[12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 01 [ 12/1/2022 1:10 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      *FREE PAGE 001* Ina the name of Allah the most beneficient, the most glorious and the most merciful. Dubun salati ga fiyayyen halitta Manzon tsira Annabin mu Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam. Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah maɗaukakin sarki mai kowa me komai da ya Wada ta ni da rai da lafiyar da na sake dawowa gare ku cikin wani salon rubutu na daban, Allah yadda ka bani ikon fara rubutun nan lafiya kasa in gama lafiya, Allah ka bani ikon rubuta abinda ze amfane ni ya amfani al'umma gaba ɗaya, ya Rabb ka hane ni rubuta abinda ze cutar dani ya cutar da ƴan uwa musulmai. At long last nake cewa hellooooooo to You my fans💃💃💃💃💃. Gani dai na sake dawowa, Ouummey ce dai taku tafe cikin wani sabuwar tafiyar da nake fatan ku so kuma ku ƙauna ce shi fiyeda littattafai na na baya, soyayyar da kuka nuna min a littafin *SARAKI da ABOTA CE KO SOYAYYA* is really amazing and unpredictable, am using this opportunity to say thank you once again, Ouummey loves you so dearly 💖. Sedai fa ba kamar baya ba this novel isn't FREE kamar na baya, it's a *PAID BOOK at ₦300 ONLY!!!.* Na sani you guys won't make me feel unloved or ashamed, nasan zaku nuna min ƙaunar da kuke min ta hanyar siyan littafina dan rubutu na ba abin yar wa bane, isn't so??!. Kar dai na cika ku da surutu, ga duk me buƙata zai/zata biya kuɗin ta ta wannan account ɗin, RABIATU ABDULLAHI 2391368231 ZENITH BANK tare da turo shaidar biya ta 09013101854 Ko a turo katin MTN ta wannan number 09013101854. Son so fisabilillah 💋💋. WANNAN LITTAFIN SADAUKAR WA NE GARE KU MY FAMILY, HEART U ALL AND ALLAH YA QARA MANA ZUMUNCI DA QAUNAR JUNA, AMEEN💞💝💖💗. ________________________📖 Gudu take cikin fitar hayyaci cikin dokar dajin dake da shegen duhu duk kuwa da cewa ba wai dare ne ba dan lokacin bai wuce ƙarfe huɗu da rabi zuwa biyar ba, takun mutanen da take jiyo wa a bayan ta yasa ta tabbatar basu daina bin ta ba haka suna daf da ita, wani irin kuka ne ya kubce mata ta shiga yin shi tana sakin numfarfashi, bata san me yasa azzalumai suka yi yawa ba a duniya, bata san me ita ko ƴaƴan ta suka tare wa maƙiyan ta ba da suke san se sun shafe labarin su ta kowace hanya, a rayuwar ta bata da abokin gaba tun daga yarinta har zuwa girman ta, kai har zuwa yanzu da take wannan gudun na ceton ranta da na ƴaƴan ta bata san dalilin neman kashe su ba. Kukan da yarinyar bayan ta fara ne yasa na gane jaririya ce sedai ba wai ɗanyar haihuwa ba dan zata kai watanni, bata rufe bakin ta ba wani kukan ya shiga tashi, se a lokacin na lura goyon gaba da baya ne matar tayi kuma da alama ƴan biyu ne dan itama ta gaban macece, wannan kukan shi ya kuma ruɗar da uwar ta saki nata kukan me sauti tana cigaba da gudun da take yi. "Yauwa gata can, ku ƙara gudu mu cin mata tun kafin ta kai ga ficewa dajin nan dan na gaban sa ya fishi duhu ba lallai mu iya ganin ta ba". Cikin azama ta ƙara gudun ta dan jin abinda wani da take zaton shine babban su yace, burin ta a lokacin be wuce ta fita daga nan ta faɗa dajin gaban ba dan tsira da numfashin su sedai bata kai ga hakan ba taji saukar katako ta bayan ƙeyar ta, su ne suka jefo mata ko kuwa daga ina yake ba ta sani ba. Faɗuwa tayi sedai da sauri tasa hannu ta dafe ƙasa dan gudun kar ƴar ta taji ciwo, jin takun su daf da ita yasa ta hanzar ta miƙewa duk kuwa da yadda taji jini na bin wuyan ta ban da kuma jirin da take gani, neman wajen fakewa take yi sedai kamar babu wani loko a dajin, a lokacin ba ta rayuwar ta take yi ba ta rayuwar ƴaƴan ta ne, ta sani ba lallai su tsira daga hannun wadan nan azzaluman ba sedai tana fata ƴaƴan ta su tsira ko da kuwa ita zata hallaka, yara ne da basu san komai ba basu kuma fara komai a rayuwar su ba dan yanzu ne suke watanni na uku da haihuwa, ba zata so rayuwar su ta tsaya iya nan ba haka kuma ba zata so maƙiya suyi galaba akan ta ba, ta sani saboda yaran ake neman kashe ta saboda kada uban su ya sami wani haske ko ƙanƙani a rayuwar sa. Bata san me yasa marasa imani suka cika faɗin duniya ba sedai tana tausayin mijin ta kuma uban ƴaƴan ta, yaran ne dukkan wani farin ciki, jin daɗi da walwalar sa shiyasa mahassada ke neman ganin sun raba shi dasu har itama ta samu nata rabon ƙaddarar, rayuwar su cike take da baƙin duhun da bata taɓa tunani ba se a yau da take wani siraɗi na mutuwa ko rayuwa, se a yanzu ne abubuwa da dama suka dinga dawowa kanta da yaci ace ta ankare da su tuntuni sedai tsabar pious heart ɗin ta yasa bata taɓa zargi ko kawo wani mummunan lissafi ba, se a yanzu ta tabbatar da tabbas tayi kuskure, kuskure kuma mafi girma na ɗaukar cewa kowane ɗan Adam kyakkyawar zuciya gare shi. Wani ɗan haske da take hangowa yasa ta nufi wajen cikin matsanancin gudu cikin fatan Allah ya kawo mata matserata ko da ta rayuwar ƴaƴan ta ne kaɗai, ta yarda ita ta mutu in har zasu rayu, tana fatan suyi kyakkyawar rayuwa ba dan saboda komai ba se dan kwaɗayin samun addu'ar su, Manzon Allah yace addu'ar ƴaƴa salihai ga iyayen su karɓaɓɓiya ce haka kuma sune kawai arziƙin da mutum ze mutu ya bari a duniya ya tadda shi a ƙiyama bayan sadaƙatul jariya wanda tasan bata da rabo a wannan ɓangaren dan ko tunanin hakan bata taɓa yi ba. ********** Kamar ko wane hutun makaranta in an yi, yau ma tafe take da ƙafa kamar yadda ya zame mata jiki ba kamar ragowar ƴaƴa masu gata ba da za'a je ɗaukar su a mota, mashin ko keken amalanke ko kuwa motar ƙurƙura, ita da ƙafa take takawa har zuwa ƙauyen su wanda tsakanin shi da makarantar tafiyar awa huɗu da mintuna ne a ƙafa, bata taɓa jin ba zata iya ba dan tana matuƙar son karatun kuma ta san in ma ba tayi ba kanta kaɗai ta cuta dan shine kaɗai gatan da take tunanin zata iya samu da ze zama sanadin canjuwar rayuwar ta da ma duniyar ta gaba ki ɗaya. A hankali ta shiga takawa lokacin dan ta gaji, tsakanin ta da ƙauyen su be wuce tafiyar mintuna Talatin ba dan ta kawo kusa sosai sedai a yadda ta gaji se take ganin in tayi yanke ta cikin daji zata fi saurin zuwa gida maimakon ta bi ta hanya sosai, ba ɓata lokaci ta danna kai cikin dajin cikin dajin ba tare da tsoro ba dan shiga daji a jinin su yake dan sun saba, in basu shiga yin itace ba sa shiga tsinkar magunguna ko kuma kayan marmari ko kuma yawon su. Ƙarar gudun da taji yasa ta ɗan dakata tana tunanin anya lafiya, jin kamar gudun ba na mutum ɗaya ba yasa ta ɗare wata doguwar bishiya da sauri ta yadda zata samu damar ganin abinda ke faruwa, mace take hangowa da goyo har biyu wato gaba da baya tana gudu yayinda wasu mutane masu riƙe da makamai suke binta, hankalin ta taji ya tashi duk da bata san me tayi musu suke bin ta ba sedai a ƙananan shekarun ta tasan ba abu me kyau yasa suke bin ta ba tun da har ga makamai banda haka kuma mutane da yawa na shiga wannan dajin dan aiwatar da munanan ayyukan su saboda duhuwar dajin na basu kariya daga idanun jama'a, bata san me yasa ba sedai kawai taji a ranta ya zama dole ta taimaki wannan matar, ba zata bar wannan azzaluman su yi galaba a kanta ba. Da sauri ta ɗirko daga bishiyar tareda nufar wajen matar da saurin ta dan gasu da suka saba da dajin bawa wani ganin duhuwar sa, da sauri ta fizgi hannun matar daidai lokacin da wani yayi nasarar sakar mata harbi a ƙafa ganin yadda take wahalar dasu, wani kogo ne na bishiya ta shigar da matar haka kuma da sauri tasa hannu ta since goyon bayan ta ganin wuyar yarinyar na reto alamun ta suma ko ta mutu, a galabaice matar ta kwanto ta gaban ma ita kuma tayi saurin tare ta. Numfarfashi kawai matar ke yi dan ta galabaita to the extent da bata iya ko da buɗe idanun ta sosai balle tayi magana, hannun yarinyar da bata san wacece ba ta ruƙo da sauri tana fizgar numfashi kamar me asthma, da ƙyar ta buɗe baki da idanun ta tayi magana mara tsayi "A...am..maa..naa, su..su..tsira..dan.. Allah". Wani irin duka ƙirjin yarinyar ya shiga yi jin abinda matar ke faɗa, da sauri ta shiga jijjiga ta, "Ki tashi Aunty mu gudu, kar ki rufe idanun ki ni ban san inda zan kai yaran nan ba wallahi". Bata iya tace mata komai ba se yatsun ta duka goma ta ɗaga mata kafin ta shiga nata nuni da zobunan dake jiki wanda guda biyar ne, uku a hannun dama biyu a hannun hagu, da sauri ta sa hannu ta cire mata dan a tunanin ta sun dame ta ne, wuyan ta ta sake nuna mata nan ma ta cire mata sarƙar jikin ta da ɗan kunne, ajiyar numfashi matar ta saki tana buɗe ido sosai cikin ƙure ƴaƴan ta da kallo kafin wannan karan cikin cikakkiyar magana tayi magana "Ki kula min dasu dan Allah, ban bar komai ba a wannan duniyar se su, sune fitilar zuciyar mahaifin su, kije dasu na baki halak malak amma dan Allah su tashi cikin kyakkyawar tarbiyya kamar kowane cikakken bahaushe musulmi, kije dasu ki kula dasu da wannan kayan sarƙar na hannun ki dan Allah kar su cimma na su kashe mu gaba ɗaya, kar ki tsaya wata magana dan ni tawa ta ƙare ko basu kashe ni ba mutuwa zan yi dan bana jin akwai ragowar jini a jikina, fatana ƴaƴana su tsira kuma alhamdulillah Allah ya turo min ke dan cetar su, ki tafi, ki tafi gasu nan, dan Allah ki tafi". Jin takun nasu da gaske kusa daf da bishiyar yasa yarinyar damƙe set ɗin sarƙar hannun ta ta zuba cikin jakar makarantar ta ta buhu dake hannun ta tare da saɓa yarinya ɗaya a ƙafaɗar ta ta goye ɗaukar tare da ɗaukar jakar buhun ta shige cikin dogayen ciyayin wajen cikin rarrafe dan kar su gan ta, seda ta ɗan yi nisa sannan ta tsaya jikin wata bishiya tana kallon yadda suka cimma matar a inda ta bar ta, haske haske sauka dinga yi da wayoyin hannun su cikin neman inda ta ɓoye yaran sedai basu ga komai ba, tsawon lokaci kafin suka koma wajen da suka bar uwar da mutum ɗaya na gadin ta, "Yanzu ya zamu yi, me zamu cewa matar nan game da ɓatan yaran?". Ɗaya daga cikin su ya faɗa kafin ɗaya ya kai ƙafar sa yana shurin matar da ke jingine har lokacin yana tambayar ta inda ta kai yaran sedai tuni ta faɗi rigija alamar rai yayi halin sa, tsabar jinin dake kwance a inda ta jingina zaka yi zaton wata ƙaramar dabba aka yanka, wani mugun tsaki mutumin ya saki kafin ya umarci ragowar su ɗau gawar tata sukai mota shi kuma ya cigaba da bincika wajen sedai dake ba sanin kan dajin yayi ba ko kaɗan be ko kai wajen da yarinyar take ba rungume da baby ɗaya a ƙirjin ta idanun ta na zubar da hawayen tausayin matar da kuma ƴaƴan dake hannun ta da yanzu suka zama marayu, bata san wane irin marasa imanin mutane ne yanzu ke rayuwa a wannan duniyar ba, ko ina cike da azzalumai, kowa ba ya tausayin kowa, kowa ba ya san kowa, kowa kan sa kawai ya sani, ya ilahi duniya ina zaki damu. Ganin kuka me sauti na neman kufce mata yasa ta miƙe wa ta shiga tafiya a hankali cikin takatsantsan dan ba zata so abinda ze jawo hankalin mutanen cen ba balle har su kashe Innocent babies ɗin hannun ta, tafiya me ɗan nisa tayi kafin ta fita daga dajin ta yanka ta cikin gonaki ta shiga ƙauyen su, garin yayi luf luf babu rana se iska me daɗi kasancewar magrib ta doso kai dan yanayin na nuna alamun be fi karfe biyar da rabi zuwa shida na yamma ba. Ba tare da  tunanin komai ba ta nufi gidan su da yake babban gida kuma ginin ƙasa ba, sallama ta shiga kwaɗa wa a ƙofar babban zauren su sedai ba wanda ya amsa mata kamar ko da yaushe, sa kai tayi ta nufi sashen da take rayuwa yayinda tsirarun mata da yaran dake babban tsakar gidan bin ta da kallo suna maganganu ƙasa ƙasa ganin ta goyon jaririya ga kuma wata a hannun ta. Wata sallamar ta kuma yi a ƙofar sashen su sedai nan ɗin ma ba'a amsa mata ba se dogon tsakin da aka ja, kai a ƙasa ta shiga ƙofar tana tafiya a hankali kamar wata ɓarauniya ko wadda ƙwai ya fashewa a ciki, inna mariya dake tsugunne bakin malalallabta tana rege shinkafa ta tsugunna har ƙasa tana gaisar wa sedai maimakon amsa se zagi da yarfe ne ya biyo baya kamar yadda ta saba "An dawo daga yawon ta zubar ɗin da sunan Makarantar boko, atoh mun dai sani ba wata wata boko se tambaɗewa da karuwa ci da ake yi ake fake wa da boko, wa ya sani ma ko an yi guzurin ɗan boko a ciki". Bata wani damu da abinda Inna mariyar ta faɗa ba dan ba yau ta saba ba, ba ita ba kusan duk ƴan gidan ma haka suke cewa, bata damuwa ne dan tasan ita karatu take yi ba yawon kafuwan ci ba kamar yadda suke faɗa, gaban ta ne yayi kwanci kwanci ya faɗi lokacin da yarinyar da ta Saɓa a kafaɗa ta calla wani irin kuka me sauti cikin Muryar ta ta jarirai, ashe ta daɗe da farkawa tun lokacin da sanyin la'asar ya buge ta amma bata dawo hayyacin ta ba se yanzu. Zabura Inna mariya tayi tana dafe ƙirji cikin zare ido "Me nake ji haka kamar kukan jarirai?". Ta faɗa tana juyowa ga yarinyar da tayi saƙare cikin tashin hankali, bata yi tunanin me ze je kazo ba lokacin da ta karɓi yaran, bata yi tunanin abinda ze iya faruwa ba dan a lokacin ba abinda ke ranta face ganin ta tseratar da rayuwar su, sam a lokacin ta manta da wane kalan mutane take rayuwa se yanzu da yarinyar ta shiga kuka kamar yadda aka san jarirai ƴan watannin ta da haihuwa. "Innalillahi, a'uzubillahi ni mariya jikar me shanu, me nake gani a hannun ki haka SALAME kamar jaririya?". Yarinyar da aka kira da salame bata iya tace komai ba yarinyar bayan ta itama ta shiga kuka alamun itama ta farfaɗo, gaba ɗaya se hankalin ta ya rabu kashi kashi, ga kukan yaran ga kuma kururuwar da Inna mariya ke yi mata, bata san me yasa taji zuciyar ta na zafi ba jin kukan yaran dan har tsakiyar ranta da kanta take jin kukan dan haka d sauri ta zauna tana ɗora ta hannun ta kan laps ɗin ta ta shiga kiciniyar kunto ta bayan ta, jijjga babyn ta shiga yi tana tapping ta kan cinyar ta dan tayi shiru shiyasa sam bata lura da mutanen da suka taru saman kan ta ba se da Muryar kawu Habibu ta ratsa kunnen ta lokacin da ya daka mata razananniyar tsawar da ta sa har ta kusa yar da ƴar hannun ta kafin tayi saurin tare ta....................✍🏻 Ya Rabb ka tsare mu daga sharrin zuciyoyin mu ka hana mu hassada, baƙin ciki da ƙyashi ga nasara da ɗaukakar wani, Ameen. ©️ Ouummey 📚✍️. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 02 [ 10/11/2022 12:16 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                       FREE PAGE 002 ________________________📖 "Dama na daɗe da sanin lalacewar ki kawai kika saka gaba shiyasa kika dage ke se kin yi wani karatun boko saboda ki samu mafaka dan kin san a nan bazan lamunci wannan iskancin ba shi kuma megari har da wani ɗaure miki katara, zaki faɗa min wanda yayi miki cikin da kika haifi waɗannan shegun ƴaƴan ko se naci uban ki, shegiya ƴar iska kawai". Kakkarwa jikin ta ya shiga yi haka ma bakin ta rawa yake tsabar tashin hankali, da ƙyar ta iya buɗe bakin ta tana sharar hawaye "Kwarankwatsa ni ba ƴar iska bace kawu, wallahi bani na haifi ƴaƴan nan ba ni ban taɓa iskanci ba ku yarda dani". Wani tokari kawu Adamu ya sake mata a bakin da take magana take kuwa bakin ya fashe ya shiga fitar da jini, dafe bakin tayi da sauri hawayen ta na ƙaruwa saboda azaba "In ba ke kika haife su ba to tsinto su kika yi?, Kaji min sheɗaniyar yarinya, wato har kin san ki buɗe wa wani gardi cinyoyi ko, Abu bani icen can me wuta, yau in baki faɗi gaskiya ba ba abinda ze hana ni kwaye fatar bayan ki da wuta". Kukan ta ne ya ƙaru ta shiga rantsuwa da magiyar su yadda ita ba ƴar iska bace sedai ina no one is willing to listen to her, ɗebe yaran Inna mariya tayi ta dangwarar da su a dandaryar jar ƙasar wajen shi kuwa kawu habibu ya shiga dukan ta da wannan icen,ihu ta shiga yin tun ƙarfin ta har Muryar ta ta dishe amma ba wanda yaji ko ɗigon imani ko tausayin ta balle ya bawa kawun haƙuri. Seda ya dake ta iya yadda yaso kafin ya jefar da icen dake fitar da hayaƙi alamun akwai wuta a jikin sa har lokacin ya dubi kawu Adamu "Kaje yanzun nan ka sanar da maigari kafin su iro su dawo mu tafi mu kai shegun yaran can, mukam Kamisu ya mutu ya bar mana annoba wallahi, haka kawai muna zaman zaman mu ya haifo shegiyar ɗiyar sa ya mutu ya bar ta gashi nan ta jawo mana abin kunya da Allah wadai zata lalata wa ƴaƴan mu suna". Da kallo kawu Adamu yabi bayan kawu habibu da ya fice yana ƙananun magana saboda masifar da ke cin sa a rai kafin ya maida hankali inda Salame ke tsugunne a takure kayan jikin ta duk sun yayyage saboda dukan da tasha, tsaki yaja ya sa ƙafa ya fice yana shura siɗaɗɗun takalman sa da suka ci duniya dan ƙullin leda a jikin su ya fi biyar. Feƙeƙƙen zanin ta Inna Abu ta tattare tana kaiwa zaune kan jar ƙasar da ta kwanta saboda ruwan da aka yayyafa mata "Ni yanzu damuwa ta saurayin A'ilo kar yace ya fasa auren ta saboda kayan kunyar da wannan annobar ta jawo mana". Ta ƙarashe tana jefa wa Salame dutsen da yayi nasarar sauka a kan ta take kuma kanta ya fashe sedai ba'a iya banbance yadda yake zubar da jini dan ciwukan jikin ta ma duk jinin suke fitar wa so se ya haɗe. "Sauƙin abin ma shima ƙanwar sa wasila ta taɓa yin cikin nan kin ga ba zasu ɗaga mana kai ba". Cikin rashin jin daɗin maganar ta Inna Abu ta haɗe rai dan duk abinda ze sa a Faɗi aibu ko a soki saurayin A'ilo bata so dan ba ƙaramin morar shi suke yi ba, wannan maganar da Inna mariya ta fara yasa ta miƙe tana ficewa da ƙafar ta da duk take cike da faso manya manyan saboda rashin sa takalmi. Hararar ƙofar da ta fita Inna mariya tayi dan ba ƙaramin haushin Inna Abun take ji ba saboda yadda take musu ɗaukar kai kan saurayin A'ilo dan gaskiya duk gidan ba wanda ya taɓa saurayi me maiƙo kamar ta dan ɗan gidan maigari ne, kukan da yaran suka kuma sanya wa a tare yasa taji takaicin ta ya ƙaru. Ji take kamar taje ta shaƙe su har se sun mutu sedai rashin imanin ta be kai haka ba so se ta dubi Salame da bata ko numfashin arziƙi saboda wahala ga kuma azabar da ciwukan jikin ta ke mata "Kin tashi kin kwashe wannan tsiyar dake neman hanani nutsuwa ko se na kwashe su na watsa a rijiya?". Duk yadda jikin ta ya kai ga nauyi saboda dukan da tasha ban da azabar da take ji amma haka ta miƙe ta shiga takawa cikin ƙarfin hali har ta kai inda suke kwance se ciccilla hannaye da ƙafafu suke yi, a kafaɗa ta ɗora ɗaya tana runtse ido saboda zafin da taji dan akwai ƙuna a wajen ɗayar kuma ta rungume ta wuce akurkin ɗakin ta da ke daf da zubewa saboda yadda ya takwarkwashe, duk da gidan dukan sa na ƙasa ne amma babu ɗaki mafi muni kamar nata dan madafar su ma tafi shi nesa ba kusa ba. Kan yagalgalallen buhun da take kwanciya ta shimfiɗar da yaran kafin ta kuma fice wa ɗauko jakar buhun ta, cikin ɗan hanzari ta ƙara sa ta ɗauke jakar ganin Inna mariya bata wajen da alamu ta shiga bayan gida ne. Cikin cije baki ta kai zaune gefen yaran ta shiga bin su da kallo tana yaba kyan su a ranta kafin kuma ta ji wani sabon so da tausayin su na ratsa ta tuno yadda aka kashe mahaifiyar su, 'duk abinda ze faru bazan yarda in rabu da ku ba, mutuwa kawai zata  raba tsakanin mu insha Allah". Ta faɗa a ranta tana jingina da bangon ɗakin sedai da sauri ta janye jin raɗaɗin da ya ratsa kwanyar ta hakan na shaida mata akwai ciwo a nan ɗin ma. Ƙofar ɗakin taje ta saya kafin ta tuɓe kayan makarantar jikin ta da suka yagalgale saboda ƙunan wuta da kuma dukan ice, wani koɗaɗɗen zani ta ɗauko wanda dama uku ne kawai da ita kuma da su take rayuwar yau da gobe ta ɗaura, wanka take son yi sedai ta san yau ko mutuwa zata yi ba zata samu ruwan zafi ba se kawai ta ƙudure yi da na sanyin ta fita zuwa ƙatuwar rijiyar su dake tsakiyar gidan. Babbar rijiya ce dan dukkan su na iya ɗiban ruwa a lokaci ɗaya dan tana ɗaukar guga sama da biyar, ƴan mata biyu ne suke ɗiban ruwa suna hirar su, tun da ta nufo wajen suke dariya suna nuna ta, duk da bata jin me suke cewa dan da ɗan tazara tsakanin su amma tasan ba abu me kyau suke faɗa ba, hakan ba sabon abu bane a wajen ta dan duk faɗin gidan ba zata iya ɗaga mutum ɗaya tace gashi me son ta da ƙaunar ta bane, daga masu ƙi da tsanar ta se kuma ƴan ba ruwa na sune wanda ba zasu dake ta ba ba zasu zage ta ba sedai ba zasu taimaka mata ba irin su kawu Adamu kenan. Ƙaramin guga ta ɗauka ta zura cikin rijiyar ignoring all the curses da suke rending mata ta shiga ɗiban ruwan ta dan tun da da basu samu dalili ba ma ƴar iska suke ce mata balle yanzu da ta zo da ƴaƴa har biyu gida, "Iyayen karuwa dai sun yi asarar haihuwa, ke in kika bibiya ma sule me shago ne yayi mata cikin da ta haifi yaran nan dan kin ga shine kaɗai yake kulata a garin nan". "Kai anya kuwa sule ne, kin ga fa Inna tace yaran sun yi kusan watanni biyu da haihuwa shi kuwa ai rabon shi da ita tun da tayi ƙaryar jarabawa ta zauna wata goma a makaranta". "Eh ba mamaki ma a can wani malamin ya ɗirka mata cikin, kin san dama buba ya faɗa mana kafirai ne". Haka suka cigaba da maganganun su na aibata ta amma bata kula ba ta ɗibi ruwan da take buƙata ta koma sashen su, da saɗab saɗab ta zagaya wani ɗan fili dake bayan ɗakunan su ta yaye zanin ta kwara wa jikin ta ruwan, sauƙin ta ruwan rijiya akwai ɗumi ban da haka kuma yau ɗin an yi rana sosai shiyasa ya sake yin ɗumi kamar an gauraya dana zafi. Zanin ta mayar tana barin cinyayyen bokitin a nan wajen ta koma ɗaki bayan ta leƙa ta tabbatar Inna mariya bata wajen, yarinyar da ta fi yin kuka ta ɗauka ta shiga jijjigawa har ta yi baccin wahala dan yunwa suke ji sedai bata san me zata basu ba, haka tayi wa ɗayar ma ta samu itama tayi bacci. Tuno da wata hamsin a jakar ta yasa ta maza ta jawo jakar ta shiga zazzage ta, kayan sarƙar babar ƴan biyu da suke zube a ƙasa ta ɗaga ta shiga kalla tana yaba kyan su kafin ta shiga hawaye sanin me su ta daɗe da zama gawa, hawayen ta share ta shiga tattara su tana mayar wa haka dan ta san a yadda suke da kyau muddun Inna mariya tayi ido biyu dasu shikenan sun zama nata. Hamsin ɗin ta shiga juya wa a hannun ta tana tunanin ta yadda zata fita daga gidan ba abin ta haura ta katanga ba jikin ta na mata ciwo. Dan son samun sauƙin fita ta siyo musu kunu ta basu ta ƙara sa inda take ajiye gishiri dan tasan hakan kawai zata yi taji sauƙin raɗaɗin ciwon har ta iya haura katanga zuwa anjima. Gishirin ta ɗauka tare da kwance ƙullin da tayi wa ledar ta ɗebo a hannun ta tana runtse ido saboda azabar da ta dan zata ji ta kai kan guraren da ƙunar take, duk yadda zugi da raɗaɗi ke ratsa ƙwaƙwalwar ta bata dena ba har se da ta gama kafin ta kwanta tana fidda numfashi ɗaiɗai kamar me cutar asthma. Wannan horon kawu habibu ne lokacin da tana hannun matar sa Inna Abu kafin ta dawo hannun kawu iro, tun tana yarinyar indai tayi laifin da aka dake ta haka kawu habibun ze ɗebo gishiri ya dinga danna mata a wajen ciwon, karon farko da ya fara yi mata da hankalin ta suma tayi amma ko da ta farfaɗo haka ya sake yi mata. A lokacin seda ta suma so uku amma ba hakan yasa ya fasa abinda yayi niyya ba, tun daga lokacin kuma yake mata wannan azabar, tun tana damuwa tana shiga tashin hankali har tazo ta daina ba kuma wai dan bata jin zafi ba se dan ta riga ta saba danne zafi da raɗaɗin a ranta. Tsawon lokaci kafin taji kamar an yi ruwa an ɗauke duk ta daina jin azaba shigar gishirin jikin ta haka kuma tuni waccan azabar ta disashe ta zafin ciwon shiyasa se ta ke jin yanzu kamar babu ciwo a jikin ta, koɗaɗɗen zanin ta ta maida tare da zura rigar sa ta salallaɓa ta fita jin an shiga sallar magrib, ta katanga ta haura kamar yadda ta ƙudira. Gudu ta sha sosai kafin ta kai ga isa wajen Sare me kunu, hamsin ɗin ta miƙa mata tana numfarfashi tare da faɗa mata ta bata na Naira goma ƙullin biyar biyar, a farar leda aka ƙulla mata ko wanne kafin a saka a baƙar leda ta miƙa mata,da hanzari ta karɓa sannan ta wuce wajen sule me shago, bata tsaya amsa tambayoyin da yake mata ba na ance ta dawo da ɗanyen goyon shegun yaran da ta haifa har biyu ba tace ya bata siga na goma se madara ta Ashirin. Madarar kusan Naira ɗari ya zuba mata haka sugan ma ya fi na hamsin ya bata yana faɗin tabar kuɗin kawai dan ba ƙaramin so yake wa Salame ba, godiya ta masa ta juya zuwa hanyar gidan su cikin gudu sosai har ta kai, ta katanga ta koma kamar yadda ta fita dan ba wata katangar arziƙi bace kun dai san fences ɗin ƙauye. Hango Inna mariya a Zaune kan tabarmar da take zama daga bakin ƙofar ɗakin ta yasa ta rasa yadda zata yi ta wuce, ta daɗe tsaye kafin taga shigowar kawu iro sashen nasu, kayan hannun sa Inna mariya ta karɓa ta shige ɗaki tana masa sannu da zuwa shima ya mara mata baya, da wannan damar ta samu ta saci kofi ɗaya cikin kofunan sashen ta shige ɗaki da sauri. Seda ta saya ƙofar duk da ba mai shigo nata dan ko neman ta Inna ke yi sedai tai ta ƙwala mata kira, kunun ɗaya ta juye cikin kofi ta sa sigar kaɗan ta juya da wani kara kana ta ɗau yarinya ɗaya ta fara tashin ta har se da ta buɗe ido, buɗe baki tayi da nufin komai Salame ta maza ta sa mata kofin a baki, cikin yunwar da ta galabaitar da ita ta shiga sha ba wani musu, sosai tasha kunun kafin ta saki tana sa harshen ta tana lashe saman cute small lips ɗin ta, murmushi Salame tayi ganin yarinya ma ta san zaƙi dan ta tabbatar da bata sa sugar ba baza ta sha da yawa haka ba. Ajiye ta tayi inda yarinyar ta shiga cilla ƙafafu tana wasa da hannayen ta, ƴar uwar ta ta ɗauka itama ta tashe ta tare da bata kunun, itama ta sha da ɗan yawa duk da be kai yawan na ɗayar ba, ajiye ta ta ƙara ɗaya na biyar ɗin kan wanda suka rage ta ƙara sugar ta shiga sha itama dan ta san yau kam ko itace tafi kowa maita ba zata samu abinci ba a gidan nan, da ɗan dama ta rage saboda kar yaran su ji yunwa su nema kuma babu, jakar ta ta ɗora ta rufe cup ɗin dashi sannan ta juya ga yaran ta ƙure su da kallo. Kyawawan yara ne Masha Allah kamar ƴaƴan turawa, ba ramammu bane dan da ƙibar su daidai sanye da kayan masu kyau suma kansu an kakkama da soso da ya daɗa ƙara musu kyau, addu'a ta shiga yi musu tana tofa masu na Mayu da baki dan akwai Mayu sosai a ƙauyen. Seda ta gama yi musu addu'a sannan tayi wa kanta ta nemi waje kan buhun ta ta kwanta dan zannuwan ta biyu ta haɗa ta shimfiɗa wa yaran da har yau bata san sunan su ba dan maman su bata faɗa mata ba ita kuma bata san da sunan da zata kira su ba. Washegari kuwa tun kiran sallar biyu da ta tashi bata koma ba, tana idar da sallah ta fita tsakar gidan su ta hau aikace aikace kamar yadda ya zame mata wajibi muddin tana garin, tana gama wa ta ɗau bokitan su ta fita rijiya ta shiga jido ruwa, se da ta cika ko ina kafin ta hau kunna ruwan komo, tana juye kokon ta kai duban ta kan ƙofar su Inna mariya dake kulle har lokacin, da sauri da sauri ta dafa ruwan zafi ta kai ɗakin ta ta ɓoye cikin wata madaidaiciyar roba sannan ta dawo wajen ta kashe wutar. Ɗakin ta ta koma ta surka ruwan a bokitin ta ta shiga yiwa yaran wanka, wankan jariri ba sabon abu bane dan tun tana shekara bakwai aka fara bata rainon yara haka kuma tana shekara sha biyu suka fara sa ta wankan jariran su, tana gamawa Hassana kamar yadda ta raɗa wa wadda taga tafi girma a idon ta ta ɗau Ussaina ta mata ita ma sannan ta ɗau ruwan nasu ta shiga banɗakin su ta kwarawa jikin ta ta maza ta fita tare da maida bokitin ta bayan ɗaki. Ko da ta koma tuni yaran sun koma bacci da alama sun ji daɗin wankan, murmushi tayi tana jan kumatun Ussaina daidai lokacin da taji Muryar kawu habibu cikin ihun kiran sunan ta.......................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 03 [ 10/12/2022 12:08 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                       FREE PAGE 003 _________________________📖 A gigice ta Fito daga ɗakin har tana yin karo da durƙusasshen bangon ɗakin wanda banda tsari da kariyar Ubangiji wata iska me ƙarfi nan in aka yi ze zube ne. A firgice ta ja baya tare da maƙewa jikin garun ganin dukkan su mazan gidan ne a wajen wanda tasan ba dan kowa suka haɗun ba se dan ita. Wani irin rawa jikin ta ya ɗauka haka ma zuciyar ta ta shiga addu'ar Allah ya taimake ta kar su ƙara mata wani ciwo da nauyin jikin da sabon dukan da ta san in ba Allahn ne ya tare ba se ta sha shi. "Shegiya munafuka me suffar muminai, tana sussunkwi da kai tana baɗala a haka kuma take cutar wasu suke mata kallon saliha ta gari se gashi ƴaƴan namu dai da ake zagin sune nagarin, kin matso kusa ko se na harbo ki da ƙafa ta, tambaɗaɗɗiya kawai". Da sauri ta matsa dan ta san kaɗan kenan daga aikin baba iro ya harba tan kamar yadda yace, ƙasa ta sa gwiwoyin ta tare da kai kanta ƙasa abinda su kuma suka fi tsana kenan dan sunce hakan wani salo ne na munafurci. "Me zata zauna tayi mana a nan iro, kawai taje ta kwaso ƴaƴan shegun nata mu wuce wajen megari dan wallahi ji nake kamar in watsa a turmi in dake shegu ita kuma uwar in shaƙe ta har se ta mutu". Baba habibu ya faɗa da iya gaskiyar sa yana demonstrating da hannayen sa, ita dai tana duƙe har lokacin dan ba'a ce ta tafin ba shawara ce suke yi a tsakanin su. Uban dundu Inna mariya ta ɗuma mata ta kuma bita da zagi "Ka ga min fitsararriyar da ba zata rama ragon sunan ta ba, wato ga sa'annin matacciyar uwar ki na magana shiyasa kika zauna kina kallon mu, to bari in kwaso shegun yaran in watsa a masai muga ta tsiya". Ai kafin inna ta gama rufe bakin ta tuni ta ɗiba tayi ɗakin a guje jin za'a watsa mata su a masai, Hassana ta riƙe a hannu yayinda ta goya Ussaina dan ta fahimci Hassanar tafi haƙuri dan bata fiya kuka ba se in Ussaina nayi ta kama. A saɗaɗe ta fito dasu wannan karon kanta a daidai tana bin su da kallo har ta kai gaban su ta sake tsugunnnawa, a yanzu kam Inna A'i da kallon da take bin su dashi ya ɓata wa rai itace ta kai mata duka a fuska, ba wai mari ba dan ba kuncin ta ta nufa ba kuma ta na sane ta kuma same ta a idon ta na dama, duk yadda idon ya ɗau raɗaɗi bata ko motsa hannun ta da niyyar taɓa wa ba. Ta daɗe da sanin idanun ta na ɗaya daga cikin abubuwan dake jawo mata tsana, kyara da tsangwama a cikin gidan, wato wani irin ido Allah ya halitta mata me kamar na maciji ko mage za'a ce, dan ƙwayar idon ta ba baƙa bace haka ma ba brown ba, wata color so similar to golden, sedai golden ɗin irin me ɗan duhu kaɗan. So da yawa su kawu, matan su ko ƴaƴan su sun sha goranta mata yanayin idanun nata duk tayi laifi, kai koma bata yi ba indai zasu haɗa ido se sun tanka mata, shiyasa tun lokacin da malamin Islamic studies ɗin su yayi musu addu'o'i ciki har da na baki shikenan ta ke yi, la haula kuwa kowane dare se tayi adadin da bata sani ba dan ba carbi ne da ita ba ta shafa a fuskar ta kafin ta kwanta haka kuma da asuba in ta tashi. Bata san a wajen wa ta gado irin wannan idon ba cikin iyayen ta dan bata yi wayo da ko ɗaya ba sedai da alama ba wajen babanta da yake ƙanin baba Habibu da baba Adamu wa ga baba iro ba ne, tafi kyautata zaton wajen mahaifiyar ta ta gado ko kuwa dai Allah ne yayi mata nata halittan daban, ko a makaranta seda hakan yaso ya zame mata barazana dan har se da shugaban makarantar ta tsawatar tukunna shiyasa har tayi ta gama bata da wasu cikakkun ƙawaye sedai na gaisuwar mutunci, kowa gudu da tsoran ta yake saboda kalar idon ta da ba'a saba gani ba cikin jama'a, tun bata saba da hakan ba har ya zo ya zame mata jiki ba ta ma damuwa. Zama suka yiyyi kan tabarmin da ke shimfiɗe a fadar me gari kafin suka shiga kai gaisuwa shikuma dattijon dake amsa sunan maigari na zaune kan kujerar ƙarfe kan sa ɗaure da rawani yana amsa musu. Kafin kace me jama'a sun fara ciki dan haka ake wa duk ƴaƴan da suka yi ciki a garin amma fa marasa galihu dan da Allah yasa ƴar maigarin tayi shiru kake ji wai maye yaci shirwa, karuɗuf ƴar magulmaciya tayi ciki, ba wanda yasan da zancen seda faɗan kishiyoyi ya haɗa shima kuma har rana wata yau ba'a yi irin wannan zaman a kanta ba gashi har ta haife tuni. Seda fadar ta gama cika sannan maigari ya fara sanar da abinda ya tara su wato dai batun cikin da Salame tayi ta haife batare da sanin su ba har gashi ƴaƴa sun kusa rufa watanni uku, hayaniya ce ta shiga tashi inda mutane da yawa ke Allah wadai da ita yayinda ƙalilan da abun ya faru kan ƴaƴan su suma suka shiga yi mata fatan Allah ya shirya a ganin su ai hakan ƙaddara ce (saboda ya faru ga nasu). Se da gurin ya lafa kafin maigari ya shiga jawabin sa kamar yadda ya saba "Bisa ga tsari na wannan gari bamu yadda da abun kunya ba ko yaya yake kuwa dan haka zamu aiwatar da abinda muka saba yi duk sanda aka samu irin wannan san zuciyar, a yanzu haka zamu karɓi ƴaƴan a kai su can nesa inda ba wanda ze san nata ne balle ayi mana gori kamar yadda muka saba tun da wannan shine karon ta na farko, da na biyu ne kuwa ko sama da haka to fa kun san hukuncin kora ne a kanta". Yana gama faɗar haka wasu fadawan sa suka nufo ta da zummar amsar yaran inda ita kuma cikin matsanancin firgici da tashin hankalin jin abinda ake kiran ze faru ta sake ƙanƙame ƴaƴan ta ta shiga kurma ihun ba ta yadda ba ba zata bayar dasu ba, kowa a gurin ya shiga mamakin abinda tayi, a ganin su ƴaƴan shegen take ihu dan za'a raba ta dasu, to meye abin so cikin ɗan shege?!. Muryar Salame da fiye da rabin ƙauyen zasu ce basu taɓa ji ba se gata ana jiyo ta tun daga farkon hayin maigari saboda yadda take ihun da iya ƙarfin Muryar da Allah ya bata, duk irin tsawa da zagin da babannin ta ke mata bata ma san suna yi ba balle ta saurare su ta daina ihun har se da maigari yasa fadawan su janye daga kusa da ita kafin tayi shiru ta sake matse ƴaƴan tana sauke numfashi sedai sam hankalin ta be kwanta ba dan tasan ba wai an ƙyale ta bane. Seda megari ya gama ƙare wa jama'ar wajen kallo kafin ya muskuta yana zarar ido "Tun da har wannan yarinya taƙi yadda da hukuncin mu to mun bata zaɓi biyu kuma a yanzu a nan gurin zata bayyana mana wanne ta ɗauka, na ɗaya ko dai ta bada yaran nan ayi kamar yadda aka saba dasu ko kuwa na biyu ta tattara ta bar mana garin ma'ana mun kore ta daga ita har ƴaƴan haka kuma duk sanda muka sami labarin shigowar ta to tabbas hukunci mai tsananin tsauri ya