasashi hawa kan gadon ya zauna kusa da'ita snn ya rike mata hannu daya kamar mai yimata tausa cikin sigar tausayawa yana f'adin h'aka zainab dita Dan Allah kiyi hakuri ki daina wnn kuka mana Dan Allah kinji". "dayan hannunsa yasa yana goge mata hawaye' gani inna na gun yasashi jawota ya rungumeta a kirjinshi yasa shafe mata baya h'aba zainabata kiyi hkr h'aka kinji k'uma Dan Allah kidaina kuka h'aka banason gani hawaye a fuskanki pls baby stop crying. "yanzu f'adimi me zakici na siyo maki"?. "shiru tai bata tanka ba". "kiyi mgn mana Zainab". "Zainab tasake shiru". "inna Hulaira dake gefe murmushi kawai tai h'ade da dauke kanta a gunsu. "gani bataga niyar mgn yasashi cewa ina zuwa' sauka yai daga kan gadon ya fita". "koda yafita bega su Hjy da Abba ba' a zcyrsa yace maybe gida sukaje". "bakin hospital yaje inda ake siyar da gasassun kaza yasiyo h'ade dasu YOGHURT DA ICE CREAM snn ya dawo ciki da sallama ya shiga dakin plate ya dauko ya zuba namar kazan a plate snn ya h'au gadon dama lkcn Zainab ba zaune ta jingina da bango da kansa yake bata a baki. "su Abba suna shigowa kenan sukai karo da zhrdee yana bawa zainab abinci a baki murmushi kawai Abba yai batare da sun karisa ciki ba yajuya ya fita". "Hjy ne ta kariso ciki dan suyi sallama da inna'inna na gani Hjy ta mike suka fita bayan sun fitane sukai sallama Hjy tace da safe zata dawo". "Inna tace babu damuwa". "bayan su fitane inna ta tsaya a waje tana jiran sugama". "zainab tai mmkin zhrdee sosae a zcyrta tana cewa kodai dama zhrdee yana sona h'aka' shine baya kulani' baya kwana a dakina' bayaso nazo kusa dashi' kodai yaudarata yakeyi' ko k'uma sbd yaga ba'a gida muke ba". "tsayawa tai tai shiru tare da zuba masa ido takasa tauna namar dake bakinta". "zahrdee ya katse mata tunani da tambyrta yahh!! dae?". "uhmm' babu komai". "kodai kin koshine?". "Eh'nakoshi". "OK to kisha yaourt din koda kadan ne". "daukowa yai ya bata a baki tasha snn ya cire ya'ije. "tissue ya dinba ya goge mata baki snn ya sauka daga gadon h'ade da cewa ni zantafi' in Allah ya kaimu da safe zanzo". "shiru kawai tai tana kallonsa cike da mmki Kodai ba zhrdee da tasani bane". "kina jina kuwa zainab?". "Allah yasa mukai". "amin ngd". "bayan ya fitane inna tashigo". "su Hjy suna hanya ne Hjy take tambyar Alhj a ina yaga yaronga?". "wafa son kike nufi kowa?". "shifa". "wlh nima bansan ta yaya akai yazo kasuwa ba'kawai ganisa nayi a kasuwa". "baka tambyesa daga ina yake ba?". "a'a ban tambyesa ba sbd gani nayi a kasuwa muke". "to amma kinsan wani abin mmki?". "a'a saika f'adi". *"da gske ne kuwa abinda doct ya fada?". "me kagani ne Alhj?". "sbd abinda naga yake mata a hospital". "himm Alhj kenan'kana mantuwa da d'an yau". "kamar yaya?". "baka tunani yayi h'aka ne kawai Dan dauke mana hankali?". "ko Hjy?". "Eh"mana". "to Allah ya'kyau ta". "amin"kadai kabarni dashi kawai". "him Hjy kenan". "su amatullah dake baya suna zaune sunaji duk abinda Abba da Hjy suke f'adi amma babu wanda ya tanka har suka isa". "suna isa Hjy da yara suka riga shiga ciki Abba ya tsaya gyara parking mota' su Hjy suna shiga ciki daidai lkcn Aisha na fitowa daga kitchen' tana gani shigowa su Hjy da fara'arta ta taresu da sannnu da dawowa". " hjy yawwa sannu da g'ida". "har Aisha zata shige Hjy ta daka mata tsawa da keee!! da sauri Aisha ta juyo' baki iya cewa ya mai jiki bane?". "kuna da mara lfy ne?". "me kikace Aisha?". "cewa nayi kinada mara lfy ne?". "lalla Aisha' koda yake bakida laifi jeki abinki". "shigewa tai batare da tattama ba". "ido kawai Hjy ta zubawa Aisha tana kallonta har tashige' a zcyr Hjy tana f'adin zakici ubanki idan dani zakiyi". "amatullah da amatulrahaman sukasa dariya". "da safe saida zhrdee ya biya hospital snn taje kasuwa' da yake shida Hjy sukaje' da yamma akai sallama Hjy ta dauki zainab zuwa g'idan ta' a dakinta ta'ije ta har zhrdee da Abba suka dawo daga kasuwa. "bayan su dawone zhrdee yana d'akin Aisha yanacin abinci suna hira' Hjy da kanta tai sallama Aisha ne ta amsa snn taje ta b'ude kofar' gani Hjy ne yasata dukawa tace sannu Hjy". "kema sannu'ina Mijin naki?". "yana ciki". "kirashi kuzo tare". "to kawai tace". "komawa tai ta sanar dashi' mikewa yai ita k'uma ta sa hijab suka fita tare". "parlour suka nufa ita dashi' suka shiga da sallama' Abba da Hjy suka amsa a kan carpet suka zauna ita dashi zhrdee yace Abba gamu". "Abba yace bani ke kiranku ba Hjy ce". "eh'nice na kiraka dama tambyarka ne nakeso nayi' baka sabarwa matarka bane game da rashin lfy dayan matarka bane?". "tasani". "tasani fa kace?". "ke Aisha". "na'am". "dama kina sane da yar'uwanki ba lfy?". "Eh". "to meyasa jiya da nake tambyarki kika nunarmi baki sani ba?". "eh' sbd bansan gutane kukaje ba shiyasa k'uma.. "k'uma me?". "babu komai". "yanzu sbd Allah Aisha kin kyauta kenan inda g'ida daya aka hadaku h'aka zaku zauna? k'uma idan ma banda abinki Aisha koda bangani ba amma naji labarin cewa koda kikai auren farko ku uku ne a gun mijinku h'aka be dameki ba sai zainab ce zata tsole maki ido? to wlh bazan yarda da wnn zama ba dole ki gyara". "shiru Aisha tai tanaji Hjy' zhrdee ne yace aa Hjy Aisha batada laifi nine me laifi sbd nine na hanata zuwa hospital din".. "salati Hjy tai snn tace lalla zhrdee yaune nasan bakada hankali' yanzu da kanka kake fadin h'aka". "shiru Aisha tai sbd tasan fadi kawai zhrdee yai dan kareta amma ba h'aka bane". "Abba dake zaune yana jinsu cewa kawai yai ke Aisha". "da sauri tace na'am Abba". "tashi kije daki". "to tace h'ade da mikewa zuwa daki". "bayan Aisha ta shige ne Abba yai gyaran murya snn ya fara da cewa son wlh bazan boye maka ba wlh ka batamin rai kwata-kwata tunda da nake dakai bantaba tsammani zakai mi h'aka ba'amma bakada da laifi laifi nane ngd da irin sakayyar da kaimi.. "menayi k'uma Abba kodai hadani dakai ne akayi?". "tsawa Abba ya daka masa yana fadin kaemi shiru' banason mgnr banza' kada ka daukeni yaro karami wanda besan abinda yakeyi ba mana. "Dan Allah Abba kaimi bayani wlh ban fahimta ba". "karaf Hjy tace kace baka fahimta ba mana ashe tunda akai aure babu abinda ya shiga tsakanika da matarka... "lailahallalahu' Muhammadu rasulillahi (S.W.A) akanka. "Dan Allah Hjy waya fadi maki h'aka?". "me garinku ne ya fadi min h'aka'kanaso kace karya ake maka ko yaya?" to bari kaji doct ya zaiyanami komai Ashe tunda aka kaita kallonta kawai kake kamar photo' nidai nasan kanada lfy banle nace.. "to nidai nidai". "kaidai me son?" wlh bari kaji wlh idan har kabari h'aka yasake kasan cewa wlh zanyi mummunar saba maka k'uma wlh bazaka sake jin dadi naba". "yanzu abinda nakeso dakai kaje ka dauki matarka mutafi gida Allah yabamu alkairai". "amin Abba". "tana dakin Hjy kwance". "to". "juyawa yai zuwa dakin Aisha". "ina zaka?". "shiru yai". "hannu kawai Abba ya nuna masa alama kada yashiga". "dakin Hjy yanufa daidai lkcn zainab ta tashi yace tashi muje gida". "to kawai tace snn ta mike". "suna fita dukawa sukai suka sallami su Abba snn suka fice". "suna fita Hjy ta mike zuwa kitchen daukowa Abba abinci' tana cikin tafiya ne su amatullah basusan Hjy na jinsu ba amatullah ta kwashe duk abinda tagani tsakani Aisha da zhrdee ta fadiwa amatulrahaman. "Hjy tai mmki sosae amma anan tabar mgnr ta karisa kitchen. "amma a zcyrta cewa tai lalla zhrdee mune zaimedamu kananu yara ko? amma ba komai. "su zainab suna isa gida dakinta suka nufa kai tsaye shida zainab ita kanta tai mmkin shiga dakinta da yai' sbd tunda tazo gidan betaba shiga ba". "suna shiga zainab tasamu bakin gado ta zauna' bayan ta zauna ne zhrdee yace wato ke Dan tsabar shan kunya da shan mutunci shine kika fadiwa su Abba da Hjy tsakanimu ko?". "ni? me k'uma nayi? Hjy ce tace na fadi mata wani abu?". "ohooo" ke kika sani koma menene yau zaki baya bashinsa". "kamar yaya?". "ta kanji akeji". "eyye". "Eh". "tashi ki tube". "kamar yya". "kamar yaya ake tubewa?" wlh idan baki tube ba da kaina zantubeki". "zainab najin h'aka da sauri ta mike zata fita daga dakin". " kafa zhrdee yasa mata'kadan yarage ta fadi da sauri yasa hannu ya jawota zuwa gado' snn yaje ya rufe kofar dakin ya dawo tubewa yai yarage dashi sai sglet da gajeran wado". "zainab na gani h'aka tasa ihu' hayewa yai kan gadon ya bita har inda take hannu yasa ya jawota da karfi' gani yana kokarin kware mata zani yasa zainab sa hannu tana bige masa nasa hannun". "zahrdee da yaga h'aka da karfin tsiya ya yaye mata zani zuwa sama h'ade da yafe pan din dake jikinta' duk irin kukan da takeyi besa ya karaya ba' da karfi ya shigeta zainab na ihu tana kiran zanmutu Dan Allah kabari' amma ina sbd shi kansa besan abinda yake ciki ba. "zainab tai kuka har tagaji sbd ihu muryanta har yakoma baya fita". "zahrdee be sauka ba saida yai mata jago jago snn ya sauka duk irin kukan da takeyi zahrdee be kalleta ba' iya kaci dauka rigansa yai yana hakki h'ade da cewa tunda abinda kikeso kenan gashi nayi maki' kinga kai kara yakare. "fita yai zuwa other room din da yake kwanciya". "gani daya zahrdee ya b'ude zainab dan kadan yarage ta hade' dagawa da tai taganta cikin jini male-male kwance akan gado wani ihu tasa hade ya jawo zani gadon hannu bibbiyu tana kallon abinda zahrdee ya aikata mata". 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘. 🌳impacing valuable knowledge and entertainment is our concern.🌳 story written by Mmn uswan☘ 3⃣4⃣ "zainab tai kuka har tagaji babu maceci' da h'aka tai tayi har safiya' tai kokarin tashi tai wanka da sallah amma ina' takasa sbd tsamin da jikinta yai ga wani uban zazzabin daya rufeta komawa tai ta kwanta taci gaba da hawaye". " zahrdee yana shiga dakin da yake kwanciya toilet ya shiga yai wanka snn ya fita h'ade da meda kayan jikinsa ya kwanta ". " shikadan a zcyrsa yake immagine irin dadin da yaji a gun zainab a zcyrsa yana cewa gskya baby tayi kota ko'ina' saidai kashhh!! bantaba jin sonta a zcyta ba dede da kwayar zarra". "inama da Aisha tace nasameta h'aka?" himm!! da taga gata da tareraya a guna ". " amma ko yanzu ba laifi' itama tanada irin nata dadin ". "da h'aka yaitayi har bcc ya daukesa". "zhrdee najin kiran sallar farko ya mike yai alwala yafita yabar g'idan masallacin uguwar yai sallah yana idarwa g'ida ya nufa gun Aisha". " Aisha na sallah zhrdee ya shigo d'akin ta babu ko sallama'itama da yake ta saba be dameta ba' yana shiga tubewa yai ya kwanta". "bayan ta'idar ne ta juya gareshi ina kwana". " lfy klau' kintashi lfy? ". " lfy klau' ya kwanar amarya?". "ha raranta yai h'ade da jawota zuwa jikinsa' Aisha na kwance jikin zhrdee tace ango mijin amarya na tambyi kwanan amarya ba'a bani amsa ba". " kina da wata amarya yane? " "a'a" kae ne dai me amarya ". " ni banida wata amarya daya wuce ke' ke kadai nasani amarya yata". "himm zhrdee kenan' kana da'ita mana' bagashi jiya ka dauketa kuka tafi ba". " muka tafi ina?" "g'idan ta". " wama yasani ko cikine da'ita". "cikin fa kikace?". " Eh " mana". "nasan dai ba kallonta zakai ba". " himm Aisha kenan' idan na f'adi maki wani mgn zaki yarda? ". " me zaihana". "idan nace maki bantaba kwana a d'akin taba zaki amince?". " kae fa😳 ". " da gske ". "kace ciwon datai ba ciki bane?". " ciki a ruwa zatasha ciki ko aina' idan ba k'uma zuwa tai dashi daga g'idan su ba". "Allah sarki har taban tausayi wlh' yanzu ido ka zuba mata?" "Eh" mana". "gskya baka kyauta ba". " to shikenan tunda ban kyauta ba' bari naje nayi ". "dagata yai daga kirjinsa h'ade da mikewa". "Da sauri Aisha ta rungumesa tana f'adin a'a wlh'duk sukasa dariya". "Aisha nasan ba lalla bane idan na f'adi maki wani mgn ki yarda' idan ma kin yarda zcyrki zata iya f'adi maki cewa dadin bakine' amma ni wlh nasan ba dadin baki bane har cikin zcyta nake f'adi". "wlh3 Aisha tunda nake a duniya bantaba son wata yar'mace ba bayan ke' a duk lkcn da mace zata tsaye a gabana tamkar namiji d'an uwana nake ganita' duk wata macen da zangani duk kimarta duk ajinta h'aka zalaka duk kyanta wlh bata birgeni idan bake bace' dalilin dayasa kenan nakasa iya daure zcyta dede da kwayar zarra na h'ada gado da zainab' sbd bata gabana bata birgeni' Aisha ke kadaice a zcyta kinriga kin samu gurin zama kinyi kane kane yadda babu wani gurbi daya rage' Aisha I really love you my eeyshat". " Aisha najin h'aka kara lafewa tai a kirjin zhrdee' shima rungumarta yai da karfi suna kallon juna ido cikin ido". "Hjy da kanta ta shiga kitchen ta hadawa su zainab abin breakfast arish da kwai sai tea Amatullah akace takai masu yya Shamsudee ne zaikata". "gaba daya cikin basket aka zuba sai plast dake dauke da tea tana gama shiri suka nufin g'idan su zainab suna isa a b'akin gate yai parking yace tayi sauri su koma g'ida". " to kawai tace' snn tashige". "tana isa b'akin kofa taganshi b'ude h'akan yabata damar shiga ciki' a parlour ta tsaya tai sallama' tai sallama yakai baki uku amma babu wanda ya amsa mata". " zainab na ciki tanaji sallamar da akeyi amma kofa ta amsa ba lallane taji sbd Akwai nisa tsakani parlour da bedroom". "da Amatullah taji ije kayan tai tajuya zata fita' sbd a cewarta duk lkcn da suka fito zasu gani". " har tasa kafa zata fita ko me tatuno k'uma oho sai takoma da baya mikewa zuwa haryan d'akin zainab tai tana tafe tana sallama har takai b'akin kofa bataji an amsata ba' kamar ta juya saidai ta karisa daidai b'akin kofar tai knocking a sanyaye zainab tace shigo". "duk tunanin Amatullah zahradee na cikine'a tsorace take b'ude kofar' gani abinda takeyi yasa zainab cewa ni kadaice babu kowa snn Amatullah ta karisa ciki". zainab na kwance gani Amatullah hawayene kawai suka zubo masa' da sauri Amatullah ta karisa gun da zainab ke kwance h'ade da cewa lfy zainab meke faruwa?" "zainab ta sake fashewa da kuka tana juyi akan gado' juyin da Amatullah zatayi gani zani dago tai da jini' a tsorace tace lfy zainab meke ruwa?' kuka ya hana zainab mgn". "da sauri Amatullah ta fita zuwa parlour snn ta kira Hjy' Hjy na gani kiran Amatullah da sauri ta daga wayar h'ade da cewa lfy Amatullah?" "cikin gigita Amatullah tace Hjy kizo zainab ce". " me yasameta? " "kizo kawai". " kafin Hjy ta sake wani mgn tuni Amatullah ta kashe wayar ". " hankalin Hjy yai matukar tashi' ko Abba bata kira ba hijab kawai ta dauka tafita batare da tatsaya sanarwa kowa ba". "a guje takejan motar kamar wanda zata tashi sama' bada bata lkc ba ta'isa g'idan' yya Shamsudee dake kofar g'idan gani Hjy yai kawai tai parking da sauri ya fito daga nasa motar h'ade da tambyr lfy Hjy?" "ina zuwa kawai tace snn tashige cikin g'idan' tana shiga da sallama a parlour ta tsaya tana sallama' Amatullah ne ta fito daga daki zuwa parlour tacewa Hjy ta kariso cikin d'akin'". " lfy Amatullah meke faruwa ne h'aka? " "kadai Hjy kariso". " Amatullah na gaba Hjy na baya suka shiga da sallama' karaf idon Hjy sai kan zainab dake kwance salati tai ta sanarwa ubangiji snn ta karisa gun ta h'ade ta tambyar meya faru?". "kuka zainab taci gaba dayi batare da tace komai ba' Hjy na tsaye ta karewa zainab kallon tuni ta gano abinda yafaru' juyawa tai gun Amatullah tace ke!!!" "na'am Hjy" "koma parlour kibani gu". " to Hjy". "bayan fitar Amatullah ne Hjy ta cire hijab ta'ije a gefe tana f'adin sannu zainab kiyi hkr kinji". "kae kawai ta daga". " h'ade da f'adin sannu miko hannu' mikawa tai da taimako Hjy zainab ta tashi ki tsaya mana da'kyau". "cikin kuka zainab tace bazan iya ba". " zaunar da'ita tai akan cushion dake gefe snn ta kwashe zani gadan takai toilet snn ta tsaya ta h'ada ruwan zafi a bawon wanka fitawa tai ta kamowa zainab hannu suka shiga toilet din Hjy tace ta cire zani amma tabar riga". "zainab ta cire zanin har zata zare sket Hjy tace ta barshi kawai basai ta cire sket ba snn tace tsshiga cikin ruwan zafi ta zauna". "zainab nasa kafa jin zafin ruwan da sauri ta cire kafar gani h'aka yasa Hjy kamata ta d'an neta da karfi a cikin ruwan zainab na kuka amma besa Hjy ta kyaleta ba har saida taga ta saki jiki ta zauna da'kyau a ruwan snn tafita ta koma bedroom". " tsayawa tai tai shiru tana tunanin abinda zhrdee ya aikata' wani zanin gadon ta dauko ta shinfida mata snn tasake ciro mata wasu kayan da zatasa' bayan d'an mintoci Hjy ta sake komawa toilet d'in ta tabi ruwan jin ya salance yasa ta h'ada tama na wanka tai wanka snn suka fito Hjy ne ta dauko mata su mai ta shafa ta mike mata kaya tasa snn ta dauki wayar ta kira family doct be bata lkc ba yazo' yana zuwa Hjy tabasu gun da kansa yake tambyar zainab tana bashi amsa snn yace ta kwanta yai dube duben da zaiyi yace ta tashi magunguna kawai ya rubuta yamikawa Hjy takardan magani sukai sallama h'ade da godiya". komawa d'akin Hjy tai da kanta ta dibi abinci a palate takebawa zainab a baki har ta koshi snn Hjy tace ta kwanta ita k'uma zataje ta dawo". "to kawai tace snn ta kwanta". " Hjy na komawa parlour tacewa Amatullah ta jirata tana zuwa". "to Hjy adawo lfy". " amin". "Hjy na fita g'ida ta kowa' ko d'akin ta bata shiga tai bangare Aisha' tana zuwa b'akin kofa tai knocking lkcn zahradee na kwance shida Aisha jin knocking ne yasata tashi ta daura zani a kirji dama shi zhrdee yanada dogwon wadone ko lfy Aisha bata tsaya tasa ba taje ta b'ude kofa h'ade da cewa waye?". " hankadeta gefe Hjy tai snn takarisa cikin d'akin'kadan yarage Aisha ta f'adi kasa' Hjy na shiga fisge bargon da yake rufe dashi tai snn tafara daukeshi da mari". "a gigice ya mike' Aisha na gani h'aka tasa kuka' shako wuyarsa Hjy tai kamar d'an akuya zuwa bangarenta' suna tafe tana tokarisa har suka shige d'akin ta". " suna shiga Hjy tai hurgi dashi gefe' zhrdee na kokarin cewa lfy Hjy.. kafin ya karisa Hjy ta sake daukesa da mari wanda yasa b'akin sa ya fashe sai jini'da sauri ya mike tsaye yana me tare jini da hannu. "gani ya mike ne yasa Hjy sake kai masa tikari tana cewa zakai d'anbe da nine?" shiru yai ya zuba mata ido duk dukan da take kaimasa be tanka ba". "gani ya tsaya a tsaye ne yasata kwashe masa kafa ya zube a kasa gwiwa bibbiyu a gaban ta' suna cikin h'aka ne amaturahaman ta shigo' gani b'akin zhrdee da jini Hjy k'uma bata dai na shake dashi tamkar mahaikaciya yasa amatulrahaman fashewa da kuka tana kira nashiga uku' hannu tasa tana kokarin cirewa Hjy hannu a wiyar yya zhrdee amma ta kasa". " gani h'aka ihu tasa ta fita a guje zuwa d'akin su waya ta dauka ta kira Abba' Abba yana gani kiranta da sauri ya daga sbd yasa ba kasafai take kiran mutum ba sai da dalili dalilinma me karfi". "yana dagawa cikin kuka take cewa Dan Allah Abba kazo g'ida yanzu nan wlh Hjy ce". "a gigice Abba yace meya samu Hjy" "ita da Yy ne". "Abba be tsaya ta karisa ba ya katse wayar h'ade da daukar key d'in mota ya kamo hanyar g'ida". "a guje yake driving sbd yasan halin Hjy sarai akan yara' tun suna kananu idan ta kamasu batayi masu da wasa' sai ka tosaya masu' h'aka har girmansu be hanata dukan su". " sbd halittan Hjy ne macce ce me zafi akan yara' har gara Abba dayake namiji idan suyi laifi ya hukutasu da ace Hjy ne". "zhrdee na duke gaban Hjy' Hjy na f'adin yadda ka fitar mata da jini kaima saina fitar maka dashi". " idonu zhrdee duk sun fito waje sbd azaba wiyarsa yai jazur sbd shaka abinka da farin mutu da zaran ya b'ude zaiyi mgn sai Hjy ta nushesa a b'akin suna cikin h'aka amaturahaman ta sake shigowa dukawa tai gaban Hjy tana kuka tana rokon Hjy da ta kyale zhrdee' amma ina mikewa tai tasake meda hannu tana kokarin cirewa Hjy hannu a wiyar zhrdee". "gani h'aka yasa Hjy tokareta ta f'adi can gefe mikewa tai taci gaba da kuka tana rokon Hjy saiga Abba ya shigo' a guje ta mike ta tarosa Abba na gani mugun aikin da Hjy zatayi da sauri ya karisa guta shima hannu yasa yana kokarin ceto zhrdee". "da yaga batada niya cire hannunsa yai snn yace Laila". "cikin zafin rai tace na'am". " kinsan tunda nake dake bamu taba samu tsala bako? ". " shiru Hjy tai". "to idan ba so kike mu bataba ki sakanmi yarona". " jin h'aka yasa jikin Hjy sanyi". "nace ki sakanmi yarina ko?". " cikin fushi Hjy ta saki zhrdee h'ade da tokarinsa ya f'adi can gefe' da sauri Abba yasa hannu ya dagosa suka fita zuwa d'akin abban". "b'akin gado Hjy ta zauna tana faman hakki' gani h'aka yasa amatulrhaman b'ude frg ta dibo mata ruwan sanyi ta mika mata snn tafita tabar d'akin". "suna shiga Abba yake tambyar son abinda ya hadashi da Hjy' shiru son yai idan banda hakki babu abinda yakeyi". " Abba yai tambaya har yagaji amma babu am'an". "gani h'aka sai Abba yace son ya zauna bari shi yaje b'akin Hjy da kansa ya tambyeta". " Abba na fita d'akin Hjy yashige'itama tana ganisa ta gyara zama yazo ya zauna kusa da'ita' saida yai gyaran murya snn ya fara da cewa h'aba Hjy a gskya banji dadin abinda kika aikata ba' ke baki gudun abin Allah ya kiyaye wani abu ya faru' kibar gani kece kika haifesa wlh hukuma batabar kowa ba' mafi yawanci lkt nasha f'adi maki kidaina hukunci cikin fushi' sbd na lura dake a duk lkcn da kikai fushi baki iya controlling zcyrki kina iya aikata komai".. "himm' Alhj kenan kana wnn mgnr d'an bakasan abinda zhrdee ya aikata neba yasa h'aka".. " to menene shi son d'in nawa ya aikata ne da har za'a kasa irin wnn hukunci?". "a nan Hjy ta zane komai ta sanar masa". " salati Abba yasa da salallami a fusace ya fita daga d'akin Hjy zuwa d'akin sa' yana shiga zhrdee ya daga ido yana kallon Abba' cikin fushi Abba yake mgn". "a gskya zhrdee baka kyauta ba k'uma kaban mmki sbd Allah yanzu irin walakanci da zakaiwa yar'mutani kenan? kenan idan akaiwa naka kanni zakaji dadi? idan ma kana gani hadaran nima maka auranta aikai bakai ka nima ba to bari kaji wlh3 babu saki a tsakanisu". "idan k'uma kana gadaran d'an kana da wata matar ne to wlh sauna haramta maka ita na har naga yadda zakai' idan h'aka tun kafin raina ya baci maza kaje ka daukota zuwa hospital' k'uma kai da kanka zakai jinyanta babu wanda zai tayaka har ta warke". "wlh zhrdee daraja daya kaci inda badan kai ne ba da wani ne daga cikin yar'uwanka wlh da sai nayi mummunar saba masa' amma ko kai d'in ma ka kiyayi fushi' d'an h'aka maza kaje ka dauketa sutafi hospital ka tabbatar anbata kyakkyawar kulawa". " to kawai zhrdee yace h'ade mikewa har yakai b'akin kofa Abba yace son". "na'am Abba". "kasan duk hanyar da zakabi kabi idan gani ka lallasheta h'ade da bata hakuri' k'uma koda wasa koda wasa banaso g'idan su suji wnn labarin' kana jiko kuwa". 'naji k'uma zankiyaye". " Allah yasa". "amin". " zhrdee yana komawa daki gani Aisha yai tayi kuka har tagaji' itama tana ganisa da sauri ta rungumesa tana kuka' shima rungumarta yai h'ade da lallashinta". "gani jini a b'akin sa yasata tambyar laifin me yaiwa Hjy da yasa ta fusata tai masa h'aka". "wlh wani laifine yai mata". " shine tai maka h'aka?". "eh h'aka take idan ranta ya baci abinda yafi h'aka ma zatayi". "kaee fa😳 " himm ni zanfita".. "ina zaka a h'aka k'uma?". " Hjy ce ta aikeni". "ina?". "nan ne babu nisa' k'uma ba lalla bane nadawo yau". "sai yaushe k'uma". " saidai na dawo kawai". "Aisha bari naje saina dawo". "Allah ya dawo dakai lfy". " amin' kikulamin da kanki". "riga yasa h'ade da daukar key d'in motarsa ya fita' kai tsaye g'ida ya nufa' yana shiga Amatullah ya gani a parlour tana kwance kan three ster tana game da wayarta' ganisa ne yasata mikewa h'ade da sannu da zuwa yaya". "yau sannunki' ina zainab d'in ne?" "tana ciki". " OK kawai yace ya karisa ciki d'akin". "yana shiga gani zainab yai kwance kan gado ido rufe kamar mai bcc amma ba bcc take yiba' karisawa yai b'akin gadon h'ade da kiran sunata Zainab zainab tana jinsa amma bata b'ude ido ba' gani h'aka hannu yasa yana bubuga pilo a hankali take hide ido' bayan ta b'ude ne suna h'ada ido da sauri ta juya masa baya h'ade tsaki". "zhrdee yace tashi muje hospital' zainab tai shiru' dake fa nakeyi zainab". " gani yai mgn har baki uku bata amsa shiba daga snn besake mgn ba juyawa yai ya dauko kyalenta ya daura a wiyarsa snn yasa hannu ya ciccibeta kamar jijira yafita". "zainab na shire-shiren saiya dauketa amma yaki' Amatullah na gani zhrdee dauke da zainab da sauri ta mike had a da cewa yya lfy?". "cewa kawai yai zo ki b'ude min kofa". "Amatullah na b'ude masa kofa yafita zuwa motar' ita k'uma tsayawa tai galala tana kallon su kamar sakarai". "saida ya dauketa snn ya b'ude mota ya sata' yana cire hannu zainab na yunkurin fita". " yace wlh idan kika fita tsiya zanmaki". "duk abinda zhrdee keyi fuskansa daure babu alamar dariya ko wasa a tattare dashi". "h'akan yasata zama tai shiru' shikuma ya zaga ya shiga mota' zainab na gani yashigo mota ta dauke kanta' shima be kulata ba yaja mota suka nufi hospital". "suna isa bayan ya fito zaga yowa yai ya b'ude mata motar h'ade da cewa Dan Allah malama ki fito' wani irin mugun kallo tai masa snn ta juye ta zuba kafar waje snn takamo murfin motar da karfi ta mike". "tana fita zahradee ya matsa gefe ta fita ya rufe motar snn ya zaga ya sawa motar key ya zagaye ko kallonta beyiba yace idan kinga dama ki biyoni". "bata tanka masa ba a hankali take jan kafar tana binsa' yana gaba tana baya' suna cikin tashiya wata mata d'an ma daidaiciya tafito daga cikin wani daki gani yadda zainab kejan kafar har ta shigesu sai ta juya da sauri h'ade da cewa kae yaro kae yaro". " kamar zahradee bazai juya ba jin takara kiran nasa ne yasashi juyowa yana dubanta batare da ya amsa ba' ido kawai ya zuba mata". "tace Dan Allah ka taimaka mata nama' baka gani yanayin jikin nata ne?". "tsaki yai cikin zcyrsa snn yasa hannu ya kamo mata nata hannu suka' matar tace yawwa ko kai fa". "Allah ya kara lfy". *" amin ngd ". " suna shiga gun doct da kansa ya kamata ta zauna snn shima ya zauna' doct yake tanbyr abinda yake tafe dasu". "cikin kunya zhrdee yake bayani' murmushi kawai doct yai snn yace pls two minute zandubata". " OK kawai yace snn yafita". "doct yai dube dube da zaiyi snn yace wa zhrdee ya shigo' bayan ya shigo ne doct yai masa bayanin da zai masa snn ya rubuta masa mgn". " sukai sallama' da kansa ya dauketa cak zuwa mota saita yasata ciki ta zauna snn ya zagayo ya shiga suka koma g'ida' h'aka ma suna shiga yasake daukar zuwa cikin' Amatullah dake zauna a parlour tai masu sannu da zuwa". "yawwa yace h'ade da shigewa cikin daki ya shinfidata bayan ta kwanta ne yaje ya dibo mata ruwa ya'ije h'ade da ledar magani akan side dirowa dake gefen gadon batare da yai mata mgn ba ya fita zuwa parlour". " yana zuwa parlour yacewa Amatullah taje g'ida saiyazo". "batare da musu ba ta dauki kyalenta sukai sallama" bayan ta fitane ya zauna akan cushion yai shiru tunani kala2 yakeyi yadda zaiyi da zainab". "bayan zhrdee ya fita ne zainab ta mike ta dauki magugunarta tasha snn ta koma ta kwanta". "Amatullah na isa g'ida sukai karo da Abba zaikoma kasuwa' Amatullah tace sannu Abba". " yawwa sannu Amatullah ya mejikin?' "jiki da sauki". " eh su dawo shiyasa ma nadawo g'ida'". "ina shi yyn naki?" "na barsa a g'ida'shine ma yace nadawo g'ida h'aka". " himm Amatullah kenan komawa zakiyi inaso kika zauna dasu zuwa d'an wani lkc' kinji?". "to babu damuwa Abba' bari na shiga ciki na dauko kayana". " to yimaza sbd saina saukeki snn na karisa kasuwa". "a gurguje Amatullah tashiga ciki koda Hjy taga tana diban kaya ta tambyeta Amatullah ta sanar da'ita yadda sukai da Abba' Hjy bata musa ba sbd h'akan ma yai mata dadi' sbd koba komai ta h'akan ne zasu samu wasu labaran abinda ke tafiya". " zhrdee tana kwance Amatullah tai sallama ta shiga ciki' ganita da jakar kaya yasashi tambyar lfy?". "Abba ne yace nadawo nan sbd na tayaku aiki". " himm kawai yace h'ade da nuna mata extra room da yake kwana' Amatullah tana ije jakar ta fito' zhrdee yace jeki kitchen ki mana abinci". "to tace snn ta shige". "Amatullah na gama abinci ta h'ada masu gu daya takai masu dinning' zhrdee ya rasa yadda zainyi sbd bazata iya fitowa ba dole yasashi tafiya d'akin ya kamota zuwa dinning ya zaunar da'ita' Amatullah ne ta zuba masu snn ta zuba nata sukaci". "kadan kawai zainab tace takoshi' bayan su gama ne ya dauketa ya medata d'akin ta kwanta". "da dare kuwa zhrdee ya rasa yadda zaiyi sbd yau Akwai Amatullah a g'idan babu damar raba daki' a dole d'akin zainab yaje kwanciya amma kowa ya juyawa d'an uwarsa baya'babu wanda yake tanka wa d'an uwarsa". "zainab da mugun bcc cikin dare ta dauki hannu ta dorawa zahradee a jiki' da sauri ya care can anjima ta sake kwashe kafa ta dora masa akan cinyoyinsa". "a lkcn bcc yariga ya k'uma shi' koda zaifalka gani kafar zainab yai a dore akan cinyarsa' da sauri yasake cirewa h'ade da tsaki". " itama tsaki tai suka sake juyawa junansu baya" bcc na sake daukar su taci gaba daga inda ta tsaya' gani h'aka dauka yai yabar gadon ya koma kan cushion". ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES. F.O.W.☘. 🌳impacting valuable knowledge and entaetaiment is our concern.🌳 story written by Mmn uswan☘ ina taya yar'uwata ummusulaimi marubuciyar TA AUREN MIJI murnan kammala Nvl dinta ubangiji Allah yabada ladan abinda kika koyar a ciki' kuskuren da kika samu Allah ya yafe mana bakin daya' Allah ya kara hazaka da zakin hannu😅 🌳🌳🌳🌳🌳🌳 a gskya fans bazan boye maku ba wlh har ga Allah banajin dadin rashin gani comment din ku' comment din ku shike kara mana kargin gwiwa' k'uma banason gani wani tnx comment kawai nake bukatar sbd kowani marubuci yana bukatar comment shike kara mana karfin gwiwa. ngd saina jiku👂👂 😄🤝 🌳🌳🌳🌳🌳🌳 where are you aminci 1-2 and Mmn uswan grp ranka cakal this page is for you, gskya kuna kokari wajan comment dan kune zankarisa shi inda badan kuba dana barsa h'aka ngd sosai Allah yabar kauna da zumuci🤝😅 and you home of Hausa novel long life a gskya baki ko labba basu da kalmomin godiya a gareku sai dai kawai nace ngd da k'aunarku gareni Allah yabar zumuci amin. 3⃣5⃣ "gani zhrdee ya sauka ya bar mata gado b'ude kafa tai ta barbaje' yana kallonta yai tsami yaci gaba da bccnsa". "da asuba babu yadda zhrdee beyi da zainab ba akan tai tafiya amma taki' da taga yanace saitai tafiya tasa kuka' gani kukan da taikeyi yakara jin haushinta'dole yasashi daukarta zuwa toilet tai alwala tana gamawa yasake daukarta zuwa bedroom ya shinfida sallaya h'ade da hurga mata hijab snn yaje yai nasa alwala yazo suka jera sukai sallah". "da safe duk da tasamu sauki amma taki nuna masa saima wani kara narkewa da tai' Amatullah nece da h'ada masu abin breakfast takai dinning' gani zainab bata fitoba yasa Amatullah cewa yya kodai za'a bita dashi ne d'akin?" "shiru yai be tanka ba' saida Amatullah takara mgn snn yace eh to". "dibawa tai cikin plate snn ta h'ada tea ta dauka har ta kami hanya zhrdee yace kaho nakai mata". " to yya'tunda h'aka ne bari kawai na h'ada maku a tre kuje kukarya tare". "cikin zafin mana ta h'ada kayan gu daya ta mika masa ya amsa ya shige ciki' zainab na kwance zhrdee yashigo tana gani shigowarsa da sauri ta rufe ido kamar mai bcc". "ijewa yai a gefe snn ya dauki nasa yakoma kan cushion yaci gaba dasha' zainab na kallon sa ta juya masa baya' shima yana gani h'aka yace idan kinga dama kitashi ki karya". " har yagare zainab bata tashiba' banason iskanci da rainin hankali malama idan zaki tashi ki tashi nasan ba bcc kikeyi ba". "snn zainab ta mike or ready yariga ya h'ada mata nata tea d'in dauka kawai tai tasha' tana gama sha tace zoka dauka na gama' saida zhrdee ya galla mata uban harara snn yace da uban wa kikeyi". " batare da ta tankashi ba komawa tai cikin bargon ta kwanta h'ade dajan bargon ta rufe". "mikewa yai ya dauki tre d'in yafita dashi yana fita zainab ta kwashe masa da dariya' jin tafiyarsa yana dawowa yasata komawa cikin bargon ta rufe' shima yana shiga bebi ta kanta ba toilet ya shige yai wanka ya shirya yafice zuwa g'idan su Hjy". " kayan da yacire hurhugawa yai kota ko'ina a d'akin harda towel d'in daya goge jiki dashi yafita yai tafi yarasa ". "yana fita zainab ta fito parlour gun Amatullah suka zauna suka hiransu duk da tana matsayin matar yayanta amma be hana ta bata girmanta ba tunda tasan ba sa'ata bace' h'aka sukaci gaba da hiransu kowa nabawa kowa nasa girman". "zhrdee yana shiga d'akin Abba yafara shiga suka gaisa snn yai d'akin Hjy itama suka gaisa h'ade da tambyar mai jiki". " tasamu sauki ". " Allah ya kara sauki". "amin' snn ya mike zuwa d'akin Aisha har ya dora hannu a kofar zai tura kenan saiga Abba da sauri Abba yace ina zaka?" "zanduba kwana Aisha ne". " lfy ke buya kasan inda ba lfy da musanar dakai' ita muna tare juya ka koma gun dayar matarka ita da batada kowa". "amm' Abba". " amma me kajuya kawai ka koma banason musu'". "shikenan Abba". " har zhrdee ya juya Abba yace son". "na'am Abba". "na haramta maka zuwa g'idan nan har bayan sati biyu k'uma ko a kasuwa banason ganika". "himm kawai yace snn yafita". "shima Abba d'akin Hjy yashige' Ashe duk mgnr da zhrdee keyi da Abba Aisha na makale jikin kofa tanaji" wani irin bakin ciki yai kulu2 ya tokare Aisha a zcy zama tai bakin gado tana ajiyar zcy". "su zainab suna cikin hira jin shigowar zhrdee yasata mikewa a guje tabar parlour zuwa daki' Amatullah dake zaune kusa da'ita har tsroro ya kamata sbd gani zainab kawai tai tasa gudu amma ita bataga abin gudu ba' tana cikin h'akan kenan zhrdee yai sallama ya shigo". "a lkcne tagano abinda zainab kewa gudu' murmushi kawai tai h'ade da snn da zuwa' be karasa ciki ba a parlour ya zauna sukaci gaba da hiran da Amatullah". "zainab na daki duk mgnr da sukeyi a kunita amma taki fitowa' h'aka sukaci gaba da zama har tsawo sati biyun zainab bata muna masa ta warke ba' duk da kwanciayar da sukeyi a gu daya amma babu wani abinda ya shiga tsakanisu' dan shi zhrdee d'in ma kusan kwana yakeyi suna chat da Aisha' da zainab ta gano h'aka idan taga dare yai sai taki bcc koda yai mata mgn bata kulashi ba yai mgn har ya gaji' gani bazata tanka masa ba" ije wayar yai ya kwanta". "tunda daga lkcn zainab tasawa zahradee ido ga duk chat ko kiye-kiyen wayar da yakeyi da Aisha' babu arziki yabar shima ya bari ne badan yanajin tsoranta ba aa sai dan gudun kada su abba suji yana waya da Aisha k'uma yana g'idan zainab". "da h'aka sukaci gaba da maza koda a kuskure zhrdee baya yadda koda hannu zainab ne ya taba' idan ma suna kwance da ya lura tanada mugun bcc pilo yake sawa a tsakiya ya jeresu a cewarsa yayi katanga kenan a tsakanisu' duk da h'aka baya hana zainab mugun bccn ta kwashi kafa ta zuba masa' wasu lokutan k'uma da gangan takeyi sbd ya sauka ya bar mata gadon". " gashi zhrdee ya tsani kwanan cushion ko kasa' a duk ranar daya kwana a cushion a takure yake sbd baya samun bcc kirki' ranar da k'uma yaga bazai iya ba dole a cushion zai kwana". "gani h'aka yasashi yanke sharawa sbd yagaji da abinda take masa cikin dare' shiyasa yakekai 12AM a parlour a cewarsa yai kallon yakeyi' itama Amatullah d'in da take tambyarsa shigewa takeyi ta barsa a gun". "yau ko da abu ya isheta allura ya samo ya ije saidai kansa ya coka a katifa ta kasa ya kwanta kamar me bcc' duk a tunanin zainab bcc ne yai sbd taga yadda ya barbaje ya b'ude kafa' saida ta kare kasa kallon snn a zcyrta tana f'adin dan so banza a tunaninka kaga gadon banza bari ka kashe ko to wlh mata kika zanyi". "hayawa gadon tai saida tabashi mini goma zuwa ashirin a hankali ta b'ude ido ta lekesa ta gadai kamar bcc yakeyi' shima a lkcn rufe ido yai yana kiran ta zuba masa kafa". " gani idonsa rufe yasa zainab murmushi keta a hankali ta fara birgima snn kwashi kafa dukka biyu ta zuba masa a fuska' shima zhrdee dake kwance murmushi yai snn yasa hannu ya hankali ya zaro allurana ya coka mata a saidai cinyarta da karfi ya danna". "ihu zainab tasa tana kiran wayyo Allah na' nashiga uku' kunama wlh Akwai kunama a gadon nan'ihu da takeyi ne yasa zhrdee kuna light d'in d'akin' zani da zainab ke daure dashi babu arziki ta kwance ta f'adi kasa tana birgiman kunama". " kallo daya zhrdee yaiwa zainab shi kansa besan lkcn daya kwashe da dariya ba' dariya sosae yakeyi harda kwalla' zainab dake kuka tsayawa tai tana kallonsa". "saida yai dariya sosae snn ya matse h'ade da cewa muguwa kawai mutum najin bcc kihanashi sbd zalinci kihanashi' babu wani kulana a d'akin ga nine nan na soka maki allura' wlh gobema idan kika sake sainayi maki wanda yafi h'aka". " cikin kuka zainab tace Allah ya'isa mugu aszalumi kawai ma cici wlh ban yafe makaba sai Allah ya sakemi". "yimi shiru ke Allah kika sani muguwa kawai sbd ke inaji ina gani aka hanani zuwa gano masoyiyata abin kauna ta abin alfaharina farin cikina". " himm zhrdee kenan aini ban yarda Aisha na sokaba' tunda har tagujeka duk da irin hanlincin da kai mata amma dayake butulune ita ta gujeka taje ta auri wani' saida yagaji da'ita ya korota tuku ta dawo gareka' koba komai a ragowa kasameta' amma shine har kake da bakin kiranta masoyiyarka". "eh dai wai kema tuku na tambyeki". " ina sauraranka". "kinsan me ake kira soyayya kuwa". " bansani saikai". "shiyasa inda kinsan abinda ake kira soyayya wlh bazaki f'ada h'aka ba". " oho dai a banza". "kece kigaka oho tunda akai maki auren cushe". "kae kae kae lallama zhrdee nice kake kira da cushe". "an kiraki d'in' ko kaeyane? wlh zainab idan banda darajan su Abbana babu abinda zaisa na zauna dake wawiya kawai". "Allah sarki rayuwa wlh zhrdee idan banda darajan iyaye wlh nima kaina babu abinda zanyi dakai' sbd a cikin tsarin samarina wlh babu wawa dolo da kiki marajan mgnr iyayensa irinka". " ke zainab wlh idan baki iyawa bakinkiba wlh saina fasashi". "wawiya kawai banza kucaka' wlh shiyasa tun farko banso aurena dake ba"... "Allah sarki zhrdee wlh bazan taba gani laifinkaba sbd nasan bakomai ke damuka ba face dakikanci da toshewar basira' kai yaune kafara nadamar aure' ni k'uma tun ranar da na daga ido naga Kaine a matsayin mijina nake nadama". "wohohoo Allah sarki Aliyu masoyina abinda kaunata abin alfaharina mejin mgnr iyayensa' nasan inda Aliyu masoyinane bazaimi h'aka ba". "Aliyu banza Aliyu wofi ke uban uban Aliyu ma na rantse da Allah zainab koda wasa nasake jin suna wani Aliyu anan g'idan wlh saina karyaki snn naje naci ubansa shege mai nima matan mutuni". " oho kai dai kasani domin babu wanda zai hanani kiran suna rabin raina"... "kafin ta karisa kiran Aliyu tsalle zhrdee yai zaikamota". "da sauri zainab ta kauce" duk da h'aka binta yaci gaba dayi' gani h'aka yasa zainab gudu suna zagaje d'akin' dakar yasamu ya kamata saidai ya danneta snn yasa hannu ya matse mata baki" jin zafin h'akan yasa zainab kuka' dakar ya saketa h'ade da cewa wlh koda wasa idan nasakejin suna banza kazamin nan wlh saina maki wanda yafi h'aka". "koda ta mike bata tankasa ba kowa yaje yai kwanciyarsa". "tun daga lkcn kowa ya kami kansa babu ruwan wani da wani' amma a zcyr zhrdee kuddun yatuna da mgnr Aliyu da zainab take f'adi saidai yai d'an karami tsaki kawai' shida kansa mafi yawanci lokaci yakan zainab ya tambyi kansa meyasa yake damu kansa akan wani banza wanda bemasan dashi ba". " me nene hadinsa da zainab ma tuku banle har wani mgnr Aliyu ya damesa' tsaki kawai yai h'ade da juya mata baya". "gani yau tsawon kwana bakwai kenan zhrdee bezo guntaba ranta yai mummunar baci tun safe take daki yau ko lekowa da takeyi ta shiga bangaren su Hjy bataje ba kwanciya kawai tai tana f'adin juyi a gado". " shima zhrdee yake yawan kiranta ko char ya rage ba kamar da' ba". "shima zhrdee ya rage kiran Aisha ne ba d'an komai ba sbd idan yanadaina jin muryanta maybe sha'awarta zai ragu masa' a nasa tunanin h'akan shine mafi saukin a garesa". ~~~ ~~~~ ~~~~ "Nasir ya samu sauki garau gani saukin daya samune yasashi daukar Fatima zuwa sauran kasashen duniya hutawa' Fatima da Nasir suyi yawo sosae' Nasir gani yasamu sauki yacewa Fatima yanaso yadawo g'ida sbd yana bukatar gani su Khadijat da Jabeer' Fatima bata musa masaba h'akan ne yasa sukasa ranar dawowa g'ida Nigeria amma sai sun koma eygip Nasir ya amshi maganinsa". "sbd uzirawa da Nasir yai yana bukatar gani yaransa a ranar sukabar India zuwa Egypt bayan su isa Nasir besamu gani doct d'an sa a narar ba dole yasa suka kwana badan Nasir yasoba' sbd a yadda yaso komai dare yau yaransa yakeson gani". "amma tunda yaji cewa bazasu samu komawa a lkcn dayaso ba cewa kawai yai Allah yasa h'aka yafi alkairi' amma saida yakira g'ida sukai mgn dasu Khadijat da Jabeer h'ade da cewa gobe yananan zuwa". "su Khadijat da Jabeer sunata murnar zuwan bbnsu' Fatima da Nasir sun kwanta lfy klau amma da safe Nasir babu kafa babu hannu gashi yanason mgn babu hali". "da sauri Fatima tai rushing d'in zuwa hospital' doct duk sukai kansa suyi iya kokarinsu akan Nasir amma ina kafin wani lkcn Nasir ya cika". "Fatima tai kuka kamar zatai hauka har riketa akeyi bayan tasamu d'an natsowane snn takira g'ida Nigeria ta sanar' a ranar yayin Nasir suka tafi Egypt duk cuku-cukun da zasuyi suyi amma basu samu fitowa da gawan Nasir ba sai da yai kwana biyu snn suka iso g'ida Nigeria' ba'a bata lkc ba aka shiryashi yadda addini ta umarcemu da muyi aka kaisa ma kwancinsa". "bilyaminu da Fatima suyi kuka kamar ba gobe' bayan addu'ar uku bilyaminu yace zai koma binni kebbi yadawo sbd Akwai abubuwan da yakeso ya h'ade su snn yadawo". " Fatima tace babu damuwa Allah ya kaika lfy' da yamma Bbn Fatima yace takoma g'ida tai takaba Bbn Nasir yace a'a d'an Allah ina rokon arziki kabatar ta zauna a d'akin ta idan yaso bayan tafita takaba saita koma g'ida ". " Bbn Fatima yace shibazaice komai ba sai abinda tace' koda aka kira Fatima abbanta da kansa ya tambyeta tazabi inda zata zauna' Fatima tace abazarta anan kawai zuwa wani lkc". "abban Nasir yaji dadin h'akan sosae' abban Fatima yace to shikenan Allah ya jikan Nasir' anan g'ida Fatima ta zauna daya daga cikin dakuna na g'idan two bedroom plat aka bata ita da yara suka zaune". ~~~ ~~~~ ~~~~ "bayan wata daya Dan bikin su zainab da zhrdee' tun cikin dare zainab take amai' ko rintsawa batai ba' shikuma zahradee beyi tunani kaita hospital ba h'aka ya tsirya ya tafi kasuwa' bayan fitarsa ne jikin zainab yaki dole yasa ta rarrafo ta fito parlour gun Amatullah ganita h'aka yasa Amatullah tsorata kuka kawai zainab keyi a take Amatullah ta kira yyanta' koda ya dauka ta sanar dashi tsaki kawai yai yaci gaba da harkokinsa'". "gani beda niyar zuwa yasata kiran Hjy ta sanar da'ita' batare da bata lkc ba Hjy ta kira zhrdee ta sanar masa' yana guguni ya dauki key d'in mota ya shiga zuwa g'ida' yana shiga a parlour ya samesu daure fuska yai h'ade da cewa Dan Allah kitashi muje' Amatullah ne ta dauko mata mayafi koda ta mike kara jirine ya dibeta zata f'adi da sauri zhrdee ya tarota suka fita zuwa mota' zhrdee yana driving yana mata masifa har suka kai' suna isa kallo daya doct yai mata yace aje a gwadata nurse na gwada zainab ciki tagani na satika". "koda doct ya sanarwa zhrdee' zhrdee yai mmki sosae dajin wnn labarin' a gani yadda zainab takeji yasa doct rikesu aka basu gado' ana sa mata drip kenan saiga Hjy ta shigo d'akin' a ladabce zhrdee ya gaidata sbd yau ba a g'idan ya kwana ba". " bayan su gaisa ne Hjy take tambyar jikin zainab' mika mata result d'an yai kawai da sauri yafita yabar d'akin". "Hjy na karantawa murna sosae tai h'ade da kiran Abba ta sanar masa' shima Abba yai murna h'ade da cewa yana zuwa' lekawa Hjy tai tacewa zhrdee yaje g'ida ya dauko masu ruwan zafi da kayan tea'". "to kawai yace yanufi g'ida' ko kafin ya'isa g'ida Hjy tai kira amatulrahman tace tasa masu ruwan zafi kafin zhrdee ys'iso g'ida". "amatulrahman tace Hjy ya mai jiki amma da sauki ko?" "cikin murna Hjy tace da sauri Ashe cikine da'ita". " cikin murna tace ciki?". "eh wlh". " lalla kam Ashe mukusa samu yaro'. "Ashe duk mgnr da sukeyi a kuni Aisha ne' da sauri ta koma d'akin ta tasa kuka tana f'adin nashiga uku"..saiga zhrdee ya shigo da sallama gani Aisha na kuka yasa zhrdee karisa wa da sauri h'ade da tambyar lfy?" "Aisha tai banza dashi gani h'ade yasa zhrdee sa hannu zai rungumeta cikin fushi Aisha ta ingijeshi h'ade da cewa mana fiki algugumi ma yau dari mai baki biyu kawai' abinda zai hana ganika a wuta saidai guma gumai makanashinsa amma ana tonewa Kaine a can karkashi kanaci da wuta".. " h'aba Aisha kinsan dawa kikeyi kuwa? ' ninefa zhrdee d'an ki... "kwarai da gske kaine fa zhrdee d'an akuya..kafin ta karisa ya dauketa da mari' jin zafin marin yasa Aisha cewa Allah ya'isa mugu d'an tunkiya.. " daga nan fa zhrdee ya h'au dukan Aisha inda yashiga banan yake fita ba' tayi kokarin gudu amma ina sbd yariga ya rufe kofa' saida yai mata duka Iya son ransa snn yafita ya barta kwance tana kuka". 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳impacing valuable knowledge and entertaiment is our concern🌳 story written by Mmn uswan ★kae kae kae lalla a gskya Aisha kinada masoya da yawa,sbd naga kowa a bayan ki yake amma k'uma fa🙄.. Akwai lauje cikin nadi, sbd zhrdee bayason bacin ran Aisha h'akan yasa ya kasa sanar Aisha mgnr auren sa snn km ya f'adin mata betaba saduwa da zainab ba, meyasa Aisha ta auri Nasir? tajuyawa zhrdee baya a lkcn da yake mararinta, km meyasa iyayen Aisha suka boyewa iyayen zhrdee matsalar rashin haihuwan Aisha, meyasa iyayen zhrdee suke nunawa Aisha halin ko ikula?★ ★fans masoya littafin aure ibada ne a gskya naji dadin comment diku wann page din rankacakal nakune danku nayisa Allah yabar kauna da zumuci😅🤝 sai mu hadu a page na gaba dan gani yadda zata kaya tsakani zainab, aishan da k'uma zhrdee including their parents tnx alot fans😋. 3⃣6⃣ "zhrdee yana fita kitchen ya shiga ya dauki plast zuwa hospital' da Aisha ta gaji da kukanta ta tashi da shiga toilet tai wanka h'ade da alwala sbd lkcn nafara kiraye kirayen sallah' tana idarwa hawa gado tai ta kwanta h'ade da tunanin makomanta a gun iyayen zhrdee". "zhrdee yana komawa hospital daidai lkcn Abba ya'iso suka shiga d'akin da zainab lkcn tana bcc, Hjy na gani Abba ya shiga ta mike h'ade da tura masa kujera Abba ya zauna snn ya tambyi mai jiki". "Hjy ce ke amsawa snn ta mika masa result' zhrdee na gani Abba ya amshi result d'in da sauri yabar d'akin ya fita' Abba ya karantawa murna ya kamashi baki har kunni yana f'adin kinga ikon Allah ko Hjy". "wlh kuwa Alhj rabo kenan". " b'ude ido zainab ne yasashi shiru". "da sauri Hjy ta karisa gun gadon h'ade da cewa sannu zainab' yana jikin?" "naji sauri". " Allah ya kara sauki' ko kina bukatar wani abu?" "a'a" "to shikenan". "Ina.. " shigowar su Amatullah d'akin NE ya hanata karisawa'. "madam din mu kenan mmn twins' ya jiki?". " zainab na mmki Mmn twins da Amatullah tace mata' a zcyt tana tambyar kanta kardai ace ciki ne dani? amma da zhrdee ya cucrni idan ciki ne dani". "Abba dake zaune yace zainab yaya jikin". "da sauki Abba". "Allah ya kara sauki". "min ngd". " mikewa Abba yai yaje gunda son ke zaune' zhrdee na gani Abba da sauri ya mike tsaye h'ade da cewa har kafito Abba?" "na fito son". " son ya maijikin?". "jiki da sauki Abba' son meyasa tunda kaga batada lfy baka kawota hospital ba har saida Amatullah ta kira Hjy Hjy tazo ta dauketa zuwa hospital?" sbd Allah inda yar'uwanta suka shigo suka ganta a wnn hali kasan bazasu dadi bako?". "nifa bansan batada lfy ba Abba". "wani irin mgn kakeyi h'aka son' kodai ba'a g'idan ka kwana ba?". "a g'idan na kwana mana Abba". "to kace bakasan batada lfy ba?". "eh' ina nufin bayan fitanane cuwon ya sameta". "OK to amma yanzu kasan tanada juna biyu ko?". " shiru zhrdee yai be tanka ba' son kana jina kuwa?" himm Abba ya mgnr kayan da mukai' k'uma yaushe sukace kayan zai iso?". "murmushi kawai Abba yai sbd yagano son kaucewa kawai yai' amma idan mgnr kayane ai suriga da suyi". "gani h'aka yasa Abba besake mgnr ba snn yace son zankoma kasuwa". " to Abba sainazo". "har wajan mota zhrdee ya raka Abba' bayan tafiyar Abba ne zhrdee ya samu gun ya zauna yana tunanin abinda yasa ya duki Aisha' to amma k'uma mezaisa bazan dauketa ba? iyayena fa ta zaga' wanda ko'a mafarki bantaba tunanin zatai mi h'aka ba' kash dana sanima da banduketa ba' kodai nakoma g'ida yanzu na bata h'aka ne? k'uma wani harzari ba gudu kada naje yanzu tasan bata huce garin bata hakuri muzo musake wani f'adan". "nasan ma ba lalla bane ta sairareni' kash nima nayi saurin hannu wlh da nasani banyiba' gashi nabar key d'in mota a dakin nasan yanzu idan naje dauka sai Hjy ta tambayi ina zani' kodai nace mata kasuwa ne zanje? k'uma idan nace nabari har sai gobe girkinta bansan hali da take ciki". "zhrdee ya karisa mgnr ne h'ade da mikewa zuwa d'akin'' Hjy na zaune kusa da zainab ya shigo h'ade da cewa ya jikin nata?" "jiki da sauri". " har yanzu bcc takeyi ne? ". "eh" wlh". "amma doct yazo ya sake dubata yace babu komai ko?". "eh suce babu komai' allurai da akai matane yasata bcc h'aka". " OK ni Hjy zanje na dawo?". "inda k'uma zaka bayan kanada mara lfy?" "wlh Hjy duwowar da nake zuba kudine a kasuwa na mance na barsa a b'ude k'uma duk cinikin da akai suna ciki ba'akai bank ba shine zanje na ciro key d'in". " ahh!! lalla kam hanzarta dauko key motarsa tai ta mika masa' idan kafita ka turomi kannika". "Hjy duk subibun fa suke nan meyasa daya bazata koma g'ida ba?". "a'a babu komai Akwai Aisha ai' kai dai hanzarta kaje' k'uma dan Allah kasanarwa Aisha koda ta waya ne zainab na hospital". " naji kawai yace ya sakai yafice da sauri". "a zcyrsa yana cewa dama nayi h'aka ne d'an kada wani yasan naje g'idan tunda ba'anan nake ba". "bayan ya sanarwa su Amatullah snn yaje yashiga mota zuwa kasuwa parking yai a inda yake parking motarsa batare daya shiga shagoba ya nimi napep ya h'au zuwa g'ida". "yana shiga daki Aisha ganita yai jigine da allon gado ta zabga uban tagumi jikin zhrdee yai sanyi bakin kofa yaja ya tsaya h'ade da zuba mata ido". " Aisha na daga kai suka h'ada ido tsaki tai h'ade da juya masa baya". "a sanyaye zhrdee ya karisa gunta a gabanta ya duka snn ya kamo hannunta bibbiyu cikin sanyi murya yake kiran sunata da sauri Aisha fisge hannunta' zhrdee yasake rikewa' Aisha na fisgewa taja da baya' gani h'aka yasa zhrdee hayewa kan gado' ita k'uma Aisha ta sauka ta barmasa gadon' still zhrdee yasake binta inda take yana kokarin riketa". " igijesa tai ya f'adi a kasa snn takami hanyan fita daga d'akin' a guje ya mike yasha gabanta duk inda ta kauce saiya bita zahradee kabani hanya". "Aisha bazan baki hanya kifita ba". " zhrdee kabani hanya ko natureka". "wlh Aisha babu inda zafi". "wlh zan tureka". "Aisha ko kasheni zakiyi bazaki fita ba". "tsaki tai h'ade dasa hannu bibbiyu tatureshi' gani h'aka yasa shi igijeta gefe ta f'adi snn yajuya yasama kofa key' yarufe ya k'uma cire key' bayan ya cire key d'in ne ya juya gun Aisha daukarta yai tsaf Aisha na wultsil2 zhrdee be ijeta a ko'ina ba sai kan gado da sauri ya haye kanta". " h'aka Aisha d'an Allah ki saurareni dan Allah Aisha". "na saurareka name? bayan day kaimi karya yanzu so kakeyi kenan nasake saurarenka ka rangadomin wata karyan kasakeyi ko?.. "h'aba Aisha meyasa kikemi h'aka sbd Allah?. " me nayi maka zhrdee? kai bakaga abinda kayi ba".. "me nayi k'uma aisha?" "dan Allah katashimi a jiki tunkafin.. " kafin me? wlh Aisha duk abinda kike tunani ba h'aka bane".. "ba h'aka ba kamar yaya' kaifa da bakinka kace baka kwanan dakinta k'uma idan har naganta da ciki to a ruwa tasha? ko kanaso kacemi yanzu d'in ma a ruwan tasha?". "a'a' ba'a ruwa tasha ba amma wlh3 Aisha sau dayane kawai' sau dayan ma bansan yadda akai ba". " wani zancen banza zancen rainin wayo... "h'aba Aisha wani irin mgn ne kikeyi h'aka sbd Allah' wlh idan sbd zainab tasamu cikine kike tunani zan sauyaki maki wlh na rantse da Allan daya halliceni bazaki taba samu h'aka a guna ba' Aisha karfa ki mance ina sonki sota har abada Aisha' wlh Aisha har gobe da jibi banga macce da takaiki ba a guna". " himm dadin baki dai irin naka' baga zainab harma cikin kane da'ita". "Ohooo my God' zainab d'in me daga ita har abinda yake cikin wlh basu gabana' idan fa kin yarda Aisha ke nakeso kece zabina tauraruwan dake haskaka birni zcyta". "A lkcn ne Aisha ta sakar masa murmushi h'ade da cewa himm Allah yasa har zucine". "Au baki yarda ba?" "ni bance ba". "kimace kigani' daga nan yajata da wasa ya more lfyrsa' bayan ya sauka ne har Aisha ta mike da sauri ya medata ta kwanta snn yafara yimata tausa a cewarsa ya gajiyar da'ita duk kanni gababinta yakebi yana jan snn ya danna a hankali sbd kada taji zafi' yanayi yana tsikaranta h'ade da wasa da kirjinta' Aisha sai faman dariya takeyi". " suna cikin h'aka kenan sai sukaji knocking d'in Hjy h'ade da kiran aisha' da sauri zhrdee ya sauka a kanta snn ya hurga mata rigan jallabiyanta tasa' shikum ya sauka ya koma gefe ya labe". "saida Aisha tasa rigan tuku taje ta b'ude kofar h'ade da yinmata sannu da dawowa". " yawwa sannu ya g'ida? lfy klau ya mejikin? jiki da sauki ashe ya sanar dake?' wlh dazu ne ya kirani yake sanar dani". "Allah sarki Ai jikin ma da sauki' nima nadawo dorawa abbanku abinci ne sbd naga lkcn dawowarsa yakusa k'uma gashi yamma yayi". " h'aka ne to kodae nazo na tayaki aikin ne?" "a'a barshi kawai inada miya tuwon kawai zanyi' to shikenan". " amma Aisha so dayawa nasha f'adi maku keda yan'uwanki banaso kuna zama kai ba dankwali sbd Allah idan su sunyi ace dan basuyi aure ba amma harda ke daya kamata kiringa yimasu f'ada shine kikeyi". "Hjy kiyi hkr za'a gyara". " Allah yasa' snn tashige ciki'". "Hjy na shigewa Aisha ta meda kofa ta rufe zhrdee ya jawota suka koma suka dora daga inda suka tsaya". "gani karfe shidda yasa Abba tashi daga kasuwa' yabari yaran shigo su meda kaya ciki' gashi har lkcn tashinsu yayi bega son yadawo ba k'uma su rabu dashi yace zaidawo kasuwa' daukar wayarsa yai yakira son har five miss call amma son be daga ba' gani ba'a dagaba yasashi zuwa shagonsa ya dubashi tun kafin ya'isa ya hango motarsa a parke a gefe inda yasaba pakawa duk da h'aka dai saida ya karisa har ciki yashiga da yaga bashi a ciki yasashi tambyar yaran shago ina ogansu?". "da farko zaifita yace zaije gun matarsa a hospital bayan ya dawo ya paka motar ko shago be shigo ba ya h'au napep daga snn besake dawowa ba". "to kilan dai yana can hospital d'in". " zhrdee yana g'ida yana kiran Hjy tazo tafita snn shima yafita' Hjy bata fita ba saida takare aikinta tsaf snn tasake wanka tafita' Hjy na fita saida tadanyi nisa snn shima yafita a gurguje yaje ya dauki motarsa saida yabiya ya siyewa zainab su ice cream chocolate gasasshen namar rago da kaza snn yakarisa hospital d'in". "daidai lkcn drip d'in da aka sa mata ya kare zhrdee yana shigowa ya cire alluran snn yasa hannu ya dagota ya jinhineta da bango motsi kadan saiyace sannu' dama shigowar Abba kenan gani h'aka yafita Hjy tace ga abinci a zubo'.. " a'a Hjy kibari kawai ga wani nan nakawo mata' jawo ledar yai ya b'ude namar kazan ya dauko ya diba har yakai mata baki da sauri ta kauda kanta' Hjy tace a'a zainab kici mana' sake kai mata yai zainab sai amai har jikin zhrdee' zhrdee ya nuna bedamu ba". "bayan ta gama kamata yai zuwa toilet ya wanke mata jiki tas snn ya sake kamota tadawo gado yaje ya wanke nasa yana fitowa doct yashigo dubata' yai dube duben da zaiyi snn yai sallama h'ade da dokoki kada tai aiki me karfi. inda so samune ko ruwa kada ta diba banle mgnr abinci' Hjy tace to za'a kiyaye" "snn ya rubuta masu maguguna yafita' yana fita Hjy ta sanarwa Abba' Abba yace tunda abin yazama h'aka su dauketa zuwa g'ida kawai idan ciki yai karfi sai takoma g'idan ta". " Hjy tace to shikenan kaga dama ga extra room na kusa da Aisha sai su zauna tare kawai' eh h'akan ma yafi. "zhrdee da kansa ya dauketa bema bari ta takafa sbd jirin dake dibanta yakaita motarsa a gaba ya'ije ta su Amatullah k'uma suna baya Hjy da Abba motarsu daban' suka nufi g'ida". " suna shiga Abba ya mikawa Amatullah key tai sauri ta b'ude masu dayan d'akin kusa da Aisha' da sallama Amatullah ta shiga' Aisha najin sallama da sauri tafito h'ade da tambyar mai jiki". "jiki da sauki anmayi sallama' Allah sar....... " Aisha ta kasa karisa mgnr tane sbd yadda sukai ido biyu da zhrdee yana dauke da zainab tamkar jijira..... ★tofa jama'a yau ake yinta★ 😋. 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘. 🌳Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern🌳 story written by mm uswan. ★kae jama'a lalla Aisha ke yar' gata ce bcoz majority suna bayanki, karkuji komai masoyan Aisha makkan nest year daku ciki★ 😘. ★Allah sarki zainab kada ki damu share hawayenki😭zhrdee na tare da Aisha ke k'uma yar' gatan Hjy da Abba ga k'uma baby d'in ki, su Aisha saiga sai hango★ 😘😉 3⃣7⃣ "suna shiga d'akin zhrdee ya dauka a kan gado ya shinfidata h'ade da rufeta da bargon dake gefe' Amatullah tana ije ledar ta fice a d'akin". "snn su Hjy da Abba suka shigo kara dubata snn suka fita' bayan su fita ne zhrdee yasamu b'akin katifa ya zauna, zainab dake kwance tace zansha ruwa, zansha ruwa". " karki tashi kije ki badai ki zauna na dauko maki' dan Allah ka taimaka ka miko mi". "ina gani kamar ruwan baya dadeki bane yasa h'aka". "zahradee ya karisa mgnr ne h'ada da mikewa yaje yana yaye labulan window' a hankali zainab ta laliba ta mike zata dauko doran swan batare data zhrdee ya Ankara ba zainab ta f'adi sbd kirin da take gani' ihu tasa tana f'adin wayyo Allah na' joyowa yai yana kallonta h'ade da tsaki ya zuba mata ido duk kukan da takeyi beyi tunanin taimaka tama ba". " Ashe Hjy tajiyo ihu zainab da sauri ta turo kofa zata shigo' da sauri zhrdee yakai hannu zai daga zainab' bige masa hannun tai taci gaba da ihu' Hjy na shigawa salati tasa h'ade da sa hannu shima zhrdee d'in yasa suka dagata zuwa b'akin dago' Hjy ke tambaya garin yaya zhrdee na d'akin yabari ta f'adi?". "a'a ruwa naje daukowa shine jiri ya dibeni na f'adi". " to kai kana ina sbd Allah h'akan yafaru?" "a'a nice ban sanar dashi ba sbd naga kamar yagaji". "ya gaji k'uma aikin me yayi da zai gaji?". " murmushi kawai zainab tai' Hjy tace dan Allah a kiyaye". "to Hjy insha Allahu'. " Hjy na fita zhrdee ya juya kan zainab makaryaciya kawai meyasa baki fadiwa Hjy gaskiya ba?". "ta kanka akeji". '"daga snn bata kara mgn ba duk mgnr da zhrdee keyi ido kawai ta zuba masa". " Hjy na fita d'akin Aisha ta nufa a b'akin kofa ta tsaya knocking tai Aisha ta fito Aisha ga maigidanki nan yadawo kikai masa abinci". "kadan kawai nayi sbd nasan ba'a yakeba". " to shikenan zo muje ki amsa ki kai masa inada ragowar na abbanku kinga daga nan ma sai Ku gaisa da maijikin". "to kawai Aisha tace tabi Hjy duk da ranta besoba amma babu yadda zatai' kitchen sukaje Hjy tasa miya da tuwo a kula ta mikawa Aisha". "amsa aisha tai tana tafe tana makosani a zcyta' zuwa d'akin zainab a b'akin kofa ta tsaya tai knocking zhrdee yace waye'? waye? mikawa yai yaje ya rude kofar sakai kawai tai tashige batare da mgn ba' tana shiga ta ije snn ta juya tafita' ido kawai zainab tabita dashi". " shima zhrdee shiru yai yana binta da ido har tashige daki' snn ya koma daki' yana shiga b'ude abinci yai gani tuwone yasashi zama yafara ci batare da yaiwa zainab bismillh ba'yana cikin ci ya shake sbd miyar Akwai yaji' tari yakeyi harda hawaye yana hasa-hasan yadda zai dauki ruwa yasha amma yakasa sbd rufewar da idonsa yai". "zainab na gani h'aka ta juya masa baya kamar batasan yanayiba". "da kar yasamu ya ziro hannu ya dauko ragowar ruwan swan d'in data sha yarage snn yasha". " yana sha ko numfasawa beyiba yace muguwa kawai ta Allah bataki ba". "idan zainab ta tanka kasa zai tanka". " ture abinci yai gefe ya mike' abincin dabe kara bi takansa ba kenan". "itama be dameta ba sbd abincin baya gabanta' har yagama babu wanda ya tankawa wani' bayan ya gamane ta mike ta dauko ledar naman daya siyo mata tafara ci' kadan kawai taci sbd ba dadi yake mata ba' snn dauki ragowar ta ije a gefe' hannu ta zura ta dauki ledar magugunarta ta dauka tacire tasha snn ta kwanta akan idan ya f'ada mata sai ta tashi tai sallolin da ake binta". " Ashe Akwai na bcc aciki tanasha sai bcc' 12-30 shap zhrdee ya mike a hankali take tafiya yaje ya b'ude kofa ya fita zuwa d'akin Aisha' Aisha na bcc ji kawai tai anfado jikinta' a birkice ta b'ude ido tana kokarin ihu' da sauri zhrdee yasa hannu ya rufe mata maki". "gani zhrdee ne yasata doguwar tsaki h'ade da igijeshi ta sauka ta bar masa gado kasa ta koma ta kwanta' da sauri zhrdee ya bita inda shima ya kwanta a bayarta mikewa tai tabar gun takoma gado' sake mikewa yai ya bita gadon' da h'aka sukai ta yawo a daki har karfe 3AM duk juye juyen da takeyi ko kala batace masa ba' gani asuba zaiyi yasashi hakuri ya bar d'akin". "yadda yafita a sace h'aka yadawo a hankali yake tura kofar yana shiga gado direct yaje ya h'au ya kwanta' zainab tace har kadawo". " me kikace?" "nace kadawo?". " bayifa naje". "baki ko?". " eh mana". "makaryacin kawai". "waye makaryaci?" "kafin kowa sani". "himm kawai yace daga snn besake mgn ba". "tun daga lkcn kullum h'aka zhrdee yake a duk lkcn da zaifita a idon zainab yake fita yakama dawowarsa zainab bata nuna masa yadameta ba' washe gari ya koma d'akin Aisha' sbd yau itace da office' yana idar da sallar asuba ya koma d'akin Aisha bebari rana tayiba kamar yadda sukeyi' koda yashiga ganita yai kwance tana' itama tana ganisa da sauri ta rufe idonta kamar mai bcc' shim kansa zhrdee d'in koda yaga abinda takeyi be nuna h'akan ya damesa ba' gefe daya ya koma ya kwanta batare da mgn ba sbd yasan koda yai mata mgn balallane ta amsashi ba". " koda zai karya da safe a bangare su Hjy ya karya sbd babu abinda Aisha tai na breakfast ". " da safe bayan zhrdee yafi kasuwa Hjy ta kirasu duk su biyun suka hadu a parlour Hjy ta fara da Aisha to Aisha ga zainab kece babba dan Allah kiyi hakuri da junarku' dama kowa yasan ranar daya ke girki kinga basai nayi wani dogon bayani ba' ga kitchen nan duk me girki ita zata gyara ko'ina kunjiko". "duk suka h'ada baki da muji". " k'uma Dan Allah banaso jin wani cecekuce a tsakaniku' ke Aisha kece babba kiyi hkr da zainab' kema zainab bance ki takataba kowa ya tsaya a matsiyinsa". "bayan h'aka Dan Allah idan kunga wani abu da ba daidai ba a tsakaniku ko gun Mijin naku dan Allah kuyi gaggawar sanarmi". "insha Allahu". " shikenan Allah yabaku zaman hkr". "amin". "saida Hjy ta mike snn suma suka mike kowa yakama kansa". "koda zhrdee ya koma d'akin Aisha mgn baya hadata dashi yayi iya kokarin sa wajan gani yashawo kanta amma ina har takare girki yakoma d'akin zainab". " gashi kwanasa biyu a d'akin Aisha amma be hanasa zuwa d'akin ciki dare ba' zainab na kallonsa ya fita, tunda yaje around 2AM yake bata hkr gwiwa bibbiyu amma besa Aisha ta hakuri ba' gani bazai samu biyan bukatar saba yasashi fita zai koma d'akin zainab". "zainab naji tafiyarsa da sauri taje b'akin kofa ta tsaya' zhrdee yana zuwa yaga zainab a b'akin kofa tsaye' lfy me kike nima cikin daren nan?". "daga ina kake?" "wani irin tambyar rainin wayone h'aka? Dan Allah malama kibani hanya nashige". " wlh babu inda zaka sai kafadinmi daga inda kake' mugu mara tsoran Allah me satan kwana". "dawa kikeyi zainab?" "dakai nakeyi' me kikace?" "nace dakai nakeyi".. " kafin ta karisa ya dauketa da mari". "ihu zainab tasa tana kuka amma still bataba da hanyar ba". " dayake dare ne tamkar a kuni Hjy da Abba' da sauri suka fita'duk mgnr da'akeyi a kuni Aisha tashi tai tana lekensu' da sauri suka kariso h'ade da tambyar lfy". "cikin rawar murya yace babu komai bigewa tai' gani yadda bakinsa ke rawa yasa Hjy tambyar zainab' cikin kuka zainab wlh Hjy tunda nazo g'idan nan narar girkina cikin dare yake satan jiki yaje d'akin Aisha bazai dawowa sai asuba". "salati Hjy tasa tana f'adi zhrdee yau she ka lalace ne h'aka sbd Allah' so kake ta haifan mana shugu a g'ida? ka dauki girkin wata ka kaiwa wata". "Hjy bafa h'aka bane wlh sharrin zainab ce kawai".. " kaimin shiru manafiki tunda kai h'aka dama kasaba satan kwana' k'uma wlh sai Allah ya sakawa duk wanda kasaci kwanta ka kaiwa yar'uwarta' k'uma kai da Allah". "h'aba Hjy yau ne kawai fa". "yau d'an garinku mari kunya da gske kenan dai kanayi' as shank wlh kabani kunya zhrdee wlh ka canza katashi daga zahradee d'in dana sani".. " h'aba Hjy dan Allah kidaina f'adin h'aka sbd dan wann laifin kike fadin h'aka'"... "kafin zhrdee ya karisa Hjy ta daukesa da mari h'ade da cewa wawa kawai wlh ilimika be amfana maka komai ba' sbd so zakaje ka hallaka kanka kasa kanka cikin masifa'ina ita Aisha manafuka alguguma kawai". " duk abinda Hjy keyi Abba bece komai ba ido kawai yazubawa son yana kallonsa". "dama zainab na gani Hjy tafara f'ada tabar gun ta shige daki". " itako Aisha tana daki tana kallonsu' Hjy tace wlh idan baki fito daga d'akin nan ba' kika bari nashigo saina maki shegen duba a g'idan nan". "Aisha najin h'aka da sauri takoma cikin d'akin". " bazaki fito ba bakar manafuka nasan ba bcc kikeyi ba' shiru da tajine yasa Hjy fusata' a fusace ta juya zuwa dakin Aisha' da sauri Abba ya riketa yana f'adin ina zaki Hjy?" dan Allah Alhj kabarni naje na fito da shegiyar yarinyan nan na koya mata hankali". "wawiya kawai mara lisafi". "a'a Hjy kada kije ki dakar masu yar' mutuni' idan ma hukunci zakiyi son ne abin hukuntawa ba ita ba". "ba tare da mgn ba'juyawar da zatayi ta maske zhrdee da bayan hannu snn tabisa da kafa tana tokarinsa". "gani h'aka yasa Abba cewa ya shige daki' a guje ya shige d'akin' Abba ya kama hannu Hjy suka koma d'akin su". " zahradee yana shiga yasama kofa key'zainab na gani shigowarsa ta juya masa baya tai kamar me bcc' daidai cinyarta yasamu ya watsa mata mari' a birkice ta mike muguwa alguguma manafuka tashi". "yanzu menayi k'uma sbd Allah?" "Ina zakisan abinda kikeyi' Ashe dama duk wata shiga da fitata ido kike sami ko?". "Eh d'in nasa ido d'in sai me". "h'aka kikace ko?". "eh h'aka nace". " wlh zainab bantaba tsanarki ba irin yau, natsaneki banasonki zainab k'uma bana kaunar ganiki". "sai me? wlh zhrdee da mgnr ka yakai zci danafi kowa murnar h'aka". " kamar yaya?" "kamar yadda ka dauka'. " zainab ki kiyayeni fa". "ko k'uma kai ka kiyayeni ba". "wlh zainab inda badan su Hjy ba wlh dana nada maki dukan dasai kinkasa tashi". " zhrdee kenan su Hjyn me a tunanina babu abinda su Hjy da Abba suka isa su hanaka' sbd bajin mgnrsu kakeyi ba". "wahh! kike fadiwa h'aka?'