hau kanta, wannan sune zaɓin". Shiru kowa yayi kallo ya koma kan Salame da take jin komai da aka faɗa haka kuma ba tare da second thought na halin da ita ko yaran zasu shiga ba sanadin zaɓin ta ta buɗe baki ta zaɓi abinda take ganin ya fiye mata "Ba gari ba ko ƙasa ce zan iya haƙura in bar ta akan ƴaƴana dan haka na zaɓe su akan komai da nake dashi ciki kuwa har da asalina". Kusan a tare duk su baba Habibu, baba Adamu da baba iro suka miƙe jin abinda ta faɗa, wato ta zaɓi ta bar garin saboda ƴaƴan ta haka ta zaɓe su akan Asalin ta wato su dangin ta kenan. Shi kan sa maigari ba haka yaso ba dan a tunanin sa zata zaɓi bayar da yaran ne tun da in ta bar nan wa ta kama?, Bata da kowa banda dangin baban ta, mahaifiyar ta kuwa bama ƴar nahiyar bace, a yawon tuƙin babban mota baban ta ya auro ta dan haka ba wanda yasan komai a kanta kamar yadda basu faɗa wa kowa komai game da ita ba har kuwa ranar da ta bar duniya sanadin hauka da aka sa mata da ya kai sedai a ɗaure ta a ɗaki. Umarni me gari ya bayar kan dogarawa su bita gida ta ɗebi abinda zata ɗauka a rakata bakin gari ta tafi sedai fir baba iro yace ba abinda ta aje a sassan sa bare ta koma ɗauka dan haka su rakata bakin garin kawai, bata Musa ba ta shiga gaba dogaran na binta a baya dan tun da ta shafa taji jakar makarantar ta na jikin ta hankalin ta ya kwanta. Seda suka tabbatar tayi nisa da gari kafin suka juya zuwa gidan maigari suka sanar dashi an cika umarnin sa inda ya amsa da cuskunenniyar fuska dan ba haka yaso ba. Abinda mutanen garin basu sani ba shine maigari siyar da jarirai yake wa ƴan birni da suka rasa haihuwa da kuma masu aikin asiri though be san me suke dasu ba, shidai kawai a bashi kuɗi shikenan, da an samu yarinyar da tayi ciki se ya hana a zubar yace ta haife shi kuma ya sami ƙarin jari. Lokutan da kuma ba'a samun na banza hatta na sunna kaiwa yake dan akwai ungozomar da suka haɗa kai in ba na shege se a kai na sunna, yadda suke yi kuwa se an gama haihuwa lafiya lafiya se ta shafawa yaron wani magani da ta samo a wata asibiti dan ta taɓa zaman birni shikenan yaro se ya birkice da koke koke, ƙin kama nono da sauran su daga nan se a nufi wajen babban me maganin da suka yadda dashi da dukkan imanin su, dake shima nasu ne se yace ai ɗa ko ƴa na aljanu ne sun ɗauke naki sun musanya miki dan haka maza maza akai daji kaza daidai wuri kaza a ajiye musu kayan su, se an kai an ajiye ita kuma tabi dare ta ɗauka ta kaiwa maigari cikin gidan sa na sirri dake can bayan gari gefen dajika inda yake harƙallar sa. Guri ta samu ta zauna tana haɗiyar busasshen yawu dan gaba ɗaya bakin ta ya bushe da ƙishirwa, tafiyar ƙafa sabon tace dan haka ba zata ce ta gaji ba sedai rashin ruwan ke neman kassara ta ga kuma ƴaƴa har biyu gaba da baya ga jaka me nayi se abin yayi mata yawa. Mutsu mutsun Ussaina da taji yasa ta san ta farka dan haka ta sauke ta dan ta ɗan huta da goyon sedai ita ba hutun take nema ba abinci take nema da bata samu ba kuwa ta buɗe baki ta shiga canyara kuka da ƴar Muryar ta na jarirai, kukan Salame ta shiga yi itama dan abin ya haɗe mata goma da ashirin. Haka Ussaina tayi kukan ta har ta gaji baccin yunwa ya ɗauke ta kafin itama ta haƙura ta goge fuskar ta ta maida ta baya dan ba zata iya riƙon hannu ba ta cigaba da tafiya. Se da rana ta faɗi gaba ɗaya kafin ta shiga wani ƙaramin ƙauye dan gaba ɗaya gidajen dake ciki basu fi a ƙirga ba haka kuma daga ganin gidajen su kasan har yau su kam suna cikin duhun rayuwa wato ba wayewa ko ta misƙala zarratin dan duk bukkoki ne ba gidan ko ƴar jar ƙasa ɗaya. Kan wani kututturen dabino ta kai zaune tana ajiyar zuciya tare da numfashin ta dake fita ɗaiɗai saboda wahala da jigatuwa, nan take zaune har se da wani tsoho ya zo wucewa ya ankara da ita kafin ya ɗan matsa nesa da ita ya shiga ƙare mata kallo Sannan ya gyaɗa kai ya wuce. Be daɗe ba ya dawo dashi da wasu dattijan da kuma matasa suka dinga magana da Yaren su da bata san wanne bane kafin ɗaya daga cikin matasan ya nufi ta. Tambaye ce daga ina take, me ta shigo nema a shiyyar su, me take buƙata haka dai, amsa ta bashi da sunan garin su wato BA MUNI wanda sunan ya samo asali ne daga yadda duk wani ɗan garin yake kyakkyawa sedai wani yafi wani amma mummuna kam babu sedai ko baƙo shiyasa suke saurin gane baƙo a cikin su. Iyayen sa ya koma ya sanar da amsar da ta bashi, sunan garin su da kuma taimakon da tace ta zo nema, seda suka kuma sake zantawa cikin dai Yaren nasu kafin wani saurayi ya tafi be daɗe ba ya dawo da wata tsohuwa sedai ba tukuf ba, nuna mata ita suka yi inda ita kuma ta ƙarasa ta kamata ta miƙe kuma cikin fara'a tace mata "Kunto min jikokin nawa mana, da alamu sun daɗe a goye". Bata ƙi ba ta kunto Hassana ta bata ta bar Ussaina "Ita ma sauko ta ta huta hakana". "Tana da kuka ne Inna". Murmushi innar tayi alamun ta gane kafin suka shiga tafiya hannun ta dafe da zanin ta dan cikin sa ta ɓoye jakar ta da zasu je wajen Maigari ashe Allah ne yayi suna da rabo da yadda kawu iro yace ba zata koma masa gida ba shikenan sun salwanta. Bukka ce me ɗan girma suka shiga sedai abin mamaki har dasu gadon ƙarfe a cikin ta, fita Inna kamar yadda ta kira tsohuwar tayi bayan ta kwantar da Hussaina tsawon lokaci tukunna ta dawo da bahon katako a hannu, ruwa ne masu zafi a cikin sa haka kuma ba fari bane da alamun an zuba wasu abubuwan banda kuma ganyayyaki dake ciki, tuɓe Hassana tayi ta mata wanka da yasa yarinyar ta ringa sauke ajiyar zuciya a jejjere, Ussaina kam ta sha ihu da ana yi mata dan alamu sun nuna ba su taɓa shiga ruwa masu zafi haka ba. Se da ta tabbatar sun gasu kafin ta ɗau abin ta fice inda Salame ta yi saurin isa ta ɗau yarinyar ta shiga jijjiga da lallashi har tayi shiru, "Ga can ruwa ki je kiyi wanka kema ko kya watsar da gajiya". "Toh Inna". Tace tana kwantar da Ussainar a hankali gudun kada ta tashi daga ɗan baccin da ya fara sanɗar ta............................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 05 [ 11/27/2022 9:24 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                     FREE PAGE 005 _________________________📖 A sittin ta runtse ido tana taune leɓen ta sabida zafin da ya ziyarce ta ita kuwa Hassana da zaƙuwa take zuƙa tana sauke ajiyar zuciya har ta ƙoshi kafin ta saki. Se lokacin ta buɗe idon ta da ya ɗan canja kala ta kalli yadda yarinyar ke numfashi a hankali a hankali tana ciccilla ƴan ƙafafuwan ta tare da wasa da hannayen ta se ta ji wani sabon farin ciki ya kamata har ma taji zafin ya tafi. Zanin ta ta gyara a ƙirji ta miƙe ta saɓa ta a kafaɗa ta shiga jijjiga ta dan tayi gyatsa, a haka baba Husaila ta tadda ta se ta kwantar da Ussaina ta karɓi Hassana ta fita da ita a kafaɗa ita kuma ta koma ta zauna tare da ɗaukar Ussaina. Haka ta shayar da ita itama sedai ba kamar Hassana ba Ussaina akwai ci dan se da ta daɗe kafin ta ƙoshi hakan ma se da ta canja mata ɗayan shiyasa gaba ɗaya ƙirjin nata ya ɗume da zafi. Tun daga lokacin take shayar dasu amma duk da haka baba Husaila na haɗa musu da ƴan dabaru musamman Ussaina da ta fahimci yarinyar akwai tsotso in aka barta bata ƙi ta wuni da nono a baki ba. Iya ƙauna da mutuntaka baba Husaila da ƴan uwan ta sun gwada mata, Abinci da abin sha bata taɓa rashin su ba, ga kula da ita da ƴaƴan ta da suke yi tun bare baba dan ko rigimar Ussaina ce ta tashi da dare bata bari ta tashi cewa take ta koma tayi kwanciyar ta ita kuma tayi ta fama har se tayi bacci tukunna hankalin ta ze kwanta. Ruwan wankan su kuwa kullum se ta sa musu magani shiyasa alhamdulillah jikin su yayi ƙwari se fatar su da ta ɗan dafe saboda zafin ruwa da kuma kalar magani duk da yanzu sun fara sabawa da zafin ruwan. Sannu a hankali har ta cinye wata ɗaya tare dasu basu ankara ba saboda zama da yayi daɗi, jakar ta kuwa baba ta adana mata dan ce mata tayi da su ne za'a bar ta ta shiga makarantar in taje, yadda ƴan uwan baba ke son ta ita abin har mamaki yake bata, wai yau ita Salame da kowa ke gudu itace yau ake so ko da yake ai ba ita ake so ba ƙaunar ƴaƴan ta ce ta shafe ta dan haka be kamata tayi wani kauɗi ba. Mace ɗaya ce ta taɓa son ta a Karan kanta yadda take wato Hajiya Hadiza principal ɗin su, Allah ya sani tana son matar a ranta irin son da bata san yadda zata kwatanta shi ba. Ta so ta a lokacin da kowa ya ƙi ta, ta bata gatan da bata taɓa zaton samu ba, a bayyane yake badan ita ba da ba zata taɓa samun damar karatun da take so ba, ita ta ɗau ɗawainiyar komai na makarantar ta, kuɗin PTA, uniform, littattafai, takalmi, Safa, abinci da komai da zata buƙata a makaranta tun da ta fara kuwa bata gaza ba har wata ɗaya da kwanaki baya da ta gama, ita kuwa ai sedai tace da ita Allah ya saka da kuma ya zame mata wajibi ta so ta. Kallon baba Husaila dake zaune gaban ta tana mata lissafi kawai take yi yayin da idanun ta suka tara ƙwalla, kuɗi ne daga kan ƙwandala zuwa na takarda wai wanda aka haɗa mata dan tafiya makarantar su da zata yi duba mijin ta in yazo (kamar yadda tace musu). Hannu ta sa ta share hawayen "Dan Allah baba ki maida musu kuɗin nan kin ji, zan fa iya zuwa da ƙafa".ta faɗa murya na rawa "Amma dai salamatu baki da kirki, ya za'a yi mutum yayi alkhairi a maida masa, to kul kar in Kuma ji ko ke kin yi hakan kin ji ko?". Da kai ta amsa wa baba kafin ta shiga yi musu godiya da addu'a kamar Allah ne ya aiko ta har se da baban ta gaji ta fice ta bar mata ɗakin. Tuhumar kanta take kan me yasa tayi masu ƙarya gashi su kuma sun yarda da ita sun zauna da ita da zuciya ɗaya, jaddada wa kanta take Allah ma ya sani ba'a san ran ta tayi ƙaryar ba, bata so a raba ta da yaranta ne kawai. Da wannan ta tattara kuɗin da suka tasamma dubu ɗaya ta zuba cikin jakar makarantar ta, ta kuma haɗe kayan ƴan biyu ta ninke ta zuba cikin jakar su ta rakuɓa nata kala huɗu da take dashi. Kashegari tayi sallama dasu cikin rashin daɗin rai dan har da kukan ta haka ma baba Husaila da ta zauna wajen ta, ji take kamar yarinyar ta dawwama tare da ita dan bata da matsala sam, yarinya ce me kirki ga ladabi da biyayya, gata ba har dama, ga nutsuwa da rashin ƙyuya, duk sanda taga ta tashi aiki bata bari tayi komai se karɓe ta shiga yi shiyasa so da yawa ma bata tashi yi saboda tasan ba zata bari tayi ba. Su kuwa ragowar ƴan gari da matasan su ƴaƴan ne suke jin kamar su ƙwace ta tafi ita kaɗai dan sun shiga zuciyoyin su barin ma Hassana da bata da rigima, in aka fita da ita har se an tausaya an dawo da ita dan bata kuka se dai in ko Bata da lafiya ko kuwa ta kai maƙura wajen jin yunwa, toh haka dai aka rabu kowa na mararin kowa, rayuwar kenan! Ganin tana da isassun kuɗi a hannu se kawai ta tare mota bayan ta fita sarari, sunan Makarantar su ta faɗa masa suka yi ciniki ta hau ya kai ta har bakin gare kuwa. Wajen baba megadi ta bada ajiyar jakar kayan su ta wuce office ɗin Hajiya Hadiza wato principal, ba abinda ya dawo da ita makarantar illa son karɓar sakamakon ta tare da certificate ɗin kammala karatun ta dan tana so a duk inda taje ta ɗora karatun ta dan shine burin ta tun bata san ze iya cika ba ko kuwa ze rushe ne har zuwa lokacin da ta fara hasashen cikar sa wato da maigari ya sanya baki a kan karatun. Ba kaɗan ba Hajiya Hadiza taji daɗin ganin Salame wadda ke amsa sunan Salama kamisu a makarantar, cikin nutsuwa ta bata takardun ta da WAEC result ɗin ta dan dama alƙawari ne tayi mata ana sakin result zata bada a ciro mata nata. Cikin ikon Allah tana da credit bakwai da excellent biyu, Salame kam har dasu kukan godiya ga Allah dan ta san shi yayi mata komai ba wai ita ba haka kuma ta sanadin wannan matar me kyakkyawar zuciya ne wato Hajiya Hadiza, godiya kam haka ta dinga zuba ta tana yi tana hawaye lokacin da take faɗa mata ga Form nan na College of Education ƴan gora, wata local government a babban garin da ƙauyen su yake ta cike ta mata submission in tana so ita Kuma zata biya mata komai, da ƙyar ta iya tsayar da kukan ta sukai sallama ta tafi. Se da ta tsaya ta karɓi kayan ta wajen Maigadi ta ma sallama tukunna ta wuce, mota ta tara zuwa tasha inda batare da tunanin komai ba ta biya motar garin GAMJI dan a can ne makarantar da take son yi take. Motar na cika aka fara tafiya inda ita kuma ta fara nata tunanin kan irin rayuwar da zata yi a can ita da yaran ta dama yadda rayuwar karatun ta zata kasance, shafa Form ɗin da Maah Hadiza ta bata ta sake yi tare da lumshe ido tana ayyana batutuwa da yawa a ranta. Zata cike Form ɗin tayi submitting a can makarantar a karan kanta batare da jiran Maah Hadiza ba dan bata jin nan kusa zata kuma komawa koda hanyar ƙauyen BA MUNI ne, da kanta zata tsaya wa kanta tayi komai sedai ta yaya tunda ba kuɗin hakan ne da ita ba, gashi yanzun nan in bata manta lissafin da Maah take mata na kuɗin da za'a kashe kusan dubu sha biyar ne, registration goma da ɗari biyar ragowar kunji kunji kuma su cinye sauran. A ina zata samo wannan kuɗin ita da ba ta da kowa bata da kuma komai? Wannan shine tunanin Salame yayinda mota ke ta tsuga gudu a titi, ragowar passengers kowa da abinda yake yi, wasu hira, wasu kallo, wasu karatu wasu kuwa bacci. Itama dai cikin tunanin ta da yake kakare mata sanadin rashin abokan rayuwa wato kuɗi nata baccin ya saɗaɗa saɗaf saɗaf yayi wuf! Yayi gaba da ita. Hayaniyar da ta cika wa kowa kunne ce ta sanar da masu barci an iso in da zasu wanda Salame na cikin su, miƙa tayi a hankali ta kalli Hassana dake ɗaure a gabanta tana baccin ta hankali kwance, tun da aka fara tafiyar bata yi wani rigima ba se Ussaina da ta ɗan yi kuka ta kunto ta ta bata tasha ta kuma maida ta bayan ta ɗan bata ruwan leda da ta saya guda biyu tun a can tasha kafin su tashi. A hankali ta sauka daga motar hannun ta riƙe da jakar kayan su ɗayan kuma jakar makarantar ta da ta saka Form da ragowar takardun ta a ciki. Tun da ta sakko taji ana shelar kowa ya kula da jakar kuɗi ko kayan sa saboda ɓarayi ta kuma damƙe jakar makarantar a ƙirjin ta ɗayar kuwa ta mata riƙon da tasan ba me iya fincike ta a hannun ta ta sauƙi. Tunanin inda zata nufa ta shiga yi se kuma ta tuno yadda suka yi da Maah Hadiza da ta tambaye ta ko ina zata zauna in ta zo karatun tace mata ai duk me napep ɗin da tace ya kai ta gidan haya ze kaita dan ba ya wahala a garin GAMJI. Bakin tashar ta fita taƙi kula duk me napep ɗin dake cikin tashar dan bata yarda dasu ba, suma zasu iya zama ɓarayi ne, a nan titi ta sami wani tace ya kai ta gidan haya. Seda suka fara tafiya ya tambaye ta gidan mutane da yawa ko kaɗan "Kamar dai biyar ko bakwai". Amsar da ta bashi kenan shima be kuma magana ba ya shiga tuƙa abar sa cike da ƙwarewa, wata unguwa ya shiga mara wadatacciyar tsafta ga nan gidaje a wajen ba fasali se uban yara da suka cika layin jikin su ba kyan gani. Gaban wani gidan bulo yayi fakin tare da nuna mata gidan "Ko a layin in kika lura gidan na cikin gidaje masu kyau haka ma ɗakunan su suka da yawa megidan ma a nan take rayuwa a ɗaki ɗaya, yanzu dai bani kuɗi na in tafi". "Tsaya dan Allah, nawa ake biya na hayar?". "Wata shida dubu uku shekara kuma dubu shida". Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta sauka tare da fidda kayan ta ta bashi Naira hamsin ɗin shi ya tafi. Cikin ɗari ɗari gaban ta na faɗuwa ta shigar da kayan zauren gidan ta shiga doka sallama kamar sabuwar warkewar makanta "Kai haba wannan wane irin bala'i ne tun ɗazu ake ta waalaikumussalam amma dan baƙin rashin mutunci an ƙi shigowa, to dan Allah mutum ya ɗige a wajen ƙarƙari in na gaji in ɗau taɓarya in jirge mutum dan na gaji da iskancin ƴan unguwar nan, me ake da gidan haya ni saratu ban da dai ƙaddara". "A ƙaddarar dai ya rufa miki asiri in ba haka ba mutum ya fita titi mana ya kwanta, se shegen baƙin faɗin rai yawa ƴar ƙaruna, naga kuɗin hayar ma har yanzu ina bin ku ciko amma har kika samu bakin kankanba ". Salame dake zauren banda zarar ido ba abinda take yi jin sabuwar duniyar da ta shigo yau da rana tsaka, a gidan hayar ma wato dai ba hutawa mutum ze yi ba, ya baro masifar dangi ya shiga masifar wasu mutanen daban kuma. "Bismilla, ina me sallama ta shigo in ga kowace da kuma me ya kawo ta tunda Allah ya rufa asiri yasa nidai ba'a sanni da cin bashi ba". "A'a Hajiya wannan magana taki kuma me kike nufi, ina ce faɗan ku tsakanin ke da saratu ne to me kuma ya shigo da ni ciki?". Matar ɗaya ɗakin ta yi but ta fito tana faɗin haka acewar ta Hajiya ita take neman faɗawa magana da tace ba'a san ta da cin bashi ba. "Ai ba zan yi mamaki dan kin yi uwa kin yi makarɓiya a zance na ba Huwaila, in ma Baki yi magana ba ai se a canja miki suna, to ni dai na faɗa ba'a sanni da cin bashi ba sedai in ke aka biyo dan kece gandun bashi mara haƙuri da kaɗan a gidan nan". Turo ɗankwali gaba Huwaila tayi da alama zata karta rashin mutunci ne se kuma ga Salame ta shigo dan ta gaji da tsayuwa ta kuma fahimci da ɗaiɗaya da ɗaiɗaya wannan maganar se ta fiddo duk matan gidan ita kuma ba zata iya jumurin su gama ba, so take ta sami wajen sauke yaran nan ta huta. Kallan kallo aka shiga yi tsakanin ta da magidanta biyu wato Hajiya da kuma saratu se kuma matashiya ɗaya wato Huwaila, "Dama nace a kai ni gidan haya zan kama ɗaki shine aka kawo ni nan". "Aiho Allah sarki, ashe abin arziƙi ne ya same ni saratu da Huwaila ke neman yi min tawaiwai, shigo baiwar Allah ai nice me gidan ɗaki kuma Allah ya soki akwai ɗaya da masu shi suka tashi". Ajiyar zuciya Salame ta saki tana ɗaukar jakar ta ratse Huwaila da saratu ta shige ɗakin Hajiya da tace ta shiga. Ruwa me sanyi ta bata ta sha kafin tayi mata bayanin kuɗin ɗakin da ya ragu be kai sauran ba dan duk shine ƙarami dan haka zata bada dubu biyu wata shida dubu huɗu kuma shekara se ta zaɓa in sunje ta ga yayi mata. Buɗe ɗakin tayi suka shiga a tare sedai gani kaya a ɗakin yasa Salame juyowa ta kalle ta "Wanda suka saki ɗakin basu sami kwashe kayan su bane?". "To ni dai abin ne da mamaki, ganin gida suka tafi basu dawo ba dama sun ce min ba lallai su dawo ba dan haka suka kwashe kayan sawar su, wannan kuma suka ce in suka rufa wata uku basu dawo ba to sun bar min, yanzu kuma ana batun watan su na shida kenan basu dawo ba, ina ta son ɗaukar kayan ina kuma tsoro amma tun da gaki ga yara kuma naga baki taho da komai ba se ki yi amfani da kayan sedai zan ɗau ƴan abubuwan amfani da nake so acikin kwanikan". Saroro tayi tana bin Hajiya da kallo kamar wadda bata gane abinda tace ba, se da Hajiyar ta taɓa ta sannan ta sunkuyar da kai "Amma Hajiya daga gani na yau har se ki bar min duk wannan kayan arziƙin bayan ke aka bawa?". "Kin shiga ɗakina fa kin gani mene bani dashi da zan ce zan ɗauka?, wanda nace ɗin ma sha'awa ce kawai irin ta ɗan Adam amma gwargwado ai Allah yayi min suttura, kinga ki kwantar da hankalin ki ni ba haka nake ba dan haka ki shiga ɗaki in har yayi miki gobe zaki bani kuɗi na". Tana faɗa tayi gaba abinta Salame ta bi bayan ta da kallo tana murmushi, da alama matar zata yi daɗin zama ɗan alamu sun nuna bata da ƙyashi da hassada haka kuma bata da san kai. Jakar su ta shigar sannan ta shiga ta tsaya tana sake bin ɗakin da kallo, labulaye masu kyau kuma sababbi, fenti me kyau ga katifa ma me taushi da tudu, flower vase ƙarama a gefe, dustbin, tiles, carpet ƙarami tabarma nannaɗe a tsaye ga kuma wardrobe madaidaiciya itama a gefe. Hamadala ta shiga yi tana hawaye kafin ta kwance yaranta ta shimfiɗe kowacce kan zanin ta ta shiga gyara ɗakin..........................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment and share please. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 06 [ 11/27/2022 9:29 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                       FREE PAGE 06 _______________________📖 Seda ta Gama gyara ko ina dan dama ƙura ce kawai a ɗakin sannan ta lura da ƙaramin toilet tsayuwar mutum ɗaya, wanke shi shima tayi da ruwan da Hajiya ta bata jarka biyu ta roƙe ta gawayi ta ɗora musu ruwan wanka. Ƴan biyu ta fara yi wa wanka sannan itama ta samu tayi, bata iya ta nemi abinci ba ta kwanta bacci saboda gajiya. ★★★★ "Haba bawan Allah, ya kamata a ce ka saurara wa kanka wannan ɗimbin damuwar, fisabilillah shikenan kai in aka ga fara'a a fuskar ka sedai fake, ka sake kayi rayuwar kamar kowa ka ƙi, in ance dalilin da yasa rayuwa take zamar maka baibai kuma kaƙi yarda". A hankali mutumin da aka kira da bawan Allah ya shiga ɗago kan sa daga sunkuye da yake har ya ɗago baki ɗaya. Tsurawa wanda ya gama magana ido yayi na wasu sakanni kafin ya miƙe tsaye yana duban agogon hannun sa, bece masa komai ba ya shiga tarkata takardun sa ya zuba cikin briefcase sannan ya fita. Baki buɗe ɗayan mutumin ya bishi da kallo kafin kuma ya gyaɗa kan sa ganin yau iskancin bawan Allah har a kan sa, halin sa ne dama Amma ze iya rantsewa ya manta rabon da ya karta masa in ba yau ba. Fita yayi yana sanar da masinjan sa ya kulle office ɗin shima ya fita, kamar yadda yayi tsammani be ga ko shatin tayar motar sa a parking space ba, tasa ya shiga ya bar building ɗin shima. ★★★★★ 'Ban san wane irin aiki na tafka ba, ban san wace irin ƙwaƙwalwa gare ni ba da kullum bata bani mafita miƙaƙƙiya, duk da Riyya ta faɗa min nayi gaggawa in jira tukunna amma ni gani nake in na zauna to zan ta jira ne har na gaban abada, in bana son haka ya faru me zanyi kenan, me zan yi?!' Wannan shine tunanin da matashiyar ke tayi tana kai kawo a madaidaicin falon da yaji kayan alatu da alama dai tana cikin state of confusion ne dan se cije yatsun hannunta take cikin son samun mafita. Shigowar wata dattijuwa ɗakin yasa ta nemi kujera ta faɗa kamar wadda bata da laka, kallon ta dattijuwar tayi tana kaiwa zaune itama kan wata kujerar kafin ta shiga mata kallon tambaya "Yanzu shikenan Anna mu haka zamu zuba ido muna kallon komai na faruwa a gidan nan, ki duba fa watan yaya nawa yanzu da rasuwa amma ba wanda ke bin takan mu ke kuma naga ma abin ko ɗaɗa ki da ƙasa be yi ba". "Ni kin sa ba wani gane magana cikin magana nake ba gwara ki fito fili ki sanar dani me ke faruwa a gidan bamu sani ba". "Amma Anna kin san in mukai sake mun kusa barin daular nan mu koma kwana ƙarƙashin gada ko?". "Tuf tuf, Allah ya tsare ni.....". Anna ta faɗa tana tofar da miyau a gefe ".....banda neman masifa da bala'i irin naki me yakawo batun komawa ƙarƙashin gada kuma da ko a mafarki na gani in na tashi se na yi sadaka". "Nima ba so nake yi ba sedai in dai bamu motsa ba abinda ke daf da faruwa kenan". "Dan Allah yi min dalla dalla dan kin san bana san jan rai a magana". "Kamata yayi ace nice Abdu ze aura amma muna nan mun zuba ido yanzu haka naji jita jitar ze aure ƴar uwar Hajiya Babba". "Kam babban bu**uba, ni za'a kawo wa iskanci har gida, lallai Hajiya Babba ta ɗebo ruwan dafa kanta, ki kwantar da hankalin ki Audu bashi da wata mataa gidan duniya suke, da alama zan gwada musu barikanci na da basu sani ba". Cikin jin daɗi matashiyar ta gyara zama tana kai fuska gefe "Atoh abinda ya kamata dai muyi kenan dan yana auro wata kin san dole zamu bar gidan nan tun da yaya da ta haɗa mu ta raba Ni kuma shine bana fata". "Ki sa a ranki hakan ma baze taɓa faruwa ba, mu da gidan nan kuma mutu ka raba, mun shigo shi kenan fita kuma ba rana". ★★★★★ "Amma dai kin san ni ke san auran yarinyar nan shine kike wani batun wancan lusarin, yanzu da nayi magana kuma kice komai dan mu kike yi, ko ina basira a wannan tunanin naki oho, na daɗe ina faɗa miki tsufa yasa duk wata basira taki gujewa amma kin ƙi yarda, to wannan karon kam sedai kiyi haƙuri dan wallahi ba zan iya bin tsarin ki ba". "Kai kam ai dama baka da fahimta, komai se an zauna an maka gwari gwari kafin kake ganewa, yanzu kamata yayi mu kama yaron nan a hannun mu kuma dole se ta hanyar matar sa dan ai shi ba sakarai bane da ze dawo ya yarda damu bayan duk abinda suka dinga faruwa, amma ina matar sa ta zama tamu ai ruwa tasha kaga ta nan zamu dinga samun duk bayanan da muke so a kan sa kuma mu dinga aiwatar da shirin mu a kan shi hankali kwance har mu kai shi ƙasa". "A soke shi, ban yarda da wannan tsarin ba in har se ita zaki aura masa to a fasa". "Zo tsaya mana jarumina, tsaya ka saurare ni kaji?". Ta faɗa tana bin bayan shi da sauri sedai ko juyowa be yi ba balle ya tsaya saurarar ta kamar yadda take so, seda ya kai bakin ƙofar falon ya juya gare ta "In har aka gabatar da tsarin nan tabbas za'a samu matsala dan haka kar kuce ban faɗa muku ba, a soke shi shine kawai kwanciyar hankali". Yana faɗa ya fice yayin da dattijuwar ta dafe kanta tana koma wa bedroom ɗin da sauri ta ɗauki phone ɗin ta ta shiga dialing wasu numbers, tsawon lokaci tana ringing amma ba'a ɗauka ba har ta katse, tsaki taja ta kuma dialing, wannan karon ma kamar ba za'a ɗauka ba dan se a kusan ringing ɗin ƙarshe aka ɗauka, bata jira wani gaisuwa ba ta shiga kora dalilin kiran da tayi "Plan cancelled, a daƙile komai a kuma tsayar da komai zuwa lokacin da zan sanar dake yanzu akwai matsala a ƙasa". Tana gama faɗa tayi hanging call ɗin tare da wurga wayar kan bed itama ta biya cikin tunaninnikan dake yawo a kwanyar ta.                          ★★★★★★                          5 years later                          ★★★★★★ Cikin sauri sauri take Rolling veil ɗin a zagayayyar fuskar ta, pin ta manna a jiki bayan ta daidaita zaman mayafin sannan ta matsa daga wajen mirrorn, rashin ganin su a ɗakin yasa ta ja ƙwafa ta kwashi bags da food flask ɗin su ta fita dashi tare da jawo ƙofar ɗakin ta sa mata key. Ɗakin dake kusa da nata ta idasa tana ɗaya labulen "Barka da asuba Hajiya". "Barka kadai uwar biyu, ina dai kun tashi Lafiya". "Lafiya lau na tashi, su kam na san tuni kin san ya suke tin da sun ƙaura nan". "Aikuwa dai muna tare da ƙawaye tun ɗazu muna gaisawa". "Ai yayi kyau, bari mu wuce mun kusa makara, Ibty, Ifty maza ku taho mu tafi". "To se kun dawo, Allah ya tsare ya bada Sa'a". "Ameen Hajiya, mungode". Daga bayan labulen Hajiya suka fito se zarar ido suke yi dan sun san sun yi ba daidai ba, ita kam bata tsaya wata wata ba ta kama hannun su a each hand ɗin ta suka fita daga gidan. Napep ta tare musu suka hau inda ta e ya kai ta Star light Academy wato makarantar yaran. Juyowa tayi ta kalli Ibty dake gefen daman ta, da sauri yarinyar ta sunkuyar da kanta haka ma da ta kalli Ifty kafin kuma su haɗa baki wajen faɗin "We are sorry Mamma". Girgiza kai tayi ta maida hankalin ta batare da tayi responding masu ba "Please kiyi haƙuri Mamma, Allah Ifty ce tace muje mu gaida Hajiya tun da baki gama da wuri ba". "So Ifty ce yayar ki ko kece yayarta?". "Ba zamu kuma ba, insha Allah Mamman musu". "Allah yayi muku Albarka". Ta faɗa tana rungume kawun su, suma sosai suka kwanta a jikin ta suna faɗin ameen. Ko da suka je school ɗin bata bar su ba seda ta raka su class ɗin su primary one Sannan ta tafi bayan ta sake jaddada musu zama good girls. Cikin rashin jin daɗi ta tare wani napep ɗin ta shiga zuwa wajen aikin ta, sam bata so ba yau tayi latti, tun da ta fara aiki dasu zata iya cewa yau ne kawai ta makara amma se ta ke jin kamar ta aikata wani crime babba duba da yadda aka dinga maimaita mata rashin son makara a gare ta kasancewar tana riƙe da post ɗin secretary ɗin C.E.O na wajen baki ɗaya. Bakin makeken building ɗin ta tsayar da me napep ta biya shi kuɗin sa ta nufi gare ɗin. Ƙarin building me da yaji glass ta kusan ko ina haka kana kallon shi zaka bashi hawa kusan biyar ko bakwai a ƙiyasce, daga can saman building ɗin aka rubuta da manyan harufan, A.A GAMJI Company. Kamar ko da yaushe yau ma se da aka caje ta duk kuwa da kasancewar ta ma'aikaciya a wajen wanda wannan doka ce hatta shi kan sa C.E.O ɗin in ze shiga ko so nawa ne se an caje motar sa da shi kan sa, wannan yasa kamfanin ke daga cikin manyan kamfanonin da ke da cikakken tsaro da doka. Tun a bakin gate ta zare baƙar after dress ɗin da ta ɗora kan white hijab ɗin ta iya kafaɗa da rigar jikin itama fara iya gwiwa se dogon dark blue ɗin wando daga ƙasa, ƙafar ta kuma sanye da blue ɗin socks da takalmin ta wedge baƙi. Da sauri da sauri ta dinga takawa batare da ta kula gaisuwar da ma'aikata ke mata ba ta wuce lifter tayi pressing kan fifth floor inda nan ne office ɗin C.E.O ɗin yake, seda tayi wani gasping air ganin yau ya rigata zuwa dan ga nan office ɗin a buɗe alamun yana ciki. Kan table ɗin ta ta ajiye jakar ta da komai ta ƙara sa cikin office ɗin sosai da sallama, kanta a ƙasa amma yaji sautin amsawar sa can ƙasa. Ta jima a tsaye shiru tana jiran yace wani abu da zata sami damar bashi haƙuri kan lateness ɗin da tayi sedai shiru bece komai ba kamar ba kowa a ciki se sautin Ac dake aiki a hankali. "Ehm..am..amm..sorry sir..for the...lateness...it wasn't intentional, am sorry please". Ta faɗa a rarrabe baki na ɗan rawa jin shiru be da niyyar cewa komai. "Any schedule for today?". Da sauri ta ɗago tana gyaɗa kai uwa ƙadangaruwa "Yes...sure sir". Ta fice da sauri zuwa table ɗin ta tare da fara ƙoƙarin ciro iPad ɗin ta, inda Allah ya taimake ta duk sanda ta zama less busy ba wai ɓata lokacin take a banza ba, a'a tana rage wasu ayyukan ne kamar wannan schedule ɗin tun jiya ta haɗa shi gashi kuwa se mata amfani. Komawa tayi office ɗin.ta matsa gaban table ta ajiye masa iPad ɗin ta shiga yi masa bayanin schedule ɗin ɗaya bayan ɗaya, seda ta gama gaba ɗaya sannan yasa hannun sa dake cike da gargasa ya ɗau ipad ɗin yana bi, sanar mata da wanda zeyi attending yayi yayinda yace ayi postponing ragowar. With due respect ta karɓa ta juya ta fita first office inda nan take, gyara kayan ta tayi kana ta zauna ta shiga aikin ta cike da ƙwarewa da sanin makamar aiki. Tana nan zaune ya taho shiga office ɗin, kamar kullum cikin mutunta juna suka gaisa dashi, tana matuƙar girmama shi domin yasan mutuncin ma'aikata haka kuma ya riƙe nashi mutuncin, manager kenan HAISAM ƘADEER, babban makusanci ga CEO ɗin su da alama dan shi kaɗai ne bashi da wani shamaki na shiga office ɗin sa a duk wadda yaso. Alarm ɗin da ya shaida mata lokacin meeting ɗin da zasu yi yayi yasa ta miƙe ta tafi duba tsaruwar wajen, komai yayi yadda ya kamata se gabatar wa kawai, komawa tayi ta sake daidaita nutsuwar ta sannan tayi knocking a ƙofar, sakanni kaɗan aka bata umarnin shiga, kanta a ƙasa ta shiga "Its time for the meeting with Al-azhar group of companies sir". Takardun kan tables ɗin sa ya tura mata ta ƙarasa ta shiga tattara su har ta gama shirya su tas sannan ta riƙe a hannun ta ta fice dasu. Duban sa ya maida kan Haisam dake zaune ba shida ko alamun tashi "Haven't you heard what she said or you're deaf?". "Won't mind repeating sir". Dukan table ɗin yayi da hannun sa cikin nuna ɓacin ran sa da ba wanda ke katarin yawan gani se Haisam ɗin "For God sake ba wasa nake ba Haisam ka kuma san ba lokacin wasan bane, when it comes to business kafi kowa sanin wane ni dan akan haka zamu samu matsala, babbar matsala wallahi cos I won't mind suspending you". "Ai fa an taɓo rayuwar ka dole bakin ka ya buɗe, dan rashin mutunci tun ɗazu nake maka magana kamin banza amma yanzu ka cika min kunne da ihu, an ƙi aje meeting ɗin in ka tashi ba suspending ba kayi firing ɗina oga sir, aikin banza kawai". Haisam ya faɗa yana ficewa daga office ɗin bayan ya doka ƙofar da ƙarfin da har yasa salma ɗan firgita. Fashionable wrist watch ɗin ta ta duba taga its five minutes past exactly lokacin meeting ɗin, me yake damun boss yau, shine abinda take tunani, he's always a man of his word and time, Yana mutunta lokaci ta yarda ba'a jiran sa sedai ya jira, wannan principle ɗin sa ne. Buɗewar ƙofar yasa ta gyara tsayuwa ta yi ƙasa da kai, seda ya wuce gaba sannan ta bi bayan sa har zuwa scheduled hall ɗin, kamar yadda tayi zato kuwa kowa ya hallara hatta da manager kuwa se ita dashi ne kawai. Wajen zaman su suka ƙarasa ya zauna ita kuma ta ajiye kayan hannun ta ta gaida mutanen wajen ta shiga gabatar da bayanan da ya kamata ta wajen ta har ta gama tsaf kafin ta zauna ana tafa mata manager ya miƙe yayi nashi ƙarin bayanin da su kaɗai suka gamsar da mutanen siyan share a Company ɗin so shi bece komai ba se negotiation kaeai da aka yi dashi. Ya daɗe yana respecting yarinyar dan ta san ta kan aikin ta uwa uba tana da kaifin tuanni ga basira ga kuma kamewa ba kamar sauran mata da ya dinga ɗauka kan post ɗin ta ba da ko daɗe wa ba sayi yake sallamar su saboda halayyar akuyancin da suke yi......................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment and share fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 07 [ 11/30/2022 3:18 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. FREE PAGE 007 ________________________📖 Seda ta tabbatar an gyara an kuma rufe hall ɗin sannan ta koma bakin aikin ta. Haka ta wuni aiki kamar yadda ta saba se in ta samu ɗan lokaci ta huta se kuma ta ɗora, ƙarfe biyu lokacin sallah yayi dan haka ta ajiye ta wuce cike da tunanin dawowa ta gyara wajen da tayi mistake. Ana idar da sallah cikin babban masallacin Company ɗin da suke sallah ta miƙe bayan ta idar da azkhar ɗin ta ta nufi komawa ta steps Wanda haka kawai taji tana son bi ta nan dan ta motsa jiki. A step na kusan Ashirin da something suka yi bumping into each other batare da sun lura ba, baya tayi zata gangara ya yi maza yasa hannu ya tallafe ƙugun ta yayinda itama cikin firgicin tasa hannun ta ɗaya ta riƙe rigar sa ta wajen ƙirji ɗayan kuma ta zagaye wuyan sa dashi. Se da tayi regaining balance ya sake ta sannan ta lura da abinda tayi, da sauri ta zare hannun jikin ta na ɗaukar rawa, raɓawa yayi ta gefen ta ya wuce yana adjusting rigar sa da ta cukurkuɗa masa. Ranar har suka tashi aiki by 4 kamar yadda suka saba she wasn't herself tana dai daurewa ne kawai. Seda ta biya ta makarantar su Ibty ta ɗebe su dan four thirty ake tashin su kasancewar boko haɗe da Islamic school sannan suka wuce gida. Ta daɗe kwance kan katifar su kafin tayi ƙarfin halin miƙewa ta dafa musu ruwan wanka ta musu itama tayi sannan ta dafa musu spaghetti Dan tana da soyayyar miya. Ranar kasa gane kanta tayi dan gaba ɗaya jikin ta ya rikice kasancewar wannan karo na farko da ta taɓa samun close intimation da namiji babba kamar haka, a duk rayuwar ta tsakanin ta da maza baya baya ne ma'ana daga nesa nesa se gashi yau itace ɗare ɗare kan ƙirjin wani baligi hannun sa a cikin jikin ta. Duk da it was an accident amma se take jin ta wani guilty, kamar wata me laifi ko wadda ta aikata wani gagarumin laifi. Da ƙyar ta yaƙi tunanin ta shiga rayuwar ta kamar ko yaushe, ka shegari bata bari sun makara ba da wuri ta miƙa su school ita kuma ta wuce. Tun daga bakin gate ta lura da wani irin kallo da security ɗin ke bin ta dashi kamar wata mai laifi ko kuwa irin kallon kin shiga ukun nan, sosai ƙirjin ta ke bugu ta dai daure ta shiga ƙara sawa kaina building, ko a nan ɗin ma bata canja zabi ba haka mazan wajen ke mata kallon kamar munafuka ko me fuska biyu matan kuma na mata kallon an ji kunya. Jiki a sanyaye ta ƙarasa office ɗin sa ta gyara abinda ya kamata itace zata gyara ta gama ta koma nata, a irin kallon da mutanen Company ɗin ke mata yau se taji sam ba zata ko iya sarrafa jikin ta wajen yin wani aiki ba har se taji ba'a sin kallon hakan ya sa ta zauna jiran CEO ko manager taji gagarumin laifin da ta aikata. Har ƙarfe tara ta wuce ba CEO ba labarin sa haka ma manager abinda bata taɓa ganin ya faru ba haka kuma ya ƙara sata cikin zulumi, se after ten sannan CEO ɗim yazo, yanayin yadda fuskar sa take a haɗe yasa ta sha jinin jikin ta ta tabbatar tabbas laifin da ta aikata maigirma ne tun bare ma da ya tsaya ya ƙare mata kallo na kusan minti biyu kafin ya shige office ɗin sa. Be daɗe da shiga ba manager ya ƙaraso shima dai expression ɗin fuskar sa wasn't helping ko kaɗan, yau kam ko da ta gaishe shi hannu kawai ya ɗaga mata ya wuce. Jagwab ta koma ta zauna cikin seat ɗin ta tana addu'ar ko meye Allah ya kawo mata da sauƙi ya kuma taƙaita yasa kar su kore ta daga aiki dan in suka kore ta ba bata san ina zata kama ba. Ta daɗe tana shan wahalar neman aiki kafin ta samu wannan da ta ke ɗaukar ɗawainiyar kanta da ƴaƴan ta dashi, ta ya ba zata yi fatan kar a kore ta ba. Kusan hours ɗaya da shigar su office landline ɗin kan table ɗin ta ta hau ƙara, manager ne ke bata umarnin shigowa office ɗin CEO ta same su, a tsarge ta miƙe ta shiga takawa zuwa office ɗin, bata jin ɗaya daga cikin su ya amsa mata sallamar da tayi dan ita dai bata ji ko tarin ɗayan su ba "Have a seat miss Salma". Taji muryar manager Haisam haka kuma baya Musa ba ta samu kujera ta zauna kanta a ƙasa "Take a look at this newspaper please". Ya sake inquiring bayan ya ajiye mata takardar kan table a gaban ta. Hannun ta na rawa ta ɗaya ta kai kan takardar tare da juya front page ɗin ta shiga bin heading ɗin da kallo, cikin mugun sauri ta yar da takardar ta miƙe tsaye jikin ta na ɓari gaf gaf gaf kamar wadda aka watsawa ruwan ƙanƙara lokacin tsananin hunturun sanyi, girgiza kan ta ta shiga yi bakin ta na rawa tana son yin magana amma takasa, daga ƙarshe tasa hannun ta biyu ta dafe kanta tare da sulalewa ta faɗa kan sofar wajen tana ambatar kalmar innalillahi wa Inna ilaihi rajiun. "Relax, take it easy miss Salma, everything is gonna be fine". Abinda Haisam ya ringa maimaita mata kenan ganin yanayin da ta shiga sedai ita ba saurarar shi ma take ba "Bani bace, it wasn't me sir, wallahi bani bace". "Is okay, keep calm Please". Shiru tayi tana sauke numfashi tare da ajiyar zuciya kamar wadda tasha tseren gudun kilomita dubu ko sama da haka, sedai ta fara dawowa daidai kafin Haisam ya sake mata magana "Shin kin gane hoton nan miss Salma?". "Bani bace sir, taya zan gane hoton da bani bace a jiki". "Har na farkon ma bake bace?". "Sure, babu ni ko ɗaya a nan, editing kawai aka yi aka sa fuska ta, taya ma zan iya wannan abun and with someone I do respect the most, wannan wani tuggu ne kawai na maƙiya". "The first picture is real, kece a jiki and nima nine a jiki, it wasn't edition". Ya faɗa for the first time tun shigowar ta office ɗin "But taya ya zama real sir, yaushe har ma, har".ta kasa ƙara sawa "Yesterday's accident, we accidentally bumped into each other shine aka sami wanda yayi snapping iya inda suke buƙata wajen ƙulla makircin su". "Hasbunallah wani'imal wakeel". Ta faɗa tana dafe kanta dan ita se yanzu ma ta tuna da abinda ya faru jiyan dan tun da ta tursasa kanta mantawa bata kuma yarda ta tuna ba sam. Tsawon lokaci suna zaune shiru bame magana kafin Haisam yayi cutting silence ɗin "He'll marry you". A firgice ta ɗago jin wani sabon batun yashin hankalin "Who, how, why?". Ya jero tambayoyi ukun a tare, duk yadda suke cikin tashin hankali seda Haisam ya murmusa ganin yadda ta kiɗime da jin batun har ma fiye da lokyda ta ga hotunan "Firstly, lemme answer your question why, ko kun san a garin nan ba inda wannan jaridar bata shiga ba lungu da saƙo inda jama'a ke ta zagi da tsine muku ke da boss ɗin naki, a dalilin haka ba abinda zaki yi da ze dakushe batun se aure dan kullum maƙiya da mahassada zasu sami sabon abin faɗe ne akan hakan kuma duk ɓacin suna ne gare ku musamman shi da yake harkar kasuwanci ya kuma zama sananne, tun farko na ke kawai kin taka sawun ɓarawo ne amma ɓacin sunan wa shi ake nema nake ba. For your question how, to yadda ake kowane aure haka kuma za'a yi naku in less than a month insha Allah. For the last question, who, the answer is Alh ABDALLAH ABDULSALAM GAMJI. Hope I answered all your questions?". Gana ɗaya she's totally speechless, ita a bayanan sa ba kowanne ta gane ba, tukunna ma Who's Abdallah Abdulsalam Gamji? "But sir who's with the name da ka faɗa yanzu?". "Your boss here, the CEO A.A.Gamji company". Zuwa yanzu kam bata da abin cewa, to me kuma zata ce. "Kiyi haƙuri, auren ne kawai ze zama solution dan a yadda aka ɓata miki suna nan da shekara goma na bana jin akwai namijin da ze yarda ya aure ki, dan dai baki karanta abinda aka rubuta bane, yanzu ki sanar damu a ina zamu sami magabatan ki". "Bana tare dasu, ina rayuwa ni kaɗai da ƴaƴana a gidan haya". A hankali ya buɗe idon sa ya zuba kan Haisam irin me wannan take nufi, kau da kai Haisam yayi "Na fahimta, sedai su ɗin a ina suke dan kin san dole a wajen su za'a nemi auren ki". "Ƙauyen BA MUNI sedai bana tunanin zasu saurare ku dan ni ɗin korarriya ce". "Bangane ba, korarriya kamar yaya?". "Nayi aure ina secondary school batare da sanin su ba inda na haifi ƴaƴana biyu, bayan mun gama WAEC muna shirin zuwa gida mijin ya gudu se ni kaɗai na koma da ƴaƴan shine suka shegan ta su suka buƙaci in ba da su akai inda ban sani ba dan gujewa abin kunya acewar da naƙi shine suka bani zaɓin bada yaran ko kuwa barin su nikuma na zaɓi ƴaƴana". Kallon kallo aka shiga yi tsakanin Haisam da Abdallah inda kowa da abinda yake kitsawa a ransa, ture komai dake ransa Haisam yayi "Ina ce dai ƴan garin ku sun san wannan labarin in Kuma na faɗa za'a gane ke nake nufi?". "Sosai ma kuwa". "Shikenan za ki iya tafiya yadda ake ciki kuma zan sanar dake". Miƙewa tayi zata fita ya dakatar da ita "Ji nan, rabon ki da garin naku shekara nawa yanzu?". "Shekara biyar da watanni". Da kika shigo garin nan a ina kika fara zama, ko kuwa kuna da ƴan uwa ne?". "Sam ban san kowa ba a nan, na fara zama a gidan haya da nake zaune har yanzu". "Waye yayi sponsoring karatun ki". "Ni na ɗau nayin kaina da sana'ar haɗa turaren wuta da na dinga yiwa wata ƴar Maiduguri tana rarrabawa a faɗin Nigeria gaba ɗaya". "Sunan product ɗin fa?". "Ƙamshin amarya". "You can go". Fita tayi tana sauke ajiyar zuciya jin wasu tambayoyi daga boss ɗin ta kamar wani ɗan jarida, bata taɓa sanin yana magana haka me tsayi ba se yau, ita bata ga wani point ba a auren ta da suka ce ze yi, ita da sun ƙyale ta dan sam ita aure baya gaban ta balle mazan gaba ɗaya sedai dole saboda ƴaƴan ta da suka kasance mata tana buƙatar garkuwa irin ta ɗa namiji wanda ba ta inda zata sama musu ita se ta hanyar auren. "Amma meye point a tambayoyin da ka dinga yiwa yarinyar?, Beside Ina cewa kayi bayan komai ya lafa zaka sake ta?". "In shi kuma yaje ya jiyo abinda mu bamu sani ba a kanta ya riƙe matsayin makamin hana auren fa?". "You so stupid man, ya Ina tambayar ka kana maida min tambaya matsayin amsa?". "And what did I say wrong?". Dunƙule hannu Haisam yayi ya kai masa duka a kafaɗa shi kuma ya goce yana sakin silent smile na ganin yadda ya harzuƙa Haisam ɗin wanda ba wanda ke iya tolerating halin sa se shi kaɗai da Allah ya sallaɗawa so da ƙaunar sa. "Please bawan Allah let's be serious, kaga wannan auren ina so ya faru at all cost ko banda hatsaniyar jaridar nan har ma da jama'ar gidan ku, na rasa gane wace irin cukurkuɗaɗɗiyar rayuwa ce ke faruwa a gidan ku, da na zauna nayi tunani dole se da mace a tare da kai zamu fahimci kome ke tafiya dan na tabbatar wanda suka farmaki nafisa zasu sake yunƙurowa tun bare ma in ya zama kai ka samo matar da kanka". "Rayuwar gidan mu bahaguwar rayuwa ce da hatta ni da nake cikin ta ba komai nake fahimta ba, abu ɗaya na sani shine kowa mara gaskiya ne, kowa macuci ne haka kuma kowa mugu ne shiyasa na zaɓi na rayu on my own haka kuma bana don shigar da kowace ƴa cikin haɗarin dake tattare da rayuwa ta dan maharana suna da yawa Haisam, dalilin kenan da na haƙura da aure amma for now ya zama dole in miƙe in har zata shiga rayuwa ta ko da na kwanaki ne kuwa". "Me kake gani, mu bata hutu zuwa lokacin da komai ze tabbata ta fara amsa sunan matar ka ko yaya?". Relaxing yayi cikin kujerar da yake kai yana lumshe ido "Kasan meye damuwa ta?, Ƴaƴan ta, bana san a cutar da kowanne saboda ni, bana a ringa cutar da yaran da basu ji ba basu gani ba saboda wani ƙiyayya da ake min". Ya ƙarashe yana buɗe idanun sa da lokaci guda suka canja kala zuwa jajaja brownish "It hurts, it deeply hurt Haisam". Ya faɗa yana dafe ƙirjin sa ɓangaren hagun sa alamun yana masa ciwo "Calm down Abu Aulad, calm down insha Allah ba abinda ze same su". Rufe idon sa yayi tare da kife kan sa kan table ɗin gaban sa ya shiga ajiyar zuciya akai akai tare da haɗiye wani ƙullutu me matuƙar ɗaci da ke taso masa duk sanda ya tuno yara, yana matuƙar san yara a rayuwar sa hakan yasa ake masa Indiya da Abu Aulad tun yana saurayi, da ya zama magidanci kuwa yayi aure burin sa da fatan sa ya haihu ne kawai, lokacin da Allah ya bawa matar sa ciki irin murnar da yayi ba me misaltuwa bace sedai Allah be nufa rayayyu bane daga uwar har ƴaƴan. Miƙewa yayi ya zafi key ɗin sa ya fice da sauri kamar ze tashi sama haka ma Haisam ya bi bayan sa, yau dai kam ba abinda suka tsinana....................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️ Ote, Comment and share fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 09 [ 12/1/2022 1:04 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable.                      FREE PAGE 009 ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. _________________________📖 tafiya ce sosai daga Gamji kafin a kai ƙauyen Ba muni dan har se dasu Ibty suka gaji da kwaramniya suka yi bacci a jikin Haisam dake baya a tare dasu. Ita kam salma wani irin nervousness da faɗuwar gaba ne ya sarƙe ta, after good five years da barin ta gida yau gashi zata koma kan mau'idin da bata san wanne bane, abu ɗaya ta sani shine akan maganar auren ta ne aka tashi tafiyar. Motar shiru baka jin tashin komai se numfashin su a hankali a hankali da kuma gudun Ac dake tashi, Haisam kam wayar sa yake pressing hankalin sa kwance yana chat abinsa da budurwar sa yayinda a ta gaban motar kuwa tamkar wasu kurame ko saƙaguna haka suke zaune. Shi tuƙin sa kawai yake ita kuwa ba abinda take se bin hanya da kallo kamar me irga bishiyun da suke wucewa, tunanin yadda zata riski garin bayan shekara biyar da tayi bata cikin sa take, maganar tarba kuwa tasan ba wata tarba da zata samu a wajen ƴan uwan mahaifin nata. Abu ne ba ɓoyayye ba cewa murna da jin daɗi suka yi lokacin da ta zaɓi barin su saboda ƴaƴan ta, irin wulaƙancin da suka yi mata na ƙin barin ta ta ɗau ko tsinke a gidan be bar kanta ba kuma bata jin ze barin har nan da gaban abada. Wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya ta saki lokacin da suka shiga garin tana me lumshe ido cikin kiran sunan Allah a ranta, a kaikaice ya kalle ta dan sosai ajiyar numfashin nata ya fito fili. Gidan maigari ya nufa kamar jiya, seda duk suka fita daga motar suka barta dan ji tayi gaba ɗaya kamar bata da wani sauran laka a jikin ta, jikin yayi mata nauyi kamar baya tare da ita, Haisam da ya lura bata biyo su bane ya juya ya tabbatar sannan ya maida kallon sa kan Abu Aulad "Madam fa bata fito ba, ina ganin kaje kaji ko da damuwa ne ni Bari in ƙarasa ciki". Ya faɗa yana yin gaba da sauri dan yasan kaɗan daga aikin bawan Allah yace shi yaje ya duba. Ganin yadda ya tafi yabar shi a wajen yasa cikin takaicin abinda tayi kamar wata ƙaramar yarinya ya koma wajen motar, murfin ɓangaren da take zaune ya kama ya buɗe da ɗan ƙarfi dan ransa ya ɓaci da abinda tayi, ya zata wani nemi waje ta zauna a mota bayan tasan suna da abubuwan yi da yawa a gaban su. A ɗan firgice ta buɗe idon ta da ke lumshe hakan yasa suka yi wani walai kafin suka shige cikin nasa da ya tsare ta dasu, da sauri ya kau da kan sa dan jin wani dam da gaban sa yayi ganin ƙwayar idon ta, be taɓa sanin haka ƙwayar idon ta take ba se yau, "Kina jira a ɗauke ki ne kafin ki fito?". Tsam tayi jin abinda ya faɗa dan bata gane me yake nufi ba "Malama ki fito mu yi abinda ya kawo mu dan ba kwana zamu yi ba kin sani ko?". Ƙafarta dake ajiye gaban motar ta ɗaga a hankali ta fitar waje kafin ta fara ƙoƙarin fitar da gangar jikin ta hakan yasa aya matsa daga tsayuwar da yayi jikin motar, seda ta gyara mayafin kanta sannan ta yi gaba shi kuma ya kulle motar da mukulli bayan ya buɗe glass ɗin baya kaɗan saboda su Ibty dake kwance suna bacci. Gaba ɗaya ido mutanen wajen suka zuba mata suna kallo yayinda ƙananan maganganu ke tashi dan jiya da yawa da suka san abinda ya faru da ita da suka ji batun ɗaurin auren ta ba ƙaramin tu'ajjabi suka yi ba barin ma da suka ga zuƙeƙen mijin da Allah ya bata. Yanzu kuwa ba wai sun gane ta bane maganganun kan irin kyan ta da kuma na kayan jikin ta ne, ƴan gayu irin ta dasu Haisam ba kasafai suke shigowa garin ba shiyasa duk sanda suka shigo suke zama abin kallo da sha'awa ga jama'ar garin. A hankali ta saluɓe brown heel shoe ɗin dake ƙafarta ta kai zaune kan shimfiɗar fadar maigari kafin cikin sanyayyar Muryar ta ta shiga gaida shi kamar yadda suke yi a al'adance. Cikin rawar jiki maigari ya amsa duk da bai shaida cewa Salame bace, a tunanin sa wata ce daga dangin su ɗan birni suka zo da ita tare maybe dan taga mahaifar matar da ya aura ko wani abu. "Ala gafarta malam, ga Salman nan gaban ka mun zo da ita dan kayi mata bayanin yadda auren ya ƙullu jiya a kuma bata sadakin ta dan ta shaida". "Ikon Allah, yaro kana nufin nan Salame ce a gabana, lallai Allah mai iko, sannu Salame, sannu kinji". Maigari ya faɗa cikin ruɗewar jin wai wannan tsaleliyar budurwar ce Salame da suka kora da goyon ƴaƴa biyu shekara biyar da suka gabata, yarinyar da ko da ta bar garin ba komai gare ta se tarin tsumma dan hatta takalmi babu a ƙafarta ranar. "Nice baba maigari, fatan mun same ku lafiya". "Lafiya lau salamatu, ya yaran naki? Ko kin bar su a gida ne?". "A'a baba suna mota bacci suka yi shiyasa ba'a ɗauko su ba". "Allah Sarkin hikima, yanzu sun girma abin su ko, hekara biyar ai ba nan bace dole yanzu sun girma". "Aikuwa dai". Ta faɗa tare da jan bakin ta ta tsuke ganin surutun na maigari bame ƙare wa bane ita kuma ta zaƙu taji bayanin da aka ce yayi mata da in ba kunnuwan ta ne basu jiyo daidai ba kamar taji ana batun an ɗaura mata aure ne tun jiya "Wato salamatu jiya yaran nan suka zo nan suka same Ni da batun neman auren ki, duk da ko a Shari'a ni me bayar da auren ki ne amma se na bawa iyayen ki haƙƙin su ta hanyar sawa a ka kira su na shaida musu abinda ke shirin aukuwa sedai dake Habibu ba ɗan bana da arziƙi bane se yace shi sam babu shi a lamarin ki haka ma iro, se Adamu ne shi dake wani sa'in yana da tunani ya saurari yaran nan amma yace sedai in a ɗaura auren a jiyan dan baze juri a Kuma tado shi daga wajen sana'ar sa domin ki ba wannan yasa dole aka ɗaura auren bisa sadakin da shi mijin ki ya biya wato dubu hamsin gashi nan a zaune, yanzu bari in tashi in ɗauko su gare ki, kin ji yadda batun ya kasance". Wani irin suya zuciyar ta ta shiga yi cikin ƙirjin ta jin irin cin kashin da ƴan uwan mahaifin ta suka aikata yayin neman auren ta, shin me ta kashewa mutanen nan ne da suke neman se sun wulaƙanta ta ido rufe?, Shin akwai ɓoyayyen dabi ne tsakanin mahaifin ta dasu ko kuwa, su dai ba ƴan uba ba balle tace ƴan ubanci suke gwada mata, ko kuwa duk ƙiyayyar mahaifiyar ta ce ta shafe ta har haka. Hannu tasa ta goge hawayen da suka gangaro kan kuncin ta daidai lokacin da maigari ya miƙawa Abu Aulad sadakin ta shikuma ya ajiye mata kan cinyar ta, murya na rawa ta shiga magana "Nagode sosai baba, Allah ya saka da alkhairi ya ƙara girma sedai Ina son ganin su baba habibun game da gado na dake wajen su". "Babu komai salamatu, ke ɗin ai ɗiya ce gare ni, abinda ya faru a baya ma saɓanin fahimta da kuma zugar iyayen ki ne, yanzu bari in aika su zo se ayi batun gadon naki". Ɗaya daga cikin dogaran sa ya aika azo dasu baba Habibu dukan su, ba'a jima ba dogarin ya dawo tare dasu suna bin shi abaya se ƙunƙuni suke na yadda ake shiga rayuwar su kan wata banza can Salame da suka daɗe da tsamewa matsayin jinin su. Gaban maigari suka zube suka yi gaisuwa, salma ya nuna musu bayan ya amsa ya shiga kora musu bayani "Ga Salame nan mijin ta ya kawo ta na mata bayanin auren su da aka ɗaura jiya se kuma gashi tazo da batun gadon ta dake hannun ku tana neman a bata kason ta". Maigari ya ƙarashe yana gyara saɓa hannun babbar rigar jikin sa tare da furzar da tiƙar goran dake bakin sa, ido waje baba Habibu da ƴan uwan sa ke kallon tsaleliyar budurwar da aka nuna musu wai Salame, cikin rashin yarda baba Habibu ya furta sunan ta "Salame". "Na'am baba barka da rana". Ta faɗa tana buɗe idanun ta sosai a kan su dan su san fa yanzu ba da bane da take shakka da tsoran su, cikin sanyin jiki baba iro yai gyara zama dan ƙwayar idon ta kawai ya kalla ya shaida ita ce. "Dama nace gadon baba na dake hannun ku nake buƙata baba dan Ina son yin amfani dashi". "Eh to, gado ko, tabbas kam kamisu ya bar gado sedai yana wajen Adamu ai bani ba". Da sauri baba Adamu da yaji baba Habibu na neman zame wa ya bar shi a ciki ya buɗe baki "Ina ce gona ce kawai a wajena Habibu?". "Ai dama ita nake nufi, am ke Salame sedai fa kiyi haƙuri dan kiwon da ya bari tuni babu su, da su ne mukai ta amfani wajen ciyar dake har zuwa lokacin da kika bar wajen mu dan haka gona dai tana nan ban da ita kuma babu komai". Ya faɗa yana kai da kai gefe cikin rashin gaskiya. Girgiza kai akwai tayi dan tasan ba wani an ciyar da ita an cinye ne kawai babu su yanzu, gonar ma tasan ban da albarkacin yanayin da ya ganta na wadata da kuma waɗanda ke tare da ita da baze bayar ba itama cewa ze yi an siyar an kula da ita. "Allah ya amfana gonar, sedai ina da buƙatar ta ujila zan yi amfani da ita". "Amma ina ce kinji ance tana hannun Adamu, shima amfani yake da ita dan haka sedai kiyi haƙuri, gona na mazaunin taki amma ya riga yayi shuka dan haka se yayi girbi se ki karɓa". Cikin rashin tsoro ko shakka ta dubi baba Habibu dake maganar cikin hatsari da gadara "Zan bar tane sabida a hannun baba Adamu take banda haka bana jin da wani ne ba shuka ba kome yayi se dai ya kwashe ya kai inda yake dashi tun da dai gona mallaki nace". Daga baba Habibu har baba iro tsumu suka yi cikin kunya dan sun san da su take, wato da ba Adamu bane dole a bata a bar ta, lallai yarinyar nan ta goge. Abu Aulad da yaji an kawo matsaya ya miƙe dan tuni yake kallon agogon hannun sa, baya san suyi dare kamar jiya dan a tsarin sa a yau yake son ta tare a gidan su dan ya nuna wa duk wani dake tunanin ce iya juya shi ko iko dashi ƙarya yake, be isa ba kuma be kai ba, anyi a da amma banda yanzu!. "Mungode sosai, ga wannan a siya horo, Allah ya ƙara girma, ku tashi ku tafi ko?". Ya faɗa yana ajiye wa maigari bundle ɗin ɗari bibbiyu, miƙewa tayi tana adjusting pin ɗin mayafin ta da taji ya ɗan matse ta, har bakin mota maigari ya raka su inda su baba Habibu suka zama ƴan kallo, Haisam ne ma yayi tunanin basu ƴan canjika dan shi uban gayya ko kallo biyu basu samu daga gare shi ba. Tun jiya mutuncin su ya zube tsaf a idanun sa saboda abinda suka yi, me ɗan daman cikin su ne baba Adamu dan shine kawai ya samu gaisuwa daga gare shi. Haisam na buɗe bayan motar Ibty ta fito tana mutsittsika ido tare da tura baki gaba cikin son fashewa da kukan rashin ganin Mamman ta, da sauri Salma ta riƙo hannun ta tare da jawo ta gaban ta. Duƙawa tayi zuwa tsayin yarinyar ta cire mata hannun ta dake kan fuskar ta, ɗaga mata gira tayi tare da jan kumatunta tana sakin mata murmushi itama yarinyar ta maida mata sannan ta shige jikin ta tana sakin ajiyar zuciya, seda ta tabbatar ta dawo daidai sannan ta kama hannun ta ta buɗe gaban motar zata shiga baba maigari dake kallon su ya magantu "Masha Allah, tubarkallah, hala wannan ɗaya daga cikin yaran ne salamatu?". "Eh baba, Hassana ce Ussaina na bacci bata tashi ba". "Allah Sarkin hikima da buwaya, tubarkallah yarinya kyakkyawa kamar ƴar turawa, Allah ya raya yayi musu Albarka, Allahu Akbar da girma yake". Da Ameen ta amsa masa tare da shigewa motar dan shima tasan borin kunya ne ya ke yi na abinda yayi mata lokacin da tafi buƙatar taimakon su shiyasa duk wani rawar ƙafar sa be ɗaɗata da ƙasa ba. Numfashi ta sauke na samun relief lokacin da motar su ta fara tafiya kan burjin har ƙasar dake garin, tasbih tare da godiya kawai take yi cikin ranta wa Ubangiji da ya canja mata rayuwa daga wata mara ma'ana zuwa wadda take ciki yanzu. Nauyi taji ƙirjin ta yayi mata lokacin da ta tuna cewa yanzu fa ita ɗin matar aure ce, matar Abdallah Abdulsalam Gamji shugaban fitacaccen kuma shahararren kamfanin A.A Gamji. Bata san wace irin rayuwa ce kuma ke jiran ta nan gaba ba a gidan auren ta sedai tana fata koma wace irin ce ta zo mata da sauƙi, akasin haka kuma Allah ya bata wuyan ɗauka ya kuma yi riƙo da hannun ta wajen ganin ta samu mafita akan dukkan matsalar da zata tunkaro ta. Ta daɗe da sanin ita rayuwar gaba ɗaya jarrabawa ce, gwaji ce da bawa ba zai daina samun shi ba har se lokacin da rai yayi bankwana da gangar jiki wadda ranar ce ba wanda ya sani tunda ita mutuwa ba sallama take ba haka kuma ba wai notice take bayarwa ba bakuna allo ne da ake rubuta jadawalin sunayen mutanen da zasu tafi yau, gobe jibi da ma kullum ba. Cikin wannan tunanin suka shigo garin Gamji, tafiyar ba kamar ta ɗazu ba yanzu kam hira ce suke yi shida Haisam jefi jefi yayinda ita tayi nisa cikin duniyar tunanin da take yi tana daga zaune rungume da Ibty a jikin ta. Haisam ɗin suka fara saukewa inda suka yi sallama da abokin nasa kuma shugaban sa kan se sun yi waya yayinda cikin nutsuwa ya cigaba da driving motar har zuwa gaban gidan su da bata san yaushe ya sani ba kuma ya wa ya sanar dashi ba. Parking yayi a ƙofar gidan, ganin yadda ya kai kai gefe yasa ta shanye mamakin ta ta buɗe ƙofa Ibty ta fita zuwa cikin gidan ita kuma ta zaga baya ta ɗau Ifty dake bacci har lokacin ta kai ciki wajen Hajiya dan bata samu zarafin tsayawa buɗe ƙofar ɗakin su ba ta koma gare shi. Gefen ƙofar da ta fita ta tsaya tare da duƙar da kai ƙasa "Mungode sosai Allah ya huta gajiya, a gaida gida Allah ya tashe mu lafiya". "Shigo". Kallon shi tayi tana sake nanata kalmar shigo ɗin da yace, to ta shiga tayi me bayan yanzun nan suka dawo tare dashi?. Ganin kallon da ya ɗago ya jefa mata yasa bata san sanda ta kai zaune kan kujerar motar ba sedai ƙafafun ta na waje...............................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 08 [ 11/30/2022 3:14 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. FREE PAGE 008 _________________________📖 Gaban tanƙamemen gare ɗin gidan ya tsaya yayi horn, cikin sakanni gate ɗin ya fara zugewa da kan shi har ya gama ya tura hancin motar cikin babbar harabar gidan. Daga kallo ɗaya in kayi wa cikin gidan zaka san gidan family ne ma'ana gida ne da ya kasu kashi kashi (parts-parts). A lot ya kashe motar ya fita cikin cikakken takun sa da yake da ƙarfi ya nufi sashen mahaifin sa, a yanzu base anjima ba yake san isar da saƙon sa gare shi. Yana yin sallama ya ɗaya labulen ƙofar tare da shiga falon, zaune kan kyakkyawar shimfiɗar da ta kewaye falon gaba ɗaya yake zaune tare da dattijuwar matar sa, dattijo ne da kallo ɗaya zaka masa kasan shekaru sun tura amma ba alamar yanƙwanewa ko wani rashin ƙarfi tattare da shi. Zama yayi gaban sa bayan ya tanƙwashe ƙafafun sa ya gaisar dashi cike da ladabi sannan ya ɗora da batun da ya kawo shi batare da ya dubi tsohuwar dake zaune ko ya nuna ya san da ita ba. "Na samu matar da nake son aura har ma mun gama daidaitawa, nasan an kawo maka wata jarida game da ni to yarinyar jiki ce zan aura ɗin, sunan ta Salma, magabatan ta na garin BA MUNI bana san a ɗau lokaci sosai ne, ba budurwa bace ta taɓa aure da yaran ta biyu". Tun da ya fara magana wani irin firgicin ya wanzu kan fuskar matar har hannun ta ya fara ɓari wanda se da ta jimƙe shi tukunna ya tsaya, da sauri ta maida duban ta ga mijin ta dan jin me zece "Amma ai ka bari ayi bincike a kan ta ko, banda rashin hankali irin naka Abu Aulad ka rasa matar da zaka aura se wadda hotunan ta ya gama zaga gari da sunan ɓatanci, to sam ban lamun ta ba ma, hakan ba ze taɓa yiwuwa ba, ga nan babar ka ta daɗe da sama maka mata tsoron halin ka yasa ta kasa faɗa maka amma ni yanzu na sanar da kai kuma sati biyu masu zuwa za'a yi auren". Wannan karon gaba ɗaya ya ɗago yana kallon mahaifin sa cikin yanayin ba fa zan yarda ba "Sam hakan baze yiwu ba Baba, a wancan karon ka kawo min nafisa ban yi musu ba amma a wannan karon kam bana jin akwai wanda ze dakatar da ni, bincike akan yarinya ni duk na gama shi, hotuna kuma nawa da nata ne sukai yawo dan haka ba matsala mata da miji dan sun zaga gari an san su, batu na wata ƴa kuwa bani da uwa balle ta zaɓar min, infact babu wani mahaluƙi da ya isa ya min auren da bana so a wannan karon, ka samin albarka dan a gobe zan je in auro ta Dan addini ya bani damar nemawa kaina aure kasancewa ta namiji, se an jima". Yana gama bayanin sa ya miƙe tare da ficewa da sassarfa, yana fasa bari nan da sati ɗaya tun da ya fahimci abin iskanci ne, a gobe ze je ya auro ta ya ga wanda ya isa yace ya sau ta in akwai shi. Dan anga yana yin shiru se a dinga maida shi wani soko ko wanda be san kan sa ba, to an shigo da'irar da ba ragayya tsakanin sa da kowa yanzu, ze fubi ifon kowane mahaluƙi da yanemi shiga hanyar sa sannan ya kawar dashi. Waya ya ɗauka ya shiga kiran Haisam da tuni ya wuce gida tun lokacin da ya tabbatar gida ya nufa, ringing bitu ya ɗaga "Ka fito bakin titi gani nan zuwa, ina nufin a ƙafa". Ya faɗa batare da ya jira jin me Haisam ɗin zece ba haka be tsaya sauraren me ze faɗa ba bayan ya gama bayanin sa ya kashe wayar. Kamar yadda ya faɗa a titin ya same shi, gefen sa Haisam ya shiga yayi wa mota wuta batare da ya sanar dashi ina suka nufa ba, shima tun da yaga yanayin sa se be tambaya ba. Gudu ya dinga tsugawa a titin har suka fara fita gari, be tsaya ba seda aka kira sallar Azahar suna idarwa kuma suka sake ɗaukar hanya. Ƙarfe biyar sannan suka shiga ƙauye BA MUNI, kai tsaye gidan me gari ya tambaya aka nuna masa ya wuce, suna zuwa suka fita sannan ya kalli Haisam "Auren yarinyar can muka zo nema, gobe zamu dawo a ɗaura aure". Baki sake Haisam ya bishi da kallo jin wani sabon tsari kafin kuma ya bi bayan shi ganin har ya kusa shigewa fadar me garin. Kan shimfiɗun wajen suka zauna maigari kuwa se rawar jiki yake yaga ƴan gayu cikin kaya masu kai da walƙiya, cikin ƙanƙanin lokaci ya sanar dashi abinda ke tafe dashi aikuwa da sauri maigari ya tashi ɗan aike aje a taho da su kawu iro. Ba'a daɗe ba se gasu sun bayyana gaban maigari kowanne futu futu dan yawancin su dawowar su kenan daga gonaki da wajen aikin ƙira. Baɓata lokaci maigari ya sanar dasu dalilin kiran, baba Habibu yayi tsalle yace shi ba shi a cikin maganar yarinyar da ya zaɓi shegun ƴaƴan ta akan su haka ma baba iro. Baba Adamu ne yayi sassaucin cewa sun bayar a ɗaura yanzu in har da gaske yake kawai dan shima ba ze yadda a Kuma tado shi daga wajen sana'ar sa ba gobe kan batun auren wata can wai Salame. Ba ɓata lokaci kuwa aka ɗaura auren Salma Khamees da Abdallah Abdulsalam Gamji bisa sadaki dubu hamsin da ya bayar lakadan ba ajalan ba a fadar maigari. Basu kuma jiran komai ba suka juyo da ɗimbin goron da suka siya a garin na ɗaurin aure, basu kai gida ba se wajejen goman dare, Haisam ya fara saukewa kafin yayi masa godiya ya wuce gida shima. ********** "Ina sam ba zan bari haka ya yiwu ba wallahi, taya ya yaran nan ze shammace ni haka bayan ina nan ina shirin aura masa shuraiha, kai dole ma ita ce aura dan ba zan yi sanyar ya ɗauko wata a waje ba, nasan duk ma wannan fuffukar ta banza ce dan haka bari gobe tayi zan yi wa tufkar hanci, auren nan da sati za'a yi inga ta tsiya". Hajiya Babba ta faɗa wa kanta cikin tabbatar da abinda zata iya taba kaiwa zaune cikin sauke ajiyar numfashin samo mafita da tayi, ta daɗe tana zaune ƙafarta ɗaya kan ɗaya tana karkaɗawa ciki sake zurfafa tunani har dare yaja kafin ta haƙura ta kwanta bayan ta sake maimata shawarwarin da ƴaƴan ta suka babbata ta ɗau na ɗauka ta watsar da na watsarwa. ******** "Anna da zafi zafi fa akan daki ƙarfe ya kamata gobe kije ki sami baba ki Masa magana kan meze hana na maye ɗakin yaya ta, kinga wancan karon shi ya Abdu yace a bar zancen tukunna amma yanzu ai yaci ace a tada maganar, shekara takwas za'a shiga ta tara da muke, kar mu tsaya garin kallon ruwa kwaɗo yayi mana ƙafa". "Bari haka za'a yi, shi Abdallahn zan fara kira nan nayi masa kuka ta yarda baze Musa min ba kinga da kan sa ma se ya kai zancen naku can wajen baban nasa ta yadda ba wanda ze zargi ni nake son tusa ƙi ko". "Sosai ma kuwa Anna, wannan idea ɗin tayi, bari in je in kwanta Allah ya kaimu goben da rai da lafiya". Da Ameen Anna ta amsa mata yayinda ta shige ɗakin kwanan ta dake part ɗin marigayiya yayar ta nafisa da suka gaje tun bayan mutuwar ta. A can kuwa baiwar Allah salma ta tasa ƴaƴan ta a gaba tana kallon yadda suke bacci hankali kwance ba abinda ke damun sa yayinda ita take cikin damuwa, damuwar da bata san dalilin ta ba wadda haka kawai take samun faɗuwar gaba duk ta tuno boss ɗin ta da auren da yake batun zasu yi, aure kuma kwana kusa in less than two weeks abinda bata taɓa shiryawa ba balle ta zauna tsara yadda ze kasance. Alwala ta ɗaura ta shimfiɗa sallaya ta shiga nafiloli tana kaiwa Allah kukan ta kan ya shige mata gaba, seda ta gaji kafin ta zauna ta ɗau ƙur'ani ta shiga karatu har seda ta ji bacci yaci ƙarfin ta kafin ta rufe tayi addu'a ta kwanta. Safiyar Laraba yazo wa mutane da dama cikin wani irin yanayi, ga salma wani irin nauyi take ji a ƙirjin ta da kanta kamar wadda ta aza dutsen dala a kanta, yaran kansu da ƙyar ta iya shirya su dan har se da suka makara yau, jiki ba ƙwari ta rakasu ajin su ta koma ta tare wani napep ɗin zuwa wajen aikin ta. Ko da taje ta tabbatar boss ya rigata zuwa amma yau bata ji wannan fargabar ba illa wani nauyi da ta tuno sunan sa da abinda ke ƙoƙarin shiga tsakanin su. Seda ta ajiye jakar ta da files ɗin hannun ta ta gyara wanda zata kai masa Sannan ta ƙwanƙwasa ƙofar, amsa mata da akayi tareda bata izinin shiga ya sa ta buɗe ƙofar ta shiga ta ƙara sa gaban table ɗin sa ta ajiye masa files ɗin duk da bata gan shi a kan kujerar sa ba, juya tayi da zummar fita amma ya dakatar da ita daga cikin inner office ɗin sa kan ta zauna ta jira shi, zama tayi ta shiga bin office ɗin da kallo a hankali cikin admiration, office ɗin ya daɗe yana birge ta ba tun ba yau ba yadda ba'a cika masa shirgi da hauragiya ba amma komai a tsare fes wajen da ya kamata. Cikin haka ta sauke duban ta kan ƙofar inner office ɗin dake buɗe ko kafin ta kai ga ɗauke idon ta tuni ya bayyana cikin shadda riga da wando ɗinkin tazarce sedai maɓallayen wuyan a buɗe suke yana gyara su, haɗa idon da suka yi yasa ta maza ta sauke nata gaban ta na faɗuwa, iya zaman ta a Companyn zata iya rantsewa yau ne ƙwayar idon su ta shiga cikin na juna dan indai tana gaban sa kanta ya kan kasance a ƙasa ne har se sanda ta bar wajen sa shiyasa ba zata iya cewa ga cikakkiyar ainahin kamannin sa ba dan kwarjinin sa kaɗai kan hana mutum iya kallon sa fuska da fuska. Idon sa a kanta ya shiga takawa har ya ƙarasa ya ja kujerar opposite ɗin ta ya zauna tare da ɗaukar wayar sa ya shiga kiran Haisam "Kasan tafiyar da zamu yi da tsawo amma kabar mutane na jira?". Yana gama saurarar abinda yace ta can ɓangaren ya kashe wayar tare da ajiyewa ya shiga gyara agogon hannun sa, files ɗin ta jawo ta shiga yi masa bayani cikin mamakin yau kam be da niyyar zama kan kujerar sa sedai tuni ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu se kuwa taja bakin ta ta tsuke. Ƙwanƙwasa ƙofa masinjan sa yayi ya bashi izinin shigowa, leda ya ajiye masa cike da girmamawa sannan ya juya ya fita, ledar ya jawo ya buɗe tare da kallon kayan ciki sannan ya tura mata gaban ta "Ki shiga ciki ki canja wannan uniform ɗin dan ba zan iya tafiya dake dasu a jikin ki ba". Binsa tayi da kallo har ya fice kafin ta sauke ajiyar zuciya, ta canja kaya to akan me, ina ruwan sa da kayan jikin ta ko basu ne suka bata a matsayin kayan aikin ta ba da yau ze kawo mata wani sabon sanaben ta canja. Haka dole ba dan taso ba ta ɗau ledar tare da shiga toilet ɗin sa ta cire kayan jikin ta ta maida wannan, doguwar riga ce ta mata se mayafin ta, kayan coffee and milk se suka yi mata kyau sosai dan tana da hasken ta daidai gwargwado. Cikin ledar ta fito tana ninke uniform ɗin ta zuba su ta sake neman kujerar da ta tashi ta zauna "Mrs Gamji bismilla ko". Haisam ya faɗa daga ƙofa bayan ya buɗe, da rashin fahimta take kallon sa jin sunan da ya kiraye ta dashi yau "Muje salma, inda zamu ba nan kusa bane". Jiki ba laka ta miƙe ta bi bayan shi dan har ya fita, Allah ya sani bata san zuwa ko ina da su tunda ba muharraman ta bane haka ba wani cikakken sani tayi musu ba banda na wajen aiki yanzu kuwa mutum abin tsoro ne bare ma ita da bata da galihu ba wanda ze tdaya mata in wani abu ya same ta. Gaban mota Haisam ya buɗe mata, cikin ɗarɗar ta shiga tana me karanto addu'a a bakin ta, wani irin sanyi ne ya ratsa fatar jikin ta na Ac dake tashi yayinda hancin ta ya shaƙo mata daddaɗan ƙamshin turaren motar da na jikin sa da suka gaurayu suka bada wani launi na ƙamshi daban. Rufe murfin Haisam yayi ya koma ya buɗe bayan motar ya shiga, tada motar Abu Aulad yayi suka fita daga Companyn yayinda ma'aikata ke aikin kallon su sedai shi kam ko mutum ɗaya be nuna yasan da zaman shi ba balle ya kalle shi. "Garin ku fa zamu je Madam". Da sauri ta shiga ta kalli Haisam da yayi maganar kafin ta juyo ta kalli Abu Aulad da idanun sa ke bisa titi, bakin ta na ɗan rawa ta furta "Taraba, suna school, ba wanda ze je ɗaukan su". "Ba ze yiwu muje mu dawo kafin su tashi ba?". Da sauri ta girgiza kanta, " ƙarfe huɗu suke tashi". "Ze yiwu muje har mu dawo". Da sauri ta shiga girgiza kanta "A'a nidai mu tsaya a ɗauke su, ba zan iya tafiya in bar su ba, pleaaseeee". Ta faɗa wannan karon directing to Abu Aulad "Ya sunan Makarantar?". "Star light Academy". Be Kuma cewa komai ba ya saki hanyar da yake kai ya ɗauki wadda zata kai shi makarantar da ta faɗa. Har ciki ya shigar da motar sannan ta fita zuwa wajen principal, uzuri ta bayar kan dalilin da yasa za'a ɗauki yaran, be Musa ba ya yarje mata dan yaran ta are one of their daily and punctual students da basa fashi sake da ƙwaƙƙwaran dalili. Rungume su tayi a tare lokacin da suka fito daga aji kafin ta ja hannun su zuwa wajen motar suna ta yi mata surutu. Tun da suka tunkaro su ya kafe yaran da ido cike da sha'awa da muradi, sha'awar dama nasa ne, muradun samun kamar su ya cike ransa. Buɗe musu bayan motar tayi suka shiga a hankali sannan ta sa musu lunch box ɗin su, gaishe da Haisam suka yi inda suka kira shi da uncle batare da sun lura da Abu Aulad ba se da ta nuna musu shi "Babies, baku gaisar da other uncle ba". "Yes, baku gaishe da daddy ba". Haisam ya gyara mata da sauri "Mamman wai daddy ne da gaske?". Gyaɗa musu Kai tayi a sanyaye dan bata so yace daddy ba, in suka girma suka san ba daddyn su ne ba fa. Da sauri Ifty da tafi ƙiriniya dan itace Ussaina ta tsallake ta shiga gaba tare da faɗawa kan shi tana tsallen kiran Daddy "Daddy dama mamma tace Mana kayi tafiya ne, daddy yanzu ka dawo kenan?". Da murmushi a fuskar sa ya gyaɗa mata kai tare da shafa fuskar ta cike da shauƙi, juyawa yayi ga ibtisam da tayi tsaye ya ruƙo ta itama ya zaunar kan sa, wasa wasa seda suka ɓata kusan 30 minutes sannan suka tafi bayan yaran sun koma baya kusa da Haisam ita kuma ta koma mazaunin ta.....................