. " kai dakai nakeyi". "kadai sann wanda zaka duka amma baniba". "Dan karami tsaki yai h'ade da kwafa snn ya kwata". " da safe kafin Abba yafita kasuwa sbd yasan halin Hjy f'ada yai mata sosae akan koda wasane kada tasake taiwa Aisha mgnr jiya tarabu da'ita kawai". *"itama Hjy bata musa masa ba' shima kansa zhrdee yarage satar kwana ba kamar dah! ba' amma fa har gobe koda wasa besake taraiya da zainab ba". "yau zainab ce da girki bayan ya gama cin abinci yazo kwanciya tace zhrdee". " meye ne?". "Dan Allah inaso na rokeka wani abu". "batare daya kalleta ba yace ina jinki". "Dan Allah g'ida nakeso naje gaida su ummata". " babu inda zaki". "Allah fa nace maka". " sai fa kiyi ". " zhrdee ya karisa mata mgnr ne da juya mata baya' tun daga snn bata sake cewa komai ba' itama kwanciya tai". "da safe lkcn zainab tashiga gaida Hjy' dama dasafe dukkansu suna shiga gaidata' bayan sun gaisa zama zainab tai taki tashi' Hjy tace zainab lfy kuwa?" "eh dama dan Allah inaso kisami bakine da zhrdee". " lfy wani abu yafaru". "a'a babu komai". " to menene?". "dama so nake naje g'ida gaidasu ummata'". " shine kawai". "eh shikenan". " to shikenan yanzu jeki ki karisa aikin ki k'uma ki shirya cikin lkc sbd saiya daukeki a g'ida snn yakarisa kasuwa". "to ngd Hjy". "cikin murna zainab ta mike zuwa d'akin ta' tana shiga daidai lkcn zhrdee yana shirin shiga wanka' toilet ta shida ta h''ada masa ruwan wanka snn tafito' tana fitowa shikuma ya shige toilet d'in gani ruwa a h'ade kafa yasa ya ture ruwan ya zube akas snn ya h'ada wani yai wanka". " kafin ya fito tun zainab taje kitchen ya h'ada masa abin karyawa duk da tasan ba lallane yaci ba' tunda bacin abincinta yakeyi ba amma be hanata dafa masa' gani Aisha a kitchen tai duk da batasan me takeyi ba amma tasan baya wuce abin breakfast take hadawa". "suna h'ada ido Aisha ina kwana". "shiru Aisha tai babu amsa". " Aisha take fa nakeyi ina kwana". "lfy klau' Aisha na f'adin lfy klau daga snn bata sake mgn ba saima juya baya da tai". " itako zainab taci gaba da aikinta tana gamawa ta kwashe zuwa daki' snn zhrdee shima yafito kenan daure da towel gaban mirrow ya tsaya yana kallon kansa a madubi". "tana ije tre d'in taje ta bayansa ji kawai ya anrrungumesa ta baya h'ade da cewa bari na shafawa mijina mai' duk da ba tsayine da'ita ba amma be hanata kwanciya masa a baya ba h'ade da kewaya hannayenta tana shageshi". "doguwar tsaki yaja h'ade da cewa wlh idan baki sakeniba saina tureki' zainab najin h'aka ta kara lafewa a jikinsa". "badake nakeyi bako". " Dan Allah ma baka goge antabaka bama". "na godime mara kunya". " wlh zainab inda badan cikin dake jikinki bako himm". "karisa mana'da saikayi me". " wlh duka zanmaki' amma ko yanzu idan kika kureni saina farfasa maki baki". "tsayuwa zainab tai h'ade da tokare kafa daya ta dauki hannu ta rike kugunta tana karkade jiki tana f'adin Allah ko' to bismillh". " dawa kikeyi zainab?" "da kai nakeyi". " ni ko?'. "Eh" kai d'in". "ni ko?". "Eh" kai ". " kikace eh' a guje yabinta' yana cewa ai da kintsaya' ita k'uma tai parlour snn ya dawo ciki". "tana fita tafara gyara parlour saida ta goge duk inda ya kamata snn tai shara tazo ta shige wanka'shima zhrdee dayake yai yai ra'ayin ci sosae yaci abinda bayan ya gamane yashiga d'akin Hjy sallamarta zaifita kasuwa". " da sallama ya shiga har kasa ya duka ya gaidata h'ade da sallamarta zaifita kasuwa' Allah yabada sa'a yabaku abinda kuke nima nace alkairi duniya da lahira yai maku Albarka dukkanku". "amin Hjy ngd'". " har ya mike yawwa zhrdee ga zainab nan idan Allah inaso ka'ijeta a g'ida' idan kataso kasuwa sai kabiya ka dauketa kudawo tare". "can kasa da murya yace to naji' k'uma dan Allah kadan samu abinda zaka bata kai tsaraba g'ida". " naji kawai yace yafice' yana fita d'akin Abba yashiga suka gaisa snn yaje Aisha gimbiyarsa da sallama yashiga' Aisha na ganisa da sauri ta juya baya". "Aisha kenan har yanzu fushi kikeyi dani? to ina kwana' kin tashi lfy?" "tsaki tasake yimasa". " Aisha ni zanfita nace saina dawo ko kina bukatar wani abu". "still babu amsa' juyawa yai yafice zuwa d'akin zainab' yana shiga yatarar ta shirya tsaf' to manafuka alguguma kin fadiwa Hjy kinji dadi ko? sai ki tashi guje". " batare data tanka masa ba' ta dauki mafiya suka fita yana gaba tana baya har sun wuce d'akin Aisha sai zainab ta dawo da baya da sallama tashiga Aisha na zaune tana buga mage a wayarta zainab tace Aisha". 'kai kawai ta daga mata amma babu mgn". "zantafi uguwa nida maigidan namu bazamu dawoba sai yamma shine nace bari na sanar dake kada kiji shiru' sai mu dawo". " juyawa kawai zainab tai tasa kai batare da ta tsaya sauraran abinda Aisha zata ceba tafice". "da zcy ya diba Aisha batasan lkcn data kwada wayarta a bango ba wayar ta tarwatse wasu kwallane suka zubo mata gado ta h'au taci gaba da kuka". "zainab na fita ta shige mota zahradee ya jasu' b'akin wani kanti ya tsaya bayan yai parking snn yafita zuwa cikin kanti siyayya yai sosae sabulai wanki dana wanka chocolate biscuits cake sweet dai sauransu yazo ya b'ude bayan motar ya zuba sukaci gaba da tafiya' ko kallon inda zainab ke zaune bayayi har suka isa' saida ya shiga cikin haraban g'idan snn yai parking suka fita b'ude baya yai ya dauko ledar tsaraban' gani zainab tai gaba da sauri yace ki tsaya". " tsayawa tai ta jirasa snn suka shige tare' har parlour suka shiga da sallama lkcn duk kannin zainab na parlour a guje sukazo suka rungumeta suna f'adin Anty oyoyo zainab na murmushi zhrdee ma h'aka' yar'utansu me suna maryam tazo ta rungume zhrdee gani h'aka yasa shima daukanta". "guje me d'an wayon cikinsu tashiga ta sanarwa inna Hulaira ga Anty tazo' saida inna tasa hijab snn suka fito tare' ganita yasa zhrdee mikewa tsaye bayan ta zauna ne shima ya zauna a ladabce ya gaidata h'ade da tambyar su Hjy da Abba". " duk suna lfy sucema a gaidaku". "ayya muna amsawa". " mikewa inna tai taje d'akin Mmn zainab ta sheda mata zuwan su zainab snn tafita kitchen taje ta dauko ruwa da juice tabawa mame kanwar zainab takai masu parlour". "shiru da taji alamar Hjy bataje gun su zhrdee ba sake binta tai d'akin dadina da yaya sanyi jiki wlh na f'adi maki sirikina yazo kifita Ku gaisa amma abu ya gagara". "nifa kada ku dameni da wani sirikin nan kubarni na kare aikina tuku". "Dan Allah yaya tashi kije idan kin dawo kya karisa". "ke!! kifita daga idona daga ke har surikinki ba'a kanku akafara ba". " abu ma harda gori' babu damuwa nidai Dan Allah aje a ganomi siriki". "inna ta karisa mgnr NE h'ade da fisge zani da Hjy ke nikewa snn ta mike h'ade dasa hijab suka fita tare' ita tai parlour inda zhrdee yake' ita k'uma inna tai d'akin ta". "tana isa zhrdee yasake mikewa taida ta zauna snn ya duka suka gaisa' suna gama gaisawa Hjy ta mike takoma d'akin ta' shima mikawa yai batare dayace mata komai ba yakami hanyar fita zainab na gani h'aka da sauri ta mike ta bishi har bakin mota' yana shiga mota ya tayar gani zai tafi yasa zainab cewa sweety dawani lkc zaka dawo". " banza da'ita yai yaja motarsa yafice' itama be dameta ba sbd idan da sabo tasaba' juyawa tai takoma ciki gani yabar ledar da suka shiga dashi yasata tunanin kodai mantuwa yai dashi' hannu tasa ta b'ude gani sabulai ne dasu sweet yasace cewa kilan tsaraba ne' daukawa tai ta shiga dashi d'akin inna". "tana ije kayan ta shiga d'akin mmn ta gaisheta snn ta dawo d'akin inna' kallo daya inna tai mata tagano cikine da ita' farfesun kayan ciki ta dibo mata h'ade da lemo kwakwa tanaci suna hira har tagama inna tace mame ta dauki plate d'in takai kitchen' bayan fita mame inna ke tambyarta yadda zamasu yake a g'idan su Hjy". "nan zainab ta kwashe komai ta fadiwa inmarta harda kuka' gashi nafi Aisha kyautata masa amma baya gani kullum cikin gefenta yake ko a dakina yake baya hanashi mgnr Aisha bayan ma batasan yanayi ba' Dan ko kyatata masa batayi yanzu da h'aka ma sufi sati uku bata mgn dashi k'uma koda shine yai mata bata tankashi amma duk begani ba".. " harda kece baku mgn?". "a'a' bandani". " to ai me sauki ne' kedai duk rintsi duk wiya duk abinda zaiyi naki ido' k'uma koda yai maki abinda bata maki rai Dan Allah ki daure' banda yawan fushi banle yakai ga gaba' koda laifine yai maki ki daure kinjiko?". "naji inna". " to kinadai gani yadda mukeyi da abbanku'". "babu ruwan ki da'ita koda tana fushi kiyi banza da'ita kikama mijinki' mijine babu kunya a tsakaniku koda fushi yakeyi dake kada h'akan ya dameki kamashi ki rungume ki jashi da wasa har yasake ya biyeki". "banda yawan musu dashi duk abinda yace to kawai idan bana sabon ubangiji ne' kinjiko?". 'naji inna". "to Ai inna koda abinci nai masa ba lallane yaci ba' se yai ra'ayi". "kada ki damu k'uma kada h'akan ya dameki wataran sai kabari' kedai kiyi yadda nace dake". " wlh duk abinda kike masa na kyautatawa yana sane k'uma yanaji dadi' kin wani namiji ba lallane idan matarsa tai masa abin kyautata ya nuna mata ba amma yaji dadi har cikin zcyrsa". "wlh idan har kika rike abinda nake f'adi maki k'uma kike aiki dashi zakisha mmki sbd wataran da kanki zaki tambayi kanki anya kuwa zhrdee d'in dana sanine? amma duk sai kinyi hkr kafin kiga h'aka". "to inna" "k'uma banda yawan kai kara gun uwarsa duk sonda take maki wataran raguwa zaiyi' sbd duk soyayyar da zatai maki ba kamar d'an data haifaba' kiyi hkr zainab kiyi hkr da mijinki' shiyasa ake cewa tsakani mata da miji sai Allah". "ina magugunar dana baki?". " duk su kare". "to bari zanbaki wasu harma sufi nada kyau' sai dai guda dayane bandashi yakare amma yaya tana dashi zan dauko maki". " to ngd". "Aisha tayi kuka har ta gaji gani babu me rarrashinta da kanta ta rarrashin kanta' ta tashi tai alwala tazo tafara sallah sbd lkcn anfara sallar azahar". "bayan ta idar ne ta kwashe wayar da b'ude wadrop d'in ta ta zuba snn ta rufe' h'aka taci gaba da zama a daki ko parlour su bata lekaba banle bangaren Hjy". "abin duniya duk yabi ya isheta' ta rasa inda zatasa ranta taji sanyi". "da yamma zhrdee yana tashi daga kasuwa ya biya daukarta' a kafar g'ida ya tsaya snn ya dauki wayarsa yai dialing number ta' zainab na gani da sauri ta daga wayar da sallama' gani a kofar g'ida idan kinga dama kifito mutafi". "to gani nan zuwa". " zainab dawa kike waya' iji inna kenan". "shine yadawo". "tsaya kawai bari na aiki mame ta kirashi yaci abinci kafin kutafi g'ida' kinga koda kuje kun huta da girki". " to kawai zainab tace". "inna ta aiki mame ta kira zhrdee ya shigo ciki'bayan su gaisa inna tacewa zainab taje kitchen ta dauko masa abinci' da zafin nama zainab taje ta dauko masa abinci ta kawo' inna tace ta kaimasa daki ne ba a parlour ba kamar bako". "extra room ne da babu kowa a ciki saidai kusan kullum ake gyarawa sbd baki suna zuwa a kowani lkc daga kauyen bbnsu". " zainab na ijewa taje ta dauko masa ruwa da abin wanke hannu duk ta kawo masa' sai da ta h'ada komai snn ta koma tace dashi bismillh' ya mike tana gaba yana baya suka shiga b'akin katifa ya zauna plate zainab ta dauka ta dibi abincin ta zuba masa h'ade da miya ta zuba akan tuwon". "tuwon shinkafane da miyar kuka wanda yaji namar rago da man shanu' gani zai wanke hannu yata dauko ruwan tana zuba masa ruwan yana wankewa' yana gama wankewa ya janyo hannunsa batare da mgn ba' snn yafara ci' duk da beyi niyar ci dayawa amma daya fara ci' shikansa besan lkcn dayai ta suburbuda ba' ankara kawai yai yaga tuwon kadan yarage kamar ya karisa kawai sai k'uma yai wani tunani a zcyrsa yace cewa anya banzama surikin zamana ba? na b'ude ciki a g'idan surukai sai faman rabkan abinci nakayi' bari dai na barshi h'aka kada rashin hankalin yai yawa". " cire hannu yai ya wanke' zainab dake zainab dake zaune ta mike ta kwashi kayan abincin ta meda su kitchen snn tazo suka fito tare zuwa parlour da sauri zainab ta shiga ciki dauko mayafinta' inna ta dauko magugunar ta bata dayan daya rage tace a'a bazan baki wnn ba sbd naga kamar cikine dake kada aje ayi barna' amma wnn zaki iya shansu k'uma banda matsa kinjiko". "nayi inna". "snn inna tashiga d'akin yaya dauko wani' dama lkcn yayan tana toilet inna nasa hannu a jakar kenan sai ga yya tafito'lfy me ake nima a cikin jakata k'uma?" "abu nake dubawa". " to bismillh' a bayan inna ta tsaya taga ikon Allah'gani ta dauko mata magani da sauri ta rike mata hannu ina zaki kaimi?' zanbamawa". "meya hana kibata naki?". " habawa yya f'adi wani abu amma ba wann ba'kema kinsan dan takarene". "to nidai gskya bazan bayarba dan mijina na siye". " bani nima sirikina zan gyara mawa". "nifa gskya ba kyauta zanbayar ba' Dan biyana za'ayi'haka kawai nasiye kayana dan gyara aure azo a dauke mu'". "hannu inna tasa ta fige h'ade da cewa bani auren yanta yafimu komai". " oho nidai nawa na sani". "nima na yanta nasani". " duk sukasa dariya". "inna takaiwa zainab h'ade da nuna mata yadda zatai amfani dasu' sukai sallama tafito zhrdee dake zaune ya mike suka fita". "be tanka mataba itama h'aka har suka isa g'ida' suna isa tafita zuwa ciki' ko daki bata shi gaba saida ta leka Aisha' Aisha najin anturo kofa da sauri ta kwanta kamar me bcc gske' gani h'aka yasa zainab cewa dama mudawone nace bari na lekaki amma tunda kinyi bcc saida safe snn tafita tai d'akin ta". " zainab na fita Aisha ta b'ude ido h'ade da cewa manafuka'". "shima zhrdee h'aka tai masa yai mgn har yagaji Aisha bata tanka masa ba' fita yai zuwa d'akin zainab' zainab na ije mayafi taje ta gaida Hjy snn tadawo lkcn zhrdee yana toilet yana wanka' shiyasa ta samu damar daukar magani da inna ta bata tasha wanda zatasha saura k'uma ta ije' yana fitowa yasa kayan bcc ya kwanta' itama tashiga tai nata wankan tasa kayan bcc ta kwanta' gani ta kwanta suna kallon juya yasashi juya mata baya' itama bata nuna ya dameta ba taci gaba da kwanciyarta". "washe gari Aisha ta amshi girki' koda yadawo d'akin ta zhrdee yayi iya kokarinsa wajan gani ya shawo kanta amma Aisha baki yarda ga sha'awa dake matukar damusa dan yakusa kai bango' kyaleta yai ya fita harkanta saida yabari cikin dare snn bcc yai nida da'ita zhrdee ya f'ada mata' a birkice ta falka h'ade da tureshi ya sauka daga kanta ta mike ta sauka kasa' zhrdee ya bita h'ade da riketa da karfi' zhrdee kasakeni". " Aisha bazan sakeki ba' Dan Allah ki tsaya kiji wlh sha'warce taimi yawa har ya kaini bango yau bazan iya jurewaba Dan Allah koda sau daya ne Dan Allah Aisha". "tsaki tai h'ade da fisge hannu ta barsa a gun". " babu irin rokon da bemataba amma taki yarda har safe' washe gari ma h'aka sukai tayi amma a banza". "ran zhrdee ya bari sosae har bayason gani Aisha kusa dashi' yana idar da sallar asuba ya koma d'akin zainab' ganisa da tai tunda asuba tasan ba lfy' sbd idan ita keda girki shine yake barin d'akin ta yana idar da sallar asuba amma idan Aisha ne sai bayan sallar isha yake zuwa d'akin ta". "da gari ya kara wayewa taje kitchen ta h'ada masa breakfast yana karyawa ya fita kasuwa' yau ko sallamar Aisha beyiba tai tafiyarsa". " h'aka yabawa zainab damar tararrayar mijinta' da yamma yana dawowa kasuwa hannu bibbiyu zainab ta amsheshi ta h'ada masa ruwan wanka saida yai snn yaci abinci' ita k'uma ta shiga tai nata wankan bayan ta fito bata Shafa mai ba saidai turaruka kawai tasa kayan bcc snn ta kwanta' shima yana gamawa yai brush yazo ya kwanta' ya kwanta ne kawai amma shikadan yasan abinda ke damusa a zcy sbd sha'awar da yake damusa gashi besan ta'ina zaifarawa zainab mgn ba' k'uma a gskya yau dai bazai iya daurewaba' gashi sbd Aisha ne yaki bawa zainab hakkinta tun ranar farko besake kulata ba' k'uma bata nuna h'akan ya dameta ba' to yanzu da'ina zanfara? gashi yau kam nakai bango' amma bari nagani". "zainab har kinyi bcc ne?". " a'a lfy meya faru?". "babu komai zainab d'in ta". "a yau ko' zhrdee najin h'aka ya yunkuro zuwa kan fuskanta' yana f'adin ke matsalata dake kenan wnn bakin yacika surutu da yawa baya shanye rada". "gani yana d'an neta h'ade da daukar mata numfashinsa a fuskanta a'a meye h'aka ka saukami a jiki mana". "ke kitsaya kiji mana wlh Allah ko' himm' daga snn yafara shafeta h'ade da tsotse2 mgnr ma ya gagara da h'aka ya tubeta shima ya tube gani zai shigeta yasa zainab sa masa kuka tana f'adi Dan Allah kabari wlh Akwai zafi' ke kitsaya bazakiji zafiba a hankali zanyi". " kafin zainab tai mgn tuni zhrdee ya shige' shi kansa ya rasa a wani duniya yake sbd ya kasa daidaita kansa' kafin asuba zhrdee yayi yakai sau gudu' kowani around yai saiya rungume zainab a kirjinsa yana kwatata irin dadin dayaji' a zcyrsa yana cewa kodan ita budurwace nasameta yasa takeda ni'ima h'aka? ko k'uma Dan wnn shine yina na biyu da'ita? idan ko h'aka halittata yake gskya na cuci kaina". "da asuba yatashi yaje yai wanka tafita masallaci shida su Abba da yayyinsa har suka dawo zainab bata tashi tai wanka ba banle sallah' da kansa yata da'ita taje tai wanka da alwala tazo tai sallah' bayan ta idar ta mike zata fita' ina zaki?" "zanje na h'aka maka abin karyaeane". " barshi kawai zo ki kwanta ki huta". "to kawai tace tadawo ta kwanta' shima kwanciya yai kusa da'ita h'ade da zuba mata ido har bcc ya daukeshi' shiyasa yau ya makara befita kasuwa da wori ba" "the nest day ma h'aka ne dan kwanta3 hanata bcc yai' tun tana daurewa har saida ya kureta' da safe kuwa da kansa ya h'ada masu ruwan wanka yana rungume da'ita sukaje sukai wankansu' zainab da kanta ta shiryashi snn tabashi breakfast yana gamawa ya mike zuwa kasuwa' tare suka fita zuwa d'akin Aisha' Aisha na zauna a kan cushion suka shigo zhrdee yana tsaye a b'akin kofa zainab tace Aisha kin tashi lfy?" "lfy klau' zhrdee dake tsaye yace gimbiyata kenan Hjy kilishi sarkin fushi da mulki dama nazo duba kwana ne' tunda kina lfy ni natafi kasuwa saina dawo". " Aisha tai banza dashi' zainab tace Aisha ana mgn dake". "wani irin kallon banza Aisha taiwa zainab' zhrdee na gani h'aka yakamo hannu zainab suka fita". " suna fita aisha tace lalla kam wlh sainayi maganinki a g'idan nan". 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES.F.O.W.☘. 🌳impacting valuable knowledge and entertainment is our concern🌳 story written by Mmn uswan. 3⃣8⃣ "har bakin mota zainab ta rakashi' ya b'ude ya shiga snn zainab ta mika masa jakarsa dake hannu hannunta ya amsa gani yatada mota zai fita sai tace kalli dakatawa yai ya tsaya h'ade da juyo mata fuska yaji abinda zatace' sakai tai cikin motar daidai bakinsa tai masa kiss💋 h'ade cewa pls kakulamin da kanka' snn ta ciro kanta' murmushi kawai zhrdee snn yaja mota yatafi". " yana tukine dai kawai amma hankalinsa baya tare sbd abinda sukai zainab jiya da dare' idan yatuno wasu abubuwa sai dai kawai yai murmushi h'ade da shafe kansa". "Aisha najin tafiyar zainab da sauri ta mike tafito har zata shige Aisha tace zainab". "na'am Aisha". " Dan Allah Dan annabi na rokeki banaso na kara ganiki a dakina". "lfy wani abune aka f'adi maki a kaina?". " a'a babu komai' nidai kawai kada kikara shiga daki". "Aisha kenan' iya kacin abinda zainab tace kenan ta shige d'akin ta". "itama Aisha shigewa d'akin tai' zainab na shiga daki bata zauna ba tafara gyara d'akin ta tana gamawa ta h'ada kayan zhrdee indices d'insa ta kwashe taje toilet ta wanke masa shi tsaf ta shanya snn taje ta gyara kayan daya cire tasa acikin wardrobe ta'ije masa bayan ta gama aikinta tas tai wanka ta kwanta". "da rana misalin 11-30 saiga kiran zhrdee kaman daga sama zainab taji wayarta na ringing da sauri ta daga wayar' gani number zhrdee ne yasata dauka h'ade da sallama' yana amsawa yace kindafa abinc ne?" "a'a" "kisa sanwa dani ganinan zuwa". " to kawai tace h'ade da mikewa' bayan ta kashe wayar kitchen kawai ta nufa tasa sanwa jolif rice da dafa masa da kifi busasshe kafin tagama zhrdee ya'iso kai tsaye d'akin zainab yashige' koda yashiga ganita yai tana sallah' b'akin gado ya zauna yana jiran ta'idar". "zainab na sallama ta juya da sannu da dawowa' yawwa sannu ya g'ida". "alhamdllh' ya kasuwa? alhamdllh' bari na duba abincin ko ya karisa". "a'a yazo kiga hannu yasa ya jawota jikinsa ya zaunar da'ita a kafarsa' hannu yasa ta cikin rigarta yana shafe mata...... da sauri zainab ta tureshi h'ade da daukan zani ta daura taje duba abinci' gani abincin yayi plate ta dauka ta diba masa snn ta dauki ruwa takai masa" "gani ta da yai da kaya a hannu da sauri ya dauki towel ya daura yaje ya amsheta suna ijewa ta sake mikewa". " ina zaki?" "wanka zayi". " a'a dawo ki zauna' tare sukaci abinda duk da ba mgn sukeyi ba amma idonsa nakan zainab' bayan su gama ne zhrdee yai second around snn sukai wanka ya koma kasuwa". "da yamma Aisha ta amshi girki zhrdee yana dawowa d'akin Aisha ya shiga lkcn tana toilet tana beyi mgn ya tube yarage daga shi sai gajeran wando snn yasamu b'akin katifa ya zauna' Aisha ta fitowa daure da towel gani zhrdee yasata daure fuska h'ade da dauke kanta". "gani h'aka yasa zhrdee mikewa kamar zaishig toilet da karfi ya dauketa ta baya sai kan gado snn ya fisge towel d'in da take daure dashi' a lkcn kam beda niyar amfani da'ita amma a lkcn saida yai' Aisha tayi kokarin gudu amma takasa sbd irin rikon da yai mata' yana gamawa ya je yai wanka' nan yabata kwance tana cizon lebbanta' baya fitowa suka h'ada ido yace lfy? ko dama kin dauka karfina kikafi?". "ita dai bata tanka masa ba' zama yai yaci abinci yana gamawa yasa kaya yatafi bangaren su Hjy dama lkcn duk suna parlour zama yai sukaci gaba da hira harda su Shamsudee da Nurudee itama tashi tai tasake wanke wanka zhrdee be dawowa d'akin Aisha ba sai around 11PM' koda yashiga be kulata ba kwanciya kawai yai. "da safe tana idar da sallah taje kitchen ta h'aka masa breakfast ta kawo ta'ije yana fitowa wanka ita k'uma ta shiga kafin tafito ya shirya karyawa yatsaya yi' tana fitowa ko kallansa batai ba taci gaba da shafa mai' yana gamawa ya kime' gani har zaifita batace dashi kala ba yasashi cewa Aisha ina kwana' tai shiru' dakefa nakeyi still bata amsa ba' daga snn besake mgn' wardrobe yaje dauka wasu takardu yana budewa wayarta ya f'adi a tarwatse yadda ta'ije'". " subhanalillah yaushe wayarki tai h'aka? ko fadowar da taine yasata tarwatsewa? dukawa yai ya dauki wayar' kae wann ma ai ta tashi a aiki babu wata mgnr gyara". "idan Aisha ta tanka kasa ma zai tanka". " meda wayar yai cikin wardrobe ya dauki abinda zai dauka yai gaba". "yana fita d'akin zainab yashiga snn tana kwance amma ba bcc takeyi ba' gani yashigo ne yasata mikewa zaine h'ade da cewa ina kwana". " lfy klau kin tashi lfy?". "lfy klau' har ya juya zainab tace dan Allah inaso mgn dakai' tsayawa yai h'ade da cewa ina jinki". "dama mgnr zuwa awone antenatal sbd lkcn da suka rubutamin yakamata tun last upper week ne yakamata nafara zuwa banjeba".. "eh ina sane ai". " to yaushe zanfara?" "sai lkcn dana shirya". " kamar yaushe kenan?". "bansani ba". " zhrdee ya karisa mgnr ne da fita' shiru zainab tai' tana binsa da kallo". "zhrdee be dade da fitata zainab taji ana sallama duk da Aisha taji amma dayake batai niyar amsawaba yasa ta kyale' zainab ce tafito duba me sallama' wata mata tagani rike da d'an ta dan kimani shekara hudu a hannu cikin girmamawa suka gaisa zainab tace wa kike nima?" "gun Aisha nazo tananan?" "eh tananan amma tsaya nadubata' shiga d'akin Aisha tai ganita zauna yasata cewa kinyi bakuwa' banza da zainab tai bata tanka ba' zainab na fita tace shiga tana ciki". " to tace". "tana shiga Aisha taga Ashe ubaida ne' tsalle tai ta rungumeta tana murna' uhmm su Aisha sarakan zumuci' tunda aka auri zhrdee aka mancemu' nidai nasan zhrdee bazai hanaki zumuci ba'idan ma nabaki haushi ina sane da labarin za'ai maki kishiya amma naki zuwa bikin sbd tunda kikai aure kika sharemu kwana2".. " Dan Allah ubaida kiyi hkr wlh ba h'aka bane". "to menene? badai kice zhrdee ya hanaki hulda da cewa ba' duk da nasanshi da kishi kamar ace akankine". " uhmm ubaida kenan mgnr dah!! ne wnn". "kamar yya Aisha?" "wlh zhrdee ya canza' dan yatashi a yadda kika sanshi' sbd komai ya canza' tunda ya auro algugumar yaringa". " kefa kawata shafami naji labari". "yanzu h'aka ma da kika gani wlh nafi wata bana mgn dashi' koda yazo banza nakeyi dashi". " subhanallh Aisha lfyrki kuwa". "lfy klau ubaida'. " h'aba Aisha auren da kikai a farko kika zauna da kishiyoyi har biyu kece ta uku be daga miki hnkli ba saina zhrdee? idan wanda nagani itace kishiyarta taki guda nawa take? kin zauna da manyan mata ma banle ita". "himm ubaida kenan bazaki gane bane". " ina ko zangane' saidai kiganar dani". "ubaida koda na auri Nasir yanada mata biyu nice ta uku' bayan aurenmu nagane cewa ya auri wasu matan kafin ni amma duk yasakesu' amma wlh h'akan be taba tami da hankali ba' sbd ban zauna dasu ba' Fatima ce kawai muka zauna tare' ita k'uma Fatima abinda na lura dashi shine bata daukeni a matsayin kishiya ba' nasan inda ta daukeni a matsayin kishiya wlh ko abinci bazata baniba". "to ba yarinya bace a haife ta haifeni dan dai Allah bebasu haihu da wuri bane' wani abu daya sama lura dashi shine Nasir yana matukar son Fatima' k'uma ko menene zai'iya yimaka idan kace zaka tadama Fatima da hankali dan ba karamin son yake yimata ba". "a kudi shekaru ilimi na zamani dana boko Fatima ta fini ubaida ta'ina zanfara' matar da take da doctoring degree daga ita har Nasir na kur'ani k'uma nasha jinta cikin dare tana karatu da asuba k'uma suyi da yara' k'uma koshi Nasir d'in ma ba baya ba' ubaida ta'ina zanfara?" "OK yanzu na ganeki Aisha' kin nunami su kinajin shoronsu kenan' shikuma zahradee baki shoransa sbd shi yarone". "ba h'aka bane ubaida". " to menene?". "wlh ubaida duk da nataba aure kafin na auri zhrdee amma bantaba jin zafin kishi kamar yadda nake kishi zahradee ba".. " kamar yaya Aisha". "ubaida aurena da zhrdee nasan dadin d'an namiji' nasan dadin saduwa".. " ban gane ba Aisha". "Aisha na mgnr ne babu alamar wasa a fuskanta". " a lkcn dana auri Nasir duk lkcn da yazo saduwa dani har fargaba nakeyi sbd a duk lkcn daya sadu dani gabana komawa yakeyi kamar ya salbe jazur yake komawa sbd azaba' nakanji raina kamar zaifita idan yanaji' da naga abin yana niman fita karfina yasa a sanar dashi' shine ya siyo wani magani TUBE JELLY PERSONAL LUBRICANT a duk lkcn da zaifara saiya shafa daya fara amfani dashi naji saukin zafin sosae ". " sai k'uma daga baya danayi rashin lfy wanda yasa harna cire rai da rayuwar duniya'🤔 ..Aisha kwaran da gske ubaida sanadiyar h'aka nasamu matsala a mahaifata wanda doct ya shedami ba lalla bane na haihu".. "Innallilahiwainnaillahraju'un' Aisha shine bantaba sani ba". " murmushi kawai Aisha tai". "amma kintaba samu ciki a g'idan Nasir?" "nasamu yakai wata uku snn ya lalace". "kinji abinda yasa nake matukar son zhrdee wlh a duk lkcn naga gansa da zainab sainaji kamar na kasheta na gaina ganita' wlh ubaida ba lallane ki yarda da abinda zanfadi maki ba amma tun bayan aurena da zhrdee Allah ya jazabceni da sosa" "son da kike masane yasa kike gaba dashi?". " a'a ba h'aka bane' koda zhrdee ya sauri zainab nunami yai baya saduwa da'ita' koda labari yazomi sai naji Ashe har ma cikine da'ita". "ciki fa kikace Aisha?". " wlh kuwa' shiyasa na hkr dashi gaba daya na barmata shi'dan a yadda nakejin zhrdee bazan iya sharing d'in sa da wata mace ba". "wlh Aisha bansan ke wawiya bane sai yau' nidai yanzu g'ida zanje sbd Bbn Abba yace kada na dade na barsama a g'ida ne yana kirana' amma koma menene kiyi kokari kizo' yanzu dai Dan Allah idan yadawo ki amfashe hannu bibbiyu sbd wlh zhrdee yana soki sosae' kizo kina masa h'aka bazaiji dadi ba' Dan Allah kiyi hkr ki sanyaya zcyrki". " to shikenan ngd ubaida' idan ba h'aka ba kinaji kina gani a kwace makishi ". " duk sukasa dariya' oho gashi kinzo ko ruwa banbaki ba " "a'a babu komai ai ba bakuwace niba". " har bakin gate Aisha ta rakata sukai sallama " "yamma nayi Aisha ta hadawa zhrdee lafiyayyar abinci h'ade da juice takawo daki ta jere masa tashiga wanka bata taba lkc ba ta fito kwalliya sosae tai ita kanta tasan tayi kyau' bata dade da gamawa ba zhrdee yai sallama suna h'ada ido yai mmki sosae a zcyrsa yana cewa to yau k'uma me aka shiya' karisawa yai ciki gimbiyata yau kwalliya ne h'aka akaimi?" "to zo kiga wani abu". " gani bata motsaba yasashi zuwa gabanta ya duka yana dafe da gwiwowinta Aisha dan Allah kiyi hkr ki daina fushi dani h'aka' wlh duk lkcn da zanshigo dakinki har faduwar gaba nakeyi' kamar fa ki mance auren soyayya mukai dake idan ma wani abu ne nayi maki me zaihana ki sanar dani amma ba kirinka fushi dani ba' wlh banajin dadi nashigo naganki kina cikin kunci' Aisha sbd dakefa yasa nake bujirewa mgnr su Hjy da Abba da k'uma zainab d'an dai naga na kyautatamaki amma duk yatashi a banza'. "idan k'uma kince mgnr aurena da zainab wlh bani na nimawa kaina ba su Abba ne' ni k'uma na amince masune sbd zabi suka bani' ni k'uma har ga Allah banason rabuwa dake shiyasa na amince masu' k'uma nima ai yakamata nayi fushi dake sakamakon buyemi mgnr rashin haihuwar' amma kinga duk banyi fushi ba sbd inasonki ko' idan k'uma mgnr cikin fans ne wlh bayin kaina bane rabon cikine ya kaini gunta a wnn ranar' k'uma koba komai ai matatace kamar yadda kema kike" "Dan Allah komai ya wuce inaso muyiwa juna uziri muyafewa junarmu Dan Allah mukoma kamar da' kinji Aisha ta". "murmushi kawai tai masa batare da tace komai ba". " zahradee yace alhamdllh hannu yasa a aljihu ya ciro sabuwar waya ya mika mata' bayan ta gani ya amsa yasa mata a caji' snn ya tube yaci abinci' a yau kam ko leka zainab beyiba balle tasan yadawo zamansa yai a d'akin Aisha ". " duk da mgnr da yai batace dashing kala ba amma da sukazo kwanciya yaga babbaci sbd duk yadda juyata yanayi batare da tace kala ba' da yagama daukarta yai ya dora akan kirjinsa sukai bcc. "yau ko zhrdee ko masallaci bejeba a daki sukai sallah tare suna idarwa suka koma gado". 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRIRES F.O.W.☘. 🌳impacting valuable knowledge and entertainment is our concern🌳 story written by Mmn uswan. 3⃣9⃣ "basu dashi ba sai around 10AM suka tashi' shine ya fara tashi snn Aisha' toilet taje tai wanka snn tasa doguwar rigan jallabiya har takami hanya zata fita' Aisha ina zaki?" "kitchen zanje hadoma breakfast". " idan Akwai rowan Lipton kikawomi kawai". "to shikenan". " fita tai taje kitchen ta dibo masa ruwan Lipton din ta kawo masa' tana fita yashiga toilet wanka' koda tashigo da bata ganaaba ijewa tai a kan table dake gefe takoma b'akin gado ta zauna tana jiran fitowarsa". "yana fitowa daga toilet jawo kajera dake gaban mirrow yai ya zauna kusa da'ita h'ade da zuba mata ido' Aisha na gani h'aka ta kau da kanta gefe". " menene h'aka Aisha ta kalleni mana' murmushi tai snn tadawo da kallonta kansa' shima zuba mata ido yai h'ade da murmushi' snn yace jeki ki dauko min mai". "mikewa tai taje ta dauko tana dawowa ta mika masa' h'aba Aisha ta shafami mana' murmushi tai snn ta dawo b'akin gado ta zauna h'aka ya dunga maka mata kowani bangare na jikinsa mata shafa masa' bayan ta gama yace ga short niker dita dauko misami". " har dama niker?" "Eh' mana". "daukowa tai tasa masa' snn yacire towel d'in da yake daure dashi' bayan ya gama sa kayansa ne yace dauranki abu daya". " me k'uma? " "bakibawa mijinki breakfast ba". "kae zhrdee wlh shagwabarka yai yawa". " Aisha kenan idan banmaki shagwaba ba wazan mawa?. "Allah ko?" "eh mana" "mikewa yai yaje ta bayanta ya rungume ta h'ade da cewa wlh Aisha dan bakisan yadda nake jinki a zcyta bane yasa' inda ana budewa da na b'ude maki zcyta kiga zahiri' amma inaso kinsan cewa kece jiya kece yau gobe da jibi ma h'aka ne' Aisha ina matukar sonki a rayuwata duk lkcn dana wayi gari naga baki tare na tabbata karshen rayuwatane yazo Aisha' Aisha ina matukar son ki Aisha I really love you' jiyota yai ta gabansa suna kallon juna' Aisha ta". " na'am" "kina sona?" "gira kawai ta daga masa tana dariya". "da gske Aisha ta?" "da gske". " kae Aisha naji dadi sosae' amma dan Allah kidaina fushi dani' koda laifi nayi maki zanfi jin dadi da'ace kina fushi dani' kinji Aisha ta". "naji" "yawwa eshat d'in ta' Allah ya barmu tare". "amin" "to zomuje kibani breakfast". " zama yai Aisha na basa a baki har suka gama snn ya mike h'ade da daukar jakansa' ni zantafi kasuwa'". "saika dawo Allah ya kare". " amin ngd". "yana fita saida yashiga d'akin zainab snn tana kwance tana tunanin zhrdee rabonsa da d'akin ta tun jiya da zaifita kasuwa' sallamar sane ya katse mata tunani dagowa tai ta zauna h'ade da cewa ina kwana". " lfy klau' kintashi lfy?". "tun jiya daka shigo da safe lkcn da zaka fita kasuwa baka sake lekowa ba Allah dai yasa lfy ne?". " lfy klau Akwai abinda tsaidanine yasa bansamu leko kiba" "shiru kawai zainab tai tana kallonsa' ni zantati saina dawo" "Allah ya kare yabada abinda akaje nima" "amin kawai yace yafice'yana fita hawaye kawai suka zubowa zainab". "zhrdee yana fita wani irin dadi ne ya kama Aisha tsalle tai ta f'ada katifa tana murna". " zainab tai kukan ta ta gaji tashi tai taje tai wanka ta sanya kaya bagaren Hjy taje ta zauna sukasha hiransu bata dawoba sai bayan azahar snn tadawo bangarenta' da yamma tai masa tuwon masara da miyar kubewa busassa wanda yaji namar rago da busheshen kifi' sbd tasan yana matukar so' snn taje tai wankanta tasha kwalliya cikin riga da sket taje kitchen ta dauko abincin tadawo daki' zhrdee be dawoba sai bayan isha saida yafara shiga d'akin Aisha yakai kusan minti 30 snn yafito zuwa d'akin zainab". "yana shiga zainab ta taresa da sannu da zuwa h'ade da amsar masa jakan dake rataye dashi a kafada snn tace kadawo lfy?" "yah!! kasuwa da k'uma jama'a?" "alhamdllh". " ruwa ta dauko ta mika masa snn tace zakaci abinci yanzu ne' ko sai kayi wanka". "me kikayi?" "tuwon masara nayi da miyar kibewa". " a'a yau banajin ci'kije ki dafami koda shinkafane kafin kafito wanka". "to kawai tace' duk da ranta ya baci amma bata nuna masaba ' toilet tashiga ta h'ada masa ruwan wanka snn tazo ta ninke kayar daya cire tazuba a wardrobe tanufi kitchen' shinkafa ta sake dafa masa wanda bewuce gwangwani daya da rabi ba' tai sanwa da ruwa plast sbd tai sauri' be dauki lkc ba ya daho ta diba ta kawo masa". " zhrdee yana kaiwa baki da sauri ya dawo dashi' zainab na gani h'aka tace lfy? banji dadin abincin bane kamar be dahuba". "a'a b'akin kane' to ko zaka gwada cin tuwon kagani". " to yace' zainab ta dauke shinkafar ta dauko tre d'in tuwon ta kawo gabansa' dibawa tai ta zuba masa a plate' snn yafara ci' zhrdee yaci tuwon sosae yana ga mawa zuwan ta kwashe ta medasu kitchen snn tadawo suka kwanta'. "yau kam yadda suka kwanta h'aka suka tashi itama zainab be dameta ba' da asuba kafin yaje masallaci saida yashiga d'akin Aisha ya tada'ita snn yafice". "suna dawowa yashige bangaren Hjy nan ya zauna har eight snn dawowa' dama tun tashi zainab da asuba bata koma bcc ba' tana idar da sallah tashiga kitchen h'ada masa abin breakfast' tana kitchen taji shigowarsa gani bata gama yasata shiga daki ta h'ada masa ruwan wanka a cewarta kafin yafito daga wankan ta gama". "yana shiga ta koma kitchen taje ta karisa kafin yafito tagama kwashewa tai takai daki' zhrdee yafito wanka daure da towel a kugunsa yaje gaban mirrow ya zauna' yana zama zainab ta dauki dayan towel din dake gefen gado tazo tana goge masa bayansa' banza zhrdee yai da'ita kamar besan tanayiba zainab na gama goge masa baya ta dauko mai har takai hannu zata fara shafa masa' me zakiyi?" "shafa maka zanyi". " kae Dan Allah banison iskanci' ni yaronki ne da zaki shafawa mai". "hannu yakai zai amsa da sauri zainab ta kaudata hannu tana f'adin Dan Allah kabari na shafa maka mana". "zainab badake nake ba". " dani kakeyi amma dan Allah bakari na shafa maka ". "tsayawa yai yana kallonta". "zainab ta fara shafa masa tana cewa kae baka ma ji dadi matar ka na shafa maka mai ba". " da sauri zhrdee ya janye kafarsa h'ade da cewa eh d'in ban gogeba". "to yi hakuri wasa nake maka kawo na karisa kaji maigidana na kaina". " zahradee najin h'aka kansa yakara fashewa yai girma' mika mata kafar yai h'ade da bonewa' zainab taci gaba' tana ga mawa ta dauko masa kayan da zaisa da taomakontane yasa kayan' suna gamawa yaje gun da ije masa breakfast bayan su zauna ta dauko plate ta dibi arish da kwai ta zuba a plate snn ta h'ada masa tea har zhrdee ya dauki spoon zaifara ci' da sauri ta dakatar dashi' amsa spoon d'in tai snn ta diba h'ade da cewa b'ude makinka". "me zangani h'aka?". "kae dai b'ude". "ke wlh bazan b'ude ba' banason rainin wayo' kodan kinga ina wasa dake shine zaki kawomi raini' da karfi ya fisge spoon d'in snn yafara ci da kansa' ido kawai zainab ta zuba masa h'ade da mmkin zhrdee' shiko ko'a jikinsa yana gama ci ya mike itama mikewa tai ta dauko masa jakarsa zainab mikomi mana". "muje na rakaka bakin mota snn na baka jakar". "tana mgnr ne h'ade da tafiyarta har takai bakin kofa da sauri zahradee ya bita zai amsa' rike jakar tai da karfi suka kamayi kamar suna wasan kokuwa' da h'aka ta jasa har parlour daidai lkcn Aisha na fitowa daga dakinta' shikuma zahradee yana rike da zainab ta baya' idan ba kagane ba zakace rungumarta yai' yana f'adin Dan Allah zainab kibari mana". " Aisha na ganisu da sauri takoma daki sbd b'akin ciki' gani h'aka yasa zhrdee binta d'akin' duk da itam zainab taji haushi sbd yadda yai kamar yana tsoron Aishan amma sai ta dan ne bata nuna komai ba" "zahradee yana shiga da cewa Aisha meyasa kika koma ciki k'uma? inace abune zakije dauka?". " kamar bazata tanka masa ko me tagani k'uma ohoo tace a'a nafasa" "duk da shima yasan rantane ta baci amma ya matse' yace toni zanfita kasuwa saina dawo". "saika dawo kawai tace ta juya baya". "ko kina bukatar wani abu". "bana bukatar komai". "to shi ke natafi' yana fita zainab dake b'akin kofa tana jiransa da sauri ta rungumesa ta gefe ta rakasa har bakin mota saida yashiga snn ta mika masa jakar' h'ade da daga masa hannu tana masa bye bye' shiko gogan bemasa tanayiba' itama zainab d'in bata nuna ya dametaba sbd tasan ba mmki Aisha na kallonsu" "saida yafice yabar g'idan snn takoma ciki'ashe kuwa Aisha nanan na lekarsu duk abinda sukeyi" "zainab na shiga d'akin ta shiga taje ta dauko kayan abincin da zhrdee yaci ta kai kitchen daga nan ta tsaya parlour sbd ta gyara duk da tai ba dattine yai ba sakamakon babu wanka yake shiga gun kam kakkabewa kawai tai h'ade da goge su TV' Aisha najin motsin zainab a parlour ta fito zainab aikine akeyi h'aka?' " wlh kuwa Aisha' kintsshi lfy?" "klau lefa" "klau wlh". " zainab kinga wayar da zhrdee ya siyemi ko". "Aisha tai mgnr ne h'ade da nunawa zainab wayar". " Allah sarki ashe har ya siyo dama cewa yai saiya samu kudi zaisiye mana tare sbd yanzu duk ya kwashe kudinsa yai order kaya da naga h'aka sai nace ya siye maki kawai tunda ni inashi yace a'a saidai ya siye mana mu biyu ko k'uma dukkanmu mu hakura da kar wlh na shawo kansa yace zai siye maki". "faskewa Aisha tai tace da gske ayya ai nagode" "Aisha tai mgnr ne kawai amma a zcyrta ba h'aka yake ba" "juyawa tai ta koma daki' tana shiga tai hurgi da wayar kasa screen d'in yafashe' zama tai b'akin gado tana namfarfaki" "itama zainab d'akin ta ta shige bakin mirrow ta zauna tana ajiyar zcy' h'ade da mmki zhrdee" "da yamma zhrdee yana dawowa daga kasuwa Aisha ya fara shiga lkcn tana zaune akan sallaya gani sallah takeyi yasashi fita zuwa d'akin zainab' duk da abinda yake damuta a zcy amma ta dan ne ta amsheshi hannu bibbiyu kamar yadda tasaba yau dai beci abincin sosae ba' yana gama ci ya kwanta yace zainab tai masa tausa sbd jikinsa yai tsami". " zainab bata musaba h'aka taci gaba dayi masa' tana ciki yine tace zhrdee" "na'am lfy?" "dama jira nake kadawo na sanar dakai wlh kwana biyun nan banajin dadin jikina' gaba daya sainaji jikina yaimi nawi" "cikin naki zaikai wata nawa?" "kamar zaikai wata gudu fa" "abu a jikinki kice bakisan watan nisaba" "to Ai ba asibiti naje ba banle nasan watan nisa' nidai Dan Allah idan ma bakada lkcn da zaka kaini da kanka toni kabani kudin taxi naje da kaina" "zainab kenan kiyi hkr zuwa wani lkc sbd a yanzu banida kudi' amma idan nasamu da kaina zankaiki kinji" "shiru zainab tai bata tankasaba sbd tasan ba rasa kudi yai ba" "zhrdee dake rigigine yace kici gaba mana" "batare da ta tanka kasa ba sauka tai tabar masa gadon" "zainab ba dake nakeyi ba? " bazan yiba zhrdee" "what???? " Eh' nace bazan yiba" "why??? zainab" "ni asibiti zanje ka hanani kudi amma ka'iya kwasan kudi sama da fifty thousand ka siyewa Aisha waya" "waya ce maki na siye mata waye?" "ita ko karya ne?" "ni ban siye mata waya ba' amma bari naje na sameta" "mikawa yai ya nufi d'akin Aisha' da sallama ya shiga tana b'akin gado zaune shima zama yai kusa da'ita' na shigo dazu kina sallah" "eh' kadawo lfy' " lfy klau' ya kasuwa?" "alhamdllh' ke k'uma Aisha h'aka akeyi sbd Allah daga na siye maki waya saiki fadiwa zainab?" "wayar banza' wayar wofi' Ashe a rayuwa bazaka iyasiyemi wani abu ba sai ansaka'ashe duk soyayya da kake cewa kanami karyane" "h'aba Aisha wacce irin mgn kikeyi h'aka? waya ce f'adi maki h'aka?" "zainab" "itace ta f'adi maki h'aka?" "eh" "ina zuwa'yana fita suka hadu da zainab a parlour zata shige kitchen da kayan abinci a hannu' ke zainab zonan" "gani ta tsaya masa a gaba' waya f'adi maki na siyewa Aisha waya? " ita " "kowa dawa Aisha kira yai tafito parlour itama tace gani' Aisha waye ya siye maki waya?" wacce waya kake mgn akai? " "ke zainab me kikace" "wayake maki karya zainab?" "kece karyaciyar banza'iji kamar zainab kenan" "tsawa zhrdee ya daka masu h'ade da cewa ya'isa haka" "Aisha taci cewe nice makaryaciya zainab?" "ance d'in banza kawai".. 'kafin zainab ta rufe baki tuni Aisha ta dauketa da mari'itako Zainab kofin da zhrdee yasha ruwa dashi ta dauka ta kwadawa Aisha' Aisha na gani h'aka ta dauki kofin zata kwadawa zainab a ciki' da sauri zhrdee ya shiga tsakiyarsu kofin ya sauka akan zhrdee' duk da h'aka be'ishi Aisha ba saida tasake dauke Zainab da kari' Zainab bata damu da cikin dake jikinta ba' tsalle tai ta haye Aisha suka kama danbe" "zhrdee yayi iya kokarin Zainab ta daga Aisha sakamakon Dan neta da tai' amma Zainab taki' duk da dan neta da tai bata daina nushinta ba' gani h'aka yasa zhrdee ya ciro igiyar radio ya h'au Zainab da duka jin zafin dukan yasa Zainab ihu tana kuka babu arziki Zainab ta daga daga kan Aisha" "daidai lkcn su yya Shamsudee sun shigo gani abinda sukeyi kai kawai suka kada snn suka karisa cikin g'idan" "Aisha na mikewa tace saita rama' zhrdee ya shiga tsakiyarsu Zainab na bayan zhrdee tana kukan dukan da zhrdee yai mata' gani Aisha ta nace yasa zhrdee yace zainab tazo ta duka tabawa Aisha hkr'". "me kace zhrdee? "zokibata hkr" "wlh bazan bayar ba" "bazan bayar ba" "ban'isa dake bako?" "ka'isa amma wlh ko kasheni ne bazan bata hkr ba" "kagani ko dan Allah kabari nai mata dukar tsiya na nuna mata niba sa'arta bane" "a'a Aisha kibarni da'ita kawai' " Zainab duka ki bata hkr' kut Allah ya wasake na rasa wanda zanbawa hkr sai kishiya' kishiyarma kucaka irin Aisha wawiwa dabba".. "sake dauketa Zainab da mari' tana kaiwa zhrdee shims yana kaiwa Zainab' Zainab na gani zasuyi mata taron dangi a guje tana nimar abinda zata kwadawa Aisha' can ta hango CD da sauri taje ta fisgo ta halbawa Aisha' Aisha na gani h'aka a guje ta ruga Zainab ta sake binta da guje' zhrdee shima binta yai tuni zainba tasake kama Aisha da danbe' duk duka da Aisha kewa zainab besa ta karaya ba' saidai a wnn karo bataci nasara akan Aisha ba' sakamakon ciwon da cikinta keyi' zhrdee yana zuwa yasake hawan Zainab da duka' duk dukan da yake mata akan Aisha take ramawa'duk da itama aishan ba kyaleta tai ba' Zainab na kuka tana ramawa gani abin zaimata yawan gashi batada matayi ihu tasa da karfi takaiwa Aisha cizo' jin ihu ne yasa Hjy cewa lfy nake jiyo ihu a bangaren yarannan?" "a lkcn ne su yya Shamsudee yace au wlh mancewa nayi surukanki sunanan suka f'ada" "dafe karjinta tai h'ade da cewa f'ada fa kace?" "eh wlh" "da sauri Hjy ta mike zuwa gun' zhrdee yayi2 Zainab ta sakarwa Aisha hannu amma Zainab taki' idonu Aisha suka cika da kwalla' jikinta har rawa yakeyi" gani h'aka yasa zhrdee yaiwa Zainab mara a baki wanda H'akan yasa b'akin Zainab ya fashe' a gigice Zainab ta saki Aisha' zhrdee zai sake kaiwa kenan saiga Hjy' da sauri ta kariso gun tana tambyar lfy?" "kuka Zainab masa h'ade da barin gun tashige d'akin ta' itama Aisha d'akin ta ta shige yarage zhrdee kawai' kai zhrdee garin yaya h'akan yafaru? nima kaina bansan abinda yahasu ba amma?.. " kamar yaya zakace bakasan abinda ya hadasu ba? shine gani kana dukan Zainab? " '"eh itace ta fata hayewa Aisha k'uma nace ta bari taki shiyasa". "to Dan Allah a kiyaye k'uma banaso na sake gani h'aka" "insha Allahu" "juyawa tai ta koma ciki' tana shiga zhrdee yabi Aisha daki' yana shiga yasami Aisha zaune rike da hannunta tana numfarfaki' da sauri ya karisa gabanta ya duka h'ade da riko hannu yana f'adin hannu ne ko?" "duk da ba ciwo taji a hannu ba sai dan zafin da yake yimata sbd jan da yai amma Aisha tace eh zafi yakemi" "to tashi muje asibiti" "a'a ka barshi kawai.. " Aisha banaso musu tashi kawai muje" "mikewa tai ya dauki key mota suka fita". " Zainab na daki tana faman kuka sbd ciwon da cikinta keyi' ji takeyi kamar zaifita' sai faman juyi takeyi a tsakar daki tana kuka" "wani prvt hospital zhrdee yakai Aisha sukaga doct maguguna aka basu' zhrdee basu dawo g'ida ba saida yabiya da'ita ya siye mata yoghurt da gasashiyar kaza snn suka dawo g'ida' kai tsaye dakinta suka shiga bayan ya tube itama ya tubeta ya daura mata zani har da kamata yai snn ta zauna da kansa yake bata namar abaki h'ade da yoghurt tana ci tana shagwaba' sai faman sannu yake cetama' bayan ta ko shine ya dauko ledar magani ya cire ya bata tasha' ta nasha tace bcc takeji' da kansa ya kamata ya kwantar da'ita' shima kwanciya yai kusa da'ita yana rungume da'ita'. juyi kadan tai saiyace sannu" "shiru2 Zainab nasa idon zuwan zhrdee amma shiru' ji takeyi kamar tatashi taje ta kirashi ko tasanar dashi halin da take ciki amma gudu kada Aisha taga gazawarta yasa ta dan ne' taci gaba da nakudar da bana haihuwaba' tubewa tai tarage daga ita sai zani ko pan bata bari ba' kuka kuwa ba'a mgn" "da yaudara Aisha tai ta jan zhrdee har suka kusan kwana tare'dan zhrdee bekoma dakin Zainab ba sai asuba lkcn anfara kiran sallah snn yakoma d'akin' ko kafin snn ma ciwon ya f'ada mata' yana shiga yaganta kwance a kasa kamar me bcc amma ba bcc takeyi ba" "be tanka mata ba gado ya h'au y kwanta yana jiran lkcn tafiya masallaci yai' kama katakwan gado Zainab tai ta mike Zainab h'ade da cewa sai yanzu kaga damar dawowa?" "eh yanzu gani damar dawowa" "amma kasan a nan kakek?" "sai me idan anan nake" "nidai ba wnn ba wlh zhrdee banida lfy ko bcc ban'iya ba sbd ciwon ciki kamar wanda zan haihu" "to meya hanaki haihuwar idan da gske ne' " da gske fa" "ke kinga alamar wasa a idona?' " zhrdee ". " meye ne?" "to wlh da safe babu abinda zai hanani fadiwa Hjy' k'uma Allah ya'isa kwanar dakai a dakinta" "dama Allah isashene ai' ni wlh baki birgejiba tunda bazakije yanzu ki f'ada mata ba" "Allah ya'isa mugu alzalumi kawai' kuka Zainab tasa" "sbd kada ta damesa pilo yasa ya tushe kunninsa" "zahradee yana fita masallaci Zainab ta sabi hijab d'in ta zuwa g'idan su". 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITERS F.O.W.☘. 🌳impacting valuable knowledge and entertainment is our concern🌳 story written by Mmn uswan 4⃣0⃣ "Zainab na fita takami hanyar g'idan su' tayi tafiya sosae dan tai nisa da g'ida' yawanci masallatai su idar da sallah' zhrdee ma yadawo g'ida d'akin Aisha ya shiga ya sameta ta idar da sallah' tana tafe a hankali sbd ta gaji da tafiya gashi gari be wayeba banle ta h'au napep k'uma kodama tasamu napep d'in batada ko sisi a hannunta" "tsayuwa tai tai shiru tana tunani kala2 a zcyrta wata zcyr tace jeki kawai wata k'uma tace a'a Zainab idan har kikabar g'idan sbd Aisha shikenan zata rainaki' zatace kin tsorata da'ita gara ki koma kawai' kuma idan ma kikaje g'ida Abba bazai bari ki zauna ba' dawowa dake za'ayi kinga koba komai Aisha tasamu na gari' tsayuwa tai tai shiru' a pili k'uma tace kaeeee Aisha wlh kinyi kadan nabar g'idan sbd ke a fusace ta juya takami hanyar g'ida" "kafin Zainab ta'isa g'ida gari ya waye tangaran'tana shiga zhrdee yana fita daga d'akin Aisha'gani Zainab ta shigo da sauri yace daga ina? banza tai dashi ta shige' da sauri ya bita Zainab badake nakeyi ba? tana shiga d'akin shima ya shiga h'ade da rike mata hannu yana f'adin ba dake nakeyi ba Zainab" Zainab ta fisge hannunta' shigewa tai zata kwanta fisgota yai yana f'adin badake nakeyi ba Zainab' fita nayi" "kika fita zuwa ina? k'uma da iziniwa? " bansani ba" "a fusace zhrdee ya shakota da iziniwa kika fita Zainab' Zainab tai shiru' ba dake nakeyi ba' Zainab babu amsa sbd irin shakan da tai mata k'uma ga dukani alama yanzu yai fushiga koma menene zai iya yimata na rantse da Allah idan kika kara fita koda nai da kofar g'ida ne duk abinda nayi maki ke kikaja' zhrdee ya karisa mgnr ne h'ade da igijeta gefe f'adi tai a kasa tasa kuka' toilet yashiga yai wanka be tsaya breakfast ba ya shirya ya fita kasuwa" da Zainab tai kukanta ta gaji' da taga kukan bazai fisheta ba sbd yunwa da takeji' mikewa tai tanufi kitchen taje h'ada abin karyawa arish ta dauko tana ferewa saiga Aisha ta shigo kitchen d'in' itama dibawa tai tana ferewa kowa na aikinsane babu wanda ya tankawa d'an uwansa Zainab ce tariga Aisha gamawa sai ta kunna gas ta dora mai' itama aisha mikewa tai ta kuna dayan gas d'in ta dora mai snn taje taci gaba da yayyankawa kananu mai yai zafi sosae snn tazuba a wuta' mai ya dunga tsalle yana dallan Zainab a hannu' Zainab ba hkr tace kiga gani ko?" "banza da'ita Aisha tai' daga snn Zainab bata sake tanka mata ba' dauko abinda take juya arish dashi ta tsuma a cikin mai snn ta yarfewa Aisha a hannu' a gigice tace h'aba Zainab baki ganine?" "Ashe kina mgn? na dauka da kurma nake tare" "a'a tsaya nema" "ke zakiga tsaya' tsaya k'uma yabiki" "wlh Zainab kyaleki nakeyi fa" "idan baki kyaleniba me zakimin?" "koda yake be kamata na biyeki ba' ko bakin cikin dana barki dashi na jiyama kawai ya'isheki' kinaji kina gani na hanasa kwana a d'akin ki sbd na isa" "duk da mgnr yaiwa Zainab zafi amma ta matse tai dariya h'ade da shewa snn tana Allah sarki Aisha d'an bakisan mgnr da zhrdee yakeyi akanki bane yasa h'aka ni wlh har tausayi ma kike bani" "cikin kosawa h'ade da faskewa tace sai me? banle ma nasan duk abinda zhrdee zai f'adi akaina saidai yabo' ba irin su oh oh ba wanda ba'asan darajansu ba" "ni wlh Aisha ma mmki kike bani idan banda rashin kangado irin naki ni har zanyi fariya da tuniya dan miji ya kwana a dakina' mutumi dayace yana dai tarawa dake ne kawai amma badan dadi ba'idan zaki lura duk ranar girkina har dawowa yakeyi da rana amma kefa idan yaje yaje kenan" "Aisha taji zafin mgnr sosae amma matsewa tai tace sae me? wlh sbd rashin dadina ko yana kuka ne sai yayi" dariya Zainab tai h'ade da cewa tana f'adin Allah sarki Aisha" "Zainab ai kece abin Allah sarki' kije ki tambyi kowa irin soyayyar da zhrdee yakemi' sbd ni har kwanciya hospital saida yai' ba kamar ke da'aka cusa masa ba" "shi zhrdee d'in ne ya f'adi maki h'aka" "ohh! ho!" nidai nasan ba karya nayiba " "da haushi yakama Zainab cewa da h'aka dai gashi zan bashi abinda kika gagara" "me kenan" "baby' ko karya nayi banza kwanko kawai' juya".. "kafin Zainab ta karisa Aisha ta dauketa da mari h'ade da ihu" "daidai lkcn Hjy na fitowa jin ihu Zainab yasa ta kariso da sauri h'ade da tambyar lfy?" "gani Hjy yasa Zainab cewa dama santsine nayi zan f'adi shine nayi ihu". " garin yaya? "h'aka kawai Aisha ta taimakami ta rikeni" "a'a to Dan Allah kirinka ki yayewa' kinga bake kadaice bako" "Dan Allah ki kiyaye banason abinda zaije ya dawo" "to zan kiyaye" "Aisha na tsaye tana kallonsu' Hjy na fita Zainab ta kwashe da dariya". "da yamma zhrdee yana dawowa ya siyewa Aisha wata sabuwar waya wacce tafi nada tsada da'kyau" "Aisha bajewa tai tai murna sosae hade da nunawa zhrdee soyayya' yau ko leka Zainab beyiba yananan like da Aisha tana kwance yana zaune a batanta suna hira yana matse mata jiki a hankali Aisha tace my baby" "na'am you a lone, " Dan Allah gobe inaso naje uguwa" "uguwa kuma"s sweedy?" "OK zakije dubomi ummata ne?" "a'a gun ubaida zaki" "ubaida k'uma?" "ubaida tafi umma kenan?" "a'a ba haka bane" "to menene" "just" himmm" "just what dear?" "idan bazakije gun umma ba babu inda zaki" "to naji zanje" "Zainab zama tai tana jiran zhrdee ya shigo amma shiru' ita kenan har shabiyun dare tana zaman jiransa amma be shigoba' ga yadda takeji a jikinta babu dadi kwanta2 zama tai taci kukanta sosae" "shiko zhrdee suna can suna holarwarsu da Aisha' kwata2 yamance da mgnr Zainab harda guje guje sukeyi suna zagaje daki ita dashi" "da asuba suna tashi zhrdee yatada Aisha yana rungume da'ita suka shiga toilet sukai wanka snn sukai sallar asuba' suna idarwa yaje ya gaida Hjy da Abba" "yana fita yaje d'akin zainab lkcn tana kwance takasa tashi dan ko sallar asuba batai ba' yana shiga a b'akin gado ya tsaya h'ada da cewa kintashi lfy?" "lfy klau" "iya kacin abinda yace kenan ya juya zai fita" "Zainab tace zhrdee" "meye ne?" "tsayuwa yai a tsakiyar daki yace ina jinki" "rarrafawa tai ta sauko sako daga gadon gabansa tazo ta duka har kasa gwiwa bibbiyu tana dafe da kafarsa hawaye ne kawai ke zuba tace Dan Allah Dan annabi ka taimakeni ka kaini hospital wlh banida lfy" "Zainab kenan aini bance bazan kaiki hospital ba' amma idan kinaso na kaiki sai kinje kinbawa Aisha hkr akan abinda kikai mata" "cikin kuka Zainab tace h'aba zhrdee kasan abinda kake f'adi kuwa? Aisha fa kace?" "kwanta da gske" "a gskya bazan iyaba naje nabawa kishiya hkr" "OK ban'isa dake ba kenan?" "ka'isa amma kasan ba abinda yakamata kayi ba kenan ko' idan har sukai laifi kamata yai kahadamu dukkanmu mu biyu kai mana f'ada idan ma na hukunci ne kai mana amma ba kazabi daya daga ciki karinka fifitawa bako?" "wah!! na fifita a tsakaniku?" "kafin kowa sani" "zhrdee nasan duk wnn abubuwan kanayimine sbd kana gadaran iyayenka ne suka haadamu badan kaine kagani kace kanasoba kamar Aisha shiyasa duk kakemi wnn abubuwa' amma abu daya da nakeso ka gane shiga koda h'akan be faruba idan har Allah ya rubuta saika aureni wlh baka'isa ka kaucewa tsarin ubangiji ba' nima k'uma kaina da nasan basona kakeyi ba wlh da ban'amice ba'amma babu komai h'aka Allah ya kaddaromi" "a lkcn jikin zhrdee yai sanyi sosae' yace Zainab waya f'adi maki bani soki?" "cikin kuka tace h'aka ne mana' bagashi har f'adi wa Aisha kakeyi ba" "shiru yai sbd yasan mgnrta gskya ne" "nidai dan Allah Dan soyayyar da kakewa iyayenka Dan albarkaci d'an ka dake cikina ka taimakeni ka kaini hospital" "to naji amma gskya ba yau ba sbd inada wani uziri a kasuwa k'uma kinga banaso kibi motar haya' kibari duk lkcn da nake free zankaiki da kaina" "h'aba zhrdee kodan ba jikinka bane" "matsalata dake kenan Zainab' rashin jin mgn" "Dan nayi mgn saikace inada matsala zhrdee babu komai jeka kawai" "kamar yana jira da sauri yafita zuwa d'akin Aisha' yana shiga d'akin Aisha ita k'uma snn tana kitchen tana h'ada masa breakfast gani h'aka yasashi shiga wanka' saida yai wanka snn ya karya itama tai wanka suka shirya cikin shadda iri daya suka fita zhrdee na rungume da Aisha har su kusa da mota Aisha tace tayi mantuwa mikewa" "inda zhrdee yabar Zainab anan take tai shiru tana kwalla' wuf taji an fado mata akai' da sauri tajuya Aisha tace dama fita zamuyi da baby shine nace bari na sanar dake SBD kada kiji shiru" "banza Zainab tai da'ita" "Aisha na fita da kwashe da dariya snn tafita gun zhrdee' tana fita ya b'ude mata mota tashiga ya rufe" "Zainab zama. tai dirshan taci gaba da kuka" "suna hanyane zhrdee ya dauki kudi yabawa Aisha wai taba umma tasiye goro snn yabiya kasuwa ya sire mata zannuwa ya siye sabulai ya h'ada mata dashi suka karisa g'ida" "bayan ya'ijeta ne ya koma kasuwa' Aisha bata wani zauna a g'idan suba taje g'idan ubaida' ubaida na gani Aisha ta shigo a guje taje suka rungume juna zuwa daki' Aisha kenan ashe talakawa na ganiku?" "kinjiki dai ubaida" "da gske" "himm ubaida kenan'ina Bbn Abba?" "Bbn Abba yatafi kasuwa kinsan abinka ga talaka" "dariya sukai h'ade da shan hannu' kwana biyu' ya k'uma fushi da miji" "h'aba ubaida Ai tunda kikaimi f'ada nadaina" "karma ki daina kina zaune a kwace maki zhrdee" "habadai badai zahradee ba" "Allah ko?" "da gske" "Allah sarki namance ban tambayi abokiyar zamanki ba? wlh yarinyar tayimi sbd kirkinta" "" Allah ko? dan bakisan waye Zainab ba shiyasa " "koma menene dai wlh Aisha kema kinada naki laifin" "ko zansan dalili dayasa kikace h'akan?" "kwarai da gske sbd kace babba akanta nasan zama da yara kananu a matsayin kishiya dole saikai hkr sbd masu yawancisu basuda kunya gani suke kaiku daya sbd abinda kika sani suma susani amma idan kikeyi hkr kika dauka ba komai bane wlh duk rashin kunyarta saita saurara maki yau da gobe bebar komai ba' amma idan kika biyeta h'aka zaku zama kaman mahaukata" "wlh ubaida kina f'adin h'aka dan bake bace" "kamar yaya Aisha?" "h'aba sbd Allah kamar Zainab tarinka zagina ina kallonta?" "kinji kenan' wlh duk rashin kinyarta idan baki biyeta dole ta saurara' ki duba lkcn da Bbn Abba yai aure babu irin cin kashin da batamiba a g'idan nan amma be dameniba sbd Bbn Abba yana taka mata birki mafi yawanci lkc nice ke hanashi idan tsiyarsa ta taso akanta yake saukewa' itama da taga h'aka dole ta sauko daga dokin da ta h'au nakoma tamkar wata uwarta' da lkcn yai nima kaina bansan lkcn daya bata takardaba' ina daki kukanta kawai naji" "to kinga inda a lkcn da suke amarci na biyeta na tabbata da nice nabar g'idan ba'ita ba' banle ma nasan yadda zhrdee yake matukar son ki bazai bari Zainab ta rainaki ba' ke kuma sai kiji tsoron Allah duk lkcn da kikaga zaiyi wani abu wanda ba daidai ba kiyi kokarin hanasa' ki nusar dashi kyakkyawar hanya idan ba hakaba kika biyeshi kuka zalumci Zainab wlh Allah bazai barkuba" "kamar yaya ubaida?" "sbd nasan halin namiji sarai idan yana sonka babu abinda bazaiyiba Dan yaga ya faranta maka rai' amma k'uma duk da h'aka ita kanta da kike gani ya aureta badan yana sonta ba' a duk lkcn da bukatarsa ya kaisa gunta bazai hanashi f'adin wani abu nakiba a gunta sbd yaga yasamu biyan bukatarsa' sbd mafi yawanci maza idan sunada mata biyu tofa makinsu biyu ne' h'aka ma idan Ku uku ne bakinsa zaizama uku' idan ban manceba kafin Bbn Abba yarabu da amaryansa akwai lkcn data cemi yace mata be taba sani f'adin mace ba saida ya aureta' ni k'uma dayazo dakina cemi yai dolene yasa yake saduwa da'ita' to kinga a lkcn dabadan Allah ya fahimtar dani ba kisan ba karami tsiya zamuyi" "to ke kinyarda da gske kenan?" "kwarai da gske sbd a lkcn kusan kullin saitami goro akan h'aka' nikuma da abin yaimi zafi har nayanke shawarar bari mata g'idan' amma k'uma danazo nayi wani tunani sai bafasa tafiya sbd nasan idan naje g'ida ba lalla bane abarni nadawo g'idan shu'aibu ba' Aisha kinfi kowa sani yadda muke son juna' shiyasa na fita harkanta' gani h'aka sai taga kamar tsoronta nakeyi' taci gaba da fadimi irin mgnr' ranar data kureni nima na f'adi mata abinda yake fadimi' hnklinta ya tashi yana dawowa ta tirkeshi ina kwance a daki ina jinsu' to kinga da banyi hkr bafa" "Dan Allah Aisha kiyi hkr Ku zauna lfy da Zainab k'uma ki nunawa zhrdee yai adalci a tsakaniku" "shiru Aisha tai tana rauraran ubaida" "k'uma yaya mgn ciki ki?" "wani ciki k'uma?" "da farko lkcn da kika auri Nasir inace kince kintaba samu ciki?" "eh nasamu" "bayan fitarsa kinkara samu wani?" "baki sakeba?" "eh" "kafin kiyi barine kikayi ciwo ko baya bari ne" "kafin nayi barine" "bayan h'aka k'uma baki sake samu wani ciki ba" "to idan ba wani ikon Allah ba zaki iya samu ciki" "meyasa kikace h'aka ubaida?" "kintuna Rabi'a Zakariyya da kai secondary tare" "eh na tunata" "kinsan tun bayan aurenta da tai wani ciwo akace bazata haihuba" "to yadda ta haihu' wani ciki nema da'ita" "Allah da gske ubaida?" "Allah sarki na tayata murna" "to yanzu abinda yakamata muyi shine zanyi kokari na tambayi Bbn Abba yabarni naje g'idan ta na tambaya maki ita wani hospital ne sukaje da mijinta har suka samu waraka" "anya da gske kina gani zansamu kuwa?" "ke matsalata dake rashin wayo' me zaihana tunda da farko kintaba samu da kamar tun farko baki samu bane sai kice" "to shikenan ngd sosae kawata shiyasa nake sonki" "dariya sukai" "amma Dan Allah Aisha ku zauna lfy da Zainab' bakisan rashin zaman lfy a g'idan magidanci yana rufe masa kofofin samuba?" dan Allah ku rungumi mijinku ku zauna lfy da abokiyar zamanki' ko mijinku kofofin samusa yakara budewa' yanzu ma kenan be rageku da komai ba' ina ga yafi h'aka?" Allah ya baku miji kyakkyawa ga kudi ga kyau kamar shine yai kansa' har gara ma Zainab tunda ita farace tas' ke kuwa f... "kinaso kice ta fini kyau kenan?" "a'a ni banceba" "to yanzu meye lfy?" "lbrin me?" h'aka kawai nabaki kizo kisa zhrdee na ihu' dariya sukai h'ade da tafi" "daukowa tai ta bawa Aisha wanda zata bata snn sukai sallama' da yamma zhrdee yazo ya dauki Aisha suka koma g'ida' kai tsaye dakinta suka shiga Aisha na ije mayafinta taje da sallama d'akin zainab' Zainab na jinta amma ta kyale da Aisha taji shiru ta dauka ko bcc ne tai yasata ta koma d'akin ta' ta shiga toilet yi fitsari taga period yazo mata yatsa ta ciza sbd bayaso h'aka ba" "fitowa tai ta shirya jikinta' shiko goge wanka yashiga yai yasa kayan bcc yazo kwanciya yau kam dole a saurara' shima kansa beyi dadi ba' dan a hannu yake' h'aka ya matse suka kwanta" "washe gari da safe bayan zhrdee ya fita kasuwa Zainab ta lallaba tafito kitchen SBD yunwa takeji' itama Aisha ta fito daga d'akin ta zuwa kitchen tana gani Zainab a kitchen tace Zainab ina kwana" "can kasa ta amsa da lfy klau' daga sann bata sake tankawaba sbd mgn ma aiki take gani" "Zainab lfy kuwa?" "banza tai da'ita" "tana diban ruwan zafi takoma daki' shiru Aisha tai tana kallonta" "tunda Zainab tashiga daki bata sake fitowa ba' har dare' ko abinci batayiba.tana kwance kawai tana faman juyi a gado ga jikinta yafara kunburi' tana kwance har zhrdee ya dawo kasuwa saida yashiga d'akin Aisha suna gaisa h'ade da hira snn yafita zuwa d'akin zainab' koda yashiga danita yai kwance' tace kadawo" "nadawo ya g'ida?" "lfy klau' ya kasuwa" "alhamdllh" "tubewa yai ya shiga wanka' duk a lkcn Zainab na kwance' har yafito bata tashiba Zainab tashi ki dauko min abinci na mana" "banyi ba" "sbd me?" "banza tai dashi' shima dagaya haka be tankaba tea kawai ya h'ada yasha snn ya kwanta' can cikin dare Zainab taji zhrdee yana shafeta' da sauri tace lfy?" shiru yai yaci gaba' gani abinda yake da niyar yi da sauri tasa hannu zata turoshi' da karfi ya riketa h'aba zhrdee wann wani irin rashin imani ne? tun yaushe nake cemaka banida lfy amma baka kulani ba' Dan ma tsabar rainin wayo tun yaushe rabonka dani?" yadda yazo d'akin ga h'aka kake fita sai yau da Aisha ta haka kanta snn zakazo guna?" "Dan Allah Zainab ki tsaya wlh ba h'aka bane" "idan ba h'aka ba menene?"