✍🏻. ©️ Ouummey 📚✍🏻. ☑️Ote, Comment and share fisabilillah. [12/13, 10:35 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 10 [ 12/1/2022 1:07 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      FREE PAGE 010 LAST FREE PAGE!!! This is the last free page, make your payment and continue enjoying the movies else you'll be left behind 😜! ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card to 09013101854, note VTU is not acceptable. ________________________📖 Shiru na ƴan wasu sakanni kafin ya motsa bakin sa "Na so ki tare yau sedai baze yiwu ba tunda munyi dare but be ready gobe da safe insha Allah zan zo mu wuce". Tsrewa, yau, gobe da safe, wucewa, gaba ɗaya bata gane ma'anar wannan kalaman ba. It may sound funny ko kuma a ɗauka rainin hankali ne but dagaske a wannan lokacin manta ma'anar su tayi, sam bata gane me yake nufi ba haka yasa tayi saurin yin magana "Wucewa, gobe, zuwa ina?". Seda ya kalle ta sosai kafin ya kau da kai trying not to look at her face again, tun lokacin da ya ga ƙwayar idon ta a ƙauyen su yaji yana sha'awar sake gani, so yake ya tantance wane kala ne da eyeballs ɗin ta tunda ya tabbatar ba baƙa bace sedai baya san ta ɗau hakan da wata manufa shiyasa yake kauda Kai "Nace ki tattara abubuwan da kuke buƙata na iya suttura zaki koma gidan auren ki gobe insha Allah". Zuwa yanzu kam she's speechless dan ba zata ce bata gane me kuma yake nufi ba yanzu tunda gwari gwari yayi mata, ita kam ta rasa a wane layi zata ajiye wannan auren nata, da neman auren da ɗaurawa duk cikin kwana ɗaya zuwa biyu aka yi su, yanzu kuna ga tariya, a al'adar malam bahaushe dangin amarya kan haɗu su rakata gidan auren ta cikin soyayya da ƙauna amma ita gata ana batun tariyar daga ita se mijin ta da ƴaƴan ta, lallai auren ta wani iko ne na Ubangiji. A hankali ta saci kallon sa cikin son furta abinda take so sedai bata san ya akayi ta tsinci harshen ta da furta abinda ba shi ne a zuciyar ta ba "Allah yasa zamu ga goben da rai da lafiya". Ameen ya faɗa daga nan kuma suka cigaba da zaman shiru, ita bata ce komai ba shi ma haka, tsayin lokaci har ta gaji da zaman ta gyara amma bashi da niyyar cewa komai "Ki taso yaran mu tafi". "Mu tafi, ina kenan bayan dare kuma yayi, its almost ten fa". "And me kike nufi da zaman da kike yi a nan?". Wani irin tuƙuƙin takaici ne ya cika mata maƙogaro, daga ɗazu zuwa yanzu ta fahimci mutumin nan wani bahago ne na daban, ko saboda ba wani kusanci ne tsakanin su na daban ba a office maybe shiyasa bata San hakan ba tuntuni. Bata ce komai ba ta fita daga motar tare da maida murfin ta rufe masa ta wucewar ta cikin gida tana gunguni ita kaɗai. Seda ya ga shigar ta gidan sannan ya tashi motar ya fita daga layin cike da sanyin jikin da gajiya ta haifar masa, wannan dogon tuƙin da yayi jiya da yau sam be saba masa ba shiyasa gaba ɗaya jikin sa yayi masa nauyi. Kulle motar yayi ya fita batare da ya kula ganin ta da yayi tsaye ba, da sauri tabi bayan sa har tana haɗawa da gudu saboda takunsa irin na cikakkun maza ne masu isasshiyar lafiya "Yaya Abdu, ya Abdu". Yana jin ya tsaf amma yayi mata banza hakan yasa ta kuma kwasa da gudu tasha gaban sa lamarin da ya tilasta masa tsayuwar dole sedai tuni ya sake ɗin ke fuska tsaf kamar wanda be taɓa sanin wani abu wai shi annurin dariya ko murmushi ba a duniya. "Dama Anna ce ke neman ka, tuntuni nake kiran wayar ka in faɗa maka yaƙi shiga, gashi ita kuma se kuka take da kiran sunan yaya nafi wuni guda yau taƙi cin komai". "Kije ki faɗawa baba". "Zuwa yanzu ya kwanta yaya Abdu, Please ka taimaka kazo muje kayi mata magana ko zata ji, na bata baki amma taki saurara ta". Sam baya son kallon ta sabida irin shigar dake jikin ta, duk da kasancewar dare ne amma gidan nasu tarwai yake da haske da ko allura ce ta faɗi tsaf mutum ze tsugunna ya ɗau abar sa ya tashi. Tun ba yau ba yasan ita da yayar ta nafisa Allah ya ji ƙan rai kamar gabas da yamma ne, sam bata inda suka yi kamanceceniya se ko ta fuska da kuma jini shiyasa ko da sam be sake mata fuska balle ta samu damar kawo masa raini bare kuma yanzu da yake jin kowa ma daidai yake dashi. "Kije zan zo in nayi wanka, nayi gumi da yawa I can't go to her a haka". Ya faɗa yana wuce ta cikin tafiyar nan tasa me cike da karfi da isa, bin bayan sa tayi da kallo cike da maɗaukakin shauƙi, lumshe ido tayi tare da rungume hannuwan a ƙirji inda take ji kamar shine ta rungume, wannan maganar da ya mata ji take kamar an mata albishir da shiga aljanna. Tun yayar ta na da rai take so da ƙaunar yaya Abdu sedai tayi ta ƙoƙarin dannewa, yanzu kuwa da babu yayar ta bata tunanin akwai abinda ze tsayar da ita kuma. A saɗaɗe ta juya zuwa part ɗin su, bakin ƙofa ta tarar da anna tsaye, da sauri ta riƙo hannun ta suka ƙara sa ciki kafin ta dube ta "Yaya, cewa yai baze zo ba?". "Yace zezo amma se yayi wanka, dawowar sa kenan baze iya zuwa gare ki a haka ba". "Kai masha Allah bari maza in shafa rob ɗin nan a ido na ɗan suyi ja su dinga hawaye, insha Allah buƙatar mu zata biya bari ki gani". Tsohuwa Anna ta faɗa tana murza Rob a fuskar ta, duk yadda idanun ta ke hawaye be sa ta fasa ba se da ta saka sosai ta yadda in ka kalle ta zaka ce ta daɗe tana kuka dan yadda fuskar ta tayi jajir kasancewar ta fara haka ma idanun ta suka yi ja suka tasa. A can ɓangaren Hajiya Babba kuwa da sauri shuraiha dake tsaye jikin window riƙe da curtains tana kallon abinda ke faruwa tsakanin Abu Aulad da Nuriyya ta saki uban ashariya "Kan uba". Ta faɗa da sauri tana sakin curtains ɗin, bata tsaya wata wata ba ta zura bedroom slippers ɗin ta tayi waje without minding cewa kayan bacci ne a jikin ta ba, burin ta a lokacin shine ta kai gare su taji me suke tattaunawa a wannan tsohon daren. Baza tayi sanyar da wata can daban zata ƙwace mata Abdallah ba bayan an gama kwaɗaita mata shi tare da lasa mata zuma a baki yanzu kuma a ce za'a janye, ina ba zata yarda ba. Sedai kash ko kafin ta kai ga fita daga part ɗin su tuni ya shige nasa part ɗin ita kuma Nuriyya ta koma nasu hakan yasa ko da ta fito compound ɗin bata tadda kowa ba se ma'aikata dake ɗan kai kawo dan wasun su ma tuni sun nemi makwanci. Haka ta koma part ɗin nasu tana cizon yatsa, taso taji me waccan karuwar ke faɗa masa wanda har ya tsaya saurara haka sedai kash bata samu ji ba, ya zama dole ta tunzura Hajiya Babba ayi ayi ai bikin su ko hankalin ta ya kwanta, daga lokacin da ta sami wannan damar a lokacin ita kanta Hajiya babbar zata raina kanta dan kallon ta kawai take itama da tata tsarin da buƙatar akan Abdallah ɗin. A hankali yake rage kayan jikin sa cike da gajiya, wanka yake buƙata yake kusan sanyi dan yadda yake jin jikin sa na ƙaiƙayi shine kawai abinda se yi yaji sauƙi. Singlet ɗin jikin sa yake ƙoƙarin cirewa se kuma ya fasa sanadin hango inuwa da yayi jikin labulen sa alamun akwai wani laɓe a ta wajen. Cikin nutsuwa ya shiga takawa har ya kai wajen yasa hannu ya yaye curtains ɗin da suka rufe tagar, tsaye take cikin shaiɗanun kayan da dasu da babu a jikin ta basu da wani banbanci, suna haɗa ido ta sake masa wani arnen murmushi cike da barikanci kafin cikin kwarkwasa ta shiga lauya jikin ta tana magana da wata seducive voice "Sannu da zuwa Abu Aulad, ga dukkan alamu ka gaji, don't mind I can takeaway all your stresses, yanzu dai muje kayi wanka ko super man?". Kamarw anda garwashin wuta ya taɓa haka yayi watsi da hannun da takai jikin sa, ya rabbal alameen be san ya zai yi da rayuwar sa a cikin wannan gidan da a wajen sa gara kabari dashi ba. Wani irin birkitaccen mafi ya watsa mata da yasa ta yin katantanwa ta faɗi can gefe kanta ya bugu da jikin Centre table ɗin dake falon, cikin wata irin zuciya da ta ciwo shi ya bita yasa ƙafa ta taka sangalalin hannun ta har se da yayi ƙarar dake shaida alamar in har bata sami fracture ba to tabbas ƙashin nan ya fita daga bigiren sa. Wani wahalallen ihu ta saki da be wani fita da karfi ba saboda tsabar wahala yasa a take Muryar ta ya shaƙe, cikin wani dakusasshen Muryar da ɓacin rai ya haifar masa ya shiga yi mata concrete warning "This is the first and last time da zan kuma ganin ki a part ɗina, na rantse da Ubangijin da ya busa min rai da second time na kuma ganin ki zan iya ɗaukar ranki dan ko banza an rage mugun iri, annoba kuma jinin shaiɗan, before the count of three ki fice min ɗaga ɗaki in ba haka ba wallahi rataye kibzan yi jikin fanka, fitsararriyar fasiƙa kawai mara kunya da tsoron Allah". Ai ko kafin ya gama bayanin sa tuni ta tarkata hannun ta tayi waje da mugun sauri dan a yadda ta gan shi da kuma rashin imanin da ya gwada mata ta tabbatar ze iya rataye tan kamar yadda ya faɗa. Da numfarfashi da komai takai kanta part ɗin ta zube kan kujera tana maida numfashi, wani irin zufa ne ke keto mata na wahala da azabar da take sha a jikin ta, bata taɓa sanin haka zafin karaya yake ba se yau. Ƙwalla take zubar wa tana bin hannun da kallo yayinda cikin ranta take shan mugayen alwashi kala kala a kan shi, tun da ta riga ta ɗora ido a kan shi takuma kwaɗaitu da shi ta rantse ita kuma se ta same shi, in kuwa ba haka ba to tabbas sedai ayi biyu babu uku ba ko ɗaya ma'ana indai ba zata same shi b ato sedai kowace mace ta rasa. Da sauri ta runtse idon ta lokacin da ta auno shi a idanun ta tare da wata mace, inaaa, ba'a haifi macen da zata amfane shi ba, ada dai tayi wannan imanin amma a yanzu zata iya yin komai in tace komai tana nufin komai wajen ganin ta saka kyakkyawar barrier tsakanin sa da duk wata ƴa mace kowace ita kuwa. Ranar haka ta kwanan cikin azaba da raɗaɗin zuci da na jiki, ga dai jinya ya kwantar da ita kuma wai batare da ya bari ta amfanu da komai daga gare shi ba, ita da ta samu abinda taje nema to da sauki ba karya ta ba ko kashe ta yayi ba zata damu ba tunda ta cika burin ta. A ɓangaren Abu Aulad ma haka ya kwana a zaune cikin wani irin yanayin da baze fassaru ba, be san da wane suna ze Kira gidan da yake ciki ba haka be san da wane suna ze kirayi mutanen cikin sa ba, be taɓa sanin bawa kan zaɓi mutuwa kan rayuwar sa ba se a kan shi, da ace kisan kai ba haram bane a musulunci da tuni ya daɗe da sheƙe kan sa ya huta. Tun tasowar sa be san wani abu wai shi farin ciki ba, kullum cikin baƙin ciki da damuwa yake tun fara wayo sa har kawo yanzu da yake shekarun sa na cikakken namiji mai ji da sabon jini da ƙuruciya. Rayuwar sa a hagunce ta faro kuma har kawo yanzu a haka take, be san se yaushe ne ze samu daidaito na rai, ruhi da rayuwa ba balle har ya samu salama, a duk sanda yaga mutane na rayuwa suna dariya da nishaɗi ya kan tsinci kansa da ayyana dama shine, so da yawa yasha kusan yin saɓo in ya zauna tunani dan ya kan dinga aiyana me yayi wa Allah da yasa ƙaddarar jarabawar tazo a haka, me yasa ba wata daban ba. Kiran sallar asuba da ake yi ne yasa shi miƙewa yana dafe kan sa dake sara masa ya shiga toilet, daga tsayen da yake ya sakarwa kansa ruwa masu sanyi sanye da wandon shaddar da singlet ɗin batare da ya cire ba, tsayin lokaci Sannan ya gabatar da wanka ya ɗaura alwala ya fito. Jallabiya ya zura a jikin sa tare da ɗaukar tasbah ɗin sa ya wuce masallaci, seda aka idar da sallah har gari yayi haske kafin ya taho gida. Jiri yake gani dan rabon shi da abinci tun na safen jiya kafin su tafi ƙauye ga kuma rashin bacci sedai kasancewar tsayayyen namiji ba wanda ze fahimci hakan se wanda yayi masa sani na sosai. Wata jallabiyar ya canja kawai ya ɗau key ɗin motar sa zuwa gidan su, ɗauko ta ze yi dan se yayi hakan hankalin sa ne kwnata, mutanen gidan su are so cunning, gwara tun kafin su farga yayi outsmarting ɗin su ya shayar dasu mamaki ya kuma basu tsoro ba kuma ta kowace hanya ba se ta kawo macen da ya nema wa kan sa auren ta cikin gidan. Ya sani in da mace a tare dashi abubuwa da yawa zasu masa sauƙi sedai matsalar shine shin itama irin su ce, wane assurance yake dashi na ba zata zama kamar su ba, shin in aka mata tayi da zunzurutun kudi ko matsayi zata karɓa ko kuwa?!. Wannan sune tarin abubuwan da tuntuni suke hana shi aure sedai a yanzu da yayi ba wai ze saki jiki da ita bane, hasalima auren su na da wa'adin da ya ɗibar masa wanda yana cika ze sauta, zaman sa shi kaɗai ya fiye masa dan be yarda da kowa ba baya kuma jin ze yarda ɗin. Yaro ya samu ya aika gidan, tana cikin sawa Ifty rigar school ta jiyo Muryar yaron na faɗin aiken da aka turo shi "Wai salma ta fito inji Abdallah". Sedai rigar ta kubce ta faɗi daga hannun ta saboda yadda zuciyar ta ta doka da jin sunan sa, hannun ta na rawa ta sake ɗaukar rigar ta shiga kici kicin sa mata sedai ta kasa saboda ruɗewar da tayi, Hajiya ce ta amsawa yaron da gata nan fitowa saboda jiya ta zauna tayi mata bayanin komai dan kamar mahaifiyar haka ta ɗauki Hajiya saboda ba ƙaramin taimako tayi mata ba a rayuwar ta. Ɗakin Hajiya ta shigo ta karɓi shirya Ifty dan tuni ta gana da Ibty "Je ki bashi uzuri daga nan ki nemo yara su fara fitar miki da jakunkunan, in an kwana biyu insha Allah zan zo in ga mazaunin ki, tashi kije". Jiki ba laka ta fita, zaune cikin motar ta same shi ƙafar sa duka biyu a waje ya lumshe idanun sa tare da jingina kan sa da makarin kujerar, seda ta tattaro duk dauriyar dake gare ta kafin ta iya gaida shi "Barkada safiya". Saukar Muryar ta yasa ya buɗe idon sa, kallo ɗaya yayi mata ya kau da kai tare da maida ƙafafun sa cikin motar ya fara ƙoƙarin kunna ta "Kayi haƙuri Ban ƙara sa shirya Ifty ba amma yanzun nan zamu ƙarasa, Bari in Sami yaro ya fitar min da jakunkunan". Fasa kunna motar yayi ya koma ya kwanta kamar ɗazu ita kuma ta matsa ta sami wani almajiri suka koma ciki tare, ko da ta shiga tuni Hajiya ta gama shirya Ifty tare da haɗa musu launch box ɗin su, manyan jakunkunan kayan su dake shaƙe ta fara jawowa tana fitarwa tsakar gida almajirin na fita dasu har suka gama, kallon ɗakin take cike da matsanancin kewar sa da zata yi kafin kuma ta maida kallon ta kan Hajiya, matar da tayi mata halaccin da har abada ba zata manta ba, a rayuwa da ita da bana Husaila sun mata abinda in har ta manta to ita ɗin butulu ce cikakiya. Nasiha sosai Hajiya ta yi mata da har tasa ta kuka ba dan komai ba se dan kewar mahaifiyar ta da kakarta da ta taso mata, ta sani da suna nan su zasu yi mata wannan nasihar. Haka Hajiya ta rakata har mota, ko da suka je tuni ya zuba jakunkunan a booth ɗin motar sa ita kawai yake jira. Duk yadda yake moody be san lokacin da ya saki fuska ba da Ifty ta ƙarasa tana ɗane shi Ibty kuma na gaida shi, haka ya ɗauke su duk biyu ya riƙe yana kallon su cike da shauƙi yana sauraren shirmensu har Hajiya ta gama mata nasihar da zata yi suka idasa bakin motar, har ƙasa ya tsugunna ya gaida Hajiya abinda yayi salma matuƙar daɗi a rai. Hala suka ɗau hanya zuwa gidan da bata sani ba tana cike da kewar rabuwa da Hajiya da ragowar ƴan uwan zaman hayar ta da basu san da maganar auren ba ma se yau da safe amma duk da haka suka bita da fatan alkhairi. Har bakin ƙofar party ɗin mahaifin sa ya kai motar sannan ya fita ya zagaya ya buɗe mata itama ta fito a ɗarare sannan ya buɗe wa su Ibty baya suka fito, hannu yasa ya ɗau Ifty yayinda ya riƙewa Ibty hannu ya nufi falon mahaifin nasa ta rufa masa baya itama. Gana ɗaya mutanen ɗakin suka zuba musu ido zuciyoyin marasa gaskiya na dukan uku uku, masu gaskiya kuma na musu kallon rashin fahimta. "Barka da safiya baba, ga salma matata da ƴaƴan ta kuma nawa". A zabure mutane shida dake falon suka miƙe tsaye kowanne da kalar tambayar da yake jefowa "What?, Me?, Kutumar uba?, Mata?, How comes?, Haba da Allah!. Wannan sune ruwan tambayoyin da suka dinga yawo a falon cikin ihun muryoyi daban daban yayinda Abu Aulad ya saki hannun Ibty ya saka hannun ya jawo salma cikin jikin sa ya rungume.........................✍🏻. Tooooooooh jama'a, gamu a ƙarshen free page da izinin Ubangiji, ko yaya paid pages zasu kasance?!. Shin wacece Abu Aulad ya karyawa hannu jiya da dare?! Wacece shuraiha?, Wai ma tsaya ita kanta Hajiya babbar wacece, meye alaƙarta da Abu Aulad?! Jarumi, jarumi!, Shin kun Tuna shi?! Wanne shi?. Nuriyya ƙanwar nafisa ƴa a wajen Anna, ko meye ƙudurin ta kan Abu Aulad?!. Yace be yarda da kowa ba se kan shi kaɗai, what about Haisam?!. Haisam, Haisam, anya shima babu wani ƙulli kuwa a under sunan nan?!. "Wai ma ku tsaya, wace irin rayuwa ce Abu Aulad ya taso a cikin ta, meye tarihin wannan gidan, wane irin bahagon rayuwa ake yi a cikin sa. Duk ma ba wannan ba, yaya rayuwar auren Abu Aulad da salma zata kasance, me kuke hangowa, gashi dai auren ya ƙayyade masa wa'adi, shin kuna ganin ze sake ta?!. Ni abinda bangane ba shine shi kan sa Abu Aulad ɗin waye shi, ina mahaifiyar sa, anya baba mahaifin sa ne kuwa, to in ba mahaifin sa bane waye mahaifin nasa?!. Shin ina labarin dangin mahaifiyar Salma, zata haɗu da dangin mamanta ko kuwa?, Baba Husaila da mama Hadiza principal, shin shikenan an rabu ko kuwa akwai wata rawa da zasu taka a rayuwar salma nan gaba?! Duk amsoshin wannan tambayoyin na cikin paid pages, sister kar ki yadda ayi tafiyar nan bake domin na tausaya miki rashin da zaki yi dan littafin ze tabbatar da sunan sa akan ki wato ANJANE (RASHIN SANI) dan da kin san irin nisa da ƙarkon da tafiyar zata yi da ba zaki yadda a yi ta bake ba,!. Ga duk me buƙatar yin payment ɗin sa ne bi ta wannan procedure ɗin, ₦300 to the below account details Rabiatu Abdullahi 2391368231 ZENITH BANK, screenshot and send the evidence of payment to 09013101854 or MTN recharge card o 09013101854, note VTU is not acceptable. ☑️Ote, Comment, share and patronize fisabilillah. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 011 [ 12/3/2022 3:45 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                     Paid page 011 _________________________📖 Kallo na sosai dattijon ya bi fuskar Abu Aulad dashi na tsawon lokaci kafin ya maida kan fuskar salma da har lokacin take cikin jikin Abu Aulad ɗin sai dai kanta na ƙasa ne haka kuma jikin ta na ɗan rawa da ba kowa ke ganin haka ba se shi da take jikin sa. "Ban fahimci zancen ka ba Abdallah". Duk da murmushi be kasance daya daga cikin abinda yake halayyar sa ba amma se da ya ya ƙoƙarta wanzar dashi a fuskar sa a lokacin, tafiya ya fara yi da ita a jikin nasa har zuwa kan three sitter dake falon ya zaunar da ita shima ya zauna gefen ta tare da ɗora Ibty da Ifty kan cinyar sa, a nutse yasa dogon hannun sa ya ratsa jikin salma ya manna ta da jikin sa sannan ya fuskanci mahaifin sa cikin danne nauyi da yar kunyar abinda yake aikatawa sedai hakan ya zama dole in har yana bukatar fahimtar murdaddiyar  rayuwar sa "Sunan ta salma kamar yadda na faɗa maka baba, jiya aka ɗaura mana aure da ita bayan soyayyar da muka jima muna yi, wannan yaran nata ne dan ta taɓa aure a baya, itace dai wadda mukayi magana a kanta shekaranjiya wadda muke tare a newspaper dinnan". Ya ƙarashe bayanin da ya kai da kyar tare da sake matsar salma da har lokacin kanta ke ƙasa, wani irin rawa na sosai jikin ta ya ɗauka jin bada sanin mahaifan sa ya aure ta ba haka kuma ga a yanayin da yake musu bayani wanda ita sam bata ga dacewar abinda yake yi ɗin ba. "Sam ba zata yiwu ba, wallahi ba zata saɓu ba wai bindiga a ruwa, wannan auren karya ne, kai koma gaske ne wallahi se an kunce shi". Hajiya Babba ke faɗin haka cikin fadan tashin hankalin da take ciki, wannan wani irin rainin hankali ne yaron nan ya zo musu dashi, yana nufin yayi aure bayan yasan ta riga tayi masa mata har ma gata a gidan, aikuwa sedai ayi wacce za'a yi dan ba ta yarda da wannan auren ba, ba ta kuma karɓe shi ba dan haka se an warware shi, wai imma da gaske ne kenan. Hayaniyar yadda kowa ke reacting kan auren na Abu Aulad yasa baba tsawatar musu, dole suka yi shiru ba dan sun so ba sedai suna jiran suji me zai ce kan wannan tatsuniyar. "Ina raye, da rai na da lafiya ta amma kayi aure ban sani ba Abdallah, kana son nuna min ban isa da kai bane ko me, ko da yake haka ne dan ka nunawa duniya ta hanyar take magana ta ka aura wadda na nuna ban aminta ba". Sam kalaman mahaifin nasa basu yi masa daɗi ba amma haka ya danne zuciyar sa ransa na sake zafafa da wariyar launin Fatar da mahaifin nasu ke nuna wa tsakanin su kamar shi da sauran yan uwan sa ba abu ɗaya bane. "Kayi haƙuri baba, ban auri salma dan baka isa dani ba se dan soyayyar da nake mata da kuma abin da ya faru dan kar a sanadin kuskure na mutuncin ta dana ƴaƴan ta ya tabu". Hajiya Babba ce tayi tsumut tasa baki cikin maganar bakin ta har yana karkarwa "Aikuwa sedai ka sake ta dan wannan auren sam ba mai yiwuwa bane dan tuni nayi maka mata matsayi na na uwa a gare ka, tuntuni kuma kasan da maganar dan har mahaifan ta sun sani dan haka yanzu base anjima ba ka saki wannan abar me suffar yan ruwa, yo banda ma rashin tunani irin naka me za kayi da bazawara me yaya biyu bayan ga budurwa yarinya danya me jini a jika". "To kaji hukuncin mahaifiyar ka wanda Nima ina bayan ta dan ban taɓa ganin bahagon aure irin wannan ba, ba wakilan ango ba komai a ɗaura aure kamar dai dangin nata sun gaji da ita ko kuwa ta ishe su". Sosai zuwa yanzu yake jin ya kai gejin da baze saurara wa kowa ba ciki har da mahaifin nasa da baida wata ra'ayi ko magana ta karan kan sa se abinda wannan munafukar tsohuwar ta faɗa "Ka gafarce ni baba dan ban da ra'ayin auren kowa se salma, ya kuma kamata Ku amshi nawa ra'ayin wannan karon dan wancan na farko ku kukai min zabi na kuma yi muku biyayya, sedai a yanzu bana jin zan iya rayuwa da wata mace da ba wannan ba, maganar mahaifiya kuwa na dade da sanin ban da ita balle har ta zaba min mata ban sani ba ko kafin ta rasu ne tayi hakan"!. Da wani irin hanzari Hajiya Babba ta ɗago cikin firfito da idanu waje na mamakin kalaman Abu Aulad, shi kan sa baba seda ya Sha jinin jikin sa da words din balle kuma ƴaƴan Hajiyar da suka zaburo tamkar masu shirin kai duka "Maza ka kiyaye bakin ka kan mahaifiyar mu dan ba zan dauki rainin ka a kanta ba, ba tun yanzu na fahimci hayaƙi kanka yake ba sedai akan Hajiya wallahi zan gyara maka zama ƙaramin mara kunya kawai". Wannan karon kam dariya yayi har se da fararen jerarrun hakwaran sa masu tsananin haske suka bayyana tare da sauke su Ibty daga jikin sa ya yunƙura daga kwantar da bayan sa da yayi jikin kujera tare da duban fuskar yar sa ɗaya tal wato sumayya da tayi maganar "Bisimilla uwar Saudah, in har kin fasa gyara min zama ke ba sumayya Abdulsalam Gamji bace, maza ƙaraso ina jiran ki". "Bana son neman fitina sumayya, magana ta ƙare tun da ka kafe kana son matarka se ka kaita wajen da zata zauna ko, kuma ka saurare ni da kyau dan, zan yi bincike na a kanta, duk na samu wani abu na assha a tattare da ita tabbas zaka sau ta dan ba zan yarda ka bata min zuri'a ba haka kuma a ko da yaushe hukuncin take magana ya ka iya riskar ka". Be damu da kalmar bincike da Baban ya ambata ba balle kalmar hukunci, ya riga ya saba da wannan dan har gwara wannan karon hukuncin akan laifin da ya aikata ne ba sharri ba. Hannun sa ya miƙa ya ruƙo na Salman bayan ya miƙe ya miƙar da ita itama kana ya sake ta tare da sunkuya wa ya sabi Ifty ya riƙe hannun Ibty sannan ya nuna mata hanya alamun tayi gaba, cikin hanzari ta nemi wucewa sedai fimcikar da aka yiwa mayafin jikin ta yasa ta dakata tare da saurin riƙe mayafin dan kar ya fita daga jikin ta. Kakkausan kallon gargadi ya shiga wurgawa sumayya yayinda hannun da tai yunƙurin marin Salman ke riƙe cikin nasa yayi masa riƙon tsauri, azabar zafin da take ji kan rikon ya kasa ɓuya kan fuskar sumayya "Ko da wasa, wallahi ko a mafarki kar ki sake attemptimg kai hannun ki jikin matata dan ban san me zan iya aikata miki ba sedai komai zai iya faruwa ciki kuwa har da zage ƙwanji dan kare martabar ta". Ya ƙarasa yana wulli da hannun nata da tayi saurin rikowa da dayan tana yarfewa, be damu da zagin da Hajiya Babba ta shiga surfa masa ba ya juya ga baba da yake nan zaune a gurin amma ake wannan iya shegen "Ban cire kowa ba ban da kai baba, Babba komin girman sa da kuma yaro komin kankantar sa yayi yunƙurin taɓa min mata to fa se inda ƙarfi na ya kare dan a kanta zan iya aikata komai, in nace komai ina nufin komai kuwa". Be saurari me baba ze ce ba ko ya kula maganganun Hajiya Babba yaja hannun yaran yayi waje dasu dan ita salma tuni ta tsufa da ficewa, tun lokacin da ya tare hannun sumayya daga sauka kan fatar fuskar ta. Batare da ya kalli inda take ba yayi gaba riƙe da hannun yaran hakan yasa ta rufa masa baya jiki a sanyaye har zuwa part din sa. Madaidaicin falon ne da ya ɗauke set na kujeru, kitchen da dining set bedroom biyu se ɗan siririn ventilation. A tsakar falon ya sake hannun twins ya nuna mata dakin without giving her a glance "Here's your room, ga can kitchen Wanda ke dauke da store, zuwa anjima zan kawo kayan girki". Kai ta gyada tare da yin godiya kana ta ja hannun babies din ta zuwa dakin, kallo ta shiga ƙare masa kusurwa kusurwa cikin yabawa da tsarin wajen, makeken bed ne lafiyayye da ke shimfiɗe da zanin gado me kyau, dressing mirror se ƙatuwar walk in wardrobe me ƙofofin glass, ƙatuwar foam a tsaye se ko ƙofar toilet dake can gefe. Ajiyar zuciya ta saki a hankali ta shiga takawa cikin sanyin jiki, kan mirror ta ajiye handbag din ta tare da neman bakin bed ta zauna twins na zama kusa da ita. Mintuna kaɗan ya shigo da jakunkunan kayan su ya ajiye tare da ficewa. Kamar wadda aka tunawa da wani abu ta miƙe da sauri ta hau cire kayan ta tare da sauya wa da uniform ɗin wajen aiki, da sauri da sauri takarasa ɗiban komai da take buƙata kafin ta ja hannun yan biyu suka fita falo. Baya nan dan haka ta shiga tunanin yadda ya kamata tayi, ta fita be sani ba ko kuwa ta zauna, makarantar su Ibty fa bayan ko jiya kamar basu je bane?, Amma kuma ya zata yi da sashen tunda ba zata bar shi a buɗe ba? Cikin fatan tadda mukulli ta ƙarasa tana duba jikin ƙofar, cikin Sa'a kuwa yana jiki be cire ba, da hanzari ta kira su Ibty suka fita tayi locking ƙofar tare da jefa keys din jaka suka nufi hanyar gate gaban ta na ɗan faduwa na tsoron haduwa da wani ɗan gidan. Ƙaƙƙarfan numfashi ta sauke lokacin da suka bayyana gaban gate ɗin ba tare da ta haɗu da kowa ba, napep ta tsare musu kamar yadda suka saba. Seda ta tabbatar da shigar yaran aji kafin a juya da ita zuwa ma'aikata. A hankali take takawa har ta ƙaraso gaban gate ɗin kana ta zare baƙar doguwar rigar jikin ta ta saka a haka yayinda security suka shiga aikin su, seda suka tabbata da bata dauke da komai na cutarwa sannan aka bar ta ta shige. "Congratulations Salma, you now Mrs Gamji". "Congratulations Salma, Allah ya sanya alkhairi". "Happy married life colleague". Ire iren wannan kalaman ta ringa receiving daga yan uwan ta ma'aikata na taya murna, ita dai bata cewa komai se murmushi da thanks yayinda cikin ranta ke cike da mamakin wa ya sanar musu sedai bata da me bata amsa. Table ɗin ta tasa tissue ta goge kafin ta zauna ta fara ƙoƙarin kunna laptop ɗin ta dan fara ayyukan ta, hankali kwance take operating din ta tana haɗa schedules da kuma gyara wasu appointments ɗin, tana gamawa ta shiga duba wasu files da ke ajiye suna jiran ta, tana tsaka da aikin Haisam ya ƙaraso wajen, file ne se shiga ya ɗauka a outer office ɗin CEO dan Yana da damar shiga iya wannan ko da shi CEO ɗin baya nan. Cikin mamaki yake kallon ta da tunanin me take yi kuma a nan ita da ta tare a gidan miji yau yau ɗin nan "Salma, me kike yi a office Kuma ke da kike amarya". Ajiye takardar hannun ta tayi ta ɗago ta shiga gaida shi mutunce kamar yadda ta saba a baya, amsawa yayi yana sake maimaita mata tambayar sa "Ehm aiki nazo". Ta faɗa tana nanata kalmar amarya a zuciyar ta tana jin ta banbarakwai jin ita ake dangantawa da ita. "Shi yace ki zo aikin?, Yana ina lokacin da kika fito?". Ɗan tsai tayi kafin ta girgiza kanta "Ba shi bane, baya nan na fito, na kai su Ibty school ne shine na taho nan". "Sam be kamata ki fito yau ba salma, ɗazu ɗazu fa kika tare a gidan ki, wannan ai se kisa a kuma buga ku a jarida ku sai shiga bakin duniya, dan Allah tattare komai ki ajiye ki tashi ki koma gida hakanan". Bata ji dadin ta koma gidan da yace ba dan ita kam tsoron mutanen gidan take ji ganin a tashin farko da ganin ta basu karɓe ta ba se ma rigima da fitina da ta tashi, bayan haka kuma ga zaman kadaici, a Ifty se 4pm zasu taso makaranta dole se ita kaɗai zata wuni a gidan. Bata iya jayayya da na gaba da ita ba shiyasa se kawai ta miƙe ta hau tattara komai kamar yadda yace tana ajiyewa inda ya kamata, sassanyan ƙamshin sa me sa nutsuwa da kwantar da hankali ne ya ratso wajen yana shaida musu isowar sa kafin kuma cikakken takun sa ya sake bayyana shi ɗin. Juyawa Haisam yayi yana kallon shi yayin da ita kam ta cigaba da abin da take yi tana sake kai kanta ƙasa. Musabaha suka yi da Haisam sannan ya wuce office ɗin sa Haisam na rufa masa baya. Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta gama haɗa komai se kuma ta ɗauka ipad ɗin da take kai masa schedules ta fara takawa zuwa office din. Knocking biyu Haisam ya amsa mata ta shiga a hankali bakin ta ɗauke da sallama, gefe dashi ta dan rusuna ta gaida shi kamar yadda ta saba kana ta aje masa ipad ɗin a gaban sa ta shiga yi masa bayani, seda ta kammala kafin ya ja wayar gaban sa yana sake duba komai, da hannu yayi mata alamar komai yayi dan haka ta juya zata fita "Be kamata ta zauna a office ba bayan jiyan nan tayi aure yau kuma ta tare dan haka nace ta koma gida". Tsayawa da duba takardun gaban sa yayi batare da ya ɗago ba kafin cikin Muryar sa ne amo ya bawa Haisam ɗin amsa "Shi kuma aikin waye ze to mata, kar ta sake take ko ina se lokacin tashi". Iya nan ta tsaya ta saurara so tana jin abinda yace ta fice tare da komawa wajen zaman ta ta fara daidaita kayan aikin ta, seda ya tabbatar ta rufe kofar kafin ya kalle shi cikin jin haushi "Kai dai wallahi baka iya abin arziƙi ba, fisabilillah wane irin aiki zata zauna tayi ita dake matsayin amarya, a ƙa'ida kamata yayi tana gidan ta tana hutawa kai kuma kana mata hidima, duk wannan be samu ba kuma se ka kasa barin ta a gida se ta zo wani aiki?, Mtsww". Be ce masa komai ba se da ya gama duba takardar hannun sa ya ajiye sannan ya daga kansa tare da wurga amsa banzan kallo.................. ✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 012 [ 12/5/2022 10:24 AM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                         Paid page 012 _________________________📖 "sedai kallon amma a buge dai bazan bugu ba, ayi bawa da shegen baƙin hali". Haisam ya faɗa yana hararar Abu Aulad sbd mugun kallon da yayi masa, banza Abu Aulad ɗin yayi masa ya cigaba da aikin sa dan yasan in ya biye wa Haisam ba zasu tsinana wani abun arziki ba  yau ɗin bayan ayyuka ne zokar ke jiran su. Kwana ukun da suka yi basu zauna ba sosai ayyuka suka taran musu barin ma da ya kasance dashi da Haisam ɗin gaba ɗaya ke ciki busy ba wai mutum ɗaya ba. Ganin fa dagaske ba kula shi zeyi ba yasa Haisam ficewa daga office din Yana maganganu ƙasa ƙasa na haushin Abu Aulad na hana salma komawa gida ga kuma baƙin halin sa na Shariya da yayi masa duk da inda sabo yaci ace ya saba. Hankali kwance take ayyukan ta kamar koyaushe dan ita kam taji daɗin zaman ta anan, Allah ya sani cikin ranta fargaba ne da tsoro na irin zaman da zata yi da mutan gidan da ƙaddara ta jefa ta rayuwa cikin su. Ba wai kanta kaɗai ba, hatta ƴaƴanta tana da fargaba akan su, su ɗin sune mahimman ginshiki kuma katangun rayuwar ta da bata jin zata iya standing wani abu ya same su komai kankantar sa kuwa. Ji take yi akan su tana iya komai ko da kuwa za'a kashe ta ne, tana iya bada rayuwar ta domin tasu dan a gare ta rayuwa babu su gwara ace itama babu ita. Kiran Sallar zuhur dake tashi cikin daddaɗar Muryar ladanin madaidaicin Masallacin dake cikin Company ɗin yasa ta dakatar da aikin da take yi cikin system ta danna mata sleep. A nutse kamar yadda ya zame mata jiki ta nufi masallacin dan a can take alwala ta gabatar da sallar ta sannan ta dawo. Gaisawa ta shiga yi da duk ma'aikaciyar da suka haɗu cikin kiyaye mutuncin kai da kuma mutunta jama'a, wasu dama ta sani ba dan Allah suka ringa gaisawa da ita ba a yau dan da yawa basa ko yi mata magana saboda ganin yadda ta samu kusanci me girma da boss din su, muƙamin ta na secretary ɗin sa ba ƙaramin bata musu rai yake yi ba hadi da assasa hassada da ƙyashin ta a ran su dan da yawa wannan matsayin suke nema ido rufe sedai basu samu ba. Scarf din ta da ta cire dan shafar kai ta ke kokarin daurawa shafi bisa tilas ta dakata dan jin wasu maganganu da tayi "Aikin banza da wofi, meye abin wani daga kai da wani budawa kan auren da mun san duk yadda akayi kutunkutun har aka yi shi, auren da ba'a gina shi kan gaskiya ba". "Ke Laila, kiji tsoron Allah fa, waye ya faɗa miki ba'a yi shi kan gaskiya ba". Matashiyar da aka kira da Laila ta yamutsa fuska kafin cikin yanayin da yake nuna tabbacin abinda take faɗa ta shiga bawa dayar amsa "An faɗa miki kowa ma irin ki ne da baya wani zurfafa tunani yake yadda da komai da ya gani haka kawai, nifa ba irin tsarin mu ɗaya ba Umah, ke wai ko abinda ya faru yau be isa nuna miki cewa auren ba shi da wata manufa ba, haka kuma akwai wata makarkashiya a cikin sa ba?". Dan ƙifta idanu Umah wadda asalin sunan ta umahmatu ne tayi "Ni banga komai ba haka banyi sensing komai ba, in Zaki faɗa min kawai ki faɗa". "Amma wallahi kin ban mamaki, ban ɗauka rashin tunanin naki ya kai can ba, ke yanzu kin taɓa ganin inda amaryar jiya jiya tarewar ɗazu ɗazu ta fita aiki?, Amaryar da ya kamata ace tana can gidan ta cikin farin ciki yayinda mijinta ze kasance kusa da ita suna shan soyayya, se ga amarya ta buge da zuwa office, haka shima angon har wa yau kuma fuskar sa a haɗe cif ba alamar yana farin ciki karewa ma se sabon kunci da yake yi". Shiru Umah tayi kafin kuma ta gyada kai a sanyaye "Kuma fa hakane Laila, amma kuma me yasa ya aure ta in har baya son ta, ni wallahi har ta bani tausayi dan maza irin su boss wuyar sha'ani gare su, ita kuma gata da kirki, ba ruwan ta wallahi, nikam ta dade tana burge ni".                        "Kirkin munafukai ba, ke irin su fa wallahi da zaki tona cikin su se kinyi mamaki, Ni bama wannan ba, a wajena da auren su da babu duk ɗaya ne kuma yanzu ne ma na ɗaura sabuwar ɗamarar so da ƙaunar boss". "Amma wallahi kin daura aure da wahala kuma in bakiyi hankali ba tsaf kin kusa barin aikin nan, gwara kiyi haƙuri ƙi sawa kanki salama dan ke kanki kin san yafi ƙarfin ki". Yamutsa fuska Laila tayi cikin jin haushin kalaman Umah "Banda rainin hankalin ki a ina kika taɓa ganin namiji yafi ƙarfin mace, aiki kuma da kike magana an gaya miki Ni mahaukaciya ce da zan tare su in ce ina son sa balle har ya kore ni, ki zuba ido kiyi kallon yadda zan buga wasa na kuma ya tafi cikin tsari, so kuma na maimaita miki yanzu na fara haka in kika ga ban aure boss ba to mutuwa nayi". Tana gama faɗa tayi gaba cikin jin haushin wai ita Umah zata cewa tayi haƙuri ta cire boss a ranta ya fi karfin ta, aikuwa zata bata mamaki. Itama Umahn fita tayi daga wajen dan dama wanke fuska ta shigo yi ba sallah zata yi ba. Jiki a matuƙar sanyaye salma ta daura scarf din ta tare da maida hijab din ta wuce cikin masallaci, kauda komai tayi daga ranta ta gabatar da sallar ta cikin nutsuwa yayinda cikin kowace sujud take kaiwa Allah kukan ta. Bata san ta ina zata fara da wannan yakin da yake tunkaro ta ba, ita ɗin me rauni ce, bata da gatan kowa bayan Allah da Manzon sa, rayuwar ta ba irin ta kowa bace haka salon labarin ta yasha bambam da na kowa, ita kwallin ƙwal ce cikin filin yakin yayinda mahara suka yi mata zobe gabas da yamma, kudu da arewa suka sata a tsakiya. Ta ina zata fara ne?, Da waye ya kamata ta fara?, Dashi mijin da ya aure ta dan kare mutuncin ta kamar yadda ya faɗa ko kuwa da salon pretending din sa na nuna yana son ta gaban jama'a kamar yadda taga yayi a dazun, a'a ko kuwa da mutanen gidan da zata fara sabuwar rayuwa dasu wanda alamu suka nuna in har baya jajirce ta kwaci kanta ba tabbas zata sha bakar wahala, a'a ko kuwa rayuwar ta da ta ƴaƴanta zata fuskanta, bata damu da irin su Laila ba dan bata da damuwa da su, ba so da kauna ba ko haɗiye shi zata yi bata da matsala da hakan. Ta daɗe da idar da sallar sedai bata tashi ba seda ta ji bata da sauran basirar yin addu'a sannan ta shafa, sake gyara zama tayi ta shiga tunani wanda ya ɗauke ta lokaci me ɗan tsawo kafin ta farga ta mike ta fita. Deliveryn da ta saba siyan abincin restaurant din su tuni ya kawo mata abinci ya ajiye kan table ɗin ta ganin be gan ta ba, sanin ta riga da ta biya kuɗin yasa ya ajiye mata ya tafi. A hankali ta ringa tsakurar abinci wanda bata wani ci da yawa ba saboda damuwa da ta cushe mata ciki, haka dole ta tattara ta ture shi gefe ta cigaba da aiki. Ƙarfe huɗu daidai ta tashi aiki, office din sa ta shiga ta ajiye masa file ɗin da ya sata aiki a kan shi tare da yi masa sallama ta fice, seda tayi signing out sannan ta fita. Doguwar rigar ta ta maida jikin ta sannan ta shiga neman napep, sosai yau ta sha wahala kafin ta samu hakan yasa koda taje makarantar twins kusan kowa ya watse saura yan kaɗan da ba akai ga ɗauka ba. Da gudu suka rungume ta kamar yadda suka saba itama ta sake ƙanƙame su kafin ta ja hannun su suka nufi gate tana musu tambayoyi kan karatun su. Yanzu kam basu sha wahala ba suka samu napep, tun da suka ɗau hanyar gidan gaban ta ya shiga dokawa saboda firgici da tsoro sedai bata bari yanayin ta ya nuna hakan ba har suka sauka bakin gate. Kuɗin sa ta bashi tare da ɗaukar basket ɗin yaran ta saka su gaba karasa gaban gate ɗin, a hankali ta shiga ƙwanƙwasawa cikin ɗari ɗari, seda maigadin ya leka ya ga itace kafin ya buɗe musu su shiga. Tun da ta saka ƙafarta cikin compound tasa addu'ar ta bata amsa ba dan shuraiha da wata mata da ta samu zaune kan fararen kujeru suna magana, kallo ɗaya tayi musu ta ɗauke kan ta batare da ta sake ba, cikin nutsuwar ta suka nufi part din su batare da ta musu magana ba dan nuna wa tayi sam bata lura akwai mutane a ta wajen ba. Ba wai rashin girmama manya bane, abinda duk ze hada ta da yan gidan ne bata so dan ta fahimci she's not welcomed a cikin su, bare kuma a kallon farko da tayi wa su shuraiha suka yi mata ta ankare da kallon banzan da suke yi musu. Ajiyar zuciya ta sauke lokacin da suka shiga falon ta maida ƙofar ta rufe, bedroom ta wuce dasu ta musu wanka tare da canja musu kaya zuwa simple gowns na zaman gida da shan iska sannan itama tayi nata. Kamar su itama gown me saukin nauyi ta zura ta saka hijab suka gabatar da sallar Asr tare da ƴaƴan ta. Bata tsaya yin wasu dogayen addu'a kamar ɗazu ba saboda aikin da zata yi, cartoon din two letter words ta kunnawa twins yayinda ta fice dan fara aikin ta. Da falo ta fara, duk da ba wani datti ne dashi ba seda ta gyara shi ta share tare da canja fasalin zaman kujerun ta saka turaren wuta me matuƙar ƙamshi irin wanda suka dinga haɗawa suna saidawa dan da wannan sana'ar tayi sponsoring karatun ta. Ɗan tsam tayi cikin tunanin ta shiga bedroom din sa ta gyara ne ko kuwa, 'ki tsaya iya matsayin ki salma, ke bawai kamar kowace mace bace a wajen mijin ta dan haka kar ki zarme balle har ki kai kan ki inda Allah ne kai ki ba'. Cikin yarda da batun da zuciyar ta tayi mata ta wuce kitchen inda ta iske kayan abinci kamar zasu yi magana a cikin store yayinda ragowar kayan haɗin ke ajiye a tsakiyar kitchen din cikin manya manyan ledoji. Ba bata lokaci ta shiga fitar dasu tana ajiye komai a wajen da ya dace, kayan miya da su nama da kifi duk ta haɗa su cikin deep freezer dake kitchen din, seda ta gama adana komai cikin inda ya dace sannan ta koma kan refreshments ta zuzzuba su ya cika manyan fridges biyu dake kitchen dan ba ƙarya kitchen din babba ne dan in bata yi karya ba zata iya cewa ya kai ko ya kusa girman falon. Jin kiran sallah yasa ta shiga ƙoƙarin sama musu abinci mara nauyi a maimakon da alkubus ɗin da tayi niyyar yi. Jallof sphagetti tayi da ta Wadata da veggies da fresh prawns, ba tun yau ba take sha'awar yin ire iren waɗan nan girke girken ba sedai dake bata da abun yi dole ta haƙura sedai so da yawa ita take yiwa Hajiya abinci in suna aikin hadin turare hakan yasa ta kware sosai kamar dama shi ta sa bayi kullum. Cikin plates masu kyau ta zuba musu ita da twins shi kuma cikin wani kyakkyawan warmer me kyau ta Kai dining ta ajiye masa tare da frutta juice. Seda ta Kai musu abincin daki sannan ta sake alwala suka gabatar da magrib, ba ƙaramin daɗi abincin yayi mata ba dan dama yunwa take ji kamar tayi yaya, da safe bata samu ta karya ba yazo tafiya dasu, da rana kuwa damuwa bata barta ta ci yadda ya kamata ba ga kuma aiki da ta dawo tasha duk ya gajiyar da ita yunwar ta karu shiyasa yanzu ta zage ta cika cikin ta. Suna gamawa ta maida plate din ta dawo suka shiga bitar karatun da akayi wa su twins, wannan sabo ne da tayi musu tun da suka fara zuwa school, kullum da daddare se sun maimaita karatun da akayi musu biyu boko da Arabia inda take kara fahimtar dasu da kuma yi masu gyara inda ya kamata. Hadith ta Kara musu guda daya dan sun iya na shekaranjiya da tayi musu, wannan special care da take bawa karatun su yasa suke cikin most talented students na ajin su dan duk wuyar karatu nan da nan suke daukewa, to dama an koya musu ana kuma kan kara koya musu dole ya zo musu da sauki. Kiran sallar Isha ne yasa suka rufe littafin suka tashi, suna idar da sallah taja su falo ta kunna musu National geography Abu Dhabi saboda Ifty da ta dame ta wai a kunna musu lion. Sosai itama program din ya burge ta yadda ake haska dabbobin daji kala kala ana kuma highlighting yanayin rayuwar su da abubuwan da suke ci matsayin abinci, gaba ɗaya hankalin ta ta maida kan Tvn dan wasu dabbobin bata ma taɓa sanin akwai su ba se gashi yau ta gan su a Tv. Yadda hankalin su yayi nisa ne yasa basu ji buɗe ƙofar da aka yi ba balle shigowar sa, ƙamshin sa da ya shige hancin salma ne ya tilasta mata rufe ido tana shaƙar shi sosai kafin kuma a ɗan razane ta maza ta buɗe idon tana rarraba su cikin son ganin inda mamallakin ƙamshin yake. Kan bayan sa ta sauke idanun ta daidai lokacin da yake dab da isa kofar dakin sa batare da ya kalli ko twins ba balle ita, a ɗan daburce ta gyara zama tare da ɗaukar remote tana rage volume din Tvn sannan ta miƙe tsaye tare da sunkuyar da kai tana faɗin "Sannu da zuwa"...........................✍🏻 Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 013 [ 12/6/2022 11:51 AM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                       Paid page 013 _________________________📖Ba tare da ya kalle ta ba ya amsa tare da shigewa ɗakin ya maida ƙofa ya rufe. Kau da kanta tayi lokacin da ya rufe ƙofa tana mamakin ko wane irin mutum ne shi kuma oho. Yanzu kenan da bata lura da shigowar sa ba haka ze shige bece musu komai ba, lallai Allah me halitta. Kashe Tvn tayi tana hannun su Ibty suka shige ɗaki dan bata san ranar su ta farko ya zama na sun takurawa me gidan, kaya ta canja musu zuwa na bacci ta canja nata itama, fitila ta kashe musu tare da lulluɓe su da spread kasancewar ana ɗan sanyi kaɗan. Ta daɗe bata amu bacci ba yayin da tayi nisa cikin duniyar tunani, ba na komai ba se na makomar rayuwar ta da ta ƴaƴan ta, zuwa yanzu tuni tayi yaki da zuciyar ta ta nemo dakiya ta sawa ranta haka kuma ta fatattaki tsoron da ke ranta akan mutanen gidan. Ta sawa ranta yin rayuwa da su a duk yadda suka zo mata, zata tsaya ta fahimci kowa ne sannan ta tafiyar dashi ta yadda ya biyo. Se kusan karfe ɗaya da rabi kafin ɓarawo bacci ya salallabo ya sace ta kamar yadda shi ba ruwan sa da damuwa ko tashin hankali, farin ciki ko wani abu makamancin haka, a kowane yanayi mutum ya kasance to fa bacci ya ƙware a iya sata. Adaidai wannan lokacin Abu Aulad na kan praymat a dakin sa yana kai kukan sa wajen me kowa me komai me duka, kwata kwata ran sa a bace yake, ba kuma dan komai ba se wata sabuwar tatsuniya da baba ya karanta masa ɗazu, be taɓa jin yana matsanancin kewar mahaifiyar sa ba se yau, ya sani in da tana raye se tayi iyakacin kokarin ta wajen ganin rayuwar sa bata kasance a bigiren da take ba a yanzu. Duk da yanayin da rayuwar sa ke ciki abu ne rubutacce cikin littafin kaddarar sa da ba makawa se ya faru amma fa tabbas akwai son zuciya da kuma rashin tsoron Allah. Baze iya cewa ga tsawon lokacin da ya kwashe be yi kuka ba sedai ya tabbatar daga lokacin mutuwar Ummu be kuma kuka irin wanda yayi ba yau, wani irin rauni zuciyar sa tayi lokacin da yake gaban mahaliccin sa, raunin da zece be taɓa jin irin sa ba a rayuwar sa, a yanzu ba shi da kowa se Allah da Manzonsa, mutum ɗaya ce iya nuna wa da kwarin gwiwa cewa nasa ne sedai a yanzu shima ɗin ya zama ba nasa ba, ya zama nasu Hajiya Babba kaɗai da ƴaƴan su. Baba Ada tsayayyen miji ne a gidan sa haka kuma jajirtaccen uba ne ga yayan sa sedai a yanzu dashi da babu kusan babu bambanci, matan abinda suke so shi suke yi yayinda uwargidan sa Hajiya Babba take abinda taga dama, take shimfida iko da mulkin ta iya iyawa ta kuma ba wanda ya isa ya daga kai ya kalle ta yace dan me se mutum biyu. Na farko shine se kuma amaryar da baba ya aura wadda bata ko rufa shekara biyu ba a gidan, cikakkiyar yar duniya ce dan zaman kanta take yi har zuwa lokacin da baba ya aure ta. A hotel ta fara ganin baba acan kasar Dubai yaje harkokin sa na kasuwanci ita kuma ta raka wani Alhajin ta, tunda ta sauke ido akan baba shikenan ta Nace masa tun bare da taji wanene shi da irin dukiyar da ya mallaka. Ba irin bibiyar da bata yiwa baba ba kan ya amince mata suyi rayuwa irin wadda take yi sedai firr yaki, kasancewar yana son ta yasa ya bullo da maganar suyi aure, ganin fa zata iya rasa shi in ta cigaba da dagewa yasa kawai ga hakura akayi auren. Gawurtacciyar mara kunya ce number ɗaya dan ko a cikin karuwan ma ita ɗin ta daban ce, ba ƙaramin wahalar ta Hajiya Babba ta sha ba kafin kuma tayi yunkuri, yunƙurin da har yau ban da ita ba wanda yasa yadda akayi sedai kawai gani akayi baba ya koma kamar wani kani ko yaron ta dan se abinda tace yake aikatawa. Ajiyar zuciya ya sauke tare da sa hannu ya shafe hawayen da suke kuncin sa ya mike ya nufi hanyar fita daga ɗakin saboda jin kiran Sallah da yayi, wai har asuba tayi ba tare da ya lura ba , ko da yake a yadda yayi nisa cikin tunani dole baze gane sauri ko nawar agogo ba. Kamar ya wuce se kuma ya ga rashin dacewar hakan dan haka ya ƙarasa bakin kofar dakin su ya shiga knocking. Bata da nauyin bacci shiyasa a bugu na biyu ta tashi, hannu ta miƙa ta kunna fitilar dakin tare da dan yi gyaran murya ta tambayi waye, shiru bata ji ance komai ba dan haka ta bude kofar dakin a hankali ta leka, wayam taga ni ba kowa dan haka da sauri kuma a tsorace ta maida ƙofar ta rufe. Cike da mamakin wa ya buga mata ƙofa ta daga kai ta kalli agogon ɗakin, ganin time ɗin subhi yayi yasa take ranta ya bata shine ya buga wato ya tashe ta sallah kenan. Toilet ta shiga tayi alwala ta fito ta yi raka'a tanul fajr sannan tayi asubar, a takaice tayi azkhar da addu'o'in da ta saba sannan ta miƙe ta fita zuwa kitchen. Breakfast ta fara haɗa musu tana yi tana duba wall clock din dake kitchen din, karfe shida da rabi ta kammala komai ta dauka ta kai kan table sedai ganin abincin da ta aje masa akan table ba'a taba komai ba se jikin ta yayi sanyi. Ajiye na hannun ta tayi ta ɗau warmer din ta Kai kitchen, tunani ta shiga yi na yadda zata yi da abincin dan da ta san be ci ba da shi zata musu warning suci da safen sedai ta riga ta gama komai. Wani dan bowl ta ɗauka me ɗan girma ta juye abinci a ciki tayi warning ɗin shi sannan ta ajiye da niyyar in zasu fita ta dauka ta ba gare man ya bawa almajiri in ya gani dan ba ta san zubar da abinci alhalin ba lalacewa yayi ba, hakan ya zama almubazaranci. Yanzu ma a daki suka karya ita da yan biyu yayinda ta ajiye masa nasa a dining, suna gamawa ta musu wanka tare da shirya su cikin uniform din su dake matuƙar daukar kyakkyawar fatar su wadda ta kasance fara ce sosai dan sun fi salma haske duk da itama ba baka bace. Da suari ta yi wanka ta shiga shiryawa itama ganin lokaci har ya tafi dan It's seven ten am, yau brown abaya ta ɗora kan kayan ta sannan ta sa farin hijab din ta da da kadan ya sauka daga kafaɗar ta. A falo ta tadda shi kwance kan doguwar kujera sanye da milk ɗin jallabiya da tayi masa matukar kyau, cikin ɗan mamaki ta kalle shi sannan ta kau da kai, to ko dai yau baze je officer bane, amma kuma yadda yasan shi workaholic indai ba dole ba baya taɓa fashin office. Da gudu Ifty ta fincike hannun ta daga na salma tayi wajen sa tare da faɗawa kan sa, a hankali ya buɗe idon sa ya sauke akan ta lokacin da take kai masa kiss goshin sa tare da gaishe shi "Good morning Daddy". "Morning pretty". Ya faɗa yana miƙewa zaune ɗauke da ita a jikin shi, itama Ibty janye hannun ta tayi ta tafi wajen sa tare da zama kan side din cinyar ta Ifty na zaune a dayan. "Good morning Dad". "Morning beauty". "School zamu je Daddy, momma tace yau zata kunna mana tiger in muka yi karatu da yawa ko Ibty?". Ifty ta faɗa tana kallon Ibty, gyada mata kai tayi kasancewar ita ba me yawan magana bace "Kun kusa makara fa babies, maza ake school ayi karatu kunji, ai kuna san kallon tiger din ko?". Da sauri suka gyada masa kan su Ifty na sakin murmushi "Yauwa to maza aje, Allah ya kiyaye hanya". Peck suka yi masa daya bayan daya a goshi kafin suka sauka a jikin sa suka koma wajen salma da take kallon su kamar ta sace saboda yadda suka burge ta, ba wanda ze kalle su a haka yace ba yayan sa bane, ba wai dan kama ba, a'a yanayin mu'amalar su. Sosai taji daɗin hakan da yayi ganin yadda suke walwala da fari ciki suka bayyana kan fuskar su. Sunkuyar da kanta tayi kafin ta shiga takowa zuwa hanyar fita, seda ta kai tsakiyar ɗakin daidai saitin kujerar da yake zaune jingine da bayan kujera idon sa a lumshe sannan ta durƙusa "Ina kwana". "Lafiya". Ya faɗa bayan yaja lokaci kamar baze amsa ba, miƙewa tayi tana satar kallon sa ganin yadda kibiyoyi kansa suka tattashi, a hankali ta juya ta fita dan twins tuni suka fice. Da sauri ta ƙarasa fita dan tunanin kar wani yayi wa ƴaƴan sa wani abu, ajiyar zuciya ta sauke da ta gan su bakin part din, karasa fita suka yi ta bawa gateman bowl din hannun ta. Suna tsaye aka buɗe gate wata mota ja me kyau ta fito, kau da kanta tayi dan bata san ko haɗa ido da yan gidan balle akai ga magana, gaban ta motar ta tsaya hakan yasa ta ja hannun babies din ta zasu wuce. "Megida ne yace akai ku inda zakuje Hajiya". Dakatawa tayi ta juyo ta kalle shi, maigida, wani maigidan kenan?!. "Yallabai Abu Aulad nake nufi". Jin haka yasa ta buɗe gidan gaba ta sa twins ita Kuma ta shiga baya. Cikin ranta kuwa sosai taji daɗi dan a yadda suka tsaya gaisawa dashi in napep zasu jira dole se sun makara, amma yanzu kalli yadda nan da nan har sun kusa isa makarantar. A parking lot yayi parking ta fita tare da kama hannun su ta rakasu har class sannan ta koma suka fita zuwa Company. A bakin gate tace ya sauke ta base ya shiga ba, ganin zata wuce yasa yayi saurin tsayar da ita "Ƙarfe nawa zan dawo Hajiya?". Ɗan jim tayi cikin jin abin wani bako, ita ake tambaya karfe nawa za'a dawo daukar ta lallai rayuwa. "Ƙarfe huɗu". Amsa mata yayi yaja motar ita kuma ta juya zuwa ciki. Karkaɗe seat ɗin tayi duk da an gyara gurin sannan ta zauna, cikin kwanciyar hankali ta shiga gabatar da ayyukan gaban ta, har ƙarfe sha biyu babu boss ba alamun sa gashi kuma suna da meeting da wasu clients in less than 30 minutes. Tuni ta gama haɗa duk abinda zasu buƙata wajen meeting din ta zauna baza ido, Haisam da ta hango yasa ta ɗan sauke numfashi. "Baze samu shigowa ba salma, tashi maza mu hada abinda ya kamata dan saura ten mins lokaci yayi". Daukar takardun tayi Haisam ya taya ta da wasu suka nufi office din sa, tsara komai suka shiga yi wanda cikin ikon Allah nan da nan suka gama. Ko a cikin hall ɗin meeting din haƙuri Haisam ya bayar kan rashin zuwan Abu Aulad ɗin, bakin basu wani ja ba saboda sun san shi jajirtacce ne dan haka suna san ba ƙaramin abu bane ya hana su zuwa so se suka amsa uzurin da aka basu. Cikin walwala da farin ciki suka sallami bakin dan an samu nasara a zaman, kwangila ce suka basu na gina estate me ɗauke da gida dari uku wanda ba ƙaramin samu za'a yi ba a aikin, basu bar wajen ba seda akayi signing akan komai suka kuma transfer rabin kuɗin aikin. Office din Haisam suka wuce riƙe da tulin papers din da akayi presenting da kuma na negotiation din, kan table ɗin sa ta ajiye masa "Bari in koma office sir". "Zauna salma". Haisam ya bukata yana cigaba da gyara takardun da suka shigo dasu wajen ware kowane zuwa inda ya kamata. Ɗan jim tayi kamar ba zata zauna ɗin ba sedai tunanin ko akan contract din yake son su tattauna ko wani aikin ze Bata yasa ta ja kujera ta zauna. Be katse aikin da yake yi ba har sead ya gama komai sannan ya zauna bayan ya ciro ruwa a fridge. Seda ya Sha ya ishe shi sannan ya ajiye a gaban sa ya ciro wani ya aje mata a gaban ta. "Thank you". Tace masa ba tare data ɗauka tasha ba dan ita buƙatar ta ɗaya ce yasan da ita dalilin zaman da ya bukaci tayi. Ɗagowa yayi ya kalle ta kafin cikin sanyin murya ya furta yayi magana "Bashi da lafiya". Itama ɗagowa tayi tana yi masa kallon rashin fahimta, bashi da lafiya?, Waye bashi da lafiyar?. "Abdallah bashi da lafiya salma, yana kwance a gida dan seda na Kai doctor ya duba shi". Wannan karon kam ta fahimci bayanin sa dan haka ta sunkuyar da kai cikin ranta tana tunani yaushe yake rashin lafiyar, dan ita dai har ta fito yana zaune a falo kuma bata ga wani alamun dake nuni da rashin lafiya ba a tattare dashi, to ita da ma kallo biyu kawai tayi masa duk yau, ta ina zata sani. "Kansa ke tsananin ciwo ga kuma ciwon kirji Wanda ulcer ce ta haddasa masa shi, likita yace yana zama da yunwa shiyasa ulcer ta kama shi sosai". "Allah ya bashi lafiya". Abinda ta iya furtawa kenan tana wasa da yatsun hannun ta "Seda aka yi masa ƙarin ruwa leda biyu tare da allurar bacci dan rashin hutu da damuwa ne suka haddasa masa ciwon kan, likitan yace a dena barin shi da yunwa haka kuma ya rage sa damuwa a ran shi da kuma yawan tunani". Sosai take sauraran maganganun nasa sedai cikin ranta mamakin dalilin faɗa mata da yake yi tayi dan bata san ma'anar hakan ba. "Na faɗa miki ne dan ke ya kamata ki sani ki kuma kiyaye dukkan abinda likita yace dan a yanzu ke keda hakkin hakan". "Amma sir ko da nayi abinci jiya na ajiye masa be ko taɓa ba balle yaci, yau ɗin ma da kyar in ya ci breakfast din da na aje masa, to me zan yi masa nikam?". "Nasan baze ci ba salma, a sanin da nayi wa Abdallah indai ta tashi ne to baze taɓa cin abincin da zaki dafa ba". Ɗagowa tayi ta kalle shi sosai wannan karon "Amma saboda me sir?". "Call me Haisam". Sunkuyar da kai tayi alamun bazata iya ba hakan yasa ya ɗan yi dariya "Okay you can call Yaya Haisam dan tuni kika zama ƙanwata". Gyada kai tayi kafin ta ɗan gyara zama cikin son jin dalilin daze sa Abu Aulad baze ci abincin ta ba........................ ✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 014 [ 12/6/2022 3:06 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                        Paid page 014 _________________________📖 "Jiya jiya kika shigo rayuwar sa shiyasa baze ci abinda duk zaki dafa ba dan be gama sanin ki ba har yanzu". Haisam ya fadi hakan ba wai dan haka yayi niyyar faɗa ba se dan tunanin da yayi yasa kawai ya fadi hakan. Numfashi ta dan ja kafin ta daga kai alamun ta fahimta "Ke da kanki ya kamata ki sa yaci abincin dan in ba kiyi hakan ba ze ta zama da yunwa ne yana shan juice da cin biscuit dan be iya yawon restaurant ba haka ba komai ma yake ci ba". "Amma taya zan sa yaci ɗin bayan a iya jiya zuwa yau na fahimci shi din wani irin mutum ne da ba'a gane ina ya dosa". "In kika dafa ba ajiye masa ya kamata kiyi ba, se ki kaima ki kuma sashi a gaba har se yaci kin gani". Zaro ido tayi jin abinda yake faɗa, kamar irin be san halin mutumin da yake tura ta gare shi ba, bayan ko shi da yake ɗan uwan sa ba wani sake mata yake ba balle kuma ita. "Na sani zaki ji wani iri amma dole hakan za'a yi, kinga a mutanen gidan su sam ne yarda da kowa ba balle yaci abinda zasu dafa, haka baze yarda in dinga taho masa da abinci ba balle kuma yaje gidan mu yaci, kinga dai a karshe dole kece last hope din, daurewa zakiyi ki kauda duk wani daridari, nauyi da kuma tsoron sa da kike ji kin ji". "Bari inje masallaci gashi can ana kiran sallar biyu". Ya faɗa yana miƙewa da sauri kasancewar yau ɗin juma'a, itama tashi tayi ta fita tana nanata maganar da ya faɗa a ranta. Aunowa kawai take yi gata ta sashi a gaba da abinci amma kallon banzan da jefa mata yasa jikin ta daukar rawa kamar an watsa mata ruwan sanyi a cikin tsakiyar hunturu. "Kai haba dai, Bama zan iya ba nikam". Ta faɗa a fili tana kaiwa zaune kan kujerar office din ta. Ban da ma dai ya Haisam da neman magana ya zaice ta wani sa shi a gaba yaci abinci se kace wani karamin yaro, to kar ya ci ɗin mana, ba cikin sa bane da har wani shi kuma ze ce wai be yarda da yan gidan su ba, ji wani fa rainin wayo, to in be yarda dasu ba da waye ze yarda. Ba ma wannan ba be yarda da yan uwan sa ba se ita ce ze yarda da har za'a ce ta bashi abinci salon a ja mata yace wani abu ta saka masa a abincin da take so dole se yaci. Cikin wannan tunanin ta tashi tayi sallah jin an idar a masallatai. Ajiye wannan batun tayi a gefe ta shiga ayyukan gaban ta musamman yau da ayyukan suka yi mata yawa dan akwai presentation da za tayi wanda a ƙa'ida shi ya kamata yayi akan tunda baya nan Haisam yace ta gabatar. Ƙarfe huɗu ta tashi aiki ta haɗa kayayyakin ta ta fita, a compound ta tarda drivern ɗazu yana jiran ta, gaisawa suka yi ta shiga yaja mota suka fita, seda suka fara zuwa makarantar su Ibty suka ɗauke su sannan suka wuce gida. Tun daga gate din gidan tasan akwai abinda ke faruwa aciki ganin yadda jama'a ke kaiwa da kawo maza da mata kamar dai wanda ake wani sha'ani. Drivern nayi parking ta fita ta shiga tafiya cikin nutsuwa, shan gaban ta da akayi ne yasa ta ɗago kanta ta sauke kan yan matan gaban ta dan da kanta a ƙasa yake. Kafe ta da idanun ta da suka yi jajir Nuriyya tayi, wani irin tafarfasa zuciyar ta take yi na tsananin ɓacin rai ga tsananin zafin da take ji saboda matsanancin kishin Salman da ya rufe ta, bata taɓa zaton haka zata ga salma ba, a tunanin ta tunda ance bazawara ce to zata ganta wata ƙatuwar haka mara fasali se gashi ta ganta yarinya danya sharaf kamar ma ta fita ƙuruciya. Ganin yadda yarinyar ta tsaya a gaban ta tana Binta da wani irin kallo da ta kasa gane ma'anar sa sedai tafi danganta shi da kallon banza yasa ta rabe ta ta yi gaba riƙe da hannun ya'yan ta, cikin sauri itama Nuriyya ta kuma shan gaban ta tana Binta da mugun kallo "Aikin banza aikin wofi, banda tsabar budurwar zuciya ina hadin ki da yaya Abdu, bazawara har da ya'ya biyu amma ki likewa mijin da zan aura har kika yi kutunkutun kika aure shi har itama waccan banzar taga wuri ko, to wallahi daga ke har ita ku shirya ba zan taba bar muku ya Abdu ba kuma daga lokacin da na shigo gaba ɗayan ku se kun fice kun bar min shi dan ba abinda ze yi da ku, bazawarar aure da bazawarar titi, mtswww". Sototo ta tsaya tana kallon Nuriyya da kawar ta da suka yi gaba suka bar ta nan tsaye, to ita kuma wannan wacece, ta tambayi kanta dan bata ganta ba jiya da safe da ta tare a gidan ba, lallai Allah me iko, yanzu kam ta fahimci shegun gidan nan da yawa ba wai kaɗan bane ya kuma kamata ta san kanta in ba haka ba cin kashin da zata gani ba kaɗan bane. Haka dai taja yaran ta suka ƙarasa part din, da key ɗin hannun ta tayi amfani ta bude kofar suka shiga ta maida ta rufe, kallo ta shiga bin parlon dashi wai ko zata gan shi zaune ko kwance sedai ko alamun sa babu. Daki ta wuce dasu sukai wanka suka canja kaya sannan ta fita ta hau aikin gyara, duk da parlon ba wani datti yayi ba amma haka ta gyara shi ta sake shara ta sa turare kana ta nufi kitchen. Seda tayi wanke wanken kayan da suka bata da safe sannan ta hau aikin girki, sanin akwai mara lafiya yasa tayi farfesun hanta da yasha kayan ƙamshi da ganyayyaki ta zuba a wani madaidaicin warmer ta rufe ta shiga ƙarasa girkin da take yi. Tana gamawa ta haɗa gaba ɗaya ta kai dining ta koma ta haɗa lemon kankana da yasha madara sosai ta sashi a fridge ya dan yi sanyi ba sosai ba sannan ta haɗa da cups din acrylic jug din ta Kai table. Wanka ta koma ɗaki ta sake yi daidai ana kiran sallah dan haka ta gabatar da sallar sannan suka fito falon tare da yara, Ifty da ta fi hayaniya ta kalla "Maza je ki Kira Daddy acikin daki muci abinci". Da gudu kuwa Iftyn ta nufi hanyar dakin, kwance kan king size bed din sa ta same shi idanun sa a rufe kamar me bacci sedai ba baccin yake yi ba, yayi yayi baccin yazo amma hayaniyar dake tashi a compound din gidan ya hana dole ya hakura ya cigaba da kwanciya. Duk da yaji alamun shigowa amma be buɗe idon sa ba dan a tunanin sa Haisam ne ya dawo sedai jin Muryar Ifty yasa ya shiga buɗe su a hankali kamar me fargabar yin tozali da abin tsoro har ya buɗe gaba ɗaya ya sauke akan ta, murmushi y ƙaƙalo ganin yadda ta wage haƙora tana yi masa dariyar ta me kyau. "Daddy ka tashi muci abinci". Ta faɗa tana jan hannun sa, a hankali ya yunƙura ya tashi zaune tare da jawo ta ya zaunar da ita a gefen sa "Babyn daddy an dawo school?". "Yes daddy, kazo muci abinci, momma ta dafa me daɗi". "Awnn babyn Daddy zata ci delicious, maza je ki kici daddy baya jin yunwa". "No daddy kazo muci kaji". "Naci abinci tun ɗazu angel, maza je kici naki kema". Duk yadda yaso yayi wa Ifty wayo sam yarinyar taƙi yarda dan dama da biyu salma ta tura ta saboda akan abinda take so akwai ta dagiya. Ganin tana kara masa ciwon kai dan dama ba wai ya tafi gaba ɗaya bane yasa ya miƙe suka fito dan t-shirt ne a jikin sa da Three quarter, ko da ya biyo ta bawai ze ci bane, yadai fito ne dan ta ƙyaleshi kawai. Daɗi salma taki ganin su sun fito, wato Ifty fa karshe ce, duk da fuskar sa babu ko ɗigon annuri amma hakan be dame ta ba, badai ya fito ba?, Dama abinda take so kenan. Kujera ya ja ya ɗora Ifty akai shima yana daya ya zauna, a ɗarare salma ta gaida shi dan presence din shi a wajen yasa duk taji ta takura ba kaɗan ba. Plate ta ja ta zuba masa couscous din da tayi wa hadi kamar dambu yasha kayan lambu se ta zuba masa miyar hantan a gefe ta aje masa a gaban sa ta kuma zuba masa hantan da yawa a wani ƙaramin bowl shima ta aje masa, lemon kankanan dama a gaban shi yake dan haka cup kawai ta sake turawa gaban sa in ze Sha ya zuba. Su Ifty ta zubawa kowa nasa suma duk da ba haka ta saba musu ba, sun saba a tare suke cin abincin su su uku, aikuwa kamar yada ta tsammata Ibty kinci tayi s kallon ta da take yi tana narai narai da idanu zata yi kuka. Ganin haka yasa salma ta hade nata da na Ibty dan yarinyar akwai kawa zuci haka kuma shaƙuwar dake tsakanin su sanin ta se Allah, ita kanta ta sani tana matsanancin son yarinyar har fiye da yar uwar ta sedai bata nunawa, ba komai yaja take son ta haka ba se yadda yarinyar ke son ta, komai ba zata ci ba se da ita, ko yaushe yana nanike da ita, duk abinda take so to shi yarinyar ke so haka in dai tace ta bar abu so daga to fa ba zata maimaita so biyu ba ba kamar Ifty dake da ƙiriniya da rashin ji ba sometimes. Tare suka shiga ci ita da Ibty tana ci tana bata a baki, ganin haka itama Ifty se ta matsa kusa dashi ta saka spoon din ta cikin abincin sa dabe ko kalla ba bare ya fara ci duk kuwa da yadda aroma din ya cika masa hanci, yunwa yake ji kamar yaci babu amma baze iya taba abinda ke gaban sa ba saboda rashin yarda. Sam be yarda da yarinyar ba ba kuma dan tayi wani abu na zargi ko kuwa rashin dacewa ba se dan yasan halin mata yayi kuma encountering din shi har kusan so uku, a yadda yake zaune cikin tsakiyar maƙiya da mahada yasani za'a iya amfani da kowa dan ganin an yake shi an kai shi ƙasa ciki kuwa harda ita, ba kowa ne ze iya tsallake tayi makudan kudade kan abinda yake ganin kankani bane balle kuma mace, macen ma irin ta dake struggling kula da kanta da ƴaƴan ta, duk da cewa ba wai tana cikin rashi bane amma mutanen zamani ba abinda ba zasu iya yi kan kudi ba. Abincin da yaji adaidai saitin bakin sa yasa ya buɗe idon sa ya sauke kan fuskar Ifty da takai masa spoon din baki tana murmushi, daga masa gira tayi tana sake maimaita masa statement din ta da tunani be bar shi yaji ba tun farko "Daddy haaa". Ɗan zaro ido yayi kafin ya girgiza kai ya sa hannun ya karbi spoon din a hannun ta ya maida abincin saitin bakin ta yayi mata alamar ta karba da ido, make kafaɗa tayi tare da kauda Kai ta karɓe spoon din ta maida masa baki tare da kwaɓe fuska zata yi kuka tana masa pointing wajen su salma da hannu. A hankali ya juya wajen su ya kalle su yadda suke cin abincin gwanin sha'awa, in Ibty ta bawa Salma se itama ta karba ta bawa Ibtyn, juyowa yayi ya kalli Ifty yana mata alamar ya gani meye, sake ɗebowa tayi ta kai masa bakin sa, duk da ya fahimci me take nufi se ya kawar da kai ya amshi spoon din ya juye abincin sannan ya miƙa hannu yaja plate din gaban salma dake gefen sa ya tura musu nashi sannan ya saka spoon din ya sa ya dibi abincin ya kai bakin sa bayan yayi bismilla. Lumshe idon sa yayi lokacin da abincin ya sauka akan harshen sa, sosai taste din abincin yayi masa ya da yasa yaji kamar kar ya buɗe ido, ya dade be ci abincin da yaji taste din sa ya kaima sa kamar wannan ba, kai in ba dan kar yayi karya ba tun Ummu na raye. Da sauri ya buɗe idon dan kar yarinyar nan tace santi yake, ba komai yasa ya janye plate din ta ba sedan ganin shi yake ci haka ba zata sa abin cutarwa ciki nata abincin ba haka kuma ze gani in zata ci nasa, in har taci to bata sa komai ba in Kuma taki tabbas da matsala. Yana buɗe idon ya sauke akan ta lokacin da ta Kai spoon na biyu bakin ta tana sakewa Ibty murmushi, kauda idon sa yayi ya bawa Ifty a baki, haka suka cigaba da cin abincin cikin nutsuwa hankali kwance. Abu Aulad be ankara ba se ganin plate din su yayi ba komai, gashi dama ba cikakke bane su salma sun riga sun fara ci, tabbas abincin yayi masa daɗi haka kuma be ishe shi ba amma baze ce akara ko ya kara ba, a yadda ya dinga nuna be san ci taga kuma ya ƙara ai da kunya dan haka se kawai ya kai hannu ya zuba juice din kankanar ya Kai wa Ifty baki tasha har ta ƙoshi sannan ya zuba shima yasha. Idea ɗin a cikin hakan dan shima lemon ya tabbatar da babu komai acikin sa tunda yasan ba zata cutar da ƴaƴan ta ba. Tissue yasa ya goge bakin sa haka ma Ifty sannan ya mike tare da ranƙwafawa yayi mata peck a goshi, kujerar Ibty itama ya karasa yayi mata kana ya nufi hanyar dakin sa ya shige. Ajiyar zuciya ta sauke na samun relief dan duk abinda take yi a wajen karfin hali ne amma ji take kamar ta zura da gudu saboda tsabar yadda kwarjinin sa ya cika ko'ina, abincin ma da kyar ta iya daurewa taci wanda hakan dan kore masa shakku da kokwanto ne dam bata manta sentence din Haisam na ɗazu ba ....."be gama sanin ki ba"..... Ita ba yarinya bace da zece wai ne gama sanin ta ba shiyasa baze ci abincin ba, kawai magana ɗaya ce be yarda da ita ba shiyasa aya share masa dukkan shakkun sa.................