... " kafin ta karisa Dan ne mata baki yai himmm". "kuka Zainab taimasa sosae yana kwance yana numfasawa Zainab tace Allah ya'isa mgu kawai" "wlh idan kika karami Allah ya'isa saina fasa maki baki".. " koda safe Zainab bata iya tashiba tana kwance zhrdee yai wankansa ya shirya zuwa kasuwa' har Zainab tabar girki zhrdee beyi tunani kaita hospital ba" "bayan kwana biyu gaba daya ta aune lallabawa tai ta mike zuwa d'akin Hjy' tana tafe tana kuka dakar take tafiya sakamakon zafin da kafarta yake mata". " tana shiga d'akin Hjy kadan yarage ta f'adi da sauri Hjy ta tareta tana fadin lfy Zainab meya sameki h'aka? " "Zainab na kuka tace banida lfy ne" "kamata tai ta zauna tana kare mata kallo taga tuburin da tayi" "daukarta tai zuwa hospital' tana isa takira Abba ta sanar dashi gasu a hospital snn ta sanarwa zahradee' cewa yai gashinan zuwa' suna shiga gun doct ya dubata yace jinitane ya h'au sosae k'uma tana bukatar hotu' daki aka kaita a take doct ya samata drip da alluran bcc" "Abba da zhrdee sukazo tare a waje Abba yatsaya zhrdee ya shiga ciki d'akin' gani Zainab na bcc yasa Hjy tace muje waje' suna fita tace garin yaya Zainab ta zama h'aka?" "shiru yai yana sushe2" Hjy tace ba dakai nakeyi ba?????? 📖🖊 ☘☘ ☘ AURE IBADA NE FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳impacting valuable knowledge and entertainment is our concern🌳 story written by Mmn uswan baki ko harshe basuda malaman da zasu furta waje godiya a gareku' a gskya naji dadin sosai yadda kuke bibiyan littafina mai' nagode nagode Allah yabar kauna da zumuci amin🤝, TSOKACI Ga masu cewa suna da nasama littafin be dace dashi ba' kuyi hkr ba haka bane rashin fahimtane' ko k'uma nace rashin sani menene AURE yake nufi yakawo h'aka' amma ga wanda yasan me ake kira AURE k'uma me AURE yake ciki tabbas yasan tana cike da kalubale kala kala' walau ka'auri wanda kakeso ko k'uma wanda bakaso' shiyasa tun farko idan baku manceba na sadaukarwa wanda Allah ya jabceta ta hanyar AURE k'uma ta cinye zarabawan' Dalilin dayasa nasama littafin suna kenan AURE IBADA NE. Dan haka Allah yasa mudace amin. 4⃣1⃣ "sann zhrdee yace dama cewa nayi ta jirani naje kasuwa na dauko abu snn mutafi asibiti" "idan na tambyeta tace ba haka bane fa". " haka nema Hjy k'uma ki tambyeta" "to shikenan' ni zanshiga daga ciki'" "to kawai zhrdee yace' Hjy na shiga zhrdee ya zauna da Abba suka fara hira" "Zainab bata tankaba sai yamma snn ta falka lkcn drip d'in dake jikinta ya kare' Hjy ta zare alluran snn ta dagota ta zauna sai faman sannu Hjy kecewa Zainab' tace zakici abinci?" "kai kawai Zainab ta kada' abaki tea' tasake kada kai' to me zakici?" "Zainab sai hawaye". " gani hak yasa Hjy kwaleta kawai' a cewarta maybe bakinta babu dadi ne" "bayan magrib yan'gidan su Zainab sukazo bbnta da inna Hulaira dasu mami'har d'akin abbanta yashiga gani gani yadda ta koma yasashi nuna bacin ransa a fili yana f'adi har yana cewa abashi ita sutafi g'ida" "daga Hjy har inna hkr kawai suke bashi h'ade da cewa hawan jinine amma da zaran ta sauka shikenan zata dawo normal yadda take" "himm kawai yace snn yace Allah yabata lfy" "Zainab na kwance tanaji duk abinda abbanta yake f'adin' kwallane kawai ya gangaro mata ta gefen ido sbd su sake meda mata da wani drip d'an k'uma" "inna dake gefenta kusa da'ita take share mata hawaye' ido kawai abbanta ya zuba mata h'ade da tunani kala2 a zcyrsa gani shirun da yai be yasa inna jansa da hira" "zhrdee be koma g'ida ba sai bayan sallar isha sbd bayan ya yabar hospital shida Abba kasuwa ya koma yaci gaba da harkokinsa' koda Abba ya lekashi a shago yana tambyarsa da wani lokacine zai koma hospital yace Akwai abinda takeyine yanzu amma yana kammalawa zaikoma' to kawai Abba yace snn yakoma nasa shagon". "zhrdee be sake leka Zainab ba koda ya tashi daga kasuwa g'ida ya koma daidai da lkcn dasu Abba dasu yya Shamsudee suma su dawo daga nasu kasuwa duk suka gaisa h'ade da tambyarsa me jiki" "yace da sauki" shigewa ciki sukai suda Abba' shikuma ya shige d'akin gimbiyarsa Aisha' lkcn tana zaune tasha kwanlliyarta ta hakince akan cushion tana jiran ya dawo' duk da tasan ba'ita ne da girki ba amma be hanata amsar mijinta ba" "zhrdee yana shiga a guje taje ta rungumesa' shima rungumeta h'ade da cewa baby na gskya kinyi kyau sosae' murmushi tai snn tace Allah ko nawa?" "Eh'mana Aisha ta" "to ngd" "murmushi tai masa snn ta amshi jakar hannunsa suka karisa ya zauna' ruwa ta dauko ta bashi' bayan ya shane take tambyarsa jikin Zainab".. "cikin mmki yace waya sanar dake Aisha ta?" "Amatullah ne ta sanar dani lkcn zasu tafi sch k'uma Hjy batanan g'ida babu komai sbd takai Zainab hospital" "eh h'aka ne' naso sanar dake amma k'uma... " amma k'uma me?" "babu komai" "zhrdee kenan' to menene Dan ka sanar dani?" nima naso tafiya na dubata amma k'uma nace bazan fita ko'ina ba bada izini mijina ba". "ido kawai ya zuba sbd jin dadin mgnrta" "gani irin kallon da yake mata yasata sa hannu ta shafe masa fuska' da sauri yasa nashi hannu ya jawota jikinsa ta fado matsota yai yana mata cakulkuli tsalle take masa a jiki tana dariya taso guduwa amma takasa' gani tana kwallane yasashi kyeleta' da sauri ta mike tabar jikinsa" "saida ta numfasa snn tace to yanzu yaya za'ayi?" "kamar yaya Aisha ta?" "nifa banyi abinci ba" "why?" "uhmm' uhmm'me?" "just like that" "konw prbm tunda yau h'aka kikaso mijinki yai Azumi dare' mikewa yai ya h'au gado ya kwanta"... " da sauri Aisha ta kamosa tana f'adin wlh wasa nakeyi ". " hannunsa ta kamo tana ja' cikin wasa yace a'a yau Azumi zanyi tunda h'aka matata keso' a'a Dan Allah katashi kaji' jawosa tai ya mike snn taje ta kawo masa abinci". "yanaci suna hira' amma idan kagama ka huta saimuje gun Zainab mu dubo jikin nata ko?" "fuska a daure yace nagaji bazan iya zuwa ba" "Dan Allah kayi hkr ka daure mana muje" "kiyi hkr kawai Aisha" "kamar yaya?" "kibar mgnr zuwa nan kawai" "Dan Allah kayi hkr ka daure muje kasan dai idan mukayi h'aka bamu kyauta bako" "ke kikasan wnn k'uma" "duk da taji dadin f'adin h'akan da yai amma ta matse tana cewa h'aka zhrdee wani irin mgn kakeyi h'aka? tunda ka'iya yiwa Zainab h'aka wataran nima kana zuwa guna". "hanlalinki daya kuwa Aisha harke kinasa ran Akwai ranar da zan walakantaki? "kwarai kuwa' tunda ka'iya yiwa Zainab". " ita Zainab d'in tafikine a guna?" "kawarai kuwa" "sbd me" "uwar ya" ya"kace ita" "pls Aisha expln to me the wy I'll undstn" "OK" abinda nakeso ka fahimta shine Zainab matarka itace uwar ya"ya"ka tunda tana dauke da cikinka a jikinta' koda yau kace ka saketa baku rabuta sbd kunriga ku h'ada jini' amma nifa idan yau kace ka sakeni shikenan mu rabu kenan tunda ba h'ada komai dakai ba' Dan h'aka Zainab ba abin walakantawa bane a gunka" "cikin fushi zhrdee ya mike yabar abincin da yakeci h'ade da cewa kada kisake fadimi mgnr banza irin wnn' ba h'aka ba wlh ba'a jimu dake" "cikin taushin murya tace to shikenan insha Allahu zan kiyaye' mikewa tai h'ade da daukar kyale tace tunda hakane kace ka gaji bari naje na shiga taxi nadubo jikinta juyawa tai takami hanyar fita". " tsawa ya daka mata kitsaya' bazaki tsaya ba? ko badake nakeyi bane Aisha" "duk tanayine idan taga abinda zaice" "gani bata tsayaba da sauri yaje ya fisgota ta dawo ciki snn yace waya kitsaya na kaiki' amma sainayi wanka tuku" to tace' toilet tashiga ta h'ada masa ruwan wanka yashiga yai' yana fita jallabiya kawai yasa suka fita zuwa hospital" "lkcn idonta biyu suka shiga da sallama Zainab na jingine a hango gani shigowarsune yasata rufe ido da sauri' har kasa Aisha ta duka ta gaida Hjy da inna "da fara'arsu suka amsa tana' Aisha tace ya maijikin?" jiki da sauki' Allah ya kara sauki'duk sukace amin" "har cikin zcyr Hjy taji dadi sosai da gani Aisha a hospital tazo gaida Zainab" "zhrdee dake tsaye shima dukawa yai ta gaidasu inna tace masa ya maijiki?" "murmushi kawai yai" "Hjy da inna suka fita" "suna fita Aisha taje kusa da Zainab daidai kafarta ta zauna' shiko zhrdee kujeran bota dake gefe ya zauna yaci gaba da latsa wayar dake hannunsa' Aisha tace Zainab ya jiki?" "batare data b'ude ido ba tace da sauki' Allah ya kara sauki' shiru Zainab tai bata amsa ba'snn shima zahradee yace ya jiki?" "da sauki tace" "daga snn besake mgn ba'itama lallabawa tai ta kwanta h'ade da kauda kanta gefe". " Sufi thirty minutes babu Wanda yai mgn tsakanisu hatta Aisha da zhrdee d'in' mikewa yai yace tashi muje" "ina?" "g'ida mana?" "nidai inda zaka yarda dasai na kwana da'ita Hjy da innarta suje g'ida'idan yaso da safe sai nadawo" "daure fuska yai snn ya daka mata tsawa da Dan Allah kitashi muje" "jin tsawar da yai ne yasa Hjy shigowa h'ade da tambyar lfy?" "a'a dama cewa nayi yabarni na kwana da Zainab idan yaso ku sai kutafi g'ida ku huta" "aiko da kin kyauta wlh" "itama inna shigowa tai' gani ta shigone yasa zhrdee fita h'ade da cewa idan kinga dama ki biyoni". "gani h'aka yasa inna cewa babu komai kutafi kawai tunda inanan' Hjy dake gefe saida taji wani iri" "da sauri Aisha ta bisa zuwa mota' shiko goga zama yai a mota tana jiranta' tana shiga yana tada mota suka nufi g'ida' suna cikin tafiya ne Aisha tace gskya zhrdee baka'kyau ta".. " Dan Allah kada ki fadimi mgnr bazan" "wani irin dadi ne ya lullube Aisha sbd gani abinda zhrdee yaiwa Zainab'amma a fili tace amma dai baka kyauta ba" "tsaki yai be tanka taba har suka isa g'ida' " bayan goma ne yya Shamsudee yaje ya dauko Hjy' inna kawai ta rage' bayan tafiyar Hjy ne inna ta tada Zainab zaune ashe tun shigowar su Aisha ta lura da halin da Zainab ke ciki' bayan ta zauna ne inna take tambyar Zainab abinda ke damuta" "shiru Zainab tai taci gaba da kuka' gani ba lfy ne da'ita ba yasa inna bata matsa mata da tambaya ba hkr kawai ta bata" "satin Zainab biyu a hospital inna ke kwana da'ita' ita k'uma uku gani yanzu Aisha na tafiya yasa bata cika zuwaba' saidai tatura su Amatullah suje tareda Aisha' idan basuda lecture ranar har dare suke kaiwa' idan zhrdee yana dawowa daga kasuwa sai yabiya ya daukosu" "Aisha na zuwa gun Zainab ne kawai amma badason ran zhrdee ba'dan dai bashida yadda zaine kawai ya hanata" "inna har g'ida tarako Zainab saida ta dan jima snn takoma g'ida" "da yamma bayan zhrdee yace dawo kasuwa ta tarasu a parlour su' ga Zainab ga Aisha snn kuma ga zhrdee" "snn Hjy ta fara da Zainab'ke Zainab" "me kika akan jikinki?" "a'a dama cewa nayi bazan iya girki ba' sbd koda tafiya nayi kafata zafi yakemi' kamar zai fashe'y yanzu tafiyar danayi daga daki zuwa parlour ba karami zafi naji ba" "to kai kaji abinda Zainab tace". " to Ai Hjy ni bansan yadda akeyi ba" "to ke Aisha aike kin zauna da kishiya". " Eh " h'aka ne" "to ina sauraranki". " Eh dama idan abu yazama h'aka tunda lalurace aba sauke mata girki" "bayan h'aka fa?" "shiru Aisha tai" "Ina sauraranki Aisha". " still shiru" "to tunda abu ya zama h'aka' ita k'uma lalura tana kan kowa' ke Zainab daga yau na sauke maki girki' k'uma miji bazai kwana a d'akin kiba sai lkc lkc zairinka shigowa dubaki' ke Aisha kici gaba da girki har Allah ya dauketa lfy" "to Hjy" "ke Zainab kin amince da h'akan?" "eh na amince". "to shikenan k'uma Dan Allah kurinka hkr da junanku" "duk suka amsa to" "ke Zainab idan kina bukatar wani abu a marmari ki sanarmi ko Aisha sai a dafo maki" "to Hjy ngd" "k'uma ki kula da magani sosae" "bayan Hjy ta koma bangaren su ne Aisha da zhrdee suka koma daki' itako Zainab saida ta juma a parlour snn takoma d'akin ta" "tun daga lkcn Zainab ta daina girki duk bayan sati biyu Hjy kesa zhrdee ya kai medata hospital kamar yadda doct yace' bayan suyi bincike da zasuyi su gama sai ya dawo da'ita g'ida snn ya tafi kasuwa' ko parlour bata fita shiyasa duk safe Aisha ke shiga su gaisa hakama da yamma' wani lkc kamar da safe kafin yafita kasuwa idan Aisha zataje d'akin zainab sai yahana ko k'uma yace tatsaya ta kare masa abin breakfast idan yafita sai taje tayi abinda zatayi tunda Zainab tafishi". "jin h'aka yasa masu yawanci lokaci sai bayan yafita kasuwa take zuwa ta dubata' mgnr abinci kuwa duk da Aisha tana samata amma be hana Hjy samata ba' mundun tai abinci da kwaryan Zainab a ciki' mgnr kayan murmari kuwa inna da kanta take mata miyar nama ko kaza ko k'uma kifi tace akawo mata' tunda bacin abu me gishiri takeyiba sbd kunburin da tai' koda ankawo saidai tace Aisha ta dauka tunda zhrdee ba shigowa yakeyi sosae ba' sai yakai kwata uku be lekataba' banlema tunda tace bazata iya girki ba shikenan kakarsa ta yanke saka sai yaga dama yake lekowa" "wani lkc saiya kwana uku wani lkc k'uma kwana biyu snn ya lekota' Aisha kuwa duk safe take lekawa' mgnr abinci shima h'aka duk lkcn da tai saita sa mata koda babu yawa saidai ba kasafai takeyi ba' saida yamma sbd lkcn ne mijinta ke dawowa' a cewarta k'uma bazata shiga kitchen sbd Zainab ba" "ita Zainab h'akan be dameta ba sbd baci takeyi sosae ba sbd gishiri' shima abbanta kamar yasan halin da take ciki yasashi siye mata kayan tea manyan gwangwanaye ya aiko mata dasu' mgnr rashin shigowar zhrdee gunta wani zcy tace jeki ki sanarwa Hjy' wani zcy yace a'a kidai bari idan tashigo' wani zcy yace kyaleshi da halinshi kawai" "zama a b'akin gado tai taci gaba da kukanta' taiga zhrdee yai sallama' ganita yai tana kuka' kusa da'ita yazo ya zauna kusa da'ita a b'akin gado h'ade da cewa lfy koda jikine?" "bazan tai dashi taci gaba da kukanta' kome yagani oho jawota yai jikinsa ya rungumeta yana lallashinta ya'isa haka kinji' Dan Allah kidaina kuka haka hannu yasa yana share mata hawaye h'ade ta jijjigata alamar rarrashi" "saida yaga ta daina kukane ya tashi ya dibo mata ruwa h'ade da dauko ledar magani daya shigo dashi" "menene wnn?" "maganiki ne Wanda doct ya rubuta asiye' bansamu na siye bane sai yau" "shiru kawai tai tana kallonsa' da kansa ya bare magani ya ciro yasa mata abaki snn ya dauko cup d'in ruwa yasa mata tahade' saida yameda cup d'in ta'ije snn yasa hannu ya ciccibeta ya kwantar da'ita ya gyara mata kafa' shima hawan gadon yai yafara yimata tausa". "da sauri tace zafi' h'ade da janye kafarta" "ohhh!! srry' bansan akwai zafiba" "dawowa yai ya kwanta kusa da'ita h'ade dasa hannu yana shafe mata ciki' Zainab najin h'aka takara lafewa a jikin zhrdee'ita kanta batasan lkcn da bcc ya dauketa ba" "Aisha nacan na jiran dawowar zahradee' shiru da taji kamar tabishi d'akin taga ko lfy' can k'uma tace baridai takara jiransa tagani" "zhrdee yana can gun zhrdee shima kansa besan lkcn da bcc ya daukesa ba' Aisha tayi jira har tagaji bcc ya dauketa' koda zhrdee zai falka ji kawai yai ana kiran asalatu' yana duba agogo 4-30 itama Zainab lkcn ta falka koda ta b'ude ido gani zhrdee tai yana rungume da'ita'jin ta motsa yasashi cewa kina bukatar wani abu?" "a'a" "OK" "gani biyar yakusa yasashi mikewa ya sauka daga gadon snn yasa hannu ya dagota ta mike' dauko mata zani yai zai daura mata' a'a bashi kawai" "hannu tasa ta amsa ta daura zhrdee ya rike mata hannu suka shiga toilet da kansa yai mata alwala tana yana gamawa yai nasa snn yasake kamota suka dawo bedroom' sallaya ya dauko ya shinfida mata snn yaje ya dauko hijab da wani zanin da zata canza da kansa ya canza mata zani h'ade da sanya mata hijab' dayake a zaune take sallar kamota yai ta zauna shikuma ya nufi masallaci" Zainab na idar da sallah takoma ta kwanta' shima zhrdee yana dawowa d'akin Aisha yashiga lkcn ta idar da tana sallar' kallo daya yai mata yasan tana cikin fushi' bebiye tataba yace ina kwana Aisha ta?" "can karkashi ta amsa da lfy" "kintashi lfy?" "karamar tsaki kawai tai masa" "murmushi kawai yai sbd yasan kishine ke damuta" "Dan Allah hadami tea nasha" "wa!!! Allah ya sauwake' kajecan inda ka kwana tabaka tea kada" "ta'iya kwana da miji banle h'ada tea ne zaimata wuya?" "zhrdee najin h'aka ya mike yakami hanyar fita' gani har yakai b'akin kofa batace dashi komai ba'suna h'ada ido ta hurga masa wata uwar harara' fita kawai yai zuwa d'akin zainab' koda yashiga tana kwance tace kadawo?" "nadawo' yajikin?" "ina kwana". " lfy klau ya jiki" "jiki da sauki" "Allah ya kara sauki". " amin ngd". "b'akin katifa ya zauna kusa da'ita' ita k'uma yunkurawa tai zata tashi" "da sauri yace mezaki" "wanka nakeso nayi" "to tsaya' mikewa yai ya cire jallabiyar dake jikinsa yarage dagashi sai gajeran wando snn yasa hannu ya dagota ta zauna' cire mata bes d'in dake jikinta snn ya dauko towel ya daura mata yasake riketa ta tashi tsaye yacire ragowar kayan cikin'suka nufi bathroom' suna shiga ya cire mata towel d'in da take daure dashi ya cire nasa saida ya gama cudanyata da sabulu snn yai nasa yana gamawa ya ije sosan yana rike da'ita ya sakar masu ruwa akah" "zhrdee na rungume da'ita ruwan yagama wankesu tass snn yakashe dauko towel yai ya daura snn itama ya daura mata' karamin k'uma ya goge masu jiki dashi' yana gamawa ya kamota zuwa bedroom tana zaune a b'akin gado zhrdee yana duke a gabanta yana shafa mata mai" "itako Aisha tanacan tayi fal kamar zata fashe sbd fushi' a zcyrta tana f'adin manafuka alguguma dama ciwon karyane tunda har ta'iya kwana da miji' zaune take ita kadan tana faman cira" "zhrdee yana gama shafawa Zainab shama ya shafa nasa yakwashi mai yameda kan mirrow' ido kawai Zainab ta xubawa zhrdee h'ade da mmkin anya kuwa zhrdee d'in data sanine? kodai wanine ba shiba?" idan ko shine Ashe dama akwai rana irin yau zaizo nagani' lalla ashe kuwa mijina yana sona idan ko hakane dole na sake dan tse na nunawa mijina soyayya k'uma nayi hkr da duk wata kalubalen da zaizo ya shiga tsakanina dashi" "wani irin sanyi taji ya ziyarci zcyrta yau kam babu ciwo dan jama take tawarke garau' k'uma a yau take kara jin so zhrdee' shiru da tai batasan lkcn da hawaye na dadi suka zubo mata ba" "ji kawai tai ana cewa subhnalallah lf" "da sauri ya kariso gunta ya duka a gabanta yana f'adin lfy?" kodai jikin ne" "a'a" "to menene?" "babu komai" "idan jikin ne kiyi mgn sai mu koma hospital" "a zcyrta tace duk da ciwon dake damuna amma ciwon sonka yafi wanda ke damuna'a fili k'uma tace a'a babu komai" "gani har a lkcn six thirty ne yace to zo mu kwanta' kamota yai suka kwanta yana rungume da'ita yana f'adin Dan Allah Zainab kirinka hkr k'uma kidana yawan tunani kinga bake kadan ce ba' yau ba ko kekadaice bazanji dadi ace wani abu ya sameki ba kinjiko my zzz". " eh naji" "k'uma banason yawan kuka idan kinsan Akwai abinda ke damuki zanfi jin dadi ki sanar dani da ki zauna kina kuka' k'uma dan Allah kirinka hkr dani' koda laifine nayi maki zanfiji dadi ki sanar dani da kikama fushi dani' "yawan fushi nasa najimi yaji ya tsami mace ko k'uma ta fita tasa arai' shiyasa nake alfahari dake a duk inda nake' Dan h'aka kikara hkr akan Wanda nasanki dashi' k'uma dan Allah ku zauna lfy da abokiyar zamanki kinji" "naji k'uma in Allah ya yarda zanyi aiki dashi" "yawwa ngd' k'uma inanan ina addu'a Allah ya saukeki lfy" "Zainab takara jin wani sanyi a ranta" "Zainab to kiyi min koda murmushi mana kin barni inata surutu ni kadai" "a lkcn ne tai masa murmushi" "dagowa yai kan fuskanta yace yawwa ko kefa' snn ya h'ada b'akin sa ta nata yana... " duk da girman cikin Zainab behanata nunawa mijinta soyayya ba' Dan a yau jin kansa take garau. "goba da rabi na suka falka'zainab na falkawa tace yunwa" "yunwa kikeji?" "eh" "to zomuje muyi wanka kada mu zauna cin abinci da najasa ajiki ko?" "to" "towel d'in su suka sake medawa sukaje sukai wanka suna fitowa towel ne kawai a kugun zahradee ya fita zuwa kitchen' yana fita daga d'akin zainab Aisha itama tana fitowa daga nata d'akin' hangosa da tai da towel a daure a zcyrta tace jarababbe nasan abin daya kaika kenan" "komawa daki tai' tafasa zuwa kitchen d'in k'uma" "shiko zhrdee bema gantaba banle yasan tanayi' kitchen kawai nufa yaje ya h'ada masu tea ya dauka zuwa daki' a gaban Zainab ta'ije snn ya zauna' da kansa yake bata a baki gani tea akwai zafi yasa idan ya diba saiya hura kafin yabata" "saida ya tabbata ta koshi snn yasha nasa'yana gamawa ya kwashe cups din yaje ya wanke snn yakifesu ya dawo d'akin' dogowar rigan atamfa ya dauko yasa mata sbd yaga shine tafi sawa sbd rashin nawinsa' snn shima ya shirya cikin carptan na shadda ya kwashi towels d'in duk ya nike ya dauko magani ya bata tashi' saida tagamasha ya kwashe ya medasu gefe snn dauki karamar jakan da yake fita dashi yace to ni zanfita" "Allah ya kaika lfy' ya tsayeka daga sharrin makiya ya k'uma bada'sa'a" "amin ngd' baki bukatar komai?" "a'a" "Allah da gske fa" "idan zan rinka samu h'aka a gareka yafi kabani duniya da abinda yake cikinta" "murmushi zhrdee yai snn yace insha Allahu Zainab d'in Allah ya tsaremin ke" "amin ngd" "daga masa hannu tai tana masa bye bye' shima h'aka yake mata har yafita" "yana fita d'akin Aisha yashige tana zaune a b'akin gado yai sallama' banza dashi tai' Aisha nafito zantafi kasuwa saina dawo" "banza dashi tai" "gani h'aka yasa be matsala yafice abinsa" "yana fita tace kada Allah sa kadawo Dan rainin wayo kawai' k'uma wlh babu inda zani' h'aka kawai takwana da miji naje gaidata' ai dadin ma sai yai mata yawa" "hayewa gado tai ta shinshifida kafa" "zahradee yana fita Zainab ta h'au gado tai kwanciyarta" "yau haka Aisha ta yini a daki ko kofa bata lekaba tananan zaune a d'akin har yamma" "zhrdee yadawo kasuwa d'akin ta yashige da sallama yashiga' kamar bazata amsashi can kuma ta amsa' snn tace sannu da dawowa" "yawwa sannu Aisha' ya g'ida?" "klau kawai tace" "gani har ya tube tana tashi daga inda take zaune' yasashi cewa tashi ki daukomi abinci" "banyi ba" "sbd me?" "ba'a dakina ka kwana ba' kaje dakin da ka kwana tabaka abinci" "amma kinsan bata girki ko" "eh bazata iya girki ba amma zata iya kwana da miji ai" "himm Aisha kenan' zo ki zauna muyi mgn" "ka f'adi kawai ina jinka" "Aisha kenan' wlh Aisha ba karami so nake makiba amma kinga niman kibata rawanki da tsalle sbd fushi' Aisha a matsayinki na babba amma wani lkc har Zainab datake kasa dake tafiki hkr' mafi yawanci lokuta wlh Aisha ni kaina nasan bana adalci a tsakaniku sakamakon soyayyar da nake maki amma behana Zainab taimi biyayya ba" "k'uma koda laifi nayi mata koda ya bata mata rai koda wasa bata taba nunashi fushi akan abinda nayi mata ba'amma ke fa duk da irin kyautata maki danakeyi da zaran wani abu yashiga tsakanimu sai kikama fushi dani'kiduba kwanaki fa har tsawon wata kina fushi dani' wani Aisha inda wata matarce ba keba da tuni na koreta' k'uma ko ke d'in nema wlh albarkacin soyayya kawai kikaci" "bazan boye makiba Aisha a duk lkcn da kike fushi da gaba dani wlh har banason na shigo g'idan mu hana ido dake' wai wanda nakeso nake kauna amma kuma tana fushi dani turrrr' da wani irin abin kunya" "bari na f'adi maki wani abu da baki saniba Aisha wlh idan mace ta cika fushi duk irin soyayyar da mijinta yake mata zaiji taragu a gusa' sbd akasarin maza basuson mace me yawan fushi' idan h'aka idan har kinaso mu zauna lfy dake to wlh saikin rage wnn fushi naki" "mgnr kice na kwana a d'akin zainab ba matatace itaba?" eyya? ". " kibani amsa?" "ko baki gani cikine da'ita idan da halima ai bekamata na barta tana kwana ita kadai ba' sbd cikin dare komai zai'iya faruwa' ke kuma kinga bakida komai abu Allah ya kiyaye koda rashin lfy ne yadda zaki tashi kiyi wani abu ba kamar ita ba tunda ba ciki dakeba kamar ita" "jin h'aka yasa Aisha sa masa kuka wai yamata gori" "nifa Aisha ba gori nayi makiba mgnce kawai sai idan baki fahimta ba" "gorine mana SBD Allah zakace ni bana haihuwa Zainab ce mai haihuwa" "nifa ba h'aka nake nufiba". "h'aka nama".. "to Aisha tunda kince h'aka ne'nace d'in k'uma wlh idan bakije kin dafami abinci yanzu nan ba na rantse da Allah sai ranki yafi h'aka baci" "zhrdee ya karisa mgnr ne h'ade da fita yanufi d'akin zainab" ~~~ ~~~ ~~~ "Bilyaminu bedawo kano ba saida ya h'ada duk wani dukiyar Nasir wanda Fatima batasan dasu ba snn ya dawo kano" "Fatima na zaune a parlour ita da yara su Khadijat da Jabeer suna wasa Bilyaminu yai sallama' Fatima ne ta amsa masa ya shigo" Khadijat da Jabeer a guje sukaje suka rungumesa suna f'adi oyoyo Bilyaminu Jabeer dayake shine karami yace ina ka ka kaimi dady na?" "murmushi kawai Bilyaminu yai snn yace dadynka yai tafiya".. " Ina yaje?".. "shiru Bilyaminu yai snn yace ubangiji ne ya kirasa". " to kake masa yadawo ya siyemi chocolate da ice cream kaji" "to naji Jabeer". " Fatima dake zaune a gefe idanuta suka cika da kwalla' Khadijat ko dayake itace babba koda batasan ma'anar mutuwa ba amma tashiji ana f'adi duk wanda yarasu baya dawowa shiyasa tunda taji akace bbnta ya rasu bata cika tambyarsa k'uma saidai duk ranar daya fado mata zama takeyi kusa da Fatima tace mome yanzu dadyna yatafi kenan bazan sake ganisaba?" "eh Khadijat dadynku yatafi kenan bazai sake dawowa ba' k'uma koda yanzu be tafiba wataran zaitafi" "sbd mome?" "sbd yazama dole duk wanda kika gani a duniyarga shima zaije inda dadyki yaje" "mome yanzu har dani dake duk muma zamu mutum" "kwarai da gske" "yanzu mome idan muma mu mutum zamuga dadynmu" "eh zakiga dadynki mana" "yawwa mome"... "Khadijat amma kinsan abinda dadinki keso a gunki?" "a'a mome" "to kullum idan kinyi sallah kirinka yimasa addu'a kinji" "naji mome' duk lkcn danayi sallah zanmasa addu'a" "yawwa Khadijat ta" "tun daga lkcn Khadijat tadaina dami mometa amma shi Jabeer dayake bame wayoneba. kullum mgnrsa kenan dadynsa dadynsa yadawo ya siye masa sweet da ice cream" "shiyasa kusan kullum sai Fatima tai k'uma na rashin mijinta" "bayan Bilyaminu su gaida da Fatima ne yace Hjy ya kari hakuri k'uma Fatima na kuka tace alhamdllh" "Allah ya jikinsa da rahma yasa ya huta yasa mutuwa hutuce gareshi' amma a gskya anyi rashi" "himmm kaidai bari kawai Bilyaminu' wlh ni abinda yafi damuna ma shine inda zasan garuruwan da matan da Nasir yake aura danaje na roka masa gafara ko zaisamu saukin kwanciya a makwancinsa' duk da ba yawo nakeyi dashi ba amma nasan Nasir bashida wata mummunar abinda yake aikatawa sai auren dayakeyi" "gskya ne Hjy'idan dan wann ne babu damuwa idan kinaso ni da kaina zankaiki sbd duk wann aure2 da Alhj yakeyi yana nunami garin matan" "to Bilyaminu har naji dadi" "Hjy dama wata mgn ya kawoni gunki" "to Allah yasa dai lfy ne" "lfyr ne ma Hjy" "ina sauraranka Bilyaminu" "dama akan kaddarorin Alhj ne" "wnn kaddarori k'uma Bilyaminu?" "takardune gasunan' mika mata yai" "tana amsa tafara budewa daya bayan daya" "na samar takardune ne na marayu da suka karkashinsa'gidan marayun dake cikin garin birni kebbi Alhj ya dauki nawin marayu sama da dari biyu yana ciyar dasu cinsu shansu suturansu iliminsu duk Alhj ne ya dauka" "h'aba Bilyaminu shine bantaba sani ba" "eh lkcn yana raye nima kaina be sanar daniba saida nayi masa alkawarin bazan fadiwa kowaba hatta ke da kike matarsa" "sbd yace alkawarine yaiwa ubangijinsa idan har zai aikata abin alkairi dan wanine ko dan duniya susani kada Allah taba shi ikon yi' acewarsa bake matarsa ba koda mahaifansane bayaso su sani' amma idan har Allah ya dauki ransa na sanar dake sbd bayaso a daina taimakawa marayun in har ba dukiyar karewa yai ba" "a kullum idan muna zaune da Alhj yasha fadimi cewa tun lkcn da Allah yasa yai girma yasan kansa duk dare yake rokon ubangiji yanaso Allah yai masa dukiya mai tarai yawa' yatara arziki me taran yawa amma kada yabashi tsawon rai" "idan har Allah ya cika masa burinsa shikuma ya dauki alkawarin bazai taba saba masa ba ta hanyar zina' koda Allah zai jarabcesa ya jarabcesa ta wata hanyar amma banta zina" "ba mmki irin nasa jarabtan kenan da Allah yai masa ta hanyar auri saki". " himm kawai Fatima tace". "dama tun lkcn da Alhj yake kwance naso sanar dake amma Alhj yahana' lkcn da Alhj ke raye duk lkcn danazo g'ida kikaga mu kebe ba komai neba duk dai akan mgnr marayune' abinda yasa ban sanar dake ba sbd alkawarin da nayi masa ne akan bazan sanar dake ba" "shine yanzu nace zansanar dake sbd gudun zargi" "babu komai Bilyaminu ngd sosae Allah yasaka da alkairi yabar zumuci" "to Bilyaminu tunda hakane insha Allahu zanyi kokarin aikatawa kamar yadda yake masu' amma idan nafita takaba dan Allah zanso ka kaini har g'idan marayun na gansu da kaina idan akwai wani abinda za'a kara akan wanda yakeyi to sai a kara" "to babu damuwa Hjy ubangiji Allah ya jikansa da rahma" "amin Bilyaminu" "snn sukai sallama yatafi" ~~~~ ~~~ ~~~~ ASALIN NASIR DA FATIMA Nasir da Fatima asalin haifanfun kano ne maifiyar Nasir itace uwar g'ida agun Alhj TASI'U sunan mahaifiyarsa Hjy RAMLATU daga ita sai Hjy BARA'UTU tabiyu kenan sai kuma Hjy HAMAMATU itace ta uku sai amarya me suna SADIYA'alhj TASI'U Nasir shine na na niyar bayan shi yanada kanni sama da ashirin sbd duk matan bbnsa suna haihuwa babu me yara kasa da goma' duk da yawansu alhamdllh be hana Alhj TASI'U bawa yaransa tarbi da ilimi boko dana zamaniba sai duk cikin yaran Alhj TASI'U yafi son Nasir sakamakon Nasir yafi sauran yaran yimasa biyayya k'uma baya aikata wani abu batare da izini Alhj TASI'U ba tun Nasir yana yaro duk wani abu yasamu na bbnsa ne gashi Allah yai masa zcyr niman na kansa gason karatu h'akan yasa yana kare secdry nasa bbnsa ya tarasa kasar waja karatu" "bayan Nasir ya kammala karatunsa ne yaci gaba da yawo zuwa kasa kasa' a gun yawosane yagane inda ake sauya fata zuwa jakuna' h'akan yasa beyi kasa a gwiwa ba yasanarwa bbnsa tunda dama sana'arsa kenan' tun daga lkcn Nasir yakoma business yana kwaso fata yana fita dashi idan yasiyar saiya siyo kayan da ake bukara anan g'ida yakawo da h'aka Nasir ya bukasa" "gani yanzu har bataci idan bakada ilimi yakoma karatu a kasar jawan yahadu da Fatima itama tajeyin master dinta abu kamar wasa suka kunle soyayya me karfi" "har suka kammala karatunsu' ita Fatima tadawo g'ida Nigeria shikuma Nasir yaci gaba da karatunsa har saida yai doctoring degree d'in sa snn yadawo g'ida Nigeria' ko kafin yadawo mahaifin Fatima ya samar mata aiki a nan kano daya daga cikin company sa" "Nasir yana dawowa ya sanarwa Alhj TASI'U da mgnr Fatima akan yanaso aje a nima masa aurenta" "Alhj TASI'U beyi kasa a gwiwa ba yatura g'idan su Fatima' amma a lkcn Alhj SHU'AIBU mahaifun Fatima yace bazaibawa Nasir Fatima ba' sbd yar'sa bazai iya riketaba' Nasir yayi2 amma ina Bbn Fatima yakasa ya tsare' tun Fatima na boye damuwarta har tazo takasa boyewa' a kowani lkc idan har yana Nigeria sunanan like da juna gani haka yasa Alhj shu'aibu yaiwa Nasir walakanci wanda koda karene bazai dauka ba" "daga lkcn yan'uwan Nasir suka tsani Fatima' shiko Nasir ko'a jikinsa' gani suna like da juna yasa Bbn Fatima ya hanata fita ko'ina hatta aikima yahana" "tun daga lkcn Fatima ta kwanta ciwo kamar zata mutu'duk da irin walakanci da ake masa amma be hanashi zuwa dubata idan bbnta yafita" "gani Fatima na niman rasa ranta yasa bbnta amincewa amma da sharadi" "Nasir yace ya amince' koda da wasane yaji labarin wani abu yasami Fatima da kansa zaizo har g'idan ya dauketa" "Nasir yace ya amince' akayi aure' bayan aure yan'uwan Nasir sukasa Fatima a gaba zagi dacin mutunci babu irin Wanda bata ganiba amma sai idan Nasir baya kasan suke mata harda karuwama sun kirata" "Fatima bata kara tsinkewa da dangi Nasir ba saida sukazo basu samu haihuwa ba'wasuma cewata sukai takare zubar wane a waje yasa da tai aure bata samu ciki ba" "gani h'aka yasa suka fara niman haihuwa duk wani hospital dake kano suje amma ba'a dace ba' gani h'aka yasa ya dauketa sukabar garin yakoma benni kebbi da zama' duk da haka basu zauna ba duk inda sukaji anabada magani sai sunje' Fatima bata samu cikin Khadijat ba saiba suka shafe shekara goma shabiyar snn suma samu" "lkcn da suka fahimci cewa burinsu ya cika daga Nasir har Fatima murna ba'a musaltawa" ~~~ ~~~ ~~~ CONTINATION zhrdee yana kwance a d'akin' Zainab ciki dare tanajin fitsari batai masa mgn ba lallabewa tai ta sauka taje toilet d'an yin fitsirin har tayi zata mike ashe sabulu ya f'adi lkcn da zhrdee yadawo kasuwa yai wanka be saniba daga kafar da Zainab saikan sabulu jinta kawai tai kamar an dauketa ne an likata da kasa " "wani irin ihu tai' daga lkcn batasan inda takeba" "a birkice zhrdee ya falka' gani ba Zainab akusa dashi toilet kawai yanufa sbd yasanta da yawan fitsiri" "a guje yashiga ganita kawai yai kwance jini na faman bulbula kamar fanfo ita k'uma bata motsi" "ihu yasa h'ade da daukar yanufi mota yana tafe yana ihu" "ihun sane yasa duk yan'gida tashi' dukkansu a guje sukayo bangarensa' tun kafin su karasa shiga suka hango jini" "itama Hjy da Aisha ihu sukasa h'ade da kuka" "su yya Shamsudee da Abba waje suka fita gani zhrdee dauke da Zainab yana ihu da sauri Nurudee yaje ya tayashi daukarta shikuma Shamsudee komawa yai ciki ya dauko key din mota suka sata zuwa hospital" "shiko Abba dake tsaye tamaza kawai yai" fow ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _~*IDAN RANA YAFITO TAFIN HANNU BATA RUFEWA'FARIN WATA SHA KALLO TAURARO TSAYA GABAN MAKIYANKI TUNRMI TSAKAR G'IDA SHA LUGUDE' MIRUCIN KAN DUTSE BAKI FITOBA SAIDA KIKA SHIRYA' CARBIN KWAI MAI WIYAR JA. SIS AMINAT KABEER KIRU ( MMN JABEER) ALLAH YABAR KAUNA DA ZUMUCI*~_ *SISTER BATUL ADAM JATAU a gskya naji dadin bayani da kika akan matan da suke yarda mazajebsu ba amfani dasu ta dubura a ganinsu h'akan shine wayewa' idan ko h'akan shine wayewa turrrr da irin wann wayewar, masu irin wnn dabi'ar ubangiji Allah ya shiryesu yasa su gane' wanda kuma basu aikata h'akan ba yawosu bane face tsarewar ubangiji' Allah ka tsaremu ka tsare imanimu' ke kuma Allah yabaki ladar fadakarwa amin* *Aminci 1-2 Mmn uswan grp especially long live our grp Hausa Nvl gskya inajin dadi nuna kaunarku da kulawarku akan wnn Nvl d'in comment d'in ku ke karamin karfin gwiwa ngd sosae da kaunarku a gareni* 4⃣2⃣ "yya Shamsudee ne kejan mota' shikuma zahradee yana rungume da zhrdee a baya yana faman jijjigata h'ade da kiran sunanta amma ina ko a lkcn babu inda ke motsi" "zhrdee dake rungume da'ita besan lkcn daya fashe da kuka ba yana f'adin dan Allah Zainab kitashi' kada ki mutu pls Zainab kitashi" "yya Shamsudee dake tuki babu abinda yakeyi sai faman zuba gudu kamar zai tashi sama" "yya Nurudee shima ya fito da mota gani Hjy zata shiga yasa Abba cewa ta tsaya a g'ida ita da Aisha sbd be kamata duk a watse abar g'ida ba kowaba' har Nurudee yatada mota Abba yatuna cewa zhrdee ya fita babu Riga a jikinsa' dagashi sai gajeran wando da sglet' komawa ciki yai ya dauko masa jallabiyarsa snn yazo suka shiga mota" "su zhrdee suna shiga hospital d'in be tsaya yya Shamsudee yai parking da'kyau ba ya b'ude mota yafita' dakar yake yawo Zainab sbd nawin datai' Shamsudee yana fita a guje yaje ya kira wata nurse sukazo da gadon daukar marasa lfy aka kinkimi Zainab zuwa ciki" "direct d'akin doct aka kaita' zhrdee yaso shiga dakina amma nurse d'in suka hanashi tsayuwa yai dab da kofar yana kwalla h'ade da lekar d'akin da glass' gani h'aka yasa yya Shamsudee kamo hannu zhrdee yajashi suka zauna akan wani betch' doct yana duba Zainab yace tana bukatar emergency operation' sbd idan ba'ayi mata operation ba za'a iya rasata gaba daya'daga ita har abinda yake cikinta" "daya daga cikin nurse d'in dake d'akin ne ta fito ta sanar masu' yya Shamsudee ne yace aje ayi ko nawane zasu biya' nurse tace waye zaiyi signtre Shamsudee ya amsa yai' saiga su Abba sun shigo" "yya Shamsudee ne yai masu bayani abinda ake cikin' a take Abba yashige gun doct mukai mgn ya biya' yya Nurudee yamikawa zhrdee riga yasa" "Abba yana gama biya kudin operation d'in aka fito da Zainab' daga ita sai wani farin kyale da aka rufeta dashi iya wiya' tana shinfide kamar gawa ko motsi batayi' saidai dan dake cikinta kawai ke motsi' har za'a shige da'ita dayake doct d'in take ne yace mijinta yazo suyi sallama' koda zhrdee yaje kan Zainab kasa cewa kamai yai sai kuka yana rike da hannunta" "gani h'aka yasa Abba kamo zhrdee rungume h'ade da cewa a shige da'ita kawai" "nasiha Abba yai tayi wa zhrdee suma su yya duk suna gefensa suna dafe dashi' saida ya numfasa snn suna koma gefe suka zauna suna jiran abinda Allah zaiyi" "duk mgnr da sukeyi zhrdee jinsu kawai yakeyi amma besa bakiba sbd yariga ya shiga duniyar tunani h'ade da dayasani abinda yakewa Zainab na rashin adalci a tsakanisu da Aisha' yanzu idan ta mutu ina zanje da hakkinta?" ta yaya zanroketa gafara ta yafemi' da sauri yace Allah madai yasa kada ta mutu " "around kwata After 1AM aka shiga da Zainab babu wanda yafito yada dasu kala' wata nurse ce kawai take kaida dawowa ita d'in ma koda su mata mgn bata sauraransu' gashi har ana niman 4AM gaba daya hankalinsu yatashi most especially zhrdee' kurum baka kawai yai yana saurarin result d'in da zaiji' idanusa ko duk su kankafe su bushe babu hawayen k'uma' shida yake gwani kuka yau dai yayi ya gaji" "yana cikin sai wata nurse ta fito daga d'akin operation d'in tana fara'a' suma ganita yasa duk suka mike tace dasu congrats ansamu baby boy' da sauri zhrdee yace what about the mother?" "vary soon zatawo dawo normal d'an yanzu dai docts suna kanta". "himm kawai zhrdee yace' gefe suka koma suka zauna' after few minutes aka fito da baby dauke cikin wani d'an karami kwale' da sauri yya Shamsudee ya tareta ta mika masa baby". " wata nurse ce tasake fitowa tace ana bukatar jini sbd ta zubar da jini dayawa' a take zhrdee yace adibi nasa" "lab sukaje aka gwada snn aka diba' Nurudee ne yake rika dashi suka dawo sbd gudun kada ya f'adi" "shiko b'akin Shamsudee har kuni sbd murna' passing2 sukeyi a tsakanisu amma banda zhrdee' ba'a fito da Zainab ba sai bayan awa biyu da fitowar baby snn aka fito da Zainab" "da sauri zhrdee ya mike yana biye dasu' suna gaba yana baya har suka isa d'akin daza'a kaita' har dashi yasa hannu aka shinfidata a gado snn suka gyara ta snn sukasa mata jini" "zahradee yana zaune rike da hannu Zainab su Abba suka shigo d'akin' gani h'aka yasa nurse tace dasu Dan Allah sufita a barta ita kadai" "su Abba ne suka fita amma zhrdee yananan zaune da'ita a d'akin'bayan su fitane Abba ya kira Hjy ya sanar da'ita abinda ake ciki' bayan su gama mgn da Hjy ne ya kira *Alhj Musa* Bbn Zainab ya sanar dashi". "Hjy na idar da sallar asuba tazo hospital d'in dauko da kayan baby's a hannu' tana shiga hospital d'in inna itama tana shiga suna haduwa duk suka karinsa ciki' yya Shamsudee ne ya taresu yai masu iso zuwa cikin d'akin" inna ce tafara shiga sbd baza'a bari su shiga dukkansu su biyu ba' bayan ta shiga ne zhrdee yafita' snn Hjy ta shiga koda suka duba Zainab kwance kawai take babu abinda motsi a jikinta inba numfashiba" "toilet d'in dake cikin d'akin' Hjy ta shiga taima baby wanka tasa masa kayan sanyi' lkcn su Abba suna masallaci suna sallar asuba' ko kafin su dawo Hjy ta shirya baby' su yya Shamsudee suka amshi sukai ta daukarsa Pict snn suka g'ida" "zhrdee yana shiga Aisha tai kamar batasan da mgnr haihuwar ba tace yah!! me jiki?" "da sauki" ansamu baby boy". "wani irin dumm taji a zcyrta a take kwalla suka zubo mata' da sauri ta goge sbd kada yagane' shiko zhrdee kwanciya yai a rigigine h'ade da rufe ido amma ba bcc yakeyi ba' kawai dai yarasa abinda ke masa dadine a ransa' duk da azirtashi da Allah yai da babban kyauta" "Aisha dake zaune gefensa shiru tai h'ade da zuba masa ido tana kallonsa' shima zhrdee dake kwance besan lkcn da bcc ya daukesa ba' saida be dade yana bcc ba' ya falka' yana falkawa bethroom ya shiga yai wanka ya canza kaya dan yaci abincin da Aisha ta kawo masa ya mike zaifita'fuskansa daure babu fara'a Aisha tace nazo mutafi?" "a'a' kawai yace yashige". " zhrdee yana shiga hospital d'in *Alhj Musa* yana shiga' dukawa yai har kasa ya gaidashi a ladabce' amsawa yai h'ade da tambayar me jiki' snn suka karisa ciki" suna shiga kallo daya yaiwa Zainab girgiza kai' sbd har a lkcn bata falka ba' "Zainab har yamma ko motsi batayi saidai numfashi a lkcn ne hankalin kowa yatashi' zhrdee yasake komawa gun doct yimasa bayani' tare sukazo yasa dubata yace babu damuwa sbd tana numfashi koma yana tafiya normal insha Allahu zata dawo daidai" "shiru kawai zhrdee yai h'ade da zubawa Zainab ido' da dare yai inna tace Hjy taje g'ida ita zata tsaya da Zainab' Hjy tace to babu damuwa Allah yabata lfy". " duk sukace amin" "zhrdee da Hjy suka koma g'ida' zhrdee yadai bi Hjy ne kawai amma hnklinsa na baya' koda Aisha ta kawo masa abinda be'iya ciba haka ta meda kitchen suka kwanta yau kam kodan hiran daya saba beyiba'asallatun farko ya tashi wanka yai kafin lkcn zuwa masallaci yai' saida yai shirinsa tsaf snn yaje sallanaci daganan bayan ya'idar yawuce hospital be tsaya jiran su Abba da Hjy ba". "yana shiga d'akin yaga inna na sallah akan Zainab kawai yanufa yadda ya barta haka yazo ya sameta kwance sharaf kai kawai ya kada alamar tausayawa' ruwa ya diba a hannu ya shafe mata fuska dashi snn yasa tissue ya goge fuskan' daidai lkcn baby ya tashi yana kuka' da sauri zhrdee yaje ya daukesa ya rungume sa'gani be daina kukanba yasa inna yanke addu'arta ta amshesa tana jijjigashi" "dukawa zhrdee yai suka gaisa h'ade da tambyar maijiki" "wlh yadda kabarta h'aka take amma doct yashigo ya dubata yace babu komai" "to kawai yace' snn yakoma ya zauna a gefenta" "da safe Aisha sukazo da Hjy dasu Amatullah duba maijiki' Abba bezoba saida zaifita kasuwa snn yabiyo shida su yya Shamsudee' bayan su gaisa su tafine' Hjy da Aisha suka koma g'ida sbd abinda' yan'uwa dangin *Uwa da uban kuwa ba'a mgn* h'aka ma bangaren yan'uwan Zainab' gani yadda jikin nata yakene yasa yyar mahaifiyarta tace zata tsaya da'ita' kanwar abbansu zhrdee me suna ina Asabe itama tace zata tsaya' inna *Hulaira* taje g'ida h'aka" "inna *Hulaira* tace babu inda zata' idan anga tabar wann hospital d'in tofa an sallami Zainab' gani h'aka yasa yyan mmnta tace to shikenan ita zata koma g'ida' yazama inna Asabe ne da inna *Hulaira* suke zama da Zainab" "Zainab bata falka ba sai dare lkcn zhrdee ne ke zaune wajan kanta yana rike da hannunta yaji alamar yatson hannunta suna motsi' da sauri yakara dubanta da'kyau snn tafara motsi da kasa' cikin murna yace *Zainab!! Zainab!!* malauuu tai da ido takara rufewa' da sauri yakira nurse sbd su inna duk suna waje daga ita saishi a d'akin" "koda nurse tazo ta ganta cewa kawai tai ta farfadone' gani idan tayi kaman ta falka tana komawa yasa zhrdee dukawa daidai kunnita yafara yimata addu'a' a hankali take b'ude ido har tabude gaba daya' snn ya dago' suna h'ada ido kwalla ne kawai ya zubo masa hannu yasa ya goge mata" "Zainab naso tai mgn Abba takasa' gani bakinta na motsi yasa zhrdee kawo bakinsa daidai kunnita ko zaiji abinda take f'adi amma ina' meda ido tai ta rufe' bata sake budewa ba' fita yai yakira su inna ya sanar dashi Zainab ta falka amma takoma bcc" "inna kanwar Abba tace to tunda ta falka a wanke nono abawa yaro sbd doct yace saita falka snn za'abawa yaro nono' inna *Hulaira* ta dauko ruwa suka b'ude nono suka wanke snn ta dauko baby ta manna masa kai' da sauri yasa baki yafara ja' zhrdee dake tsaye yana kallonsu shiru kawai yai" "jin motsin ana tsotsonta yasata motsi da karfi da kakafuwanta amma ido rufe' saida ya jima yanasha snn suka canza masa wani' duk da bata farfade duka amma yau kam zhrdee yaji dadi' ba kamar sauran kwanakin ba" "tun daga lkcn h'aka sukewa baby tun nono baya kawo ruwa har yafara kawowa sbd yau da gobe' itama Zainab kullum ana kara samu ci gaba' saidai har yanzu bata mgn' amma kunburin datai a hankali yake sauka' kwanan baby uku Abba yace zhrdee yasa masa suna' zhrdee yace sunansa yakeso wato suna Alhj' shiyasa Abba yai masa suna da *Kailani* amma suna kiransa da *Akbar* Zainab bata fara mgn ba saida takai sati snn tafara mgn". " sai bayan wata daya sann aka sallamesu' lkcn abban Zainab yana gun' jin yafara mgnr zai dauketa yasa zhrdee satan jiki yashige gun Zainab tana zaune b'akin gado tanabawa *Akbar* nono shima hawa b'akin gadon yai ya zauna cikin sanyi murya Zainab tace lfy?" "zhrdee yace Zainab Dan Allah inaso muyi mgn ta fahimta dake k'uma nasan insha Allahu bazaki musamiba sbd nasanki me biyayyace a gareni shiyasa nake alfahari dake" "murmushi kawai Zainab tai" "yawwa umman Abbana' Dan Allah Zainab naji Alhj abbanki yana cewa zai daukeki kutafi g'idan ku' ni k'uma har ga Allah banaso kuyi nisa dani dake Abbana' k'uma bayan h'aka insha Allahu Zainab bazaki kara samuna da rashan adalci a tsakaniku keda Aisha ba insha Allahu nayi maki alkawari Zainab duk wani abu danake maki bazan karaba wanda dama nayi maki a baya Dan Allah kiyafemi kinji Zainab dita". " naji babu komai na yafe maka" "yawwa Zainab dinta ngd' k'uma idan ma idan aikine zanrinka taimaka maki saidai idan yafi karfina kinji" "shikenan naji.... " jin motsin tafiyane yasa zhrdee mikewa yaje bayan kofa ya labe' abbanta yana shiga' shikuma ya fita' hannu Abba ya mika ya amshi *Akbar* snn yace Zainab" "na'am' Abba" "dama na yanke shawarace batare dana tambyeki ba". "na fa Abba?" "Zainab na yanke shawaran daukarki zuwa g'ida ne sbd kisamu kyakkyawar kulawa" "shiru Zainab tai kanta a kasa" "Zainab bakice komai ba". "a lkcne kwalla suka zubo mata tace Abba kayi hkr inda so samune nafiso na koma dakina" "d'akin kifa kikace Zainab ke baki gani yadda kika lallane kika rame' k'uma ni ba cewa nayi idan kintafi kin tafi kenan ba' a'a zuwa wani lkc bayan kindawo daidai saikidawo koya kika gani?" "h'aka ne' amma Dan Allah Abba kayi hkr' wlh Hjy ma tana kokari sosae a kaina" "to shikenan Zainab nima in Allah ya yarda zanrinka zuwa ina dubaki" "to Abba ngd" "nima ngd sosae Zainab da Allah yabani yarinya irinki me tunani" "fuska cike da kwalla Zainab tai murmushi jin dadi" "mikewa Abba yana rungume da *Akbar* yasa dayan hannunsa ya kamota ta sauko snn ta dauki hijab tasa suka fita daga d'akin' su inna suka komai suka kwashe kaya' zhrdee yana hango Abba dauke da yaro da sauri yazo zai amsheshi Abba yace yabari kawai' snn yace yaje ya b'ude mata mota" "to yace dan jin abinda Abba zaice yasashi zuwa gun motar Abba ya na kokarin budewa" "a'a zhrdee naka zaka b'ude' atake wani irin dadi ya ziyarci zcyr zhrdee a guje yaje ya b'ude mata gaban mota tashiga snn Abba ya shinfida mata yaro a cinyarta wasu kwallane suka sake zubowa Zainab hijab tasa ta gode" "Abba na tsare har suka gama sa kaya a mota' gani inna tashiga motar su Zainab yasa Abba cewa ina zaki k'uma?" "Alhj Dan Allah kabari na raka yan'ta g'ida' muna isa ba zama zanyiba zandawo" "to kawai yace' snn zhrdee yafara jin motar" "Abba dake tsaye dagawa Zainab hannu yai yana mata bye bye" "da sauri Zainab ta kauda kai sbd kuka' zahradee yaja mota suka tafi" "inna *Hulaira* da inna Asabe suna mata dariya 📖🖊 ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _*ALLAHUMMA INNAKA AFFUWUN TU HIBBUL AFFUWAN FA AFFUS ANNA' ALLAHUMMA INNAKA AFFUWUN KARIMU AZIMU ALIMU TU HIBBUL AFFUWAN FA AFFUN ANNA*_ _*Alhamdullilah masha Allah' Allah shine me kowa me komai' ina taya yar'iwata SAFIYA ADBULLAHI HUKUMA samu sauki h'ade da dawowa' ubangiji Allah yasa kinfara a sa'a ya k'uma kara lfy' ya jikan wanda suka rigamu ameen*_ ~_*wnna page sadaukarwace gareki Hjy zaliha yola (Mmn Ahmed and Faisal) Allah ya rayasu nisa sunnah yasa masuyiwa musulumci hidimane ya albarkaci rayuwarsu yasa masujin kan iyayene ameen ya rabbi*_~ _*MASOYA DAN ALLAH KUYI HAKURI NA JINA DA KUKAYI SHIRU KWANA BIYA WLH RASHIN NETWEK NE YASA I'M SORRY PLS*_ _*oyoyo sis Haleema auwal ina tayaki murnar dawowa ubangiji Allah yasa kinfara a sa'a amin*_ 4⃣3⃣ "suna isa g'ida bayan zhrdee yai parking zagowa yai ya b'ude mata murfin sa hannu yai amsa *Akbar* ya rungume snn yasake sa hannu ya kamota ta fito yana rike da hannunta daya dayan k'uma yana rungume da *Akbar* suka shige ciki" su inna suka kwashe kaya zuwa d'akin g'ida kai tsaye d'akin ta ya kaita' suna shiga ya kwantar da yaro snn ya kamata ta kwanta' su inna d'akin Hjy suka shige' Hjy ta taresu da fara'arta bayan su gaisa snn tasa aka kawo masu abinci' inna Asabe ne kawai tana itako *inna Hulaira* taki ci a cewarta sauri takeyi' dama ta rako maigidanta g'ida yasa tazo da bazata zoba " "duk dariya sukasa inna da mike Hjy da inna Asabe suka rikata bangaren Zainab har cikin daki suka shiga Zainab na kwance zhrdee na rike da Abba yana masa wasa". "gani su Hjy yasashi mikewa da sauri mikawa inna Asabe har zaifita Inna tace a'a katsaya dama sallamarku nazoyi zantafi g'ida" "har kasa zhrdee ya duka sukayi sallama h'ade da godiya zhrdee yakaita har g'ida snn yadawo' duk a lkcn Aisha na daki bata fitoba' d'akin ta yashiga h'ade da sallama' tana zaune akan cushion tana games a wayarta' kusa da'ita ya zauna su Aisha kenan manyan gari" "kadawo" "fuskar Aisha a daure tace kadawo?" "nadawo'ya g'ida?" "g'ida klau" "duk Aisha na ngmr ne batare data kalli zhrdee ba sbd hankalinta na game datayi". " gani h'aka yasa zhrdee cewa inaso muyi mgn ne fa" "batare data kallesa ba tace OK" "hannu yasa ya amshe wayar datake game d'in dashi" "snn Aisha ta juyo" "ledar daya shigo dashi yaja zuwa gabansa yaciro dukule daya yace ga wnn turmi niyar ne nabaki kiyi hkr dashi babu yawa" "NA mefa?" "eh gani tunda ba suna za'ayi shiyasa baku wnn Ku duka a madadin na suna' hannu yasa yafito da ragowar yace wnn na Zainab ne' shikuma turmi bakwai ne' sbd itace mai haihuwa' ko ba h'aka akeyi ba?" "h'aka ne" "k'uma abinda yasa ba dauka maku iri daya ba sbd gani nayi kalar tatanku ba daya bane' ke bakace ita k'uma fara shiyasa" "to babu komai ngd Allah ya amfana ya kara budi" "amin ngd" k'uma Zainab fa tadawo tana daki" "to bari zanshiga na dubata". " to kawai yace ya mike h'ade da daukar ragowar kayan ya fita zuwa d'akin Zainab' yana gani gani abbansa yai yana shan nono" "zama yai b'akin gado yamika hannu Zainab ta cireshi daga nono ta bashi' zhrdee yana amsa h'ade da cewa Abbana kai baka gajiya da nono ne?" " *Akbar* dake hannu bbnsa yasa kuka yana motsi da baki' daga Zainab har zhrdee dariya sukasa' gani bashida niyar daina kukan mikashi yai akaci gaba da bashi nono " "saida yasha ya koshi snn ta kwatar dashi' zhrdee ya yawo ledar ya ciro kayan ya mikawa Zainab.. " NA menene wnn?" "kayane baku dake Aisha k'uma Dan Allah kiyi hkr da mgnr sunan da Abba yahana kinji" "himm babu komai ai" "to ngd ga kayan nan' nariga nabawa Aisha nata" "to ngd Allah ya kara budi yasa kafi h'aka" "amin ngd" "gani *Akbar* ba bcc yakeyi ba daukarsa yai suka nufi d'akin Hjy" "Amatullah na ganisu da sauri ta amshesshi suka fita daga d'akin'bayan su gaisa Hjy tace amma ka hadasu kai masu mgn ko?". " mgnr me k'uma Hjy?" "akan aisha zataci gaba da girki har Zainab tayi arba'in snn ta amshi girki" "to Hjy dama h'aka akeyi ne?" "to shikenan zan masu mgn". "da yamma bayan isha zhrdee ya hadasu a parlour ke Aisha dama ba komai yasa na hadaku ba mgn ne zamuyi" "to ina jinka" "mgnr girki ne' kenan Aisha zakici gaba da girki har Zainab tayi arba'in' bayan arba'in Zainab zata amshi girki" "to babu damuwa' ke Zainab kin amince?" "eh na amince" "washe gari da yamma lkcn zahradee yana dawowa kasuwa kayane ya siyowa *Akbar* kamar hauka harda keken wasa' yana sallama Aisha ta fita taroshi' ganisa da tai da kayan a take ta daure fuska' shiko zhrdee ko'ajikinsa d'akin Zainab ya shiga Zainab dake kwance gani zhrdee da sauri ta mike taje zata amsheshi yace tabari kawai" "d'akin Aisha ta koma rai bace tana tafarfasa' ji takeyi zcyrta kamar zai fashe' ta rasa wanda zata sanar mawa taji sanyi". " can mgnr ubaida ya fado mata' da sauri ta dauki wayarta ta kira ubaida' bugu daya tai ubaida na gani number Aisha ta daga h'ade da sallama' "Aisha najin mgnr ubaida ta fashe da kuka" "Subhanallh tace snn tace Aisha lfy?" meke faruwa?" "nan Aisha ta kwashe komai ta sanarwa ubaida" "gani akwai Bbn Abba agun yasa ubaida bata samu damar sakewa tai mgn ba" "gani h'aka yasashi cewa lfy?" "Aisha ce babu lfy shine ta kirani take sanarmi" "to Allah ya sauwake' kibari da safe kije dubota" "to kawai tace" "shiko zhrdee yana can zama yai dirshan akan carpet yana hadawa bbnsa keke' Zainab dake zaune duba kayan daya siyo masa takeyi daya bayan daya' zhrdee yana f'adin sunada kyau ko? Ai dama cewa mai kantin nayi ya zabarwa Abbana kaya masu kyau". " ita dai Zainab batace komai ba sai murmushi datakeyi" "zhrdee be koma d'akin Aisha ba sai bayan goma' saida yakare gyara mata ko'ina yasa keke a gefen gadon mmnsa ya kwashi kaya yasa a cikin wardrobe snn sukai sallama yafita" "koda yashiga d'akin Aisha ganita yai tana kuka' da sauri ya karisa gunta zama yai kusa da'ita yasa hannu ya jawota ya rungumeta yana f'adi lfy aishata?" "Aisha bata tanka ba taci gaba da kukanta" "Aisha Dan Allah kiyi mgn mana' kodai bakida lfy ne?" "kai ta daga masa' alama a'a" "to menene Aisha ta' Dan Allah ki fadimi" "babu komai' kawai tace" "Aisha ta cewa zhrdee babu komai ne kawai sbd bazata iya sanar masa abinda ke zcyrta ba" "shima zhrdee dayaga h'aka duk da f'adi masa abinda ke zcyrta ba amma yagano wasu abubu tun lkcn da akaiwa Zainab aiki' hannu yasa ya share mata hawaye snn ya dago mata fuska yace Aisha" *na'am tace" "Dan Allah Dan annabi Aisha inaso ki cire komai dake ranki wlh duk abinda kike tunani wlh ba h'aka bane' kada kiga Dan Zainab ta haifanmi d'an kice zan kiki wlh kinanan a zcyta kamar kullum' koda wasa bantaba jin sonki ya ragu daga a raina ba' asalima karuwa yai" "wlh Aisha ina sonki' nima kaina mmkin irin son da nake maki' amma nasan ba lallane ki yarda ba' amma wlh Aisha ina sonki sosae Aisha ta" "k'uma dan Allah duk wani abu da kikaga nayiwa Zainab banaso ki tada hankalinki' kinga koba komai dole Zainab zataci albarkaci yaro' idan banyi dan itaba dole nayi mata d'an yaro' bawai ina nufin bana sonta bane dukkanku ina sonku' amma kinga ba lalla bane abinda nayi mata nayi maki' k'uma koda kece yau kika haihu h'aka kema zanmaki" "nima kai Aisha mgnr rashin haihuwarki wlh yana damuna' ni k'uma gashi bansan komai akan irin wnn harkanba saidai idan ba hospital zamuje ba' amma wani abu da bansani ba shine ke Aisha tun farkon rayuwarki baki taba samu ciki bane a g'idan tsohon mijinki?" "cikin sanyi murya tace na taba". " to ina cikin yake Aisha" "barewa yai" "wani irin bari Aisha?" dama h'aka kawai mace na barine ciki yafita?" "eh". " to wlh bantaba saniba' to yanzu me kike gani zamuyi?" "kamar yaya?" "ke koda a cikin garin nan koda labarine baki taba jin wani doct yana taimakawa ta irin wnn laluranba?" "a'a saidai mutabayi mgnr da ubaida tace wata kawarmu *Rabi'a* ta taba samu irin wnn matsalar mijinta yakaita wani hospital k'uma sun samu waraka yanzu da h'aka yaransu biyu tanada ciki NA uku" "Aisha kenan' dama kinsan da h'aka shine baki sanar daniba Aisha' naje na samesa ya nunamin ko Allah zaisa mudace". "dama ubaida ce tace zata tambyi rabi'a suna hospital d'in" "to shikenan gobe ki shirya idan zanfita kasuwa saina saukeki a g'idan ta ko?" "a'a tace gobe zatazo" "to shikenan' yanzu share hawayenki k'uma Dan Allah banaso nasake gani hawaye a fuskanki" "kina jinako". " naji" "tashi ki daukomi abinci" "dauko masa tai yaci snn yai wanka suka kwanta' cikin dare zhrdee suka kwance da Aisha yajiyo kukan *Akbar* da sauri ya dauka ya dauki towel ya daura yakami hanya' Aisha tace ina zaka?" "ina zuwa kawai yace yafita" "tsaki kawai Aisha tai itama ta mike ta daura zani h'ade dasa hijab tabishi" "yana shiga ya h'au Zainab da f'adi' h'aba Zainab wani irin bcc kikeyi h'aka kika barni yarona yana kuka". "wlh ba bcc nakeyi ba' nafa bashi nono yasha amma be daina kuka ba" "hannu Aisha tasa ta amshesa h'ade da cewa kodai cikinsa ne' ke ciwo?" "zhrdee najin h'aka ya amshesa zonan Abbana' menene yake damuka' jijjigasa zhrdee keyi h'ade da yimasa mgn a kuni" "shiru *Akbar* yai yana sauraran bbnsa" "komawa d'akin Aisha yai da yaron' itako Zainab mikawa tai ta kwanta' suna shiga zhrdee ya kwanta h'ade da dorasa akan kirjinsa' suka koma bcc' itama Aisha kwanciya tai' saida zaitafi masallaci snn ya medashi gun mmnrsa" "uban na kare aikinta tai wanka tazo g'idan su Aisha' saida tashiga taiwa Zainab barka snn suka shiga d'akin Aisha' bayan sun gaisa ne Aisha ta kwashe duk yadda sukai da zhrdee ta fadiwa ubaida" "to dama kece ai kince zaki dawo baki dawoba' NA tambya maki rabi'a ga number wayar doct d'in ma tabani" "kai ubaida ngd sosae" "amma tace maigidanki ne zaikira sbd doct koda kin kira ke mace bazai daga ba" "to babu damuwa idan yadawo zanbashi yakira suyi mgn" "eh ikon Allah kenan Aisha" "NA mefa ubaida?" "ke kinga yaron zhrdee kamarsu daya' babu inda yabar bbnsa" "himm kedai bari kawai ubaida' idan NA kalleshi sainaji inama da nine NA haifeshi" "dako yakara sonki' amma insha Allahu kema zaki samu naki" "Allah yasa ubaida' gashi NA lura zhrdee ba karami so yakewa yaron gaba" "to Aisha mutu zai haifi abu a cikinsa yace beso?" kema kanki kibi a hnkli wlh duk son da yake maki idan kika kuskura kika yiwa yaringa wani abu wlh rufe ido zaiyi yai maki rashin mutunci'idan h'aka ina baki sharawa kibi a hnkli" "himm ubaida kenan ngd Allah yabar zumuci" "ubaida bata koma g'ida ba sai yamma" "bayan zhrdee ya dawo yaci abinci Aisha ta bashi number doct d'in snn tai masa bayani" "gani dare yai yasa zhrdee cewa subari da safe zai kirasa' h'akan yasa da safe be fita kasuwa da woriba saida yakira doct sukai mgnr da zasuyi yace suje yana office". "Aisha ta shirya suka tafi hospital d'in' bayan su gaisa zhrdee yai masa bayani" "doct ya juya kan Aisha yafara mata tambyoyi' tana amsawa" "snn yace ai wani ba wata matsala bace da zata hana haihuwa ba' idan ba waya yai ba" "da yawa ana samu irin wnn matsala amma idan takula da dokokin magani insha Allahu zata warke" "Dan Allah doct wani ciwone wnn?" "ba wani ciwo bane *Infection* ne' k'uma dama idan yai yawa yana rufe b'akin mahaifa'amma idan akabi dokan doct za'a samu waraka" "to yanzu doct menene abinyi?" "eh yadda taimi bayani yanzu magani zanbata tazaman amfani dashi na tsawon wata biyu' bayan wata biyu zaku dawo asake dubata' idan na canza magani ne sai a canza" "to doct ngd sosae" "babu damuwa Allah yasa adace" "amin" "bayan ya rubuta sukai sallama suka fita". ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRIRES. F.O.W.☘. 🌳 *Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* *sadaukarwa gareku* *fasaha hausa Nvl 1-4 GRP* *Maryam L'I gital Hausa Nvl GRP* *Nagarta writes Hausa Nvl GRP* *cool of Nvl make up and ktch Hayat yya Hayat admin of admin hausa GRP* *Hafsat Hausa Nvl H2 GRP* *💤💤💤 fasaha hausa Nvl GRP* *Mmn Jabeer grp Hausa Nvl GRP* *Home of Nvl long life Hausa GRP* *Hausa Fulani and Duniya marubuta Hausa Nvl GRP* *YAR mutum wudil Hausa Nvl GRP* *duniya kabari Hausa Nvl GRP* *Mmn Ahmed Hausa Nvl GRP* *maryam muh'd 1-2 Hausa Nvl GRP* *Halienma Ammin Hausa Nvl GRP* *Aisha muh'd Hausa Nvl grp* *Dadai sauran da bansamu ambatosu ba, duk kuna raina* *Allah yabar kauna da zumuci ya kara h'ada kanmu b'akin daya amin* 🤝🤝 *fatan alkairi gareku yar'yar' abin alfaharina' Allah ya rayaku bisa sunnah manzon tsira shugabanmu annabi Muhammed (S.A.W.)* *Firdausi* *Abdul najin* *Abdul shakur (uswan)* *Big dady salis* 4⃣4⃣ "saida ya kai Aisha g'ida snn ya karisa kasuwa' bayan sallar la'asar bbn Zainab ya aiko mata da kaya akwai biyu' akwati daya shake yake da zannuwa shadda laces' daya k'uma kayan *Akbar* shake Hjy tai godiya sosae h'ade da bada tukwaici mai yawa' inna *Hulaira* ta cirewa Hjy turmi biyu na Holland ita k'uma Aisha aka bata English turmi daya" "duk sukai godiya" "tun daga lkcn suke zaune lfy babu me jinsu' ita k'uma Aisha taci gaba da shan maganin da doct ya dorata akai" "ita Zainab akai akai zhrdee yake medata hospital sbd duba lfyrta' a yau ne Zainab ta amshi girki tuwon masara tai masa da miyar kuka dayaji busaeshiyar kifi da mana snn ta zuba man shanu da aka kawo mata daga g'idan su' snn tai wanka ita da *Akbar* daya daga cikin kayan da aka kawo mata daga g'idan tasa'shima *Akbar* aka shamasa kwalliya' ba karami kyau sukai ba' bayan ta idar da sallar isha zama tai a b'akin gado tana jiran dawowar zhrdee" "can tajiyo muryansa yai sallama yashigo rike da leda a hannu' saida yashiga d'akin Aisha suka gaisa snn ya kima mata nata ledar yafita zuwa d'akin Zainab' yana sallama da sauri Zainab ta mike saida ta shinfida *Akbar* snn taje amsheshi ledar dake hannunsa h'ade da cewa sannu da zuwa" "yawwa sannunki da g'idan' ina Abbana?" "gashi can kwance" "yawwa Abbana'hannu yasa ya daukesa ya rungume sa" "Zainab na ije ledar bathroom ta shiga ta h'ada masa ruwan wanka snn tafita ga ruwan wanka na h'ada maka' kawosa kaje tai wanka' to Zainab rikemishi d'kyu kafin nafito wanka" "to" hannu tasa ta amsheshi snn zahradee ya tube yashiga wanka' yana fara goga sabulu yaji *Akbar* yafara kuka batare da yatsaya bata lkc ba watsa ruwan kawai yai da sauri ya daura towel ya fito h'ade da tambyar Zainab me kikai masa ne yake kuka h'aka? " mi komin shi" "zonan Abbana me akai maka ne?" "gani be daina kuka ba yace Zainab tabashi nono' zama tai b'akin gado tana bashi nono zahradee na gabanta duke yana rike da hannunsa' yana sha yai bcc' Zainab ta shinfidashi snn taje ta daukowa zhrdee abincisa tadawo ta'ije masa h'ade da ruwa da abin wanke hannu" "ko towel zhrdee be cireta ya zauna snn yasa hannu ya dauko ledar yai yace zo ki zauna mana gimbiyata saukowa tai ta zauna tana fuskantarsa b'ude ledar yai ya ciro dunkule saurin kada snn yasa hannu ya dauko extra plate ya juye namar aciki' snn ya dauko yoghurt shima budewa yai ya tsiyaya a cup daukar namar yai ya kai mata baki h'ade da murmushi" "cikin jin kunya Zainab ta amsa tana murmushi' saida ya kai mata s'au uku snn ya dauko cup d'in yoghurt har zai kai masa baki da sauri Zainab ta dauke kanta h'ade da cewa bana shan ruwan sanyi" "kisha mana kadan ne fa". " a'a an hanani". "to shikenan' bari nasha kayana'amma kici namar". " to kawai tace" "snn tafaraci da kanta shikuma yanacin tuwo' suna gamawa sukai burosh snn suka kwanta' har bcc yafara daukar Zainab taji ana lalibota da sauri ta mike zaune tana f'adin lfy?" "ke dawonan ki kwanta'bcc zamuyi". "a'a wlh banfa warke bafa" "h'aba Zainab wani irin warkewa k'uma idan baki manceba ko kafin kidawo g'ida kinfi wata a hospital snn muka dawo g'ida' duk da h'aka Hjy tace sai kinyi arba'in' bayan wnn kwanakin da kikai saida kika kara kwana arba'in fa' Dan Allah Zainab kizo mu kwanta wlh sha'awarki nakeyi" "ni wlh tsoro nakeji" "kada ki damu a hankali zanyi" _*AFTER EIGHT MONTH*_ yau Zainab ta tashi da zazzabi tun dare take amai har safe' ko rintsawa basuyi ba' Allah yasa zhrdee a d'akin ta yake shiyaketa raino" "gani amai yaki tsayawa da safe daukar *Akbar* yai yakai shi gun Aisha yace tai masa wanka su zasuje hospital Zainab ce babu lfy " "to tace tasa hannu ta amshesa' shikuma ya koma daki ya taimaka wa Zainab tai wanka ko kwalliya batai ba kaya kawai tasa suka fita" "suna zuwa hospital gwajin farko doct ya sheda masa cikine na wata daya' Zainab najin h'aka tasa kuka' shima zhrdee hankalinsa ya tashi gani irin kuka da Zainab keyi" "suna shiga mota bayan shima ya shiga ya zauna snn yace Zainab kukan me kikeyi h'aka?" "Zainab tai shiru bata tankasa ba'taci gaba da kukanta" "Zainab ba dake nakeyi ba?" "still kuka taci gaba dayi" "tun daga lkcn besake tanka taba yaja mota suka tafi g'ida' suna shiga suka samu *Akbar* yana kuka har da ijiyar zcy a bayan Aisha' itama tai lallashi har tagaji' da sauri zhrdee yasa hannu ya amshesa" "Zainab bata tsaya a ko'ina ba' sai d'akin ta' Aisha dake tsaye a gaban zhrdee tace ya mejikim?" "jiki da sauki" "be tsaya bata lkc ba d'akin Zainab' yana yana shiga ganita yai ta rum da ciki akan gado tana kuka" "da sauri zhrdee ya karisa kan gadon inda take' Zainab Zainab lfy?" me nene abin kuka h'aka k'uma sbd Allah?" "duk da kukan da *Akbar* keyi amma h'aka zhrdee ya shinfidashi yasa hannu ya dago Zainab zuwa jikinsa ya rungumeta' Zainab Dan Allah menene abin kuka k'uma?" ko duk sbd cikin ne yasa kike irin wnn kukan?" "yanzu kinga Abbana yana kuka Dan Allah ki taimaka ki basa nono idan yai shiru sai muyi mgn dake" "dauko *Akbar* yai ya dora akan cinyarta snn ya daga mata riga ya ciro nono *Akbar* na gani nono da sauri ya kama yafara sha" "yana yai bcc' daukar yai ya shinfidashi a gefe snn ya jawo Zainab ya kwantar da'ita a jikinsa yace Zainab" "cikin kuka tace na'am" "nasan laifina kikekike gani dan Allah kiyi hkr wlh nima bansan H'akan zai faruba' k'uma idan banda abinki abinda ya kamata kiyi murna shine kike kuka" "h'aba zhrdee wani irin murna?" da yaro karami h'aka' wanda ko tafiya bayayi' k'uma baka gani irin wuyar danashi a wanca karo' shine zanyi murna" "idan operation kika tunani insha Allahu a wnn karo baza aimiki ba' in Allah yarda da kanki zaki haihu kinji Zainab" Abba k'uma insha Allahu Allah zai raya mana shi' babu abinda zai samesa".. "haihuwa fa kace?" "kwarai da gske Zainab" "ni gskya ban yarda ba" "to yanzu me kikeso ayi?" a cire ko me?" "Eh" "Eh kikace?" "eh" "ke Zainab bakijin tsoron aje cirewa wani abu ya sameki? ke baki taba jin labarin matan da sukaje cire ciki suka mutu bane' idan yanzu kika mutu ta wnn hanyar me zakicewa ubangijinki?" "shiru Zainab tai" "to wlh Zainab idan bakiso ni inaso k'uma babu wanda ya'isa ya ciremi cikina" "Zainab najin h'akan da sauri ta mike ta zuba masa ido tana kallonsa" "mikewa zhrdee yai yanufi d'akin' Hjy" "da sallama yashiga' ganisa yasa Hjy gyara zama' zhrdee ne" "Eh" nine Hjy' a ladabce ya gaidata snn ya samu gu ya zauna' zhrdee yah!!!! akai ne" "wlh Hjy Zainab ce babu lfy' subhanalillh!! me yasameta?" "kwana tai tana amai' amma muje hospital danzu" "to' yya jikin nata?" "jiki da sauki" "ambata maguguna ne?" "eh" amma yace cikine da'ita". "ciki k'uma?" "eh Hjy" "ikon Allah kenan" "yanzu ina Zainab?". " wlh tana can tana kuka' wai saidai acire ciki " "acire ciki😳" "to wlh bari kaji babu wani cikin da za'a cire' shegema ta haifa banle na halak' wlh idan kabiyeta kuka cire cikin nan ban yafe makaba k'uma nida kaine a g'idan nan" "a'a Hjy nima dama cewa nayi baza'a cire ba" "yanzu ina abban naka yake?" "yana gun Zainab yana bcc" "kaje ka lallasheta amma babu mgnr cire ciki" "to Hjy" mikawa yai yafita' nima inanan shigowa nayi mata mgn ". _*BAYAN WATA BIYAR* "ranar zhrdee yana d'akin Aisha ne yana shiga wanka Aisha taje kitchen h'ada masa tea' kafin yafito ta h'ada ta kawo masa' ijewa tai a gefe snn takoma kitchen" "zhrdee yana fitowa daure da towel yajiyo kukan *Akbar* daga d'akin Zainab' da sauri yafita yaje duboshi' koda yaje ganisa yai yana kuka Zainab tai banza dashi tana kallonsa sai faman ihu yakeyi a tsakar d'akin'" "da sauri zhrdee yaje ya daukesa yana wa Zainab f'ada' h'aba Zainab wann wani irin walakancine h'aka'' zaki barmi yaro a walakance yana faman kuka kamar mara data" "to me kakeso nayi masa bayan na lalla shesa yaki shiru" "h'aka ne kika lallashesa?" Dan Allah Abbana zomuje wani walakaci' kisake barimi yaro h'aka kiga yadda zamu kwashe dake a g'idan nan " "daukar dan'sa yai zuwa d'akin Aisha' har kan gado ya ije *Akbar* snn ya dauko wayarsa ya kunna masa ringinto yabashi *Akbar* najin h'aka yai shiru yaci gaba da wasa" "shima zhrdee gaban mirrow yaje yana shafa mai' Aisha tashigo rike da plast a hannu gani *Akbar* kan gadon ta' h'aba zhrdee sbd Allah idan yai min fitsarifa kana gani ko pampas be dashi k'uma kasan yanada yawan fitsari" "cikin wasa zhrdee yace tunda Abbana nane babu komai idan yai fitsarin zansiye maki wani katifar" "duk zhrdee yana mgnr ne batare daya juya ba" "Aisha tace a'a wlh hannu tasa ta daukeshi kasa snn tafita' gani babu komai a hannunsa juyawar da zakiyi yana niman kayan wasa a guje ya rarrafa yaje ya jawo plast d'in" "Ashe Aisha bata rufe da'kyau ba gaba daya yabude ruwan yai jikinsa" "ihu yasa yaci gaba da juyi acikin ruwan' ihun sane yasa zhrdee juyowa a guje yaje ya daukesa shima yana ihu a guje yafita zuwa d'akin Hjy' Aisha najin ihunsa itama gudu tasa zuwa d'akin taga abinda ke faruwa" "zhrdee yana zuwa Hjy ta tarasa h'ade da salati garin yaya h'akan yafaru?" amsarsa tai ta cire masa riga gaba daya jikinsa ya salube amma banda fuska" "rikesa tai tana masa addu'a tana tofa masa' zhrdee yace Hjy muje hospital' Hjy tace a'a barshi mu gani tuku" "juyawa zhrdee yai yakoma d'akin yana shiga sukai karo da Aisha zata fito zuwa d'akin Hjy' yanzu Aisha abinda kikaimi kin kyau kenan?" "me nayi k'uma?"... " kafin ta karisa ya dauketa da mari h'ade da tokari' tana f'adi yasake binta ya hayeta da duka' yana f'adi Dan tsabar b'akin ciki sai ki konami yaro.. "Aisha naso tayi mgn amma ina zhrdee be barta da fukaba" "jin hayaniya yasa Zainab b'ude kofa tafito daga d'akin ta' jin hayaniyar daga d'akin Aisha ne yasa ta zuwa nan' gani Aisha ta dan'no a guje zuwa d'akin Zainab' gani h'aka yasa itama Zainab komawa a guje suka shiga d'akin suka rufe" "biyosa zhrdee yai d'akin Zainab tabawar da zaiyi yaji shi a rufe' kofa yasa yana tokarin kofar yana f'adi dan baki b'ude ba wlh saina fasa kofar' gani zai fasa da gske yasa Zainab b'ude kofar" "batare daya tsaya duba ko wayeba fisgo Zainab yai waje" "ihu tasa tana f'adi a'a banine ba" "snn yasake ta ya koma kan. Aisha' ko kafin yai kanta Aisha takoma d'akin ta' a guje zhrdee yabita kamar mahaikaci' gani zai rufe kofa da'ita a d'akin yasa Aisha daukar mayafinta a guje tabar g'idan" "duk da h'aka binta yai shima da gudu' a guje Zainab tazo ta rikesa ta baya tana ihu h'ade da kuka" "zhrdee yai kokarin tureta yabi Aisha' amma kuka ko mai yagani ohoo tsayawa yai yana ajiyar zcy" "itama Zainab tai h'aka ne sbd gajeran wandone kawai a jikinsa" "kamo Zainab yai suka koma cikin' gani zasu shiga bangaren Hjy yasa Zainab cewa a'a kaje kawai" "Aisha na fita kai tsare g'idan su tanufa' a kasa kafa babu ko takalmi 📖🖊 ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and Entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _*I didecated this page to Ahmad (FAHIM) Zhrdee Yahya maburya kwantagora*_ _*gareku masoya aure ibada ne ngd sosae da soyayyarku a gareni ngd sosae*_ _*masoya Aisha duk naga conmment naku k'uma ngd sosae' but kunsan ba kowani mutum ne yake ina controlling kansa a lkcn da yai fushi bako' k'uma dole zhrdee ya nuna nushinsa akan Akbar sbd zaiga kamar da gangan tai masa h'akan' zai ma iya cewa dan bata haihu bane yasa tai masa haka*_ _*idan har namiji mai son yarane koda kece kika haifa saikinyi hkr dashi akansu sbd duk abinda kikai baki iya bane' k'uma bazai ganiba' banle ba kece kika haifa ba' shiyasa Aisha sai tai hkr sosae da zhrdee' duk da irin soyayyar da yake mata' karkuga laifinsa' saidai dukan da yai matane too much wlh har taban tausayi*_ 😉😉 _*Aisha kada ki damu zhrdee nakine forever cool ur mind*_ 🤣 🇮🇳 *_FASMA NIGER_* 🇮🇳 _*ina tayaki murnar kammala littafinki mai suna (sanadin accident) hakika kin wa'azartar k'uma kin nishadarta' dukkan kura' kuran da kika samu a ciki ubangiji Allah ya yafe maki' wa'zartarwa da kikai kuma Allah tabada ikon aiki dashi' Allah ya kara basira da zakin hannu ameen. sai mujiki a littafi na gaba*_ 🤣🤣 4⃣5⃣ "zhrdee yana shiga d'akin Hjy gun *Akbar* yanufa' gani yadda yake faman kuka yasashi zama kusa dashi h'ade da daukarsa har zai rungume kenan Hjy ta daka masa tsawa" "h'aba zhrdee menene kakeyi h'aka baka gani ciwone a jikinsa zakaje ka rungume sa' ka shinfidashi kawai yasha iska" "to ai gani nayi be daina kuka" "to ba dole yai kuka ba kuna wasane' wai ma garin yaya akai ya konene?" "wlh jawo plast yayi jikinsa" "to idan banda hali irin naku' kusan akwai yaro me rarrafe zakuje ku ije plast a inda yaro zai iya ja" "wlh Hjy tsotsayine" "tsotsayi ko ganganci' wani halin banza kawai"... " dan Allah Hjy kiyi hkr" "waini ina matan kane gaba dayan su fa babu wanda ya leko" "duk Hjy na mgnr ne tayiwa angon nata fifita" "tananan" "ban gane tananan ba' tananan ko sunana" "who Zainab tana ciki" "ita Aisha fa?" "shiru zhrdee yai" "da kaifa nakeyi" "nakoreta g'idan su" "g'idan su kace' me tai maka?" "laifine taimi" "eh" "wani irin laifine tai maka h'aka da har zaka koreta g'idan su" "laifi dai tayi' Hjy yaronga har yanzu be daina kuka ba' kodai na daukesa na kaisa gun mmnsa tabashi nono ko zaiyi shiru" "a'a bassa kawai taji da kanta' kamar cikinta zaikai wata bakwai ko" "eh tashiga na bakwai kenan" "to kagani ko' kyalesa kawai itama tasamu ta huta k'uma taji da kanta" "Hjy ban fahimata ba?" "yayesa za'ayi kawai" "yaye fa kikace Hjy da wnn ciwon?" "eh' kada karamu babu abinda zai samesa" "Hjy Dan Allah kiyi hkr a barsa har yawarke" "zhrdee kenan idan akace a barsa har sai ya warke ashe zasu sha nono tare da kanisa kenan" "kamar yaya Hjy?" "snn ta haihu mana" "yanzu Hjy kina nufin Abbana bazai warkeba har Zainab ta haihu" "to Ai kuna h'aka take" "himm kawai yace" "snn yace to Hjy yanzu menene abinyi?" "kamar yaya?" "wlh Hjy nidai nafi aminta da akaisa hospital" "to shikenan tashi muje' amma kafin mufita jeka ka kirami Zainab" "to kawai zhrdee yace snn ya mike' yana shiga d'akin Zainab ya sameta kwance' Zainab Hjy nakira" "tace h'ade da mikewa tanufi d'akin Hjy' riga yasa kawai yafita" "da sallama Zainab ta shiga Hjy ta amsa da shigo' "har kasa Zainab ta duka tace gani Hjy' duk a lkc *Akbar* bebar kuka ba' shiyasa Zainab ta dauke kanta daga garesa bata kallesa amma tanajin zafi kukan da yakeyi har cikin zcyrta" "waini Zainab ko kinsan abinda ya h'ada Aisha da zhrdee da har ya koreta g'ida?" "nima bansani ba' ihunta naji tashigo dakina a guje' yana biye da ita" "subhanallh' harda dukane?" "wlh a guje tabar g'idan' ko takalmi babu" "dawa ya tambyeki' waya tashi ki koma daki"... "ita kanta Zainab da hjyn basusan zhrdee ya shigoba" "da sauri Zainab ta mike har zata fita *Akbar* ya rike mata haban zani yana kuka ta daukesa" "da sauri zhrdee ya daukesa cikin tsomma' gani yadda Abba ya koma kwallane kawai suka zubowa Zainab ta saurin fita sbd kada Hjy ta gani' amma zhrdee yagani' kai kawai ya kada' hijab kawai Hjy tasa snn suka fita" "saida Hjy ta shiga mota ta zauna snn zhrdee ya mika mata *Akbar* ya shinfida mata shi a cinyarta snn ya zaga yashiga suka nufi hospital' a hanyarsu na tafita hospital ne Hjy take sake tambyarsa abinda ya hadasa da Aisha" "duk da h'aka shiru zhrdee yai yaki fadan abinda Aisha tai masa" "dama ni bance dole sai ka sanar dani tsakanika da matarka ba' amma koma me tai maka inaso yazama shine farko k'uma shine karke kada kasake dukan ko daya daga cikinsu' kanaso ka zama namiji me dukane?" to wlh kada ka kasake h'aka" "to naji Hjy k'uma ngd" "idan har laifi ne tai maka meyasa bazaka hukuntata a d'akin taba' bayan ka duketa k'uma ka koreta?" to wlh kada ka sake h'aka' k'uma muna dawowa daga hospital inaso kaje ka dawo da'ita" "shiru zhrdee yai be tanka ba" "kana jina kuwa?" "eh' naji Hjy' amma dan Allah kibari zuwa yamma snn natafi daukota" "amin amma ka tabbata yau tadawo" "eh zanje ai" "suna isa hospital doct ya dubasu' maguguna ya basu suka dawo g'ida" "waya Zainab ta dauka ta kira inna *Hulaira* inna na dagawa Zainab tasa kuka' a gigice inna tace lfy Zainab' meke faruwa?" "cikin kuka Zainab take fadiwa inna *Akbar* ne ya kone" "subhanallh' Zainab garin yaya?" "cikin kuka tace nima ban saniba a d'akin Aisha ne" "Aisha fa!!!" "eh Aisha" "nima ban saniba Bbn sane ya kaisa d'akin" "to shikenan Zainab amma dan Allah ki daina kuka h'aka' k'uma in Allah ya yarda idan bbnki yadawo kasuwa munanan zuwa" "to inna sai kunzo" "to Zainab' amma fa kidaina kuka kinga bake kadai ace bako" "Zainab na kashe wayar zhrdee yashigo' ita k'uma Hjy tai bangaren ta da *Akbar* Zainab naji shigowar zhrdee da sauri ta share hawayen dake fuskanta' tace kadawo" "nadawo' amma yah!!! naga kina kuka?" "wasu kwallan suka sake zubowa tace babu komai" "matsowa yai kusa da'ita snn ya jawota jikinsa ya rungumeta h'aba Zainab kuka me kikeyi h'aka kiyi hkr mana abban ma da kike kuka danshi yasamu sauki har yai bcc' " himm kawai Zainab tace" "da gske Zainab" "to garin yya akai ya kone?" bayan ka daukesa lfy daga nan d'akin?" "tsotsayine kawai Zainab". " tsotsayi kamar yaya? " kodai Aisha ce ta konasa"... "a'a ba'ita bace' tsotsayi nedai kawai" "idan ba'ita bace to metai maka da har kai mata irin wnn duka h'aka' bayan tunda nake dakai baka taba koda marintaneba banle duka". " laifi kawai taimi raina ya baci yasa nayi mata duka' amma ba'ita ce ta kona Abba ba' *Akbar* a hannuna ya kone" "a hannunka k'uma kai da kake daki ina kasamu ruwan zafi da har kasamu ruwan zafi?" "eh ninace takowomi daki' bayan tadawo ta'ije har na b'ude plast d'in sai naje dauko abu kafin nadawo shine *Akbar* yaje ya yawo plast d'in jikinsa" "himm kawai tace amma bata yarda da mgnrsa ba" "kiyi shiru Zainab" "yanzu ina Abba d'in?" "yana gun Hjy yana bcc" "zama Zainab tai a b'akin gado taci gaba da sharban hawayenta" "da yamma bayan sallar isha'i zhrdee yaje g'idan su Aisha' da sallama yashiga cikin g'idan' ummata ta amsa da shigo mana" "bayan su gaisa shiru zhrdee yai" "umma tace yaya dai zhrdee?" "gun Aisha nazo" "kwanawa Aisha kira tai" "da sauri Aisha tazo' tana zuwa taga zhrdee duka gaban umma' tsaki tai ta juya zata wuce" "tsawa umma ta daka mata' waye sa'arki anan da mikewa tsaki" "nifa banji dake ba" "to dawa kikeyi?" "tai shiru" "dawo nan ki zauna" "tsayawa tai gefe tana kwashe zhrdee da harara' shiko bema san tana yiba" "badake nakeyi ba?" "snn aisha ta dawo ta zauna' tana zama abbanta yai sallama ya shigo" "gani zhrdee yasashi karisowa da fara'arsa' juyawa zhrdee yai suka gaisa snn Abba yace lfy ko?" "Abba yai tambyarne sbd bashi a g'ida Aisha tazo lkcn yana kasuwa' ummace ta zayyana masa abinda ke faruwa" "Abba yace duk subisa parlour sa' bayan su shiga kowa ya zauna Abba yasake tambyar zhrdee gskyar lamari" "wlh Abba duk da nasan tsotsayine amma harda laifin Aisha'... "laifina k'uma?" "kwarai laifine Aisha" "to meye nawa a ciki dan yaronka ya kone' ko k'uma sharri kazo kai?"... " kafin takare tuni umma ta buge mata baki " "Abba yace ina sauraranka" "wlh Abba yaro na kuka naje d'akin mmnsa na daukesa zuwa d'akin Aisha' inda tasan bataso na rinka shiga mata daki da yaron wlh da bazan shiga mata dashi dakinta" "idan na dorasa akan gadonta ta saukesa kasa'ni. kuma na do rasa ne sbd rarrafe yakeyi kada yaje yai mata barna' ita k'uma tana zuwa ta saukesa kasa wai sbd zaibata mata gado' harfa wasa nake mata cewa idan yabata gadon zansiye mata wani' amma besa Aisha ta kyalemi yaroba ta saukeshi yaje yajawo plast ya kone yanzu h'aka yananan gaba daya yasalbe" "dukkansu subiyu salati sukasa" "zhrdee yaci gaba da cewa koda nazo inayi mata mgn sai tarigani da fushi ni da haushi ya kamani na duketa"... "umma tace ni wlh banji dadi bama inda so samune da kai mata wanda yafi h'aka' wawiyan yarinya kawai' wanda batasan me sonta ba" "kuka Aisha tasa' gani h'aka yasa umma dauketa da mari ta h'au dukanta' zhrdee na kallonsu amma beyi kokarin hana umma ba" "Abba dake zaune yace Hafsat kyaleta h'aka' umma na cire hannu daga jikin Aisha' Abba yace zhrdee" "na'am Abba" "Dan Allah Dan annabi kayi hkr' badan inaso na goyi bayan Aisha ba a'a sai dan bamu da wani kalmar da zamuyi amfani dashine wajan baku hakuri' amma ga Aisha nan ka dauketa ku tafi duk hukuncin da kaga yadace kai mata' sbd koda nine taiwa h'aka bazan yarda ba' jikin zhrdee yai sanyi" "Aisha najin h'aka tasa wani sabon kuka' abbanta yace wlh na rantse idan kika bari na tashi sai kinyi nadamar zuwanki g'idan nan" "Aisha najin h'aka da sauri ta mike tabar d'akin hijab dinta ta dauko babu wanda ta sallama tafice'. zhrdee na gani fitarta ya sallami su Abba snn ya mike" "Abba yakara bashi hakuri h'ade da alkawarin zuwa ya duba me jiki" "babu komai Abba basai kazo bama" "ina ya yuwu' kai dai sai muzo kawai" "to shikenan Abba ngd" "muke da godiya' Allah ya kara lfy" "amin" "zhrdee yana fita yaje ya samu Aisha a gefe kusa da mota ta tsaya' batare daya tanka mata ba yabude mota ya shiga' Aisha dake tsaye batazo ta shiga ba' shiru2 da yaga batada niya shiga ta glass ya leko wlh idan bakizo kin shiga ba' sai nazo da mota na nikeki a gu" "tsaya tai kamar bada ita yakeyi ba" "tada mota yai a guje yai kanta' gani h'aka yasa Aisha tsalle snn taje ta shiga suka tafi' har suka isa babu wanda ya tankawa d'an'uwarsa' yanayi parking Aisha ta b'ude mota zata fita' kitsaya" "snn ta tsaya" "fuska a daure' to ba nadawo dake ba' saura koda wasane kibari Zainab ko Hjy susan da hannunki a cikin konewar Abba' idan kika bari daya daga cikin mutani g'idan nan suka sani wlh duk abinda akai maki babu ruwana" "Aisha bata tankashi ba ta b'ude mota ta fita shima shima fita yai' suna shiga sukaga iyayen Zainab duk sunzo harda bbnta dukawa sukai suka gaisa snn Aisha ta shige cikin dakinta" "zama zhrdee yai kusa da abbansa' itama Zainab na zaune kusa da innarta mahaifiyar Zainab k'uma tana kusa da maigidanta' Hjy k'uma tana kusa da Alhj' *Alhj Musa* yaiwa zhrdee Allah ya kyauta" "murmushi kawai zhrdee yai" "inna tace toni wai garin yaya ako konami maigidana ne h'aka?" "murmushi zhrdee yana shafan kansa h'ade da cewa wlh tsotsayine kawai Allah ya kawo" "Allah ya kiyaye na gaba" "amin yace" "tunda yazama h'aka abani maigidana kawai naje na kula da kayana" "dariya Hjy da Abba sukai Hjy tace wlh da dai yafi nima nahuta" "zhrdee dake zaune ya daure fuska" "Mmn Zainab dake zaune duk mgnr da sukeyi bata tanka masu ba saidai tai murmushi kawai" "da suka tashi tafiya inna ta mikawa Hjy *Akbar* snn sukai sallama Zainab da zhrdee har b'akin mota suka takasu' bayan sun wuce snn suka dawo ciki" "zhrdee d'akin Aisha yashiga' yana shiga ganita yai zaune tana kuka' Aisha har yanzu kuka kikeyi' ba mgn ya wuce ba?" "Aisha tai banza dashi taci gaba da kukanta" "Aisha badake nake yiba?" "still tai banza dashi" "zama yai kusa da'ita h'aba Aisha Dan Allah ki daina kuka h'aka' kinsan tsotsayine idan Allah ya kawo babu wanda ya'isa ya hana faruwan abu". " fisge jikinta tai h'ade da cewa tsotsayin banza tsitsayin wofi' ai kai bakasan da h'aka ba' ida kasan da h'aka da bakaimi abinda kai ba" "to naji yanzu dai abar mgnr yawuce" "hannu yakai zai riketa' da karfinsa ta igijeshi kadan yarage ya f'adi' yana mikewa ya dauketa da mari' kafin ta mike yasake kai mata wani' har ya daga kafa zai kai mata tokari mgnr Hjy ce ya fado masa yasashi meda kafarsa yana cizon lebersa" "Aisha tasa ihu tana kuka' hannu yasa ya toshe mata b'aki sbd Zainab zata iya ji" "besan tun gaba lkcn da yashige d'akin Zainab ke makale tana jin duk abinda sukeyi ba" "Aisha na kokarin kwace kanta' zhrdee ya igijeta gefe yana cewa banza kawai' kin dauka wani abu nake nima a gunki' da har kike nima ki walakantani?" ke d'in me' nifa kikaiwa laifi' amma ban dubi laifinba nazo ina baki hkr shine dan tsabar raina hankali kike tureni" "halin kin dauka nazo niman wani abune a gunki?" wlh Aisha idan badan darajan soyayyar da nake makiba wlh da... "himm kawai yace' snn yace anya kuwa Aisha bakida aljannu? gani nayi konami yarofa kikai k'uma har kinada b'akin mgn" "banza dashi Aisha tai' taci gaba da kukanta' suna h'ada ido saidai ta hararesa" "shima tsareta da ido yai yana mmkin ta' da haushi ya sake kamashi yace wlh Aisha inda badan darajan Hjy ba na rantse da yau nai maki shegen duka amma ki kiyaye" "hanyar kofa yai zaifita' Zainab naji tafiyarsa a guje tabar gun' Aisha na gani zai fita f'adi tai a kasa taci gaba da kukanta' " gani abinda takeyi yasa zhrdee dawowa daukarta yai tsaf kamar yarinya ya kaita gado ya kwantar da'ita yana rarrashinta shima kanshi yaji babu dadi a zcyrsa 📖🖊 ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O .W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _*oyoyo my special aunt ina maki barka da dawowa my sister' yadda kika fara lafiya ubangiji Allah yasa kigama lafiya' duk wani kura kuran da zaki samu a ciki ubangiji Allah ya yafe maki' tare damu daki daya amin' Rahma Rufa'i nalele Hausa Fulani ina yinki sosai wlh my sister*_ ❤ 🤝 _*OYOYO SIS AYSHA ALIYU GARKUWA'INA TAYAKI MURNAR FARA SABON NOVEL NAKI' UBANGIJI ALLAH YASA YADDA KIKA FARA LAFIYA KIKARE LAFIYA DUK WANI KUSKURE DA ZAKI SAMU ACIKI UBANGIJI ALLAH YA YAFE MANA BAKI DAYA AMIN' GASHI BAN'IYA FILLANCIBA SISTER BANLE NA SUBURBUDO MAKISHI DA FILLANCI AMMA HAKA KIYI HAKURI DASHI. ALLAH SARKI BABANA ABUBAKAR KATAFI KABARNI DA KEWARKA UBANGIJI ALLAH YA JIKANKA YASA KAHUTA AMIN SISTER ALLAH YA KARA DAUKAKA*_ 4⃣6⃣ "zhrdee yana fita daga d'akin Aisha na Zainab yashige' yana shiga daidai lkcn Zainab na zaune a b'akin gado tana hawaye' gani shigowarsa ne yasata share hawayen dake fuskanta" "fuska a daure tace kashigo' nashiho Zainab ya naga kamar kika kuka" "kuka k'uma?" babu wani kukan danakeyi" "amma ga alamar kinyi kuka" "kawai kewar Abbana ne" "kewar Abba k'uma bayan yanzu suka fita wanda ko g'ida basu kaiba" "kwanciyata tai bata sake tanka masa ba" "gani taki sauraransa yasashi fara tsirguwa kodai taji mgnr da sukai da Aisha ne" "zuwa kusa da'ita yai ya kwanta h'ade da shafe mata ciki' yana f'adin Zainab kodai wanine ya bata maki rai?" "kai kawai ta kada masa" "to meya sameki' kodai bakida lfy ne?" "kai tasake kadawa" "nine na bata maki rai?" "Zainab tace a'a" "jawota yai jikinsa ya rungumeta yana cewa zona matata Dan Allah ki daina kuka h'aka wlh banajin dadin ganinki kina kuka" "k'uma kinga gash bake kadai bace' Dan Allah kibari kaga irin laluran daya sameki a lkcn cikin Abba yasake kamuki kinji Zainab" "zhrdee yana rungume da Zainab ne duk yake wnn mgnr" "a zcyr Zainab ji takeyi kamar ta f'adi masa mgnr dataji sunayi da Aisha' amma k'uma idan tafadi zai gano cewa labe take masu' ko k'uma yace dama h'aka takeyi' ita k'uma wnn shine farkon labe da tai' shidima Allah ne yasa da k'uma rabon zataji mgnr da sukeyi' har tawuce jin zhrdee yana cewa *kecefa sanadiryar konewar Abba* jin h'aka yasa yadawo da sauri" *Dan dama tuni ta dade da zargin h'akan a zcyrta' h'ade da k'uma yadda zhrdee yake mata nuku nuku lkcn da ta tambyesa garin yaya Abba ya kone' duk wata hanyar da zaikare Aisha saida yabi ya kareta" "wani zcy na cewa wlh kije ki fadiwa Hjy ne kawai" "wani zcy k'uma ta yace kyaleta kawai gaba yafi baya yawa".. " shiru da tai ne yasa zhrdee cewa Zainab tunanin me kikeyi h'aka?" "saida Zainab ta share hawayenta snn tace babu komai" "mikewa zhrdee yai ya tube ya kwanta har bcc yafara daukarsa Zainab tace tashi kaje' ka mance kamar ba nan kakeba bane" "mikewa yai ya fita batare daya dauki kayansa ba' yashige d'akin Aisha" "washe gari da yamma lkcn *Alhj Kailani* wato abban zhrdee da shi kansa zhrdee da yayyinsa duk suna g'ida a zaune a parlour su Hjy yya Shamsudee ne ke rike da *Akbar* suna hira iyayen Aisha sukai sallama' dayake sai kawuce parlour su Aisha snn kashige nasu Hjy yasa abbanta da ummanta tsayuwa a d'akin kofar g'idan" "jin muryan bbn Aisha ne yasata fitowa da sauri tana f'adi lahh!!!! Abba!! kune h'aka?' sannu da zuwa snn tace dasu bismillh" Abba yace a'a ina maigidan naku?" "yana ciki Abba" "jeki ki sanar dashi zuwanmu" "to Abba' juyawa tai takoma ciki' dakinta ta shiga ta dauki waya ta sanar dashi zuwan iyayenta" "mikewa kawai yai batare daya cewa su Hjy komai ba" "kai tsaye waje yaje yai masu iso zuwa cikin parlour' bayan su shigane ya duka suka gaisa a cikin girmamawa snn yasake mike h'ade da yaiwa Aisha signal da ido mikewa tai suka koma daki' suna shiga zhrdee yace Aisha yaya zamuyi?" "da mefa zhrdee?" "kinsan har yanzu su Hjy basusan yadda akai ba' k'uma yanzu gashi su Abba suzo kada suyi mgnr da zaisa a gane tsorona kenan" "shiru Aisha tai tana kallon zhrdee" "Aisha kiyi mgn mana" "eh to bari naje na sami ummata nayi mata bayani' kai yanzu ina zaka?" "zan sanarwa su Hjy ne" "to jeka kafin kafito zan mata bayani" "to shikenan' bari na shiga gun su" "fita tai taje kitchen ta dauko ruwa da lemo ta dawo parlour' bayan ta ijene tacewa umma" "na'am menene Aisha" "inaso mgn da kenan" "ni k'uma?" "eh kenan" "to f'adi ina jinki" "muje daki" "a'a f'adi kawai anan duk daya ne ai" "uhmmm""""" "uhmmm"" "kiyi mgn mana Aisha" "dama zhrdee ne yace na sanar damu".. "kin k'uma yi shiru karisa mana" "dama wai"" wai ""!!. " wai " me? " "dama cewa yai Dan Allah bayaso Ku nuna cewa""". " cewa' me?" "cewa' me?" "cewa bansan komai ba akan konewar yaronsa" "salati umma tasa h'ade da cewa yanzu boye masu kukayi?" lalla Aisha"... "sallamar su Abba da Hjy ne ya katsasu' abban zhrdee yaje sukeyi musa baha h'ade da gaisawa' su hjy suma suka gaisa h'ade da yimasu Allah ya kyauta" "daukan yaron umma tai tana kallon yadda jikinsa yai h'ade da tosaya masa' k'uma har cikin zcyrta taji babu dadi" "Abba dake gefe kallo daya yaiwa *Akbar* be kara na biyu ba" "Zainab da ba'a sanar da'ita ba' fitowa tai sanye da hijab suka gaisa ta koma dakinta" "basu jima sosae ba sukai sallama h'ade da fatan samu sauki" "Hjy da Abba suka rakasu har b'akin mota' saida su kaga tafiyarsu snn suka koma ciki" *AFTER TWO WEEKS* tun dare Aisha ke amai har asuba' ga zazzabi jikinta har rawa yakeyi' ko sallar asuba ba'ayi ba zhrdee ya dauketa zuwa hospital dayake prvt hospital ne ya kaita suna zuwa aka tallafa masu' wani doct dayazo ya dubeta h'ade da tambayoyi tana bashi amsa' snn ya amshi fitsrinta yaje aka gwada yadawowa zhrdee da good news" "zhrdee kamar betaba samu wani da' a duniya ba' tsalle yai h'ade da rungumar Aisha dake kwance da drip a hannu a take ya dauki waya ya kira Mmn Aisha ya sanar da'ita Aisha na hospital" "Allah ya kara sauki tace h'ade da cewa tananan zuwa' snn zhrdee ya sanarwa Hjy Aisha na hospital batada lfy doct yace cikine da'ita" "murnar Hjy tai h'ade da cewa sai tazo" "mikewa tai ta dauki hijab tasa har ta kai b'akin kofa *Akbar* yasa kukan zaibita' gani h'aka yasata daukarsa ta kaisa gun Zainab h'ade da sanar mata Aisha na hospital babu lfy" "Allah ya sauwake" "amin Hjy tace snn ta fita" "tana isa hospital umma Aisha itama tana isa' haduwa sukai suka karisa cikin d'akin' zhrdee yana ganisu da sauri ya dauka daga kan gadon inda yake zaune gefen Aisha yaje ya amshi Mmn Aisha kayan dake hannunta" "bayan ta zauna ne suka gaisa a ladabce tai masa sannu da me jiki' lkcn Aisha na bcc' dukkansu basu tafi g'ida ba sai da yamma umman Aisha ta koma g'ida' ita k'uma Hjy saida su Abba sukazo snn suka koma tare" "bayan su koma ne aka turo Amatullah ta kwana da Aisha' ko kafin Amatullah ta iso fita zhrdee yai yaje ya siyo masu abinci a restaurant h'ade da yoghurt da nama snn yadawo' yana dawowa lkcn Aisha ta tashi drip da aka samata k'uma ya kare hannu yasa ya zare mata alluran snn ya dagota ta tashi zaune toilet ya shiga ya dauko kwanu silver ya dawo b'ude ruwan swan yai yasa mata a baki ta kuskure bakinta snn ya meda kwanu toilet ya dawo shims hawa kan gadon yai ya dauko ledar nama ya b'ude da kansa yake mata har ta koshi snn yaci nasa" "har Amatullah tazo zahradee be tafita zama tai sukai ta hira harda aishan' gani 11MP yai yasa Amatullah cewa yya tashi kaje g'ida kaga dare yai" "eh zan tafi amma sai anjima' bata tanka masa ba' sukaci gaba da hiran har 2-30 nan ma tasake mgn' duk da h'aka be tashi ba sai kwata after 1AM ya zari key d'in mota sukai sallama da Aisha h'ade dayi mata kis snn yatafi" "tsaki kawai Amatullah tai ko kallo basu ishetaba" "ko kafin ya'isa g'ida Zainab tai bcc be tada ita ba tubewa yai yai wanka snn ya kwanta' da asuba kuwa koda yafita masallaci bedawo g'ida ba saida ya yaje hospital yaga kwana Aisha misalin goma snn ya dawo g'ida" "ko kafin yadawo ta h'ada masa abin breakfast yana dawowa yai breakfast snn yai wanka ya shirya yafice" "ido kawai Zainab ta zuba masa bece mata kala akan Aisha ba itama bata tambya ba' yau ma h'aka ne zahradee bedawo g'ida ba sai daya saura' washe gari akayi sallama' da kansa ya daukota ya dawo da'ita g'ida' yau ko babu inda ya leka sunanan leke da juna duk da ba'itace keda girki ba" "da dare har Zainab ta kwanta zhrdee ya tada ita' ta mike h'ade da tambyar lfy" "Dan Allah kifito parlour inaso muyi mgn ne" "mikewa tai suka fita' yana gaba tana baya' bayan su zauna snn itama Aisha tana zaune a gefe' shima ya zauna a tsakiyarsu' snn yace Zainab" "tace na'am" "ba komai bane yasa nace kifito nan muyi mgn sbd Aisha ne".. "wani abune ya sameta?" "eh batada lfy ne" "shine bansani ba' kodai akwai abinda kuka kullane yasa za'a sanar daniba" "Dan Allah kiyi hkr ba niman masifa nakeyi ba" "ina jinka". " dama akan mgnr girki ne' gani nayi tunda yanzu tanada ciki be kamata tarinka aikin wahala ba shine nace daga yau kece zakici gaba da girki har zuwa wani lkcn" "ciki!!! ciki fa kace?"!! " eh' ciki "!! " niba cikine dani ba?". "ai naki ya girma' ita k'uma nata yarone kamata yai abashi kyakkyawar kulawa sbd kada wani abu ya sameshi"!!!!!! "h'aka nefa' dama mancewa nayi' tunda a yaune aka fara yimaka ciki a g'idan nan' koda yake ba laifinka bane matar so ce" "Zainab ni kike fadiwa mgnr banza?" "kayi hkr ni ba mgnr banza NA f'adi maka ba' Allah ya iganta' mikewa tai tashige d'akin ta" "mikewa zhrdee ya ya kama Aisha suka shige dakinta" "Zainab na shiga daki tasa kuka' tai kuka har tagaji babu me rarrashinta' Dan kanta ta hakura" "tun daga lkcn ita ke girki rana da yamma wanke wanke shara gyara parlour duk wani aikin g'ida yadawo akan Zainab' itako Aisha tana zaune a daki' koda Zainab tai akinci ba lalla bane Aisha taci' mafi yawanci lkc saida abawa almajirai ko a zubar' gobe be hana Zainab yin wani abinci' duk da itama yanzu manaji takeyi da jikinta sbd hawan jikin da take dashi tun cikin Abba amma be hanata yi" "ita kanta Hjy taga csnji wajan yadda da yake kulawa da Abba yanzu bayayi' koda magani ko madararsa ya kare sai Hjy tai ta fama dashi snn yake siye wasu" "bata kawo tunani komai a zcyrta ba sbd ta dauka yanayin kasuwa ne' shiyasa wani lkc idan be siyeba saidai tasa su yya Shamsudee su siye masa" "shiko zhrdee koda ranar girki Zainab saiya raba dare a d'akin Aisha snn yake dawowa daki Zainab' itama yanzu ta saba shiyasa bata nuna h'akan yana damuta' " tunda doct yace Aisha tafara zuwa awo (intinatel) wani lkc rana daya yake fito masu amma zhrdee baya tsayawa jiran Zainab saidai ya dauki Aisha sutafi' idan Zainab tai mgn sai yace mancewa yai' shiyasa yanzu idan ba shine yace ta shirya ya kaitaba bata masa mgn zuwa' saidai bayan ya tafi kasuwa taje tabi napep taje ta dawo" "duk da h'aka bata bari Hjy tasan halin da take ciki ba' daga ita sai ita sai k'uma shi zhrdee d'in dayake mata" "da yake yau ta tashi jiki babu dadi ko girki batai ba tana kwance a daki har dare' koda zhrdee ya dawo yaje kitchen daukar abinci yaga babu komai k'uma gashi Aisha tace masa tun safe bataci abinci ba sbd Zainab batai ba" "d'akin Zainab ya shiga ya ganta a duke a gefen gado kanta a sunkuye' Zainab meyasa bakiyi abinci ba kikabar Aisha da yunwa?" "Zainab na duke tace banida lfy ne" "karya kikeyi manafuka yar'bakin ciki' wato kinaso yunwa ya kashe ya kashe abinda yake cikinta ko?" to ta Allah ba takiba' yanzu zantafi na siye mata abinci" "a fusace yafita kai tsaye restaurant yanufa" "yana fita Zainab ta fasa da kuka' tayi kokarin ta mike amma takasa sbd duk kafafuwanta su rike' zama tai firshan a gefen gado har cikin ya f'adi mata" "yana fadawa ta mike taje tai wanka snn tai sallah taso shan koda ruwan Lipton ne amma takasa sbd bakinta babu dadi' haka ta kwanta" "tana cikin bcc misalin 12AM wani sabo ciwon mara yatashi babu ji babu gani tun Zainab na dauriya har yakai ta kasa' tana duke a gaban mirrow gani asabar yai yawa tasa kuka lalabawa tai ta dauko wayarta number zhrdee tai dllng' tayi kira yafi ten Miss call zhrdee be dauka ba' bemasan tana yiba sbd yasa wayar a silent' da Zainab taga ba'a daga ba k'uma da shi tafara gani abu ta gabanta rarrafawa tai taje b'akin kofa ihu tasa tana kwadawa Hjy kira" "a birkice Hjy ta ta tashi daga bcc tana tunani ko mafarkine' jin ansake wani ihu yasata fitowa taga wake ihu' ashe su yya Shamsudee suma duk su tashi sbd ihu da sukaji' amma bada su zhrdee da Aisha' a lkcn ne ma Aisha taka lafewa a jikin zhrdee ta kankamesa" "tare suka iso gun Hjy da su yya harda Abba gani Zainab da tai h'aka yasata salati a rude tace su yya su tayata kamata duk cikinsu babu wanda yasa hannu' kinkimarta Hjy tai zuwa cikin daki" "gani duk hayaniyar da akeyi besa zhrdee da Aisha su fito ba kyale Zainab tai taje tasa kafa ta tokare kofar da karfi kofa ta b'ude' dama ba key sukasa ba' turawa kawai sukeyi' su yya suna gani kofa ya b'ude da sauri suka kauce a gun harda Abba" "a gigice zhrdee suka tashi' da sauri ya dauki riga yasa snn yafito' itama Aisha zani ta daura h'ade dasa hijab tafito' zhrdee yana fitowa Hjy ta daga hannu zata kai masa mari da sauri ya kauce' " shida Hjy suka kama zahradee akasata a mota zuwa hospital yya Shamsudee ke tuki' suna isa ko minti goma basukai ba Zainab ta haihu baby girl" "Hjy tai murna shima zhrdee d'in babu laifi duk da yaji dadi a zcyrsa amma a fuska be nuna ba' bayan Zainab ta shirya aka bata bedrest' bayan sallar asuba aka sanarwa g'idan su Zainab' ba ai minti gomaba saiga inna *Hulaira* tazo' Zainab na gani innarta tasa kuka" "bayan Hjy ta fitane inna ke tambyar Zainab meke damuta?" "Zainab tace babu komai" "inna tace to ta daina kuka h'aka tayi hkr komai yai zafi zaiyi sanyi" "tunda zhrdee yabar hospital be dawo ba har yamma gashi anyi sallama' bayan anbasu sallama ne inna da Hjy suka kwashe kaya zuwa mota" "inna tasa hannu ta kamo Zainab h'ade da mika mata hijab tasa' saida Zainab tasa ta gyara tsaf inna tace kawo hannunki muje ko" "inna babu inda zanje" "me kikace Zainab?" "Zainab tai shiru" "Zainab ba dake nakeyi ba" "Zainab tasa kuka tana f'adin babu inda zani inna" "Zainab kanki daya kuwa Zainab?" idan baki koma g'idan mijinki ba ina zaki?" "gidan mu zani" g'idan ku fa kikace Zainab?" "murmushi takaici Hjy tai snn tazo ta dafa kafadar Zainab' Zainab kiyi hkr ki koma d'akin ki kinji Zainab' idan ma wani abu yake maki inaso ki sanar dani da kaina zan dauki mata ki akai" "Zainab tasa kuka batare da tace kalaba" " babu irin mgnr da Hjy da inna basuyiwa Zainab ba amma taki yarda" "duk da ran Hjy ya baci amma h'aka ta dan ne fushinta tacewa Inna tunda abin yazama h'aka babu damuwa ta dauketa sutafi g'idan kawai idan yaso daga baya lkcn ta huce sai lallabeta ta dawo d'akin ta" "inna tace ita wlh bazata iya daukar Zainab ta medata g'ida ba' amma tunda abin yazama h'aka bari ta kira Alhj kila idan yasa baki zata koma g'idan ta" "waya inna ta dauka ta kira Alhj ta sanar dashi abinda ake ciki' Abba yace abawa Zainab wayar suyi mgn' koda inna ta mikawa Zainab wayar Zainab taki amsa" "gani h'aka yasa inna kashe wayar' shims Abba dake g'ida mikewa yai ya dauki key d'in mota ya kamo hanya' ko kafin yazo inna tana tabawa Zainab baki amma Zainab takafa ta tsare' Abba na isowa Zainab na ganisa ta fashe da kuka murmushi kawai Abba yai snn ya kariso gunta" "gani irin kukan da takeyi ne yasa Abba zuwa kusa da'ita snn yace Zainab naji wani mgn ne a gun innarki Zainab kiyi hkr ki koma d'akin ki mana Zainab" "cikin kuka Zainab tace Abba kayi hkr bazan koma ba" "h'aba Zainab kodan darajan yaranga kiyi hkr ki koma kinji Zainab" "Abba Dan Allah kayi hkr kawai" "nayi hkr dame Zainab" "Abba nagaji da aure' banayi k'uma" "Zainab3 idan har nine na haifeki umurni nake baki kibisu kawai kutafi" "dukawa Zainab tai har kasa gwiwa bibbiyu tana rike da kafar abbanta tace Dan Allah Abba kayi hkr ka yafemi amma wlh bazan koma g'ida zhrdee koda shikadai ne yarage a duniya na hakura dashi" "wani irin kuka tasa har jikinta na rawa" "Hjy dake tsaye jikinta yai sanyi sosae h'ade da kunya' zcyrta tana tambyar kanta wani irin abune zhrdee yakewa Zainab h'aka da har tace bata sonsa?" "gani irin kukan da Zainab keyi yasa Abba sa hannu ya dagota ya rungumeta' itama rungumesa tai taci gaba da kuka" 📖🖊 ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _~*A GSKYA NAJI DADIN CONMMENT D'IN KI SOSAE SBD TUNDA NAFARA WNN NOVEL BABU ABINDA SANCEWA UBANGIJI SAI GODIYA' SBD DAUKAKAR H'ADE DA FARIN JINI' WASU CONMMENT D'IN MA HAR NAKAN KASA KARANTAWA SBD YAWANSU' SHIYASA A KULLUM NAKE KARAWA UBANGIJI NAGODE' K'UMA MASOYANA NAGODE NAGODE SOSAI ALLAH YABAR ZUMUCI*_ _*SADIYA LONG LIFE HAUSA NOVEL GRP' A GSKYA TUNDA TAFARA WNN NOVEL NAKE GANI CONMMENT AMMA BANTABA GANI CONMMENT DAYA BIRGENI BA IRIN NAKI NAJI DADI SOSAI ALLAH YASAKA DA ALKAIRI' IDAN HAR KINADA AURE ALLAH UBANGIJI YA BAKI ZAMAN LAFIYA DA MIJINKI' IDAN K'UMA BAKIDA AURE ALLAH UBANGIJI YABAKI NAGARI NAGODE*_ 4⃣7⃣ "Abba yace dan Allah idan bazaki damuba ki d'an bamu waje" "Hjy Mmn zhrdee kenan' batare da tanuna damuwa ba tace babu komai Alhj snn ta fice' ita da inna *Hulaira* bayan su fita ne *Alhj Musa* ya kama Zainab ta zauna a b'akin gado' shima ya jawo kujeran dake gefe ya zauna kusa da'ita suna fuskantar juna" "snn yace Zainab" "na'am Abba" "banaso kiboyemi komai a tsakani zamanki da zhrdee' inason sani abinda yake maki sbd na dauki dan ba baiwa na bashi ba" "cikin kuka Zainab tace babu komai Abba nidai kawai nagaji da zama dashine" "a'a Zainab ruwa baya tsami banza" "shiru Zainab tai tana share hawaye batare da tace komai ba" "himmm Zainab kenan naji dadin h'akan sosae' da kika zamo mace mai sirri' k'uma ina alfahari dake a matsayin *yan* a gareni" "yanzu kinga abinda za'ayi kiyi hkr ki koma d'akin mijinki' kinga duk uban na gari bazaiso ace shine sanadiyar mutuwar auren yar'sa ba" "ni kaina nasan kina zaune a g'idan dan nine' h'aka shima zhrdee albarkacin mahaifinsa yakeci' sbd *Alhj Kailani* idan da ana daukar mutum ayi kyauta dashi gaba daya dana bashi dan yafi h'aka a gareni' *Alhj Kailani* mutum ne mai matukar mutunci da sani darajan dan'adam a dai irin zaman da mukayi tun kafin mu auri iyayenku dashi komai nayi masa ban yarba" "Dan h'aka ina mai bafi hkr da ki koma d'akin ki' k'uma banaso kimi wani fahimta banayi h'aka da wata manufa ne ba a'a sai dan duk wata mace da kike gani batada inda yafi dacewa da'ita face d'akin mijinta' dan h'aka dan Allah kiyi hkr kinji" "naji Abba" "wlh Zainab inda ace yau zhrdee d'in ne da kansa ya b'ude baki koda da wasane yace baya sonki da tuni kin Dade da barin g'idan' amma tunda bashi bane kiyi hkr dan Allah' sbd idan har na biyeki muka kashe wann aure dole wani zaki aura kinga shikuma bamusan irin nasa hali ba" "h'aka ne Abba" "to kin gani kenan' k'uma banaso yarinya dake azo ana kirga maki aure' dan h'aka kiyi kinji' dama ita rayuwa tagaji h'aka' shikuma *AURE* kanshi da kike gani *IBADA NE* dole sai kinga abubuwa kala kala a ciki' k'uma banaso ki teallaka kibar yaran nan sbd idon *Uwa* ba karami abu bane' shiyasa nakeso kije ki rike yaranki sbd kada su walakanta" "jikin Zainab yai sanyi sosae' tana kwalla tace to Abba babu komai na hakura" "yawwa Zainab ngd' Allah yai maki Albarka yadda kikaimi Allah yabaki masu saka maki" "amin Abba" "sbd kiyayyar da k'uma jin mgn ta da kikaiyi ki f'adi duk wani abu da kikeso idan har befi karfin arzikina na maki alkawarin zanyi maki shi ko menene" "shiru Zainab tai tana kwalla" "kiyi mgn mana Zainab" "still shiru tai takasa mgn sai hawaye kawai" "to kinga karki damu tunda ga innarki nan zata rakaki har g'ida idan kunje sai ki f'adi mata kawai" "kai kawai Zainab ta daga masa" "snn ya mike h'ade da cewa ni zantafi g'ida kinga nadawo kasuwa kenan ban hutaba na sake fitawa" "hawaye kawai Zainab kenan' Abba ya shafe mata kai h'ade da cewa Allah yai maki Albark' ya kara lfy snn yafice" "yana fita suka hadu dasu Hjy' inna ce ta tareshi da yaya dai Alhj?" "kije kije dauketa kawai ku tafi g'ida' amma kada ki zauna" "murmushi kawai inna tai snn ta koma taje Zainab tafito suka shiga mota Hjy ce ke drive sbd su yya duk su riga su koma g'ida'. k'uma shi zhrdee d'in ma ba kasafai yake zuwa hospital ba banle tasa ran zaizo ya daukesu" "suna shiga g'ida Zainab da inna sukai d'akin Zainab' ita k'uma Hjy tai tana bangaren' sufi minti goma da shiga snn Aisha ta shige yiwa Zainab baraka' babu yabo babu fallasa a fuskan Zainab inna ce ta mika mata baby" "bata jima ba tafita' bayan ta fitane inna take tambyar Zainab' babu abinda Zainab ta boyewa inna komai ta kwashe ta fadiwa inna harda kukanta" "hakuri kawai inna tabata snn ta tafi g'ida sbd Abba yace kada ta dade" "da yamma lkcn zhrdee ya dawo Hjy da kanta tazo ta kira zhrdee zuwa bangaren ta' bayan su shiga a ladabce zhrdee ya gaidata snn ya zauna a kasa kusa da kafafuwanta snn yace Hjy gani" "yanzu sbd Allah zhrdee abinda kayi ka kyauta kenan" "cikin taushin murya yace menayi kuma Hjy?" "abinda kakewa Zainab mana" "wani abune tace nayi mata?" "koda batace ba halamu ya nuna zhrdee" "wani irin halimu k'uma Hjy' idan mgnr rashin zuwa hospital ne wlh yanayi ne yasa h'aka" "wani irin yanayine da zai hanaka zuwa hospital' haihuwa fa sukutun akai maka zhrdee' wlh shiyasa koda Zainab tace bazata dawo g'idan nan ba banga laifinta ba' sbd duk macce da takejin dadi a gun mijinta bazata gujeshi" "h'aka ne amma nidai nasa babu wani abinda nakewa Zainab na kuntatawa' k'uma ko cikin dare da take labour wlh duk ihun da takeyi wlh Hjy na rantse da Allah banji bane" "h'aba zhrdee ace bakaji ba' har nida nake nan naji" "wlh nace Hjy" "shikenan na yarda' amma dan Allah karinka kiyayewa" "insha Allahu" "yanzu Zainab d'in tana ina?" "tana d'akin ta" "wlh Hjy nidai nasan tsakanina da Zainab babu wata matsala a tsakanina da Zainab' nasha f'adi masu idan nayi masu wani abinda bemasu su sanar dani na gyara sbd gaba' amma meye amfanin taje hospital tana f'adi sbd Allah"... "a'a zhrdee a daiji tsoron Allah' yanzu fa kai ba yaro bane tunda kafara tara iyali' yanzu sbd Allah inda bbnta besa bakiba nasan da bata bimu mu dawo g'idan nan ba' dakar saida *Alhj Musa* yasa baki snn Zainab tabimu muka tadawo g'idan" " himm Hjy kenan' to meyasa da take kukan baki tambyeta dalilin kukan ba" "wlh babu irin tambyar da bamuyi mata ba amma taki f'adi' harda innarta' iba kuka ba babu abinda takeyi" "amma ina zargin ko ta fadiwa *Alhj Musa*' dan Allah zhrdee duk abinda zakayi a tsakani matanka kasa tsoron Allah a ciki' idan bamu gankaba Allah yana ganika' kana gani kenan dai yanzu kasamu mace duk wani abu da zakayi na rashin kyautatawa a gun matanka kaima za'ayi naka". " h'aka ne Hjy" "to Dan Allah ka kiyaye" "insha Allahu Hjy" "mikewa yai zai fita' *Akbar* dake kwance ya rike masa riga yana kuka" " *Abbana* yaya akai ne?' ka daukesa mana" "a'a Hjy bari dai nadawo tuku" "to shikenan' kamasa tai snn zhrdee yasa ya fice ihu Abba yasa yanabin bbnsa da ido" "d'akin Zainab zhrdee ya shiga tana zaune a b'akin gado rike da baby a hannunta' gani zhrdee ya shigo tace sannu da shigowa" "kema sannu' ciwo nakeyi da kike cemi sannu?" "au!!! sannu ma da nace yazama laifi?" "ke kika sani yar' niman gindin zama' ance kina kuka kince bazaki dawoba yanzu me yadawo dake g'idan" "bansani ba" "kada Allah yasa kisani bazan mara zcy" "nidai ba nine banza ba" "saiwa?" "wanda ya tanka". "ni kenan?" "kafi kowa sani" "na rantse da Allah Zainab idan kika zageni sai maki shegen duba" "kae kasani' mugu azalimi wanda ranar lahira zai tashi da barin jikinsa shanyayye kawai' wlh Allah ya'isa duk abinda kai mi ban yafe maka ba" "wlh Zainab kina bani mmki' nidai a rayuwa nasan sai mutum ya nimi a yafe masa snn za'ace anyafe ko ba'a yafeba' to nifa babu ko daya da har kike bata b'akin ki da baki yafe ba" "nasa ai k'uma dan kafadi h'aka bazanyi mmki ba sbd jahilci yariga yai maka katutuwa a rayuwa h'ade da bazar matarka banle ta nuna maka hanyar gskya" "kaeee Zainab duk abinda zakiyi da rashin mutunci da zakiyi wlh ya tsaya kaina' koda wasa kada kisake sa Aisha a mgnr ga" "kace h'aka mana tunda na tabi matar so' to wlh baka isa ba koda itace a tsaye a gabana idan har tai ba daidai ba saina f'adi mata"... " ashe ko kinada aiki' bazan mara zcy kawai wlh har ga Allah banso nadawo g'idan nan na gankiba' so nayi daga hospital kiyi g'idan ku" "ai badan kai na dawo g'idan ba' darajan Abbana ne" "ke kika sani wawiya kawai" "ni ba wawiya bace Kaine wawa marajin mgnr iyayensa kawai".... " kafin Zainab ta karisa zhrdee ya dauketa da mari". "kuka Zainab tasa taci gaba da f'adi masa bakaken maganganu" "dariya zhrdee yasa ya fita yabar d'akin" "tun daga rana besake shiga d'akin Zainab ba' h'aka ma Aisha idan tashiga su gaisa da safe bata kara lekawa sai wani safen k'uma' amma Hjy tana iya kokarin ta duk wani abu da tasan maijego zata bukata Hjy ta siyewa Zainab' innarta itama ba'a barta a baya ba' kusan kullum take zuwa duba Zainab' sauran aiki kuwa Amatullah da amatulrahaman sukeyi' ita kanta Aisha ta tsargi kanta shiyasa bata iya leka ko b'akin kofa' idan har tasake to zhrdee yadawo ne shidinma a daki ne" "kwana uku yarage suna lkcn Hjy na d'akin Zainab kamar daga sama zhrdee ya shiga' bayan su gaisa ne Hjy tace to zhrdee yau dai saura kwana uku suna me aka shirya ne?" "wani suna k'uma Hjy?" "wani suna kake dashi?" "nifa gskya Hjy babu wani suna da za'ayi' dan wlh banida kudi" "h'aba zhrdee wani irin mgn kakeyi h'aka sbd Allah' suna farko ba'ayi mata ba h'aka ma na biyu' to wlh baka isa ba' wai ma zhrdee dan Allah na tambayeka mana" "shiru yai be tanka ba" "wani irin yaro kakeso kazama sbd Allah' anya kanaso ka gama da duniya lfy kuwa?" "nifa ba wani mgn nayi ba' wlh duk kudin da suke hannuna nariga na siye kaya dasu' k'uma yanzu babu kasuwa kamar dah idan kina gani kamar karya nakeyi ki tambyi Abba ma" "himm zhrdee kenan' nidai nariga na f'adi suna babu fashi' kuje kasamo koda babu yawane kabata" "wlh Hjy banida kudi' tayi hkr kawai wani karon tayi amma banda wann karo' zhrdee ya karisa mgnr ne da fita daga d'akin" "lalla zhrdee Allah ya shirya' itama mikewa tai tafita a d'akin" "da rana da inna tazo take tambyar Zainab mgnr suna" "yace bazayi suna ba sbd beda kudi" "beda kudi?" "eh h'aka yace" "Hjy tasani?" "eh tasani" "koda tai masa mgn bema saurareta ba". "fita har kansa kawai dan rainin hankali suna k'uma babu fashi" "ni zantafi tunda abin yazama h'aka' yanzu medame kike bukata?" "Zainab ta lissafa wa inna' mikewa inna tai' kai tsaye daya daga cikin shagon *Alhj Musa* taje ta zabowa Zainab shadda laces material h'ade da atamfa' saida ta karisa cikin kasuwa tai siyayya snn koma d'akin Zainab" "gani kayan Zainab tai murna sosae harda kukan ta' inna ta kwashi kayan da zata tafi g'ida tabiya takaiwa tela" "Abba yace Hjy ta tambyi Zainab wani suna takeso?" "Zainab tace sunan innarta takeso' daga nan Hjy ta kwashe duk yadda sukai da zhrdee ta f'adi masa' bece komai ba jijjinawa kawai yai" "ana gobe suna duk wani abuda ake bukata Abba yabawa Hjy kudi ta siyowa Zainab' shima zhrdee ya siyewa Aisha dinkaukun shadda galila kala biyu yace tasa ran suna" "ranar suna Zainab me jego ansha kyau dangin Uwa dana uba duk suzo g'ida yacika fakil inna harda akwati taiwa takwaranta' gani yadda g'ida yacika yasa Aisha mmki" "ranar suna da dare Aisha tanatayiwa zhrdee kuka wai cikinta na ciwo lfy' hankali zhrdee ya tashi ya rasa inda zaisa kansa' kusan kasa bcc yai tana kwance a cinyarsa shikuma yana zaune jigine da bango yana yimata sannu" "da safe yace suje hospital zhrdee yaiwa doct bayani yadda suka kwana' doct yace suje suyi scanning' fita sukayi zuwa gun scanning' koda sukayi ya nuna lfy klau k'uma yan'biyu ne a cikin duk maza" "murna agun zhrdee kamar yagoya Aisha yakeji suna barin hospital *ATM* ya biya ya ciro kudi suka tafi supermarket siyayyar kayan baby boys yai sosae kamar mahaukaci harda kayan wasan yara yasiye babu abinda yarage be siye ba komai biyu yake dauka' kaya yacika mota tam gaba ne kawai ba'a saba kaya ba snn suka dawo g'ida" "zhrdee ke kwashe kayan da kansa yai zufa yai sharkam' koda Aisha tasa hannu zata dauki kayan da sauri yace tabari kawai" "Zainab na kitchen tana kallonsa duk da taji ciwo abu amma ta dan ne tai kamar bata gansu ba" "tun daga lkcn wani sabon shagwaba Aisha keyi' koda zhrdee yace Zainab taci gaba da yiwa Aisha abinci babu yabo babu fallasa' babu eh balle a'a" "daga batada lkcn su yasa kullum idan yana dawowa daga kasuwa yake siyo mata abinci" "bayan kwanaki cikin dare Aisha na bcc taji kamar an mutsileta a gigice ta tashi da ihu' zhrdee dake kwance shima a gigice ya falka' gani yadda Aisha takeyi be tsaya fadiwa kowa ba daukarta yai zuwa hospital" "tunda zhrdee ya kaita take labour ba'ita kega haihuwa ba sai safe tasamu baby girl" "nurse d'in da suka amsheta daya daga cikinsu tafito da murnar ta' zhrdee yana ganita ya mike yazo inda take h'ade da tambyar lfy?" "tace congrats ta sauka'ansamu baby girl" "ake murnar zhrdee ya koma ciki" *to fa Aisha kwalelenki da twins* 😋😋 📖🖊 ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* *MARYAM HAUSA NOVEL GRP* *MMN AHAMED HAUSA NOVEL GRP* *MMN USWAN HAUSA NOVEL GRP* *AMINCI 1-2 HAUSA NOVEL GRP* *LONG LIFE HAUSA NOVEL GRP* *RAIHANA HAUSA NOVEL GRP* _*NAGODE SOSAI DA BIBIYAR NVL D'IN NAN DA KUKEYI ALLAH YABAR KAUNA DA ZUMUCI AMIN*_ ________________________________________ _*godiya tare da jijinar bangirma gareka abdulrhaman Hausa Nvl GRP Allah yabar kauna da zumuci yakawo Anuty ta gari*_ 🤣 4⃣8⃣ "zhrdee yace zan'iya ganita?" "bismillh mana" "OK' tana gaba yana baya yana biye da'ita suka shiga d'akin" "lkcn Aisha na kwance akan bedrest baby k'uma k'uma tana kwance a gefen Aisha' gani zhrdee ya shigo Aisha ta fashe da kuka' da sauri ya karisa guta ya rungumeta yana f'adi lfy Aisha ta' kodai wani abune ya sameki" "kai kawai ta kada h'ade da nuna masa baby dake kwance gefeta" "mutuwa tayi' ko yaya" "a'a' baby girl ne aka samu" "to menene Dan ansamu baby girl Aisha' dah da bamu samu bafa' Dan Allah ya'isa haka banason gani hawayen ga dake zubowa a fuskanki' karfa ki mance haihuwa kikai fa' kina kuka wani shi yazo ya sameki haka kawai" "hannu yasa yana share mata hawaye' saida ya share tsaf snn yaje ya dauki baby h'ade da zuba mata ido yana kallonta' Aisha ta yunkura zata mike da sauri zhrdee ya'ije baby a dayan gadon dake side snn yasa hannu ya dago Aisha ta zauna" "bayan ta zauna dayake d'akin akwai light baby ya dauko snn yadawo gun Aisha rungumeta yai sukai ta daukar Pict shida Aisha da babynsu a rungume a jikinsu" "shigowar nurse ne ta katsisu' gani abinda sukeyi ita kanta saida suka bata sha'awa' snn tace to idan kungama zaku iya tafiya g'ida tunda lfyrta klau" "OK' mugode sosae" "babu damuwa nima ngd" "hijab ya dauko ya samata da kansa snn ya dauki jakar da sukazo dashi ya dauki baby' gabar mota ya b'ude mata ta zauna snn ya dora mata baby ya b'ude baya ya ije jaka ya shiga mota' a hankali yake driving har sukakai g'ida" "zhrdee na dauke da baby suka shiga daga ciki' bayan su shiga dakine ya kwantar da baby Aisha itama ta kwanta snn yace yanzu me kike bukata" "ruwan zafi" "me zakiyi dashi?" "wanka mana" "OK' fita yai zuwa kitchen yaje ya kunna gas yasa ruwan zafin' yana kan dorawa kenan saiga Zainab ta shigo dorawa *Islaha* ruwan wanka' gani zhrdee a kitchen tace lfy" "ruwa nazo dorawa" "me zakai dashi k'uma?" "Aisha ce takeso" "Aisha' shine bazata iya fitowa ta dora ba?" "a'a kinsan ai ta haihu ne shiyasa nace ta huta na dora mata ruwan" "haihuwa fa kace zhrdee?" haihuwa wasane da zata haihu babu wanda yaji ".. "Eh' kyace h'aka mana' kin dauka ita irinki ne da uban kowa sai yasan zaki haihu' duk kibi ki wahalar da jama'a kisa mutum kashe kudin da beyi niya ba".. "au' abinma harda gorine?" "nayi d'in raguwar banza kawai" "nine fa zhrdee?" "Dan kece sai fa?" "himm zhrdee kenan' dadin abin bani na dorawa kaina ba Allah ne ya dorami dan h'aka sai kayi dashi amma ba daniba' wlh rashin ilimi na damuka zhrdee" "uban waye mara ilimi?" "kae" "hannu ya daga zai kai mata mari' wlh kana marina saina zuwa bar da ruwan zafi naga ta tsiya" "muguwa azaluma yar' b'akin ciki'ai ni tun ba yanzu ba nasan kina b'akin ciki dani" "Ohooo dai' da nayi niyar dora mata ruwan ne amma tunda abin naka yazama rashin mutunci wlh cokali bazan kaudaba" "saime?" dama waya gaiyaceki a gun? wlh Zainab ko d'akin kika shiga ban godeba" "fita Zainab tai ta nufi d'akin Hjy' zhrdee yaki kaucewa daga gun" "Zainab na shiga lkcn Hjy na zaune akan sallaya tana lazumi dukawa tai gaban Hjy tana jiran da shafa' itama Hjy gani Zainab d'in ne yasa ta shafa h'ade da cewa Zainab har kin shigo?" "eh Hjy ina kwana?" "lfy klau' ya kwana yara"... "Hjy yanzu sbd Allah abinda zhrdee yai ya kyauta kenan?" Zainab tana mgnr kwalla suka zubo mata". "lfy Zainab? wani abune k'uma yai maki?" "Ashe Aisha ta haihu amma babu wanda yasani a g'idan". " haihuwa?" wani irin haihuwa Zainab?" "wlh kuwa Hjy naje sawa *Islaha* ruwan wanka shine na ganshi yana sawa Aisha ruwan zafi" "mikewa Hjy tai h'ade da cewa zomuje' Hjy na gaba Zainab na baya suka nufi d'akin Aisha' suna shiga sukaga Aisha zaune rike da baby a hannunta' gani Hjy yasata cewa sannu da shigowa" "Ashe da gske ne kin haihu?" "eh' cikin dare ne da naji shine muka tafi hospital" "amma yanzu sbd Allah Aisha kin kyauta kenan?" idan bazaki fadiwa Zainab sbd ita kishiyarne to nifa?' ko nima din kin daukeni a matsayin kishiyane?" idan shi zhrdee beda hankali kefa?" wlh Aisha idan abinda kike mana ko kike igiza zhrdee yake mana na rashin biyayya a d'akin nan mukace zamu rama kinsan bazakiji dadin zama a g'idan bako?" "idan kina gadaran sbd yana sonki ne karfa ki mance ni uwarsace idan naga dama a yau din nan zan'iya sawa ya sakeki' saki k'uma ta har abada sbd na isa dashi' daga shi har abinda ya mallaka duk suna karkashin iko nane".. " ashe zhrdee yana bayan Hjy karaf a'a Hjy ba laifinta bane"... "wuf tai da bayan hannu ta watsa masa mari' tunda daga lkcn shuri yai besake mgn ba" "Hjy taci gaba da cewa dan h'aka ki kiyaye' idan kinason zama da zhrdee dole ki bi abinda keso' Aisha kada kiga kamar bansan abinda kuke kullawa keda zhrdee bane akan Zainab duk abinda kukeyi ina sane dan h'aka ki kiyaye" "snn ta jiyo kan zhrdee kai k'uma zhrdee duk abinda kikeyi kaci gaba ina sane da duk shiga da fitanka a g'idan nan' kada ka mance ku biyar Allah yabani a duniya tunda kuka taso babu wanda ya taba jin kanku sbd h'aka har kwatance akeyi daku' most especially kai yadda kataso cikin ladabi da biyayya da k'uma kyautatawa iyaye amma tunda Aisha ta dawo rayuwarka komai ya lalace' zhrdee bazance ka saki Aisha ba amma inaso kasan wani abu guda daya zhrdee Aisha da Zainab matankane ko dasu ko babu su zaka iya rayuwa kamar kowa' amma bandani' bazan maka baki sbd Aisha ba amma ka kiyayi bacin rana" "juyawa tai gun Zainab dake tsaye kusa da'ita tace ke'!! muje' suna fita suka bar d'akin" "suna fita Aisha tasa kuka' da sauri zhrdee yazo inda take ya rungumeta yana bata hkr' bayan tayi shiru ne zhrdee ya kira g'idan su Aisha ya sanar dasu haihuwa' murna sukai h'ade da yimasa barka' daga g'idan su Aisha aka aika g'ida ubaida' ubaida tai murna sosae' washe gari taje g'ida mai jego sukasha hiransu sosai bata koma g'ida ba sai da yamma" "kwana biyu da haihuwar Aisha kanwar bbnta tazo daga kauye' ita ke tayata aiki sbd Zainab taki kauda koda cokaline' ubaida k'uma ba kullum take zuwa ba' goga zhrdee kafin yaje masallaci yakesa mata ruwan wanka'kafin yadawo ruwan yai zafi" "ana gobe suna zhrdee ya siyewa Aisha kaya na gani na fada yakai kala goma duk dinkanku h'ade da sarkan zinare' kayan baby ma h'aka' raguna biyu ya siyewa Aisha' itako Zainab ko kyale bata gani ba" "ranar suna baby taci suna *Laila* sunar Hjy kenan Mmn zhrdee' dangin Aisha na birni dana kauye duk suzo" "minti da minti Aisha saita canza kaya ita da baby da uban baby' Pict kuwa ba'a mgn" "tunda Zainab taga h'aka tana Zaune a d'akin ta sai yan'uwan zhrdee da suka shigo mata suna ta hiransu har yamma kowa ya watse" *a gurguje dan Allah kuyimin uziri* "ana gama suna zhrdee ya me kwana da Aisha ta tafi haka ya gode" "gani yadda dama yake kasa zaune ya kasa tsaye yasa bata musaba ta h'ada kayanta' zhrdee ya h'ada mata goma ta barziki ta tafi" "bayan tafiyarta zhrdee ya koma d'akin Aisha da kwana duk dare shike raino Aisha tana bccita' gani baby tai bcc yasa zhrdee shinfidata shima ya kwanta' Ashe bcc yana daukarsa combortion ya kama yarinya har tasankare ta mace basu saniba" "sai guraren asuba Aisha ta falka' tana falkawa kan yarinya tai koda Aisha ta dauketa bata motsi' da sauri ta tada zhrdee h'ade da mika masa ita' koda zhrdee ya dauketa kallo daya yai mata yagano batada rai" "cikin gigita yace Aisha garin yaya batafa da rai" "me kake zhrdee?" "batare daya saurareta ba a guje ya nufin gun Hjy" "ihu Aisha tasa h'ade da f'adi a kasa tana ihu"""""" 📖✍ l ☘☘ ☘ *AURA IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 4⃣9⃣ "a guje zhrdee ya shiga d'akin Hjy' a birkice Hjy ta tashi daga bcc tana f'adin lfy zhrdee?" "mika mata baby yai kawai batare da yace komai ba" "Hjy na amsar baby taga tariga ta cika' salati tai h'ade da shafe mata fuska" "ta mutu ko Hjy?" "Allah yai wa *laila cikawa zhrdee" "zhrdee yana salati jikinsa na rawa' mikewa Hjy tai tace muje' d'akin Aisha suka koma' suna shiga gani Aisha tai tana kwance a kasa sai faman birgima takeyi tana kuka" "shigewarta tai batare da tace mata kala ba' gefen gado taje ta shinfida gawar a kasa snn ta fita" "tana fida da sauri zhrdee yai kan Aisha ya dagota ya rungumeta h'ade da bata hakuri" "rarra fawa Aisha tai taje kan gawar ta b'ude tasake fasawa da kuka' zhrdee na rungume da'ita a gaban gawar suma kwalla yakeyi" "Hjy na fita d'akin Alhj ta shiga taje ta sanar dashi abinda ke faruwa' mikewa Alhj yai yaje ya tada su yya Shamsudee duk suka fita parlour su Zainab' " Zainab dake bcc tanajin hayaniyar mutani falka lekowa tai gani su yya a zaune yasata komawa taje tasa hijab snn tasako fitowa' gani Hjy ta shiga d'akin Aisha yasata itama shiga d'akin" "tana shiga gani Aisha da zhrdee suna kuka yasa ta tsorata da sauri tai inda suke zaune' gani gawa yasata salati ta sanarwa ubangiji" "hannu Hjy tasa ta dauki baby har zata shiga toilet da sauri Zainab tace a'a Hjy" "meyasa cikace a'a" "gara ayi mata a d'aki kawai kamar zaifi kyau" "to shikenan" "shiga toilet d'in Zainab tai ta dibo ruwa mai tsarki da tsafta h'ade da baho na wanka tafito dashi zuwa bedroom ta'ije h'ade da cewa ina zuwa" "komawa d'akin ta tai ta dauko turare da ruwan zamzam da take bawa *Islaha* har zata fita *Islaha* ta falka tana kuka" "daukarta tai suka fito dare' mikawa yya Shamsudee tai ita snn tashige d'akin Aisha" "har zasu fara wanka Hjy tace zhrdee ya fita parlour' Zainab da kanta taiwa baby wanka h'ade da shiryata Hjy na zaune bayan ta gama ta shinfidata a kan" "yya Shamsudee ya kira Hjy ya mika mata *Islaha* sbd zasu tafi masallaci dan asuba yai lkcn" "itama Hjy tafiya tai taje sallah' itako Zainab na zaune da gawa' gani *Islaha* zata dameta da kuka yasa ta goyata" "bayan su yya sun dawowa ne yya yai sallama yace Zainab ta miko gawar' mikewa tai ta dauko *laila* tacewa Aisha dake zaune gefe gata kuyi sallama" "Aisha na amsan *laila* kankameta tai tasa ihu' gani bazata iya jurewa ba' yasa Zainab fisgeta taje ta mikawa yya dake tsaye b'akin kofa" "ihu Aisha tasa tana kuka' bayan su tafine Zainab ta h'au Aisha ta f'ada' h'aba Aisha meye kikeyi h'aka kamar ba musulma ba' sai kace a kanki aka fara gani mutuwa' wanda ke kanki ma baki wuce shiga amma kike kuka h'aka?' banza da Zainab Aisha tai taci gaba da kukanta" "yanzu Aisha bazaki shiru d'in ba' sbd Allah' kamar ba mai ilimi ba' wlh abinda kikeyi ko jahili bazaiyi h'aka ba".. " shigowar Hjy ne ya katse Zainab' kin dawo " "har sun tafi da'ita ne?" "eh" "to Allah ya jikanta' ni zanko ciki" "Hjy na fita Zainab itama ta fita zuwa d'akin ta taje sallah" "da safe duk yan'uwar Aisha sukazo harda ubaida' kanni bbnta saida akayi addu'ar uku snn suka koma' a ranar da akai uku zhrdee ya dawo d'akin Aisha" "tana kwance tana kwalla zhrdee ya shiga' gani tana kuka da sauri ya karisa kanta h'ade da dagota ya rungumeta yana bata hkr" "gani yadda yake bata baki yasa Aisha sake fashewa da kuka' tana f'adi yanzu shikenan Hjy ta tafi kenan?' yanzu na rasata kenan zhrdee?' zhrdee nashiga uku zhrdee" "h'aba Aisha baki shiga uku ba Aisha ta' Allah daya bamu shine zai kara mana wani kinji Aisha' Dan Allah ki daina WNN kukan h'aka" "rungumarsa tai tana hawaye" "da asuba bayan zhrdee ya dawo daga masallaci' d'akin Hjy yaje gaidata' bayan su gaisa ya jima suna hira har ya mike sai fita Hjy tace zhrdee" "na'am Hjy" "nace ba' mai zai hana a cikin kayan da kuka siye na takwarata tunda ga yadda Allah yai ikon sa ka dauki keke daya mana kabawa *Islaha* da d'an ragowar wasu kaya' tunda naga kun siye kayan da yawa k'uma yanzu batanan" "a'a Hjy' kibari kawai idan nasamu kudi zan siye mata nata itama" "kullum aikin kenan idan akan Zainab ne ko yaranta" "a'a ba h'aka bane Hjy' idan har na Aisha taga na dauki kayanta na bawa Zainab Ai bazataji dadi ba ko?" "eh' tunda ga Azumi kanwar uwarka ba' zhrdee kenan a addu'a ta dakai Allah ya shirya mikai' yasa kagane" "fita kawai zhrdee yai batare da yace komai ba" "tunda *Akbar* yafara samu kafa da kansa yake zuwa gun mmnrsa' haka ma yau dayake zhrdee tunda Aisha ta haihu a d'akin ta yake kwana sai da safe idan yaga dama yaleka d'akin Zainab' h'aka ma yau da zhrdee ya leka Zainab har zai fita *Akbar* yaje ya rike bbnsa daukarsa zhrdee yai suka nufi dakin Aisha" "suna shiga zhrdee yace Aisha" na'am" "hadomi tea nasha' yunwa nakeji" "to kawai tace tafita zuwa kitchen' tana h'ada masa ta kawo' amsa zhrdee yai yafara sha' Abba na zaune a gaban bbnsa" "har ya kusan shanyewa Abba ya mika hannu" "Abbana zaka sha ne?" "to bari na baka a baki ko' Abbana" "har ya dauki spoon zai fara bawa *Akbar* kenan Aisha tace h'aba zhrdee meye kakeyi h'aka' komai ne kaci saika bashi' ko kuma sare sarin koyawa yaro kwadayi' ko'ina yaje yaga anacin abu yace sai yaci" "Aisha bari na bashi koda kadan ne" "bazaka bashi ba" "kinga kuka zaiyi ko" "ba kuka ba yayi kukan jini ma" "har zhrdee yakaiwa *Akbar* tea d'in da sauri Aisha tazo ta fisge cup d'in tea d'in" " *Akbar* na gani h'aka yasa kuka" "zhrdee yace kingani ko" "Aisha tace naga me?' babu wani tea d'in ta zai sha' idan yunwa yakeji yaje d'akin uwarsa yasha" "duk Aisha tana mgnr ne h'ade da zunguro *Akbar* a goshi" "shiko *Akbar* kuka yasa har yana sukewa" "gani h'aka yasa Aisha daukarsa ta fitar dashi waje' daidai b'akin kofarta ta'ije shi' tana ijeshi Zainab na fitowa daga d'akin ta' da sauri takariso' kafin ta iso Aisha ta tura kofa ta rufe" "daukar Abba kawai Zainab tai suka koma d'akin ta h'ade da cizon yatsa" "bayan kwana biyu Zainab na zaune a dakinta da'ita da yara suna wasa sai ga kiran inna yashigo' da sauri Zainab ta daga cikin girmamawa ta gaida ta'bayan su gaisa inna tace yan'ta albishirin" "goro inna" "kinsan me?" "a'a inna sai kin f'adi" "amma fa za'aban tukuici" "eh naji zanbayar inna f'adi dai naji" "to abbanki ya biya maki *hajji* " ihu Zainab tasa h'ade da tsalle tana murna' godiya sosae taiwa inna snn sukai sallama' sbd murna har tarasa abinda zatayi" "da yamma lkcn zhrdee ya dawo daga kasuwa da yake yau a dakinta yake' tayi tunanin yadda taji muryansa shigowa Zainab' zama tai a b'akin gado tana jiransa" "shiko yana d'akin Aisha suna hira' Zainab tai zama har tagaji zhrdee be shigoba' bcc ya dauketa' zhrdee be shigo d'akin Zainab ba sai around 1AM snn yashigo' tanajin shigowar sa amma taba tashi ba' shima kwanciyarsa kawai yai sbd yariga yai wanka a d'akin Aisha" "bari tai da safe lkcn ya dawo daga masallaci bayan ta gaida shi' shine take sanar dashi mgnr hajji" "shiru yai sai da takare snn yace kiyi hkr babu inda zaki"... " da sauri Zainab ta mike daga duken da take a gabansa h'ade da cewa me kace?" "nace babu inda zaki" "sbd me?" "sbd na isa dake" "to shikenan' abinda kawai Zainab tace masa kenan" "fita tai daga d'akin' batare da tace masa kala ba' kai tsaye d'akin Hjy taje' a ladabce ta gaida ta' tanayi tana kwalla" "lfy zainab me kuka ya faru?" "Zainab na kuka ta fadiwa Hjy yadda sukai da zhrdee" "haka yace?" "Eh" "tsaya ina zuwa' wayarta ta dauko ta kira zhrdee' zhrdee yana gani number Hjy da sauri ya daga wayar h'ade da sallama" "kazo ina niman ka" "to gani nan' gari ya meda snn ya nufi d'akin" "yana shiga yaga Zainab duke a gaban Hjy' daure mata fuska yai' snn ya duka gani Hjy" "yaya kukai da Zainab?" "mgnr hajji ne kuma nace tabari" "sbd me?" "sbd Akwai abinda nake shiryawa idan nagama zanbiya masu ita da Aisha sutafi tare" "a'a bazai yuwuba' kabari kawai ta tafi idan tadawo in har da gske kakeyi kanada niyar biya mata saita koma a na biyu' fanninka daban NA bbnta ma daban" "a'a Hjy da dai tabari NA biya masu" "bazai fa yuwuba' dama wani ne ba kai ba' h'aka kawai kai baka biya mataba k'uma baka bari taje Wanda bbnta ya biya mata ba" "toni gskya" "gskya me?" "gani nayi ga yarinya karama kada WANI abu yazo ya sameta" "babu abinda zai dameta idan ma mutuwa tai Allah ya jikanta amma tafiya babu fashi' k'uma kafin kaje kasuwa kabiya g'idan su kaiwa Alhj Musa godiya" "to kawai yace ya mike' yana fita yace wlh babu inda zani" "Zainab dake biye dashi bata tanka masa ba" "dayake a kurarren lkc ne shiyasa Zainab tafara zuwa training d'an ma Allah yasa tanada ilimin addini sosae yasa be bata wuya ba" "kwanaki yaragewa Zainab su tashi' tana kitchen tana aiki zhrdee yana parlour yana kallon boll sbd TV Aisha yasamu matsala shiyasa ya fito parlour' yana cikin kallo *Islaha* ta rarrafo ta fito daga d'akin mmn hango bbnta yasa ta nufi gunsa' tana isa da sauri tasa hannu zata kamosa" "Aisha dake gefe ta riketa tana f'adin ke dakata" "shima zhrdee hannu ya mika zai dauke Aisha ta hana" " *Islaha* naso taje gun bbnta gani an hanata yasata kuka" "zhrdee yace mikomi ita" "a'a bazaka dauke taba baka gani fararen kayane kasa idan ta bata maka fa" "eh k'uma h'aka ne fa' ijeta mmrta tazo ta dauketa kawai" "Zainab najin h'aka da sauri tazo ta dauketa h'ade da cewa banza yar'iska' dabba' wacce batasan darajan yaro ba' ta Allah ba takiba k'uma insha Allahu baki isa ki rabasu da bbnsu wlh" "shiru Aisha tai bata tanka ba' zhrdee ne yace bacemi da gani a nan' tun kafin natashi" "komawa kitchen tai batare da ta sake mgn ba" "ana gobe zasu tashi ta h'ada kayan yaranta gaba daya ta kaisu gun inna" "gani h'aka itama Hjy bata tambyi dalili h'akan ba" "washe gari har d'aki Zainab taje tana kuka tana sallar Hjy' itama Hjy kuka tai sosae h'ade da fatan aiki cikin sa'a' snn ta fito zuwa gun Aisha' itama har daki tabita rungume Aisha tai tana kuka sukai sallama" "itako Aisha dake tsaye yamutsa baki tai domin ko a jikinta" "zhrdee dake mota yana jiranta haushi ya kamashi sbd dama dakar Hjy ta lalabeshi akan saiya raka Zainab har airport' tana fitowa suka tafi' ko kafin su isa tuni inna da abbanta suna gun' tana zuwa kayi kawai tashige' gani anzo kanta zata shige' kome zhrdee ya gani oho!!! da sauri yaje ya rungumeta a jikinsa na dan mintoci snn ya saketa tashige" "saida sukaga tashinsu snn kowa yakama hanyarsa *Dan Allah kuyi hakuri da wannan abubuwanne sai a slow* 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES. F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 5⃣0⃣ "g'ida zhrdee yadawo lkcn Aisha na kwance' rigigine tai kamar mai bcc amma ba bcc takeyi ba" "da sallama zhrdee ya shiga d'akin gani yai sallama bata amsaba ya dauka ko bcc ne takeyi' leka fuskanta yai yaga idonta biyu' yasashi hayewa jikinta yana f'adi my wife tunanin me kikeyi h'aka?" "nannauyar ajiyar zcy tai h'ade da cewa babu komai" "h'aba Aisha babu komai shine kika f'ada duniyar tunani h'aka' idan kinsan Akwai abinda ke damiki dan Allah ki sanarmi Aisha' " da gske nace babu komai" "himm Aisha kenan' nifa mijinki ne be kamata kina boyemi wasu matsalolinki ba' a yadda na dauka nidake duk daya ne' amma boyemi wasu matsalolinki da kikeyi shi zaisa naga kamar kina ware tsakanina dake ne" "lahh!!!!! zhrdee kenan wlh ba h'aka bane" "to menene?" "babu komai". " ban yarda ba" "kinga" "dago fuska tai tana kallonsa" "Aisha" "na'am" "kalleni nan' idanu ya zuba mata yana kallonta" "a hankali ta dago fuska tana kallonsa cikin ido" "hannu yasa ya kamo mata habarta snn yace kina sona?" "shiru Aisha tai h'ade da zuba masa ido" "dakefa nakeyi Aisha' kibani amsata" "kai ta daga masa alamar eh" "yawwa ko kefa' Aisha idan har da gske kina sona to inaso ki fadimi abinda ke damuki" "shiru Aisha tai sai kwalla" "subhana lillahi' Aisha lfy kuwa" "kuka kawai ta fasa masa" "hannu yasa yana share mata hawaye h'ade da rungumarta yana sake tambyrta" "cikin kuka Aisha tace dama mgnr haihuwa ne" "haihuwa kuma Aisha" "eh" "h'aba Aisha' idan banda abinki kwata kwata watanki nawane da haihuwa abinda ko warkewa bakiyi ba" "wani irin warkewa k'uma' abinda watana na uku kenan fa" "to yanzu me kikeso ayi" "hospital nakeso mukoma" "hospital k'uma?" "eh" "to shikenan' gobe ki shirya muje" "murna Aisha' tai h'ade da rungumarsa" "a ranar zhrdee be fita kasuwa ba sai bayan azahar snn ya fita" "washe gari koda sukaje hospital doct cewa yai babu komai zata iya ci gaba da haihuwarta batare da wani matsala ba" "nan suka dawo g'ida" "Zainab suna sauka *Saudi arebia* innarta tafara kira suka gaisa snn ta kira abbanta shima suka gaisa' bayan su gama da Abba takira zhrdee lkcn yana zaune da Aisha suna hira saiga kiran Zainab yashigo" "gani bakon number yasa zhrdee be dauka ba' Zainab tai kira har five miss call amma besa ya daga wayar ba' gani haka yasa Zainab kiran Hjy suka gaisa snn sukai sallama" "zhrdee da asuba lkcn ya shiga gaida Hjy bayan su gaisa ne Hjy ke cewa Zainab ta kirani mu gaisa"... " da sauri zhrdee yace nima ta kirani ai" "Allah sarki' to Allah ya taimaka" "amin Hjy" "har zhrdee ya mike Hjy tace zhrdee" "na'am Hjy" "dan Allah koda zuwa gobe ne idan kasamu lkc kaje ka dubo yaran nan kaji" "yara k'uma?" "eh mana" "to shikenan Hjy Allah ya kaimu" "amin' amma dan Allah idan zaka kadan rike masu koda sweet ne kaji" "naji Hjy" "bayan ya fitane yana shiga d'akin Aisha yace Aisha" "na'am" "ashe bakuwar number da aketa kirana dashi Zainab ce" "kallon banza tai masa h'ade da cewa toni ina ruwana" "lkcn zhrdee ya riga ya juya baya' Allah sarki Zainab kawai yace" "Aisha tai banza dashi" "duk da Allah sarkin dayace besa zhrdee tunanin kiran Zainab ba" "itama da take can tunda bata sake kiran zhrdee ba sbd tana gani koda ta kirasa ba lalla bane ya daga' shiyasa Hjy kawai take kira su gaisa" "tunda Zainab ta sauka a kasa me sarki duk inda taje ibada babu abinda takeyi sai addu'a akan Allah ya dorata akan maigidanta ya sanya masa soyayyar ta a zcyrsa" *bayan kwana biyu da tafiyar Zainab Hjy tace zhrdee ya kaita g'idan su Zainab' a take gaban zhrdee ya f'adi sbd tunda Zainab tabar kasan be taba lekasu ba balle yasan halin da suke ciki" "bayan Hjy ta shirya ta fito parlour su Aisha h'ade da kwadawa zhrdee kira' Aisha najin kiran Hjy ne yasata fitowa har kasa ta duka suka gaisa' Hjy tace Aisha' manyan gari kodan lekowa ciki bakyayi' idan kinajin kunyar hira dani baga kanni mijinki nan ba' amma sai kiyita zama a daki kekadai". " karaf zhrdee yace wlh Hjy nima kullum abinda nake f'adi mata kenan' amma bataji" "kila zaman gu daya baya damukine yasa h'aka" "murmushi kawai Aisha tai h'ade da shigewa d'akin ta' suma su Hjy ficewarsu sukai" "suna fita Hjy tace sai su biya kasuwa tai masu siyayya snn su karisa g'idan" "wani supermarket ya kaisu Hjy da kanta take zaban abinda takeso' wanda tasan yara zasuyi sha'awa" "kaya sosai ta diba snn zhrdee ya biya suka shiga mota zuwa g'idan su Zainab" "suna isa har cikin g'idan zhrdee ya shiga yai parking snn suka fita' Hjy tace zhrdee ya dauko kayan' tana gaba yana biye da'ita a baya suka shiga har parlour h'ade da sallama" "jin sallama ne yasa Hjy *maryam* mmn Zainab fitowa gani zhrdee da Hjy ne yasata komawa da sauri taje ta fadiwa inna *Hulaira* inna da fara'arta ta fito ta tarbesu" " *Hjy maryam* hijab tasa snn ta fito suka gaisa snn ta koma ciki d'akin ta' inna ce taje ta kawo masu ruwa da abinda h'ade da su juice' snn takoma ta dauko yara suka fito tare' *Akbar* yana gani Hjy a guje yaje ya rungumeta itako *lslaha* gun zhrdee tanufa" "Inna na gani h'aka ta mikawa zhrdee *Islaha* cikin jin kunya zhrdee ya amshi *Islaha* yana murmushi" "itama Hjy daukar *Akbar* tai tana masa wasa" "sun jima su hira snn Hjy tace zasu tafi' dauke *Akbar* tai itako *Islaha* gani zhrdee yanada niyar dauketa kuka tasa h'ade da makalewa a jikin bbnta" "duk dariya sukasa shiko zhrdee dake dauko da'ita kunya ne ya kamasa' sbd kunya kasa mgn yai sai faman murmushi kawai yakeyi' gani ta kara makalewa a jikinshi h'ade da rike masa riga hannu bibbiyu tana kuka" "banbareta yai daga jikinsa ya mikawa Hjy snn yafita' duk dariya sukasa' itama Hjy mikewa tai h'ade da mikawa inna ita snn sukai sallama' *Akbar* dake tsaye dagawa Hjy hannu yakeyi alama sallama" "suna tafe Hjy tacewa zhrdee Allah sarki tsakani dah da mahaifi kenan".. " menene k'uma Hjy" "wlh wani irin naji da yaringa ke kuka' kodai mukoma mu daukota ne?" "shiru zhrdee yai be tanka ba" "zhrdee ko baka jina ne?" "dauko wani zance yai" "daga nan Hjy ta gano kunya ne yakeji irin na Hausa Fulani" *dama duk wanda yasan Hausa Fulani an sansu da kara da kunya h'ade da girmama na gaba dashi* itama data gano h'aka bata sake mgnr ba har suka isa g'ida'sai wani hiran suka dauko" "ranar da Zainab zasuyi hawan arfa' tana tsaye a gaban ka'aba daga hannunta tai sama hannu bibbiyu tace *ya Allah ga baiwarka nan tazo da kokon baranta' Allah kafi kowa sani halin da nake ciki a g'idan aurena' Allah kai ka halitceni kafi kowa sani damuwata' ya ubangiji Allah dan tsarkin mulkinka' dan kadaitarka' dan tsarkakanken littafinka wato alkur'ani mai tsarki' dan fayayyan halittarka' shugabanmu annabi muhammedu (S.A.W.) Allah ina rokon ka kada dorani bisa kan mijina' kasanya masa soyayyata nida yarana a zcyrsa' Allah kada kabashi ikon walakantani' bashi bama duk wani abin halitta' ya Allah ka dorani bisa kan kishiyata, ni k'uma ya ubangiji Allah kabani hakuri da juriya a tsakani zamantakewar cikin g'idan aure na' kabani hakuri da juriya akan duk wani abu da zangani a gun maigidana, Allah kafi kowa sani ina cikin jarabawa a zaman aure na' Allah kabani hakuri da juriya akan h'aka' Allah ka ganar da mijina,3 ka k'uma shiryarmin da yarana shirin addini musulumci* *Allah nayi tawassali da sunayenka tsarkaka' Allahu' arrahaman' almuminu' almihaiminu' alkundusu'' Innamaza amru iza aradda lahu an yakuluna lahun kumfa yakun* snn Zainab ta shafawa' ko a madina masallaci annabi Muhammad (A.S.W.) nan ma taita addu'a akan niman zaman lfy tsakani ta da zhrdee da k'uma Aisha" "bayan kwana biyu da tafiyar su Aisha hospital ta samu ciki wanda ita kanta batasan ta samuba sbd bataji kowani halimu ba' sai dai yawan tsardan da miyau da takeyi' dayake zhrdee bayaso sbd kyama h'akan yakeji yasashi yimata f'ada akan bayaso' tayi kokarin dai nawa amma abu ya gagara gani h'aka yasashi cewa suje hospital' gwajin farko doct ya gano ciki ne da'ita na sati biyu zuwa uku' koda aka fadiwa zhrdee murna yai sosai daga shi har Aisha" "tun daga lkcn ya daina matsa mata' aikin komai ma ya hanatayi a g'idan" "tunda Zainab ta tafi zhrdee be kirataba' itama tunda ta kirasa be daga wayar ba yasa bata sake kiransa ba" "sai yau kamar wanda akaiwa asiri yaji yanaso yaji koda muryanta ne' bayan ya fita kasuwa yai rechaging sosai ya kira Zainab' gani number zhrdee yasata mmki' da sauri ta daga sbd kada ya tsinke' da sallama ta daga" "zhrdee yace hjyta ina fatan kina lfy?' k'uma da fatan bakiyi fushi dani ba" "dariya Zainab tai h'ade da cewa fushi me idan da sabo ai nasaba" "kamar yaya Zainab dinta?" "a'a babu komai" "idan ma kiyi fushi ne to dan Allah kiyi hakuri" "a'a wlh ni na'isa nayi fushi da maigidana" "dariya Zainab yai h'ade da cewa Allah ko Zainab din ta" "itama dariya tai snn tace yanzu kana lafiya ya g'ida dasu Aisha da k'uma kasuwa" "duk alhamdllh" "ina fatan kimi addu'a ko?" "wace ni' ni na'isa ace naje kasa me tsarki sukutun banwa mijina addu'a ba?' ai dana dawo kai a kafata" "da gske Zainab" "Allah kuwa ai kafi da h'aka" "kaee naji dadi sosai Zainab dita' Allah ubangiji ya kara maki hakurin nan dana sanki dashi" "dariya kawai Zainab tai" "yanzu dai nasan kun kammala aiki wani lkc ne zaku dawo?" "lahh!!! yanzu da haka ma a layi muke" "da gske Zainab" "wlh kuwa" "kice yau ko gibe zanga amaryata" "dariya Zainab ta sake yi masa" "yanzu me kikeso ayi maki" komai ma Zainab" "nidai bana bukatar komai' abu daya kawai nake bukata a gunka" "kaimi addu'a Allah yakawomu lfy"... "in Allah ya yarda ma zaku dawo lfy Zainab" "Allah yasa h'aka" "amin Zainab dita" "to shikenan yanzu sai kin dawo ko" "to ngd" *I lov u* *lov too* "snn sukai sallama' suna sallama mikewa zhrdee yai h'ade da daukar key' mota ya shiga zuwa g'ida" "yana shiga kai tsaye dakin Zainab yaje yasa key ya b'ude d'akin' tubewa yai daga shi sai gajoran wando gaba daya ya kwabe mata kayan daki ya h'au mata kwalima' lungu da sako saida ya shire snn yq canza mata gado ya koma dashi wani gefe h'ade da mirrow" "Aisha na ciki tana bcc jin motsi yai yawane yasata lekowa taga waye' gani zhrdee ne ke kwalima yasata komawa taci gaba da kwanciyarta" "zhrdee saida ya gyara ko'ina snn yai wanka ya kwanta sbd gajiya" "washe gari da asuba saiga kiran Zainab' a birkice ya falka dubawan da zaiyi yaga number Zainab ce da sauri ya daga h'ade da cewa har ku iso ne?" "Zainab tace eh" "to ganinan zuwa" "to kawai tace" "Aisha naji taja wata uwar tsaki h'ade da juya masa baya" "ko kafin zhrdee ya'isa tuni abbanta da inna suna gun' amma Zainab tace bazata bisuba zhrdee take jira" "abbanta be nuna damuwa ba yace babu komai" "zahradee yana isa can nisa ya hangosu a guje yaje ya rungume Zainab a jikinsa yana murna" "itama murna tai sosai h'ade da jin dadi yadda mijinta ya nuna damuwa a kanta" "zhrdee yana rike da hannunta sukaje suka shiga mota" "shima Abba da inna nasu motar suka shiga" "zhrdee cike da doki da murnar gani matarsa tadawo lfy' baki har kuni yake kallonta' itama nuna nata irin farin ciki takeyi har suka isa g'ida". 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 5⃣1⃣ "zhrdee suna isa g'ida tun daga b'akin kofar shiga parlour yake kwadawa Aisha kira' Aisha najin muryar zhrdee da sauri ta mike zuwa b'akin kofa' ganisa rike da kaya Zainab na bayan sa yasata jan tsaki ta koma ciki tai kwanciyarta' karisaw ciki yai zuwa d'akin Zainab' saida ya ije kayan dake hannunsa snn ya b'ude kofa suka shiga ciki" "suna shiga cikin d'akin Zainab ta zauna h'ade da cewa wash Allah na' snn Zainab yace snn ya'ije kayan dake hannunsa fita yai zuwa kitchen yaje ya dauko mata ruwa da juice' ko kafin ya dawo Hjy ta shigo d'akin' jin muryan Hjy ne yasa Aisha fitowa zuwa d'akin" "gani Hjy talk shigo yasa Zainab mikewa da sauri taje ta rungume Hjy' itama Hjy rungumarta tai snn ta duka har kasa suka gaisa' bayan ta gama gaisawa da Hjy ne Aisha na tsaye tana kallonsu Zainab ta rungumeta itama sukai wa juna murnar sake haduwa snn suka gaisa" "Zainab yana shigowa da ruwa h'ade da juice mika mata cup yai h'ade da goran swan' Hjy na gani h'aka fita tai' itama Aisha ta fita zuwa nata d'akin' kadan kawai Zainab tashi ruwa zhrdee ya sake zuba mata juice yace tasha' tana sha zhrdee yana kallonta yace Zainab kinyi kyau amma kin rame" "murmushi tai h'ade da cewa ba dole ba' dukawa tai har yasa tace ina kwana" "murmushi zhrdee yai alamar jin dadi kansa ya kara girma' snn yace lfy klau' ya gajiyar hanya" "Zainab tace alhamdllh' hannu Zainab yasa ya dagota ya rungumeta a kirjinsa' itama rungumarsa tai' sukai minti goma a h'aka babu Wanda yai ko motsi suna rungume da juna' sallamar kanni Zainab ya katsesu da sauri suka saki juna" "suna shigowa bayan su gaisa da zhrdee ne yafita ya basu gu'yana fita Zainab ta dauki *Akbar* ta rungume *Islaha* na gani haka ta kakame mmnta' dariya Zainab tai h'ade da daukarta itama" "nan suka Zainab sunata hiransu har yamma' koda zhrdee ya fita gani rana yayi kiran Zainab tai yana tambyar ta mezataci ya siyo mata?" "a'a ka barshi kawai innata ta yomi abinci da aikomi dashi" "to shikenan sukai sallama" "da yamma luck kannita zasu koma g'ida sukace inna tace kada abar yara" "Zainab bata musaba suka koma g'ida tare" "zhrdee yana dawowa daga kasuwa shida Abba dasu yya Shamsudee' biyowa parlour su zhrdee sukai dukkansu harda Abba' zhrdee ne ya shiga ya kira Zainab tafito suka gaisa snn suka koma ciki itama da zhrdee" "namar kaji yasiyo gasassu h'ade da yoghurt dauko ledar yai saida ya koma kitchen ya dauko tre yadawo snn ya juye namar a tre yace tazo suci' duk da a koshe take amma sbd kada yaga kamar bata yaba da abinda yai mata ba yasata saukowa ta zauna a kasa suna kallon juna' da kansa yake bata a baki h'ade da yoghurt har saida tace ta koshi snn ya daina bata yaci gaba da cin nasa" "bayan ya ko shine Zainab tace ya kamo mata jakar da tadawo dashi kama mata yai suka kwance, saida taje ta rufe komar da key snn ta dawo ta b'ude kayan' set din kayan maza ta fito masa dasu tace ya zabi wanda yai masa a ciki" "haka zhrdee yai ta zaba saida ya zabi kala shida snn yace ya gode' idan Akwai wanda kakeso ka kara" "a'a Zainab wann ma ya'isa ngd" "to shikenan" "hannu tasa ta b'ude handbag dita ta dauko agogon zinare ta bashi h'ade da wasu takalma" "zhrdee yai murna sosae h'ade da godiya" "snn Zainab ta cire jallabiya guda biyu tace yabawa su yya Shamsudee, na mata ma guda biyu Amatullah da amatulrahaman' saina Hjy itama kala biyu da hijab' shima Abba kala biyu aka bashi h'ade da dadduma" "zhrdee yai murna sosae' Zainab ta sake cire kala biyu na jallabiya tabashi tace yabawa Aisha ita da mmrta" "bayan ta gama ne yasake taimaka mata ta meda sauran bayan snn yace suje suyi wanka' wnn karo kam zaune Zainab take zhrdee keyi mata wanka saida ya gama wanketa tsaf snn yai nasa wankan" "har Zainab ta yunkura zata dauko towel ta daura zhrdee ya hanata' saida ya gama nasa snn ya dauko towel ya daura mata shima ya daura nasa yana rungume da'ita suka dawo bedroom" _~*WAIWAE*~_ *ina masu cewa Zainab batada zuciya?' ba haka abin yake ba' a zamantakewar aure akwai tausayi, yafiya jin kai, da k'uma rauni. duk yadda namiji yakai ga cutar matarsa' mace nada raunin da bazata iya ramawa ba, idan ko tace zata mara tabbas wataran zata rame, dan haka kudaina gani laifin Zainab' tsakani mata da miji sai Allah* "yau ko sallar asuba zhrdee bejeba babu yadda Zainab batai da shiba amma yaki fita masallaci' a daki sukai sallar' bayan su idar ne zhrdee ya dauki ledar kayan da Zainab ta kawo masu saida ya fara shiga d'akin Hjy bayan su gaisa snn ya mika mata kayanta yace Zainab ce ta bata' snn ya baya nasu yya dasu Amatullah h'ade dana Abba" "Hjy tai murna sosae h'ade da sa mata Albarka'" "mikewa zhrdee yai zuwa d'akin Aisha' tana kwance ya shiga da sallama' kamar bazata amsa ba' can k'uma ta amsa' zhrdee yace gimbiyata kenan kin tashi lfy" "wata uwar harara ta watsa masa snn tace lfy klau" "bebi ta kanta ba mika mata kayan da Zainab ta bata yai snn ya fita sbd bayaso wani mgn' Dan a yadda ya ganta yasan akwai mgn a bakinta" "d'akin Zainab ya koma har ta mike zata fita" "da sauri yace ina zuwa?" "abin breakfast zan h'ada maka" "a'a barshi kawai zo mu kwanta" "Zainab bata musaba haka tabi umarnisa" "duk da gajiyar da tadawo dashi amma bata hana zhrdee hakkinsa ba' saida ya gamsu dan kansa snn".. "bayan kwana biyu gani ba'a dawo da yara ba' zhrdee yace Zainab taje ta kwaso masa yaransa' bata musa masa ba' yace ta shirya lkcn da zai fita kasuwa zai sauketa a g'idan su' k'uma ta jirasa har sai yadawo daga kasuwa sai yabiyo ya dauketa su dawo g'ida" "Zainab tace to' h'aka ta shirya suka fita' saida Zainab ta shiga ta sallami Aisha snn suka fita" "babu yabo babu fallasa a fuskan Aisha' itako Zainab batasan tanayi ba" "tun daga lkcn da Aisha taga zhrdee ya canza mata' sbd yanzu koda ya shigo dubata idan yadawo daga kasuwa baya zama suyi hira kamar yadda da yakeyi mata' h'aka ma da safe yana shiga suka gaisa zai fita ya koma d'akin mai girki" "idan Zainab ce da girki' idan k'uma Aisha itama h'aka yake mata' " gani h'aka yasa Aisha ta dauracewa zhrdee' duk yadda yakai ga sha'awarta haka yake hkr' duk ranar da yaga bazai iya hakuri ba koda karfine sai yayi' duk k'uma ranar da yai mata na karfi kusa kwana take tana masa kuka' idan zhrdee ya tambyeta sai tace cikinta ke mata ciwo' shikuma hankalisa ya tashi ya kasa zaune ya kasa tsaye' bayan har cikin zcyrta ba h'aka bane' kawai dai a rayuwar Aisha tana kishin taga zhrdee yana wani mu'amala da wata bcc ba ita ba' h'akan yasa ta yanke wa kanta shawarar hkr dashi bazata kara bari wani abu ya shiga tsakanisu ba' shiyasa duk ran girkinta sai ta nade tace batada lfy" "shiko zhrdee haka kwai a rayuwarsa bayaso yaga Aisha cikin damuwa balle har ya takura mata da kansa' k'uma gashi idan har yana ganita tare dashi koda yace zai hakuri ya kyaleta baya iyawa' shima kansa ya rasa dalilin h'aka' shiyasa idan ya roketa ya gaji ko da kartine saiya biya bukatarsa idan yaso da safe sai ya bata hakuri" "bangaren Zainab kuwa tunda taga h'aka da duk ranar girkinta zhrdee baya daga mata kafa yasata tambyesa unguwa g'idan su" "a'a me zakiyi?" "Akwai wasu kaya nane dana mance dasu ranar da naje dauko su Abba" "a'a babu ida zaki' ga waya ki kira inna kice tabawa mamy ta kawo maki" "mika mata wayarsa yai" "a'a ka barshi kawai idan baka amince naje ba' sbd Inna batasan inda na ije kayan ba' nima kaina koda naje saina duba" "to naji' amma koda kinje bazaki Dade ba" "eh naji' NA biyo motar haya kenan na dawo?" "wani irin mugun kallo yai mata h'ade da cewa yaushe muka fara h'aka dake" "cikin wasa Zainab tace Allah ya huci zcyr maigida' nima gwadaka nayi danji abinda zakace" "to ai kinji idan banda rainin wayo h'aka kawai kije kina h'ada jikinki dana wasu kartan banza" "mikewa yai ya shige wanka' da zai fita kasuwa suka fita tare snn yanufi kasuwa" "saida Zainab tashiga suka gaisa dasu inna snn batarwa inna *lslaha* da sauri taje hospital dake kusa da g'idan su tai alluran planning snn yadawo g'ida' bayan ta dawone taiwa innarta mgnr ta h'ada mata magani" "da tace itace keda girki' tun a gun inna tabasu wasu tasha snn tasake h'ada mata wasu wanda zataje dashi g'ida masu kyaun gske" "yamma nayi zhrdee yazo daukarta' har ciki ya shiga suka gaisa da inna' inna tace saidai ya tsaya yaci abinci' Zainab ta kawo masa abinci yaci snn sukai sallama yana dauke da *Islaha* suka fita zuwa mota" "suna isa g'ida Zainab tai dakinta shiko zhrdee saida yashiga gun Aisha ya dubata snn yai mata saida safe yana rike da *Islaha* a kafada" banza dashi Aisha tai' shima dariya kawai yai ta fice" "ko kafin yaje har Zainab ta shiga wanka' zama yai yaci gaba da wasa da yarinyarsa har tafito' tana fitowa shikuma ya shiga nashi wankan' kafin yafito Zainab ta lallabi *Islaha* tai bcc snn itama tai kwalliya cikin kayan bcc" "zhrdee yana fitowa daure da towel turare kawai ya fesa snn yasa kayan bcc" "tun daga lkcn zhrdee ya daina matsawa Aisha' ranar girkinta idan ya lallaba yaga batada niya saiya kyaleta sbd duk a tunaninsa maybe cikine' tunda yasan dah ba h'aka take masa ba' k'uma gashi yanzu cikinta ya tsufa harma ta shige watan da hospital suka bata' shiyasa yanzu duk ranar girkinta saidai abinda baza'a rasaba' na tsakani mata da miji" "itako Zainab kwankwaran musu bayaso ya shiga tsakanisu da'ita' saidai halin yau da gobe da tafi wasan yaro' su *Akbar da Islaha* duk wani abin sha'awa na wasan yara idan zhrdee ya gani saiya siyo masu' sbd *Islaha* bata tafiya yasa zhrdee siye mata keken koyan tafiya' Zainab na gani h'aka a kullum cikin kara gyara kanta take shiyasa zhrdee har bayaso ta fita a girki' sbd yasan koda yazo idan ba a dakinta yake ba bata yarda' wani lkc ma har yai fushi da'ita dan kansa k'uma yake saukowa" "wata safiyar asabar Aisha ta dashi da nakuda' ranar zhrdee yana dakinta ne' h'aka ya dauketa zuwa hospital' suna isa labour room aka kaita' shiru2 zhrdee yanasa ido afito ace ta haihu amma shiru' har azahar' gani h'aka yasashi kira Hjy ya ranar mata' duk da ranta ya baci amma babu yadda zatayi h'aka ta shirya tacewa Zainab tazo suje' Zainab tace babu ida zata sbd ida yaso tasani Ai yanada number da zaikirata ya sanar da'ita" "Hjy tace kinada gskya toni bari naje" "koda Hjy ta'isa hospital duk fadawar da takewa zhrdee be tanka ba idan ba hkr ba babu abinda yake bata" "gani h'aka yasa ta hakuri' Aisha dake labour room bata haihu ba sai dare' tasamu twins mace da namiji" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 5⃣2⃣ "nurse ne ta fito daga labour room ta nufo gun dasu Hjy suke da zhrdee' zhrdee yana gani nurse ta fito da sauri ya mike h'ade da cewa madam ta haihu ne?" "eh ta sauka' ansamu twins mace da namiji" "Allahu Akbar' zhrdee yace" "Hjy dake zaune mikewa tai zuwa gun h'ade da tambyar ta sauka ne?" "eh ta sauka Hjy' ansamu mace da namiji" "masha Allah' ya ita mai jegon?" "nurse dake tsaye tace ta nanan lfy saidai ambata bedrest sbd ta huta" "OK zamu iya ganita?" "bismillh' tana gaba suna baya suka shiga d'akin' suna shiga zhrdee yai kan Aisha take kwance ya rungumeta h'ade da cewa sannu Aisha" "murmushi kawai tai" "Hjy na kan yaran' gani abinda zhrdee kewa Aisha yasa Hjy kulewa dan masa tsawa tai h'ade da cewa fita ka bani gu" "murmushi kawai zhrdee yai snn ya fita' yana tafe yana juyowa yana kallon Aisha' daure fuska Hjy tai" "bayan ya fitane Hjy ta dawo kan Aisha tana gaidata da jiki" "zhrdee yana fita ya kira umma mmn Aisha ya sanar mata haihu" "murna sosae mmnta tai h'ade da cewa Allah ya raya" "Zainab na g'ida har yamma zhrdee be kirata ba balle ya sanar da'ita" "koda ya dawo g'ida duk da ba itace keda girki ba amma koda ya dawo bata hanashi abinci ban' yana zaune a parlour Zainab ta kawo masa abinci' tana zaune yanaci suna hira amma be b'ude baki ya f'adi mata haihuwar Aisha" "har yagama gani ya mike zai sake fita ne tace ina zuwa k'uma da daren nan?' idan taji abinda zaice" "fita zaiyi" "zuwa ina k'uma" "wani irin tambya kikemi h'aka kamar dan gaban ki" "to kayi hkr idan tambyar da nayi maka ya bata maka rai" "ya wuce' kawai yace' har yasa kai zai fita Zainab tace zhrdee" "meye ne k'uma?" "yanzu sbd Allah abinda kakeyi ka kyauta kenan" "me k'uma nayi?" "Ashe Aisha ta haihu amma baka iya f'adi min ba?" "eh mancewa nayi' k'uma ansamu twins" "yayi kyau' yanzu yaushe zanje dubata?" "a'a kibari kawai' basai kinje ba" "sbd me?" "nace kidai bari kawai' idan naje zance kina gaidata" "amma sbd Allah h'akan da kai kana gani kayi daidai kena" to wlh idan yan'uwanta suka zagrni akan rashin zuwa banyafe ba" "eh kidai bari kawai maybe ma yau tadawo" "himm zhrdee kenan" "shima fita yai batare daya waiwayo ya dubeta ba" "kwana Aisha biyu a hospital aka sallamosu suka dawo g'ida' kanwar mmn Aisha ke dauke da babys zhrdee na rike da Aisha suka shigo da sallama" "duk da bacin ran da Zainab take ciki amma be hanata fitowa tai mata barka" "tun daga lkcn bata sake shiga harkansu ba' tsakanisu saidai gaisuwar safe bayan h'aka babu komai a tsakanisu" "ana gobe suna zhrdee yai wa Aisha siyayya kamar dama yaran basu da kayan sawa' kaya sosae zhrdee ya siyo masu daga ita Aisha har yara" "ido kawai Zainab ta zuba masu duk shiga da fitar da zhrdee keyi ana gobe suna irin uban kudin da yake kashewa" "ana gobe suna yan'uwa su Aisha na birni dana kauye duk suzo" "zhrdee yaso canzawa yara suna amma Hjy da Abba suka hana' Aisha me jego ansha kyau' sbd zhrdee ba karami kudi ya kashe mata ba' gani h'aka g'ida ya cika fal dangi da abokan arziki' yana Zainab itama ta kira kannita' basubar g'idan ba sai dare" "tun haihu Aisha zhrdee a d'akin Zainab yake kwana duk da kokarin Zainab wajan gani ta kyautatawa zhrdee wajan biya masa bukatarsa da kiyaye duk wani abu da zai bata masa rai amma be hanashi abinda yai niya wajan nuna banbanci tsakani su *Akbar* da su *shahid da shahida* yaran Aisha' duk da jirajiraine k'uma ba rasa kayan sawa sukai ba amma kullum Allah keda kullum idan yana dawowa daga kasuwa saiya siyo masu kaya" "duk da uban kayan da yasiyo masu llcn da aka haifesu ga kuma tun NA wacce cikin da ta rasu duk sunanan amma be hanashi siye masu wani' yau dayake ya mance har saida yashiga d'akin Zainab yana cikin cin abinci snn ya tuna hannu yasa ya dauko ledar h'ade da mikawa Zainab yace tashi kikaiwa Aisha" "bata musaba k'uma bata tambyesa meke cikin ledar haka ta mike ta kaiwa Aisha kayan snn ta dawo' ko kafin ta dawo ya gama cikin abinci kwashe kayan tai takai kitchen' tana dawowa ta dauki *Islaha* tai mata wanka suka kwantar' dama *Akbar* a d'akin Hjy yace kwana" "cikin dare Zainab na bcc kamar a mafarki taji ana shafeta' banza dashi tai' duk wani halamu zhrdee ya nunawa Zainab amma besa ta nuna tasan yanayi ba' mikewa yai yazo daidai kunnita yake kiran sunata" "Zainab' Zainab bcc kikeyi ne?" "banza dashi tai bata tanka ba" "Zainab duk bcc ne h'aka?" h'aba Zainab dinta d'in gyara mana' nasan kina jina Zainab " "Zainab dake kwance tana jinsa hawaye ne kawai takeyi" "Zainab dakefa nakeyi' k'uma nasan kina jina' still babu ko motsi' gani h'aka yasashi kwantar da murya yana cewa Zainab dinta d'in gyara kigani kinji wlh kadan ne zanyi dan Allah' zhrdee yana mgnr ne h'ade da jawota jikinsa" "Zainab najin h'aka ta fisge jikinta' mikewa zhrdee yai zai hayeta Zainab ta tureshi snn ta sauka ta barmasa gadon" "mikewa zhrdee yai ya kunna light d'in d'akin yaga Zainab zaune akan kujera tana kuka" "zuwa yai ya zauna kusa da'ita snn yace Zainab lfy?' Zainab taci gaba da kukanta" "hannu yasa ya jawota jikinsa ya rungumeta yaci gaba da tambyrta" "cikin kuka Zainab kwashe komai ta f'adi masa" "h'aba Zainab d'an nasiyewa su *shahid da shahida* kaya shine kike b'akin ciki kike kuka Zainab' wlh kinban kunya h'ade da mmki' a hkri dana sanki dashi wlh be kamata d'an wnn abu ya dameki ba' inda wanine ya fadimi h'aka ba keba wlh zance sharri yake maki amma yau da kanki kika b'ude baki kike f'adin h'aka" "kwata kwata wasu kayane na siye masu da har zaki dami kanki' k'uma koda na siye idan kika duba aisu yarane akan naki' a matsayinmi ma su Abba ne zasuzo suna maki kukan h'aka kibasu hkr bake da kanki zaki zauna kinayi ba" "amma babu komai yanzu nasan waye ke Zainab' yanzu me kikeso ayi maki?" "ni bana bukatar komai saidai kasa Abba a sch" "Zainab kenan' kwata kwata shekaran amma nawane da zan kaisa sch' saikace a kasa nake dibo kudi' yaron da ko mgn be gama iyawa ba" "amma naga wanda basu kaisa bama suna zuwa" "eh ba abin mmki bane dan sa'ar Abba suna zuwa sch' amma nidai kam ba yanzu ba' ke bari na f'adi maki gskya a yanzu da h'aka banida kudin da zaikai Abba sch" "to sai yaushe?" "sai yadda kagani" "himm kawai tace" "yanzu dai Dan Allah zomuje kibani hakkina" "tsaki kawai Zainab tai ko kallo be'isheta ba" "Zainab dakefa nakeyi" "kayi hkr bazan Iya ba" "kamar yay Zainab" "Ohooo" "ni kike cewa Ohooo Zainab?' amma kinsan hakki naneko?" wlh inda Aisha nada tsarki babu abinda zanzo nayi a gunki bazan kawai" "mikewa yai yaje ya kwanta h'ade da juya mata baya" "kallo kawai ta bishi dashi h'ade da girgiza kai" "da asuba zhrdee yaje masallaci yai sallah har yadawo yashiga wanka be tankawa Zainab ba' gani h'aka kitchen taje h'ada masa abin breakfast tana kitchen tana aiki tajiyo kukan *Islaha* zhrdee dake daki ya dauketa b'akin kofa yazo ya tsaya batare da yace kala ba' Zainab na hango shi da sauri tabaro kitchen tazo ta amsheta' saida tabari ya koma d'aki snn itama ta shiga zani ta dauka tana goya *Islaha* h'ade da cemasa ina kwana?" "banza yai da'ita" "duk da tasan yaji amma bata gajiba h'aka tasake cewa ina kwana" "lfy klau ya daga snn besake tankawa ba" "fita tai ta koma kitchen gani kamar sauri yakeyi yasata itama sauri tai ta gama ta dauko ta kawo masa d'aki dukawa tai ta'ije h'ade da dauko plate ta zuba masa" "bayan ya kare sa kaya zama yayi akan cushion yai breakfast yana gamwa mikewa yai ya tsallaka tre din yafice daga d'akin" "Zainab dake zaune b'akin gado mikewa tai ta h'ada kayan zuwa kitchen" "tun daga lkcn Zainab taki yarda da zhrdee duk dare h'aka yake rokonta yana roko har yagaji' h'aka ma yau tun goman dare zhrdee yake rokon Zainab amma taki yarda' da yaga bazai iya jurewa ba da karfi ya kamota' Zainab tana f'adin kabari kaga da yarinya ko". " saime idan ga yarinya ina ruwana da'ita".... "bayan kwana biyu Aisha tayi arba'in' zhrdee da kansa ya dauki kanwar bbnta wanda take zaune da'ita ya medata g'idan su Aisha' a ranar yace ta amshi girki' kamar tasan da h'aka shiyasa tana kai yara Immunisation daga nan tai alluran planning" "tun daga lkcn zhrdee besake rokon Zainab ba k'uma' itako Aisha da yaranta kusan niman zhrdee a gunsu yake tafiya h'aka ma kaya da saran amkawo sababbi wanda beyi yawa a gari ba saiya cirewa Aisha. " gani h'aka yasa Zainab fita har kansa gaba daya' k'uma duk yadda takai gason abu saidai ta tambyi Hjy ko k'uma ta hkr dashi' sbd tasan koda taiwa zhrdee mgn bazai yimata ba' H'akan yasa ta dauki al'amarinta gaba daya ta mikawa ubangiji' kowani dare nafila baya wuceta da karantu kur'ani mai girma" "amma duk da h'aka shiru bataga canji ba" "bayan kwana biyu ranar a d'akin Aisha yake' bayan ya dawo sallar asuba yashigo duba tashi Zainab da yara' bayan su gama gaisawa yana zaune b'akin gado Zainab na duke a gaban sa' zhrdee yace Zainab" "na'am" "Dan Allah mgn zamuyi dake' amma inaso ki fahimceni' wlh ba zanyi h'aka dan na walakantaku bane a'a wlh nima kaina dorowa yai' amma dan Allah koda na f'adi maki inaso kimi kyakkyawar fahimta" "babu komai' ina sauraranka" "Zainab aure zankara' harma nakai kudi a yanke mana rana' nanda sati biyu masu zuwa" "aure fa kace zhrdee" "eh wlh" "hayane ka kama?" "a'a wacce extra daki din can zanturo zuwa gobe a gyara mata' kinsan dayake bazawarane" "himm' babu komai Allah yasa ayi a sa'a" "amin ngd Zainab" "mikewa yai yafita' yana fita Zainab ta fasa da kuka' itama fita tai zuwa d'akin Hjy" "da kuka Zainab ta shiga' Hjy na ganita tace lfy Zainab" "cikin kuka Zainab ta fadiwa Hjy mgnr auren zhrdee' Hjy bata rufe baki ba zhrdee yai sallama ya shigo" "gani Zainab a gaban Hjy yasa kara ta kawo' bayan su gaisa Hjy tace zahradee" "da gske ne mgnr auren ka?" "eh wlh" "Zainab" "na'am Hjy" "bamu waje zamuyi mgn" "to tace h'ade da mikewa ta fita" "yanzu kai zhrdee sbd Allah tara matane a gabanka?' baka gani ga yayyinka nan ko na fari basuyi ba balle na biyu' amma kai da yarintanka zaka tara mata h'aka' mata biyu ma ya kakare dasu balle har kakara wata" "Hjy kenan dagani har su Allah ne ke rike damu' k'uma ko su da kike mgn babu abinda suka rasa' itama wanga da zan aura yarinya cefa ba babba bace" "nidai inda zakayi tawa da ha hkr" "h'aba Hjy Dan Allah kiyi hkr wlh ina sonta sosae Hjy" "nifa ba hanaka zanyi ba' amma abinda nakeso kaduba guda nawa kake da har zaka tara mata uku" "Hjy babu komai' nidai nafiso kisawa al'amarin Albarka" "shikenan zhrdee Allah yasa ayi a sa'a" "amma yar'gidan waye?" yar' g'idan *Alhj isa* ne na kan kwana " "wane kenan?" "manager banking d'in nan" "oho!! dama yanada wata yarinya ne h'aka" "eh kwanaki akayi aure' to wlh Mijin data aura ne wlh dan'iska ne yasaketa' wlh yarinya kyankyawa Hjy ga hankali' saima kin ganta" "to shine kai kuma zaka diba ko?" "eh wlh Hjy" "zhrdee ina rabaka' wani abin Albarka ne aure wata gudu ace har ya mutu shine kai zaka dibowa kanka" "Hjy kenan kedai kada kinji komai" "mikewa yai yafita zuwa d'akin Aisha" "yana shiga ganita yai zaune a b'akin gado tanabawa shahid nono shahida k'uma na kwance tana wasa' zama yai kusa da'ita Aisha ta kenan" "na'am zhrdee" "Aisha Dan Allah mgn ta fahimta nazo muyi dake' nasan kece me fushi amma Dan Allah a wnn karo banaso kiyi fushi dani' dan wlh duk lkcn da kike fushi dani banaji dadi" "murmushi kawai tai h'ade da cewa f'adi inaji" "a'a Aisha ba mgnr kina jiba' nidai Dan Allah inaso kimi kyakkyawar fahimta' kinga ko Hjy da take mahaifiyata dana f'adi mata fatan alkairi tai mi balle ke" "himm nidai nace f'adi" "to dan Allah kiyi hkr wlh bazan h'akan da niyar walakantaki bane' Aisha kinfi kowa sani ina matukar kaunarki' wlh duk wata matan da zan aura bayanki ne" "dakata zhrdee badai kace mi aure ne zakayi ba" "ni bance maki h'aka ba" "h'aka ne mana zhrdee" "eh to tunda kince h'aka ne' to h'akan nema" "mikewa tai h'ade da cewa to wlh baka isa ba" "h'aba Aisha' zomana ki saurari abinda zan f'adi maki" "Dan Allah katashi kabani gu' aure nedai wlh baka isa kayi ba" "ban isa bafa kikace Aisha?" "eh baka isa ba zhrdee' idan k'uma ka'isa to ayi mugani" "Dan Allah ja kibani gun wawiyar banza kawai' idan kudikine basai mugani ba" "nidai ba wawiya bace' saidai kaine wawa"..... " kafin Aisha ta kare zhrdee ya dauketa da mari a baki' saida bakinta yai jini" "ihu Aisha tasa h'ade da hurgi da shahid" "da sauri zhrdee ya cabke yaransa' snn yai mata tokari saida ta f'adi" "ihu taci gaba dayi' zhrdee yana kwantar da yaro ya h'au dukan Aisha' duk da h'aka bakinta be mutuba' shikuma be daina dukanta ba" "jin abinda sukeyine yasa Zainab zuwa ta kira Hjy' tare sukazo Hjy tana shiga ta kori zhrdee yabar d'akin snn ta kamo Aisha ta zaunar da'ita"""""" *to fa yau ake yinta' wannan shine batan baka tanta* 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES. F.O.W.☘ *story written by Mmn uswan* *Fans naga sakonku k'uma nagode sosai' haka nakeso a duk lkcn da kukaga wani abu daya shige maku duhu kada kuji komai ku tambayeni' sbd ta hakane zamu kara fahimtar juya da'kyau' dan haka nagode sosai* *amsar tambayarku shine' Aisha ba asiri taiwa zhrdee ba' tsabar sone da yake mata yasa idanusa rufewa' bafa sai zhrdee ba' ko nace maku littafi' ko kece Allah ya jarabceki da son mijinki' to duk irin abinda zaimaki wlh bazaki gani ba saidai wasu su gane maki' to hakama namiji' saidai wani yana iya dan newa yaki nunawa a tsakanisu amma wani k'uma a bayyane yake abinsa* *Duk abinda akace maki akwai soyayya tofa ta rufe komai' shiyasa ba'a shiga tsakani masoya' soyayyar gaskiya ita kebin yan"yan" da jikoki har karken rayuwarsu* *Sai matsalar anan Aisha tana matukar son zhrdee amma batasan yadda zata nuna maso irin soyayyar da take masa ba' sbd tanada fushi' ba Aisha kadai ba' duk mace mai yawan fushi takan ragu a gun maigidanta' hausawa suce mai yawan fushi baya mulki' shikuma a rayuwar da" namiji yanaso mace mai hakuri' shiyasa a kullum muke addu'ar Allah ubangiji ya kara mana hakuri da mazajen mu amin* *nagode sosai masoya littafin aure ibada ne* 🤝😄 5⃣3⃣ "zhrdee yana fita waje yaje gun motarsa ya b'ude ya zauna' a zcyrsa yana f'adi kedin banza' uwar data haifeni bata hanani abinda nake soba saike" "wlh aurena babu fashi duk wanda taga zata zauna ta zauna wanda k'uma bazata zauna ba bismillh hanya a b'ude take" "Aisha tana zama gani *shahida* na kuka yasa Hjy daukarta ta mikawa Aisha ita snn ta dauki *shahid* ta fita dashi zuwa d'akin ta" "tana shiga lkcn Abba shima ya shigo d'akin gani *shahid* a hannu Hjy yasa Abba karbansa yana masa wasa' Hjy tace Alhj" "na'am Hjy" "gani hnklin nakan *shahid* yasa Hjy cewa dan Allah kabani hnklinka nan" "sann ya bata hankalinsa' saida ta gyara murya cikin girmamawa tace Alhj kana sane da mgnr auren zhrdee?" "wani aure k'uma Hjy?" "himm' wlh nima dazu Zainab tazo da kuka take fadimi mgnr auren" "toke Hjy kin tambyesa?" "eh na tambyesa" "me yace maki?" "cewa yai harma yariga yakai kudi"? "da izini wa?" "wlh ban saniba" "ni wlh Hjy al'amari son yafara bani tsoro' ki dubafa mata biyu yaya ya kare dasu' da har zaije ya dauko wa kansa wani aiki k'uma" "wlh Alhj nima kaina abinda na f'adi masa kenan amma ya nace akan shifa saiyayi auren nan' abu daya kawai nake dubawa kada na hanashi bansan rabon dake tsakanisu ba' ko k'uma sanadiyar h'aka suzo suna aikata alfasha' kaga k'uma hakki a kanmu" "Hjy kenan' me k'uma ya kawo irin wnn mgnr?' yaro da aureansa' matarsa biyu fa?" "Alhj kenan masu mata hudu wanda suka haifeshi su aikata balle shi" "Allah ma ya tsare' insha Allahu bari zuri'a taba" "niba bance zan hanashiba amma ina masa tunanin abinda zaije ya dawo ne' sbd yau da gobe sai Allah' amma tunda yace yanaso mu babu abinda zamuce sai dai Allah ya sanya alkairi" "amin Hjy" "amma wani hanzari ba gudu ba' yar' g'idan waye?" "yace yar' g'idan *Alhj isa* ma'aikacin banking ne" "wani *Alhj Isa* kena" 'wanda dai kasani" "to Allah ya kyauta' amma a gaskiya tarbiyan yaran g'idan ne sai a hankali' amma tunda yagani yace shi tayi masa mudai bamu da tacewa" "hakane Alhj Allah ya rufa isiri" "amin Hjy" "yawwa Hjy dama akwai mgnr da nakeso muyi dake akan yaran nan" "wasu yara dama ciki kenan Alhj?" "su Shamsudee da Nurudee mana" "wani laifin sukai maka ko Alhj?" "a'a' basuyi min komai ba' amma a gskya Hjy bazan boye maki ba' nagaji da ganisu h'aka' batare da aure ba' sbd Allah zhrdee nefa kasa dasu amma gashi zaikai ga mata uku su basu ga ko daya". " gaskiya kam Alhj' to yanzu menene abin yi?" "abinyi kenan su fito da yaran da sukeso a h'ada dana son kawai' idan yaran da suke jira' iyayensu basu shirya yimasu aure ba to babu dole da kaina zan nima masu" "to shikenan Alhj duk yadda kai daidai ne" "kamar yaya Hjy?" "to Alhj me zance?' gani nayi dani' dasu' da k'uma abinda muka mallaka duk suna karkashin ikon kane" "Alhj najin haka kansa yai kato' murmushi yai h'ade da cewa hjyta kenan' shiyasa har gobe nake ji dake' koda yau ne farkon haduwarmu sai h'aka" "murmushi Hjy tai h'ade da cewa Alhj kenan kafara dadin b'akin nan nakako" "au dadi bakine ma kikace?' wlh da gske nake" "himm kawai Hjy tace" "gani kamar bata yarda ba yasa Abba ije yaro a gefe h'ade da cewa zoto kiga wani abu' jawota jikinsa yai ya rungume....... " h'aba Alhj meye kakeyi h'aka" *wohohoo jiya ba yau ba' ancewa tsoro wa tai rawa' tace d'an nan ta'ina zanfara' su Abba antada komado* 😋. "zhrdee be shigo cikin g'ida ba sai around 12AM lkcn kowa yai bcc amma banda Aisha" "tana zaune zhrdee ya turo kofa ya shiga' can cikin zcyrsa yai sallama' ko kallon inda Aisha take beyiba shigewarsa yai ya tube har zai kwanta yaga ta shinfida yaro a inda zai kwanta' dayan kuwa tana hannunta' yace gyara shi" "banza tai dashi" "dake fa nakeyi" "nan ma tai shiru" "nan ma tai masa shiru" "Aisha"... "ciki tsawa tace meye dan Allah" "wlh na rantse da Allah idan kika sake dakami tsawa saina maki dukan tsiya' dama ba gamawa nayi ba' Hjy ce ta katseni' mara kunyar banza kawai"... " nidai ba nice mara kunya b..... "kafin ta karisa ya dauketa da mari" "ihu Aisha tasa' gani h'aka yaje yasawa kofa key ya rufe snn ya dawo wlh idan naji ko tarine kikeyi saina maki wanda yafi wnn" "gani da gske yakeyi yasa Aisha hadiye kukanta" "zhrdee yana tsaye a kanta yana f'adi mari kunyar banza mari kunyar wufi kawai' inda kinada kunya dan nace zanyi aure har zaki ta da hankalinki' inda ba'a aure ke za'a auroki?' ko k'uma kinga ina nuna fifiko a tsakani keda Zainab shine zaki kawomi iskanci' to wlh daga yau dagake har Zainab babu wanda zan dagawa kafa' aure k'uma babu fashi';idan zaku kwantar da hankalinku Ku kwantar idan k'uma bazaku kwantar da hankalinku ku kuka sani" "aurenka din me ina ruwana da aurenka" "kimayi runki dashi" "himm kai ka sani' domina kaje ka auri mata dubu ma" "kinfi kowa sani ba'a auren mata dubu' inda anayi da sai nayi" "shigewarsa yai yaje ya kwanta" "da safe bayan ya dawo daga masallaci ko leka Zainab beyiba'dakin Aisha' ya koma' lkcn tana kan sallaya tana lazumi' gashi k'uma *shahida* ta tashi amma ba kuka takeyi ba' shire2 takeyi tana niman ta tada *shahid* hannu zhrdee yasa ya dauketa h'ade da cewa babyna zomuje kada kitada bros ko' k'uma kinga mumy tana sallah" "daukarta yau suka nufi d'akin Abba' da sallama ya shiga d'akin Abba' Abba dake shingide ya amsa da fara'arsa yana f'adin son har kashigo" "eh Abba' dukawa yai a ladabce ya gaidashi snn ya zauna' hannu Abba yasa ya dauki baby snn yace son" "na'am Abba" "naji wata mgn a gun Hjy da gske nan?" "eh da gske ne'tace har kakai kudi g'idan su yarinyar?" "eh haka ne" "kai da kanka ne kakai?" "a'a Abba SALE ne ya kaimi" "meyasa baka sanar daniba' kafin akai kudi" "kayi hkr Abba" "ba mgnr nayi hkr bane hujja nakeso" "kayi hkr kawai Abba" "to shikenan' Abba kada ka sake" "insha Allahu" "budurwace ko bazawara?" "bazawara ce" "kasan abinda ya fito da'ita daga g'idan mijinta?" "eh ta fadimi dalili" "ka gamsu?' k'uma kayi bancike akai?" "to shikenan' Allah ubangiji yabaka ikon adalci" "amin ngd".. "zhrdee be karisa ba su yya Shamsudee sukai sallama" "matsawa zhrdee yai ya basu gun suma suka zauna" "a ladabce suna gaida shi yya Shamsudee yasa hannu ya dauki *shahida* yana yimata wasa' Abba yace Shamsudee dama inaso ganiku kaida d'an uwarka" "to Abba Allah yasa ba laifi mukai ba" "a'a ba laifi kukai ba' duk da dar kusan da mgnr amma zan sake tuna maku". "na maifa Abba?" 'yah!!! mgnr yaran da mukai a baya?" "wane kenan Abba?" "wanda kukace iyayensu sunce sai sun kare karatu snn zasuyi masu aure?" "OK sunanan Abba" "Nurudee dake gefe yace Abba lfy?' wani abune ya faru?" "ba wani abu ya faruba dama mgnr aurene" "aure k'uma Abba?" "kwarai da gske" "nidai gskya Abba hkr za'ai mi' dan gsky aure ba yanzu ba" "Nurudee kanka daya kuwa?' kasan abinda kake f'adi?" "Abba ina sane mana" "kaita Shamsudee me kace?" "nima Abba ba yanzu ba" "menene hujjanku NA f'adin h'aka" "babu komai nadai kawai daiii". " dai me" "duk sukai shiru" "Abba yace to wlh bazai yuwuba' idan ma bcc kukeyi to ku falka' idan anawa mace auren dole to wnn karo maza zanyimawa" "bazan yarda da iskancin banza ba' ta yaya za'ayi maza kosassu kamarku kuce bazakuyi aure ba'idan har abinda kuka yankewa kanku kenan to wlh bana ko kaffara kuna zina a waje" "da sauri sukace kaee Abba" "da gske' idan ba zina kukeyi ta yaya namiji me shekaru kamarku kuce bazakuyi sha'awa ba' to wlh bazan yarda da shashanci ba' na baku nan da sati kudawo ku sanarmi da yadda kukai idan yaso saina tura abbanku SALE" "sbd so nakeyi na h'ada gaba daya naku nada son" "da sauri sukace wani son k'uma" "ina da wani son ne wanda yafi wann" "Nurudee yace badai wani aure zhrdee zai kara ba?' Shamsudee dake gefe yace ga zahiri kuwa" "zhrdee dake gefe dukar da kai yai kasa' Abba yace idan aure zai kara saime' aini yafimiku tunda gashi har mata nasamu" "duk murmushi sukai' snn Shamsudee yace Abba sbd Allah zhrdee ya dunga tara mata kenan da kuruciyarsa" "zhrdee najin h'aka mikewa yai yafita a d'akin" "bayan ya fitane Abba yace nima kaina nayi tunanin h'aka amma tunda ya nuna yanaso yaya zanyi dashi" "yaya zakayi dashi fa kace Abba' hanashi zakayi' iji Shamsudee kenan" "a'a ni bazan hanashi ba' tunda banike ciyar masa dasu ba" "shiko yya Nurudee da ba mgn yaci ka yiba mikewa yai ya fita' shima yya Shamsudee fita yai yabi d'an uwarsa" "bayan su koma d'akin sune yya Shamsudee yace kae bros kanajin Abba kuwa?' to ba tare muke ba?' to yanzu me kagani?" "ni dama koda Abba beyi mgn ba inaso nayi masa mgn' amma abinda ya hanani yimasa mgn inaso sai ku daidai da'ita tuku" "wahh!!! k'uma?" "haybat mana" "waye k'uma haybat?' ina mgnr AMINA?' wacce Amina k'uma yar'raini wayo' wlh idan ba Allah ne yai zan auri Amina ba' wlh bazan aureta ba' yarinyar da ta medani kamar ATM card k'uma rana daya nace ban dashi ko daga wayarta batayi' to kai kana gani h'aka ina k'uma ga idan muyi aure' wlh yarinya karama zan aura wanda zan juyata ta yadda nakeso" "kayi daidai d'an' uwa" "nima abinda ya hadani da SALAHA kenan' shiyasa tuni na fita har kanta' yanzu wacce na samu this year ta kare SSCE dinta idan mu daidai ita zan aure nima" "to shikenan Allah ya datar damu' amma mata sun zama abinda suka zama' ta hakane ake samu a cucesu" "Shamsudee yace wawaye ba" ~~~ ~~~~ ~~~~ "Fatima tana fita takaba'daidai da lkcn Bilyaminu ya tattaro dukiya Nasir wanda yake hannunsa ya kawo g'ida kano' Alhj mahaifin Nasir yace tunda da kansa ya roki arziki cewa koda bayan ransa kada a daina kula da marayun da yake kula dasu amma shidai yanzu babu abinda zaice duk abinda Fatima ta yanke shikenan" "Fatima na kuka tace babu damuwa insha Allahu zanci gaba har karken rayuwata' bayan in gaba h'ada dukiyar tsaf Fatima tace ta wakilci Bilyaminu da yazamun juya dukiyar yaci gaba da business d'in yana fita dasu' k'uma zata kira customers dinsa ta sanar masu" "Bilyaminu yai murna sosae dajin h'aka" "bayan tafiyar Bilyaminu ne Abba Bbn Nasir yake cewa Fatima ba naki taki bane' amma me zaisa ki dauki dukiya me yawa h'aka ki dankawa yaran aikin Nasir' halin mutum yanzu sai Allah" "h'aka ne Abba' ai bazan sakar masa duka bane' bayan kwana biyu nima zanfara business din da kaina' idan yaso duk wasu abu da ake bukata sai karinka aikosa yana siye ya kai mi can" "to shikenan H'akan ma yaya" "tun bayan fitar Fatima takaba zawarawa suke zirya' dana Allah dana allaro' mafi yawanci dan kudin da Nasir yabarine yasa suke zuwa' amma Fatima bata saurarsnsu' Bbn Nasir yai f'adi har ya gaji amma a banza' gani zai matsa mata da mgnr aure yasa ta kwashi yaranta ta koma g'idan bbnta da zama' ita da yara' koda bbnta ya tambyeta dalilin dawowa g'ida babu abinda ta boye masa' h'akan ne yasa yace ta zauna zuwa wani lkc" *dan Allah kuyi hkr zaku ganisa a gurguje* ~~~ ~~~~ ~~~~ "mgnr su zhrdee da yayyinsa saura sati daya' g'ida sai faman gyara gyare akeyi' da yake yau Aisha ce keda girki zhrdee yai wanka zai fita yace Aisha" "na'am" "Dan Allah masu aiki zasuzo gyara d'akin *Rukayya* inaso kiyi masu abinci" "Aisha ta kallesa days sama har kasa snn tace baza'aiyi ba" "me kikace?" "nace bazanyi ba" "ninefa Aisha" "Dan Kaine sai me" "h'aka ne Aisha'bakida laifi' Allah ya shiryeki" "kai kasani" "be tanka taba fita yai zuwa d'akin Zainab tana zaune a b'akin gado ya shigo' fuska a daure tace har zaka fita kenan" "eh zanfita kenan' dama nazo na sanar makine masu aikin d'akin amarya zasuzo gyara Dan Allah abinci nakeso kiyi masu' Akwai kayan biya jiya NA karo suna cikin frg" "to kawai tace snn yafita' yana fita hawayene kawai suka zubo mata" "mikewa tai taje kitchen tafara aiki tun kafin suzo sbd kada ta makara' ko kafin takare suzo su fara aiki' Aisha na gani zuwarsu ta shirya zuwa uguwa' babu uban data sallama' daga gidan su tawoce g'idan ubaida' sukasha hiransu' bata dawo g'ida ba sai bayan isha' zhrdee yana shiga g'ida itama ta shiga" "ganita tana shigowa ta gate mmki ya kamashi amma bece da'ita komai ba har tashige dakinta' dayake ubaida tariga taiwa yara wanka' shiyasa Aisha na zuwa kwanciya kawai sukai' sbd mmki zhrdee kasa mgn yai ido kawai ya zuba mata" "washe gari da safe bayan zhrdee ya fita Zainab itama ta shirya ta nufi g'idan su ita da yara' bata dawo g'ida ba sai bayan magrib' Ashe zhrdee yau be dadi kamar yadda yasaba dadewa ba' Zainab na sallama zhrdee yazo parlour yaja ya tsaya' tana shiga yace da izini uban wa kika fita?'" "Zainab tai shiru" "badake nake yiba" "kayi hkr" "banason mgnr banza' wai me kukeso Ku meda nine eyya?' wani sabon iskanci kuka dauko' kowani shege ya rika fita bada izini naba' to wlh bazan dauki rainin wayo ba' duk wanda ya kara fita ko nan da b'akin gate ne wlh saina karkkarya masa kafa' idan kunce karyane ku gwada" "Aisha na dakinta tana dariya h'ade da cewa Allah ya kara badai komi nayi kice sai kinyi ba' idan wani yai rawa ya samu kudi waniko saidai duka" "Zainab na shiga daki zhrdee shima ya shiga har kasa ta duka tace dan Allah kayi hkr wlh mancewa nayi na dauka na sanar makane" "banza yai da'ita ya h'au gado ya kwanta" "ana sauran kwana biyu biki zhrdee ya kawo masu turame zannuwa super wax kala bibbiyu h'ade da kayan yara' *shahid da shahida* kala uku uku h'ade da takalma" " *Abba da Islaha* kala bibbiyu" "ranar juma'a ana saukowa masallaci duk aka daura masu aure'yya Shamsudee yya Nurudee da zhrdee" *turrr kashi wannan shine ake cewa kara da kiyashi* *Allah ya kyauta* 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 5⃣4⃣ "g'ida cike yake da jama'a' dangin Abba na birni dana kauye duk su zo' hakama Hjy yan' uwa da abokan arziki duk su hallara" "bangaren su Zainab da Aisha su babu laifi sbd yan' g'idan su Zainab suzo mata' na Aisha' kuwa ubaida duk tabi sch mate d'in su wanda suka kare sch dare ta gaiyata suma suzo babu laifi' kodan suzo suci banzama sazo" "komai zhrdee ya'ije masu available d'an h'aka yan' biki kowa yake iya yinsa" "yamma nayi kanni Hjy dana Abba sukaje dauko amare' saida aka fara kawosu family hause gun Hjy snn aka daukesu zuwa can gidajensu' comfort daya ne saidai kowane da apartment dinsa" 'itako ta zhrdee d'aki kawai aka kaita' yan'uwa da abokan arziki kowa yai irin nasa f'adin snn suka tafi g'ida' around 11PM Ruslayni ya rako ango daki' dama sai h'akan ta kama ake nimansa' yai masa nasiha iya abinda yasani a matsayinsa na tuzuru' d'an baza'ace masa saurayi ba k'uma' snn sukai sallama" "a wnn dare zhrdee a angwance kayansa' Aisha' dake d'aki tayi kuka har taji babu dadi' Zainab ko gani tunani zai dameta da yawa mikewa tai taje bathroom tai alwala tazo ta fara jere nafila saida tai raka'a takwas baya tayi taihiya da sallama daga hannunta tai sama tana cewa *ya Allah ga baiwarkanan tazo da kokan baranta' Allah kaine maji rokon bayinsa' wanda baka gajiyawa wajan biya mana bukatunmu' ya ubangiji Allah kaika halitceni kafi kowa sani halin da nake ciki Allah' wannan auren da maigidana yayi idan da alkairi a cikinta Allah ka sadamu dashi' idan k'uma babu alkairi Allah ka tarwatsashi' duk wani sharri da tazo dashi Allah kada kabata ikon cin galabarmu' duk da kafimu sani waye ita Allah' Allah ka karemu da kariyanka' ka doramu bisa kan makiyanmu' ba'ita kadai ba' duk wani halitta da yake nufinmu da sharri daga har maigidana da yarana Allah' ba wayonmu ko dabaranmu bane face gani damarka' Allah ka yassare mana' ka kara budawa maigidana a gun nimansa Allah' allahumma jah'alal kur'ana lana fid duniya karina wafil kabari mu'unisa wa'alal suradih nura wafil kiyamatu shafi'an wa'ilal jannati rafi'an wa'minal nari suturan wahijaban wa'alal hairati kullihi dalilan wa'imamman bifadlika wa'judika' wa'karamika yyyyya akramal'akrami* ... "saida takai har karke snn ta shafe' bayan ta shafane ta dauko casbaha taci gaba da wuridi. " Zainab bata kwantaba sai bayan sallar asuba" "zhrdee ango yau ko masallaci bejeba yana d'aki shida amaryansa Rkkuya' duk kowa yana nasa d'akin' zhrdee be fitoba sai around 10AM snn ya fito' d'akin Zainab yanufa da sallama ya tura kofa ya shiga lkcn Zainab na bcc ita da yara zhrdee ya shigo' gani bcc takeyi ya tada ta' tashi tai ta zauna snn tace ena kwana" "yana tsaye a b'akin gado yana hamma yace lfy klau' wlh bcc samu nayi bcc bane yasa yake ta damuna" "banza dashi Zainab tai sbd tasan ba shine a gabanta ba' k'uma koda be f'adi ba tasan ba kallon juna zasuyi ba" "Zainab kina jina kuwa?' yaya banga kin kawo mana abin breakfast ba?" "duk zhrdee yana mgn ne h'ade da lumshe ido" "Ai ba nice da girki ba' Aisha ce". "Ohooo h'aka ne fa' to bari naje na sameta" "fita yai daga d'akin Zainab' yana tafe yana layi' kamar wanda yasha kwaya" "yana shiga ganita yai zaune b'akin gado tana wasa da yaranta' daga kai Aisha tai ganisa da tai a tsaye kusa da b'akin kofa yasa taci gaba da wasa yaranta' Aisha" "cikin tsawa tace meyene batare data kallesa ba" "Aisha Ashe kece da girki shine baki kawo mana abinci ba kika barmu muna jiranki' dan tashi kije ki h'ada mana breakfast" "duk zhrdee yana mgnr ne yana mika h'ade da bin bango" "mikewa Aisha tai batare da tai mgn ba tana isa inda zhrdee yake tsaye hannu tasa da karfi ta igijesa waja ta sawa dakinta key ta rufe snn ta koma kan yaranta" "zhrdee yai knocking h'ade da kiran suna Aisha har ya gaji amma bata b'ude ba' gani h'aka ya koma d'akin Zainab' tana kwance yace Zainab" "b'ude ido tai h'ade da cewa na'am" "dan Allah tashi ki h'ada mana abin breakfast kinji Zainab dita da Allah" "to kawai tace masa" "ba toba Zainab Dan Allah mike wlh yunwa takeji har dani ma" "bata tanka masa ba ta mike" "yawwa ko kefa' maza kiyi sauri Dan Allah muna jira' kina gamawa ki kawo mana daki" "tana fita shima ya fita zuwa d'akin Rukky' ita k'uma kitchen ta shiga' arish ta dibo ta fara ferewa' dayan kan gas din k'uma tasa ruwan tea' or reedy ta riga ta dora mai a wuta shiyasa tanayi tana zubawa a mai" "Zainab tana aikine amma zcyrta a cunkushe babu dadi" "jin motse a kitchen yasa Aisha fitowa ta leka gani Zainab ce ke aiki taca Zainab badai aikin zhrdee kike yiba?" "Zainab tai banza da'ita" "Zainab da kefa nakeyi" "dakefa nakeyi" "Ohooo ke kika sani' idan ma kinyi dan niman gindin zamane babu inda zai kaiki' k'uma koda kinyi babu lada sbd daga gani bada son ranki kike wnn aikin ba" "fita Aisha tai zuwa b'akin kofar d'akin Rukky tana cewa wlh ba'ayi shegiyar da zan zauna na girka mata abinci tana zaune taci banza ba" "duk abinda Aisha ke f'adi a kunnisu' da tagaji da masifarta takoma d'aki tana cewa Zainab wlh kekikaso kibawa kanki wahala" "Zainab tana gamawa ta jeresu cikin tre ta dauka zuwa d'akin Rukky b'akin kofa ta tsaya h'ade da sallama' zhrdee yace turo ki shigo mana" "da sallama Zainab tashiga lkcn Rukky na kwance akan gado shikuma zhrdee yana zaune ta dora akanta akan cinyarsa gaba daya hannayesa yana jikinta' gani Zainab nan yasa Rukky cewa washhh Allah on" "yaya akai ne amaryata?" "jin h'aka yasa Zainab ije tre d'in da sauri ta mike daga duken da take" "har takai b'akin kofa Rukky tace wlh duk cinyoyina zafi sukemi" "zhrdee yace to Ai kece Ai" "duk a kunni Zainab hawaye kawai suka zubo mata' da sauri ta shige dakinta ta fashe da kuka' *Akbar* dake wasa da *Islaha* zuwa yai ya tsaya gabar mmnsa yana kallonta" "sauka sukai zhrdee da kansa ya diba ya zuba a plate snn ya h'ada masu tea yake bata abaki' idan ya bata itama diba takeyi ta bashi' da h'aka har suka kare" "b'ude kofa yai yana kwadawa Zainab kira akan tazo ta kwashi kayan abinci' duk kiran da zhrdee keyi a kunni Zainab amma bata amsa shiba' da yaji shiru da kansa ya dauka zuwa kitchen snn ya koma suka dora daga inda suka tsaya" "kowa na dakinsa babu wanda ya fito har bayan azahar around 3-30 zhrdee ya sake fitowa zuwa d'akin Zainab' gani ya shigo juya masa baya tai' yace Zainab ina abinci ranarmu?" "Zainab tai banza dashi" "Zainab dakefa nakeyi" "Ai banice da girki ba" "idan ba kece da girki bafa sai me?'