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 015 [ 12/6/2022 10:54 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      Paid page 015 _________________________📖 suna gama cin nasu ta kwashe ragowar da suka bari taje ta aaje inda ba zasu lalace ba sannan ta koma falo ta kunna wa twins MBC 3, ƙarfe takwas da rabi ta kashe komai suka wuce bedroom suka yi shirin bacci suka kwanta. Yau ma shi ya tashe ta daga bacci kamar jiya haka kuma bata gan shi ba, da alamu yana mata knocking yake tafiya yabar wajen. Breakfast ta haɗa ta gyara inda ya kamata kafin ta koma ta shirya yan biyu itama ta shirya, yau kam a hanyar fita daga falon suka same shi, da alama office ze tafi dan a shirye yake cikin Armani suits din sa coffe color da ya amshi skin din shi ya haska shi sosai, a yadda yayi kyau ba wanda zece wai yayi rashin lafiya sedai wanda suka san shi sosai. Ifty da ta dane shi ne yasa ya juyo daga fitar da ze yi duk da ya riga ya bude kofar, ɗaga ta yayi rungume tana gaida shi yana amsawa dadai lokacin da Nuriyya ta sako kai zata shige zuwa compound dan daga part ɗin su se an biyo ta wajen part ɗin sa za'a kai compound. Tsayawa tayi tana kallon su batare da ta wuce ɗin ba, fahimta da yayi akwai wani a tsaye yasa ya shiga takawa cikin takun sa na ƙasaita da yar sassarfar sa ya kai gaban salma dake shirin dukewa da niyyar gaishe shi. Sauke Ifty yayi ya miƙa dogayen hannayen sa dake cike da gargasa fatar sa luwai luwai kamar baya shiga rana ya jawo ta jikin sa ya rungume tare da kai bakin sa ya sumbaci kan ta. Tsayin mintuna biyu sannan ya zare ta daga jikin sa amma har lokacin yana rike da hannun ta, ƙasa ƙasa yayi magana yadda ko su Ifty ba suji me yace ba balle Nuriyya dake can da ɗan nisa "Anyi rescheduling general meeting zuwa 8:00am dot, make sure baki makara ba". Yana gama faɗin haka ya sake pecking goshin ta sannan ya saki hannun ta ya juya yayi pecking twins ya fita. Tun da ya saki hannun salma Nuriyya tayi gaggawar juya zuwa sashen su dan ta ma hakura da fitar, tsananin ɗacin da zuciyar ta ke mata baze bar ta ta iya fita ba. Tafiya kawai take yi bata ko sanin ina take jefe ƙafarta yayinda zuciyar ta ta kasa dena hango mata yanayin da ta riske su, tsananin soyayyar da ta gani tsakanin su shike shirin hallaka ruhin ta, yaya Abdun da take matuƙar so, yaya Abdun da ta daɗe tana burin mallaka, yaya Abdun da tayi wa kanta tanadi tsawon shekaru yau shine take gani cikin yanayi na shaukin so da kauna da wata mace, wata da ba ita ba, watan ma bazawara. Wasu irin zafafan hawaye ne suka balle kan kuncin Nuriyya da yasa ta kasa cigaba da tafiyar da take yi se kawai kwasa tayi da gudu zuwa part din su. Ita kam salma se bayan fitar sa da kusan mintuna uku kafin ta iya jan numfashi tare da fara kikkifta idanu kamar sabuwar kamun hauka, zare ido kawai take yayinda zuciyar ke tsananin bugu kamar ta fito daga ramin ta, kwata kwata kwakwalwar ta ta kasa lissafin abin da ya faru mintuna uku baya, did he just hug her, ya Allah, he hug her, wallahi he hug her in his broad warm chest. Hannun ta dake rawa tasa ta shafo saman hijab din ta da yayi pecking ta gangaro zuwa gaban goshin ta da shima ya samu kason sa, ya gaffar wannan mutumin ze haukatar da ita. Lumshe ido tayi tare da shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren sa da ya tafi ya bar mata a jikin sa, tsananin daɗin ƙamshin turaren yasa salma tunanin anya ta taɓa jin ƙamshin da ya kai shi daɗi da sanyi tare da ratsa jinin jiki ya sanya nutsuwa da kwanciyar hankali cikin jikin mai shaka kuwa?. Bata farga daga halin da take ciki ba seda Ibty ta shiga jan hannun ta tana kiran su tafi school kafin jiki a sanyaye ta daukar musu baskets din su taja hannun su suka fita. Yau ma drivern jiya ne ya kai su wnada alamu suka nuna yanzu aiki su yake, zaman su yake yi. Bata dawo cikakken hayyacin ta ba seda ta ganta bakin Company sannan yake tuanwa da batun sa na kar ta makara anyi rescheduling meeting. A hanzarce ta sallami drivern ta shiga Company ɗin bayan an caje ta, jakar ta kawai ta ajiye ta nufi office din sa tayi knocking, buɗewar da kofar tayi yasa ta shiga bakin ta ɗauke da sallama ta ajiye masa ipad ɗin schedules a gaban sa kana ta fita zuwa ragowar ayyukan ta. Ko minti biyar ba tayi da zama ba ya fito, se yanzu ta sami damar ƙare masa kallo ta kasan ido, shirin nasa ba ƙaramin burge ta yayi ba tun bare ma sumar kansa dake kwance luf luf tasha mayuka ta gyaru tsaf kamar ba kan dan nigeria ba. "Should we wait for you?". Da sauri ta miƙe jin bakar maganar da ya dankara mata, kai ita wannan dan kusancin da suka samu ya sa ta san shi ɗin ya ƙware a iya fadar bakar magana. Meeting ne suka yi kan wani babban contract da suke nema, tsare tsare akayi na yadda za'a tsara hall din da zasu sauki baƙi dan a shekara biyu baya ma basu sami babban contract kamar shi ba shiyasa aka tara manya manyan Company ɗin dake da alaka da hakan. Ana gama meeting kowa ya koma bakin aikin sa inda ita kam take tare da boss Abdallah kan issue ɗin wasu takardu. Huɗu nayi yau ma ta bar office zuwa makarantar su Ibty ita da drivern su da yace sunan sa Tukur, duk yadda take jin ta a gajiye bata zauna ba seda ta yi girki ta gama ta wa yaranta wanka, yau kam da wuri suka yi bacci saboda Ifty da bata jin dadi su kuma a ƙa'ida in daya be da lafiya dayan ma taya shi yake hakan yasa itama Ibty nan da nan jikin ta ya ɗau dumi shiyasa ta basu magani basu daɗe da sha ba kuma suka yi bacci. Ganin ita daya ce yasa bata fita falo ba tayi zaman ta a bedroom ta buɗe sabon Novel din da ta samo ta shiga karantawa. Sosai hankalin ta ya dauku ga karatun da har bata san shigowar sa ba se sautin buɗe ƙofar dakin sa da ta ji, da sauri ta ajiye wayar tare da fita sedai tuni ya shige har ya maida ƙofa ya rufe. Zama tayi a falon ta cigaba da karatun ta har yayi wanka ya canja kaya ya fito, a hankali ta miƙe tare da sunkuyar da kanta tana masa sannu da zuwa, a takaice ya amsa mata da Lafiya. Ganin ya nufi ƙofar fita daga falon yasa tayi saurin fadin "Angama abinci fa". Kamar baze tsaya ba se kuma ya tsaya dan rabon shi da abinci tun na daren jiya har yanzu se ko malt da yasha. Kujera ta ja masa tare da bashi waje ya zauna ita kuma ta shiga serving din shi, seda ta zuba komai ta juya dan tafiya kafin taji shi cikin bada umarni "Dawo ki zauna". Duk da bata san dalilin zaman ba amma se bata yi musu ba ta dawo taja kujera ta zauna, abincin ya tura mata gaban ta tare da tsare ta da ido alamun taci. Ranta ba ƙaramin ɓaci yayi ba da hakan dan tasan me yake nufi, wato taci dan ya tabbatar bata saka komai ba, wallahi ba dan Haisam ba da ba zata ci abincin nan ba sedai yaki cin, mutum se shegen rainin hankalin tsiya, in yaci abincin cikin wa ze ciwa, ina yunwar shi take wahalar wa ba wani ba. Duk wannan maganganun a ranta take yi yayinda a fili ko alamar ɓacin rai babu a fuskar ta, dama fa duk kuri ne, ita kanta tasan ba dan wani Haisam taci ba, a yadda ya haɗe rai ya bata umarnin ko ita wace bata isa ta saba shi ba dan gaba ɗaya se take jin ya cika falon saboda tsananin kwarjini sa, se take jin ta kamar wata kiyashi a gaban shi. Se da taci kusan loma huɗu kafin ya ja abincin gaban sa yayi bismilla ya soma ci, kafin kace meye ya tashi da na gaban sa haka yasa ta ƙara masa tare da zuba masa fruit juice din da ta hada naturally a cup. Shi kan sa rabon da yayi irin wannan cin abincin ya manta , wani irin nutsuwa da kwanciyar hankali yake ji a tattare dashi, ya dade rufe da ido akan kujera bayan sa jingine da kujerar kafin ya buɗe ido ya kalle ta, hankalin ta gaba ɗaya yana kan karatun da take yi dan haka bata ma san ya gama ba. Ɗauke kan sa yayi "Ki sako hijab muje". Ɗagawa tayi daga kallon screen ɗin ta kalle shi amma tuni ya maida idanun sa ya lumshe, bata fahimci komai a maganar tasa ba illa ta sako hijab Dan haka ta mike zuwa ɗaki, mintuna kaɗan ta fito jikin ta sanye da maroon din hijabin da ya haska ta matuƙa. "Na saka". Ta faɗa a sanyaye kanta a ƙasa hannun ta rike da wayar ta, tashi yayi batare da yace mata komai ba ya nufi kofa, sakin baki tayi tana kallon ikon Allah kafin kuma ta girgiza kai ta bi bayan sa. Tsaye ta sameshi bakin part ɗin su, tana fita yasa mukulli ya kulle part ɗin sannan ya matso kusa daf da ita wanda hakan ya haifar mata da rashin numfashi na wasu sakanni kafin ta fisgo shi da kyar, tafin hannun sa masu tsananin taushi kamar ba na namiji ba ya saka ya lalubo nata tare da jimkewa cikin nasa sannan ya shiga tafiya. Bata da zabi illa bin bayan sa amma gaba ɗaya ji take kamar ba ita ba, wasu irin abubuwa ke gudu cikin jinin ta yayinda take jin jikin ta yayi mata nauyi dan hatta tafiyar da take yi kusan shike jan ta. Yanayin da take ciki ya hanata gane part din baba suka nufa wanda suna zuwa kofa yaja ta jikin sa ya zamana rabin jikin ta na cikin nasa haka shima nasa, a lokacin kam ƙiris ya rage ta zube a wajen dan shi kan sa seda ya fahimci hakan sedai be kula ba ya yi sallama ya shiga falon. Yau ma kamar kullum falon cike yake da ahalin da suka kasance na gidan har ma fiye da rannan hakan yasa jikin salma daukar rawa fiye da da. Kasan carpet Abu Aulad ya zaunar da ita kana ya zauna gefen ta har jikin su ma gogar na juna ya kuma sa hannayen sa masu taushi ya ruƙo nata tareda sarƙe yatsun su hankalin sa kwance ba wani kunya ko jin nauyi. Gyaran murya baffan sa yayi wanda ya kasance cousin din baba haka kuma mafi kusanci dashi duk cikin yan uwa, duk da yaji gyaran muryar ya kuma san dashi ake amma be ko kalli wajen ba balle ya nuna yaji har ila yau yatsun su na sarkeda na juna yana murza tafin hannun ta cikin nasa a hankali. Murya na ɗan rawa salma ta gaisar da baba kana ragowar mutanen da ta gani cike da dakin dan dukkan su sun girme ta se ƙalilan da ba'a rasa ba, kanta na kasa ta gaishe su irin gaisuwar nan ta jimilla banda baba da ta ware, hakan kuwa ba ƙaramin konawa Hajiya Babba rai yayi ba dan a ganin ta ai Salman bata girmama ta ba haka kuma ta nuna bata ɗauke ta da daraja ba tunda bata haifi mijinta ba sedai sanin irin tsiyar da ta shuka musu yasa ta watsar da wannan batun a ranta. Baba da baffa kaɗai ya gaisar ya ɗauke kan shi gefe tare da gyara zama yana sake matse wa salma waje wadda take dan janye wa. Kau da kan shi baba yayi dan duk suna ganin meke faruwa, cikin ran sa kuwa mamaki yake na yadda akayi Abu Aulad ya zama fitsararre haka dan shi kam a da yasan ba haka dan shi yake ba sam. "Ka bude mana taron da addu'a Adam". Baffa dake amsa sunan Adam ya gabatar da addu'a kamar yadda baba ya umarce shi kafin yayi shiru suka shiga sauraren jawabin da baban yake korowa kamar me karantawa a littafi "Jiya da safe Abdallah ya zo gidan nan tare da wannan yarinya matsayin matar sa wadda ta taɓa aure har ma da albarkar yaya biyu, a kwanaki uku da suka wuce ne yazo yake sanar da ni ya sami matar da ze aura kuma ba kowa bace face wadda aka buga hotunan su a jarida, duk da jaridar bata yi wani tasiri ba sosai amma na nuna ban amince ba, Abdallah be saurari umarni na ba yaje ya auro ta saboda taƙamar shi namiji ne ze iya yiwa kan sa aure haka kuma yana da kudin da ze yiwa kan sa komai ba tare da ya jira niba. A tsaurin ido irin nashi ya zo min da ita gidan nan matsayin ya dauko matar sa ta tare, a gabanin ayi haka da sati ɗaya babar sa wato Hajiya gata nan ta same ni kan batun rashin auren nasa da yadda abun ke damun ranta har ma take sanar da ni in ba damuwa ta yiwa iyayen wannan yarinya shuraiha magana kan hakan domin yarinyar ta daɗe tana son shi, nayi farin ciki da maganar domin mahaifin yarinyar sananne ne a wajena dan haka bana da ko dar kan tarbiyyar ta, bayan haka kuma nima zaman sa hakan yana damu na, wannan dalili yasa na yiwa mahaifin nata magana aka san da batun duk da ba sa rana akayi ko something officially ba, a bisa laifin da Abdallah yayi min na aure batare da yarda ta ba yasa na aura masa ita shuraiha a yau juma'a bayan an sauko masallaci. Ba zan ce dole se ya zauna da shuraiha ba amma zan faɗa masa dole in har baze zauna da ita ba to fa itama zaɓin sa sedai ya hakura da ita, zaman zaɓin sa daidai yake da zaman shuraiha haka ma fitar ta gidan daidai yake da fitar wannan yarinya da ya kawo, wannan shine hukunci na a matsayin na na mahaifin Abdallah, akasin umarni na kuwa sedai ya nemi wani uban ba Abdulsalam Gamji ba".............................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 016 [ 12/7/2022 12:42 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                        Paid page 016 _________________________📖 Shiru falon yayi baka jin komai se fitar numfashin mutanen cikin sa seko shessheƙar kukan Nuriyya da ta fara fitowa a hankali, ba wanda ya kalle ta balle ya nuna yasan me take wanda hakan ya dada tunzura ta ta kifa jikin mahaifiyar ta Anna ta fashe da kuka sedai bame sauti bane. Baffa ne da ya lura Abu Aulad bashi da niyyar cewa komai se kallon su kawai da yake yi, in ya kalli baba se ya kalle shi kamar wanda yake son ganin wani abu na daban a jikin su "Baka ce komai ba Abdallah bayan kuma kaji bayan nan mahaifin ka". "Me zance baffa, ina an riga an daura auren, kuma yace umarni ne ko, to kar ku damu na karba, bashi kenan ba?". Tsira masa ido Hajiya Babba da baffa suka yi dan jin yayi saurin amincewa abinda basu taɓa zato ba, sedai ita Hajiya Babba sam bata yarda da wannan kalaman nasa ba, dole cikin ransa ta san akwai abinda ya shirya, tabbas akwai abinda yake tsarawa. Takaici ne ya cika ta na sanin bata yadda za'a yi ta iya sanin abinda ya ɓoye cikin ransa, wannan damar kam har abada ba zata taɓa samun ta ba, amma ba komai shima har yanzu be gama sanin ta bane sedai yana gab da sanin nata matuka har ma ya bawa wani labari in yayi ƙarkon kwana fa kenan. Dogon tsakin da yaja ne yasa Hajiya farga da cewa har yanzu fa yana nan, da sauri ta juya wajen sa tare da riƙe hannun sa biyu tana masa magana da ido dan tasan sarai waye dan ta, be ki ya fallasa komai asirin uban kowa ma ya tonu ba. Ɗauke kan sa yayi daga gare ta yana ciccin magani kamar wanda ya haɗiyi madaci, abu ɗaya ne yasa ya yarda da plan din su, ba kuma komai bane illa son cimma manufar sa, hakan na samuwa kuwa dole ya kwace abinda ya kasance nasa ne mallakin sa shi shi kaɗai batare da uban kowa ba, a wannan lokacin kuwa baze saurari kowa ba ciki kuwa har da ita Hajiyar dake amsa sunan mahaifiyar sa. Mabiyar sumaya mai suna Nadiya ce ta kalli salma cikin rainin hankali da son tusawa mutum haushi ta shiga fadar maganar da ta san farkon fadin ta amma bata da masaniyar abinda ka iya biyo baya "To uwargida se ayi haƙuri a dangana a taya miji biyayya ga iyaye dan kin san ana iya canja mata amma iyaye kam ko makwafin su ba a samu, saboda adalci irin na iyayen mu ki kalla fa basu tilasta shi sakin ki ba duk da cewa har wa yau bamu tabbatar da asalin ki ba, auren ki na farko gaskiya ne ko suna?, Yaran sunna ne ko akasin haka amma duk suka kau da kai, aka yi aure ba'a ga ko dangi naki daya ya rako ki ba asalima ni labarin da naji wai zaman kan ki kike, kin ga kuwa ai dole iyayen mu su zaba masa mata mai cikakken asali, tarbiyya da nagarta, ko ba haka ba?". Wani irin damƙe hannun Abu Aulad dake cikin tafin hannun ta tayi jikin ta na daukar rawa gaf gaf gaf ba dan komai ba se najin ana neman tozarta nasabar ya'yan ta, ana neman shegan ta mata ƴaƴan ta, ƴaƴan da zata iya dafa Alkur'ani ta rantse na sunna ne, ko da ita kanta bata san asalin su ba amma meze kawo maƙiya son hallaka ƴaƴan shege alhalin su masu farin ciki ne in abin kunya ya sami wanda basa so?, Tabbas ma ƴaƴan ta na halak ne kuma wallahi ko daga wajen waye ba zata lamunci a bata mata nasabar su ba ko da kuwa shi wanda ke amsa sunan miji a gare ta ne da kansa. "Hmm adai bar maganar kawai Nadiya, yara se shegen kyau kamar su suka yi kansu, kin san fa dama ance shegu sun fi ya'yan halak kyau". Ba zata iya cigaba da zama tana sauraren waɗan nan munanan kalaman a kan yayan ta ba, abu ɗaya ya hanata ramawa da mai da martani wato darajar baba dake zaune a wajen, sedai rantsuwa ce tayi na bashi suka ci kuma se sun biya, biyan ma da abu mafi raɗaɗi, tabbas zata nuna musu wannan salman ta yanzu ba ta da bace, salmar kauye tuni ta dade da mutuwa, wannan kuwa sabuwa ce mara ɗaukar wulaƙanci daga wajen kowa, wannan me yakin kare mutunci da martabar ta da ta ƴaƴan ta ce, wannan salmar da ta kauye kamar gabas da yamma ne da ba zasu taɓa haduwa ba. Duk da yaji sanda ta zare hannun ta cikin nashi be hana ta ko riƙe ta ba dan shi ma ze fi son ta fitan, baba kawai ta kalla cikin danne bacin ran ta tayi wa sallama ta fice, wannan ma ya Kuma konawa Hajiya Babba rai tare da kara hura wutar tsanar Salman a ranta, ita kuwa salma tana sane tayi hakan dan bata ga abin da zesa ta yi musu magana ba daga ita har baffa alhalin suna zaune ake zagi da cin mutuncin ta amma ba wanda yayi ko alamar tsawatar wa ga yaran dan haka gare ta sam basu da wani daraja bare girma, shi kan sa baban ta daure ne saboda darajar dan sa amma zuwa gaba in haka ta cigaba da faruwa bata san me zata aikata ba ko da kuwa a gaban nasa ne. Seda ya tabbatar ta wuce kafin ya tashi daga kan rug din da yake ya koma kan one sitter ya zauna sosai, irin zaman nan na isa da iko dan kafar sa daya na kan ɗaya ne yana girgiza ta a hankali "a gani na da auren bazawarar titi so dubu adadin da za'a sake bani zaɓi gara auren bazawarar da tayi aure ta raya sunna har ta haihu kana qaddara ta raba ta mijin auren, baffa a wannan zamanin yan mata da yawa lillibin biri ne, akace kura da fatar ajiya, to haka suke, a zahiri gasu dai yan mata ne da ko auren fari basu yi ba, a badini kuwa ko matar auren da ta shekara biyar a gidan miji ba zata nuna musu komai ba akan sanin da namiji, ayi ciki a zubar, ayi ciki a zubar se ayi yafi nawa kafin auren, shiyasa da yawa Allah yake hana su haihuwa a gidan auren kuma kaga su zo suna ta neman ta ido rufe, to taya ma zasu samu bayan an gama tambadar da ƙwayayen tun a waje?!. Nikam in har na auri budurwa na same ta a bazawara, ba ita dake matata ba hatta iyayen ta se nayi Shari'a dasu dan sun cuce ni sun ha'ince ni da suka bani second hand ko ma multiple hand ne a matsayin sabo". Wani irin gau Hajiya Babba taji maganganun nasa kamar ya kwaɗa mata mafi zafin mari, tsananin raɗaɗin da take ji a ranta da zuciyar ta kuwa ya kasa ɓuya dan lokaci guda idanun ta suka canja launi zuwa ja sosai, jikin ta har wani dan barin ɓacin rai yake yi. Ba ita kadai ba kowa na falon seda ya ɗauke numfashi na wasu sakanni domin dai maganganun sa a bayyane suke cewa da Nadiya yake saboda ita ce ta taɓa rashin ji lokacin da tana budurwa, abin babu dadin ji dan so biyu tana cire ciki ban da kuma magungunan planning din da ta sha wanda an sha kamata dasu ba so daya ba, kai da abin yayi tsanani ma har barin gida take ta kwana waje, da taimakon sa na jajircewa wajen sa mata ido da bibiyar ta da kuma na addu'ar da ake yi da rubutun da ake bata aka samu komai ya wuce kamar ba'a yi ba, sedai babban kuskuren da suka yi shine basu fadawa wanda ze aure ta komai kan abinda ta aikata ba aka lulluɓe aka kai ta, ba irin yadda be yi da baba a faɗa masa ba amma Hajiya ta fututtuke ta hana dole ya hakura ya zuba musu ido. Ba kuwa ƙaramin tashin hankali aka kwasa da mijin ba dan yace an ha'ince shi, shi da sun faɗa masa gaskiya shi me iya haƙura ne ya karbi ƙaddara amma boyewar da suka yi shine ɓacin ran sa, abu dai yaki daɗi haka dai auren ya mutu ta dawo gida, se bayan shekara sannan ta sake wannan auren da take dashi. Kuka Nadiya ta fashe dashi hannu bibbiyu aka tana faɗin yayi mata gori yaci zarafin ta, ko kallon ta be yi ba se Hajiya da yake kallo dan yasan komai Nadiya ta faɗawa Salma da sanin ta da kuma sa hannun ta shiyasa bata dakatar da ita ba, kuma da biyu yace ze yi Shari'a da wanda ya bashi second hand matsayin budurwa wanda wannan kuma da shuraiha yake shiyasa abin ya hadewa Hajiya, ga bakin ciki ga kuma fargaba da tsoro. "Kaga baba kayi masa magana akan abinda yake wa yan dakin mu, jibi fa maganar da ya fadawa yaya Nadee kuma in yi magana ace bani da kunya". Abdulkarim dan autan Hajiya da ta ke kira da jarumi ya faɗa yana harare harare, ba ƙaramin haushin Abdallah yake ji ba sedai yayi kaɗan ya tunkaro shi shiyasa ya saka baba a lamarin dan watarana da ya taɓa kuskuren yi masa rashin kunya wani mari da yayi masa seda ya wuni be san wake kan sa ba, haka hannun sa da ya daga da sunan kai wa Abu Aulad ɗin duka seda aka ɗora shi dan baras ya balla shi shiyasa yake tsoron sa, wannan maganar ma dan kar Hajiya ta balbale shi da fadan matsoraci ne in sun koma part din ta. "Me kuma ya kawo batun gori cikin maganar nan Abdallah, me kake so ka zama ne, kai ne fa me tare mata in kaga wani na neman tozarta ta amma kai ne ma me yi mata, wace irin rayuwa ce wannan?". Cikin rashin damuwa ya gyara zaman sa yadda ze fuskanci baba sosai "Ko mintuna bakwai ba'a yi ba da yarinyar nan ta buɗe ƙazamin bakin ta tana fadawa matata maganganu, shin hakan da tayi daidai ne, martabar matata da mutuncin ta fa ta taɓa a gaban ku duka amma shin wa ya ce mata tayi ba daidai ba?, Babu, shin ba ita ya kamata in taga za'a ci zarafin salma ta tare ba Baba, amma me tayi yanzu?!. Am sorry to say kayi haƙuri baba Amma tun shekaranjiya na faɗa sedai ko in Kun manta, duk wanda ya taɓa min mutuncin mata ba zan kyale shi ba, kowaye shi kuwa, babba duk girman sa haka karami duk kankantar sa ban cire kowa ba se inda ƙarfi na ya ƙare, kai ne kadai zan iya kau da wa kai a kan ta, dan haka gwara su kiyaye". Ko sallama be yi wa kowa ba hatta baba dan ya bashi haushi ya ficewar sa zuwa sashen su, falon shiru ba kowa haka ba haske sosai alamun itama ta kwanta kenan, dakin sa ya shige ransa ba daɗi ta wani bangaren kuwa farin ciki ne dan ganin yadda Hajiya Babba ke sharar hawaye haka ta kasa cewa komai alamun ta kai maƙura wajen ɓacin rai kenan. Acan falon baba kuwa shima baffa sallama yayi musu ya fice zuwa sashen sa dake can da nisa dan wasu ɗauka suke ma ba'a cikin gidan part din yake ba saboda nisan sa zuwa na baba. Shifu falon yayi se tashin ajiyar zuciyar Hajiya Babba, ɗagowa tayi zata yi magana se kuma idanun ta suka sauka kan su Anna da Nuriyya da suka zuba tagumi suna bin kowa da kallo, wata shegiyar harara Hajiya ta watsa musu da tasa Anna janye idon ta daga kan su ta fara yunkurin tashi haka itama Nuriyya ganin Anna na miƙewa itama se ta tashi, sallama suka yi wa baba suka wuce sumi sumi suka fita. Seda taja tsaki kafin ta maida hankali kan baba dan da zafi zafi zata tafi da komai in ba haka ba kuwa yaron nan dab yake da sa mata ciwon zuciya. "Banji kayi maganar tariyar yarinyar nan ba Alhaji, kasan fa yadda a kayi auren nan in ba dagewa akayi ba haka auren ze lalace dan kasan dama ba son ta yake ba, ni kuwa ba zan zuba ido ya kare rayuwar sa da yarinyar da bamu san asalin ta ba, ko banza gwara shuraiha mun san iyayen ta mun san sana'ar su dan hatta wasu daga cikin ƴan uwan su na sani, ga yarinyar akwai tarbiyya ga girmama na gaba, amma ya kace?". Numfasawa baba yayi kafin cikin sanyin da yayi saboda hayaniya da be fiya so ba yanzu kan sa se ya fara ciwo, ta nan wajen kam shi Abu Aulad ya gado "Ba matsala, zan sa a gyara side din dake gefen nasa se ta tare ko nan da zuwa sati ɗaya ne". "Har sati Alhaji, be yi yawa ba kuwa?". "To shikenan, nan da zuwa kwana uku ai nasan yayi ko?". "Sosai ma, Allah ya kara buɗi kaga se in sanar da iyayen ta dan su tanadi komai". Bece mata komai ba se lumshe ido da yayi dan kansa dake dan ciwo, ganin haka yasa Hajiya miƙewa dan ba ita me da girki ba dama, amarya ce wadda yau kwana uku kenan basu haɗu ba, ta dai ji wai ta fadi kan hannun ta ya karye dan haka taje jiyya gidan wan ta, ita kuma yau ba zata zauna da Alhaji ba dan tana bukatar su tattauna da ƴaƴan ta kan abinda ke gaban su. ★★★★ "Amma Anna yanzu haka zamu zuba ido mun tashi ba mu ga tsuntsu ba mu ga tarko, yanzu ana nufin in zuba ido in kalli yaya Abdun da nake matukar so zaune da wasu matan da babu ni a ciki, eye Anna ki fa ga kallon da hajiya tayi mana yau, da ni matar yaya Abdu ce ta isa tayi?, Kalli dai yanzu yadda ya shigar wa matar sa faɗa, wayyo ni Nuriyya na shiga uku". Nuriyya ta faɗa tana fashewa da kuka wanda tun da suka dawo sashen su dama abinda take yi kenan.......................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 017 [ 12/7/2022 1:01 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      Paid page 017 _________________________📖 "Bar kira min shiga uku kinji ko, ba zanga shiga  ko daya ba balle uku insha Allah, in ta San wata ai ba ta san wata ba ita Hajiyar, mu zuba ni da ita muga waze nasara". "Wancan karon ma fa haka kika ce Anna, Kuma ita din tayi nasarar dan gashi ta aura masa waccan shegiyar me goshi kamar jirgi ya doso tasha". "Wannan karon kuma ki zuba ido ki kalli yadda zan buga wasan, kin san yadda akayi tun farko ya auri yar uwar ki nafisatu?, To shima tsari nane yanzu ma kuma ze aure ki ko be so ba". Rungume Anna tayi tana yar dariyar farin ciki "Na gode Anna ta, Allah ya bamu Sa'a, in ya aure ni har Makka zan sa ya kaiki dan ni ba irin yaa nafisa bace". "Allah ya yarda diyar arziki, ni dama nasan ke ɗin ba irin ta ba ce dan ita ta cika sanyin jiki da nawa". Nan suka cigaba da hirar su kamar basu da wata damuwa yayinda Anna ke ta sake saken neman mafita a ranta. Can ɓangaren su Hajiya da ƴaƴan ta kuwa sashen ta suka yi masauki cikin babban falon ta da ya lakume set ɗin kujeru biyu, ita dai Nadiya har lokacin sharar hawaye take lokaci zuwa lokaci dan ba kaɗan ba taji ciwon maganganun da Abu Aulad ya faɗa mata hakan yasa ta ƙudiri niyyar bada goyan baya kan dukkan wani tsari na Hajiya wajen fafutukar ƙwatar musu yanci. "Shi wannan shashashan har yanzu be san me duniya take ciki ba, da anyi magana yace so, son banza son wofi, Kai a yanzu an gaya maka akwai wani so bayan son kuɗi, ai kuɗi sune rayuwa malam, in Basu Kuma babu rayuwa haka ba wanda ze kalle ka har ko ita da kake iqirarin kana so ɗin, duk fafutukar da nake yi domin ku nake yi musamman ma kai, in aka samu nasara zaka daukaka ka shahara har fiye da yadda shi yayi suna, haka ma yan uwan ka zasu fi karfin wulaƙancin namiji da duk wani treats din sa, dan haka nake so duk ku bani hankali da tunanin ku mu haɗu mu hada karfi da karfe mu yaki abokin gabar mu da ba kowa bane face Abdallah". "Ni dama kin san tuntuni ina bayan ki akan komai, wadannan biyun ne ke neman bamu matsala musamman ma Kareem dan gara Nadiya ita kawai shiga cikin sha'anin ne bata yi". Sumayya ta faɗa tana duban nadiya da idanu suka yi wa jajir kamar an watsa mata barkono "Yanzu kuma ina ciki yaa sumayya, ina goyon bayan duk wani tsarin Hajiya dan haka ba kuda matsala yanzu dani". Nadiya ta faɗa tana jan hanci, muskutawa Hajiya tayi cikin jin daɗin yadda ƴaƴan nata yanzu duk suka hau kan hanya "Atoh gwara dai ki san ciwon kan ki, yanzu fa jibi maganganun da yaron nan yayi, da akwai bako a wurin yakike gani za'a ɗauki maganar, dan haka ba zamu bar abinda yayi a banza ba dole a bi miki kadin hakan, ita ma kuma matar tasa se ta raina kanta, bari dai yarinyar can ta tare". "Me ya haɗa tariyar ta da tsarin mu Hajiya?". "Aikuwa ita ke da alaka da tsarin mu dan dole muna bukatar makusanci gare shi sosai wanda ba kowa bane face matar sa, aikin mu ze Fara ne daga zarar ta tare, zamu dinga samun information a wajen ta na shige da ficen sa, yanayin kasuwancin sa, takardun kadarorin sa da dai sauran su". Sosai suka gamsu da kalamai da hangen Hajiyar suka kuma cigaba da tattauna tare da kulla mugayen nufin su. ********* A hankali ta sauko daga kan gadon tana addu'ar bacci wadda Manzon Allah ya koyar, miƙa tayi a hankali sannan ta sauke tare da nufar toilet dan yin alwala. Ta daɗe tana addu'a cikin sujjada da kuma bayan ta idar, kukan ta take kaiwa wajen da zata sami magani musamman yanzu da matsalar ta suka karu dan ta tabbata wannan auren da aka yi masa ba iya shi kaɗai ze zamewa matsala ba har da ita. Bata san wace yarinyar da ake batun an aura masa ɗin ba sedai tasan tun da ta biyo ta bangaren Hajiya mutunci kam se in Allah ne yayi tana da rabo, kwana biyu da tayi cikin gidan sosai ta fahimci matar bata san wata kalma da ta danganci mutunci ba ko kadan haka ma kuma ƴaƴan ta dan duk sun gwada mata hali ta gani, namijin ne kawai shi kuma ba abinda ya haɗa ta dashi balle taga nashi kalar rashin darajar. Praymat ɗin ta ninke tare da maida ta inda ya kamata kana ta shiga ayyukan gidan kamar yadda ta saba, tana gamawa ta shiga hidimar ɗora breakfast Shima ta jera sannan a gurguje ta shiga ta tashi yan biyu tayi musu wanka tare da shirya su ta bar su kan suyi sallah ita ma ta shiga nata wankan. Cikin gogaggun uniform din ta set uku ta dau ɗaya ta zura tare da jawo Ash and black ɗin kimono ta ɗora kan kayan, ba ƙaramin kyau tayi ba haka kuma zagayayyar fuskar ta ta fito sosai. Bata ga su Ibty a dakin ba tasan sun fita falo ne dan haka ta dau handbag din da zata tafi da ita kalar silvern takalmin ƙafarta wedge me fuskan slipper. Kamar yadda tayi hasashe kuwa falon ta same su zaune kan sofa Ifty kwance kan cinyar Ibty dan har yanzu jikin ta ba wani kwari sosai, zama tayi gefen su ta dau Iftyn ta maida kan cinyar ta tare da duban Ibty "Maza je ki kira Daddy yazo muyi breakfast". Tashi yarinyar tayi zuwa dakin daddyn nasu dadai yana bude kofar ze fito, murmushi ya sake mata tare da tsugunnnawa ya buɗe mata hannun sa ta shige jikin sa ya mike da ita, "Good morning Daddy". "Good morning babyn Daddy, hope kin tashi lafiya". "Lafiya lau Daddy Amma Ifty Bata da lafiya". "Soobhanallah, me ya same ta?, tana ina?". Ya tambaya a rude dan kwana ukun da suka yi tare ba ƙaramin shiga ran sa yaran suka yi ba tun bare ma Iftyn dan ita tafi shige masa ita Ibty ya fahimci momma's girl ce. "Fever ne Daddy, tana wajen momma a parlor". Falon ya shiga takawa yana ƙarasawa kuwa idanun sa suka sauka kan su har lokacin suna zaune kan sofar Salma rungume da Iftyn a ƙirjin ta. Sauke Ibty yayi ya ƙarasa gaban Salman tare da duƙawa yasa hannu ya cire Ifty a jikin ta sannan ya nemi waje ya zauna ɗauke da ita ya shiga tattaba jikin ta wai ko zeji zafi sedai babu se dan dumi Wanda normal ne a jikin kowa. "Sannu Angel, how are you feeling?". A hankali ta bashi amsa da "Fine Daddy, good morning". "Taci abinci ne?". Kallon sa salma tayi jin abinda ya faɗa sedai se taga hankalin sa da idon sa baya kanta yana ga Ifty ne, kamar tayi masa shiru se kuma ta bashi amsa "Dama kai muke jira muje muci". Bece komai ba ya tashi zuwa dining ɗauke da yarinyar a ƙirjin sa, kujera ya sa kafa yaja ya zauna itama ya gyara mata zama kan cinyar sa, itama salma miƙewa tayi tare da riƙe hannun Ibty suka ƙarasa dining ta ja mata kujera ta zauna sannan ta shiga serving din su. A hankali yake bawa Ifty shima yana ci dan yau salma bata jira ya bata umarnin dandanwa ba, tun kafin ta zuba wa kowa tayi spoon uku a gaban sa Sannan ta zuba masa ta zubawa kanta haɗe da Ibty. Itama kan cinyar ta ta ɗora Ibty tana bata tana ci har suka gama, sun riga su Abu Aulad gamawa saboda rarrashi da lallaɓa iftihal da ya zauna yi, ba kaɗan ba girma da darajar sa suka karu a idanun salma ganin wannan special care din da yake bawa yarta, aka ce me da wawa to gare ta itama haka ne. A kafada ya saba iftihal tare da ɗaukar basket ɗin ta yayi waje itama suna rufa musu baya hannun ta riƙe dana ibtisam dayan kuma basket din Ibtyn da handbag. Ita ta rufe part din dan shi har sun ɗan yi nisa, itama daukan ibtisam tayi dan kar yarinyar taji ba daɗi duk da ma dai ba ruwan ta amma dai ai yan biyu ne. Mugun tsaki sumayya da ta fito zata tafi wajen aiki ta saki kafin ta bi bayan sa da "An dai yi asara, duk jiji da kai da takama da dukiya aka kare a bazawara me yaya biyu, mijin tace kawai". Be ko kalle ta ba balle ya nuna ya san tana yi dan ita kam ya san bata ƙi a zauna ayi ta hayaniya ba shikuma sam hakan ba dabiar sa bace, wanda yake yi ma yanzu kure shi suka yi. Bayan motar ya buɗe yasa Ifty tare da basket din ta daidai lokacin da su salma suka ƙaraso ya karbi Ibty a hannun ta itama ya sata sannan ya rufe, zagayawa yayi ya buɗe ma salma front seat, wani dindirindindin haka taji lamarin a ranta, yau ita ake budewa mota, kuma wai Mr Gamji ke buɗe matan, lallai Allah me iko. "Shiga muje mana". Da sauri ta dawo hayyacin ta jin maganar sa cikin kunne ta ta shiga shi kuma ya mai da kofar ya rufe sannan ya koma masa side din na driver ya shiga. Mamaki take yi ganin shi ze tuka motar da kansa abinda ta san ko shi driver ke kai shi office dan ban da ranar da suka je BA MUNI bata taɓa ganin yayi tuƙi da kansa ba tun da take Company ɗin. A hankali ya kunna motar tare da yin addu'ar shiga abin hawa kana ya juya ta suka nufi gate, tun kan su karasa aka buɗe masa kofar dan haka yana zuwa ya fice tare da hawa kan titi. Hankali kwance yake tuka motar yana yi yana receiving call har suka kai a school ɗin twins, parking lot ya kashe motar tare da budewa ya fito, back seat ya buɗe ya dauki Ifty ya riƙe a ƙafaɗar sa tare da daukan basket din da other hand, ya maida ƙofar da kafar sa ya rufe. Itama salma budewa tayi ta ɗau Ibty da abincin ta ta rufe bangaren suka yi arean class din, har kan chair ya aje iftihal yayi pecking kuncin ta haka ma ibtisam da salma ta aje sannan ya juya ya fita itama tabi bayan sa. Seda suka hau kan titi sosai sannan yayi magana idanun sa a kan kwalta "Makarantar ta zama dole ne da se an je ta ko ba'a da lafiya?". Tasan da ita yake tun da su biyu ne a motar "Babu inda zan aje ta in bata je school din ba". Bece komai ba ya maida hankalin sa ga tuƙin da yake yi har suka kai Company, parking yayi aka gama bincike motar sannan ya shige, inda aka saba parking motar shi ya kai motar tare da kashewa sannan ya fita. Har ya danyi gaba ya dawo side din ta yasa hannu ya buɗe mata daidai lokacin da ta gama tusa kimono din ta cikin jaka dan dama abinda ya tsaida ta kenan bata fito ba lokacin da ya gama parking. Akan idanun Laila da Umah komai ya faru dan fitowar su kenan daga mota suma dake maƙota ne tare suke tahowa a motar Umah dan iyayen ta masu rufin asiri ne akasin Laila da ita ke kula da gidan su dan mahaifin ta bashi da karfi. Zaro ido Umah tayi ta kalli Laila da ta daskare a wajen, ta gaban su suka wuce batare da kowacce ta iya ƙwaƙƙwaran motsi ba tun balle Laila da tayi mutuwar tsaye, a kusan tare suke tafiya duk da ya ɗan zarta ta kadan dan takun namiji da mace ba ɗaya bane har suka shige main building. Jijjiga Laila umah ta shiga yi ganin bata ko kyafta idanu, dogon numfashi taja tare da juyowa ta kalli umahmatun "Da gaske ne abinda ido na ya gane min ko mafarki nake Umah?". "Aikuwa dai gaske ne Laila dan nima na gani, akan ido na boss ya buɗewa miss Salma mota ta fito ya maida ya rufe kuma suka jera zuwa cikin building". Laila bata iya cewa komai ba se aniyar zuciya da ta dinga sauke wa akai akai, tsayin lokaci kafin ta ɗago ta kalli Umah a raunane "Hakan na nufin yana son ta kenan?". Kau da kai Umah tayi dan a yanayin da lailan tayi magana dole ne ta baka tausayi, sedai ya zama dole ta haƙura ta farka daga mafarkin da take yi wanda take da 99% assurance baze faru ba "Kin taɓa ganin namiji ya kashe kudin sa ya auri matar da ba ya so, balle kuma mata irin su miss Salma da ba kowa ne namiji ne ze iya tunkarar su ba, kiyi haƙuri ki sawa zuciyar ki salama laila, ki buɗe ido ki kalli zahiri rayuwa ba bandini ba, kina da masu son ki dadai gwargwado kuma dukkan su suna da rufin asiri, akan me zaki zauna kina ɓatawa kan ki lokaci kan wanda be san kina yi ba, na tabbatar miki in da za'a tsare boss da bindiga kan ya suffan taki wallahi sedai a harbe shi dan baze iya ba, kai ko gaban sa aka kawo ki aka ce ya fadi sunan ki na tabbata baze iya faɗa ba dan be sani ba". Lumshe ido Laila tayi hawaye na gangarowa daga idanun ta zuwa kan kuncin ta, ta sani tabbas gaskiya Umah ta faɗa amma kuma ai ba ita ta ɗorawa kanta son shi ba, akan me za'a dinga ganin laifin ta, ta ina zata fara yakin cire son da ta riga ta bari ya zaga ko ina cikin faɗin zuciyar ta ya kafa rassa?, Tabbas ba zata iya ba!, Bata haƙura ba, haka ba ta fidda rai ba, tana ji a jikin ta watarana zata zo da A A Gamji ze dube ta da duba irin na soyayya har ma su kasance ƙarƙashin inuwa ɗaya wato aure. Wannan false assurance din da zuciyar ta ta bata yasa bata kuma saurarar Umah ba tayi gaba zuwa main building tana sake karfafawa kanta gwiwa......................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 018 [ 12/8/2022 11:46 AM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* Paid page 018 _________________________📖 Yau kam da wuri suka tashi kasancewar Asabar karfe biyu ake tashi, bata san yadda akayi ba se ganin driver tayi yazo daukar ta dan ita a fitowar da tayi niyyar ta taje ta hau adaidaita sahu ne. Gida ya kai ta saboda weekend su Ibty 3:00 pm suke tashi, akwai ragowar hour daya kenan. Wanka tayi ta saka riga da wando sakakku sannan ta nufi kitchen dan yin girki. Tsayuwa tayi a kitchen din tana ƙarewa komai kallo cikin tunanin me ma zata dafa, ta dade tsaye kafin ta fara firfito da kayayyakin da zata buƙata wajen girkin. Cikin abinda be gaza awa ɗaya ba ta gama malmala tuwon ta na shinkafa da yake nan fari tas dashi ta zuba a warmers, a dan kwanakin da yake cin abinci dasu ta fahimci ya fi cin dambun couscous da tayi wanda a nata fahimtar ta gane ya fi son abinciccikan gargajiya. Tukunyar miyar ta buɗe, lumshe ido tayi saboda ƙamshin da ya daki hancin ta, buɗe wa tayi ta juya miyar dan ganin ta ƙarasa dafuwa ko kuwa, ita kanta tasan miyar ta haɗu ko a iya ido balle kuma ina aroma din ya shiga hancin mutum. Kashe gas din tayi tare da zuba wa cikin daya warmer din mahaɗin na tuwon, cikin jin daɗi ta haɗa kyakkyawan kunun gyaɗa ta juye cikin flasks sannan ta haɗa komai takai dining ta jere komai. Falon ta shiga gyarawa though ba wani datti gare shi ba, tana gama wa kuma ta koma bedroom din ta shi ma tayi masa thorough sanitation, kwata kwata sabida aiki ta manta da lokacin dauko su Ibty yayi, gaba ɗaya se ta ringa ganin ai se four Kamar ragowar ranaku. Wanka tayi tare da sauya kaya zuwa doguwar rigar atamfa pitch color dinkin A shape, sosai rigar ta zauna a jikin ta haka ma kalar ta karɓe ta kai kace purposely dan ita dama akayi ta, ɗankwali ta ɗauka zata daura se kuma ta dakata jin kamar Muryar yaran ta, da sauri ta daga kai ta kalli agogo se taga har hudu saura mintuna biyar, se lokacin ta tuna wai ashe fa three za ah tashi. Da hanzari ta fito ko ɗankwalin ma bata daura ba yana dai riƙe a hannun ta, so take taga waye ya dauko mata su dan dai bata ce driver ya ɗauko su ba balle tace shine, sam bata son wani na zuwa dauko mata yara dan a kan su bata yarda da kowa ba se kanta kawai. Ƙamshin sassanyan turaren sa shi ya shaida mata shima yana falon dan ko da ta gama gyara falon turaren wutan da ta ke sawa ya riga ya fara kama falon. Bata gama tunanin ta ba taji Ibty a jikin ta, durƙusa tayi ta rungume ta cike da ƙaunar ta, janye Ibty tayi daga jikin ta ta miƙe riƙe da hannun ta ta ƙarasa gaban Abu Aulad zaune kan kujera Ifty na kwance a jikin sa, sunkuyawa tayi tana taɓa wuyan yarinyar kafin ta sa hannu ta ɗago ta "Baby zazzaɓi ne ya dawo ko, sannu bari ayi wanka ko?". Ta faɗa tana neman daukar ta, riƙe yarinyar yayi yana kauda kan sa gefe saboda yadda gaba ɗaya ƙamshin mayukan dake gashin ta suka cika masa hanci dan sunkuyowar da tayi gashin har taɓa masa fuska yake. "Kashe ta zaki yi da zaki mata wanka da wannan zazzabin a jikin ta?". Dakatawa tayi daga daukar nata ta daga kai ta kalle shi, gashin ta da ya rufe mata fuska yasa ta tuna bako ɗankwali a kanta, baya tayi da sauri tare da yafa ɗankwalin a kanta cike da kunyar yaga gashin ta. "Ki canja musu kaya muje hospital". Daukan Ifty da ya kwantar kan kujera tayi yayinda Ibty tabi bayan su zuwa bedroom, Shima nashi bedroom din ya shiga dan yayi wanka ya kuma canja kaya. Falo ta zaunar dasu itama ta zauna bayan ta yafa mayafin da ya hau da kayan, hannun ta riƙe da karamar purse kalan mayafi da takalmin da tasa, sanye da farin yadi kal dashi ya fito dan har ana ganin vest ɗin da yasa sanya a ciki, kansa na sanye da farar hula itama kar da ita ta zauna tayi matukar kyau a kansa yayinda kwantacciyar sumar sa ta fito ta baya se sheki take, takalmin ƙafar s fari ne dam gaba ɗaya shigar farare yayi. Sosai yayi wa salma kyau a idanu da har seda ta ɗago ta shiga kallon sa batare da ta sani ba, ganin babu shi a wajen yasa ta dawo hankalin ta ashe tuni ya fice ɗauke da Ifty a hannun sa, kama hannun ibtisam tayi wadda ke shirye cikin doguwar riga yar kanti pink color ita da yar uwar ta, kanta kuwa bakin scarf ne haka ma takalmin ta baƙi ne, rufe kofar gidan nasu tayi sannan suka bi bayan sa, gaban wata Black din mota dake ƙyalli ta tadda shi yana buɗewa, zaman ta a gidan har ta gane motocin sa, motoci hudu dake ƙarƙashin wata bakar tempole duk nasa ne. Gaban wata motar ta buɗe ta shiga tare da fita Ibty akan cinyar ta kamar yadda taga yayi wa Ifty, a hankali ya tada motar ya fita daga gidan. Slowly yake tafiya kan titin kamarw wanda ba shi da lafiya, ita dai kan ta na window tana kallon hanya dan ko so daya bata kalle shi ba tun da suka shiga motar. Gaban NOOROL HAQ special hospital ya ƙarasa yayinda masu gadi suka buɗe masa gate ya shige, parking yayi tare da bude motar ya fita dauke da iftihal itama ta fita tare da riƙe hannun Ibty dan Allah ya gani ita kam ta gaji da dauke ɗauke nan, yaran tubarkallah gasu da ƙiba daidai gwargwado ai dole ta gaji. Jerawa suka yi har ciki yayinda jama'ar dake kai kawo a farfajiyar hospital din suke bin su da kallo cike da sha'awa da burgewa, a yadda suke din they make a perfect family, a very perfect ma kuwa. Gaban office din da ta ga san sa Dr. Habeeb ya tsaya tare da knocking duk da cewa akwai mutane kaɗan da suka samu zaune. Kofar office din ce ta buɗe wata nutse ta fita tare da maida ƙofar ta rufe tana faɗa musu doctor Yana tare da patient, Salma ce kawai ta amsa mata dan shikam wayar sa ya fidda ya kira Dr habeeb ɗin, sam baya son jira a rayuwar sa shi yasa shima baya bari a jira shi, sedai wanda su ka yadda suyi masa hakuri dan shikam baze iya bin layi ba. Da Fara'a Dr habeeb ya ɗau wayar yana masa kirari kamar yadda ya saba wanda ke cike da tsokana kasancewar sa abokin karatun sa tun na primary, be biye masa ba ya sanar dashi gashi a bakin office din sa ya kawo patient, jin haka yasa Dr habeeb kashe wayar ya tashi ya buɗe musu kofar da kan sa tare da basu hanya suka shiga. Kan sofa suka zauna shikuma ya ƙarasa sallamar patient din gaban sa kafin ya maida attention din sa kan su Abu Aulad "A.A Gamji kunyi wuyar gani". "Ba wani wuya habeeb B kune dai bakwa neman mutane". "Aikuwa ba zaka ce haka ba dan ko last haɗuwar mu Ni na shige wajen ka a Company kaga kuwa na fika zumunci". "Kasan ayyukan mu ga kuma jama'a shiyasa ba ma samun wani lokacin hutu". "Hakane kam, Allah dai ya shige mana gaba, kaga hankali na ya dauku gare ka ko gaisawa bamu yi da Madam ba, Madam Barka da safiya". "Ina kwana, ya ayyuka". "Lafiya lau alhamdulillah, Gamji waye patient din anan?". Dr habeeb ya faɗa yana kallon Ibty da ta gaishe shi ya amsa cike da murmushi, ba kaɗan ba babyn ta burge shi, gata kyakkyawa ga kuma adon da aka yi mata. "Ga ta nan, tun jiya take fama da zazzabi, ta bata magana ya sauka amma ya dawo". "Ayya sannu baby, twins ne amma ko". "Eh". Abu Aulad ya bashi amsa lokacin da yake miƙa masa Ifty, karɓar ta Dr yayi ya kwantar da ita kan wani gado dake office din ya shiga duba ta, yana gamawa ya maida wa Abu Aulad ita shi kuma ya shiga rubutu kan takarda dake gaban shi, intercom din dake kan table ɗin sa yayi pressing se ga nurse ta bude kofa ta shigo. Takardar da yayi rubutun ya bata "Ki karbo min wannan magungunan yanzu". Amsa masa tayi tare da juya wa ta fita shikuma ya maida hankalin sa kan Abu Aulad "Malaria ce take damun ta duk da bata yi karfi ba dan haka zan mata injection ɗaya se Kuma drugs da zata dinga sha, a kiyaye barin ta cikin sauraye pls". "Insha Allah". Kawai Abdallah yace masa a ransa yana faɗin ba a gidan sa ta samo malaria ba tafiyayya ce daga gidan su dan shi kam gidan sa ko alamar abinda ya danganci sauro ma babu. Hira suka cigaba da yi ana tuna da duk da majorityn hirar Dr ke yi shidai ƙarkari yayi dariya se kuma jefi jefi yayi magana, abun ya bawa salma mamakin ganin Dr habeeb ne wani damu da hakan ba sema sabbin hira da yake masara alama shima yasan halin sa na miskilanci da rashin son magana shi yasa hakan be dada shi da ƙasa ba. Abin da salma bata sani ba shine yanzu ma Abu Aulad yayi sanyi akan da tun da yanzu ya kan yi responding magana ko kuma yayi doguwar magna abinda da sam ba yayi kenan, a da magana ma da kyar yake yi, hira kuwa duk kalar wadda za'a yi masa amsar bata wuce uhm, uhmuhm, eh da kuma a'a. Da yawa daga cikin malaman su da wasu daliban kallon kurma suke masa saboda basu taɓa ganin sanda yayi magana ba, shiyasa sam shi duk wajen da hayaniya take baya son ta dan nan da nan take haddasa masa ciwon kai. Irin ƙiriniya da rashin jin nan na yara kuwa sam shi Allah be ɗora masa ba, ta wani bangaren in ya kalli ibtisam se yake ganin yarinyar kamar shi lokacin da yana yaro dan shima haka yake da kulafucin maman sa, ba ruwan sa da ƙiriniya da rashin ji, komai nasa a nutse yake yin sa, girma da shiga jama'a da ya zama dole saboda harkar sa ta kasuwanci yasa miskilancin nasa raguwa sosai amma fa a ganin sa dan ga salma ita a hakan ganin sa take wani miskili number one. Suna nan zaune nurse ɗin ta dawo da leda me ɗauke da tambarin hospital din ta ajiye wa Dr habeeb tare da fita bayan yayi mata godiya, allurar ya haɗa yayi wa Ifty da sam bata wani tsoron allura ba kamar Ibty ba da duk abinda ze taɓa fatar ta take adawa dashi. Sallama suka yi masa tare da godiya dan yaƙi karbar ko sisi hannun Abu Aulad ɗin yace ai ƴar sa ce shima dan haka ba se an biya ba dan ya kula da lafiyar yar sa. Har gurin da suka yi parking ya raka su sannan ya koma bayan yaga fitar su, ba ƙaramin girma da karamcin Dr habeeb Abu Aulad ya gani ba ya kuma ƙudure a ran shi insha Allah shima ze biya shi ta wata hanyar da duk ta kama. Yanzu ma a kafada ya dauki Ifty dan har ta mayi bacci saboda allurar da akayi mata da ta kashe mata jiki, tun daga nesa Hajiya Babba da Hajiya Ainah suka zuba musu ido kamar wnada zasu halaka su dashi, ba komai ne yasa hakan ba face baki ciki da takaicin ganin su a hakan da suka yi yayinda cikin ran su kowa da manufar hakan a ransa. Ita Hajiya bakin cikin ganin Abu Aulad a raye kuma cikin walwala da farin ciki hadi da jin daɗi shine bakin cikin ta, dan a yadda suke din nan ba wanda baze yi zaton wasu shahararrun masoya bane su wanda suka dade da nitse wa tare da yin ninkaya a kogin kaunar juna, yadda suke jero se ya bawa kowane me kyakkyawar zuciya sha'awa da burgewa dan sun matukar haɗuwa daga iyayen har ƴaƴan. Ita kuwa Hajiya Ainah bakomai ne bakin cikin taba illa ganin Abu Aulad da wata macen ba yar ta shuraiha ba cikin jin daɗi da soyayya gami da ƙauna, a yadda idanun ta ke mata gizo har dariya da magana taga Abu Aulad ɗin nayi wa matar tasa da a wajen ta yanzu bata da makiyya sama da ita haka kuma tana jin ta kowace hanya se ta kawar da ita daga rayuwar gidan Abu Aulad ta yadda yar ga zata sakata ta wala tayi yadda ta ga dama batare da samun wani tsaiko ba. Abinda Hajiya Babba bata sani ba shine manufar auren Abu Aulad dake ranta wanda ta fallasawa aminiyar da bata da kamar ta a duk fadin duniya wato Hajiya Ainah babar shuraiha ba ita a ranta ba, itama tana da nata manufar na daban da ya sa take son hadin auren haka itama shuraiha kamar yadda suke da nasu tsari da burikan to itama tana da nata wanda ita kam ba komai bane face son ta rayu da Abdallah da take matsanancin so da kishi. Ita kam Hajiya Ainah babban burin ta be wuce ace yau ita ke da wannan tulin uban dukiyar da Abu Aulad ya mallaka ba, ta sani ba fa hanyar da hakan se faru se dole ta haɗuwar jini, hakan ne kawai ze legally bata damar mallakar tarin kadarorin da su kam basu san adadin shi ba maybe ko shi me su ya sani. Burin ta shuraiha ta aure shi ta haifa masa da, daga lokacin da ta haifi namiji ita kuma zata san yadda ta yi tasa aka kawar dashi daga doron duniyar, ana zuwa wannan gabar kuma komai ze zama mallakin yar ta da jikan ta ne, in kuwa hakan ya faru ta tabbata kamar ita ta mallaki dukiyar ne shikenan ita kam burin ta na duniya ya gama ciki. Lumshe ido Hajiya Ainah tayi lokacin da ta kai ƙarshen tunanin ta tare da hangowa a idanun ta har ma komai ya faru, zungurin ta da Hajiya Babba tayi yasa ta buɗe ido, suna yin four eyes tatu saurin daidaita yanayin ta da bata so haifar ta gane akwai wani kulli a ranta yanzu, gwara zuwa gaba komai se farau ya dade be faru ba in har yar ta ta shiga gidan Abu Aulad....................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel:                      Paid page 019 _________________________📖 "Babban bakin ciki na shine ganin wannan takadirin yaron cikin farin ciki da walwala dan haka ki dada nanatawa shuraiha karatu na, itace babban makami na a wannan yakin duk da ba da ita kadai na dogara ba, dan haka ta kasance cikin shiri, jibi zata tare a dakin ta kamar yadda nayi miki bayani dan haka ta shirya dan bana san nawa ko nauyin jiki, da zafi zafi nake bukatar faruwar komai domin idanu da zuciya ta ba za su jure ganin sa cikin walwala ba, yanzu haka ji nake kamar na dora hannu aka nayi ta kurma ihu koo naji sauƙin zafin da ke addabar kirji na". "Kar ki samu damuwa domin ina tabbatar miki za kiga aiki da cikawa har fiye da yadda kike zato domin ni da shuraiha a shirye muke tsaf dan ganin komai ya tafi yadda aka tsara sedai kin san dole baze saki jiki da ita tun farkon nan ba kasancewar ta fito ne daga ɓangaren ki, amma da sannu komai zai auku yadda aka tsara ko ba komai ai ribar tamu ce duka ko, ban da haka kuma ya zama dole mu shiga tsakanin sa da wannan tsinanniyar matar tasa me ido irin na aljanu, wannan shine mataki na farko da ya kamata mu fara ɗauka, in mukayi haka kinga mun ci ribar wanzar da damuwa da bakin ciki a rayuwar sa daga nan se mu san ta yadda zamu saka rashin yarda a tsakanin su, hakan na samu wa raba su baze mana wahala ba kinga se ta tattara ƴaƴan ta ta ƙara gaba ta bamu waje daga nan kuma se babban aiki in da zamu kawar dashi gaba ɗaya ta ruwan sanyi". "In ma yaki rabuwa da ita ban da mu da a kashe ta ba kamar yadda za'a kashe shi, ita ta siyowa kan ta saboda shegen kwadayin abun duniya wanda na tabbata sabida shi ta aure shi". "Duk yadda kika ce haka za'a yi Hajiya, Ni Bari in ƙarasa in duba masu gyaran jikin da na tura in suna aikin su yadda ya kamata". Da sauri Hajiya Babba ta katsewa Hajiya Ainah numfashi "Ban gane masu gyaran jiki ba, ke da na cewa bana so komai na auratayya a shiga tsakanin su me kuma ya kawo batun gyaran jiki, ko kuwa kin manta da batun kareem da yake mugun son shuraiha ne?". Cikin iya kissa da kwarewa wajen tsara tuggu da makirci hajja Ainah ta dubi Hajiya Babba "Da dina dake gaggawa da hanzari, ta ina zan manta da maganar dan albarka da nake fatan ya zama sirikina na har abada, ina sane da batun sa, gyaran jiki kuwa ba na komai bane illa jan hankali, a yadda yake da wannan tsaleliyar matar dole se mun samu abinda ze ja hankalin sa ga shuraiha wanda ta hakane yarda da aminci ze kullu tsakanin su yayi da tuni na saka an yi masa aikin da baze iya zama namiji a gaban shuraiha ba, kinga ko daga nan ya gwada yaga ya kasa ai matar sa ze zarga ko, yayin da cikin kissa ita kuma raiha zata dinga kwatanta masa ai matar sa ce tayi masa abun da baze iya kasancewa da ita ba saboda kishi, daganan mun yi nasarar dasa zargin ta a ransa se ragowar abubuwa su biyo baya". Ajiyar zuciyar samun relief hajiya Babba ta saki ta a yake haƙora "Daɗin yin magana dake kenan, shi yasa har yanzu na kasa samun ta biyun ki, yanzu kam na gane na kuma fahimci komai na ciki tsarin se fatan samun Nasara". Haka Hajiya Babba suka rabu da hajja Ainah bayan ta sake jaddada mata nasara tasu ce yayinda ciki ranta kuwa dariya take yiwa hajiya ganin yadda ta yarda da ita ta bata dukkan wani aminci wanda sedai tayi hakuri itama tana sowa kanta abinda Hajiyar ke hange wato dukiyar Abdallah. A can sashen su salma kuwa har bedroom din su Abu Aulad ya Kai Ifty, tun da ya bude dakin daddaɗan ƙamshin turaren wutan da ya haɗe da ƙamshin kayan da salma ke amfani ya bada wani kalan ƙamshi me ɗauke da sinadaran kwantar da hankali da sanya nutsuwa ga duk ruhin da yayi nasarar shaƙar sa. A hankali ya kwantar da Ifty kamar wata kwai kana ya nemi drower jikin gado ya zauna tare da bin ɗakin da kallo, komai a nutse a kuma gyare a wajen da ya kamata, babu shirgi ko daya balle kuma datti a ɗakin, ajiyar zuciya ya sauke tare da yin luuu da idanun sa kamar ze rufe se kuma ya buɗe ya sauke cikin wardrobe ɗin dake buɗe, kayayyaki ne kala kala ninnike a jere tsaf tsaf kamar ba'a taba su ba tun da aka jera, Allah ya sani shi mutum ne me matuƙar son tsafta a rayuwarsa shi yasa baya shiri da kazami ko kazan ta, abu kaɗan ke iya tayar masa da hankali da zuciya shiyasa gaba ɗaya baya ta'ammali da mutumin da be yarda da tsaftar shi ba. Maida duban sa kan Ifty yayi dake bacci numfashin ta na fita a hankali alamun zazzabin ya sauka ba kamar ɗazu da take numfarfashi ba. Ƙure fuskar ta yayi da kallo yana jin wani yanayi dangane da ita a ransa, shi ɗin mutum ne me matuƙar son yara shi yasa ma tun yana yaro abokai da yan uwa suka sa masa Abu Aulad se gashi sunan ya bishi har girma, duk miskilancin sa a gaban yara zama yake kamar wani aku dan biye musu yake su yi ta shirme, son yaran sa ne ma yasa duk irin dukan da Hajiya take masa baya fashin shiga sashen ta lokacin da ta haifi Nadiya, haka ze dauke ta a ɓoye batare da Hajiya ta sani ba, in kuwa ta gani ranƙwashi mari da dundu ne se yasha ranar amma ba hakan ze Hana ya koma anjima ba. Akayi na Nadiya aka gama aka zo lokacin haihuwar Abdulkarim, tsananin so da kaunar da ya nunawa kareem ba kaɗan bace hakan yasa yaron ya taso da so da kaunar sa dan lokacin ya zama saurayi Yana junior school lokacin, duk wani kuɗin break ɗin sa akan kareem da kayan wasan sa yake ƙarar dasu, komai ya gani na kareem ne, ci banza ci wofi haka ze kashe masa su gaba ɗaya, tun Ummu na masa fadan ya dinga siyan abinci a school har ta haƙura take masa abinci ya tafi dashi dan komai yawa komai kankantar kuɗin da za'a bashi ba fa ze kashe ba se ya dawo tare da kareem su kashe. Tsananin shaƙuwar dake tsakanin su ne yasa Hajiya shiga da fita har se da ta raba su kafin hankalin ta ya kwanta dan tace muddin tana raye ba yayan ta ba dan miji, sam sam bata yarda ba ba kuma zata yarda ba. Dole ba dan yaso ba Abdallah ya hakura da kareem saboda yadda yaron ya ƙware a rashin kunya tashi daya, ban da kuma janye masa da yayi, duk yadda yakai ga kulafucin sa seda ya hakura dan ko hanyar da yabi kareem baya son bi. Yayi addu'a har so ba adadi kan Allah ya bawa Ummun sa ciki itama ta haifa amsa qani sedai iya shi ɗin Allah ya rubuta zata haifa shiyasa har ta koma ga mahaliccin ta ko bari bata sake yi ba bayan shi. A hankali ya lumshe idanun sa tare da kai hannu kan kyakkyawar sumar iftihal dake gyare ya shiga shafawa cike da matsananciyar ƙauna, ba wai irin gamagarin kauna da yake ji kan Kowane yaro ba a'a, wannan gangariya ce ta daban da take yawo cikin jinin sa tana zagaye dukkan jikin sa. Da kyar ya haɗiye wani irin ƙullutu me matuƙar ɗaci da ya tsaya masa a makogaron sa, wasu shekaru can baya da suka shuɗe na dawowa cikin kwalkwalwar sa daki daki kamar a lokacin komai ke faruwa, sake runtse idanun nasa yayi da matukar ƙarfi yana hango su kwance cikin jini, kowanne lullube da farin kyalle, wani irin dum kan sa yayi masa da ya sashi sanya hannayen sa biyu ya dafe kan dan ji yayi kamar ze fado. Bisa tilas ya buɗe idanun sa ko ya samu ya dena ganin abinda ke barazana ga rayuwar sa, fararen idanun sa sun kada sun yi jajir saboda tashin hankali, sake kallon iftihal yayi amma a maimakon ya ganta, su ya sake gani hakan yasa aya mike ya fita daga ɗakin har lokacin yana dafe da kan sa. Dakatawa tayi daga shirin kai tuwon bakin ta ta zuba masa ido cike da mamakin yanayin da ta ga ya fito dashi, me kuma ya same shi?, Ta tambayi kanta sedai bata da amsar hakan. Tana ji tana gani ya shige ɗakin sa tare da maida ƙofar ya rufe da karfi dan har seda ta runtse ido haka ma Ibty, kwata kwata se taji abincin ya fita a ranta saboda damuwar yanayin sa, sosai taji ta damu da halin da yake ciki ba dan komai ba se dan irin so da kauna hadi da kulawar da yake nuna wa ƴaƴan ta, bata damu da yadda baya ko kallon ta ba balle ya damu da ita, iya kaunar sa kan yan biyu ya wadace ta ya kuma isa dalilin da zata damu da damuwar sa. "Allah ka yaye masa ko me ke damun sa". Ta samu kan ta da yi masa addu'a, haka ta cigaba da bawa Ibty abincin har ta ƙoshi batare da ta kuma ci ba dan ko da tayi attempting hakan kasawa tayi dan se taji gaba ɗaya daddaɗan dandanon abincin ya juya ya koma tsananin daci kan harshen ta , ta haɗiye ma kasawa tayi se tissue ta ɗauka ta tofa a ciki ta nannaɗe. Haka taja hannun Ibty zuwa bedroom din inda suka iske har lokacin bacci Ifty ke yi, kaya ta canja wa ibtisam zuwa na bacci masu ɗan kauri dan kiran sallar magrib ake yi lokacin haka ma iftihal ta canja mata, alwala ta ɗaura tayi sallah kana ta zauna gefen iftihal tana kallon fuskar ta yadda ta rame daga jiya zuwa yau. Bata san yaushe bane se kawai tsintar kan ta tayi da shiga tunanin abinda yasa mood din sa ya canja alhalin har ya shiga kwantar da Ifty idanun sa tar suke farare tas dasu babu ko alamun ɓacin rai se gashi ya fito ido yayi masa jajir gashi kuma dafe da kai wanda ga dukkan alamu ciwo yake masa. ........."Seda aka yi masa ƙarin ruwa leda biyu tare da allurar bacci dan rashin hutu da damuwa ne suka haddasa masa ciwon kan, likitan yace a dena barin shi da yunwa haka kuma ya rage sa damuwa a ran shi da kuma yawan tunani".......... Maganganun da Haisam ya faɗa mata suka dawo mata kamar bitar karatu, kenan yana da damuwa aransa?, Amma wace irin damuwa ce wannan da take haddasa masa shiga wani hali irin haka in ya tuna?!. A nata hasashen da kuma tunanin babu wanda ya kai ta damuwa sedai tana kokarin ɓoye hakan, damuwar yadda ta rasa iyaye biyu a shekarun rashi wayo, damuwar rashin dangin da suka damu da ita da rayuwar ta se kuma damuwar yadda rayuwar ƴaƴan ta za ta kasance a nan gaba in suka bukaci sanin asalin mahaifin su ko kuma suka gano ba Abu Aulad ne baban su ba, ita kuwa in haka ta faru yaya za ta yi, me zata ce musu?, Wannan sune fargabar ta da damuwar ta a ko yaushe sedai tana kokarin ɓoyewa da yin rayuwa daidai gwargwado ko dan walwalar ya'yan ta Ashe za'a iya samun wanda ya fita damuwa ko kuwa dai tsabar ragwantan zuciya ne yasa abin da be kai ya kawo ba yake sa shi cikin wani hali?. ..'aa salma, be kamata ki yanke hukunci batare da kin san me ke damun sa ba, watakil damuwar sa tafi taki, watakila ta ninka taki ninkin banin kin dan ko kema in Baki buɗe baki kin faɗa ba babu wanda ze San kina da wata damuwa, to kowa ma hakane, never judge a book by its cover'.. Abinda wani bangare na zuciyar ta ya tunatar da ita yasa ata sauke ajiyar zuciya tana yarda da hakan da har se da ta jijjiga kai a fili, tabbas haka ne, kai dai kawai ka kalli dan adam a yadda ka ga zahiri sa yake rayuwa, wani in da ze buɗe maka zuciyar sa kaga tarin kunci, damuwa da tashin hankalin da yake ciki yake rayuwa a zuciyar sa se kaji naka ba komai bane, se kaji kai baka ma da sauran damuwa, se kaji kai be kamata kayi kuka ba sam, se kaji kai ɗin a aljanna kake. Ba wai kuɗi ne jin dadi da kwanciyar hankali ba, a'a su ɗin wani sashe ne na hakan, babban ginshikin jin dadi shine kwanciyar hankali, duk rayuwar da ta kasance ba kwanciyar hankali hadi da nutsuwar ruhi to tabbas babu jin dadi a cikin wannan rayuwar. Masu kuɗi da yawa na rayuwa cikin daular kudi, komai na buƙatar rayuwa akwai shi a wadace amma su ɗin basa cikin jin daɗi, meye dalilin hakan?, Rashin kwanciyar hankali! Misalin kamar rayuwa ce ada lokacin iyaye da kakannin mu da kuma rayuwa a yanzu lokacin mu. Ada babu yawaitar mahaukatan kudi amma akwai kwanciyar hankali saboda wadatar zuci da rashi tsadar rayuwa amma a yanzu da kudin ya yawaita se kuma aka rasa cin kuɗin cikin daɗin rai saboda rashin kwanciyar hankali. Ada gidan mutane kan kwana a bude, mutane kan kwana a waje batare da tsoron komai ba, amma a yanzu gida bayan an sa masa kofar da mutane da yawa ke gadi se an kara da su security camera, security wire da ragowar ababen tsaro amma na cikin gidan hankalin sa be kwanta ba, ko yaya yaji ƙarar wani abu me amo se ya firgice cikin tsoron hari ne aka kawo ko ana neman farmakar sa ne. Talakawa dake ganin su basu dashi so da yawa kuma sukan fi masu kudin kwanciyar hankali, talaka ya bar gida a bude yayi bacci batare da wata fargaba ba, talaka yayi yawo ko ina batare da wani me tsaro ko kula dashi ba hankali kwance, amma me kuɗi fa?!. Jin dadin rayuwa ya ta'allaka ne kan ginshikai uku 1- kwanciyar hankali 2- wadatar zuci 3- kuɗi Wannan sune ginshikan jin dadi sedai kuma a cikin nasu kuma muhimmin shine kwanciyar hankali, Allah ka wanzar da kwanciyar hankali a zukatan mu, unguwannin mu, garuruwan mu, kasashen mu da ma duniya baki daya. A hankali salma ta sauke ajiyar zuciya lokacin da ta zo nan a tunanin ta tare da cire tagumin ta wanda bata san sanda tayi ba..................... ✍🏻. Ouummey 📚✍🏻[12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 021 [ 12/9/2022 12:40 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                                            Paid page 021 _________________________📖 Da kallon banza ta raka bayan Nuriyya tare da jan tsaki kana ta tashi ta sakawa kofar key dan bata bukatar wata hayaniya kuma bayan wadda tayi yanzu su kuma ta fahimci ahalin gidan ba abinda suka fi kwarewa a kai kamar neman rigima da faɗa. Kan kujerar ta koma ta zauna tana sake bitar kalaman Nuriyya daki daki, wani tsakin ta kara saki ganin wai duk wannan hakilon da zubda mutuncin duka akan wancan miskilin take yi, mutumin da ita banda kyau da iya daukar wanka bata ga abinda ze sa ayi ta wannan haukar akan shi ba da sunan so. Tasan tayi karya in tace bashi da abinda za'a so shi domin shi dan tasan shi ɗin ko acikin kyawawan maza nasa kyan daban ne, gashi se kyan ya haɗu da iya ado da gayu, basu kadai ba ko ita in har ze shiryo ya fito se tayi dagaske take iya hana kan ta ƙure shi da ido saboda yadda adon ke zauna wa a kyakkyawan jikin sa, mutumin yasan kala haka yasan takan kaya shi yasa ko a can office mata ke hauka a kan sa dan ma Company ɗin na da strict orders and rules da ta tabbata har dambe se an dinga yi a kashi. To amma banda wannan kyan ai bai da wani abu da ze sa a so shi, shegen miskilancin za'a so ko kuwa wulaƙanci, Shariya da jan aji, ita in Yana wani abun ma har mamaki yake bata dan ko mace ba kowacce ce zata iya jan ajin da yake yi ba. Kofar shigowa da take fuskanta ta makawa harara saboda tuno wulaƙancin da yayi mata, ƙwafa tayi tana me jin haushin Nuriyya da ta zo ta katse mata baccin ta kan wani can namiji da baya gaban ta kamar yadda tayi imanin shima bata gaban sa. Da kyar ta samu ta koma baccin ta wanda bata tashi ba seda akayi sallar Asr dan Azahar kam tun sha biyu da rabi tayi abin ta. Taji daɗin baccin ba kaɗan ba dan ta daɗe bata yi me tsawo kamar sa ba, wanka ta sake ta saka yar shimi da wando ganin ita kadai ce a gidan, yau kam pounded yam take son ci shiyasa ta dauri niyyar yi, nan da nan ta hau ferayar doya ta ɗora kan gas kana ta koma hada miyar da take son ci da ita,  jar miya zata mata saboda Ifty da bata da lafiya ba zata yi taushe ba kar cikin ta ya saki. Cikin electric pounder ta nike doyar tayi matukar laushi kana ta malmale su a leda ta zuba a warmer, wasa wasa aikin da ta raina se da ya kai ta har magrib dan ana kiran sallar take kwashe farfesun kayan cikin da tayi. A gurguje ta gyara kitchen din tare da jera a dining, wanka ta sake ta saka milk din Arabian gown tare da daure kan ta dashi, powder da lipstick da kwallon ta saka kana ta tashi tayi sallah. Turaren ta me sanyin ƙamshi ta fesa