. maza kitashi kije ki dora mana abinci" "bazan yiba" "me kikace Zainab?" "cewa nayi bazan yiba" "ban'isa dake bane komai?" "ka'isa amma yine bazan yiba" "Zainab tashi kije kiyi" babu inda zani " "ki tashi kawai" "bazan tashi ba" "hannu zhrdee yasa ya shako mata wiyar riga ya dagota' take idanu Zainab suka ciko da kwalla" "janta zhrdee keyi zuwa kitchen' har yakai b'akin kofa' jin zafin shakar da yai mata yasa Zainab cizonsa a hannu" "zhrdee najin h'aka ya dauketa da mari saida da f'adi kasa' kuka tasa' *Akbar* dake zaune shima kuka yasa' zhrdee ya sake sa hannu zai jata zainab taki yarda' yayi3 amma taki yarda yajata' sbd haushi yasa zhrdee sake dauke Zainab da mari" "Zainab tace Allah ya'isa ban yafe ba' kafa yasa zai shureta ta rike masa kafa" "Zainab ki sakarmi kafa ko nayi maki duka" "bazan sakeba" "sakarmi kafa" "bazan sake ba" "da karfi ya fisge kafarsa snn yasa hannu ya shakota ta mike daidai kan fuskanta yake mata mgn' wato ke kinaso ki koyi rashan jin mgn ko' da har zansaki aiki kice bazakiyi ba ko' wlh idan kika sake sai kinyi mmkin abinda zamaki a g'idan nan" "Dan Allah ni ka sakeni" "waye kike cewa Dan Allah?' wnn shegen b'akin na rashin kunya saina farfasashi naga karyan rashin kunya" "kai kasani' duk abinda zakayi zhrdee kaje kayi idan wani be gankaba Allah yana kallonka k'uma wlh sai Allah ya sakami' mugu anzalumi kawai".... " karaf tasake jin saukan mari h'ade da tokari' kuka tasa ta f'adi a kasa" "Abba dake tsaye yasa kuka h'ade da rikewa bbnsa kafa" "hannu zhrdee yasa ya janye Abba daga jikinsa snn ya fice yana cewa magani mara kunya kenan" "f'adawa jikin Zainab Abba yai yaci gaba da kuka" "d'akin Aisha ya shiga' Aisha na gani shigowarsa ta daure fuska' kusa da'ita zhrdee yaje snn yace Aisha ta" "cikin galatsi tace meye?" "h'aba Aisha ta ninefa zhrdee dinki" "to idan Kaine saime" "a'a babu komai wlh' hannu yasa ya rungumeta ta baya h'ade da cewa kin sanine aishata" "ni kasakeni" "wannan ne k'uma kikai karya" "kina jina my Aisha" "saika f'adi" "Dan Allah ba" "uhhm nace ba' nace ba" "kace me?" idan zakai mgn kayi kawai" "nace Dan Allah ki taimaka Dan Allah badan niba kidan dafa.... "na dafa me?' badai abinci ba" " eh shi d... "h'aba dai kaima kasan abinda bazai wuyu bane' wlh bazan dafa ma kowace shegeya abinci taci ba' idan yuwa ya dameta tafito ta shiga ciki ta dafa da kanta" "h'aba Aisha jiya jiya da zuwanta ace ta shiga kitchen?" "to sai me?' Dan tashiga kitchen OK wata ga yar gold ka dauko ko?" "wahh ni banceba' Dan Allah ki rugami asiri" "to Dan Allah koda indomie ne ki taimaka ki dafa mana... "zhrdee fita ka bani gu" "Aisha bazan fita ba" "kafita banida lkcn ka" "toai ni inada lkcnki aishata" "hannu tasa ta tureshi tana f'adin fita mara zcy kawai" "eh naji idan akankine bazan tabayin zcy ba" "yana fita d'akin Rukky ya koda snn ya dauki wayarsa ya kira Amatullah yace tazo' bata bata lkc ba tazo' kitchen ya shiga ya dauki kula yace taje gun Hjy ta amso masa abinci" "koda yamma yai be tsaya jiran kowa ba fita yai yaje ya siye masu kaji fa yoghurt leda biyu snn ya dawo yana shiga saida ya fara kaiwa Aisha leda daya snn ya karisa d'akin Rukky" "Zainab na d'akin ta batasan abinda ake ciki ba" "tun daga lkcn baya sauraran sai ankawo masu abinci ba wani lkc a gun Hjy yake dibowa wani lkc k'uma restaurant yake zuwa ya siye masu har girki ya dawo gun Zainab" "koda ya dawo d'akin Zainab babu abinda ke shiga tsakanisu idan ba gaisuwa ba' bayama shigowa d'akin sai bayan 11PM wani lkc yana d'akin Rukky wani lkc k'uma d'akin Aisha" "gani har zata fita girki da safe lkcn yana shiryawa zai fita kasuwa' tura Abba tai gun Hjy snn ta rufe d'akin da key tazo har kasa ta duka a gaban zhrdee snn tace Bbn Abba" "zhrdee yana jinta yai banza da'ita yaci gaba dasa botur din rigan sa" "tasake cewa Bbn Abba dakai fa nakeyi" "cikin tsawa yace meye ne?" "a take Zainab ta fashe da kuka" "tsaki kawai yai h'ade da janye kafarsa" "da sauri Zainab tasake binsa ta rike masa kafa dukka bibbiyu cikin kuka tace dan Allah Dan annabi duk abinda nayi maka kayi hkr ka yafemi" "kara fisge kafar zaiyi Zainab ta rungumesa takara rusawa da matsananciyar kuka tana Dan Allah zhrdee kayi hkr" "a lkcn ne zhrdee ai dama nasan rana irin wnn zaizo' wato Zainab kema so kike ki dauki abinda Aisha' keyi kema kikeso kiyi ko?' har nasaki aiki kice bazakiyi Dan ke kin isa da kanki ko Zainab" "Zainab na duke idan ba kuka ba babu abinda takeyi" "ni bani da abinda zance maki' ki tashimi a gaba kije duk abinda kikaga dama kiyi Zainab' tunda yanzu kin zama yar'kanki ban'isa da keba" "kafa yasa ya hambareta yaje ya b'ude kofa yai tafiyarsa' faduwa Zainab tai taci gaba da kukanta" "da yamma Rukky ta amshi girki' itama daga bakinta saina zhrdee ta dafa" "itama Aisha fitowa tai tasa nata sanwar' gani suna kai kawo a kitchen din yasa Zainab hkr da nata girkin' dukkansu suke aiki amma babu wanda ya tanka wa d'an uwarsa" "shima zhrdee dayake yasan yau ranar amarya ce yasashi dawowa da wori 5 na yamma ya masa a g'ida da gangan Aisha ta dora spoon din silver akan gas Rukky na parlour zaune da zhrdee suna hira' mikewa tai tashiga kitchen din duba abinci' tana gama dubawa har ta juya zata fita Aisha ta dauki spoon d'in ta nanawa Rukky hannu" "ihu Rukky tasa tana kiran wayyo Allah na' a guje zhrdee ya shigo kitchen d'in juyawar da zatai daga hannu tai zatakaiwa Aisha" "juyawar da Rukky zatayi takaiwa Aisha mari' Aisha bata bari mari ya sameta ba ihu tasa h'ade da ture tukuyar abincin Rukky" "nan kokuwa ya tashi' da sauri zhrdee ya shiga kitchen d'in' tsakiyar su yashiga yawo Rukky yai tafito daga kitchen din' Aisha na tsaya tana mata gwalo batare da zhrdee ya gani ba" "duk da rashin hkr irin na Rukky amma a wann karo ta hkr' amma can cikin zcyrta tana cewa wlh saina rama koba yanzu ba" "Zainab na dakinta ko kafa bata lekoba" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* *Fans duk naga sakonniku k'uma ngd sosai*. _*~ga masu korafi akan zainab~*_ *ga masu korafi cewa be kamata ace duk irin addu'ar da Zainab keyi ace har yanzu bata samo biyan bukata ba?" Ba h'aka bane idan kukai la'akari k'uma kuka duba lkcn da ANNABI Musa yake rokon Allah subhnahu'wata'ala be samu biyar bukatar saba sai bayan shekara arba'in' ina k'uma gamu d'an Adam' dan h'aka abinda nakeso kusani bawai Allah be amshi addu'ar Zainab bane' a'a ya kyaleta ne sbd yaga iya imanita' duk mumini Allah yakan jarabceshi da abubuwa dayawa a rayuwa mai kyau ko akasin h'aka' badan baya sonsa bane' a'a saidan yaga iya imanisa' shiyasa duk lkcn da kai sallah yanada kyau kayi addu'a Allah ya zarabcemu iya imanimu' ya k'uma bamu ikon cinye wnn jarabawar* 5⃣5⃣ "zhrdee yana rike da hannu Rukky suka shiga d'akin ta' itama Aisha tunda niman mgn ya kaita kitchen k'uma bukatar ta ya biya dakinta itama ta shige" "zhrdee suna shiga ya rike hannu yana hura mata' sbd b'akin ciki kasa mgn Rukky tai ido kawai ta zuba take kallon zhrdee' gani irin kallon da take masane yasashi jawota jikinsa ya kwantar da'ita a cinyarsa yana shafe mata kai" "shiru kawai tai amma abinda yake zcyrta sai Allah' idan shi kadai yasan abinda take tafe dashi' da k'uma abinda take shirin aikatawa" "gani shirun da taine yasa zhrdee kiran sunata yana f'adi Rukky badai zafin bane yasaki yin shiru?" "murmushi yake tai masa h'ade da cewa babu komai Ai ya huce baya zafi k'uma" "idan kinsan har yanzu yana zafi kitashi mu tafi hospital" "a'a babu komai' kada da damu" "to yanzu me zakici naje restaurant na siyo maki" "a'a kada ka damu' ka barshi kawai" "zhrdee yana fita daga d'akin Rukky d'akin Aisha ya shige' Aisha tana gani zhrdee ya shigo ta daure fuska tai kicin kicin da rai' gani haka yasashi kasa mgnr daya kawoshi shafa kan *shahid* kawai yai dake hannunta snn ya fita" "yana fita da bishi da dariya tana f'adi badai kana zaune lfy kace aure ba' muzuba mugani shege ka fasa' daukar danta tai tana masa tawai" "zhrdee yana driving tunani kala kala yakeyi akan Aisha' meyasa Aisha take h'aka ne' meyasa ta canza daga aishan dana santa ne' kodai dan auren dana karane' amma idan ba'a aure ita kanta da ban aureta ba' kodai wanine yake sata duk irin wnn abubuwa da take aikawa' ko k'uma sbd taga Allah ya jarabceni da sontane yasa duk take abinda takeso' ko k'uma sbd taga tun farko nafi fifitata akan Zainab ne' ko k'uma dai hakkin Zainab ne yake bibiyata' idan ko hakkin Zainab tabbas ina bukatar gyara a dukkan al'amurin gidana' sai k'uma kashhh inadai zaune da Zainab kawai badan ina sonta ba" "amma k'uma mgnr soyayya ko kiyayya takare sbd ga yaran dake tsakanimu da'ita' gashi Zainab tanamin biyayya duk abinda na umarceta bata musu' duk da ba wani kyautata mata nakeyi ba' k'uma koba komai yakamata Zainab taci albarkacin iyayena'sbd Abba yami dukkan komai a rayuwata' na tabbata idan na kyautatawa Zainab tamkar na kyautatawa abbane' nasan Abba zaiji dadin h'akan' insha Allahu zanyi kokari wajan gani na kyautatawa Zainab' komai komai yakamata taci albarkacin su *Akbar da Islaha* daga iyayena saisu banida wanda suka fisu a f'adin duniyarga" "sbd tunani zhrdee har ya wuce inda zaije' saida yasake dawowa da baya' al'saheel restaurant yaje ya siye masu abinci dukkansu ya siye masu leda uku snn ya juya ya dawo g'ida yana shiga d'akin Aisha ya fara shiga yabata nata'ba sannu bate ngd ido kawai tabishi dashi' snn ya fita ya kaiwa Zainab itama nata' Zainab dake kwance tace ngd' nan ma fita yai zuwa d'akin Rukky' koda shiga ganita yai kwance amma ba bcc takeyi ba' gani shigarsa ne yasa Rukky mikewa ta amshi ledar dake hannu zhrdee b'akin gado ya zauna ita k'uma fita tai zuwa kitchen ta dauko plate da spoon snn tazo ta jiyo suka zauna sukaci snn sukai wanka suka kwanta" "da safe Aisha na tashi taiwa yara wanka ta shiryasu bayan ta basu nono susha suyi bcc itama tai nata wanka ta shirya' zhrdee yana shiryawa sukai sallama da Rukky ya bita tana rike da jakarsa wanda yafita dashi' a parlour ta tsaya jiransa' d'akin Zainab yafara shiga sbd shine yafi kusa dashi sukai sallama snn ya fito zuwa d'akin gimbiyarsa Aisha tana zaune tana gyara hannu jakar da zata fita dashi ga kayan ta''ije a gefe gun zhrdee yai ya zauna kusa da'ita h'ade da dafe kafadarta cikin murmushi yace my madam yaya aikaine" "himm babu komai' katashi lfy?" "lfy klau' ya kwana yarana'da k'uma mmnrsu" "murmushi Aisha tai snn tace lfy klau" "jaka kike gyarawa?'" "kawo to na tayaki gyara wa" "hannu yasa ya amsa yaci gaba da juya mata karfen da takeson juyawar' yana gamawa ya mike mika mata snn ya mike" "gani su *shahid da shahida* susha kwalliya suyi kyau sosae yasa zhrdee cewa my children's ya kwalliya ne kuka sha h'aka?" "eh wlh uguwane nakeso naje" "uguwa k'uma Aisha?" "eh wlh" "g'idan kuzaki ko ne?" "eh daga nan k'uma zan tafi g'idan kawayena nayi masu ban gajiya da zuwamin biki da sukai" "wani biki k'uma?" "bikinka mana" "himm Aisha kenan' amma wnn abubuwa da kike niman fitowa dasu koya maki akai ko" "h'aba zhrdee wani irin koyami k'uma' wato ni kenan banida abin kaina sai an koyami" "eh mana Aisha idan ba koya maki akai ba nasan duk wann abubuwa wlh ba haliki bane' ko k'uma kawaye da kika fara bine suke koya maki h'aka?' nidai aishata dana sani mgn ma be dameta ba"... " himm zhrdee kenan dama can ina mgn abuna" "OK ni kenan dai akewa rowa ko" "nidai yanzu na tashi ka saukeni a kofar g'ida?" "kinga Aisha kiyi hkr kibari zuwa wani lkc amma ba yau ba" "a'a zhrdee ni yau nakeso naje'sbd akwai abinda zanyi ne a g'idan mu" "a'a Aisha kada muyi h'aka dake' nafiso idan nayi maki mgn kice to" "ni gsky sai naje" "sai kinje fa kikace?' to bismillh' na rantse da Allah nanda bikin gate naji ance kin leka mai rabani dake sai Allah a g'idan nan' idan k'uma kince karyane ki gwada" "ficewarsa yai' ko tari Aisha batai ba har yafita" "yana fita Rukky ta rungumesa' daidai lkcn Zainab na fitowa daga d'akin ta' tana gani h'aka da sauri ta dauke kanta daga gunsu' Rukky na rungume da zhrdee suka fita zuwa gun mota' saida ya shiga yatada mota snn ta mika masa jakarsa h'ade da daga masa hannu' saida taga tafiyarsa snn ta juya zuwa ciki g'ida" "d'akin Hjy Zainab taja tana shiga taga Hjy na gyara gado' da sauri da sauke *Islaha* dake hannunta ta amshi aiki' gani h'aka yasa Hjy ta amshi yarinyar Zainab taci gaba da aiki' Hjy na zaune kan cushion tana wasa da yarinyar" "Rukky na shiga parlour ta samu ta zauna h'ade da kunna TV dauko remote tai tunda tafara kara value bata bariba saida takai 100' gaba daya g'ida ya dauko da saurin *HAMISU BREKER* yanayi tana bi" "Aisha naso ta kwanta amma karan sautin da Rukky tasa ya hanata' gani bazata iya jure jin karanba mikewa tai tafito parlour kai tsaye gun TV ta nufa' tana zuwa ta dauki remote ta rage karan" "Rukky dake zaune Aisha na ijewa Rukky ta sake karawa h'ade da rike remote d'in a hannunta" "Rukky kirage jarannan sbd inaso NA kwanta amma kara ya hanan" "bazan rageba Aisha' ko kinada ayin yine?" "nike nakeda abin" "to bismillh" "dukawa Aisha tai ta cire soket d'in gaba daya' ta yunkuro zata mike kenan Rukky ta kaimata mari' itama tana tashi ta rama" "daga nan suka kama danbe' garin danbe suka rikito TV dake like a bango suka rikitoshi ya fado kasa" "Zainab tana gama gyara gado ta dibo kayan Hjy da taga suyi datti ta kwashe zuwa inda machine ya nan takami wankesu" "su Aisha danbe sukai sosai babu kowa a gun balle ya rabasu' glass ya soki Rukky ya kafa gashi yai mata yanka sosai' jini ko yace d'an bakayi kabani gun' gani jini ne yasa ta rabu da Aisha tai ta kanta amma badan taji tsoron Aisha ba' Aisha na gani h'aka tai dariya h'ade da shewa tana f'adin yar'iska karamar kabuwa' wlh idan har ina g'idan nan sai kin barshi" "Rukky dake rike da kafarta tace kwarai da gske bance bazan bar g'idan ba amma wlh koda zan bari kafin nabari saina bar ki da tabo a jiki k'uma muzuba mugani nidake shege ka fasa' dan f'ada be karaba' yanzu aka fara" "nima dama abinda nakeso kenan ai" "to shikenan kin kuwa samu" "mayafi tasa ta fita zuwa chemis taje akai mata treatment d'in kafar h'ade da maguguna snn ta dawo" "Zainab saida takarewa Hjy aiki fam snn tadawo bangarensu tana shiga parlour taga TV a kasa h'ade da jini' kamar ta juya taje ta tambyi Aisha amma k'uma sai tafasa tashige d'akin ta" "kowa yana dakinsa babu wanda yasake fitowa parlour har yamma lkcn dawowar zhrdee' yana shiga g'ida yaji gabarsa ya f'adi' innalillahi'wainna' ilalhim raju'un kawai yace snn ya karisa" "yana shiga parlour abu na farko da yai karo dashi shine TV da sauri ya rumtsa ido snn ya b'ude sbd gani yake kamar a mafarkine' gani jini a gun yasashi karisawa da sauri" "cikin ihu ya kwadawa Zainab kira' Zainab dake kan salaya tana lazumi da sauri ta mike h'ade da cewa na'am" "zhrdee yana tsaye a gun yana cewa garin yaya TV dake bango ya fado' k'uma waye yaji ciwo a g'idan?" "ni wlh bansani ba" "wani irin mgnr banza ne kikeyi h'aka' baki g'idan ne' ko k'uma idan nafita kema fita kikeyi" "babu inda naje" "mgnr banza kikeyi' ina zuwa tuku' d'akin Aisha yanufa yana shiga ta nuna tamkar babu komai a ranta da fara'arta ta taresa h'ade da sannu da dawowa" "kema sannu' Dan Allah Aisha su waye sukai mana barna h'aka?' a take Aisha ta daure fuska h'ade da nima bansani ba" "wani irin mgnr banza ne kikeyi h'aka'kowa na tambya sai yace besani ba' to wlh idan ma wani abu kuka kulla wlh sai kun warwareshi" "nan ma d'akin Rukky yanufa' yana shima tafashe da kuka' ganita da kakafa a daure yasashi karisawa ciki da sauri h'ade da rike mata kafar yana tambyar lfy?" "nan ta kwashe komai ta f'adi masa' a fusace yafita zuwa parlour kwadawa Aisha kira yai tafito' itama Rukky fitowa tai" "yanzu Aisha sbd Allah abinda kikai kin kyauta kenan?" "to meye nayi?' aini a yadda nakeso bansamu ba' wlh saita bar g'idan nan tuku zaka samu kwanciyar hankali" "Aisha kin kosan abinda kike f'adi?" "kwarai da gske' ni wlh banga abinso da mugun irin ba zhrdee duk matan dake garin nan karasa Wanda zaka dibo sai Rukky wacce batada aiki sai yawon farka' gata ka tambyeta wanda ya sakota farka ya kamata dashi sanadiyar haka har kotu sunje anan cikin garin gwambe".. " Dan Allah ja banza da kikiya wanda bata wayeba Dan ankamani da farka wani abu? shikeci a yanzu" "kema Ai ba kin auri zhrdee sbd Allah bane wiyane kikaji da k'uma duniya data koyar dake"... " zhrdee dake tsaye jikinsa yai sanyi sbd mgnr da Aisha ta f'adi' wani irin zufa ne suka faso masa wanda shi kansa besaniba" "ido kawai Zainab ta zuba tana kallon ikon Allah" "Aisha tace sai me' alhamdllh duk abinda nayi mijina be taba kamani da yaron aikinsa ba' nafadi na kara nace karuwa" "zhrdee dake tsaye ya daka masu wani irin tsawa a guje yabi Aisha d'aki' itama gudu tasa tana shiga tasawa d'akin ta key tarufe' " itama Rukky d'aki takoma a zcyrta tana mmkin inda Aisha tajiyo wann labarin" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _~*writes*~_ _*gaisuwata gareku anuts' manya magani kanana Allah ya kara basira da daukaka' h'ade da zakin hannu*_ *Halieymarh Ameen (Jalilah)* *Rahma Rufa'i nalele (Likitan zuciya)* *ZZZ makawa ( Tarko)* *(Ciki da gaskiya)* *Fasma niger (sanadin accident)* *Batul adam (amfani soyayya)* *Mineel Musa (kowani bakin wuta* *Safiya Abdullahi Musa hukuma* *Dr Zain (yan' gudun hijira)* *Isa king boy ( nida fatalwa)* *up up up* *brothers and sisters' insha Allah* ________________________________________ *poster's* *Hjy zaliha yola ( mmn ahamed)* *Hjy Hanna* *Isah ramcy journalism* *abdulrahman H2* ____________________ ____________________ *gaisuwa da fatan alkairi' Allah ubangiji ya kara girma da daukaka' ya raya mana zuri'a albarkacin manzon tsira' ya kara bamu zaman lfy da mazajenmu ameen* 5⃣6⃣ "zhrdee yana shiga d'akin Rukky gun ya samu b'akin gado ya zauna h'ade da zabga uban tagumi hannu bibbiyu ido a rufe" "gani h'aka yasa jikin Rukky yai sanyi' a zcyrta tana cewa Allah yasa ba yarda yaida mgnr tsinannircan ba' idan ko yarda yai tofa dole na canza salon takuna' idan ba h'aka nayi ba tabbas ina gab da barin g'idan tun burina be cika ba' duk da nasan ba zama nazo yiba amma bazanso nabar g'idan a irin wnn lkcn ba' idan ko nasake h'akan ya faru to menayi achieving a aurena dashi' dan Allah ma shedani k'uma shikadai yasan abinda nake tafe dashi a zcyrta" "yanzu mafita dayane kwantar dakai sanyi na lallabashi dan yasamo ya saki jiki dashi' daga lkcn ni k'uma sai na f'ada aikin daya kawomi' idan k'uma h'akan besamuba tofa wlh hatta shi daya daukoni ba raga masa zanyi ba saida ayi kan me uwa da wani" "amma k'uma ainane bakar sgegiyarnan tasamo labarina?' ji shegiya yadda take mayarwa kamar anyi a gabanta' lalla ni Rukky inada aiki a g'idan nan' idan ba dagewa nayiba da alama zanbar g'idan nan tun lkc beyiba" "to idan ma nayi ina ruwanta ance mata ni ina zama da namiji daya?' in dama ta kwantar da hankalinta ni ba zama nazo yiba kasuwa kawai nazo naci' amma ga duk alama batasan waye Rukky bab ba' sunana kawai takeji ko nace labarina kawai takeji' idan ba rana daya nasamu na farke shegiya bane bazata gane tana ganganci ba" "gani har wnn lkcn zhrdee be dagoba yasata makewa taje ta dauko masa ruwan sanyi ta kawo masa' yau har kasa ta duka snn ta bashi' koda zhrdee ya amsa ijewa kawai yai batare da yai mgn ba" "gani haka yasa Rukky fashewa da kuka tana f'adin nasha uku na lalace yanzu fa ka yarda kenan' wlh wlh duk abinda tafadi karyane k'uma sharrine kawai amma bansan komai akai ba" "amma idan karyane take maki meyasa a lkcn da take mgn baki musaba?".. " eh nadai amsane kawai sbd nasan ban aikata h'akan ba: k'uma banyi tunanin abin zai maka zafiba amma tunda h'aka ne kayi hkr Dan Allah" "k'uma dama tsoron f'adi maka nakeyi sbd kada nazama me h'ade h'ade k'uma gashi ban dadi da zuwa g'idan ba ace daga zuwana nafara h'ada guri' amma wlh kullum idan kafita kawaye Aisha' ke kawowa g'ida su cika maka g'ida' gashi duk cikinsu babu ta arziki amma idan mgnr yai maka zafi kayi hkr" "himm kawai yace' besake mgn ba mikewa yai ya tube ko wanka beyiba ya kwanta' gani h'aka itama tubewa tai ta kwanta kusa dashi' ta dauka bcc ne yakeyi tafara shafesa da sauri ya cire mata hannu daga jikinsa snn yasake matsawa. " har safe babu abinda ya hadasu' duk da abin ya dameta amma ta matse bata nuna damuwa ba tai masa yadda tasaba yana gama shiri ya dauki jakarsa zai fita har yakai b'akin kofa da sauri Rukky tabi shi h'ade da cewa kawo jakar na rike mata" "fuska a daure batare daya kalletaba yace barshi kawai yai ficewarsa" "bayan zhrdee ya fita kasuwa parlour Rukky ta zo ta zauna shiru shiru babu wanda ya leko yasata mikewa zuwa d'akin Zainab da sallama tashiga lkcn Zainab na shirya *Islaha* hannu tasa ta amsheta snn ta zauna akan cushion din dake gefe bayan ta zauna ne suka gaisa" "bayan ta zauna ne tace eh su mmn Abba kenan wlh ba karami birgeni kikeyi ba".. " Zainab na rike da kayan *Islaha* a hannu tace na mefa? " "gani nayi duk cakwakiyar da akeyi a g'idan nan naki ido kawai kike zubawa" "to Rukky kenan me zance?" "wlh k'uma h'aka nefa 🤔 har kin birgeni wlh' inama da lkcn da nayi aurena na farko nasamu kishiya irin wlh dah babu me jinmu' rashin ganewar mutanine fa zakiga da zaran mijinsu ya kara aure susa amaryan a gaba' bagashi kaddaran da Allah ya doromi ba har anami sharri". " sharri k'uma?" "eh mana jiya bakiji irin sharrin da Aisha ta kantamomi ba" "himm Allah ya kyauta" "wlh sharri nefa' duk mgnr data f'adi bansan komai a kaiba" "to yaya za'ayi Allah dai ya kyauta" "keko mmn Abba duk mgnr da mutum zaiyi saidai kice Allah ya kyauta" "to me zance?" "Allah sarki shiyasa wlh tun ranar dana shigo cikin g'idan nan babu wanda ya kwantamin a rai irinki' gskya kinada hkr dayawa daga ganima irin wnn hkrin nasan zaman hkr kikeyi a g'idan nan' ga halamuma ya nuna dubi yadda idonki duk suka zurma' duk da bandade da sanankiba amma alama ya nuna zaman hkr kikeyi a g'idan' shiyasa nazo idan har zaki yarda inaso mu h'ada kai dake mukoma tamkar uwa daya uba daya' mukashe mu rufe batare da wani ya saniba ko Mijin da muke zamansa ba lallane yaji sirrinmu ba balle wata banza kishiya' mu zauna mu rungumi ya" yan"mu batare da wani yaji kanmu ba" "Zainab dake zaune mikewa tai ta kwanta h'ade da cewa to naji" "yawwa wlh har naji dadi' muhada kanmu mu zauna abinmu babu ruwanmu da wata shegiya" "sbd Zainab batason mgnr rufe ido tai kamar me bcc" "wlh kinga koba komai nasamu a bokiyar shawara.... " au mmn Abba Ashe bcc kikeyi" "matsewa Zainab tai h'ade da cewa wlh bcc ne ya rufeni" "to bari naje da'ita kidan samu ki rintsa" "a'a kawota itama bcc takeji' mika hannu tai' Rukky ta kara kankame yarinya' gani haka yasa *Islaha* kuka'a dole ta mika mata yarinya snn ta fita" "tana fita sukai karo da Aisha tafito kitchen' babu wanda ya tankawa wani kowa yai harkan gabansa' Rukky na fita Zainab ta rufe d'akin' ta' dama sbd Abba ne take barin kofa a b'ude koda yadawo daga d'akin Hjy saidai ya tuwa ya shigo kawai basai yaita wahalar knocking ba" "cikin dare suna kwance har zhrdee ya h'au jikin Rukky da ya tuna da mgnr Aisha sauka yai ya kwanta' Rukky ta tashi zaune tace lfy me k'uma ya faru' ko har yanzu baka yarda dani bane?" "ba h'aka bane Rukky' a gskya bazan boye makiba zcyta har yanzu tana wasuwasi a kanki' inaso kiji tsoron Allah idan ban gankiba Allah ya ganki' k'uma kada kimin karya' nafison ki fadimi gskya' tsakaninki da Allah da gske ne kin aikata abinda Aisha ta f'adi koko sharrine?" "saida Rukky ta marerece snn tace wlh na rantse da Allah bantaba sani kowani dah namiji ba idan ba wanda na aure ba sai k'uma kae" "duk tana mgnr ne tana hawaye" "kin rantse da Allah fa kikace Rukky?' idan har karya kikaimi kinsan bazan yafe makiba ko?" "wlh ba karya nayi ba" "to shikenan share hawayenki matsonan mu kwanta" "jin h'aka yasa Rukky harda shakshekar kuka" "jawota yai ya rungumeta yana f'adi ya'isa haka".. "da safe b'akin Rukky har kunni tunda sassafe ta tashi hadawa zhrdee breakfast' lkcn yana bangaren Hjy tunda ya dawo daga masallaci shida d Abba ya shige be fitoba' zama yai a d'akin Hjy shida Abba da'ita kanta hjyn suna hira' Abba karami da yake yau a d'akin Hjy ya kwana har dashi ake hiran'duk da bayan ma'anar abinda suke f'adi bane amma yana jikin Abba' kamar da batai masa tsauriba idan Abba yafadi shima saiya f'adi" "Rukky na gamawa wanka tasha tai kwalliya cikin kananu kaya' parlour ta fito ta zauna tana jiran yafito' Zainab na b'ude kofa sukai ido biyu da Rukky' gani *Islaha* a hannun mmnta a guje Rukky ta mike zuwa gun Zainab tana f'adi oyoyo my daughter Aisha dake dakinta taajin h'aka ta b'ude kofa ta tsaya daidai b'akin kofarta tana kallon" "Zainab da akeyi dan ita galala ta tsaya kallon Rukky' Rukky na isawa hannu ta mika zata amshi *Islaha* *Islaha* na gani za'a amsheta kankame mmnta tai taki yarda" "h'aba my daughter kada kibari su Oh Ohooo suyi mana dariya mana' da karfi ta fisgota daga hannu mmnrta*Islaha* na gani h'aka ta h'au bori tana wuntsile wuntsila' garin h'aka ta finciko a cucumazan da Rukky tai ya f'adi a kasa" "gani kan babu komai yasa Aisha kwashewa da dariya tana f'adi andaiji kunya ashema duk uban a cucumazan da akeyi shegiyar kan babu komai abu kamar kwakwah" "itama Rukky dayake ta iya bariki faskewa tai tacewa Zainab amsheta na gyara a cucumazana dashi na rudi bbnki yarinya" "Zainab na amsar yar'ta takoma daki h'ade da rufe kofar" "wlh andaiji kunya karuwa da kan kwakwah" "dadin abudai uban watama yazo nima daidai banba dakai bane balle bori ya h'au" "badai ubana ba saidai ubanki.... " hango zhrdee ne ya hanata karisawa da sauri takoma cikin dakinta " "zhrdee yana shiga daki Rukky ta h'ada masa ruwan wanka' kafin yafito ta kawo masa abin breakfast' baya gama shiryawa ya karya agurguje ya fita' tana rungume dashi leka d'akin Zainab kawai yai suka gaisa snn ya leka d'akin Aisha itama suka gaisa snn ya fice' Rukky na rungume dashi har b'akin mota" "yau girki yadawo gun Aisha' tun azahar take kitchen tana aikin abinci sbd yanzu ba dadewa yakeyi a kasuwar ba' kafin biyar na yamma Aisha tagama komai tai wanka ita da yara around six o'clock zhrdee ya dawo g'ida Zainab dake zaune a parlour tace kadawo?" "eh kawai yace batare daya tsaya kallonta' itama gani h'aka yasata daukar yaranta suka koma d'aki' yana shiga Aisha ta taresa da fara'arta ta rungumesa, shima murmushi yai h'ade da rungumeta tai masa sannu da zuwa bayan ya tube ne ta h'ada masa ruwan wanka har takawo abinci yace a'a tabarsa sai ya dawo daga masallaci snn zanci" "to shikenan kawai tace' har zata kauce zhrdee ya rike mata nnu ya jawota jikinsa Aisha tana zaune a jikin zhrdee lkcn yara duk suna bcc' zhrdee yace yawwa Aisha dama wata mgn nakeso muyi dake" "na mefa?" "Dan Allah Aisha wani irin rayuwa kikeso ki daukarwa rayuwarki".. "me k'uma nayi?" "babu abinda kikai' amma wlh kwata2 banajin dadi h'aka' idan banda abinki wayece maki ana yarda da kawa" "wacce kawa k'uma zhrdee?" "cemifa akai idan nafita tara kawaye kikeyi" "iji waye ya f'adi maka h'akan?" "ni ba f'adi nace kiyi ba' tambyarki kawai nayi" "mikewa tai h'ade da cewa ina zuwa' fita tai zuwa d'akin Zainab' Zainab na zaune Aisha ta shigo da sallama Zainab tace Aisha lfy?' tunda ba shiga dakinta takeyi ba" "zhrdee ne yake kira" "zhrdee k'uma?" "eh" "Allah yasa dai lfy' mikewa tai tace muje' Aisha na gaba Zainab tana baya' suka fita zuwa parlour" zhrdee yanajin muryansu a parlour ya mike ya fito shima' gani zhrdee ya fito yasa Zainab samugu ta zauna' shiga d'akin Rukky Aisha tai tace fito tsohowar manafuka' jin h'aka yasa zhrdee mikewa yana kiran Aisha' Rukky tace babu inda zani" "wlh sai kin fito" "Aisha meye h'aka ne kikayi sbd Allah?' waya kizo ki fita mata a d'akin" "wlh babu. inda zani sai tafito" "nima k'uma babu inda zani dan baki isaba wlh" "Aisha wai badake nakeyi ba bane' ko ban isa dake bane?" "ka'isa amma wlh saita fita" "idan har na'isa dake to kifita a dakinga" "naji zan fita amma wlh itama tafi" "naji fita dai" "Aisha tana fita zhrdee yace kema shige muje" "Zainab na zaune idan ta tanka kasa ya tanka" "Aisha dake tsaye gefe tace wacce mafukanne take idan zhrdee ya fita ina tara kawaye?" "zhrdee dake tsaye yace Aisha wai meye kikeyi h'aka ne?" "karaf Rukky tace nice nan na f'adi" "ai dama nasan sai ke bakar alguguma' asirine dai bazan fasa tona makiba" "himm Aisha kenan' yadda kikasan tawa haka nima nasan naki" "idan kin sani saime?" alhamdllh duk abinda zaki f'adi bana shayi sbd nasan bantaba karuuwanciba mijina be taba kamani dakwartoba' nafadi na kara karuwa kawai" "tsawa zhrdee ya daka masu snn sukai shiru" "juyowa yai gun Zainab yace Zainab" "na'am" "Dan Allah inaso ki fadimi gsky' Dan Allah idan bani suwaye suke zuwa gun Aisha?" "nima bansani ba" "kamar yaya baki saniba?' idan nafita kema fita kikeyi komai?" "babu inda nake zuwa wani lkc ina bangaren Hjy ne' wani lkc k'uma ina d'aki kwance" "ina zaki sani tsohowar manafuka alguguma' ina zaki iya f'adi tunda bakinku daya ne' banza mara zcy wanda batasan right dintaba' Allah ya rabani da zcy irin naki wanda batada kima da mutunci a gun mijin da kike zamansa' zamanki dashifa saidai yai maki ciki ki haihu".. " jin h'aka yasa Zainab mikewa tabar gun h'ade da fashewa da kuka " "hannu zhrdee yasa ya dauke Aisha da mari" "duk da h'aka b'akin Aisha be mutuba taci gaba da cewa Allah ya rabani da auren cushe' mutum dashi da kashi daya yake a gun miji'... " sake dauketa da mari zhrdee yayi " "gani h'aka yasa Rukky kwashewa da dariya' juyawar da Aisha zatayi ta haye Rukky da danbe' zhrdee yayi iya kokarinsa wajan gani ya rabasu amma ina" "kusan ance danbe sa'ane ba karfi bane' da Allah yabawa Aisha sa'a tahaye Rukky babu abinda take hari sai biraziliya kulu da aka cuko dashi' tunda tasamu ta camkoshi bata sakeba saida ta tugeshi kan Rukky yadawo kwankwarankwa saidan abinda baza'arasa" "a lkcn zhrdee yasamu ya babbaro Aisha daga Rukky' Aisha taci gaba da cewa karuwa mai kan kwakwa" "gani h'aka yasata shiga kitchen ta dauko wuka knife a guje tayo Aisha' gani h'aka yasa Aisha sa gudu' shima zhrdee a guje ya bita itama Rukky a guje take bin Aisha" "shan gabansu zhrdee yai ya tsare b'akin kofar Aisha' Rukky tana zuwa tokari ya kaimata' wukar ya f'adi duk da h'aka kokarin shiga d'akin takeyi' zhrdee ya dauketa da mari snn yaci gaba da tokarinta" "duk da h'aka bata daddara ba kokarin kutsa kai takeyi" "gani h'aka yasa zhrdee rufeta da duka kamar Allah ya aikoshi gareta' a guje Rukky ta nufi dakinta h'ade da cewa wlh sai nayi ajalinta" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 5⃣7⃣ "gani ta shaga daki yasa zhrdee shigewa d'akin Aisha' h'ade da rufe kofar da key' ko kallon inda take beyiba amma ya shige toilet yai alwala sbd anriga an idar da sallar isha' duk yana g'ida gun rabon f'adi" "yana gama alwala fitowa yai ya fara sallah' itama mikewa tai taje tayo alwala tazo ta fara sallah' suna idar da sallah zhrdee yace Dan Allah ki tashi ki kawomi abinci' masi fanfiyar bazan kawai" "batare da ta tanka ba ta mike taje ta dauko masa ta kawo" "yanaci yana hararanta'gani h'aka yasa taje ta kwanta ita da yara' shima yana gamawa kwanciya yai' a rigingine tunani kala kala yakeyi' gani yai shiru ko motsi bayayi saidai yayi Dan karami tsaki kawai" "Aisha tace zhrdee lfy?" "banza da'ita yai" "zhrdee da kaifa nakeyi" "kinfi kowa sani' yanzu sbd Allah Aisha irin sakaiyar da zakimi kenan?" "na me k'uma?' me k'uma nayikallo duk wani masifa idan ya tashi a g'idan nan kece' sbd da Allah meye Rukky tai maki h'aka da har kika tsaneta?" "wani irin kallo tai masa h'ade da murguda baki tana cewa na dauka wata mgnr arziki ne Ashe mgnr wann banzan ne ma".. " Rukky yan ne banza Aisha?" "wlh banza ma yafita a guna' banza kawai karuwa me kan kwakwa". "wai ke Aisha meyasa kike kiranta da muguwar sunanga h'ak?" "wlh na rantse da Allah karuwa ce' da aurenta fa takebin maza' ba abin mmki bane ma idan aka ganta da HIV" "kai Aisha abin har ya kai ga h'ak?" "nidai Dan Allah Aisha nafiso kiyi hkr Ku zauna lfy"... " dawa?!!! Allah ya sauwake' wlh idan har kaga gidanka ya zauna lfy to wlh tabar gidan nan". "🤥 Aisha!!!! " meye ne? "to wlh baki isaba daga ke har ita zamana kukeyi' babu wanda ta isa ta kori wata tunda duk kana karkashi nane Dan h'aka wlh bazan lamunci wani iskancin a g'ida naba". "aham saifa kayi' nidai abu daya nasani wlh sai tabar g'idan tunda ba g'idan ubanta bane' shegiya karuwa kawai" "Dan Allah kimi shiru me shegen b'akin tsiya' inda ba barta dan daba sai waniki k'uma ba keba ba" "Allah ya sauwake Ai ko danzu sbd tazomi ba shiri ne amma wlh yanzu a shirye nake a kowani lkc ina jiranta" "shiru zhrdee yai yana kallon b'akin Aisha' gani ta nace yasashi cewa Aishata kinga zo kiji wata mgn' jayota yai jikinsa sbd a lkcn yara duk suyi bcc' a hankali yake bugun cikinta" "aishata kenan Dan Allah a ina kika samo irin wnn labarin h'aka aishata?" "bazan f'adi ba' sbd koda na f'adi maka nasan ba yarda zakai ba" "h'aba matata ta kaina me zai hana" "himm kasanine?' ina ramlat dina class mate dinmu?" "wacce kenan fa?" "wacce ranar candy dinmu tace saidai ta shiga tsakiya muyi Pict da'ita" "OK yanzu na tunota" "kasan itama tayi aure Ai" "eh h'aka dai naji" "yawwa to kanwar iwar mijinta take kishiya mmn Rukky ai" "to sai k'uma akayi yaya" "a nan ne naji labarin duk abinda Rukky ta aikatawa mijinta" "kae fa Aisha kinsan yadda duniya take' banaso kananar mgn" "wlh na rantse da Allah' k'uma idan kace karyane kaje ka binciko gskya kaji" "himm Aisha kenan" "Allah da gske k'uma har yanzu tsohon maigidanta nimanta yakeyi' be gantaba k'uma wlh har yanzu ba hkr yayi ba' inda yasan tananan da yazo ya kamata" "kaifa Aisha sbd me?" "ance sata tai masa' a lkcn da asirinta ya tonu suna cikin shari'a cikin dare daje da wasu maza wanda besan suba suka daure Mijin suka kwashe masa dukiyarsa' k'uma fa bakasan wani abuba da makwabcinsu take kwartanci".... " ke Dan Allah nagaji dajin tatsuniyar gizo da koki" "au h'aka kace?' to shikenan Ai ba'awa me rai karya" "eh naji dai' tashimi a jiki haka k'uma" "Zainab dake daki taci kuka har tagaji' amma a ganita zhrdee ne yake f'adi masu irin wnn mgnr" "da safe kuwa koda da zhrdee ya shiga gaisawa da'ita fuska a daure take amsawa ko kallensa batai ba" "yana fita d'aki Rukky ya shiga zama yai a b'akin gado snn suka gaisa' har Rukky ta mike yace dawo ki zauna' dawowa tai ta zauna snn yace Rukky" "na'am" "meyasa kikaimi karya?" "karyan me k'uma?' inace mgn yaringa ya wuce" "ki saurari mgn da zanmaki' k'uma inaso ki fadimi gskya" "to' ina sauraranka" "meye hadinki da makwabcin tsohon mijinki" "wane k'uma" "kifi kowa sani" "rau'rau' tai da ido snn a take tai creating karya" "eh'to kasan mijina dan siyasane to shine wata rana baya gari yaje yawaon siyasarsa cikin dare barayi suka shigo g'idan" "ido kawai ya zuba mata' gani tayi shiru yasashi cewa ina sauraranki" "shine inajin motsin shigowarsu a guje nabi ta kofar baya na f'adi g'idan makwabta shine nasamu nayi shine na samu na tsira" "Rukky inaso kiji tsoron Allah" "kuka tasa tana cewa wlh na rantse da Allah idan ma gani kake kamar karya nakeyi to bari nakira mmta ka tambyeta" "cikin kuka ta mike ta dauko wayarta har tafara dealing number".. "da sauri zhrdee ya amshi wayar yana f'adi daga mgn k'uma sai kice zaki kira Hjy?" "tana sheikshekar kuka tace gani nayi kamar baka yarda daniba". "" a'a ba h'aka bane' nidai abinda nakeso dake shine Dan Allah duk abinda zakiyi kiji tsoron Allah" "insha Allahu" "yawwa k'uma Dan Allah Rukky kiyi hkr akan abinda ya faru jiya tsakaniki da Aisha kinji" "himm kawai tace" "Dan Allah Ai nace' ki bita Ku zauna lfy pls".. " nabitafa kace? " "eh mana" "sbd zamanta nakeyi a g'idan ko me" "ba zamanta kikeyi ba' amma kinsan itace babbanku ko" "Allah ya saukake wlh' ni da ita Ai yanzu muka fara shege ka fasa' k'uma wlh dub abinda taimi saina rama" "ban'isa dake ba kenan?" "ka'isa amma fa saina rama". " to shikenan wanda ya fasa' fita yai zuwa d'akin Hjy" "yana fita zama Rukky tai a b'akin gado a zcyrta tana cewa itanane bakar shegiyar ga take samu cikakken labarina h'aka' kodai wani take sawa yake mata bincike a kaina?' amma ba komai zanyi maganita na gwammace sanadiyar haka nabar g'idan' Dan naga kamar bayason laifinta" "Aisha fitowa daga dakinta zuwa kitchen zata h'adawa zhrdee breakfast' tana shiga Rukky tajin motsi a kitchen itama ta fito ta tsare b'akin kofar kitchen d'in batare da tai mgn ba' duk da Aisha ta ganta da gefen ido' banza tai da'ita kamar bata ganta ba' bari tai saida tazo fita snn tasa hannu ta igijeta snn tasa kai" "mikewar da Rukky fisgo Aisha tai sukaci gaba da danben su" "Abba yana fitawa daga d'akin Zainab Aisha ta ture Rukky kadan yarage ta f'adawa Abba' Allah yasa Zainab tana biye dashi itama turesu tai suka f'ada can gefe snn yaja d'anta suka koma d'aki' zhrdee yana d'akin Hjy amma hankalinsa be kwanta ba' gani faduwar gaban yai yawa yasashi mikewa ya baro d'akin" "yana isowa ganisu yai suna b'akin aiki' be tanka masuba d'akin Aisha ya shige ya dauko belt yazo ya fara zuwa masu' Rukky na gani ita yafi duka yasata rike belt din' babu yadda beyiba akan tasake amma taki' itama k'uma Aisha' ta h'aka ne tasamu cin galaban Rukky" "duk abinda sukeyi Zainab na d'aki tana jinsu' Aisha tana daina dukan Rukky ba' zhrdee dake tsaye bemata mgn ba saidai ma kokarin kwace belt dayakeyi' zcyr daya dibi Rukky sake belt din tai snn tasa hannu ta hankade Aisha' Aisha taje ta f'ada a jikin kofar Zainab kofa ya b'ude' dama ba key tasaba turawa kawai tayi" "Zainab dake akan cushion da sauri ta juyo gani Aisha ne tsaki kawai tai h'ade da juya mata bayan' Rukky taso bin Aisha tasamu ta hayeta amma zhrdee ya hana' kukan kura tai ta kwace tayo kan Aisha' Zainab na gani h'aka mikewa tai da sauri hannu tasa ta hankade Rukky taje ta hadu da cushion d'in dake parlour, Aisha Dale yunkirin bin Rukky Zainab ta dauka shigowa zatayi d'an samo mafaka hannu Zainab tasa ta ture aishan itama snn tasa key ta rufe kofarta" "tura Aisha da Zainab tayi Aisha taje ta f'ada jikin Rukky' Rukky dake kokarin mikewa tayo kan Aisha h'aka ta sake komawa da karfi ta buga kai a taiss' da sauri zhrdee ya finciko Aisha zuwa d'akin' gani h'aka yasa Rukky juya f'adin kan Zainab' zagi inda take shiga banan take fita ba' duk abinda Rukky tafadi sai Zainab ta meda mata' " jin haushi yana kama Zainab tace Dan Allah ja kibani gu wawiyar banza alguguma da kikiya' wanda yakamata kiyi bazakiyi sai Wanda be kamata ba' a gabanafa har karuwa aka kiraki dashi amma babu abinda kikayi" "b'ude b'akin Rukky tace uwar kice karuwa banza mara tushe mara asali karya mara zcy' wanda dake da babu duk dayane a g'idan mijin da kike zamansa besan darajanki da mutujciba' jakar banza kawai wacce batasan right din taba" "Zainab tace uwarkice jaka dabba' wlh Rukky duk abinda zakiyi bazanga laifinki ba daliliko shine gaba daya rayuwarku da haram aka ginashi" "ubanwa yace maki h'aka?" "ubankine shegiya karuwar banza bara lasisi" "ba ubana badai saidai ubanki Musa me tunbi haram".. " Zainab yana fitowa yace ya'isa haka" "duk da h'ak basu bariba" "Zainab ke banaso nasake jin bakinki" "gani Rukky bata daina zagan mata iyayeba yasa itama bata dai meda mata ba" "da haushi ya kama zhrdee kafa yasa ya bige kofar ta b'ude yana shiga ya h'au Zainab da duka" "Zainab tayi kokarin kwacewa amma takasa shikuma be daina dukantaba gani zai mata illa yasata kamo masa gaba ta murde yana duka h'ade da cewa bazaki sakeba' itama k'uma Zainab tanaja tana kuka' Abba danwarsa suma suna kuka suna mmnsu duk inda tabi da zhrdee' duk da jikin zhrdee yai sanyi sbd ja da take masa bana wasaneba amma bedaina karfin halin dukanta ba" "saida ta tabbata koda ta sakesa babu abinda zai iya snn ta sakesa a guje ta rarumi hijab da yaranta tabar g'idan' tana sakewa wani irin zufane ya karyo masa har juwa yake gani' gu yasamu ya zauna tuku" "a ranar kasuwan da bejeba kenan' da kafa Zainab tai ta tafiya har ta'isa g'idan su' tana shiga parlour sukai karo da inna gani yadda jikinta yai yasa inna yankewa da salati' itama Zainab dake tsaye kuka kawai tasa' inna ta kamata suka zauna babu irin tambyar da inna bataiwa Zainab ba amma babu abinda Zainab tace sai kuka' gani haka inna tace ta shige ciki ta kwanta" "zhrdee yafi minti goma kafin ya'iya tashi'saida hankalinsa ya dawo jikinsa snn ya mike parlour ya koma ya kwanta' lkcn babu kowa a gun" "suna tunda sukaga h'aka babu wanda yasake koda tarine a g'idan" "shiru shiru Hjy bataga *Akbar* ya shigo gunta ba har dare k'uma ba h'aka yasaba ba' sbd mafi yawanci lkta ma zamansa a gun Hjy yafi yawa' mikewa tai da kanta tazo dubashi' tana leka d'akin h'ade da kiran sunansa taga daki wayam babu kowa' dawowa parlour tai snn ta kwadawa zhrdee kira lkcn yana dakin Aisha ya kwanta. " zhrdee yana fitowa Hjy tace ina Zainab taje h'aka har dare sbd Allah' idan ma uguwa taje tunda kaga dare yayi me zai hana bazakaje ka dauko ta' ka barta ta dawo da kanta k'uma kasan tanada yara" "kan zhrdee a kansa yace ba uguwa tajeba" "kamar yaya?" "nima bansan inda tajeba" "wani irin mgnr banza kakeyi h'aka" "tofa Hjy dan suyi f'ada da Rukky ni k'uma nayi mata f'ada shine tawuce g'idan su" "shine baka bitaba" "kam Hjy ai babu inda zani' tunda bada izinina tafita" "h'ak ne k'uma fa' kayi gskya to Allah ya taimaka" "juyawa tai ta koma bangaren ta' tana tafe tana mgn" "shima komawa d'akin Aisha yai suka kwanta" "bayan Abba yadawo suna hira da Hjy tace Alhj yanzu sbd Allah abinda zhrdee yai ya kyauta kenan?" "name k'uma Hjy?" "gani banda yaronga ya shigo bane tun safe shine har dare naje dubashi naga babushi babu uwarsa" "shine baki tambyi son inda tajeba' nasha f'adi masa yadaina bari sunakai dare a uguwa" "himm Alhj kenan' koda na tambyi zhrdee wani irin mgnr banza yake fadimi' wai suyi fadane da Rukky shine ta wuce g'idan su' kaduba fa sbd Allah duk irin hkrin yarinyarnan amma saida suka kureta" "a'a gskya abu beyi dadi ba" enafa yaga dadi" "babu komai zansamesa nayi masa mgn akan yaje ya dawo da'ita" "to shikenan Allah yasa yaji naka" "Bbn Zainab yana dawowa bayan ya huta inna take sanar masa Zainab tadawo g'ida" "lfy ta dawo g'ida?" "wlh nima bansani ba" "wani irin baki saniba Hjy?" "to Alhj wlh babu irin tambyar da banmata amma taki mgn" "kiromi ita" "to kawai tace snn tamike taje kiranta' tate suka dawo" "dukawa Zainab tai cikin ladabi ta gaidashi snn yace lfy Zainab kika dawo g'ida?" "kan Zainab na kasa tace babu komai baba" "a'a Zainab idan kinsan akwai matsala kifadi" "babu komai Bb gajiya kawai nayi da auren" "dukkansu dariya sukasa' snn yace Zainab kenan' antaba gajiya da aikin ladah?" "ba'a taba ba amma nikan Allah yagani na hkr" "Zainab' " na'am Bb" "kinfi kowa sani bazan yarda ki zauna a g'idan nan bako?' dan haka gara kitashi kawai ki dauko kayanki na medaki" "Bbn kasan tunda nake dakai bantaba bujirewa mgnrka bako?" "kwarai da gske" "Bb yau kam saidai kaya hkr sbd babu inda zani' idan k'uma ka matsami wlh barin garin zanyi" "barin gari k'uma Zainab?" "shiru Zainab tai" "Bb yace to tashi kije daga ciki" "babu yadda iyayen Zainab basuyi ba Dan tafadi masu abinda ya hadasu amma Zainab taki' daga karke kyaleta sukai" "kwanan Zainab uku zhrdee yai sallama a kofar gidan su ko ciki be shigaba' gani mamy kanwar Zainab tana dawowa daga sch zhrdee ya kirata yace taje ciki tacewa Zainab tabashi yaransa" "mamy na shiga ta fadiwa Zainab' Zainab najin h'ak ta mike taje ta dauko yaran tabata takai masa' zhrdee yana amsansu ya sasu a mota sai g'ida" "gun Hjy ya kaisu' lkcn Hjy na sallah zama yayi yana jiran tashafa" "tana shafawa tace wanga yaran k'uma fa?" "kwaso yarana nayi" "waye zasu rikesu?" "Rukky ne zanba mawa" "wlh na rantse da Allah idan baka kwashi yaran nan ka medasu gun uwarsu ba ranka sai yayi mummunar baci' wayar nan she gun yara alzaluman ne zaka basu yara rike?' kada ka bacemi da gani a gaba ba" "mikewa yai a sanyaye ya kwashe su ya medasu gun uwarsu" "gidan zhrdee kullum cikin lalura na yau daban na gobe daban" "Zainab nada sati uku su Hjy da Abba sukaje bawa iyayenta hkr' Alhj Musa yace aini babu abinda kukaimi amma dai Zainab ce bazata koma ba' idan har zhrdee yanaso ta koma sai yazo da kansa ya bata hkr h'ade da alkawarin bazai kara walakantami yarinya ba'sbd yanzu idan nabaka ita kuka komai bazaisan yayi kuskure ba" "Hjy tace babu komai k'uma ko nama dana haifesa na goyi bayan h'ak" "nan dai sukai sallama *Akbar* yasa kukan zaibi Hjy' Hjy tace ya zauna zata dawo ta daukesa sutafi g'ida" _*~BAYAN WATA BIYU~*_ tun safe sukewa juna gani gani' Aisha ta dorawa yara ruwan plast wanda take dama masu kunu' Ashe Rukky tana kallonta' Aisha tana fita Rukky tazo ta zubar da ruwan h'ade da kashe gas d'in " "Aisha tazo juye ruwan taga gas a kashe nan ta h'au f'ada' tana f'adin wacce shegiyar nan ta zubarmi da ruwa k'uma ta kashe gas d'in?" "Rukky tace nice" "Ai dama nasan saike shegiya karamar yar'iska karuwa" "da'kyau kamar kinsan rana irin ta yau nake jira" "kekika sani shegiya kawai" "uwarkice shegiya" "uwankidai wlh karuwa nafadi na kara k'uma wlh sai kinbar g'idan" "kwai da gske zanbar g'idan amma saina barki da tabo k'uma bari kigani" "zhrdee dake d'aki yanajin h'ak da sauri yafito" "wuka Rukky ta dauko gani h'ak yasa Aisha gudu' itama Rukky na binta' a guje zhrdee yasha gaban Rukky itama tariga tayi setting wuka h'ade da rufewar ido' yana shiga tsakiyarsu Rukky ta d'an na masa wukar a ciki" "gani h'ak yasa Aisha tai tsayawa' gani ta tsaya yasa Rukky ciro wukar daga cikin zhrdee ta d'an nawa Aisha itama a ciki" take zhrdee ya f'adi sumanme' itama Aisha binsa tai' jini kuwa yace idan bakayi kabani gu" "d'aki Rukky ta koma ta h'ada kayanta ta kara gaba" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRIRES F. O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 5⃣8⃣ "daga Aisha har zhrdee sumewa sukai' jini kuwa sai faman rushing yakeyi kamar anyanka akuya" "Hjy dake bangaren ta haka kawai taji gabanta yai mumanar f'adi' babu abinda take anbato sai innalallahi'wainna'ilaihim'raju'un" "shahida da shahid duk su tashi' garin kokuwar sauka daga gado shahida ta f'adi' nan ma takara sa wani kuka" "har a lkcn hankali Hjy be kwanta ba' sake sake takeyi kala kala a zcyrta' h'ade da tambyar kanta kodai wani abune zai faru da'ita yasa hankalinta keta faduwa' gani zaman d'aki ba zaikai mataba yasa tamike tana zagaye g'ida h'ade da tasbihi a zcyrta" "lungu da sako na g'idan saida ta leka har tayo kwantar parlour su Aisha' wata zcyta mezakije kiyi a bangaren yara?" "juyawa tai zata koma wata zcyr tace a'a Hjy gara dai ki leka" "juyawa tai ta shige bangaren su Aisha' tun daga nisa take hango gangarowar jini kamar anyanka rago' salati tasa jiki yana rawa ta karisa gun" "dukkansu ganisu tai kwance Aisha na jikin zhrdee duk babu me nimfashi a cikinsu' cikin dimuwa da tashi hankali ta dago Aisha' daga jikin zhrdee itama ta shinfida mata ta a kasa' a guje ta juya takoma bangarenta ta dauki waya' Abba ta kira' cikin Sa'a dugun farko ya daga wayar h'ade da sallama" "cikin kuka ko amsa sallama batai ba cewa kawai tai Alhj g'ida babu lfy" "abirkice Alhj ya mike yana salati' kafin yace komai Hjy ta katse wayar' Allah yasa lkcn Shamsudee yashigo gun Abba sbd akwai mgnr da zasuyi dare' cikin gigita Abba yace Shamsudee muje g'ida kawai" "gani halin da Abba ke ciki yasa Shamsudee amsar key din motar Abba suka dauki hanyar g'ida';duk su biyu kowa da abinda yake aiyanawa a zcyrsa" "suna isa bangaren Hjy suka nufa'batare da subi ba cikin parlour su Aisha ba' suna shiga sukaga batanan a gun' jugun kawai Abba yai batare daya uffan ba' Shamsudee ne yafita zuwa kitchen ko tana gun' gani batanan yajuya ya dawo bangarenta sbd yasan bata shiga bangaren su Aisha" "itako a lkcn tana kan su Aisha da zhrdee jingine jikin bango tana faman sharban kuka' sbd ta dauka mutuwa sukai' ba'ita ba duk wanda zai gansu a lkcn dauka zai gawane ke kwance" "Shamsudee yana komawa yace Abba banganta ba" "batare daya tanka ba waya yasake daukowa ya kira numr ta' Hjy na dagawa cikin kuka tace kushigo kawai zhrdee zhrdee' jin h'ak yasa Abba fita a guje yana f'adin me yasamu son d'in ne?" "kafin Abba ya'isa gun yya Shamsudee yariga shi' ganisu kwance yasa yya Shamsudee fasawa wata irin kara yana kira know brother' f'adawa yai kansa yana jijjigashi' shima Abba mutuwar tsaye yai yakasa karisowa gun balle yaga abin b'akin ciki da takaici' hawaye kawai wasu kebin wasu Abba keyi" "rungume zhrdee yya Shamsudee yai yana faman kuka'hjy take tsaye itama kuka kawai takeyi'gani yadda yya Shamsudee yake jijiga zhrdee ne yasa Abba karfin hali yazo ya amshesa ya shinfida shi snn suka koma kan Aisha' itama disem bata ko motsi' cikin kuka Abba yace Hjy kina ina aka halakamu h'ak?' wayene yai mana h'ak?' k'uma me mukai masa?" "cikin kuka yya Shamsudee ya ciro wayarsa ya kira yya Nurudee ya sanar masa rasuwar zhrdee" "what yace' shikansa besan lkcn daya fasa da kuka ba" "duk mutani dake gun sai faman cewa suke lfy?' h'ade da yaran shagonsa" "batare daya tanka ba mota kawai yashiga zuwa g'ida' daga yaran shagon har abokan binsa sukai zuwa g'idan" "suma yaran shagon zhrdee dana Abba h'ade dana yya Shamsudee duk labarin rasuwar zhrdee ta riskesu" "suma duk rufe shagonar sukai zuwa g'idan' a nan nema Bbn Zainab yaji labarin rasuwar' saida ya sanar g'ida snn yanufi gun zana'idar" "cikin kuka Hjy take f'adin wlh bansaniba Alhj nima ina bangarena' bansan ko wayeba Alhj' shikenan zhrdee" "Abba yace ina Rukky take?' "a lkcn ne Hjy ta tuno da wata Rukky ya' da sauri suka nufi dakinta maybe ita a d'aki aka sameta akai mata nata" "gani kofa b'ude suka kutsakai dukkansu su uku'wayam sukaga daki babu Rukky babu akwatin kayanta' " cikin mmki Hjy tace Alhj me zangani haka' kodai kidnapping dinta sukai" "shiru Abba yai sbd tunani da yakeyi h'ade da kokonton abinda zcyrsa take raya yasa" "yya Shamsudee yace wani irin kidnapping Hjy' kidnapping ne shine harda ja kan kayanta' ni wlh ma nafara zarginta' idan ba itace ta aikata to turowa tai aka aikata' "shiru Abba ya a zcyrsa yana cewa yanzu na rasa son kenan?' yanzu mutuwa yai kenan' me nayiwa mutuni da suka aikatamin irin wnn dayar aiki?" "Abba yana f'adin haka ne sbd duk cikin yaran da Allah ya bashi zhrdee yafi jin kansu' a rayuwar zhrdee bayaso yaga su Abba da Hjy su shiga wani hali saidai idan be dashi'koda be dashi sai yayi yadda yai ya biya masu bukatansu koda ba duk ba' in bandama yanzu daya tara iyali amma be hanasa yiwa iyayensa" fita Hjy tai daga d'akin Rukky zani ta dauko' yya Shamsudee ya amsa ya rufe zhrdee har ya juya kan Aisha can ya hango babban yatsar hannu zhrdee yai motsi' ganisa yai kamar gizone goge ido yai Dan tabbatar da gskyr abinda idonsa ya gane masa' still hannu yasake motsi' a guje yya Shamsudee ya yaye masa zani h'ade da sa wata uwar ihu yana f'adi be mutuba Abba wlh be mutuba Abba" "yya Shamsudee be rufe bakiba su yya Nurudee suka shigo' jin kamar be mutuba yasa Nurudee ciccibar zhrdee zuwa mota batare daya cewa kowa kome ba' jama'ar da suka shigo suka taimaka masa' itama Aisha akace a h'ada da'ita' yya Nurudee gudu yake subsea kamar Wanda zai tashi sama" "suna shiga hospital dict yana ganisu yace bazai amshesuba sai sun kawo statement of of police babu irin rokon da basuba amma suki yarda su tabesu sbd rules d'in kasa ne" "dole saida akaje aka dauko police sukai cike ciken da zasuyi snn doct ya tabesu' bayan ya gama binciken da zai ya tabbatar masu duk su biyu suna raye amma duk sai anmasu operation especially shi zhrdee dayake nasa yatabi hanjinsa' k'uma sakamakon bleeding da sukai suna bukatar jini" "jini su yya aka diba' itako Aisha koda aka gwada beyi maching da nasu ba' dole saida bbnta a kanita Abdul yazo snn akayi amfani da nasu" "Rukky tana fita nai tsaye tashar motar kaduna ta nufa'cikin sa'a mutum daya yarage yasa tana shiga bayan su biya kudi mota ya tashi" "suko police komawa g'idan Alhj sukai suka kara fadada bincike'duk binciken da zasuyi suyi k'uma ya tabbatar masu da cewa Rukky ta aikata h'akan" "h'akan yasa suna fita g'idan su Rukky suka nufa'daidai lkcn bbnta yana g'ida gateman ya shiga yai sallama da bbnta' jin ance police ne yasa bebata lkcn yafito ganisu' yana fita bayan su gaisa ya suka nuna masa *ID CARD* nasu snn sukace suzo niman Rukky ne" "bbnta yace batanan tana g'idan mijinta' nan suka warware masa abinda su tafe dashi snn k'uma suzo tafiya da'ita ne" "duk irin bayani da Bbn Rukky yaso masu amma suki sauraransa har ciki suka shiga duk wani binciken da zasuyi suyi amma basu gantaba' Dan h'aka suka tafi da bbnta' h'aka suka tafi dashi a motar police aka rates dashi nan danan area ya dauka ankama *Alhj isa* cikin g'ida kuwa sau faman kuka da kuka" "duk irin tafiyar da akeyi fuskan Rukky a rufe a mafiya' taki yarda ta b'ude fuskan" "inna najin labarin zhrdee ba mutuwa yai ba amma yana hospital ana masu operation shida Aisha' yasa inna cewa Zainab tatashi suje' duk da abin yana damuta amma cewa tai babu inda zata' inna tayi tayi amma Zainab ta kafe akan bazataje ko'ina ba' yaje Allah yabashi lfy' h'aka inna taje ita kadai" "tunda aka shiga dasu zhrdee Abba sai faman addu'a yakeyi kala kala' baya kare wnn zai kamo wnn' ita kuwa Hjy tana g'ida sbd g'ida yacika tamkar babu nasake tsinke' dangin uwa dana uba da makwabta h'ade da abokan arziki" "Rukky tana isa Kaduna tashar *kawo* tasake niman motar kano" *Allah ya rabamu da son zuciya da k'uma aikin danasani. idan ba aikin danasani ba' mezai kawo me tafiya kano Kaduna? " ina kano ina bauchi?' Allah yasa mufi karfin zuciyarmu amin* "nan ma tasamu sai yanzu aka fara lodi' door sai yacika kafin mota yatashi' gani h'akan yasa tafita tafara zata tashar ko zata samu wani wanda bazai bata lkcn" "duk union data tambya sai suce dukane idan ba motar da take lodi ta cikiba' wata motar bata isa tayi lodiba' dole yasa ta hkr ta koma ta zauna" "dama tunda tashigo wani union yasa mata ido Dan tabbatar da abinda idinsa ya gane masa gskyne koko akasin h'akan ne" "saida ya tabbatar tabbas Rukky ne snn yakoma gefe yai aron waya a gun Dan uwarsa snn yasa num yai plashing na farko gani ba'a kiraba snn yasake" "yana shiga a karo na biyu *Alhj Imran* yabi numr" "basho yace yayyyyy Alhj kananan abuka" "Inanan abuna basho' ba kagujeni ba?" "h'aka Alhj kaima kasan wlh tsohuwace ta rike wuta shiyasa' amma yanzu kasan me?" "a'a saika f'adi" "ina tsohuwar matanka a kake nima?" "to gata nan a tasha" "Rukky fa?" "kwarai da gske Alhj" "INA zata?" yanzu dai da h'aka tashiga motar kano amma bansan Iya inda zata tsaya ba" "to yanzu basho menene abinyi?" "a'a ya Alhj kasan natuba da irin wnn aiki' sai nasa ayi maka" "to yaya zasuyi?" "kada kaji komai ya Alhj' yanzu dai kyaleta zamuyi har sai tabar tasha snn na tura yara daidai gadar Zaria inda zaka haye zuwa kano' a nan ne zasu tare motar su dauko maka ina" "alhamdllh' ni k'uma daga nan zantura nawa yaran zuwa Jos' yaranka suna kawota Jos nawa yaran zasu amsheta zuwa gwambe" "shikenan za'ayi yadda kace' amma fa katara kudi' kasan dai bani bane sawa nayi k'uma ya kamata suji dumus" "kada kadamu basho" "na sanka ne ai Alhj wlh idan banga da'kyau ba da kaina zan biyoka har gwambe" "bama zamuyi h'aka dakai ba basho" "to yanzu Alhj samu kati na kirasu" "to shikenan" "suna gama mgn ya medawa me waya wayarsa' snn yaje yaci gama da kiran passenger" "ana gama masu operation aka fito dasu one after the other zuwa d'akin da zasu kwanta' daki daya aka ijesu shida Aisha snn aka jona masu jini" "bayan fitar inna zuwa hospital Zainab ta koma daki taci gaba da kuka'dama tunda sakon mutuwar zhrdee ya risketa take kuka har izuwa yanzu' duk da taso ganisa sbd taga wani hali yake ciki amma h'aka ta daure zcyrta taki zuwa hospital d'in" "mota yana ciki passenger sukabada kudi snn mota ya tasho" "basho na gani tashin motar ya sanar masu' tafiya sukai suna jiran zuwarsu' su Rukky suna isa gun daidai zaka haure gadan a guje suka fito hannunyesu ririke da bindigu suka tare motar" "police da suke tsaye can gefe suna amsar five naira ten naira suna gani h'aka a sittin sukabar gun" "mota yana parking suka b'ude motar wani mutum da yai gaggawar fitowa daga motar tokari daya daga cikinsu ya kai masa saida ya f'adi masa' snn suka fara searching motar sbd *Alhj imran* yariga ya tura masu da Pict nata' can suka hangota zaune sukai pointing nata sukace tafito" "h'aka tafito jiki na rawa' duk cikin motar babu wanda ya tanka hatta direban" "tana fita suka sata a nasu motar h'ade da rufe mata ido da kyalle suka dauki hanyar Jos" *BAYAN WASU AWANNIN ZHRDEE YA FALKA' HADE DA AMBATO SUNA ZAINAB' A BAKINSA' GEFEN IDONSA YANA GANGAROWA DA KWALLA* "gani h'ak yya Shamsudee yazo kansa yana masa addu'a har Allah yasa yai normal' amma bedaina ambaton Zainab ba" "itama tana can tunda tai sallar la'asar tana kan sallaya tana addu'ar Allah yabawa zhrdee sauki" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _*I WISH THE OF PEOPLE'S NIGERIAN HAPPY INDEPENDENCE DAYS' PROUD OF MY MOTHERS LAND' MAY ALLAH PROTECT OUR COUNTRYS AND GUIDE OUR LEADERS TO THE RIGHT PATH*_ 5⃣9⃣ "gani yadawo normal ne yasa yya Shamsudee yawo kujerar roba ya zauna kusa dashi yana rike da hannu zhrdee" "can itama Aisha tafara kokarin yunkurawa' gani h'aka yasa yya Shamsudee mikewa da sauri ya kira mmn Aisha' da sauri tazo ta riketa har ta falka h'ade da kiran zhrdee" "zhrdee yariga ya koma bcc besan abinda take ciki ba" "Rukky suna isa garin Jos daidai kusa da tashar kano kusa da farin ruwa kafin kikai gurin wani bakaniki sukai parking' boys d'in *Alhj Imran** suna isowa suka mikata snn suka juya" "duk a lkcn basu budewa Rukky ido ba' h'aka sukaci gaba data tafiya zuwa gwambe' ga uban yunwa da kishin ruwa dake damuta amma ba halin mgn sbd bakinta a rufe yake" "zhrdee yana falka a wani lkcn yafi wacce lkcn dawowa daidai jiyawar da zaiyi ya hango Aisha kwance, ita k'uma lkcn tana bcc mmki ya kamasa yana tambyar kansa mekuma ya samu Aisha kodai itama caketa da wukarne Rukky tai?'.. " Abba ne ya turo kofa ya shigo d'akin' gani ido zhrdee biyu yasa Abba sauri karisowa gurin h'ade da shafe kan son dinsa snn ya zauna kusa da son ya zauna ido kawai Abba ya dubawa son yana kallonsa a zcyrsa k'uma yanawa ubangijinsa godiya" "police suna tafiya da *Alhj isa* kai tsaye police station suka nufa dashi' sufesa sukai a cell' a cewarsu koda beli akazo bazasu bayar da belinsa har sai Rukky ta kanta hannu hukuma" "da yamma Bbn Zainab yace tazo suje gaida zhrdee' Zainab tace a'a baba ka yafi kawai basai naje ba' *Alhj Musa* yace a'a Zainab kizo muje kodan niba kodan albarkaci yara" "Dan Allah Abba kayi hkr ka tafi kawai' wlh babu inda zani Abba" "to Zainab shikenan' tunda haka kikace' amma dadai kiyi hkr' fice warsa yai" "kafin su Rukky su iso garin gwambe tuni Honorable ya sanarwa police' su Rukky basu iso garin gwambe ba sai around ten o'clock' suna isowa yai handling d'in Rukky gurin police snn ya sallami boys d'in da suka kawo masa ita" "Abba besa kamar police su kama Bbn Rukky ba sai da kanni *Alhj isa* sukaje station niman beli police sukace bazasu bayar da subada bill dinsa ba sai in har sukawo Rukky' sukuma a yanzu da h'aka basusan inda zasuga Rukky ba'asalima rabo da suha ido da Rukky tun ranar da suka daura mata aure da zhrdee basu dake ganita ba" "h'akan yasa suka nufi g'idan su zhrdee dan niman alfarma akan yabasu bill d'in dan'uwarsu idan yaso duk lkcn da Rukky tadawo garin su amince yasa a kamata k'uma ya yanke mata hukunci daya dace da'ita" "koda sukaje Abba yace yanzu da h'aka mgn ba'a hannunsa yace ba yana hannu hukuma ne dan h'aka duk abinda shari'a suka yanke akanta daidai ne' babu irin rokon da basuyi Abba yaki yarda daga karkema tashi yai ya bar masu parlour' suma gani h'aka dole yasa suka mike suka bar g'idan" "tun daga lkcn yar' uwa da abokan arziki aka suga niman Rukky' sbd idan ba kawo Rukky sukai ba ba basu bill yan'uwarsu za'ayi ba' k'uma kusan ace shine g'ida *head of the family bafa na girman shekaruba' kusan yanzu wata yanayine muka shiga idan har Allah ya b'ude kama ya k'uma hore maka abin hannu to fa kaine babba a g'ida me f'ada aji' Allah ya rufa mana asirin duniya da lahira amin* dole duk inda zasu shiga zasu dan ceto yan'uwarsu daga halin dayake cikin' kowa a family nasa advance d'in' daya daga cikinsu mai suna Bb Habu yace tunda abu ya zama h'aka me zai hana baza'a tambyi tsohon mijinta ba ko Allah zaisa a dace" daya daga cikinsu yace ta yaya za'a kirasa bayan irin labarin da mukaji akan abinda data aikata masa' ko so kake allura ya tone galma' to wlh koda wasane wani ya sake ya kirasa nidai babu hannuna a cikin abinda zaije ya dawo" "duk jama'ar dake zaure babu Wanda ya tanka' bcoz Alhj isa shine me kudin g'idan' k'uma idan ba shiba babu wanda zai'iya jada Honorable' dan h'aka kowa ya shiga juyayin ta'ina zasu bolewa lamarin?' "a h'aka dai metting ya tashi babu wata mafita da suka samu" "zhrdee a hankali jiki yananan yana sauki shida Aisha' duk da ba wani sauki yaji sosai ba amma baya sauraran Aisha' koda safe yayi tana kwance idan tace masa ina kwana' lfy kawai yake cewa daga snn bazai kara amsawa ba' idan ko har ta tanka mata tofa lkcn duk yan'uwa su hadune anata faman hira shine yake sa baki';shima jifa jifa yake sawa" "duk da iskancin Aisha amma a wnn karo tayi sanyi sosai' kome tagani Ohooo?" "tunda Honorable yasa aka rufe Rukky besake lekawaba' itama kanta tasan dai a station take amma batasan wanda yasa yaka kamotaba sbd kwanta kwanta bata kawo tunanin Honorable zaiyi mata h'aka ba' a tunaninta yariga ya yafe mata" *waye Honorable* *_Alhj imran_* _haifanfen garin gwambe ne tun farkon rayuwarsa besan kowani irin sana'aba idan ba siyasaba tun yana concilor har ya kai ga chiaman' bayan ya dauka daga chiaman ne jama'ar gari suka siye masa takardan dan majalisan dattawa gani su samu progress a local government nasu yasa suka sake siye masa masa wata takardan na *house of rep* (Dan majalisan ta raiya) wata rana yana dawowa daga abuja to gwambe ne ya hadu da Rukky duk da a lkcn kanta be waye kamar yanzu ba' sbd a lkcn secondry kawai takare' daga sann mgnr aure ya shiga tsakanisu' koda ya aureta yanada mata daya da yara biyar dan h'aka ita ya barta a gwambe kowani weekend yake zuwa' yaban saukarsa yai parking ya dawo g'ida gaba daya' wata shekara da yazo yafito niman senator' duk uban kudin daya kashe beciba' sakamakon matsala daya samu anhada baki da abokinsa aka manaficcesa' k'uma gudumuwar Rukky sbd abokin Honorable tunda ya lura Rukky yarinyace meso kudi yasashi amfani da wnn damar ya yaudareta da kudi duk wasu sirikan mijinta tana bashi' daga hakane suka koma farka da junarsu' ko kafin Honorable ya falka suriga suci gari' a lkcn da yaso hukutata Rukky ta nimin kasheshi akan idan ya mutu saita kwashi dukiyar taje ta auri abokinsa' Allah ba arzalumin bawansaba asirinta yatonu' a lkcn da yakeda shirin kamata Rukky ta kwashe masa dukiya tabar garin_ "bayan sati biyu da kwanciyar zhrdee a hospital Bbn Zainab ya matsa mata adole sai taje ta gaida zhrdee' a yau kam babu yadda zatayi sbd abbanta ya sata gaba' ciki ta koma tai kwalliya cikin riga da sket na material pink colour h'ade da mayafinta snn taiwa *Islaha* itama kwalliya cikin Dan kanti duk suyi kyauta abbanta ya sata gaba yace suje *Islaha*na hannunsa suka shiga mota' saida zaiyi driving ne ya mikewa Zainab yarinya" "suna isa yasake daukarta suka nufi d'akin da zhrdee ke kwance' Abba na gaba Zainab na baya suka shiga da sallama gun zhrdee kawai suka nufa lkcn yya Nurudee ne kawai a d'akin' cikin girmamawa ya gaida Bbn Zainab shima ya amsa' Zainab suna h'ada ido da zhrdee ya sakar mata murmushi' ita kuwa daure fuskanta tai babu alamar wasa a cikinta" "kujeran da yya Nurudee yake zaune ya mike yabawa Bbn Zainab ya zauna' *Islaha* NA gani bbnta ta mika hannu ya dauketa murmushi zhrdee yai h'ade da mika hannu" "Abba na gani h'aka ya ije kasa yarinyar kusa dashi' juyawar da zaiyine ya tuno Aisha na d'akin' suka gaisa h'ade da gaisheta ta jiki" "gani har a lkcn Zainab batace kala ba' kallo daya yai mata ta fahimci abinda yake nufi snn ta gaida zhrdee da jiki" "b'akin zhrdee har kunni ya amsa' juyawa tai ta gaida Aisha itama' a cikin zcyrta tana f'adi sbd Allah' matsawa zhrdee yai yace tazo ta zauna' ko kallo be Ashe taba tamkar bada ita yakeyi ba" 'gani h'aka yaci gaba da wasa da yarsa' saida suka juma snn Abba ya mike sukai sallama' yaso daukar yarinya amma gani yadda zhrdee ya riketa yasashi fita a d'akin' hannu Zainab tasa zata dauki yarta zhrdee ya rike mata hannu' Aisha dake kwance tana gani h'aka ta juya masu baya" "ido kawai ya zuba mata yana kallonta cikin ido h'ade da murmushi' fisge hannunta Zainab tayi ta dauki yarta tafice daga d'akin" "shiru shiru da police sukaji akan Rukky tunda Honorable ya basu ita besake waiwayarta ba' sukuma yan'sanda suna niman guri ije wasu yasa suka kaita kotu' daganan aka wuce da'ita pirizi"""""" ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES. F.O.w☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* _*Dan Allah kuyi hakuri na rashin jina kwana biyu'mahaaifin mai g'ida nane Allah yayi masa rasuwa shiyasa'duk da nasan Mmn ahamed ta sanar amma ba lalla bane ace kowa ya sani' ngd sosai Allah yabar zumuci*_ _~*masu kirana suma ngd Allah ya kara kauna da zumuci amin*~_ 6⃣0⃣ "bayan kwana biyu da kai Rukky prizi'bbn Habu kani mahaifin Rukky ya yanke shawaran kira Honorable ya tambyesa ko yaji labarin ta' amma k'uma kada allura ya tono galma' wata zcy tace kirasa kawai' idan ma yaji ko allura ta tono galma menene?' Ai dama ba'a gane maci tuwo sai miya ya kare' k'uma inda ba kasa Ai nan ake gardaman kokuwa' indama Allah zaisa a ganta a sakomi dan uwana ita ba damuwana bace' kowa yadibo da zafi bakinsa" "wayarsa ya ciro daga aljihunsa ya lalibo numr Honorable kira biyu a cikin na uku ne ya daga wayar gani numr Bb Habu ne yasashi kwantar dakai h'ade da sallama' dama dabi'ar Alhj imran ne akwai girmama na gaba dashi'balle k'uma ace sirikinsa" "Bb Habu yaji dadin irin amsawar da Alhj imran yai masa dama yasa wala kanci ba halin Alhj imran bane amma dan adam yana iya canzawa a kowani lkc' shiyasa yai shayin kiransa' jin yanayin yadda ya amsa sallamar yabawa BH Habu karfin gwiwan mgn' bayan su gaisa cikin shakku h'ade da nuna kunya ta Hausa Fulani Bb Habu yace dama!!! dama!!!" b"dama me?" "murmushi ya karayi snn ya sake da dama' yana susakansa kamar yana ganisa" "baffa idan akwai wata matsala ce kayi ngd kawai kada kaji komai" "dama Dan Allah wata tambya nakeso nayi maka amma bansan yadda zaka dauki abinba" "babu komai baffa isha Allahu' Allah k'uma yasa nasani" "dama mgn ce akan Rukky?"... " wacce Rukky k'uma baffa?' ai ni yanzu banida matsala da'ita" "eh musan da h'aka' amma Dan Allah koda labarinta bakajin?" "a'a baffa banaji" "Ohooo!!! innalillahiwainnailaihi raju'un' mukan mushiga uku da wann yarinyar?" lfy baffa kake irin wnn salati da salallami" "kaidai Alhj bari kawai' wlhy wata matsalace ta taso". " wacce irin matsala haka baffa?" "hiimm wlhy dai to" "a'a baffa Dan Allah kayi mgn mana" "to wlhy dai matsala ce wacce tazama dole sai da Rukky agun snn matsalar zata warware" "wacce irin matsalace h'aka wacce baza'a iya warwareta ba saida Rukky" "amma baffa idan baka mance ba lkcn da muka samu matsala da Rukky ban boye maku komai ba a matsayinku na magabatanta sai dai k'uma mmkin da kuka bani baffa bazan boye maku ba k'uma ni kaina nasan Rukky tana tare daku kuka boyeta kukace bata tare daku' inaji ina gani h'aka na tafi na kyaleku' badan kufi karfin naja daku ba a'a sbd alkawari nayiwa kaina idan bera na yawo mage na yawo wataran za'a hadu' shiyasa na tafi kawai" "eh h'aka ne amma wlhy ba laifina bane' indama anbi tawa wlhy tun kofar da bahaka ba" "amma Dan Allah kayi hkr ka taimakemu idan har kasan inda take ka sanar mana' badan mu ko ita zakayi ba Dan Allah zakayi" "toni baffa yanzu bansan abinda kake bukata a guna ba" "eh to tunda abin tazama h'aka kasan hausawa suce ranar wanka ba'a boye cibi' abokin kuka ake fadiwa mutuwa inda kasan zaka tsira nan zafa rabe' ba komai bane yasa nake rabe rabe amma tunda abin yazama h'aka dole na sanar maka da komai' ko lkcn da kazo niman Rukky bazan boye makaba Rukky tana cikin g'ida amma abinda yasa banyi mgn ba sbd kada ace Dan bani na haifeta ba' kasan yadda mgnr duniya yake yanzu kaji dalilin kenan" "himm baffa kenan' bayan haka k'uma?" "eh bayan wasu lkcn shine tasake wani aure' bari na yanke maka labari bayan watanni da aurenta suka samu matsala da maigidanta ta sokesa da wuka k'uma ta soke abokitar zamanta' tana aikata h'aka ko g'ida bata zoba barin garin tai tunda ta tafi babu lbrinta' hukuma tasa aka kama ubanta' yanzu da h'aka ubanta yanana a rufe bazasu bada belinsa ba sai ankawo Rukky' wlhy babu inda bamujeba amma batanan" "ikon Allah yanzu bbnta yana rufe?" "wlhy kuwa" "baffa kenan' bazan boye maka ba' Rukky tana tare dani' yanzu da h'aka tana hannu hukuma' a nan cikin garin gwambe" "Allah me iko' to yanzu Alhj babu yadda za'ayi?" "eh to bazan iya cewa eh' ko a'a ba' sai abinda hukuma suka yanke akanta" "to shikenan Alhj mugode" "bayan suyi sallama ne Bb Habu yaje cikin family hause yake sanar masu yadda sukai da Honorable' daga nan suka kwashi zoga zuwa g'idan Alhj Kailani Bbn zhrdee' da fara'arsa ya amshesu bayan su gaisa ne bba Habu yace dama Alhj Dan Allah muro cin wata arziki ne a gunka" "murmushi kawai yai sbd yariga yasan abinda ke tafe dasu' saidai ya matse h'ade da cewa ina sauraranka" "akan mgnr d'an Uwa nane Alhj' Dan Allah Dan annabi Dan soyayyar da kakewa shugabanmu annabi muhammadu ( S.A.W.) d'an soyayyar da kakewa iyayenka Alhj" "murmushi Abba ya sukeyi snn yace to yanzu me kukaso ayi maku ne?" "Alhj Dan Allah ka taimakemu kasa b'akin a sako mana d'an Uwa' wlh Alhj duk lkcn da Rukky ta dawo garin nan ni da kaina zankawo maka ita" "himm Malam Habu kenan' yanzu sbd Allah idan danka akaiwa haka zakaji dadi?' kashin kaifa taso yi Dan ma Allah ya takaita abun da kilan duk su rasa ransu" "eh duk musan da h'aka mudai Dan Allah hkr kawai zakayi' tunda ma Allah ya takaita abu" "Malam Habu kenan nifa har yanzu ban fahimceka ba' nasa hannu a sakota ni k'uma jini dana yatafi a banza kenan' shine ban fahimtaba' yarinyar banza kawai ni wlh tun farko banso auren ba d'an dai kawai lekewa da yai ne amma idan ba h'aka ba me ake da yar'daba" "uhmm Alhj adaiyi hkr wlh kasan yadda yaran zamaniga suke sarai ka haifi mutune baka haifi halinsaba' k'uma nima kaina banso abari Rukky ta sake wani auren ba' tunda ba'ariga an gama kashe wacan wutar ba' to amma babu yadda na'iya" "kamar yaya ban fahimceka ba Malam Habu?" "ina nufin tunda ga case din g'idan tsohon mijinta ba'ariga an kashe ba" dama kusan da h'aka ne kuka bari dana ya aure?" "to mudai Dan Allah hkr zakayi" "tambya nayi baka bani amsata ba Malam Habu?" "eh to dama'''' daga nan ne Malam Habu ya zare ya fadiwa Alhj Kailani komai akan Rukky' babu abinda ya boye masa" "shiru Abba yai yana jijina lamarin h'ade da Allah ya kyauta snn ya mike h'ade da cewa tashi muje' suma mikewa sukai zuwa station d'in" "suna isa bayan ya shiga daga ciki ne police da suka tsare da *Alhj isa* suka gaisa snn police sukace Alhj lfy?' Abba dasu tsaye yace yanaso gani *D P O* daya daga cikin police mai suna Anthony ba Hausa ne yakeji sosai ba *duk da dama minority not majority ba wani ilimine dasu a akwai qua(means dakikai) wanda koda statement basu iya rubutawa* yace daga ciki but before yau enter late me tolk to him" "Abba dake tsaye yace OK *Sr* " yana shiga ya fito yacewa Abba yashiga' Abba yana shiga suka gaisa bayan su gaisa ne Abba yace dama akan case d'in nan ne shine nazo a badashi beli" " *DPO sa'eed* yai murmushi snn yace amma Alhj kasan koda kai kayafe government suna da nasu hakkin ko? " "eh *DPO* nasan da h'aka amma d'an Allah kuyi hkr sbd Allah idan yarinyar tadawo garin nin ni da kaina zankawo maka ita insha Allahu" "to *Alhj Kailani* dama duk wnn fineting d'an kai mukeyi da k'uma kare hakki a matsayinsa na d'an kasane amma tunda h'aka kace babu damuwa" "shiru Abba yai be tanka ba' *DPO Sa'eed* yabashi wasu file ya cika h'ade da *SING* snn yasa aka fito dasu'da sauri Malam Habu yaje ya rungume d'an uwansa' ko kallonsu Abba beyiba yai ficewarsa" ~~~~ ~~~~ ~~~~ "bayan fitar dakaban Fatima zarawara sai faman tururuwa sukeyi zuwa gunta' wasu suzo Dan Allah suwa k'uma d'an abinda Nasir ya bari mata" _*wata yanayine yanzu Allah ya kawomu mundu Allah yaiwa mijinka rasuwa balle yanada abin hannu ko nace rufan asiri' to fa zawarawa saika turo' badan sbd komai ba' sbd kwadayin abinda aka barmaka" Idan suka samu wawiya k'uma shikenan sai abinda Allah yayi' sbd zasuyi iya kokarinsu wajan gani su aurenka' bayan aure da d'an kwanaki ko watanni daga lkcn zasu fara tunanin yadda zasu shawo kanka wajan gani su cinye d'an abinda miji ya bari maka' ba damuwarsu marayun da aka barki dasu ba ko k'uma kedin a'a damuwarsu dukiyar da mijinki ya bari miki' da zaran su yayi dukiyar shikenan dama abinda yakawosu kenan' Allah yasa mudace' ya karemu da sharrin irin su amin*_ _*shiyasa yana da'kyau mu mata mukula da'kyau Dan Allah a duk lkcn da h'akan ta samesu' muyi kokarin kai hakalinmu nisa da k'uma yaki da zcyrmu wajan gani mu yaketa' sbd ba lalla bane ka gane na Allah' tunda abin ba'a goshi yake rubuce ba balle kace ka gane na k8rki' a lkcn da idan kac3 kanada marayu zakaji zawaràwan suce babu komai su amince' bayan anyi auren suna kwashi dukiyar shikenan' idan k'uma h'akan be samuba sai kaga rawa ya canza' da zaran kida ya canza dole rawa shima ya canza' daga lkcn sai kaga ayi ta dauki ba dade kakoma kana yaya zakayi kana dakasani' Allah ya rabamu da aikin danasani duniya da lahira amin*_ "gani h'aka yasa mahaifin Fatima ya sameta har daki lkcn ta idar da sallar isha tana zaune kan sallaya tana lazumi abbanta yai sallama' ya shigone yasa Fatima shafawa snn ta amsa da Bb kaine da kanka h'ak?" "wlh kuwa Fatima dita' sallah kikeyi ne h'aka?" "eh Bb amma na'idar" "Allah ya karba" "amin Bb" "Fatima dama guki nazo" "ni k'uma Bb?" "eh wlh" "Allah yasa dai lfy" "dama ba wata mgn bace Fatima mgnr zawarawankine Fatima a gskya banajin dadin yadda kike walakansu Fatima'idan baki sonsu be kamata kina walakanta su' idan kisan zcy ko b'akin wani Ai bakisan na wani ba' k'uma ke ba abin alfahari bane ace baki dade da fita takaba ba kika samu manimi ba' ki duba fa sbd Allah yadda *Alhj AMINU* yake ta ziriya a kanki"... " wani *Alhj Aminu* k'uma bba? " *Alhj AMINU* mana wanda yake aiki a *ministry of foreign affair* amma yanzu yana zaune a London ne shida matarsa" "himm kawai Fatima tace" "wlh Fatima ya kwana biyu yanami mgnrki yanason zuwa amma yana tsoron yadda kikewa masu zuwa shima kizo kimasa shiyasa yazo ta hannuna yai min mgn" "nidai gskya Abba kayi hkr kawai" "nayi hkr dame Fatima?' h'aba Fatima wacce irin yarinya kikeso ki zama ne sbd Allah yanzu kin gwammaci ki zauna h'aka babu aure?" "kuka Fatima nata f'adin nidai wlh babu wani auren da zanyi' sbd Allah d'an mijina ya rasu akace dole sainayi wani aure aini ba h'aka mukayi dashi". " shiwa k'uma Fatima. *Alhj AMANU* kowa? " "a'a shidai Nasir d'in". " h'aba Fatima kanki daya ne kuwa yanzu har wani alkawari kuka tsakaniku ke dashi?" "eh Abba k'uma ni bazan iya cin amanarsa ba" "to wlh baki isaba Fatima aure k'uma dole sai kin yita" "Fatima najin h'aka tasa ihu h'ade da kiran wayyo Allah na Nasir katafi ka barni Nasir wayyo mutuwa nashiga uku na lalace" "gani irin kukan da Fatima keyi yasa Abba cewa Fatima kukan ya'isa h'aka d'an Allah nifa ba cewa nayi dole sai kinyi aure yanzu ba balle ki nimi ki tarami jama'a kina jina Fatima" "cikin kuka Fatima ta daga masa kai" "to ya'isa h'aka banaso ina gani hawaye suna zubowa daga fuskanki' kina jini na bar mgnr tunda bakiso' amma sai kinbar kukan nan da kikeyi' hannu Fatima tasa ta guge hawayenta' daga snn bbnta yaita janta da hira har tasaki jiki sukai hira sosai" "mahaifin Fatima yai mata hakane sbd a rayuwarsa bayason gani ranta ya baci balle har shine yasata kuka da kansa' yanzu ya kyaletane zuwa wani lkc snn yasake tutubarta da mgnr' k'uma yasan babu wani alkawarin da sukai da Nasir tsabar soyayyar da sukewa junane kawai yasa Fatima take f'adin h'aka" "tun daga lkcn Bbn Fatima besake tutubarta da mgnr *Alhj aminu* koda yazo iya kacinsa gun bbnta kawai' a kullum hkr abbanta yake bawa *Alhj aminu* shima dayake wayayyene cewa yake babu komai kada ya damu yarinya ce wataran sai labari' *Alhj aminu* ya f'adi h'aka badan abin baya damusa bane a'a saidan darajan soyayyar da yake yibata" " *Alhj AMINU da matarsa mai suna MARIYA haifanfun yan' bauchi ne shida matarsa tun bayan samu aikinsa a cikin garin abuja ne ya dauki matarsa da yaransa suka dawo abuja da zama da yaransa guda hudu dayake rayuwar turawa ne sukayi' daga snn aka turasa London tun daga lkcn acan yake zaune shida iyalansa' Alhj AMINU dan kimani 45-50 years ne matarsa kuwa saidai suzo sa'a da Fatima' Mariya macce me kirki da mutunci kusan halaiyansu daya da me g'idan ta' saidai kash mutum tara yake becika goma ba' sbd Hjy Mariya macce ba meso alkairi ba k'uma bataso mijinta yai shima daya gane h'aka koda abu zai baka saiya duba idan batagun sbd a zauna lfy badan tsoro ba' amma bayan h'aka batada kowani matsala* ~~~~ ~~~~ ~~~~ "a yau ne 17- 5- 2018 za'a shiga kotu da Rukky da honorable karfe ten o'clock shapp suka shiga kotu bayan aalkali ya shigone duk jama'ar dake zaune cikin kotun suka mike tsaye' bayan alkali ya zauna ne suma suka zauna alkali ya bukaci Honorable ya gabatar da kansa' bayan Honorable ya gabatar da kansa snn itama Rukky ta gabatar da kanta alkali yace ina lauyanlauyan dake kare Alhj imran *barrister al'kasim* yace gani" "snn alkali yace ina lauyan dake kare Rukky?" "Rukky batadashi" "alkali yace governing zata baki lauya' alkali ya umarci *Alhj imran* yai mgn h'ade da rantsuwar zai f'adi gskya' ni *Alhj imran* ina zargin tsohowar mamata Rukky da cin amanataamanata amanata" "amana kamar yaya?" "tanabin maza da aurena akanta h'ade da kwashemi dukiya ta" "alkali yace ke Rukky kinajin abinda tsohon mijinki yace yana zarginki dashi ko?" "eh najisa amma abinda yake zargina dashi bansani ba" " *Alhj imran* to kaji abinda tace" "wlh karya takeyi idan ta musa h'akan inada sheda" "shedar yananan ne?" "a'a bayanan saidai abani lkc nazo dashi" "alkali yace andaga wnn shari'a zuwa 7-6-18' daukar Rukky akai aka medata zuwa g'idan maza" "yau ne aka sallami zhrdee da Aisha su Abba da yya Shamsudee da Hjy suka kwashi kaya zuwa mota' har su h'ade dana Aisha zhrdee yace acire nata kayan g'idan su zataje" "Abba da Hjy har suna h'ada baki wajan tambyarsa kamar yaya' itama aishan dake tsaye jikinta amace yake idanunta duk su ciko da kwalla" "fuska a daure yace nace tatafi gidansu ko yayane?" "son kanka daya kuwa?" "klau nake Abba aurene da'ita banayi" "Aisha najin h'aka tafashe da kuka" "zhrdee wai menene h'aka ne' ke Aisha shige muje" "na rantse da Allah idan kika shiga motar nan idan ban maki dukan masifa faba kice me?" "wani irin duka k'uma zhrdee idan ba kasheta zakayi ba?" "gara yar'banza tamutu kowa ya huta ni ba kasheni taso ayiba?" "wlh Hjy ta tafi kawai tun kafin na yanke alakata da'ita kwata kwata muguwa alzaluma mara jin mgn kawai' wlh Aisha na tsaneki banason ganiki kwata kwata k'uma sai Allah ya sakami nida Zainab" "shiru Abba da Hjy sukai'aisha dake tsaye dukawa tai a gaban zhrdee h'ade da rike masa kafafuwarsa tana kuka tana ambaton kayafemi d'an Allah" "duk da a rike yake amma behana zhrdee sa kafa ya tokare Aisha ba tafadi kansa tana kuka" "har ya sake daga kafa zai kaimata wani da sauri Abba yazo ya rikesa aka sashi a mota" "Abba yace Hjy taraka Aisha g'idan su kawai" "zhrdee yana zaune yana faman huci' duk da azabar zafin da yakeji amma be hanasa bala'i ba" "Hjy ta kama Aisha zuwa mota' su Abba sukai hanyar g'ida' ita k'uma Aisha da Hjy sukai hanyar g'idan su Aisha""""" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 6⃣1⃣ "suna cikin mota suna tafe Abba yace gskya son banji dadin abinda kaiwa Aisha ba"... " h'aba Abba bakaji dadi ba kace?' to wlh kadan nayi mata' inda ta sake ta biyoni g'idan nan Allah kadai yasan irin abinda zanyi mata' wawiya kawai dakikiya mara jin mgn" "is OK son kaga bakada lfy ko?' kayi hkr h'aka" "himm Abba kenan' sauran itama Rukky wlh har g'idan ubanta zantura a kamota" "wacce Rukky k'uma?" "Rukky mana Abba" "yanzu son duk abinda nayi akanka baka gani ba kenan?" "kayi hkr Abba bansan kayi wani abu akai bane shiyasa" "h'aba son a aikata maka danya danyar aiki irin wnn ace ban dauki mataki ba?' kaima kasan sai inda karfina ya kare" "h'aka ne Abba ngd" "tunda aka shiga mota Aisha kewa Hjy kuka' Hjy tayi lalashi har tagaji Aisha batai shiru ba' gani h'aka yasa tafita harkanta har suka isa g'idan su' bayan yya Nurudee yai parking Hjy ta taimaka mata ta fito daga motar snn ta riketa har cikin g'ida' Bbn Aisha da ummata tayi mmki gani sudawo da Aisha g'ida' sbd basu lkcn da akayi sallama'bayan Aisha ta zauna ne suka gaisa cikin girmama juna abbanta Aisha cikin kosawa yace yaya naga Aisha kindawo da'ita nan ba g'idan mijinta?" "Aisha najin h'aka tasa kuka' dama dan tutuben harshe suka samu ita sa maigidan nata amma insha Allahu idan komai ya daidai anjima zanzo na dauketa mutafi" "to Allah ya kyauta" "amin Hjy tace h'ade da mikewa sukai sallama tafita" "su Abba suna g'ida bayan Abba ya fito snn yarike wa son hannu shiga yafito suna shiga bangaren zhrdee yya Shamsudee yace Abba bekama a barsa nan ba tunda babu kowa" "eh k'uma hakane' to yanzu abinda za'ayi mukaisa dakina kawai' d'akin ka k'uma Abba?' eh dakina kaga ku yanzu ba g'ida kukeba balle nace zanbarsa a bangarenku' bangarensa k'uma babu kowa a gun' to shikenan Abba" "d'akin Abba suka shiga da kayansa sukuma suna zaune a parlour Hjy tai sallama' ganisu a parlour ne yasa itama ta zauna' duk mgnr da sukeyi akan su Aisha zhrdee be tanka masu ba har sukayi suka kare" *Rukky* "a yau ne Rukky da zhrdee zasu koma kotu' bayan alkali ya zauna snn ya umarci Honorable ya fito bayan ya fito ne akace Rukky itama ta fito duk saida suka fito snn akace idan shedan da Honorable yace zai kawo yazo yafito" "jin haka Honorable yace eh yana kusa" masinja yace ya shigo dashi' bayan Bb maigadi ya fito ne alkali ya ke tambyarsa alakarsa *Bbn idi maigadi* yace nidai gadi nakewa Alhj imran tsowon shekara goma sha biyar' bayan aurensa da Rukky idan yana abuja gun matarsa uwar gidansa lkc lkc nakan ganta tayi wanka ta fita' idan tafita tun safe bazata dawo g'idan ba sai dare misalin goma' wani lkc k'uma *Alhj Rufa'i* makwabcin Honorable wasu lkta ma har cikin g'ida yake zuwa" "alkali yace Dan Alhj Rufa'i ya shigo cikin g'idan Alhj imran shine zakai masu mummanar zato?" "a'a ba haka bane" "ko zamusan dalili?" "wata rana bayan Rukky ta fito ta zata tafi uguwa ta sallameni ta fita shine na leka daga waje naga Ashe ita da Alhj Rufa'i ne zasu fita' tana fita ya b'ude mata mota suka tafi' tunda sukabar uguwar basu dawoba sai bayan takwas na dare har kofar g'ida yazo ya sauketa snn ya karisa nasan g'idan" "Dan zata fita ya dauketa k'uma tana dawowa kaga ya sauketa shine kake zarginsu?' kasani ko rage mata hanya yai a lkcn da zata fita' h'aka lkcn da take dawowa suka sake haduwa ya dauketa a matsayinsa na makwabcinsu?" "a'a ranka ya dade ba h'aka bane" "muna sauraran dalilinka" "bayan daukarta da yakeyi suke fita akwai wani lkc da yashigo har cikin g'idan lkcn Honorable baya gari' ina cikin dakina na masu gadi bansa da shigowarsaba sai fitansa dana gani" "a matsayinka na megadi tayaya har mutum zai shigo cikin g'idan da kake gadi batare daya saniba? " eh lkc ina d'aki na kwanta' ban dade da kwanciya ba bcc ya daukeni" "OK kanaso kace a cikin bcc kenan kagano fitan Alhj Rufa'i" " a'a lkcn idona biyu" "kace kana bcc' yanzu k'uma kace idoka biyu' duk iji lauyar dake kare Rukky kenan?" "eh' a lkcn nariga natashi daga bcc" "OK Dan kaga fitar Alhj Rufa'i daga cikin g'idan Honorable shine kake zirgin suna cin amanar maigidanta ko" "a'a ba h'aka bane" "to menene' kafin h'akan yafaru kowa dai yasan alamar dake tsakani *Alhj Rufa'i da Alhj imran* amma yanzu d'an wani abu ya shiga tsakanisu shine za'akawo wasu abubuwa na sharri a rankafawa Alhj Rufa'i ko" *opjuction my lord* "alkali yace a kiyaye" "Bb maigadi yaci gaba da cewa bayan kwana biyu da ganisa danayi h'aka yasake dawowa g'idan Alhj imran" "a matsayinka na maigadin g'ida tayaya aika kabari ya shiga g'idan bayan kasan maigidan bayanan" "a'a bansan lkcn da yashiga bane?" "OK bakasan lkcn shigarsaba?" "eh" "amma kasan lkcn fitarsa' kenan ko a gun kanuna rashin kwarewa da aikin ka" *opjuction my lord* "a kiyaye" *OK Sr* "a'a ba haka bane" "h'aka ne mana Malam idi" "a'a wlh ko oga ma yasan ina iya kokarina wajan kare a gum aikina" "yasan kana Iya kokarin ka amma shine har aka shiga g'idan batare da kasani ba' kenan duk a haka yana mana nuna da kwarewar aiki ne?" "a'a wlh ba haka bane" "to menene?" *opjuction my lord* *korafi be karbuba* *thank u Sr* *ina sauraranka Malam idi megadi " "a ranar da Alhj Rufa'i yazo g'ida. ita Rukky ta aikeni kasuwa" "kenan kana mana nuni da cewa kullum take aikenka?" "a'a ranarne kawai" "wato kanaso kace tayi amfani da h'aka kenan a matsayinta wacce ta kware da irin wani harkan kenan ta aikeka dan tasamu ta shigo ta Alhj Rufa'i ko yaya?" "eh to nidai bance h'aka ba" "kanadai zarginta kenan?" "a'a ba zarginta nakeyi ba?" "to menene?" "a lkcn da Alhj Rufa'i zaifita daga g'idan Alhj imran shine na ganisa" "a lkcn da kagansa yana fitowa daga cikin g'idan kai k'uma kana ina? " nafito daga dakina rike da buta a hannu zanyi alwala" "alwala karfe nawa?" "na isha'i' "da yazo fita kamar yadda kace ya ganka ko be gankaba ba?" "ya ganni har mu gaisa" " kun gaisa?" "da kuke gaisuwar yaya kaga yanayinsa ya koma a matsayinsa ba mara gskya?" eh to gsky bazan Iya cewa komai akan hakan ba sakamakon akwai duhu a gurin" "kace akwai duhu a gurin tayaya akayi ka gane cewa Alhj Rufa'i n" "Ai ba ranarne farkon ganisa ba" "kenan ka dade kana zarginsa?" "a'a ni bana zarginsa face abinda na ganewa ido na" "idan ba zarginsa kakeyi ba to menene?" "cikin zafin rai barrister *mudasir yasake cewa opjuction my lord* *a kiyaye* *OK Sr* " akwai watarana nima kaina bansan Alhj Rufa'i yana cikin g'idan ba' lkcn Rukky tasa na kunna mata bohall sakamakon babu ruwa a cikin g'ida da tankoki' bayan na kunna zuwa wasu awanni tankuna suka ciki ruwa yanata zuba gani h'aka shine naje na sanar da'ita idan tagama sai na rufe bohall din' a lkcn nayi ta sallama babu wanda ya amsa' gani ba'a amsa ba yasani komawa da baya nace kodai bcc takeyi " "duk da h'aka ruwan be daina zuba ba gani almubazaranci zaiyi yawa yasa nasako komawa nayita sallama babu wanda ya amsa' gani h'aka yasa na leka cikin parlour naga ko lfy' ina lekawa mukayi karo dasu and parlour suna rungume da juna" "su ganka ko basu ganka ba a lkcn da kace ka gansu cikin wann yanayin?" "eh su gani" "da suka ganka yaya sukayi a matsayinsu na marasa gskya?" "tsawa Rukky ta dakemi h'ade da cewa fita da iziniwa ka shigo?" "ni k'uma jin h'aka yasa nafita da sauri jikina yana rawa" "a lkcn da kace ka gansu rungume da juna wani irin suturane a jikinsu?" "shidai Alhj Rufa'i daga shi sai gajeran wando' ita k'uma rigan bcc ne a jikinta" "a duk cikin wnn second nine ka kare masu kallo h'aka?" bayan kace kana shiga ta umarceka da kafita batare da bata lkc ba" "shiru Malam idi yayi be tankaba ba" *barrister al'kasim* ya juya ga alkali yana cewa ya mai girma mai shara'a kaji shedar da Malam idi maigadi a g'idan Alhj imran ya bayar" "alkali ya juya gun Rukky dake tsaye yace toke Rukky kinajin shedar da idi maigadi ya bayar a kanki ko kinada ja akan h'aka?" "eh to amma nidai nasan babu abinda ke tsakanina da Alhj Rufa'i sharrine kawai irin ta Alhj imran" "Alhj dake gefe yace karya takeyi yallabai" "alkali dake zaune yace ya daga shari'ar zuwa 20-6-2018 k'uma ana bukatar gani Alhj Rufa'i a ranar" ~~~~ ~~~~ ~~~~ akace d'an da mahaifi sai Allah' cikin dabara Bbn Fatima ya lallabeta ya shawo kanta har ta saurari *Alhj AMINU* suka daidaita mgn aure a matsanisu amma da yarjejenir bazata tafi da yaranta ba' duk yadda Alhj AMINU yaso Fatima ta dauki yara sutafi tare amma Fatima I taki' a cewarta bayan kwana biyu yadda taga zamanta dashi ya kasance zatazo ta kwashi yaran " "dole yasa Alhj AMINU ya hkr amma badan yasoba dan bashida yadda ya'iyane kawai" " *FRIDAY 14-6-2018* bayan saukowa masallacin jama'a aka daura auren *Fatima da Alhj AMINU* " "Fatima dake cikin g'ida tanajin ance an daura aurenta da Alhj AMINU tasa kuka h'ade da zubewa jikin mahaifiyarta tana kiran suna Nasir" *Allah sarki rayuwa inji masu iya mgn kance Uwa mafi uba koda uba sarkine* mahaifiyar Fatima tai ta lallashinta h'ade da bata baki' kalamomi masu kwantar da hankali har Fatima ta numfasa bayan sallar isha akakai Fatima g'idan Alhj AMINU dake *G.R.A* batare da bata lkc ba masu kai amarya suna kaita Alhj AMINU yasa direbobinsa suka kwashesu zuwa g'ida' yarage daga shi sai ita a g'idan" "around 9PM abokanan ango suka rakosa'kowa yai irin tasa nasihohin snn suka tafi' duk a lkcn kan Fatima na kasa lulufe da mayafi' idan ba kuka ba babu abinda takeyi" "bayan yadawo daga rakiyane yazo sukai sallah duk yadda yakai ga abusa dole ya hkr sbd bega ido ba' washe gari bayan su karya saida ya kaita gidansu ta sallami iyayenta snn suka nufi airport zuwa London" "suna isa hotel ya kama masu suka sauka' a nan sukaci amarcinsu na tsawon 1week babu inda yake zuwa suna tare' itama Fatima h'akan be dametaba sbd duk yadda Alhj AMINU yakai tofa Nasir dinta na gabansa' h'akan yabawa Alhj AMINU damar yin yadda yakeso" "ana gobe zasu cika sati daya Alhj AMINU ya kira matarsa *Hjy Mariya* akan gobene zai taso daga Nigeria zuwa London' tace babu damuwa Allah ya kawoka lfy" "dama tunda yafara niman auren Fatima yaki bari asani sbd surutu jama'a' wanda ma yazama dole susani ya hanasu sanarwa kowa har Allah ya cika masa burinsa" "Fatima dake zaune gefe tayi mmki mgnr da yai' bayan suyi sallama ne take tambyarsa dalilin h'akan" "murmushi yai snn yace Mariya macece bame matsala ba' k'uma kinga be kamata nayi amfani da wnn damar nashiga hakkinta ba ko?" "hakane" "yawwa gobe nakeso na karisa inda take idan naje a hankali zan mata bayani yadda zata gamsu' bayan komai ya daidai sai nazo na daukeki kikoma can' ko yaya kika gani?" "babu komai" "yawwa Fatima dinta ngd sosai da Allah yasa kema me fahimtace kamar Mariya Allah yasa ku zauna lfy" "amin. ~~~~ ~~~~ ~~~~ " bayan kwanaki da dawowar zhrdee g'ida gani jikinsa ya kara samu sauki yacewa Hjy yanaso zai leka kasuwa amma ba zama zaiyi ba " "Hjy tace to saika dawo Allah ya tsare" "amin Hjy ngd" "wanka yai ya shirya cikin jallabiya fara sal ya dora d'an karami hula itama fara" "abinka da fari dama ba jiki ne dashi ba sai yafito kamar balarabe" "yana fita kasuwa ya nufa saida yaje gun Abba snn yanufi nasa shagon' yaran shagon suna ganisa duk suke mike suka basa gu ya zauna' a ladabce suka gaishesa one after the other' snn ya duduba abinda zai duba be dade sosai ya kira daya daga cikin yaran shagon ya aikesa siyo sweet dasu chocolate h'ade da kayan yara na maza dana mata bayan d'an Aiken ya dawowa ne zhrdee ya mike sukai sallama yana fita kai tsaye g'idan ta zainab yaje" "har parlour yashiga lkcn ba mmn Zainab sai innarta yarama duk suna makaranta'jin motsin mutum ne yasata cewa Zainab ta leka taga waye" "batare da musuba Zainab ta mike tayo hanyar parlour dama ido zhrdee yana kan hanyar batare data ankara taga waye a parlour ba ta kariso' zhrdee yana ganita ya sakar mata murmushi daga kanda Zainab zatayi suka h'ada ido da zhrdee yace Zainab sannu da fitowa zo gagu ki zauna" "tsaki kawai tai batare da tasake kallonsa bajuya ta koma" "gani h'aka yasa zhrdee mikewa da sauri yana fadin zo mana zahradee' Dan Allah kidawo" "ko wayge batai ba tashige" "tana shiga inna tace waye yazo?" "nima bansan suba inna" "baki snn suba kikace Zainab akwai wasu mutani dasuke zuwa nan g'idan da har zakice bakisansuba Zainab saidai kice su shige maki'amma bari naje naga suwaye" "shiru Zainab tai bata tanka ba" "inna da fara'arta ta isa parlour tana gani zhrdee takara fadada fara'arta' zhrdee yana ganita da sauri ya mike' inna na gani yana kokarin mikewa dayake tasan ba cikankiyar lfy ne dashi tace zauna kawai d'an Allah" "ko kafin takare mgn yariga ya mike' bayan ta zauna ne shima ya zauna snn suka gaisa bayan su gaisa ne inna ta mike takoma cikin d'akin" "Zainab na kwance Hjy ta shigo d'akin h'ade da cewa dama zhrdee ne yazo shine kikace bakisan ko waye ba Zainab' sbd Allah meye hakane?' wlh banji dadin abinda kikai ba wlh Zainab" "shiru Zainab tai bata tanka ba" "maza tashi ki gyara jiki kije yana jiranki"... "turo kafar *Akbar* ya katsawa inna mgn' ganisane yasata cewa jeka parlour akwai abbanka yazo" "Akbar najin h'aka a guje yafita zuwa gun bbnsa" "zhrdee yana hango abbansa murmushi kawai yai' Abba yana isowa ya rungume bbnsa'shima zhrdee rungumesa yai yana mejin dadin gani d'an'sa" "zhrdee yace Abbana ina kanwar ka?" "cikin tsami baki yace tana gurin mmna'bari naje na dauko maka ita".. " *Akbar*be rufe bakiba Zainab tafito dauke da tre ruwa ne da juice a kai fuskan nan daure babu alamar dariya" "dukawa tai ta'ije a gabansa snn ta zuba masa juice d'in a cup ta mike can gefe takoma ta zauna' tunda ta shigo kallonta kawai zhrdee keyi' gani ta koma nisa dashi ta zauna yasashi cewa *Akbar* Abbana" *Akbar* yace baba" "jeka ciki ka dauko min kanwarka" "a guje *Akbar* yaje dauko *lslaha* gani Akbar ya shige yasa zhrdee mikewa ya koma inda Zainab ke zaune' da sauri ta yunkura zata mike hannu zhrdee yasa ya riketa da sauri h'ade da cewa h'aba my wife guduna k'uma kikeyi?" "waye matarka?" "ke mana". " tabdi kawai tace' duk a lkcn zhrdee yana rike da hannu Zainab' ita k'uma tana kokarin kwace hannunta" "zhrdee yace kinga zauna d'an Allah gunki nazo mgn nakeso muyi dake kinji Zainab" "gani har a lkcn yana rike da hannunta h'akan yasata zama' tana zama ya sakar mata hannu' snn yace Zainab Dan Allah d'an annabi kiyi hkr wlh kuskurene amma wlh na rantse maki da Allah wlh idan kika koma koda da wasane bazan sake memeta abinda nake maki ba kinji Zainab" "waye zai koma g'idan ka?' Allah ya sauwake ai nabar g'idan ka kenan na har abada' ni yanzu abinda yarage tsakanina dakai shine takarka d'an shi kawai' ya batami lkcn da bakazo ka sameni a g'idan nan ba" "kae fa' da gske?' idan na baki takardan ina zaki?" "aure zanyi d'an yanzu nasamu wanda nakeso shima yana sona' wanda yasan mutuncina''.... " kafin ta karisa hannu yasa ya tushe mata baki h'ade da cewa karya dai' wlh kema kanki kinsan mgnrki zancene kawai' idan banda yaudaran kai ina kika taba gani nayi aure akan aure? Zainab kenan idan kanki ya kwance na iyayenki be kwance ba' idan nayi imani ba mahaukatane ba" "himm ta kanka akeji' nidai abinda nasani kawai takardana zaka bani" "wani irin kallon banza yai mata h'ade da mikewa yace bari na tafi sbd gani nayi kamar kinsamu matsala a kwakwalwarki tura mata ledar kayan yai gabanta' itama ido kawai ta zuba masa' har zhrdee yakai b'akin kofar parlour ya juyo yace Zainab kinsan abinda kikeso ki aikata haramune ko?" "Zainab tai banza dashi" "wlh Zainab idan har kikabar g'idan nan da suna kinfita sauraron wani katon banza banyafe makiba" "duk da h'aka batace dashi kala ba" "kai kawai ya kada snn yafita daga parlour zuwa inda yai parking din motarsa" "duk abinda zhrdee da Zainab sukeyi inna tana jinsu' ita cema ta hana Akbar zuwa da Islaha gun" "zhrdee yana fita Zainab ta fashe da kuka' jin kukanta ne yasa Inna karisowa parlour tana lallashinta h'ade da bata mgn har ta numfasa tayi shiru" "shima zhrdee yana fita motarsa ya zauna yana faman tunanin kala kala' ta hakane yake tambyar kansa to ita Zainab me take nufi ne?' tanaso tace ta daina sona kenan ko me?" kae a'a wlh Zainab bata daina sona ba' to idan da gske abinda zcyta take fadimi gsky ne yaya zanyi da soyayyar da nake mata?' ga k'uma Allah yasami so Zainab wanda h'akan yasa nakejin kaina idan ba tare da Zainab bane zanyi rayuwa aikin banza ne?' to amma idan yazamu ita a nata zcyr ba h'aka bane yaya zanyi?" "kae rayuwa kenan'allah babu ta inda baya jarabtar bawansa' a rayuwata ban taba tunanin zan tsinci kaina haka ba wai yau nine zhrdee na kasa sukuni akan Zainab' nakejin bazan iya rayuwa ba idan ba da Zainab ba' gskya nayi kuskure a rayuwata dana walakanta Zainab ban dauketa da mutunci ba' bana bata hakkin daya dace a matsayinta ta matata' duk da'itama nasan a farko kuruciyane yasa Zainab takasa babbance tsakani so da kiyayya' takasa fahimtar inda na dosa kafin aurenmu' h'ade da biyayyar iyayenta" "ita kenan yarinya taiwa iyayenta biyayya balle ni dana mallaki hankalina' meyasa nabari soyayyar Aisha ta makantar da zcyta wanda babu abinda nake gani idan ba'ita ba' soyayyar Aisha ya hanani yiwa iyayena biyayya sanadiyar soyayyar Aisha nake sabawa ubangijina nakasa sauke hakkin da Allah ya dorami' lalla ba karamin kuskure na aikata ba' idan ma Allah yasa iyayena masu fahimtane' duk da soyayyar danakewa Aisha besa tana gani iyayena da mutunci ba tunda na auri Aisha idan Safiya yayi bataci magani taje ta gaida iyayena ba' batasan idan taga hjyta tana aiki ta tayata ba' balle h'aka kawai taje ta tambyeta yadda Zainab keyi' lalla Zainab matar kirkice' dole na daura dinmaran gani duk yadda zanyi sainayi dan gani Zainab tadawo gareni" "abu na farko daya kamata nayi shine naje na roki su Hjy da Abba gafara h'ade da suzo su rokami iyayen Zainab ko Allah zaisa nadace su amince tadawo gareni' idan nasan Zainab yarinyace me biyayya da gani girman nagaba da'ita' gashi k'uma dama tanajin kunyar Hjy fiye da yadda ba'a tsammani" "dayan zcyr tace ita k'uma Aisha fa' shiru yai yanabawa kansa amsa a zcyrsa' lalla Dan so inaso Aisha amma bazan dawo da'ita ba saina nuna mata kuskurenta' Dan bazan yarda ranar lahira natashi da barin jikina shanyayye ba' idan har zatabi dokokin da zan gindaya mata kofa a b'ude yake' idan k'uma tace a'a wlh duk irin sonda nake mata zan'iya hkr da'ita na k'uma roki ubangiji ya ciremi sonta idan har h'akan shine zaisa nasamu tsira duniya da lahira" "shiru yai yarasa ta inda zai fara' can da yaga tsayuwa a g'idan su Zainab bashine mafita a garesa ba' Jan motarsa yai yabar g'idan" g'ida yanufa direct bayan yai parking d'akin Hjy ya nufa kai tsaye' yana shiga ya ganta zauna rike da kit d'in abin sarkokinta tana gogewa yana sannu da g'ida" "kadawo?" "nadawo Hjy' dukawa yai har kasa gwiwa bibbiyu yace Hjy" "na'am zhrdee lfy?" "Dan Allah Dan annabi duk abinda nayi maki kiyi hkr kiyafemi Dan Allah Hjy" "shiru tai ta zuba masa ido h'ade da mmkin zhrdee" "shirun da yaga tayine yasashi cewa kinji Hjy" "him zhrdee kenan' babu komai' ni dama bakaimi komai ba' na yafe maka Allah k'uma ya yafe mana baki daya" "amin ngd' snn ta tashi zaune yaci gaba da cewa Dan Allah Hjy wata alfarma nakeso kimin" "na mefa zhrdee?" "Dan Allah g'idan su Zainab nakeso kije ki tayaki bawa iyayenta hkr ko Allah zaisa su amince tadawo dakinta" "him zhrdee kenan ai tun ba yanzu ba mukaje da abbanka babu irin hkri da bamu bashi ba amma wlh yaki yarda Zainab tadawo' amma tunda kai mijinta ne kaje ka lallabeta ko Allah zaisa a dace" "to shikenan Hjy ngd' insha Allahu zanyi iya kokarina har Allah yasa adace" "to ita Aisha k'uma fa?" "a'a abarta k'uma" "a'a zhrdee kada muyi h'aka dakae sbd Allah ta yayama h'akan zan kasance mutum daya saba da mata uku ace yanzu babu ko daya?" "eh babu damuwa zanci gaba da maneji h'aka har lkcn da Allah zai warwaremi" "to amma gskya kaje ka dubata ita da yara" "idan nasamu lkc zanje" "shikenan Allah yabada iko" "amin ngd" "saida ya jima a d'akin Hjy snn ya koma d'aki abbanasa' gun ya samu ya kwanta amma ba bcc yakeyi ba' tunanine kala kala yakeyi ta inda zai bulowa Zainab" "bayan kwana biyu da fitar *Alhj Isa* Bbn Rukky daga prizi Malam Habu ya zaiyana masa duk yadda sukai da *Alhj imran* Bbn Rukky beyi mmkin haka ba sbd yasan abinda yafi h'aka Rukky zata aikata' tunda gashi shima da kansa ta jawo masa abin kunya a uguwa d'an ma Allah yasa babu Wanda be sansa mutumi karki bane' d'an dai ance ka haifi mutum baka haifi halinsa bane" "nidai Allah ya gani nayi Iya kokari na akan yaran nan amma duk abu betaro ya zama daya ba' amma ba laifin kowa zan gani ba sai laifin *HAbiba* wato mmn Rukky kenan' sbd duk cikin yarana ya"ya" dakinta sufi lallacewa d'an ma a tsaye nake inda ba haka ba Allah kadai yasan yadda zasu zama a cikin garin nan amma babu komai Allah yana gani' k'uma nasan Allah bazai kamani da laifin banbasu tarbiya ba sbd duk burin uba nagari ya"yan"as suma suzana nagari' kae ko lalatacce ubane balle nagari' duk a cikin zcy kenan yake mgn' Malam Habu ne ya katse masa tunaninsa da cewa ISA lfy tunanin me kakeyi h'aka? " "nanauyar ajiyar zcy Alhj isa yai snn yace himm Habu kenan wlh idan nace mgnr Rukky baya damuna nayiwa kaina karya' sbd Allah kaduba irin halin da yaranga suke niman jefani ciki fa" "to koma menene abinda ya faru yariga ya faru sai Allah ya kyau gaba' yanzu abinda nakeso dakai *Isa* shine d'an Allah kayi hkr ka shirya mutafi gwambe gurin yarinyar nan Rukky".. " sbd me Habu?' me zanje nayi mata?" "a'a *Isa* zuwan tafi' yanzu idan bamu jeba wata kila kasan yadda duniya tazama sai aga kamar duk abinda take aikawa da sanimu' amma idan muka tafi komai za'a zargemu ba kamar ace bamu jeba" "himm Habu kenan sai yadda nagani" ~~~~ ~~~~ ~~~~ washe gari da yamma bayan magrib *Alhj AMINU* yakira *Mariya* matarsa ya sanar da'ita cewa ya'iso ga shinan a hanyar zuwa g'idan ta' cikin doki da murna Mariya tace shine babu ko sanarwa balle nayi maka abinda' a'a kada kidamu duk abinda kika dafa zanci' cikin jin dadi Mariya tace to ubangiji Allah yasa kakariso lfy" "amin kawai yace snn ya kashe wayar" "cikin murna da doki Mariya ta shiga kitchen d'an h'ada masa abinci wanda bazai bata lkcn ba' tana gama h'ada sanwa a gurguje ta shige wanka' tana fitowa ta duba sanwa snn taje tasha kwalliyarta cikin riga da sket na Holland me ruwan ganye tayi kyau sosai' bayan ta gama shirine taje ta juye abinci cikin food plast takai dinning ta'ije" "Alhj AMINU tashi yai yashiga wanka yana fitowa yasa kaya snn sukai sallama ya dauki jakarsa zuwa g'idan Mariya" "yana isa Mariya a guje ita da yara sukazo suka rungumesa suna oyoyo Abba' shima rungumesu yai yaja mejin dadin gani iyalinsa cikin koshin lfy daukar karami yai hannu daya k'uma yana rungume da Mariya ita k'uma tana dauke da jakar daya iso dashi" *Mariya ba karamar yarinya bace' dan a kalla zatakai fourty years zamansu a kasar turawa shine ya kawo masu h'aka' in short kusan nace kowa yasan yadda zaman turai yake' basai na bata lkc ba wajan bayani* "suna shiga kai tsaye bedroom suka shiga ita dashi bayan ta ije jakar hannunta ta taimaka masa ya tube ya shiga wanka' yana shiga ta dauko masa jallabiyarsa ta'ije yana fitowa tasa masa suka nufi dinning' yanaci suna hira yana kururuta kwalliayar da tai masa" "Mariya baki har kunni sbd jin dadin yadda maigidanta yake yabo kwalliyarta" "suna gama cin abinci bayan ya kalli news ya mike zuwa kwanciya' dayake Alhj AMINU me wayone babu wani canji da Mariya tagani' yadda yasaba yimata duk lkcn da yai tafiya h'aka ma yau yai' da safe kuwa tai tunanin ko zai leka office ne amma yace babu inda zaije sbd be gaji da ganita ba" "h'aka suka zauna cikin karantawa juna rai' bayan magrib yace zaije siyowa yara ice cream' duk yadda Mariya taso binsa kamar yadda suka saba amma a wnn karo AMINU ya hana a cewarsa ba zama zaiyi ba" "yana fita gun Fatima ya nufa nan ma be Dade ba yasake komawa g'ida gun Mariya' h'aka Alhj AMINU yaci gaba da rayuwa batare da Mariya ta gane ba' satin Fatima daya' gani tagaji da zaman gu daya yasata sanarwa Alhj AMINU cewa zataje gun bnz din Nasir wanda a yanzu da h'aka ta dora Bilyaminu akai" "Alhj AMINU be nuna damuwa akai ba' saima kara mata mata karfin gwiwa da yai' idan zaije office yake zuwa ya dauketa ya kaita' idan tagama abinda takeyi tadawo da kanta'tunda dama ba bakuwa bace a London d'in" ~~~~ ~~~~ ~~~~ tun bayan komawa Aisha g'idan su zhrdee be lekataba tsawon satinta uku kenan gashi koda ta kirasa baya dagawa takanyi kira yakai ten miss call koda yana gani bazai daga ba' tun Aisha na boye damuwarta har yakai baya boyuwa' kusan kullum cikin kuka take' gudun kada damuwa yai mata yawa yasata b'ude wSApp koda tabude tasha ganisa a online amma koda tai masa mgn baya amsawa' idan yaga zata damesa saiya sauka' idan taga ya sauka binsa takeyi ta kirasa still bazai daga ba har wayar ta tsinke" "hankali Aisha yai mummunar tashi' cikin kwnkani lkc tarame tayi baki' ummata tayi mata nasiha har tagaji amma besa Aisha ta daina kuka ba" *dama h'aka rayuwa take yau gareka gobe ga wani* "tun daga lkcn da zhrdee yabar g'idan su Zainab besake komawa sbd koda kiranta yai a waya bata amsawa' idan yai mata text message ma haka bata reply' idan ya ganta a online yai mata mgn shima shiru' ko b'ude text d'in batayi balle tasan meke ciki" "hankalin zhrdee ba karami tashi yai ba akan abinda Zainab keyi masa' gashi babu hkr duk abinda take masa saiya sanarwa Hjy' ita dai saidai tace kakara hkr watan sai labari' amma a zcyrta ba karami dadi tajiba yadda Zainab ke gara zhrdee" "idan yakira yaga numr busy yai kamar zaiyi hauka sbd kishi""" *Allah kenan shiyasa me hakuri yana tare da rinjaye a rayuwa* 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES. F.O.W. ☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* *kuyi hkr da jina shiru wlh sai a slow ne' h'akan yasa bansoyi posting amma sbd masu yawan tambayane yasa kuka jini a yau* *_~masoya nagode da bibiyar littafin AURE IBADA NE da kukeyi Allah yabar kauna da zumuci~_* 6⃣2⃣ "h'akan yasa zhrdee ya kasa hkr' zuwa yamma bayan la'asar zhrdee ya shirya zuwa g'idan su Zainab' zhrdee yana isa Zainab na dawowa daga uguwa g'idan kanwar innarta taje gaidata sbd zazzabi da tai yasa taje gaidata" "zhrdee yana isa kofar g'idan su Zainab' Zainab itama tana isa tadawo uguwa' wani mutum ne ya sauketa daga mota' ashe zhrdee yana can akan titin area dinsu yana kallonta' da sauri yai parking ya fito daga motarsa' itako Zainab batasan yana kallonta ba' tana sauka ta dauki yar' ta h'ade da sallama har tajuya zata shige g'ida *Islaha* dake hannu mmnta tasa kuka zata bisa' sbd yadda tagansa kamar zhrdee ne a tsaye" "farine sal ga hanci har baki gashi beda jiki kamar d'an Fulani saidai tsayi' h'akan yasa tunda suka shiga motarsa *Islaha* ta makale masa sakamakon ganisa takeyi kamar bbnta" "gani kukan da tasa yasa mutumi fitowa daga motarsa yasa hannu ya dauketa yana dariya' yana daukarta tai shiru' dagashi har Zainab d'in dariya suke mata' a guje zhrdee ya kariso gun h'ade da fisge yar'sa daga hannu mutumi yana f'adin bani yan'ta d'an rainin hankali kawai' waya baka izini tsayuwa da matata?' ko an f'adi maka sakinta nayi' to idan itace wlh daga kai har ita karya kukeyi' manafuki algugumi wanda besan darajan aure ba" "duk mgnr da zhrdee keyiwa mutumi besa ya tanka saba saidai ma murmushi har ya kare snn mutumi yace h'aba Malam da hankalinka da k'uma tunaninka kake dabi'a irin ta marasa hankali' kamata yai ka tamb"... " d'an Allah Malam kaimi shiru wlh na rantse da Allah idan nasake ganika da matata kotuce zata rabamu dakai " "Zainab dake tsaye mmkin zhrdee ya kamata gani rashin mutuncin da yakewa mutumi h'akan yasata cewa d'an Allah kayi hkr d'an makwabcinmune k'uma yanada matsala a kwakwalwarsa shiyasa" "jin h'aka yasa zhrdee fusata hannu yasa ya fisgo Zainab zuwa cikin g'idan' mutumi dake dake tsaye ya dauka da gske ne mgnr da Zainab tai na rashin hankalin yasashi tsalle yashiga tsakiyar su yana kokuwa da zhrdee akan saiya saki Zainab' duk kokuwar da zhrdee keyi *Islaha* na hannunsa yaki sauketa' *Islaha* na gani h'aka tasa kuka duk kokarin zhrdee kada mutumi ya taba masa Zainab' shima dayake me addini ne duk da besan tsakanisu ba beyi tunanin rike Zainab din ba' duk kokuwar da sukeyi hannunsa yana kan na zhrdee ne" shikuma zhrdee kokarin sa yaga Zainab ta shige cikin g'ida idan yaso duk abinda zasuyi sai suyi" "Zainab na gani yadda *Islaha* ke kuka hannu tasa ta fisge yar'ta daga hannu zhrdee snn tashige cikin g'ida' ko juyowa batai ba balle tasan abinda suke ciki' zhrdee yana gani ta shige yakama mutumi da f'ada' da yake bamafadacine ba' be tankawa zhrdee ba zagawa yai ya shige motarsa yabar gun' sbd tsabar kishi da takaici zcyr zhrdee kamar yakama da wuta yakeji a fusace yaje ya shiga motarsa yabar gun' g'ida yanufa kai tsaye yana shiga dakinsa yaje ya kwanta h'ade da ijiyar zcy' a zcyrsa yana fadin bazai kara zuwa g'idan su Zainab da sunar rokon tadawo g'idana ba' to k'uma idan nayi haka ai ban nuna mata kuskutenta ba' kamata yai ya kirata koda a wayane na f'adi mata abinda ke raina idan yaso daga lkcn saina fita harkanta' tunda har tana sauraran wani banza ba niba' harma cewa takeyi banida hankali' lalla Zainab saina nuna mata kuskuren yin h'akan' k'uma daga snn na kwashe yarana da suke hannunta" "shiru yai h'ade da rufe ido kamar me bcc amma ba bcc yakeyi ba' wani irin zafi yakeji a zcyrsa wanda shima kansa besan dalilin h'aka ba' daga nan har bcc ya daukesa' bcc yai nisa da zhrdee har akai magrib da isha be saniba' kiran Aisha ne ya tadashi daga bccn dayakeyi a gigice ya tashi h'ade da daukar wayar yaga ko waye' gani Aisha ne yasashi tsaki yai hurgi da wayar" "gani after eight yasashi mikewa yaje toilet yai alwala yazo yai sallolinsa bayan yai addu'ar sane ya shafa yasake dauko wayar batare daya tashi daga kan sallayar ba yana dauka bayan ya kare dube duben da zaiyi b'ude data dinsa yai yashiga fcbk yaita karance karancen da zaiyi bayan ya kare yakoma kan WhatsApp yana hawa yaga Zainab da Aisha dukkansu su biyun kowa idan yashiga nasa sai yaga suna tp' be tanka masu ba ije wayar kawai yai ya zuwa masa ido" "Aisha na ganisa a online tai sama SLM' zhrdee yana kallo be amsa ba' tasake cewa SLM" "tsaki kawai yai yafita a gun' yakoma gun Zainab' Zainab tana kallonsa a online amma batai masa mgn ba' taci gaba da harkan gabanta' gani bazai iya hkri ba yai mata sallama da assalamu' alaikum?" "koda taga sallamarsa banza tai dashi' duk da h'aka be daddara ba yasake sallamar' gani zai dameta yasata blocking nasa snn taci gaba da abinda ke gabanta" "batare daya luraba yace Zainab ninefa zhrdee' yanzu har kece da kanki kike walakantani Zainab' ninefa mijinki k'uma uban ya"yan" Zainab' Zainab Zainab" "duk da haka bega antanka masa ba" "himm walakanci ko Zainab?' babu komai kici gaba' sauka yai ya rufe data dinsa ya'ije: wayar a gefe' can k'uma me yagani yasake dauko wayar ya kira numr Zainab' tunda yafara kiranta Zainab tana kallo amma bata daga ba' da taga zai dameta ije wayar tai a gefe tasa a slint snn ta kwanta" "tana kwanciya bcc ya dauketa' duk uban kiran da yakeyi tana bcc batama saniba' miss call kuwa yakai *30* gani wayarsa tana nuna masa betttery low yasashi hakura amma badan yasoba' ranar ko abinci beciba h'aka ya kwanta da yunwa" "da safe suna dawowa daga sallar asuba shida Abba' Abba yake tambyarsa su Aisha da Zainab' zhrdee yace duk suna lfy" "eh nasan suna lfy' hausana kana lekasu k'uma yaushe zasu dawo" "eh to Abba a gsky mgnr Zainab dai har nafara fidda rai da'ita' sbd duk yadda zanyi nayi amma taki yarda ma ta saurareni balle taji abinda naje dashi' rannan fa harda wani nadansu ya dauketa daga mota' da alama nimanta yakeyi" "a'a son' kada kabari zcy ta bata maka auren ka da'ita' kasan aure da zargi babu aure ko" "wlh kuwa Abba" "a'a son' nasan su waye iyayen Zainab' ni nafika sanin waye *Alhj Musa* wlh ko da da wasane bazai bari Zainab ta saurari wani ba da aurenta' kilan dai wani Dan' uwarta ne' Wanda ba lalla bane ace ka sansa" "himm Abba kenan" "da gske son k'uma kaje ayi bincike kaji" "to shikenan Abba" "to son yaya mgnr ita aishan?" "tana lfy itama" "nasan tana lfy kana zuwa dubata ita da yara?" "a'a Abba" "sbd me son? " ita da bance Zainab daban? " "to a gsky son idan har haka zakayi ina me tabbatar maka bazamu shirya ba' idan har kanaso mu shirya kaje ka dubosu' ni bazan matsa maka akan saika dawo dasu ba tunda baniike zama dasu ba' kai kasan halin kayanka amma kaje ka dubasu k'uma kada kaje hannu kawai" "to kawai zhrdee yace snn suka karisa cikin g'idan" "yana gama breakfast yai wanka ya shirya snn yazo ya sallami Abba da Hjy yafita' supmkt yaje yai siyayya ba laifi snn yakarisa g'idan su Aisha' tagama shirya yara kenan zhrdee yai sallama ya shigo cikin g'idan' *shihid* yana zaune akan cinyar umma' ita k'uma *shahida* tana gun mmnta' Aisha na gani zhrdee da sauri ta mike cikin doki da murnar ganisa' umma take zaune hijab tasa h'ade da gyara zama" "Aisha taje suka shiga tare har kasa ya duka a ladabce suka gaisa snn umma ta fice daga d'akin ita kuwa Aisha kitchen ta shiga ta hado masa tea sbd a lkcn safene ta jere masa a tre ta kawo zhrdee yana dauke da *shahid* Aisha ta shigo da sallamarta har kasa ta duka snn ta'ije masa a gefe bayan ta'ije tace ina kwana" "fuska a daure tace lfy klau' ya kuke?" "lfy klau" "daga snn besake mgn ba" "yawo tre d'in tea tai zata zuwa masa a cup' zhrdee a'a a koshe nake ngd" "batare komai ba ta meda ta'ije" "gefe ta koma ta zauna h'ade da baza kunni ko zai wani abu' shima bebi ta kantaba yaci gaba da wasa da yar'sa' gani su kwashi mintoci bece komai ba' ji tai kamar tai masa mgn amma k'uma batari sbd kada ya rainata' sun kwashi kusan thirty minutes babu Wanda yaiwa d'an uwarsa mgn amma duk abinda yakeyi idanu Aisha na kansa' da zhrdee ya lura da haka yakara daure fuska snn ya mike h'ade da mika mata yarinya yace zantafi dama nazo na duba yara nane" "jin haka ran Aisha ya baci' ta kasa hkri tace dama sbd yaranka kazo badan niba kenan?" "duk yadda kika dauka hkne" "haka kace zhrdee" "ta kanki akeji' ni kinga tafiya ta' fice warsa yai batare da sallama ba" "Aisha na f'adin wai zhrdee me kake nufi da nine eyye zhrdee" "ko juyawa beyiba balle yasa tanayi' Ashe duk abinda suke ciki ummata na jinsu' kuka Aisha tasa tana kuka tana masifa' ummata ne tashigo d'akin ta hauta da f'ada' duk yadda Aisha taso meta mgn umma ta hanata d'an batason jin abinda ke tsakaninta da mijinta' dole yasa Aisha ta hkr da f'adin' tai kukanta har tagodewa Allah Dan kanta ta hkr" "zhrdee yana fita kasuwa ya wuce koda suka hadu da Abba a kasuwar yake tambyar su *shahida da shahid* zhrdee yace duk suna lfy" "har zhrdee yai zcy akan bazai kara kiran Zainab ba ko yaje g'idan su amma k'uma h'akan beyuwuba d'an yakasa daurewa da h'akan' da yamma bayan yadawo daga kasuwa *around 9-30* yaje g'idan su Zainab sbd yasan lkcn abban Zainab yana g'ida" "cikin shigarsa ta alfarma babu yabo babu fallasa k'uma babu karyan arziki': ba karami kyau yai ba yaje g'idan su Zainab har parlour yashiga da sallama' lkcn mamy kanwar Zainab ce ke tana kallon wani prgm da akeyinsa a *zeeworld me suna LAALI* zhrdee yai sallama yashiga mamy dake zaune ta mike da sannu da zuwa bayan su gaisa ne yace tai masa sallama da Abba" "a guje taje tai sanarwa Abba suka fito tare' bayan ya zauna ne suka gaisa h'ade da tambyarsa lfy?" "zhrdee babu kunya yace karar Zainab na kawo Abba" "karar Zainab k'uma?" "eh wlh Abba" "murmushi Abba yai h'ade da daukar wayarsa ya kira inna yace sufito da Zainab zhrdee ne yazo" "to inna tace h'ade da sanyo hijab ita da Zainab suka fito tare" "Zainab na hango zhrdee ta daure masa fuska' itako inna da fara'arta ta kariso gun' zhrdee ya duka har kasa suka gaisa snn ya zauna" "Abba dake zaune yace surinkikine ya kawo karar yar'ki" "karar ya"ta k'uma subhanallh" "zhrdee yaya akayi ne?" "wlh inna Zainab ce nagani da wani a tsaye suna hira" "hira k'uma zhrdee?" "eh wlh inna" "ke Zainab yaushe kika zama h'aka? da aurenki zaki rinka fita kina sauraran wasu mazan Zainab' to ni wlh babu ruwana bazaki jawomi mgn ba" "ni wlh inna sharrine kawai irin tasa amma ni bantaba tsayuwa da kowa ba" "karya kikeyi k'uma' ina Wanda naganki dashi rannan" "duk abinda sukeyi abbanta ido kawai ya zuba masu kafin yafara masa" "tsaki Zainab tai h'ade da cewa *Isma'il yaron inna hasiya dine saurayina*? " Ohooo kinfi kowa sani" "a'a kae dakata' wanda kake mgn akai yaron kanwata ne fa" "eh shine' ranar da naje gaidata da batada lfy har na fito daga g'idan shine iskan ruwa ya taso gashi nariga nayi nisa da g'idan ba halin komawa' ita cikin tafiya kenan saiga *isma'il* yana dawowa aiki shinefa ya tsaya da daukoni ya kawoni g'ida' shinefa kikaji yake mgn akai" "karya takeyi inna" "wlh ba karya bane k'uma a kirasa ma a tambyesa" "kinada numrsa?" "eh!! to' gashi dai kaduba da kanka' sbd gani nake kamar nagoge wanda nake dashi" "Abba yana amsa ya duba cikin sa'a yagani' yace gashi nagani' daukar numr yai yasa a tasa wayar ya kirasa' yana pinking call d'in Abba yasa a hadfree kowa yaji' duk mgnr da Abba keyi da *isma'il* zhrdee naji har akai sallama dashi" "bayan Abba ya kashe wayar ne yacewa zhrdee kajiko' kenan dama zartinta kakeyi?" "a'a wlh Abba ba zarginta nakeyi ba' ni dama abinda yafi bakantami rai harda dariya take masa" "Abba najin h'aka yasan kishi ne kawai kecin zhrdee' snn yace amma inaso wann yazama farko k'uma yazama karke wlh koda dawasane kada nasake jin irin h'aka ya kasance' sbd bazan yarda ka shafawa yan'ta b'akin fentiba" "to Abba za'a kiyaye" "ke tashi muje mubasu gun" "suna tafiya shima zhrdee mikewa yai' gani yamike itama ta mike har ta juya zata shige daga ciki' hannu yasa ya fisgota da karfi suka fita daga parlour Zainab tayi kokarin kwacewa amma ta kasa har cikin mota ya kaita shima ya shiga cikin inda take ya zauna h'ade da rufesu daga ciki" "Zainab na kokarin turesa ta fita daga motar' dariya kawai zhrdee yai h'ade da cewa fita mana" "koda tasa hannu zata b'ude taji motar rufe gam da key' wani irin dariyar keta zhrdee yai snn yace h'aba Zainab meyesa kikemi hakane sbd Allah' ke nalura kodan kewata bakyaji ko Zainab?' dan Allah kiyi hkr kizo mukoma g'ida".. " cikin tsiwa Zainab tace wani g'idan? " "g'ida mana Zainab?" "Allah ya kiyaye' nida gidanka har abada na barsa kenan' haka kawai naje na zauna da wanda besan mutunciba duk kokarin da nake masa d'an gani na kyautata masa amma begani' dani da baiwa babu maraba, " gashi duk iya kokarin da nakeyi d'an gani na kyautata maka baka gani k'uma baka ragami' ita kuwa Aisha dayake ta fini mutunci a gunka duk da rashin biyayyarta da rashin sani darajan su basu Hjy da Abba' amma baka gani laifinta sbd YAR" lu'u'lu'uce"!!!! "lalllilahaillahu h'aba Zainab waya f'adi maki h'aka?" "h'aka ne mana" "wlh ba h'aka bane Zainab" "hakane mana' shiyasa ni yanzu nan zanje na auri wanda nakeso k'uma yake sona' wanda ba cusani ai a gunsa ba balle naje g'idansa matansa suzo sunami gori cewa aurena da mijinsu cushene"... " da sauri yasa hannu ya toshe mata baki h'ade da cewa h'aba Zainab waye yake f'adi maki h'aka sbd Allah? " "aikafi kowa sani tunda a gabanka ake komai' k'uma nayi imani inda baka f'adi masu hakaba babu wacce ta'isa ta f'ada h'aka a gabanka" "wlh Zainab ba h'aka bane kawai dai"..... "a'a basai ka rantse ba' karike rantsuwarka kawai kaje Allah ya h'ada kowa da abokin azikinsa" "h'aba Zainab kinsan abinda kike f'adi kuwa?' kinsan yadda nakeji sbd rashinki a tare dani kuwa?' kinsan yadda soyayyarki take wahalar dani babu dare babu safe harfa kasa bcc nakeyi sbd zafin rashinki kusa dani Zainab amma shine zaki iya kallon tsabar idana kina fadimi h'aka' kodan bakisan yadda nakeji bane Zainab" "koma me kakeji Allah ya yaye maka" " daka mata tsawa yai hade da cewa to wlh baki isaba Zainab da raina da lfy ta' bafa sakinki nayi ba balle kice" "Zainab najin h'aka tasa kuka tana f'adi nidai wlh babu inda zani h'aka kawai na koma kuzo kuna walakantani kaida Aisha"... " h'aba Zainab aishan me wlh na rantse maki da Allah bata iya ta walakantami keba Zainab' idan ma baki saniba yau zansanar dake wlh sbd ke nakori Aisha g'idan su' kinga ko su Abba da Hjy banbari susan dalili koranta ba".. "nidai kadaina cewa sbd nine ka kori Aisha"... " wlh sbd kece' tun daga ranar bankara zuwa g'idan su ba' idan banda Abba yaimi mgn shine naja' wlh Zainab alkawari na daulawa kaina idan baki komaba itama Aisha bazata koma g'idan ba" "kai kasani da dadin bakinka" "wlh Zainab ba dadin baki bane idan kina gani kamar karyane bari na ciro maki wayarta daga aljihu kiga text da kiran da takemi" "hannu yasa a aljihunsa zai ciro wayar' Zainab tace a'a ni babu ruwana wann tsakaniku ne" "to kiyi hkr Dan Allah Zainab wlh nayi maki alkawari insha Allahu bazan kara aikata kwatankwaci abinda da nake aikata maki a baya ba' kinji Zainab?" "naji". " yawwa Zainab dinta' amma fa banji kince kin yafemi ba?" "Allah ya yafe mana" "a'a Zainab h'akan yana nuni da ba'a yafe maka ba kenan'/idan har da gske kin yafemi cewa zakiyi ni Zainab na yafewa mijina zhrdee duniya da lahira" "ita kanta dariya mgnr yabata" "h'akan yasashi jawota ya rungumeta shima yana dariya' " gani yadda ta kwanta a jikinsa yasashi cewa yawwa ko kenan yanzu abinda za'ayi jeki ki dauko yara mutafi g'ida"... "da sauri Zainab ta cire jikinta daga nasa tana fadin wani g'idan k'uma?" "h'aba Zainab meyasa kikeson meda hannu agogo baya' bayan mugama mgn k'uma' na lura dake Zainab yadda nake sha'awarki da d'akin gani mu kasance tare ke bakyayi' idan ba haka ba yanzu fa kusan wata biyu bamu tare dake kina g'idan ku'idan banda abinda ke ko gajiya da zaman gidan bakiyi' naga wasu mata idan aka sake su har kuka sukeyi sbd basuson zama g'ida amma banda ke Zainab" "su ai kace' su k'uma daban nima daban" "to yanzu dai tunda bazaki bini yau ba zanzo na daukeki mutafi?" "nima bansani ba" "shikenan tunda hakane bari yanzu na shiga na tambayi inna da Abba" "a'a kabari kawai zan tambayesu da kaina" "yawwa ko kefa har naji dadi my Zainab' amma d'an Allah idan so samune inama gobe kidawo" "a'a wlh saidai nanda sati biyu" "na shiga uku sati biyu fa kikace' Ashe kinaso natare anan gidan kenan" "himm kawai Zainab tace' snn zhrdee yace ina wayarki?" "yana cikin g'ida" "gobe zan aiko da sako idan beyi makiba sai kiyi mgn" "Allah ya kaimu tace' nan sukaci gaba da hiransu zhrdee bebar g'idan su Zainab ba sai around 12AM snn sukai sallama h'ade da daukar kudi yabata ko zata bukaci wani abu" "washe gari zhrdee yana fita kasuwa waya yasiye d'an karere h'ade da zannuwa masu kyada tsada yabawa yaron shagonsa ya kaimata har g'ida" "Zainab ta nunawa innarta kayan' Inna tace Allah ya amfana" "tun daga lkcn kira da chat akai akai wani lkc har gajiya takeyi da zhrdee" "tun daga lkcn zhrdee besake zuwa gun Aisha ba' itama da rashin hkri koda ta kirasa baya dagawa k'uma besa tayi fushi' ta daina kiran ba' kullum cikin kiransa take tai kuwa baya kirguwa duk zhrdee yana tarasu batare daya krantasu ba" "duk da ba fita takeyi ba amma saida Aisha tasamu labarin Zainab zata koma gidan zhrdee' shiryawa tai ta musanman tacewa ummata zata g'idan ubaida' Aisha na fita bata tsaya ko'ina ba sai kasuwa shagon zhrdee" "duk da mmkin ganita da yai amma sai ya matse sbd kada yaran shagon sa susan halin da suke ciki' da fara'arsa yace har kin kariso?' kawo *shahida* sbd itace ke rike a hannu' yana daukarta suka shige cikin shagon' inda yake zaune yace ta zauna" "tunda suna zauna babu wanda ya tankawa d'an uwarsa' saima daure fuskan da zhrdee yai mata' jin motsi za'a shigone yasashi mikewa da fara'arsa yace tashi muje g'ida' yaran shagon a ta waje yatsaya yai sallama' tare suka fita daga cikin dakin karami dakin ganisa yasa zhrdee cewa bari naje na dawo" "a motarsa ya dauketa koda suka shiga be sake mata fuskaba har suka isa kofar gidan su' bayan yai parking har ta b'ude zata fita yace dakata" "tana tsayuwa yace da iziniwa kika fita' k'uma waye yace kibini kasuwa' yaushe muka fara haka dake?" "Aisha ja gani h'aka tasa kuka' ba kuka na tambayeki ba' amsa nakeson ji daga gareki" "cikin kuka take cewa d'an Allah kayi hkr sbd binka kasuwa danayi' amma k'uma abinda yasa na bika sbd koma na kiraka baka dagawa k'uma idan nayi mata text bana gani reply" "shine akace ki biyoni kasuwa?" "a'a ji nayi ance Zainab zata koma shine nazo na tambyeka har danine zankoma?" "idan inada bukatar ki koma da ban sanar dake ba?" "ko akace maki ita Zainab d'in gaban kan tayi batare da izinina ba?" "h'aba zhrdee meye haka sbd Allah? laifin me nayi maka h'aka?" "wlh Aisha idan ta nine babu abinda kikai mi' saidai Zainab" "ita tace nayi mata wani abu?" "wlh Zainab batace komai akanki ba' amma kinsan idan Zainab bata yafe manaba Allah ma bazai yafe mana bako?' wlh Aisha ba karami cutar Zainab mukeyi ba nidake' a lkcn soyayyarki ya rufemi ido bana gani kowa sai ke Aisha' kekuma kikai amfani da wnn damar kike yadda kikeso' Aisha tunda na aureki koda da wasane bantaba gani safiya yayi kinje kin gaida Hjy ba balle Abba' Aisha bakisan mutunci iyayena ba da yan'uwana' kinfi kowa sani banida wani gata a duniya face su' duk wani mataki da zantaka sune sila amma besa ki dubesu da wnn darajan ba' wnda nayi imani ida iyayenkine bazaki iya masu haka ba' wlh Aisha sbd ke yasa na daina jin mgnr iyayena' na daina masu biyayya duk sbd ke' wlh Aisha nayi nadamar aurenki".... " toni ina ruwana?" "wlh idan bakimin shiru ba a yadda nakeso yanzu saina rubuta maki takardanki".. " tunda Aisha taji haka bata sake mgn ba" "zhrdee yaci gaba da cewa wlh Aisha kinban mmki asanadiyar najasa yiwa iyayena biyayya' sbd soyayyar dake tsakani da da Uwa ko uba yasa suka nimamin auren Zainab amma sbd soyayyar ki nakasa rike amanr da suka bani' inda ace su mutu kafin na rokesu gafara ba' yaya kikeso nayi" "Aisha sbd soyayyar ki har sabawa ubanagijina nakeyi na dauki hakkin wata nabaki baki taba nunami h'akan da nakeyi ba daidai ba ne' na lura dake Aisha idan za'a bakanta ma wata ke a faranta maki ba damuwarki bane" "to wlh bazan yarda ba Dan bazan yarda sbd ke ranar lahira natashi da barin jikina a shanye ba' idan har zakibi yadda Allah yace kofa a b'ude take idan k'uma ba hakaba Allah ya h'ada kowa da abokin arzikinsa' wawiya mara kunyar banza kawai' wlh Aisha dukan abinda kikemi inda Zainab ce bazatayiba' sbd Zainab tafijin mgn ta' gashi sbd rashin jin mgnrki zakisa abanza kawai" "to bari kiji nagaji da irin wnn halin taki' idan bazan yarda Allah yakamani da laifi ba" "kuka kawai Aisha keyi har zhrdee yakare mgnrsa'ga yara a hannunta da suke bcc" "bayan ya karene tace to yanzu wani hukunci ka yanke akaina?" "idan har kinason zama dani saikinje kinbawa Zainab hkr' dan ita muka zalunta k'uma kece sila ga duk abinda na aikata" "naje nabawa Zainab hkr kace fa?" "kwarai da gske' ko ban'isa bane?" "ka'isa amma bazani ba saidai idan sanadiyar haka yazamo itace silar rabuwarmu dakai" "alhamdllh' tunda ke kika zabi haka' Allah ya h'ada kowa da abonki arzikinsa" "Aisha tace amin" "fitami daga motata" "batare da musuba tabude ta fita rungumeta da yara a hannunta" "ina zaki kaimisu?" "shiru Aisha tai ta zuba masa ido" "ko kallon ida take beyiba yace zubami yarana" "Aisha dake tsaye tasake fashewa da kuka" "da kefa nakeyi ko bakiji abinda nake fadi bane?" "Aisha najin h'aka ta zuba masa yaransa a mota' hannu yasa ya jawo murfin motar yarufe snn ya fisgi motarsa yabar layin" "ihu tasa tashige cikin g'ida tana kuka" ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES. F.O.W. ☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* 6⃣3⃣ "Aisha tana shiga cikin g'ida da ihu tana kuka' jin kukanta ne yasa umma fitowa a guje daga dakinta h'ade da tambyar lfy Aisha?" "cikin kuka Aisha ke cewa umma zhrdee' zhrdee umma" "zhrdee' me yasamu zhrdee d'in Aisha?" "zhrdee ummata wayyoo zhrdee" "mutuwa ne zhrdee d'in yayi komai Aisha?" "kukane yaci karfin Aisha yasa takasa mgn" "gani h'aka yasa umma ta kama Aisha zuwa d'aki' bayan su shiga dakine umma ta dauki waya ta kira Abba bbn Aisha a kasuwa' yana gani kiran hafsatu ya daga sbd yasan ba kasafai take kiransanba idan yana kasuwa sbd wasu lkta yana cikin jama'a" "yana daga bayan su sake gaisawa cikin natsuwa Abba yace lfy umman yara?" "murmushi umma tai snn umma tace dama Aisha ce bayan ka fita kasuwa itama ta sallameni akan zataje gidan su ubaida"" "shiru umma tai' alamar jijina" "Abba dake rike da waya a kunnisa yace umman yara ina sauraranki" "snn umma taci gaba da cewa shine ta dawo g'ida tana kuka h'ade kiran suna zhrdee k'uma babu yaran data fita dasu' nayi iya kokarin wajan tambyrta amma bata bani amsa ba" "to meya sami zhrdee d'in?" "wlh nima ban sani ba" "to bari ba kira Alhj Kailani naji" "to ina sauraranka" "to yace h'ade da kashe wayar' ya kira Alhj Kailani'bayan su gaisa Alhj yace lfy?'gani ba yasaba kiransa bane yasa Bbn zhrdee tambyarsa' abban Aisha ya shashe da lfy klau' ya g'ida da yaran?" "kowa lfy" "gani bece dashi komai ba yasashi be f'adi dalilin kiransa ba' SAI yace dama kwana biyu ne bajika yasa nace bari na kira mu gaisa" "aiko nagode sosai Allah yabar zumuci" "bayan su sallama ne Bbn Aisha yake tambyarsa kansa cewa to kodai ba zhrdee d'in sa bane' to idan ba shiba mezaisa Aisha ta tada hankalinta h'aka?" kodai iyayensa basusan abinda ya faru dashi neba?' kae ba h'aka bane' to kodai sakinta yai snn k'uma ya amshi yaransa' kae koma menene ubangiji Allah ya jishemu alkairi" "abban zhrdee shima mmki yakeyi h'ade da juyayin kiran da Bbn Aisha yai masa' a daya bangaren k'uma ya tunanin kodai akan mgnr Aisha da zhrdee ne yasa shi kira amma k'uma yakasa tambya' amma koma menene insha Allahu yau idan nakoma g'ida zan tambyi son naji dalilinsa nayi h'aka" "kai tsaye g'ida zhrdee ya nufa da yaransa' bayan yai parking ya kwashi yaransa ya rungumesu zuwa bangaren Hjy' ganisa da yara yasa Hjy tambyr lfy h'ade da mika hannu ta amshesa yaran" "saida ya zauna snn tasake tambyarsa' zhrdee yace eh amsosu nayi" "meyasa ka rabasu da mamarsu?' kodai kadawo da'ita ne?" "a'a ban dawo da'ita ba' tana g'idan su" "kamar yaya zhrdee ka b'ude ka warwaremi kaimi bayani ta yadda zan fahimta" "eh to rabuwa mukai da'ita" "salati Hjy tasa da lallalami tana tambyar garin yaya?" "rabuwa mukai da'ita na saketa...kaeeee subhanallh h'aba zhrdee kanka daya kuwa' meyai zafi h'aka' to wlh baka isa ba' k'uma Abba zandawo NA sanar masa' banda rashin hankali irin take waya cemaka ana saki haka kawai' saki banza ne? idan wani abu tai maka meyasa bazaka sanar manaba SAI kaje ka yanke hukunci da kanka' to wlh bari kaji idan ma ganinane yasa kake h'aka garama kabari idan nine yau gobe bani bace' sbd h'aka ga yaranka nan ka medasu gun mamansu' bazanyi wahala dakai naji da yaranka ba"..? " zhrdee naji haka ya mike yabar d'akin ".. kae kae zhrdee ba dakae nake ba?" "koya wayga balle yasan tanayi" "da umma taji shiru yasata kiran Bbn Aisha taji yadda suke' yana shagon koda yaga kiran be daga ba har yagaji ya tsike" "itama be daga ba yasa ta hkr da kiran' itama Aisha da taga uwar bari d'an kanta ta hkr da kukan" "da yamma bayan ya dawo daga kasuwa' lkcn yaran duk su bcc suka cikin hira da Hjy ne Amatullah ta kawo Husaina tatashi daga bcc tana kuka yasa takawota gun Hjy" "Abba yana ganita yace yaushe amaryata suka dawo?" "murmushi Hjy tai snn tace dama akwai mgnr da nakeso muyi amma bari nayi ka huta tuku" "lfy ko?" "a'a lfy klau " wlh Hjy dazu ina kasuwa kakan yaranga ya kirani duk da becemi komai ba amma a nawa tunanin sai nake gani kamar akan mgnr son ne da matarsa' amma k'uma tunda sun daidaita shikenan" "murmushi Hjy tai snn tace dama mgnr nasune Alhj" "nasu k'uma?" "eh wlh" "kana kasuwa ne zhrdee ya kwaso yaranga ya kawosu' koda na tambyesa shine yake cewa wai shifa ya sauwake mata".. " subhanallh wnn ai mgnr banza yakeyi' ina son d'in yake?' bansaniba ko yana ciki' bari na kirasa ta waya" "kiran farko zhrdee ya daga wayar h'ade da sallama' Abba yace kazo inason ganinka yanzu nan" "to kawai yace snn ya mike zuwa gun kiran abbansa' dama yana cikin g'idan ba fita yai ba" "da sallama zhrdee ya shigo d'akin' shahida na gani bbnta ya shigo tasa kukan ya dauketa' gani shure shuren da takeyi yasa zhrdee daukarta snn tai shiru' gu yasamu ya zauna a kasa' Abba da Hjy k'uma su kan cushion zaune" "Abba yace son bayan nadawo kasuwa ne Hjy take fadimi wata mgn amma ban gasgantaba nace sai naji ta bakinka" "eh hakane Abba" "kamar yaya h'aka ne' idan ban fahimta ba" "abinda Hjy ta f'adi maka" "a'a son kada muyi h'aka dakai' amma koma menene nafiso kaimi bayani da kanka ta yadda zan fahimta" "eh laifi taimi ni k'uma da sharadan dana gindaya mata idan har tanason cigaba da zama dani' ta nunarmi bazata iya ba shine nace shikenan ta tafi kawai Allah ya h'ada kowa da abokin arzikinsa" "amma dai babu saki ko my son?" "shiru zhrdee yai" "son dakaifa nakeyi" "Akwai" "subhanallh' h'aba son meyasa ka aikata haka?' kamar kabada manya?' meye amfanimu?' wlh banji dadin abinda ka aikata ba kwata kawata son" "to kayi hkr Abba" "yanzu saki nawa kayi mata?" "dayane Abba" "alhamdllh' Allah ya kiyaye gaba" "amin Hjy tace" "kabata takardan ne?" "a'a batama sanda saki ba" "yanzu ina takardan yake?" "ban rubuta bako" "to shikenan yanzu abinda nakeso dakai shine kayi hkr' idan kana biyewa mata SAI ku hadu ku zama iri daya' yanzu dai kaje ka dawo da matanka".. " wafa kenan' Abba? " "Aisha da Zainab mana" "kae Abba idan Aisha ce na hkr da'ita" "sbd me son?" "kawai dai haka Abba" "a'a son ban yarda ba' rankane kawai ya baci amma nasan kanason matarka" "Allah kuwa Abba"... " kae son' banaso na tsaya muna h'aka dakae' nasan yadda kakeson Aisha kawai bacin raine yasa kacewa haka" "Allah kuwa Abba". " kae son' koda zaka kwana kana rantsuwa ba yarda zanyi ba" "wlh Abba idan har bazatabi umarninaba wlh na hkr da'ita" "kae son" "na'am Abba" "ina aishan take?" "tana gidan su?" "tashi muje na rakaka ka meda yaranga' k'uma nabaka nan da sati kaje kadawo da matarka' banason kace uffan sbd umurni nabaka" "mikewa Abba yai h'ade da cewa kae nake jira' gani haka yasashi shima ya mike suka fita' Abba da kansa yake driving' zhrdee yana rungume da yaran babu wanda yai mgn tunda suka fara tafiya har suka isa" "a wnn kara zhrdee kin shiga gidan yai a b'akin kofar gidan suka tsaya shida Abba' zhrdee ya nimo yaro ya aikesa ciki yai masa sallama da abban Aisha' da fara'arsa yafito' gani Alhj Kailani ne yasashi cewa su shigo daga cikin g'idan' Aisha najin ance abban zhrdee ne yasata naunayar ajiyar zcy' duk da batasan abinda yake cikin zcyr zhrdee ba" "bayan su gaisa ne abban zhrdee yace bayan nadawo kasuwa ne Hjy take fadimi abinda yafaru tsakani yaran nan" "kae Alhj kenan' wlh babu komai dan nasan ruwa baya tsami banza' haka kawai zhrdee bazaiwa Aisha haka ba' k'uma ni kaina nasan inda tanada gsky da tazo g'ida data f'adi abinda ya hadasu amma dayake batada gsky tunda ya korota daga hospital har izuwa wnn lkcn babu abinda tacewa kowa dake gidan nan" "h'aka ne amma ai"... " a'a Alhj Kailani kada muyi haka dakai' wnn Ai tsakanisu ne' wlh idan ta ninema Aisha bwzatakai wnn lkcn a g'idan nan ba' amma a yanzu idan suka daidaita tsakanisu ya dauketa sutafi" "to Alhj nidai wlh banida abinda zance saidai godiya ubangiji Allah ya kara girma da daukaka" "amin Alhj Ai duk yiwa kaine" "snn Abba ya juya gun zhrdee h'ade da cewa to kai son kaji abinda abbanka yace" "eh naji k'uma ngd" "yanzu tazo muje ko?" "a'a ta zauna kawai Abba" "haka son meyasa kake h'aka?" "a'a Alhj duk yadda akai akwai abinda tai masa' nidai inaso koma menene abi abu a hankali" "shiru Abba yai h'ade da hararan zhrdee" "shiko zhrdee ko daga ido beyiba balle yasan Abba yanayi" "gani haka abban Aisha yace bari na turo maka ita ko' mikewa yai ya nufi d'akin ummata' abban zhrdee yanaji haka shima ya mike har Abba yakai b'akin kofar sukai karo da Aisha' dukawa tai har kasa ta gaidasa snn ta mike ta karisa ciki inda zhrdee yake" "zhrdee yana gani ta ya kara daure fuska har kasa ta duka tace ina yini" "lfy kawai yace daga snn besake mata mgn ba" "gun tasamu ta zauna a gabansa h'ade da tsaresa da ido" "gani irin kallon da take masane yasashi cewa lfy?" "cikin sanyi murya tace kayi hkr Dan Allah" "hkr me kike bani?' bayan kince kin hkr dani' ni yanzu babu wani abu daya rage tsakanina dake' ki tashi ki tafi kawai" "jin h'aka yasa Aisha fashe da kuka h'ade da zubawa shahida ido dake hannunsa" "kintashi kije kawai' k'uma zan aiko maki da takardan sakinki" "jin haka yasata kara ruwa wani kukan h'ade da rike masa kafa tana kuka" *ba komai yatada hankali Aisha illa irin soyayyar da takewa zhrdee' Dan a yanzu ji take idan ba zhrdee ba bazata iya rayuwa da kowani da namiji ba. Dama h'aka rayuwa take duk abinda ka walakanta wataran sai kanima ido rufe. tamance lkcn da itama taiwa zhrdee h'aka lkcn dayake h'au kan sonta* "gani irin kukan da takeyi yasa zhrdee mikewa h'ade da rungumar yar'sa zai fita' a guje Aisha take tasha gabansa ta zube gwiwa bibbiyu tana kuka' fisge kafarsa zhrdee yai yana kokarin fita" "gani h'aka yasa Aisha cewa Dan Allah katsaya wlh naji k'uma NA amince duk abinda ka umarceni zanyi idan har zaka barni na koma dakina' duk zhrdee yaji dadin haka amma be nuna mataba saima kara daure fuska da yayi" "cikin kuka Aisha take fadin Dan Allah zhrdee' Dan Allah" "fuska a daure yaji naji' amma kafin nace komai sai kinje gidan su Zainab kin bata hakuri snn zansan abinda yadace nayi' k'uma idan kinje ki kirani lkcn kuna tare sbd ba tabbatar da kinje" "cikin muryar kuka tace naji kuma na amince" "bayan ta mikene ya mika mata yaran snn yafice batare da sallama ba" "koda zhrdee ya shiga mota becewa Abba komai ba' shima Abba bece da komai ba har suka isa g'ida" ~~~~ ~~~~ ~~~~ *COURT* "20-6- 2018 a yau ne ranar da su Rukky da su Alhj Rufa'i da Alhj imran da k'uma Bb idi megadi duk suka hadu a court h'ade da k'uma Bbn Rukky da Malam Habu" "snn alkali yace yana bukatar gani Alhj Rufa'i yafita ya sake gabatar da kansa a gaban kowa" "bayan Alhj Rufa'i ya gabatar da kansa' snn alkali yace Alhj imran yana zarginka da cin amanarsa kae da matarsa Rukky' ko kanadaja akan h'akan?" "a gsky banida jan akan h'akan" "ko zamusan dalilinka nayi h'akan a matsayinka na shakikinsa?" "eh to h'aka yafarune sakamakon Rukky ta kasance me shegen son kudine' shiyasa ni k'uma nayi amfani da wnn damar wajan gani nayi amfani da wnn damar nasamu biyan bukatata na niman kujeran da Alhj imran yake nima" "har a zcyta banso wani kazamin alaka ya shiga tsakanina da'ita ba amma babu yadda zanyine sbd ne yasa" "kamar yaya babu yadda zakayi?" "shiru Alhj Rufa'i yai" "snn alkali yace kenan' kai kasa tanimi kashesa sann k'uma bayan ku kashesa SAI ku kwashe masa dukiyarsa ko?" "a'a wnn k'uma aikintane bansan da haka ba' idan nima kaina ba karami kudi ta satanmi ba" "koda alkali ya juya kan Rukky' duk abinda Alhj Rufa'i ya f'adi akan Rukky bata musaba" "snn juya gun Alhj imran yace to kae kaji duk abinda sukace' yanzu me kake bukata a gunsu?" "ranka ya dade babu wani abnida nakeso illa Rukky ta dawomi da kudina' Dan wlh sisi bazan yafe mata ba' shikuma Alhj Rufa'i yaje shida Allah' Allah kadai zai sakami akan abinda yaimi ba mutuba' na barsa da fitan rana da komawarsa" "toke Rukky kinji abinda Alhj imran a kanki' ko kibadana cewa?" "a'a bandashi ranka ya Dade" " snn alkali ya yake da cewa ina yar'uwanta? " "Rukky ta nuna bbnta" "koda alkali ya tambyesa' cewa yai duk da yanada abinda zai fanshi Rukky dashi amma ba zaiyiba sbd yanaso h'akan yazama ezina a gareta' ba ita kadai ba ga duk me hali irin nata' Dan haka duk hukunci daya dace ayi mata kawai" "h'akan yasa alkali ya yankewa Rukky zaman gidan yari NA tsawon shekara uku' batare da taraba" ~~~~ ~~~~ ~~~~ washe gari bayan Aisha ta kare aikinta zata tai tai shiru tana tunanin ta'ina zata fara gashi a yadda takeji yanzu bazata iya rabuwa da zhrdee ba'kuma a daya bangaren tana gani idan taje gidan su Zainab ta bata hkr tana gani wani ci bayane a gareta' wata zcy tace kada kije Aisha' wata zcyr k'uma tace shi kije idan har ba h'aka kikaiba kinaji kina gani kaidai ki hkr da zhrdee " "wuf tai ta mike h'ade da shiga wanka' kwara ruwan kawai tai tafito tazo tasa kayan h'ade da kwashe yaranta ta rungumesu snn taje d'akin umma tace umma saina dawo" "ina zuwa h'aka?" "yarane zankai alluran riga kafi" "shine da rananan h'aka?" "mancewa nayi wlh" "yimaza kudawo lfy" "amin tace snn tafice' tana fita ta nimi napep zuwa area d'in su Zainab" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES F.O. W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* vote me on wattpad gmail:hauwaszaria@mail.com 6⃣4⃣ "Aisha tana sauka a napep gefe guda ta koma ta tsaya tai shiruuu tana tunanin ta'ina zata fara' h'aka kawai iyayen Zainab su ganta a gidan su'to idan su tambyeta me tazoyi tace dashi me?' badai nace zhrdee ne yace nazo nabawa Zainab hkr ba" "to idan ba h'aka ba k'uma mezance ya kawoni gunta tunda Susan ba wani zaman dadi mukai da'ita ba' balle ace idan babu daya kaji wani irin' anya Aisha bazaki koma g'ida kawai ba' idan yaso ki hkr da zhrdee din ba" "wata zcyr k'uma tace yanzu idan har kikace kin hkr da zhrdee shikenan kedashi' a'a Aisha idan har haka shine magani matsalarki gara kije kibata hkrn kawai zaifi maki' amma idan kikace bazaki a yadda zhrdee yakeji yanzu zai iya hkr dake' k'uma idan har h'akan ya kasance shikenan fa dake zhrdee kun rabu kenan' a wani bangaren k'uma tana tambyar kanta anya kuwa zhrdee zai iya hkr dani kuwa' kisan ba karami so zhrdee yake makiba' ba lalla bane mgnr da yai yakai har zcyrsa' koma g'ida kawai' da kansa zai biyoki" "wata zcyr k'uma tace a'a Aisha idan har kikai haka zaki aikata babban kuskure a rayuwarki'tafiya kibawa Zainab hkr kawai mafita a gateki'idan har ko kika dake ta zcyrki lalla zakiyi babban kuskure na har abada' zhrdee k'uma da kike mutuwarsa kin rasashi kenan' shima har abada" "gani yadda takeso zhrdee a birkice Aisha ta juya ta shige gidan so Zainab''dama a gefen gidan take tsaye' har cikin parlour tai sallama' lkcn inna da Zainab ne suke zaune sai k'uma mame kanwar Zainab wacce ta kare junior waec dinta shiyasa bataje sch ba' " duk da Zainab tai mmkin gani Aisha amma be hanata amsarta ba' cikin zafi nama h'ade da fara'arta ta mike tana fadin Aisha kece yau a gidanmu h'aka?' hannu tasa ta amshi shahida dake rungume a kafadar Aisha' snn Aisha ta kariso daga ciki" "bayan su gaisa da inna mikewa tai ta shige daga ciki' ita Zainab d'in mikewa tai taje kitchen ta dauko mata abinci da ruwa snn ta dawo' mame dake zaune ta amshi addu'a yaran suka shige dakinta suna wasa tare" "bayan Zainab ta dawo suka sake gaisawa snn tace Aisha lfy kuwa? " wlh Zainab gunki nazo" "guna k'uma?" "eh wlh Zainab" "Allah yasa dai lfy" "murmushi kawai Aisha tai" "mikewa Zainab tai h'ade da cewa tashi muje daga ciki' dakin inna' bayan su zaune ne Zainab tace Aisha ina sauraranki" "saida ta danyi gyaran murya snn ba komai bane dama zuwa nayi na rokeki akan duk wani abu da yafaru a tsakanina dake' Dan Allah kiyi hkr ga duk abinda ya faru a baya insha Allahu h'akan bazai sake faruwa ba kinji Zainab" "himm tace snn tasake cewa Aisha kenan' ni dama wlh ban taba kwana dake a zcyta ba k'uma dama duk abinda kikeyi nasan Akwai rana irin wnn tana zuwa amma tunda har kingane h'akan Allah yasa har cikin zcyrkine' Allah yasa kinyi tuban da bazaki sake komawa ba da shi' na tafe maki Aisha ubangiji Allah ya yafe mana duniya da lahira" "amin Zainab ngd" "ga abinci kici" "kada kawai ta tsakura snn ta ije'sukaci gaba da hiransu' suna cikin hira saida kiran zhrdee ya shigo wayar Zainab' Aisha dake zaune da gefen ido ta leka' gani numr zhrdee ne yasata dauke kanta gefe' Zainab tana dagawa hade da sallama" "amin' amaryata ya kike?' ina fatan kina lfy' inaso yarana' duk a lkc daya zhrdee ya tambyi Zainab" "murmushi tai h'ade da fadin duk suna lfy" "what about u?' "nrml" "alhamdllh' yanzu me kikeyi?" "babu komai' ga Aisha tare dani" "kafi taji abinda zaice ta mikawa Aisha wayar h'ade da mikewa taje kitchen dibo abinci" "da sallama Aisha ta kara wayar a gefen kuunita' amin kawai yace' gani a gidan su Zainab din" "kinyi abinda na umarceki ko kuwa" "eh nayi" "naji' ki tashi ki koma g'ida haka' to kawai tace ya kashe wayar' bayan Zainab ta dawo Aisha tace ni zantafi Zainab" "to Aisha ngd gaida su umma" "zasuji' suna fita Zainab taje dakin su mame ta amshi yara tazo ta rakata har b'akin titi ta h'au napep snn ta juya ta dawo g'ida' bayan ta dawo ne inna take tambyeta me yakawo Aisha gidan nan?' Zainab ta sanarwa inna abinda tazoyi" "duk da bata gamsu da mgnr ba amma cewa kawai tai Allah yasa da gske nan har zcyrta" "koda Aisha ta koma g'ida bata bari umma ta gano inda taje ba' tana shiga g'ida dakinta kawai ta shige ta kwanta tana juyayin al'amarin duniya sbd koda da wasane bata taba kawo dede da rana daya zhrdee zai iya mata haka ba' amma gashi yau ita yake turawa taje tabawa Zainab hkr', wasu kwallane suka zubo mata ta gefen ido" "da yamma gam da magrib saiga kiran zhrdee yashigo wayar Zainab' suna tare da inna a kitchen bayan tai receiving call din tafice a guje zuwa dakinta innar' dayake inna ta gane murmushi kawai tai' Zainab na shiga d'aki h'ade da fadin hello" "Zainab" "na'am" "me kikeyi yanzu?" "babu komai sallah ne zanyi" "OK nima ganinan zuwa g'ida".. " gidan mu" "eh' gidan ku" "Allah ya kawoka lfy" "amin ngd" "suna kashe wayar Zainab ta shiga wanka bayan ta fitone tai sallah gani har anfara kiran isha yasata hadawa gaba daya tai kawai snn tai kwalliya cikin material orange colour ba karami kyau tai ba' tana fitowa daga d'aki sukai karo da inna' mmki ya kama Inna' tace kae ya'ta wnn irin kwalliya h'aka' kodai surikina yana tafene?" "murmushi kawai tai batare da amsa ba" "gani h'ak yasa Inna kwashe yara tai masu wanka' ko kaya ba'a sa masuba duk sukai bcc" "eight daidai saiga zhrdee yai sallama yashigo har parlour' dukawa yai suka ya gaida Inna' bayan su gama ne inna taja su mame suka shige daga ciki" "inna na shigewa zhrdee yazo inda Zainab take zaune shima ya zauna h'ade da kallonta yana aika mata da wata shu'umin murmushi h'ade da daga mata gira' matata kinyi kyau fa' kara bakinsa yai daidai kunnita yana fadin menene shirin wann irin kwalliya h'aka" "kunyane ya kama Zainab hannu tasa ta rufe fuskanta tana masa dariya" "hannu yasa ya cire mata nata hannu yarike gam' duk yadda Zainab taso ta kwace hannunta takasa' motsin dayajine yasashi sake mata hannu' mikewa Zainab tai' da sauri yace ina zaki?" "abinci zan dauko maka" "a'a kibarshi kawai' ngd" "Abba yadawo kuwa?" "eh' yadawo yana d'akin sa" "to yaya zamuyi yanzu sbd gunsa nazo" "saidai na fadiwa Inna ta f'adi masa" "OK ina jiranki" "da zafin namarta taje ta sanarwa inna' ita k'uma inna ta fadiwa Abba suka fito tare' zhrdee dake zaune yana ganisu ya mike' bayan su zauna ne shima ya zauna" "Abba yace gani zhrdee ance kanason ganina" "eh dama akan Zainab ne" "to lfy?' kodai wani laifin tasake yimaka?" "a'a' dama nazo rokon arzikin inaso ta koma ne" "takoma Inna k'uma?" "murmushi yai h'ade da cewa dakinta" "zahradee kenan' ni dama tun farko ban hana Zainab komawa gidan kaba' abu dayane kawai bazan lamunta dashi ba' shine bazan baka Zainab kaje kaci gaba da walakantami itaba ba' rashin sani mutunci ta yasa har matanka suke mata gori da cusa maka ita akayi' wlh Allah ma shedane zhrdee mahaifinka da kansa yazo ya nima mak auren Zainab' bani nakai tallanta ba balle kace h'aka' ko a lkcn da Alhj Kailani yazo nima maka auren Zainab nariga nayi mata miji' k'uma badan ta rasa masoyaba saidai gudun irin h'aka' k'uma inda nasan zanbaka Zainab kaje ka azamtarmi da'ita wlh da ban baka itaba' idan bangaji da'ita ba" "inna dake gefe tadan shafi kafar Alhj alama yai hkr" "Abba yaci gaba da cewa wlh zhrdee' albarkaci mahaifika kawai kaci" "jin haka yasa zhrdee' ya duka har kasa yana cewa Dan Allah Abba kayi hkr' wlh kuskure k'uma insha Allahu h'akan bazai sake faruwa ba" "ni yanzu Allah yagani idan da na takura mata akan zaman gidan ka' yanzu bazan takurawa Zainab akan zaman gidan kaba' idan taga zata koma wnn ruwanta ne idan k'uma tace a'a shikenan' ke Hjy jeki ki kirami ita" "zhrdee na duke bece kala ba' inna ja shiga suka fito tare da Zainab d'in' kusa da inna Zainab ta zauna' Abba yace Zainab ga mijinki nan yazo akan yana bukatar kikoma gidansa' yaya kika gani?' kinada ra' ayi koko a'a?" "shiru Zainab tai kanta a kasa" "zhrdee dake duke ido kawai ya zuba mata" "Zainab dakefa nakeyi' idan bakida ra'ayi babu me takura maki" "inna dake zaune dayake tariga ta ganosu cewa tai Alhj tunda kaga tayi shiru sunriga su daidaita tsakanisu" "wai h'aka Zainab?" "hannu tasa ta rufe fuskanta' " to shikenan Allah ya kara hkrin zama' amma wani hanzari ba gudu ba zhrdee' wlh koda da wasane Zainab tasake dawowa gidan nan da sunar kasake aikata abinda kai a baya' kae ko matarka wlh bazata sake komawa gidan ka".. "a'a Abba insha Allahu hakama bazai faru ba" "to shinan ga matarka nan ka dauketa kutafi" "cikin jin dadi zhrdee yace a'a Abba Dan Allah hkr zaka karayimi zuwa jibi sbd akwai gyara da zanyi a gidan" "to shikenan' duk lkcn da ka kammala kazo ka dauketa' Abba ya karisa mgnr ne da mikewa shida inna suka shige ciki' bayan su shine zhrdee shima ya mike h'ade da riko mata hannu ya jata zuwa waje har cikin mota ya kaita snn ya sakar mata hannu' shima shiga yai snn ya jawota ya rungumeta yana f'adi wlh Zainab da Abba yafara mgn babu abinda gabana keyi idan ba faduwa ba' rsorona daya kada yace bazaki koma ba' kenan ngd sosai da hadin kai da kika bani' k'uma insha Allahu zanyi kokarin kiyaye duk wani abinda zaije ya dawo kinji Zainab dita" "babu komai Bbn Abba' nidai fatana Allah yabaka ikon adalci a tsakanimu" "amin Zainab ngd' hannu yasa ya jawo wata leda dake gefe ya mika mata snn yasa hannu cikin aljihunsa ya dauko kudi a dunkule ya dukula mata a nata hannu h'ade da rufewa yana f'adi babu yawa kiyi hkr" "sbd dadi rungumesa Zainab tai tana fadin ngd ngd ubangiji Allah ya kara girma da daukaka yasa kafi haka ya kara arziki da b'ude' b'akin zhrdee har kunni sbd jin dadin addu'ointa rungumeta yai yana f'adi ngd Zainab Allah ya barmu tare" "amin me gidana na kaina" "ni zantafi Zainab sbd inaso nabiya gidan su Aisha kafin naje g'ida" "nan sukai sallama snn yatafi gidan su Aisha'. yana isa ya kirata ta waya' dama ba bcc takeyi ba' tana gani kiran zhrdee da sauri ta daga da sallama' bayan ya amsa yace kifito gani a kofar g'ida' to tace h'ade da mikewa ta zafi mayafi ta kwashi yara ko mgn batai wa umma bafita' lkcn ummata na tare da abbanta a dakinsa' nata fita zhrdee dake mota ya hangota ya fito daga mota ya tareta h'ade da amsar daya daga cikin yaran' bayan su koma gefene yake cewa ke meyasa duk inda zaki saida yarane?" "idan NA barsu kuka sukeyi" "to suyi mana' idan suyi su gaji zasu bari' amma sbd Allah dan fitarwar da zakiyi gashi k'uma darene shine SAI kin fita dashi' to wlh kada ki karami h'aka" "shiru Aisha tai bata tanka ba' " zhrdee yana rungume da shahida ya koma mota yaje ya dauko dayan ledar yazo mata dashi ya baya h'ade da kudi " "amsa kawai tai h'ade da ngd" "snn yace kiyi hkr ban sanar dake akan lkc ba".. " babu komai" "jibi nakeso kukoma keda Zainab' abinda yasa bazaku koma gobe ba sbd feti nakeso a sake maku kinjiko" "babu komai Allah ya kaimu" "ni zantafi sbd sauri nakeyi' to shikenan' yanzu dai fara komawa dashi kiji kidawo" "to kawai tace' daukar ledar tai tashige ciki ta'ije snn tasake fitowa' lkcn zhrdee ya koma mota' har mota ta bisa ta dauki shahida snn sukai sallama' sake fitowa yai ya rakata har ciki h'ade da rungumeta snn sukai sallama yatafi" "wani irin dadine ya ziyarci zcyr Aisha' har zai shiga mota da sauri yasake dawowa h'ade da kwanda mata kira' tana juyowa yace kiyi hkr fa' idan Allah ya kaimu jibi Dan Allah kafin la'asar nakeso kudawo" "to babu damuwa Allah ya kaimu' iji Aisha kenan" "snn suka sake sallama yatafi" "yana hanyane ya kira Zainab ya sanar mata da lkcn da yakeda bukatar tadawo' itama bata nuna damuwa ba" "zhrdee' yana isa g'ida bangaren Hjy yashiga' bayan su gaisa take tambyarsa ina yatsaya da bedawo g'ida akan lkc ba" "gidan su Zainab naje da Aisha' lfy?' eh lfy klau jibi zasu dawo dakinsu" "alhamdllh naji dadi sosai Allah ya kara hkr' k'uma kaima Dan Allah akiyaye" "insha Allahu Hjy" ~~~~ ~~~~ ~~~~ "bayan sati uku Alhj AMINU suna zaune da Hjy Mariya a lkcn yaso f'adi mata amma k'uma yarasa ta'ina zai bulo mata' k'uma gashi a gsky idan ba f'adi mata yai ba' in har yace zaibar Fatima taci gaba da zama a hotel Akwai cutarwa' tunda yanzu Mariya tafara ganosa shiyasa yanzu ta rike masa wuta kota ko'ina" "h'akan yasa koda ranar da Fatima ne kada girki baya kwana idan yaje da safe zuwa 4PM yake barin g'idan ta sai k'uma gobe' gani haka zai iya jefasa cikin halaka da kuma gudun kure ita fatiman tunda bata nuna masa damuwa akan hakan ba' yasashi shima ya yanke shawarar sanarwa Mariya" "bayan kwana biyu suna kwance da Mariya bayan sallar asuba yace Mariya" "na'am Alhj" "Dan Allah Akwai wata mgnr da nakeso f'adi maki amma besan yadda zaki dauki mgnr ba" "Alhj kenan kada kaji komai kafadi kawai" "himm Mariya kenan' kisan duk cikanke musulmi ansansa da rungumar kaddara me kyau ko akasin h'akan ko?" "kwai da gske Alhj na shiyasa a kullum nake alfahari dake a matsayinka na megidana' ubangiji Allah ya barni dakai" "murmushi kawai yai" "Alhj bakace amin ba" "kina jina Mariya" "ina sauraranka tunda kaki cewa Aminci" "Mariya kenan a nawa tunanin muriga mu wuce wnn guri kum' sbd yanzu muzama daya keda' amma tunda haka kikace to amin amin matata ta kaina Allah ya kara dankon kauna da soyayya ya kuma kara mana hkr da juna" "amin me gidana na kaina Allah yabar min kai" "amin" "yanzu ina sauraranka Alhj" "dama ba wani abu bane Mariya kin dai San tsawon shekaru da muka diba dake babu wanda ya taba jin mu dake to dan Allah ina rokonki a yanzu ma koda na f'adi maki banaso ki daga hankalinki wlh duk abinda zai shige cikin rayuwarmu ni AMINU nayi maki alkawari inash Allahu bazan taba juya baki baya ba' Allah kafin na f'adi maki koma menene Mariya inaso kiyi min alkawari" "Alhj kenan ni wlh duk NA koda naji ko menene' amma alkawarin me kakeso nayi maka" "Mariya kafin muyi aure dake shine besan waye keba amma tun bayan aurena dake a kullum nake daga hannanye sama nakewa ubangiji godiya daya azirtani dake'' wani abu da baki sanida Mariya a kullum idan nayi sallah saina daga hannu sama ina rokon ubangiji daya barmu tare har mutuwa' Mariya ina sonki kuma ina alfahari dake ba sbd komai ba sbd kyawawan halayenki wlh Mariya koda cikin a bokaina nake idan kowa yana fadin laluran gidan sa abin har mmki yake bani sbd ban taba samu haka dake ba' kuma nasan ba komai ne jawo haka ba sbd tarbiyan da kika samune daga gidan ku' shiyasa ka aure mace yar'babban g'ida ma yanada kyau" *_idan akace g'ida mafi yawanci al'umma sukan dauka kudine' basusan ba haka abinya yakeba' idan akace babban g'ida ana nufi gidan tarbiya' gidan da idan ka auri daya daga cikin zuru'ar g'ida bazakayi da kasani da aurensu ba' sbd tun farkon asalin gidan su Riga so dora jini gidansu akan turba me'kyau ne. amma yanzu ba haka bane duk Wanda yaji akace babban g'ida zakaji ana tambyar waye ubanta' ko k'uma YAR' gidan waye' ba'a dubi da tarbiya' nasaba' tsatstsasu gidan ta tafito, al'ummar yanzu idan suna niman aure basu duba irin wnn abubuwa, idan uban yarinya yanada kudi' tofa angama samu tarbiya a wnn gidan' tunda dama shine damuwarsu ba tarbiya ba. ya ubangiji Allah ka hure mana ta hanyar halas_* wlh shiyasa a kullum nake alfahari da aurenki h'ade da zabgawasu Alhj da Hjy addu'ar akan irin tarbiyan da suka baki " "Mariya naji haka jikinta yai sanyi tace babu komai Alhj nayi maka alkawari insha Allahu koma wani irin maganane bazan taba nuna maka damuwa ko bacin rai akansaba" "saida ya tashi ya jingina bayansa da gado snn yace Dan Allah Mariya kiyi hkr sbd nasan ban kyauta ba Dan kamata yai NA sanar dake kafin na aikata amma h'akan besamuba sakamakon yadda abu yazomi" "Mariya najin haka zubawa AMINU ido tai jikinta har rawa yakeyi h'ade da son jin abinda zai f'adi mata' ita kanta batasan lkcn da hawaye suka wanke mata fuska ba" "Alhj yace nasan za'ayi haka Mariya amma Dan Allah kiyi hkr' hkrin nan Dana sanki dasu inaso ki kara" "cikin kuka tace dama kenan idan kace zaka gidan Nigeria ba nan kake zuwaba?" "nan nake zuwa Mariya" "ka Dade kenan da auren?' k'uma aina take?" "a'a ban Dade da auren ba' idan bekai wata ba' k'uma muna tare da'ita anan London" "batare data sake mgn ba mikewa tai tafita tabar masa d'akin' koda yake kwada mata kira besa ta tsaya ba' gani haka yasashi binta da sauri" *_TO HAUSAWA SUCE KISHI KUMALLON MATA_* ~~~~ ~~~~ ~~~~ "zhrdee yana fadiwa Zainab lkcn da yakeso su koma ta sanarwa innarta' itama inna tunda taga an daidaita ta hadawa Zainab hadandun maguguna nasha Dana matsa take amfani dasu" "yau ne ranar da zata koma gidan zhrdee' sbd ita keda girki yasatace Zainab ta shirya akan lkc' duk wani shirin da zatayi tayi ana sallar azahar inna ta sata gaba ta rakata' Zainab tai kuka kamar yaune farkon zamanta da zhrdee" "suna isa saida tasake kaita gun Hjy sukai mata f'ada sosai snn suka koma bangaren su' itama inna takoma g'ida' gani yamma yayi yasa Zainab shiga kitchen tai abinci ta zubawa zhrdee nasa a kula ragowa kuma ta barsa a tukuya' tasake wanka tasha kwalliyarta takoma d'aki ta zauna sbd itadai tayi abincine kawai amma batasan me girki a cikinsu" "Aisha bata dawoba sai bayan isha' sbd su tsaya jiran kanwar bbnta itace zata rakata' suna shiga gidan zhrdee shima ya shigowa' bece dasu kalaba yashige bangaren Hjy har saida masu rakota suka fita snn ya dawo bangarensa" "a parlour ya zauna Zainab najin motsinsa ta fito ta kawo masa ruwa da abinci har zata zauna yace taje takira Aisha' tare suka fito da'ita Zainab ce tafara gaidasa snn Aisha itama ta gaishesa" "zhrdee dake zaune yace to Allah ya kawomu Dan Allah ina rokonku da ku zauna lfy a tsakaniku zamane na gsky da amana nakeso muyi daku' dukkanmu a cikinmu babu wanda baya kuskure amma idan h'akan yafaru da ko waye Dan Allah kada kaji komai kafadiwa mutumi da yai kuskure sbd gyara" "duk suna zaune sukace inash Allahu" "abu na biyu k'uma bazan zauna daku baku gani iyayena da daraja da mutuncin ba' sbd duk wani mataki da zantaka a duniya sune sila Dan haka kuga albarkaci nakeci ba ni kadai ba harda ku' Dan haka duk meso zama dani dole tabi abinda nakeso' dokane naso idan kutashi da safe kafin kuyi aikin komai aje a gaidami iyayena' koni ban yarda a gaidaniba batare da angaida su Abba da Hjy ba" "NA biyu kuma wlh wlh wlh koda da wasane naji wata taima wata gori a b'akin aurenta' koma jina ko" "duk sukace eh" "snn ya juyo kan Aisha' ke danace kudawo kafin la'asar meya zaunar dake har wnn lkcn?" "su ummata ne tace natsaya inna Asiya tazo ta rakoni" "yayi kyau' inna Asiya ko' yanzu abinda za'ayi kinga Zainab taji mgnta ta dawo a lkcn dana bata gashi k'uma harda abinci tayi kinga yanzu idan nakwana a dakinki banmata adalci ba' yanzu hkr zakiyi zuwa jibi' ke Zainab dauki abinci muje daga ciki" "shiru Aisha tai' zhrdee yace tashi kije ki kwanta saida safe" "to saida safe" "mikewa tai tashige dakinta' Aisha na shiga ta rusa da kuka' sbd a nata tunanin yau a dakinta zhrdee zai kwana""" 📖✍ ☘☘ ☘ *AURE IBADA NE* FASAHA ONLINE WRITES. F.O.W.☘. 🌳 *impacting valuable knowledge and entertainment is our concern* 🌳 *story written by Mmn uswan* vote me on Facebook gmail:hauwaszaria@gmail.com *JIJINA* *_A gaskiya banida kalaman da zanyi amfani dashi wajan nuna farin cikina a gareku' nagode nagode sosai ubangiji Allah ya kara girma da daukaka ya kara budi ya albarkaci mana zuri'a' ya shirya manasu shirin addinin musulci' yasa masu yiwa musulumci hidimane' ameen ya allahHAJIYA ZALIHAT YOLA (mmn ahamed) .HAJIYA HANNA. Abdulrahman Hafsat Hausa Nvl H2 and Muhammed Allah yabar kauna da zumuci amin_* *_YAN'UWA RAKIN JIKI' IDAN AKWAI WANI KALMAR DAYAFI HAKAMA WLH KUNFI DA HAKA GARENI UBANGIJI ALLAH YABAR ZAMAN TARE' YA ALBARKACI RAYUWAR YA"YA"MU' YASA MASU JIN KANMUNE YA MASU YIWA UBANGIJI BIYAYYANE MUMA SUYI MANA BIYAYYA' YAKARA BUDAWA MAZAJANMU WAJAN NIMO MANA HALIS YA KARA MANA HAKURIN ZAMA DASU HAJIYA AMINAT KABEER KIRU. HAJIYA ZULAIT YOLA MMN AHAMED_* *_~WRITES~_* *_manya magani kananu' jagaba kun riga kunyi gaba' saidai ta Allah amma bata mutum bakiba' sama da ikon Allah' hasken garin wata sha kallo tautari tsaya gaban makiyinku_* *UP* ❤ *UP UP* ❤ *UP* *_~DA ALBARKAN ME MANA RUWA DA ISKA~_* *RAHMA RUFA'I NALELE* *BATUL ADAM JATAU* *AMINAT KABEER KIRU* *REAL DANBU CE (MMN WALEED)* *SAFIYA MUSA A HUKUMA* *ZAINAB IBRAHIM (MAHABEE)* *CIKI DA GASKIYA* *ANTY RUKKY(MMN ABDUL JALAL)* *UMMUSULEMAN* *MARYAM L.I. GITAL* *ZAINAB MAKAWA* *FASMA NIGER* *HALEEMA AUWAL* *HALIERMIER AMEEN* *ZAINAB SHU'AIBU* *KING BOY* *_jijina gareku masoya na' hakika kun cika cukankun masoya na gaskiya shiyasa a kullum nake alfahari daku a duk inda kuke' ubangiji Allah yabar kauna da zumuci. amin_* *_especially my momcy Aisha magaji taki da ban ne uwata ta kaina ina yinki wlh Allah yabar kauna da zumuci_* *THE* 🔚 6⃣5⃣ "suna shiga d'akin gani Abba kwance kusa da Islaha zhrdee yace a'a Abba har bcc ne?" "eh' ina gama masa wanka yai bcc" "bari na kaisa d'akin Hjy ya tayata hira' hannu yasa ya daukesa zuwa dakin Hjyn da sallama ya shiga' tana amsawa yace ga Abbana yazo tayaki hira" "murmushi kawai tai masa' snn ya shinfidashi sukai sallama yakoma dakin Zainab' ko kafin ya koma tun tashiga badroom ta h'ada masa ruwan wanka snn tafito" "yana dawowa zama yai yaci abinci snn ya mike ya tube' yana tubewa Zainab tana ninke kaya saida ya kare snn ta h'ada kayan ta zuba a wardrobe shikuma ya shiga wanka' yana fitawa suka kwanta.... " yau ko masallaci zhrdee bejeba a g'ida yai sallarsa shida Zainab suna idarwa suka sake Zainab ta mike har takai b'akin kofa' zhrdee yace Zainab ina zaki? " "zanje na gaida Hjy ne" "OK amma kada ki Zainab kidawo yanzu ki h'ada mi tea" "to kawai tace snn ta fice daga d'akin' mikewa yai yakoma ya kwanta yana jiranta" "gani bata dawowa da sauri ba yasashi mikewa zuwa dakin Aisha' yana shiga ganita yai tana zaune kan sallaya' itama tana gani yashigo tai sauri ta shafe addu'arta dama tariga ta kare' mikewa tai h'ade da gaidashi ina kwana" "lfy klau' kutashi lfy?" "lfy klau" "Aisha na mikewa ta haye gado ta kwanta kusa da yaranta' gani haka yasa zhrdee cewa tashi kije ki gaidasu Hjy snn kidawo ki kwanta" "batare da musuba ta mike ta fita zuwa bangaren su Hjy' yana zaune yana jiranta har saida tadawo snn shima ya mike yafita ya koma dakin Zainab' yana shiga yaga har tadawo rike da tea a hannu' karisawa yai h'ade da tambyar dalilin dadewarta" "koda naje be sameta a dakinta bane tana d'aki Abba har najuya zanfita sai gata ta shigo to kawai yace h'ade da amsar tea d'in yasha" "a zcyrsa yana f'adi Ashe kenan Aisha bata tsaya su gaisa da Hjy ba tadawo?" "yanasha yasake kwanciya' duk yadda Zainab taso daurewa amma saida zhrdee ya kureta har yakai ga ta nuna gazawarta snn ya barta ta huta' yau kam zhrdee be fita kasuwa ba sai around 12PM snn yaje kasuwa" "bayan kwana biyu Aisha ta amshi girki' dayake tasan yafi son towun masara da miyar kuka ko kubewa yasa tai masa' koda zhrdee ya gani yaci sosai yana gamawa ta kwashe kayan ta meda su kitchen yana gamawa wanka yashiga' suna kwancene zhrdee yace aishata" "tana makale a jikinsa tace na'am zhrdee dina" "Dan Allah Akwai wata mgnr da nakeso na f'adi maki amma Dan Allah banaso haka ya tada maki da hankali' da banyi niyar fadiba amma gani nayi barin kashi a ciki yaba magani yuwa k'uma ya kamata ace kinsani tun a lkcn to dayake Akwai Dan abubuwan da suka shiga shiyasa" "ido Aisha ta zuba masa tana kallonsa" "zhrdee yace amma kiyi hkr k'uma insha Allahu h'akan bazan sake faruwa ba' shiru yai yana jijina lamarin snn k'uma yace akwan sati daya daya shiga tsakaninmu..... " a gigice Aisha ta fisge jikinta daga nasa tasa kuka'tana salati h'ade da nashiga uku" "kamota zhrdee yasakeyi ya jawota jikinsa yana bata hkr' cikin kukan Aisha take tambyer saki nawa yai mata' dayane kawai' k'uma in Allah ya yarda h'akan bazan sake faruwa ba' a lkcn Aisha taso tambya ita kadane h'akan yafaru da'ita ko harda Zainab' amma gudun kada ta kunna wa kanta wani wutar da bazata iya kashewa ba yasa tabar tambyar" "tayi kukan har tagaji' shima zhrdee be bantaba har saida yaga ta daina kukan ta hkr" "tun daga lkcn taka tsantsan takeyi a zamansu' yanzu kam alhamdllh domin zhrdee yana iya kokarinsa wajan gani yamasu adalci a tsakanisu' shiyasa suma yanzu komai nasu tare sukeyi babu mejin tsakanisu' duk da dama Zainab bame damuwa dace sbd ta dashi taga gidansu da kishiya' shiyasa koda taga wani abu yazo mata yakan zama ba sabon abune a guntaba' aishane ma take nuna damuwarta akai' sbd yanzu idan iskanci zhrdee ya tashi dukkansu yake masu' Aisha ce kecewa zata masa mgn' Zainab ke hanata ranar a d'aki suke niyi' shima sbd yariga ya saba da f'ada ko kasuwa baya fita akan lkc yana zaune a parlour niyi yakeyi yana masifa ko yaran dake g'idan susan da zamansa" "tuda kida ya canza dole rawa shima ya canza' kuma inda zhrdee ya godewa Allah matarsa duk suna shakkansa gashi dai karami ruwa ne dashi amma tsiyarsa yafi na babban. *_shiyasa hausawa ke karin Hausa da fankan fanka bata kilishi' wani lkc azabar karami mutum har yafi na babba' snd daga aisha har zainab suna shakkansa koda mgn ne suna shakkan meda masa' babu duka balle zagi' sbd tun bayan dawowarsu yadaina dukan su amma ido kawai ya ishesu sunan abinda yake nufi. kuma ba komai ya jawo masa haka ba sbd zhrdee ya tsare gidansa raina biyar babu wacce zatace ta kara masa a cefane gidansa' duk da dai d'an adam tara yake be cika goma ba' amma yana Iya kokarinsa wajan gani ya kyautatawa iyalinsa' hakama iyayensa. Shiyasa yanada kyau namiji ya tsare hakkin da Allah ya dora masa' rashin h'akan kuwa shikesa aita samu matsaloli a zaman takewar auratayya ga rashin gani girmansa sbd duk hakkin da Allah ya dora masane ya kasar maka. Allah datta damu masu irin halinma ubangiji Allah ka ganar dasu, ameen ya Allah_* ~~~~ ~~~~ ~~~~ tun daga ranar da Alhj AMINU ya sanarwa Mariya mgnr aurensa bata sake kulawa ba' koda mgn yai mata tanka masa har tsawon kwana biyu" "gani h'akan ba shine mafita a garetaba tun aikin gama yariga ya gama' aurene dai yariga yai' kuma koda beriga yayi ba ban isa na hanasa ba' idan ma nace zan hanasa badai zarginsa nakeyi amma kada wajan kokarin hanasa yasashi yaje ya f'adawa halaka yakoma niman matan bazan' kaga garin niman gira na rasa ido kenan' k'uma bansan matsayinta a zcyrsa ba" "ballema me afkuwa ya riga ya afku wata kilanma tana nan da ciki tunda da alama auren ya dade' amma koma menene daurewa zanyi na kuma rumgumi aure h'ade da kwantar da hankalina na rungumi mijina' sbd idan har na daga hankalina nasan karsheta dai shine ya mikami jan takarda' tunda Alhj ba meso damuwa bane. "idan kuma na kuresa nasan karshanta ya sakeni' idan har kan ya kasance yaya zanyi da yarana haka kawai wata Wanda bansan irin tarbiyanta ba tazo ta rusami nawa tarbiyan da naiwa yara' gara kawai nayi hkr na sanyaya zcyta' ta hahakane ma zanji komai akan auren amma idan na tada hankali babu abinda zanji sbd abinda hkr be bakaba rashinsa bazai bakaba. " mikewa tai ta bisa hat d'aki inda yake kwance daidai lkcn idonsa biyu da sallama tashiga har kan gadon tabisa ta zauna h'ade da cewa Alhj har katashi daga bcc ne? " "cikin taushin murya take masa mgn" "Alhj AMINU dake kwance mmki Mariya ne kawai ya kamashi' duk da yasa tun da Allah yasa ya aureta wani abu makamancin haka betaba hadasu ba' tun suna Nigeria abokansa har mmkin irin zamansu sukeyi' shiyasa koda tai masa haka yai mata uziri sbd yasan ba laifinta bane harda kishi h'ade kuma da jin zafin auren da yai batare daya sanar da'ita ba' kuma ba itaba kowaye dole zaiji haushin h'akan" "shiru da yai yasa Mariya cewa lfy Alhj tunanin me kakeyi haka?" "lfy klau Mariya' yaya dai?" "babu komai' ido kawai ya zuwa mata yana kallonta' gani irin kallon da yake matane yasata cewa h'aba Alhj wnn irin kallo h'aka? " himm Alhj kenan' kace kai aure kuma matar tana nan amma bantaba ji koda da wasa neba kace zaka gunta';kodai dama wasane kakemi?" "h'aba Mariya tunda nake dake nataba f'adi maki h'aka?" "a'a haka taba ba" "to amma meyasa baka zuwa kwana a gunta' kake kwana anan' baka tsoron Allah ya kamaka da laifin h'akan?" 'shiru yai kamar bazai bata amsaba can k'uma yace kae AMINU bari kwai na f'adi mata koma menene hausawa suce ranar wanka ba'a biyan cibi' ina zuwa mana" "kamar yaya bangane ba' sbd tunda nake dakai koda da wasa bantaba ji kace zakaba' amma yanzu k'uma kace kana zuwa" "tun Mariya tana dabarane Dan bugun cikin Alhj AMINU" "shima daya gano haka yasa yake kokarin wayance mata" "Alhj da kaefa nakeyi" "nima tunanin da nakeyi kenan" "shiyasa sbd tsoron kada Allah ya kamani da laifin h'aka' " yanzu tunda ka aureta babu wani alaka daya shiga tsakaniku' gaskiya baka kyauta ba" "da gefen ido ya kalli Mariya h'ade da cewa uhmm" "yanzu a aina take?" "yawwa ko kefa abin son ji kenan" "ehhh' tooo' tana gidan yan'uwanta" "h'aba Alhj sbd Allah tsawon wata daya mutum yai aure amma k'uma tana gidan yan'uwanta' gsky haka beyiba' idan har ka amince yau din nan zata tare anan g'idan" "ehhh' too' way dah haya naso kama mata" "h'aba Alhj hayafa kece duk dakunan dake gidan nan' a'a wlh babu komai tazo mu zauna tare';menene duniyar' menene a ido idan ba ruwa ba? " Mariya tai hakane sbd bataso Alhj AMINU ya rabasu' tafiso su zauna gu daya sbd duk abinda zasuyi ayi akan idonta' daga gani yadda yakeyi da ido da alama Akwai wani abinda yake boye mata' amma idan ta tare anan Ai karyansa yakare idan ma satar jiki yakeyi yana zuwa gunta to tazo karke" "yanzu bari naje na h'ada masu kausar da halif kayansu gu daya' idan yaso SAI amaryan naka ta zauna a daki dayan ko yaya kagani?" "eh to babu damuwa' amma da kinbari kawai na kama mata haya" "a'a wlh kabari kawai wnn ma ya'ishemu mu zauna' kudin da zaka kama mata haya ya'isa ka kara mana wann abu a g'ida' tunda abu da yawa" "baridai naje na gyara daki idan yaso da yamma saimuje na dauko amaryata ko... " da sauri Alhj AMINU yace a'a kibari kawai basai kinjeba" "h'aba Alhj... " nace dake a'a ko ban'isa bane" "daga abin arziki' tunda bakaso shikenan' fita tai zuwa dakinta h'ade da juyayin lamarin mijinta anya kuwa babu abinda yake boye mata?" "tana fita taje yasawa kofa key snn ya kira Fatima' bayan su gaisa yace da ita ta h'ada kayanta anjima zaizo ya dauketa tadawo gidansa da zama" "Fatima tai murna dajin haka sbd itama ta gaji da zaman hotel d'in da takeyi kamar wata karuwa ko Mara gata' ita kenan saidai idan yazo ya biya bukatarsa ya tafi ya barta bazai kara zuwaba SAI wani ya ka masa' amma yanzu ne zatasan tai aure' mikewa tai tashiga h'ada kayanta dama ba wasu kayane masu yawa tazo dashiba tunda tasan yadda zaman London din yake" "Mariya na kare tunaninta ta mike taje ta kwashe kayan ta hadasu daki daya snn ta share ta kankabe' yamma nayi Alhj yaje ya dauko Fatima suka dawo g'ida Mariya dake zaune a parlour tana zaman jiransu jin sallamarsu saida gabanta yai mummunar f'adi' injalillahiwainnailaihijlraju' kawai take f'adi a zcyrta" "duk da haka a lkcn ta dane zcyrta tai masu kyakykyawar karba harda abinci ta kawo masu' duk da Alhj yaso mgn a lkcn amma hanasa Mariya tai tace in Allah yai dare gari zaiwaye' dan haka suje su kwanta idan yaso da safe sai suyi mgnr da zasuyi" "haka suka mike yana rike da jakarta suka shige cikin d'akin' itama tashi tai taje nata d'akin' tana shiga ta rusa da kuka' Mariya tayi kuka sosai saidai bcc barawo da yazo ya dauketa" "tunda Alhj suka kwanta babu abinda ya shiga tsakanisu da Fatima' sbd gani yake kamar idan ya kwana da'ita ba nata bane hakkin Mariya' Dan tunda aikai aure yake kwanciya da'ita saidai idan lkcn da yaje tana period ne' gani k'uma babu halin fadiwa Mariya h'akan sbd yace mata be taba kwana da Fatima ba' yanzu idan yafafi yai zama masa matsala' shiyasa kawai zai kwana a dakin Fatima" "da safe kuwa Mariya ta h'ada masu abin breakfast ta kai dinning table snn taje ta sanar da Alhj ta waya suka fito harda ita suka hadu suka karya' a lkcn ne Fatima ta kare mata kallo taga ba komai bane Mariya sbd ta zauna da kishiyoyin da suka fita komai k'uma su buga da'ita su bari balle ita" "bayan su gamane Alhj yai gyara murya snn yace Mariya ga Fatima' Fatima kenan ga Mariya' idan bakusan juna ba yanzu ne zakusan juna k'uma kusan halayyar junanku' nasan dai duk a cikinku babu yaro duk kusan ciwon kanka to Dan Allah ina rokonku da Ku zauna lfy da junarku' idan laifin daya taima daya zaifi dacewa da kusabarwa junarku d'an samu warware matsalar ba karike mutum a raiba' dan Allah" "duk suka h'ada baki da insha Allahu" "Fatima dake zaune tace ina yaran gidan ne?" "Mariya tace duk su tafi sch" "yawwa Mariya kiyi hkr na mance ban sanar dake ba' itama Fatima tana da yara biyu Khadijat da Jabeer" "Allah sarki' ina suke?' ko kinbarsu a gun bbnsu ne" "a'a ai rasuwa yai?.. "Allahu Akbar' ubangiji Allah ya jikinsa da Rahma" "amin Mariya" "Alhj da kabari ta taho dasu kasan d'an sai uwarsa balle mawuyacin lkcn ga da muke ciki' duk da bangansu ba amma wlh har naji tausayinsu" "himm Mariya kenan' ai nima ba laifina bane' babu yadda banyi da'ita akan tazo dasuba amma taki' amma tunda hakane duk lkcn danaje g'ida tare zamu dawo dasu" "gsky kam da yafi' ai rike maraya ba karami lada bane' SAI kaga sanadiyar haka Allah ya kara buda maka" "kan Fatima na kasa tace ngd sosai" "tun daga lkcn Alhj AMINU kan SAI son Barka sbd yadda suke zama babu mejin kansu itada Mariya' yaransu ma h'aka sumeda Fatima tamkar itace uwarsu sbd yadda take masu' kamar ranar da ba sch idan zataje duba bnz din ta tare suka zuwa da sauwama wani lkc k'uma da hakif" "bayan wasu watanni Alhj AMINU yana zuwa gani iyayensa a kano yaje har gidan su Fatima ya sanar dasu idan zai koma tare zasu koma da yara' Bbn Fatima bemusa ba koda Alhj AMINU ya tashi tafiya tare suka wuce" "koda su halif sukaga su Khadijat suyi murna sosai sbd su kara samu abokan wasa' d'an kusan Kansu dayane' Khadijat da sauwama Jabeer da halif shiyasa koda Alhj ya kaisu sch class d'in Khadijat daya da sauwama shikuma Jabeer class dinsu daya da halif' yanzu gaba daya kusan yaran kudawo gun Fatima ne sbd koda assign aka basu guta suke zuwa shima kanta Alhj yaji dadin h'akan sosai itama Mariya tun tana dari dari da Fatima har tazo ta saki jiki da'ita" "saidai duk tsawon zaman da sukai Fatima bata sake samu ciki ba Mariya ce kawai ta kara haihuwa har sau biyu mace dana miji' Alhj AMINU ba karami son yake yaga ya haihu da Fatima ba amma Allah be yarda ba' itako Fatima abin be dameta ba itadai addu'ar ta kullum Allah ya raya mata su Khadijat da Jabeer" "dukiyar da Nasir ya barima alhamdllh dan abin sai son barka' wani lkcn idan Fatima taga Alhj beda kudin biyawa yara kudin sch Fatima ke biya sbd kowa yasan yau da gobe sai Allah" "shima Alhj AMINU be boyewa Mariya komai ba akan waye Fatima tun daga lkcn takara samu girma a gun Mariya sbd da zarginsu takeyi akan Alhj ne yake bata duk kudin da take kashewa' ita k'uma idan ta tambyesa ba lalla bane yabata sai yace be dashi amma ita Fatima kuwa harkokin gabanta kawai takeyi batare da ta tsaya zaman jiransa ba" *shiyasa sana'a yanada kyau kodan cirewa kai takaici* ~~~~ ~~~~~ ~~~~ "yanzu kam gidan zhrdee SAI son barka sbd kan matarsa a h'ade yake ko shida suke zamansa wani abin har sai sukahe su rufe bejiba' haka k'uma koda matsala suka samu har sai suci su sube bazai saniba" "gani bikin su Amatullah da amatulrahman yataso duk haduwa sukai a parlour Abba suna shawaran yadda za'ayi' yya Nurudee da yake yasan heda niyar kula abin arziki koda ake mgn bece uffan ba' " gani mgn yana gaba yana baya yasa zhrdee tambyar Abba me ake bukata ne da ake ta mgn da betaru ya zama daya ba " "wlh son kafi kowa sani yanzu kam banida kudin da zanmafi kayan daki irin wnda sukeso' shiyasa nace kuhadu idan ma h'ade kudi za'ayi sai a h'ada a ciye masu" "himm Abba kenan sbd kayan dakine aketa wnn mgnr?" "himm son kenan' kaima kasan inda inada kudi wlh bazan tsaya sauraranku ba amma yanzu da kaga duk natsaya ina niman taimakonku kasan babu ne" "haka ne Abba' kada kadamu idan kayan dakine insha Allahu bazan gagara ba" "bangane ba son?" "murmushi yai snn yace na dauki nawin kayan d'akin" "him son kenan' kaidai baka gajiya' ngd ubangiji Allah yai maka Albarka yasashi kagama da duniya lfy' ya baka masu saka maka' amma k'uma naga ga matanka da ciki anya abu bazai maka yawaba?" "Abba kenan kada kadamu Allah zai rufe asiri" "haka ne zhrdee Allah yai maka Albarka ya kuma sauki matanka lfy" "amin Hjy" "juyawa tai gun su yya Nurudee tace kukuma fa' kune manya amma yazama na kawai' himm Hjy kenan nidai kufi kowa sani karfina amma tunda yazama haka na dauki nawin abinci da za'aci" "to kaikuma fa Alhj kankamo' tun ake mgn kayan kanka gefe kayi shiru sbd bakada niyar kunla abin arziki" "himm Hjy kenan' wlh banida shine shiyasa amma ayi hkr kuwa wani lkc" "Nurudee kenan wlh kana bani mmki amma inda ace na gidan matarka ne kaine gaba ko dayake wnn yazama na gidan kune kuma idan kaya kana gani kamar aikin banzane sbd bamuda abinda zamu baka kamar matanka shiyasa' nidai bazan maka bakiba amma kasani bakada wnda yafimu duk wiya duk dadi muna tare" itako wacce kake mutuwa akanta wlh ba baki nayi makaba amma tana gani baka dashi ba lalla bane ta zauna dakai" "Dan Allah Hjy kiyi hkr wlh duk abinda kike tunanin ba h'aka bane' amma tunda amma tunda abu yazama haka shikenan duk abinda babu zansiye amma ni wlh kallon kudi kawai kikemi nikuma bedashi" "kaeda kasani ni dama tun kana yaro abin hannunka ba ciyuwa yakeyi ba" "bayan kowa ya watse Abba yace Hjy" "na'am Alhj" "wlh shiyasa a kullum nake kara son son sbd kokarin sa' ga shidai shine karami amma abinda yakeyi a gidan nan koda nine iyakaci kenan" "hakane Alhj mudai babu abinda zamuce saida Allah ya saka masa da alkairi ya bashi masu saka masa" "ni babu abinda yaimi dadi irin gidan da yasiye" "gsky ne Hjy" "kaga bayan biki sai su koma gidan su kawai" "Allah ya kaimu lkc" "amin Alhj" "ana gama b'akin su Amatullah zhrdee da matarsa sukai parking zuwa gidan su' satinsu biyu da komawa Zainab ta haihu baby boy' kwana uku da haihuwar Zainab Aisha itama ta haihu baby boy h'akan yasa zhrdee ya h'ada suna kawai rana daya yai masu suna' kowa sunar bbnsa aka sa masa' kayan kuwa kusan iri daya yai masu saidai kowane da ruwansa' sbd Aisha bakace ita k'uma Zainab fara" "bayan shekara biyu aka sako Rukky daga prizi bayan ta dawo g'ida bauchi da kwana biyu har kasuwa shago tabi zhrdee da kukanta ido bibbiyu zhrdee ya yafe mata k'uma ya medata dakinta" "waww ni Rukky Dan Allah kirufami asiri Dan yafe maki kam NA yafe maki amma kije can kisamu daidai ke'aini kinfi karfina Rukky" "Dan Allah zhrdee" "hkr zakiyi ki tashi ki tafi' ni yanzu ma da kika gani banida niyar aure idan kinga nayi wani aure to kila SAI a kiyama idan anayi' Dan matana su gamami komai" "jiki a sanyaye Rukky ta tashi tatafi" "tana tafiya zhrdee yace ni Rukky idan kin gani a kiyama wlh kaeni akayi' haka kawai nazo NA mutu lkcna beyiba" "yaran dake shagon sukasa masa dariya" "shima kansa dariya yai yana f'adi ni Rukky Ai har namutu bazan mance dake ba" *_TAMMAN BILLAH_* *_alhamdllh duk da banso tsayawa anan ba amma babu yadda zanyi ne ngd ngd ngd sosai masoya littafin AURE IBADA NE abinda nafadi ciki ubangiji Allah yasa ya amfanar da jama'a kuskuren da nayi k'uma Allah ya yafe mana baki daya_* *_godiya ta musamman ga Hjy sabba'u Jos plateau bukur pack ubangiji Allah ya kaya girma da daukaka_* 📖✍ 📖✍ 📖✍ 📖🖊 📖🖊 📖🖊 📖🖊 📖🖊 Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen2⃣)