a jikin ta sannan ta fita takarawa falon turaren wuta dan har lokacin basu dawo ba, nan tayi zaune tare da kunna Tv ta Kai zee Aflam daidai suna haska tsohon Film ɗin jarumi Amitabh bachan me suna ganga jamuna saraswati, cikin farin ciki ta gyara zama tare da maida hankalin ta kan Film ɗin dan tun da ta fara kallon Tv a ɗakin hajiya da finafinan India ta fara kuma ba ƙaramin burge ta suke ba most especially jaruman Bollywood. Seda aka yi sallar isha suka dawo lokacin har ta yi tata ta koma gaban Tv dan film din be Kare ba, kallo ɗaya tayi musu gaba ɗayan su ta ɗauke kai dan taji haushin yadda ya kwashe yaran su kayi tafiyar su suka bar ta ita kadai a gida kamar wata sabuwar mayya. Ibty ce ta fara zame hannun ta daga nashi ta tafi ta faɗa kan ta tare da rungume ta tana faɗa mata sun je unguwa, ko kallon ta kin yi salma tayi, yaga abinda tayi amma ko kallon ta be yi ba maimakon zaman da yai niyyar yi se ya hau kiran Ibty dan dama ita Ifty bata sake shi ba. "Come on babyn daddy zo muje ayi wanka". Ba musu itama Ibtyn ta tashi ta koma gare shi lamarin da ya tilasta wa salma buɗe baki tabi su da kallon mamaki batare da ta san lokacin da tayi hakan ba. Suna shiga dakin ya kalli yaran tare da ajiye ledan hannun sa yana sakin smirk ganin yadda ta saki baki tana kallon su kamar wata doluwa, to an faɗa mata shi ɗin na wasa ne, ai shi da yara sedai in be so su maƙale Masa ba amma duk kiwar yaro in dai yazo kan shi dole ne ma ya yarda dashi, ko an faɗa mata a banza yaci sunan Abu Aulad ɗin. Da kan sa ya tube su Ifty yayi musu wanka kowacce ya daura mata kananan towels din sa na goge kai, cream din sa ya shafa musu kana ya bar su cikin dakin ya fita. Tana nan zaune inda suka bar ta sedai wannan karon kam tagumi ta buga hannu bibbiyu ta na bin kofar dakin nasa da kallo, yana fitowa tayi zumbur ta miƙe sedai ganin babu twins bayan sa yasa ta koma ta zauna, yanzu ma bece mata komai ba ya shiga bedroom din ta ya ɗebo musu night wears ya fito ya koma ɗakin sa. Tun daga nan bata kuma jin ko motsin su ba duk su ukun, shi kuwa a can daki haka ya saka musu kayan sannan ya zauna kan bed tare da kwantar dasu a jikin sa ya buɗe ledar da ya shigo da ita ya ɗauko wani bedtime story book ya Fara karanta musu, sannu a hankali tun suna saurara har bacci ya ɗauke su. Nan kan gadon ya gyara musu kwanciya kana shima ya shiga wanka ya canja kaya zuwa na bacci, seda yayi musu addu'a gaba ɗaya har shi sannan ya kwanta bayan ya kashe fitila. Hajiya salma kuwa ana can falo ana baza idon ganin ta inda twins zasu fito, wasa wasa tun tana duban agogo har ta dena ta zubawa kofar dakin ido, bata ankara ba har sha daya tana nan zaune kafin jiki a saluɓe ta tashi zuwa bedroom dan ta gama sadakar da can za su kwana. Kwata kwata kasa bacci tayi dan tun da ƴaƴan ta suka zo hannun ta har zuwa jiya basu taɓa raba wajen kwanciya ba se yau, gaba ɗaya se taji gadon yayi mata fadi ita kadai, tayi ta juye juye cikin rashin jin dadi kafin dab da asuba barawon ya lallabo ya sace ta. Ko da asuba da ta farka tayi tsammanin zata gan su kwance kusa da ita sedai wayam ba kowa a dakin se ita kaɗai, alwala tayi ta gabatar da sallah sannan ta fita nema musu abinda zasu yi breakfast da kuma wanda zasu tafi dashi school dan tayi zuciya itama ba zata kuma neman su ba tun da sun samu bare sun manta da ita da take dolen su shiyasa ko da ta fito falo bata kalli ko inda sashen dakin sa yake ba ta wuce kitchen. Tana cikin juye ruwan tea cikin flask ya dawo daga masallaci, ta ji shigar shi falo amma se ta share ta cigaba da aikin ta duk da tana so tace masa su fito ta shirya su zuwa school se kuma ta yi shiru ta zuba musu ido taga in school ɗin ma shi ze musu shiri. Aikin ta take inda ta bada dukkan hankalin ta shiyasa bata ji shigowar sa ba se karan buɗe fridge da taji, a firgice ta saki stirrer din hannun ta da take kwabin cake da za suje school da, gaba ɗaya ta maƙale jikin bangon kitchen din idanun ta a runtse bata ko ƙwaƙƙwaran motsi, kallo ɗaya ya mata ya ɗauke kai tare da daukan fresh yo din da ya kawo shi kana ya sa kai ya fice, seda ya kai bakin ƙofar daze koma falo kana cikin tattausar Muryar sa kamar ko yaushe yayi magana "Ba zasu je school ba yau, se Angel ta samu sauƙi". Yana gama isar da sakon sa ya fice, da sauri ta buɗe ido jin Muryar sa sedai kama aljani ta neme shi ta rasa, shiru tayi cikin tantamar anya shine ko ba shi bane, se kuma sassanyan ƙamshin sa da ya mamaye ilahirin kitchen din ya tabbatar mata da shi ne. Hararar kofar tayi kafin cikin siririyar Muryar ta ta shiga mimicking abinda ya fada "Ba zasu school ba yau, se Angel ta samu sauƙi". Mtsww se kuma ta ja tsaki, ƙasa ƙasa ta shiga gunguni, wani wai Angel Kamar yar sa, haka kawai a ga mutum da ƴaƴan sa ba'a san taya ya haife su ko ya same su ba a ringa neman yi masa fin karfi. Zaro ido tayi lokacin da ya shigo ya aje cup din tangaran din da yayi amfani wajen shan fresh milk din, 'innalillahi, Allah dai yasa be ji me na faɗa ba'. Ta faɗa a ranta, a fili kuwa se ta ringa satar kallon sa kasa ƙasa dan san ganin alamun ya ji ta ko be ji ta ba. ''huh''. Ta sauke ajiyar zuciya lokacin da ya fita daga kitchen din, cikin sanda take takawa har ta kai bakin ƙofar tayi maza ta rufe tare da saka lock sannan ta sakin wa kanta murmushi alamun tayi abin kirki. Girkin ta ta koma ta cigaba da yi tana yi tana kananan maganganu ita kadai ba kuma da kowa take ba se Abu Aulad, baƙin halin sa na miskilanci, wulaƙanci, disgi hadi da yankwana mutane duk se da ta faɗa tana sharhi akai har da kwaikwayon yadda yake yin komai. Se da ta gama abinta kuma sannan ta daga kai ta shiga bin kitchen din da kallo ido a waje, "Na shiga uku ni salamatu uwar biyu, Allah asa ba CCTV camera a Kitchen din nan". Tsaf ta gama ƙarewa kitchen din kallo amma bata ga komai ba, ajiyar zuciya ta sauke tana dafe ƙirji "Wai, Allah ya rufa min asiri ai da wannan me baƙin halin se yace ma wani abu in ya ji ina maganar sa bayan Ni haushi kawai ya bani, bari dai kiga na maida hankali na gama abinda zan yi". Kamar yadda ta faɗa kuwa hankalin ta maida ta ƙarasa baking cake din ta sannan ta fita da breakfast ta Kai dining, a gurguje ta je tayi wanka ta shirya cikin uniform din ta, tana tsaye gaban mirror se kuma tayi turus cikin tambayar kanta "To kuma ya zanyi da yaran nan tun da ba zasu school ba?". Ta dade tsaye cikin rashin mafita kafin kuma ta waina kyawawan golden brown eyes din ta tare da tura lips din ta gaba "Oho ma meye ruwana, ya tafi dasu ma duk inda ze Kai su tun da ya kwace su". Tana fadar haka ta ƙarasa gyara zaman blue ɗin abayar jikin ta, komai da take bukata seda ta zuba cikin handbag din ta sannan ta dauka ta fita falo. Dining ta same su sun baje suna breakfast batare da sun ko jira ta ba, haushi ya kara kume ta ganin ita da ta sha wahalar haɗawa ma ba zasu ko neme ta ba kamar wata baiwar su. A fusace ta ja kujerar ta zauna ta zuba abinda zata ci ta fara aikuwa cikin ta, ko da twins suka gaishe ta harara ta balla musu hakan yasa yaran sake matsawa jikin Abu Aulad, tuƙuƙin ɓacin rai kawai ranta ke yi mata shiyasa ko kallon sa bata yi ba bare ta gaishe shi. Shi ya riga ta gamawa dan haka ya miƙe tare da sa tissue ya goge bakin sa kana ya sunkuya ya sumbaci kuncin twins Suma suka masa sannan ya nufi ƙofar fita riƙe da briefcase din sa yana bading ɗin su tare da faɗa musu he loves them, da sauri cikin jin daɗi suka hada baki wajen replying din sa da "We love you too Daddy". Da sauri salma ta mike ganin yana shirin tafiya ya bar ta da yaran bayan sun gama cusa mata haushin su, aiko ba zata saɓu ba. "To ni ina zan kai yaran bayan kuma aiki zan je". Dan tsayawa yayi tare da juyowa "Ki zauna ki kula dasu, ba zaki koma aiki ba se sun koma school". Tun kafin ya rufe bakin sa ta bashi masa da "Ni dai wallahi a'a, ina ce ka kwace su ai se ka zauna dasu, ni dai aiki na zan je". Be sake juyowa ba ya cigaba da tafiyar sannan yana bata amsa a haka "I said it and it's final, ki kula dasu har su koma school". Tana ji tana gani haka ya fice ya bar ta da yaran, aikuwa harda hawayen ta kafin fuuu ta wuce ta koma bedroom ta Gama kukan ta sannan ta cire uniform din ta maida wardrobe tareda sauya kayan zaman gida. Bata koma falo ba se yaran ne da suka gama cin abincin suka biyo ta, da sauri ta ture Ibty dake neman shiga jikin ta tana hararar su, kwaɓe fuska suka yi dan basu taɓa ganin this side na momma din su ba, duk da tana faɗa in suka yi ba daidai ba amma haɗe rai irin haka basu taba ganin tayi ba. "We are sorry momma". Suka hada baki wajen faɗa kamar yadda suka saba duk in suka yi laifi, kai ko da ba su biyun suka yi ba in dai ɗaya tayi to ɗayar na taya ta bada haƙuri ne shiyasa yawancin kalmar su we ne ba I'm ba. Ɗauke kanta tayi gefe taƙi kallon su hakan yasa Ibty fara hawaye dan bata san taga momma din ta na fushi, itama Ifty ganin yar uwar ta na kuka se ta buɗe baki ta shiga taya ta da nata da ke da sauti, duk yadda taso da kar ta kula su kasawa tayi dan su ɗin sune rayuwar ta, farin cikin ta haka kuma walwala da jin dadin ta shiyasa take matuƙar adawa da dukkan abinda ze Bata musu rai balle ma har ya saka su kuka. Hannuwan su ta jawo ta rungume su a jikin ta haka suma kowacce tasa ka yan ƙananun hannayen su suka rungume ta, tsayi lokaci kafin ta cire su daga jikin ta ta zaunar dasu kan bed ta zauna a gaban su itama "Shine kuka yi tafiyar ku jiya ku da Daddy ku ka bar ni ko?". "We are sorry momma, daddy yace kin yi bacci kuma ba'a takurawa mommma in tana bacci shine muka tafi". Wato laifin ba nasu ba ne nasa ne, "Kuma baku kwana tare da momma ba kuka kwana wajen daddy". "Daddy yace kin yi aikin kin gaji mu bar ki ki huta". Lallai ma Daddyn nan, wato so yake ya rabata da ƴaƴan ta bayan be san wahalar da tasha akan su ba, aikuwa ba zata yarda ba......................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 020 [ 12/9/2022 12:40 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      Paid page 020 _________________________📖 Tana nan zaune har iftihal ta farka, abinci ta ba ta taci se kuma magunguna suka biyo baya. Alwalar sallar Isha tayi ta koma falo tare da praymat ɗin ta zauna jiran a kira Sallah, bakomai yasa tayi hakan ba se son ganin ze Fito sallar Isha din ko kuwa dan dai bata ji fitar sa Sallar magrib ba. Har aka idar da sallar bata ji ko motsin sa ba balle ya fito, haka ta tashi ta gabatar da nata ta koma ta zauna tunani na sake kawo Mata hari, dan hana hakan se kawai ta janyo wayar ta ta shiga karatun novel, Bata ankara da dare yayi ba se da fitsari ya matse ta, tana kuwa daga kai akan Designer wall clock din su ta sauke dake nuna karfe goma har da rabi. Bata kuma tsaya wa komai ba ta kashe wutar falon haka ma ta kitchen ta dau wayar ta ta koma bedroom, murmushi ta saki ganin yadda twins suka rungume juna sun zagaye bayan su da hannayen su. Gaban su ta dawo ta kwatanta tare da jawo su jikin ta ta kwanta tare da yi musu addu'a bayan ta kashe fitilar dakin, babu jimawa bacci ya ɗauke ta dan jin ƴaƴan ta rungume cikin jikin ta be bar wata damuwa wanzuwa a ranta ba balle har ta hana ta bacci. Ko da asuba yau be tashe ta ba, dama ba wai ta dogara da tashin nasa bane dan itama ta saba tashin, ranar nan ma gajiya ce taso sawa ta makara se kuma gashi ya tashe ta. Alwala tayi ta gabatar da nafilolin da ta saba sannan ta zauna karatun Alkur'ani kafin ayi kiran sallar biyu, alama ta saka kan ayar da ta tsaya kana ta rufe Kur'anin ta tashi tayi sallar asuba. Falo ta fita ta zauna kan sofa tana fuskantar dakin sa se kuma ta tashi ta koma bedroom tana fadawa kanta in har be fito zuwa lokacin da gari ya waye ba kawai zata bishi ɗakin ne taga yanayin da yake ciki. Baccin da ta ɗan koma be yi wani nisa ba ta farka saboda Ifty da ta tashe ta zata je toilet, Banda rashin kwarin jikin ta san ba abinda ze sa ta tashe ta dan tun kafin sukai haka take koya musu yin wasu abubuwan da kan su so in dai ba pupu ba bata ma sanin zasu shiga toilet. Kai ta tayi tayi fitsari sannan ta mata wanka da ruwa masu dumi kana ta sa tayi alwala suka fito, haka ma Ibty sannan ta shirya su cikin riga da wando masu kyau kala ɗaya, wandon pencil jeans se loose riga red color ta sa musu red ribbon jikin gashin su, hijabs ta saka musu suka yi sallah kana suka cire. Wanka tayi itama sedai ita ba riga da wando ta saka ba, pencil black skirt se red loose t shirts se ta saka hijab da ya kai mata har gwiwa, hannayen su ta riƙe suka fito falo kana cikin yar fargaba suka nufi ɗakin sa, knocking tayi har so biyu kafin ta murɗa handle din, take kuwa kofar ta buɗe dan be saka key ko lock ba, twins ta fara tura wa gaba kafin ta shiga daga bayan su kan ta a ƙasa, sallama suka yi gaba dayan su sedai shiru ba'a amsa musu ba, ɗagowa tayi a hankali a kuma sace dan ganin ko baya dakin ne se kuwa idanun ta suka faɗa cikin nasa, yana zaune kan bed ya zuba musu ido kawai yana kallo. Cikin gaggawa ta janye nata idon dan se taji kamar ana ɗaɗɗaure mata jiki da ta kalli idanun sa da har yanzu basu koma launin su na ainahi ba sedai sun rage jajir ɗin da suka yi, shi kam ido kawai ya zuba mata yana kallo cikin ran sa yana ayyana wane irin sakaci yayi da har yarinyar nan ke neman raina shi, raini mana tunda gashi har ta kai su ga ta fara shigo masa daki nan gaba kuma ai se kan bed din sa daga nan kuma Allah kaɗai yasan me zata so yi masa. Wani irin haɗe rai yayi wanda bata taɓa ganin haka daga gare shi ba kira sunan ta karo na farko tun sanin ta da shi dan hatta a office baya kiran ta da sunan ta sedai miss. "Salma". Da gaggawa ta ɗago tare da ƙure su da golden brown eyes din ta dake wani maiƙo maiƙo kamar wadda ke neman tara hawaye sedai ba hawayen ba ne a haka idanun ta suke, wannan karon shi yayi azamar janye nasa kafin ita ta sunkuyar da kai, seda ya kausasa har she da Muryar sa kafin ya fara magana "Ko da wasa kar in Kuma ji balle gani, wannan ya zamo na farko kuma na karshe da zaki shigo min bedroom, bana buƙatar sake ganin ko da alamun ki ne a daki na balle ke da kan ki, kome kike bukata ko son sanar da ni zaki iya jira har in Fito". Ƙasa ma tunanin komai salma tayi cikin ran ta, me wannan mutumin yake nufi da maganganun sa, ko me take buƙata ta jira har ya fito, to wa ya faɗa masa ita akwai abinda tazo nema ko bukata a wajen sa?, Ita ɗin ba me roko bace balle yace kudi ko wani abu tazo tambayar sa, ita ba cusa kanta take wajen sa ba balle ya nemi faɗa mata magana, dan haka cikin muryar dake nuna taji zafin kalaman sa batare da ta kalle shi ba tace "Ni ba abinda nazo nema ko bukata a wajen ka, na ga tun da ka shiga ne tun jiya da magrib baka fito ko yin Sallah ba shiyasa nazo duba ko lafiya dan sauke hakkin da Allah ya dora min, amma kayi haƙuri insha Allah ba zaka kuna gani na ko a bakin kofar dakin ba balle cikin sa". Tana gama faɗa ta fita daga ɗakin da sauri idanun ta na kawo ruwa, ita kam ta tsani wulaƙanci da disgi abinda shikuma ta lura ya fi kwarewa akai kenan dan haka daga yau zata nuna masa ita ɗin macece me daraja, in ya Saba mata na bin sa yake tunanin itama haka to tabbas yayi kuskure dan ita ɗin da darajar ta da ajin ta ba zata bari ya wulaƙanta ta ba. A fusace ta zauna kan gadon tana hararar bedsheet din dake shimfiɗar kamar shi yayi mata laifin kafin kuma ta tashi ta shiga ayyukan da ya kamata, se da ta gama breakfast ta jera kafin ta shiga ƙwalawa su Ibty kira tana hararar bakin kofar dakin nasa cikin ranta kuwa se gunguni take yi, yace kar ta kuma zuwa masa daki yanzu kuma ya wani riƙe mata yara a ciki, ai dai ya'yan ta ne ba na wani ba dan haka se suma ya bar mata abin ta. Cikin haka ya fito hannun sa riƙe da kowacce, yayi wanka har ya shata kaya zuwa three quarter da farar body hug na zaman gida, ya riga ya saba da zaman sa haka cikin sashen sa dan haka zuwan ta baze sa ya sauya komai ba dan shikam ba zata takura masa ba a kawai. Kan table ɗin ya zaunar da twins kana shima ya zauna, kamar ta share shi se kuma taga be kamata ba dan haka ta yi serving din su ta zauna ta cigaba da cin nata dan lokacin da suka fito har ta fara cin nata ganin sun ki fitowa. Yau kam su ukun suke ci tare, in ya bawa Ibty se ya bawa Ifty su ma se duk su bashi, gaba ɗaya se yaji zaman wajen ya ishe ta ganin yadda suka ware ta ita kadai uwa mayya, a ranta har haushin twins din duka take ji ganin yau har Ibty suka wani manta da ita. Bata tsaya sauraren su ba tana gamawa ta wucewar ta bedroom cikin ranta tana faɗin Allah ma dai yasa su ƴan biyun ya'yan ta ne ba nasa ba da ya tura mata haushi ai duk da yanzu ma ta shaka. Bata san fitar su ba se fitowa tayi ta tarar basa nan, duk yadda tace ba zata kuma zuwa kofar dakin sa ba kasawa tayi da taga har sha biyu bata ji motsin su ba, a hankali ta buɗe ƙofar tare da dan zura kan ta ciki sedai wayam ba kowa, har ta juya zata fita se kuma ta kuma kallon dakin, a gyare yake sedai ba tsaf ba, kamar ta gyara se kuma ta tuna gargaɗin wulaƙancin da yayi mata ɗazu dan haka taja tsaki tare da rufe masa ta koma falo. Wato dai dagaske yaran nan sun manta da ita tun da gashi har sun fita batare da sun sanar da ita ba, aikuwa zasu sani dan se ta zane su zasu dawo su same ta ne. Bacci ta kwanta abinta dan ta gama gyara komai tun da safe dan haka ba aikin da zata yi kuwa, abincin rana kuwa ba ma zata fara ba tunda masu ci ɗin ba sa nan, ita kuma bata jin yunwa bare ta dafa. Nan kan sofa tayi baccin ta cikin kwanciyar hankali batare da fargaba ko tunanin wani abu ba da har aka bude kofar aka shigo bata sani ba saboda kofofin sa ba irin masu muguwar karar nan bane. Tsaye Nuriyya tayi a kan ta tana bin ta da mugun kallo idanun ta cike da tsantsan kishi, ƙyashi hadi da hassada ganin yadda take baccin da kallo ɗaya zaka mata kasan hankalin ta a kwance yake ba ta tare da ko wace irin damuwa. Cikin fushin zuciyar da ya tuko ta ta ƙarasa tare da sa hannu ta finciko ta, hakan yasa ta fado kasan kujerar dan bacci take bata san meke faruwa ba balle ta kare kanta. Cikin baccin da yayi matukar mata daɗi taji an wani kwashe ta an watsar hakan yasa ata shiga ƙoƙarin buɗe idanun ta, bata gama dawowa hayyacin ta ba zafin buguwar da kanta yayi da carpet ya ratsa kwnayar ta da ya tilasta mata wartsakewa nan take. Ganin mace tsaye a gaban ta yasa ta miƙe da sauri tana bin Nuriyya da kallon Lafiya?, Ke kuma wace kafin bakin ta ya furta abinda ke ranta "Baiwar Allah lafiya zaki shigo min gida ba neman izini ki kuma zo ki min tsaye akai kamar kin bani ajiya ko naci miki bashi ban biya ba?". Tana sane ta fadi haka dan ta gane Nuriyya, itace suka tare ta ita da wata yarinya lokacin da ta dawo daga aiki, itace ta nemi zagin ta koma tace ta zage ta a fakaice da kalaman ga masu harshen damo dan haka ta sake ɗaure fuska kamar bata taɓa sanin kalmar dariya ba dan kar ma Nuriyyar ta kawo mata wani iskanci ko raini. "Baiwar Allah tana ƙauye, lafiya kuma to babu dan baki biyo hanyar lafiyar ba balle har ki tambaye ta, bashi kuwa ai base na faɗa ba kema kin san akwai shi kuma dalilin shi ya kawo ni har nan gurin, haɗe rai ko wani abu da zakiyi baze sa na fasa isar da sakona gare ki ba duk da na fahimci karamar ƙwaƙwalwa gare ki da har kika kasa fahimtar sako na tun a karon farko, well, ba damuwa zan sake maimaita miki amma fa for the last time dan in har kika bari na kuma zuwa sashen nan ba gargadi zan yi ba cika aiki zan yi". Kallon sama da ƙasa salma tayi mata kafin ta koma kujerar ta zauna abin ta "Allah ya baki lafiya". Abinda ta faɗa kenan wanda ya kular da Nuriyya ya kuma fusata ta to the core bata ma tsaya wani tunani ba ta daga hannun ta da nufin kashe fuskar salmar da mummunan marin da ze tafi da gani da jin ta yadda ko ance gaba ta sake mata irin wannan iskancin ba zata kuma ba. Sedai tuni Salman tayi zafin nama da azamar riƙe mata hannu batare da ko kusa da fuskar ta ya kai ba, kyakkyawan murmushin ta ta sake da yake ƙara bayyana tsantsar kyan da Allah ya bata ya ke kuma ƙara mata kwarjini, dayan hannun ta da baya rike da na Nuriyya ta daga ta kai daidai fuskar Nuriyyar ta shiga kada shi "Kar ki fara wasan da baki ko tanadi players ba a cikin sa, kar ki ɓallo ruwan da baki da abin tare shi balle sa ma masa matsuguni haka kar ki sake ki yi tunkari mayunwaci namijin zaƙin da ya daɗe a yunwace dan yin hakan tamkar wasa da rayuwar ki ne dan kin san in wannan zaƙin ya riƙe ki da iya faratan hannu da kafar sa tabbas sedai wata ba ke ba, to kamar wannan namijin zakin mijina yake komawa duk in akayi yunkurin taɓa ni, yi tunani ki auna meze yi in aka tabani in har se zama kamar wancan zakin saboda kawai anyi yunkuri. Ke ɗin shashasha ce da har yau dakikiyar kwakwalwar ki ta kasa baki cewa mijina baze taɓa auren ki ba domin baya cikin tsari da layin irin matan da yake so yake kuma bukatar rayuwa dasu, in ke me tunani ce se ki lissafa shekarar ku nawa cikin gida ɗaya amma be taɓa daga ido ya kalle ki da wata manufa ba, ke in ƙarƙare miki zance in za'a ɗorawa Abu Aulad wuka a maƙoshin ace ya siffan to ki sedai a kar shi, the sooner you realise the bitter truth the better for your life lady". Ta na gama faɗa ta wancakalar da hannun Nuriyya da jikin ta ya ɗauki ɓari da tsumar kalaman salma, bata taba tunanin yarinyar nada baki haka ba, a yadda ta ganta ranar da suka tare ta ta zata ko da an sa mata yarda a baki bazata ciza ba, yadda ta farfada mata maganganu batare da ta yanka ba ta zata haka take bata iya kare kanta, ashe lambo tayi, ashe lumbu lumbu tayi musu suke mata kallo kamar dan Zomo se gashi ta bayyana gare su a yar damisa. Tabbas ba zata bar ta ba, ba zata taɓa barin ta taci bulus ba, yanzu aka fara wasan kuma se ta tabbatar tasa ta lashe aman ta, badai ita Nuriyya ta faɗa wa wannan kalaman ba, to ai in tasan wata bata san wata ba. Tuna hakan yasa ta saki murmushi wa salma da har lokacin take tsaye gaban ta tana bin kowane move da canjin yanayin fuskar ta da kallo, hannu ta kai gaban fuskar salma ta yi das das dashi irin mu zuba mu gani.................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 022 [ 12/10/2022 10:44 AM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                        Paid page 022 _________________________📖 Bata kuma cewa komai kan Daddy ba suka cigaba da hirar su cikin kaunar juna kamar yadda suka saba, suna ta bata labarin Daddy ya Kai su zoo, Daddy ya Kai su park, Daddy ya siya musu icecream, Daddy ya siya musu chocolate and many more. Tun tana iya gane me suke fadar an siya musu har ta koma ba abinda take ganewa face sunan Daddy din da suke ta ambata. Tagumi kawai tayi tana bin su da kallo a ranta kuwa wani sashi na farin ciki da hakan ganin yadda yau yayan ta suka samu soyayyar uba abun da suka rasa tsawon shekarun su biyar sedai kuma ta wani bangaren fargaba ne zokar na ganin dagaske fa mutumin nan yake ya shirya kwace mata ƴaƴa. .....'Ba wanda ya isa ya kwace ƴaƴan ki a hannun ki se Allah, kauna ce kawai yake nuna musu fisabilillah amma ba da wata manufa ba, da ga ni yana da son yara ne, ke baki ji sunan sa ba ma, Abu Aulad!'..... Wata zuciyar ta faɗa mata haka, se taji ta yarda da hakan har kuma hankalin ta ya ɗan kwanta da har ta saki jiki cikin su Ifty suka yi ta shirmen su tana taya su, hakan kuma ya ƙarawa Ifty kwarin jiki dan ba zaka taɓa cewa bata da lafiya shekaran jiya ba. Da rana kam bata yi girki ba, sakwarar da tayi wadda ba wanda ya taɓa se ita kaɗai da taci ta dauka ta ɗumama musu dan a fridge tasa ta har da miyar ganin basu da niyyar ci a jiyan duk da cewa bata ma tunanin miyar zata yi matsala sedai ko farfesun kayan cikin. A tsakar dakin suka baje suka ci abincin su bayan ta nade Centre carpet din dan kar su bata shi da miya. Wunin ranar tayi shi cikin jin dadi tare da yan ƴaƴan ta a jikin ta, bata tashi daga cikin su ba se after four sannan ta shiga ƙoƙarin ganin me zata dafa musu da daddare, tuna cewa be ci tuwon da tayi rannan ba yasa yanzu ma tayi tuwon amma wannan karon na semovita ne ba shinkafa ba, miyar taushe tayi wadatacciya da taji gyaɗa se tashin ƙamshi take yi. Tana gama jerawa ta dan ƙara gyara falon dan ya ɗan yi datti saboda dabdalar wasan da suka yi a cikin sa, tana gama wa ta kunna turaren wutan ta me ƙamshi a burner sannun taja twins bedroom. Wanka tayi musu ta shirya su cikin three quarter red jeans da farar t shirt daidai jikin su, a wajen siyan ire iren wannan kayan wa ƴaƴan ta kuɗin albashin ta yake tafiya, ba wani ƙarfi ne da ita ba se taimakon Ubangiji amma a haka bata siyawa ya'yanta suttura mara inganci, tafi ganewa ta siya abu me tsada da ze zauna a jiki yayi kyau haka kuma ba wai daga sawar farko ya lalace ba, shiyasa majorityn kayan su designers ne masu ɗan karen kyau. Tana gama shirya su ta bawa kowacce hijab kan tayi sallah dan anyi kiran sallar magrib wasu masallatan ma har an idar, wanka tayi itama ta gyara jikin ta kana ta saka doguwar rigar ta ja me touches din fari, jan ribbon ta sa ta kama sassalkan gashin ta me matsakaicin tsayi dan da kaɗan ya wuce kafaɗar ta sedai bakikirin ne gashi da cika da kalli tun bare ma in yaji mai wanda hakan ke ɗaukar idon wanda ya kalla. Farin scarf ta ɗaura a kanta sannan ta ƙarasa gaban mirror ta dau turaren ta ta feffesa tare da wadata cat eyes din ta da bakin kwalli me kyau, bayan haka lip gloss da powder kaɗai ta saka amma ba ƙaramin kyau tayi ba, kyan ma irin special kyau ba wai gamagari ba. Kallon kanta ta shiga yi tana tunanin anya ta fita da wannan rigar ko kuwa dai ta canja kaya?, Ba wani abu rigar tayi ba dan bata kama ta ba asali ma loose ce Wanda mafi yawancin kayan ta haka suke se ko atamfa, yadin ne kawai me ɗan rawa hakan yasa yake bin jiki. Gaban wardrobe ta koma zata canja kaya se kuma zuciyar ta ta dakatar da ita ..'ba wani kaya da zaki canja, ai shima haka yake yawo da Three quarter wai shi me gida ba za'a takura masa ba, ai kema bake kika ce ya aure ki ba dan haka ba zaki takura kan ki ba.... Da wannan tunanin ta juya tare da saka wadataccen hijab din ta na sallah ta gabatar da magrib ɗin ta, azkhar da tasbih ɗin da ta saba tayi ta gama sannan ta fito falo wajen twins dake zaune suna wasa. Bata ko kai ga zama ba shima ya turo ƙofar falon ya shigo da takaitacciyar sallamar da iya shi kaɗai yaji kayar sa, kafin ma ya ƙarasa shigowa yaran sun tafi da gudu sun dane shi hakan yasa ya saki ledar hannun sa ya tare su tare da daga su a tare ya rungume. Be san wane irin so ne ba yake wa ƴaƴan nan, abu ɗaya ya sani yana jin su a can karkashin zuciyar sa, cikin jinin sa, ruhin sa kai komai ma na jikin sa. Yana ɗauke da su ya durƙusa ya ɗau ledar da ya saki tare da ƙarasawa kan three sitter ya zauna ya zaunar dasu a jikin sa, ledar ya buɗe ya shiga firfito da kayan ciki wanda suka sa twins sakin ihun murna. Kayan wasa ne ya siyo musu ganin basu da ko ɗaya dan salma bata ma bari su fita wani wasa, kullum suna tare da ita a daki suna hira ko karatu shiyasa yanzu da suka ga wannan bakin su kamar ya yage dan dariyar murna. Baby doll ne manya manya guda biyu duk mata, irin su ɗaya sedai kayan jikin su ne suka bambanta, Ifty ta dau me blue ɗin gown ita kuma Ibty me pink, ragowar kuwa tarkacen kayan saitin gado da kujerun wasa ne, motoci, jirage har dasu jirgin ƙasa. Daga inda take ta kame ta kasa motsi, idanun ta kuwa ko ƙifta su bata yi daga kan sa tun lokacin da ya fito da baby dolls din nan har zuwa yanzu da ya sauka kasan carpet cikin su yana haɗa musu train din tare da kunna shi ya fara tafiya, ihu suke yi cikin jin daɗi shikuma se murmushi yake yi koma tace dariya dan hakwaran sa gaba ɗaya na waje ne abinda bata taɓa gani ba se yau, yau ɗin da yake tare da ƴaƴan ta. Wasu irin hawaye ne da bata san na mene bane suka cicciko idanun ta, gaba ɗaya she's speechless, tun da yaran nan suka zo hannun ta ake nuna musu so da ƙauna, misali mutanen ƙauyen su baba Husaila, ga Mama Hadiza principal, ga Kuma Hajiya me gidan haya amma babu wanda ya taba nuna musu zurfafaffiyar kaunar da lokaci guda taji zuciyar ta tayi amanna da ita kamar shi, tsantsar soyayyar ƴaƴan da ta hango cikin idanun sa da ayyukan sa yasa taji kamar zuciya ta na narkewa a tsayen da take. A hankali ta lallaɓa ta kai zaune kan kujera mafi kusa da ita sannan ta fara sauke numfashi da sauri da sauri wanda ta riƙe, se da ta tabbatar ta dawo daidai kafin ta sulale ta zauna kusa da Ibty wadda ke hannun daman sa, Muryar ta can ƙasa saboda sanyin da tayi "Sannu da zuwa Daddy". Be yi niyyar kallon ta ba amma jin sunan da ta kira shi dashi ya tilasta masa kallon nata. Cikin tsakiyar golden cat eyes din ta da suka sha kajol ya sauke nasa, ba tun yau ba yake son sake ganin ƙwayar idanun ta, duk da ya tabbatar ba bakake bane amma be san wane kala bane dan bata bari su haɗa ido shiyasa yanzu ɗin ya tsai da idanun sa cikin nata yana faman karewa idon ta kallo. Lumshe ido salma tayi dan ba zata iya cigaba da kallon shi haka ba, wanda tayi ma ji tayi gaba ɗaya kamar ya sa ƙaƙƙarfar igiya ya ɗaɗɗaure mata jiki haka kuma kafufuwan ta ji take kamar an sa gatari an sassare mata su, inda Allah ya taimake ta tana zaune ne da tsaye ne kuwa ta tabbata ba abinda ze Hana ta zubewa. Wani irin yanayi salma ta tsinci kan ta a ciki, yanayin da bata taba jin ko makamancin sa ba a kaf rayuwar ta, a tsayin shekarun ta na 21 bata taɓa jin ko da kaso daya ne cikin goman abinda take ji yanzu ba, idanun ta da ta lumshe kuwa har lokacin suna rufe amma ji take yi har yanzu waɗan nan kaifa dan idanun nasa masu matuƙar kwarjini da sa jikin mutum ya mutu nan take suna kanta, a hankali ta buɗe idanun da suka yi wani maiƙo maiƙo kamar zasu zubda ƙwalla sedai ba kwallan zata yi ba, yanayin da take ciki ne suka haifar da hakan. Ajiyar zuciya ta saki tare da komawa ta jingina bayan ta da jikin kujerar ganin yanzu kam idanun sa ba ya kan ta haka ma hankalin sa baya tare da ita yana wajen su ibtisam yana kunna musu jirgin sama suna ta dariya ganin yana tashi. A yadda jikin ta yake mace ji take kamar zaman ma ba zata iya ba , gagarar ta yake son yi dan a yanzu ba abinda tafi bukata kamar ta ji ta kwance kan gado, ita kadai ɗin ta dan so take yi tayi birgima iya yadda zata iya ko taji sauƙin yanayin da take ciki. Kiran sallar isha da aka yi yasa ya tattare kayan wasan gefe ya riƙe hannun yaran zuwa bedroom din sa, alwala yayi musu yace su tafi wajen momma suyi Sallah kana shima yayi alwala tare da canja suit din jikin sa zuwa jallabiya ya fita Masallaci da kudirin in ya dawo ya gyara dakin sa da ya zubar da kayan ciki kan bed garin dauko kayan da zesa ɗazu da safe. Ana idarwa yayi azkhar ɗin sallah be tsaya yin tasibihan da ya saba ba ya dawo alabasshi in ya gama gyaran dakin yayi su a nutse, tuni su salma suka hallara a dining se shi kaɗai suke jira, har minti biyar shiru be fito ba hakan yasa ata aika Ibty kiran shi bata ade ba ta dawo tace ai Daddy aiki yake yi, mamaki ya kama salma ta tambaye ta aikin me se kuwa ta faɗa mata gyaran daki. Duk da yara ne se taji amma gaba daya ta muzan ta, yanzu da da wani ɗan uwan sa ko wani na waje a nan gurin se fa a ga laifin ta ko, bayan tun ainahi be bata damar shigar masa daki ba, duba shi ma da ta shiga yi be ko gode mata ba se guzurin wulaƙancin da ya biyo baya. Kai wai dai ita mace duk yadda tayi ba zata fita ba se an ga laifin ta, ta tabbatar da akwai dan uwan sa a nan abinda zasu fara cewa shine ta mallake shi hatta gyaran dakin ma shi yake yi. Haka dole suka jira ya gama kafin ya fito aka ci abincin, duk da be buɗe baki yace mata abincin yayi daɗi ba yanayin sa ya nuna, be gode mata ba amma yadda ya cinye tuwon har da kari ma ya shaida mata godiyar sa. Ko da suka gama ci tuni yaran suka koma falo suka cigaba da wasan su ita kuma ta tasa su kamar Tv tana kallo cikin jin dadi, shi kam har lokacin yana kan kujerar dining idanun sa a rufe. Yanayin ƙwayar idanun ta ba abu bane da aka fiya gani kasafai cikin jama'a, wasu kan ringa gudu ko tsoron mutanen da ƙwayar idon su bata kasance baka ko brown ba sedai shi tun a karon farko da yaga idanun ta yaji sun burge shi, kalan su da yadda suke yin maiƙo maiƙo lokaci zuwa lokaci shi yafi daukar hankalin sa sedai be nuna ba ma dan kar ta raina shi. Yanzu haka da ya rufe ido tunani yake yi na daban amma kuma yanayin idanun nata lokacin da suka yi kallon kallo ɗazu shike masa shawagi cikin na sa idanun, tunanin sa ba na komai bane illa zuciyar sa da yaji ta fara kwantawa cikin son yarda da yarinyar, ba wai yarda akan komai ba, a'a yarda akan cikin sa wato abincin sa. Tun ranar da aka ɗaura musu aure ya sassaka CCTV cameras a sashen sa, irin yan ƙananun nan da bakowa ze san akwai su ba, yasha bibiyar ayyukan ta a kitchen musamman lokacin da ta fara aiki masa da tayin cin abinci, a lokacin sam be yarda da ita ba gani yake wani abu ne a ranta shiyasa tayi hakan, wannan dalilin yasa kusan kullum se ya bibiyi moves din ta a sashen tun bare ma ayyukan ta na cikin kitchen sedai har zuwa yau da zata cika she sati ɗaya a tare dashi gobe be kamata da rashin gaskiya ba ko ƙanƙani, a kan komai ma be ga alamun cutarwa ba tattare da ita sedai ba wai ya gama yarda bane ze cigaba da bibiyar ta har nan da zuwa ko watanni nawa ne baze gaza ba har se yaji hankalin sa ya ida kwanciya da ita. Tun bayan mutuwar Ummu be kuma cin abincin da dandanon sa ya ratsa zuciyar sa ba se shigowar ta rayuwar sa, haka be san ya akayi tasan yana son abincin gargajiya ba sedai shikam hakan yayi masa dadi dan yanzu bashi da fargabar samun wani ciwo dalilin yunwa sedai kuma wani bangaren. Ajiyar numfashi yayi tare da buɗe idanun sa ya sauke kan yaran dake guje guje suna bin kayan wasan su, fari kal yake jin ransa in Yana duban su, se yake ganin kamar wadancan ne suka dawo, haka cikin ransa matsayin wadancan ya basu shiyasa basu da shamaki cikin ran sa da kuma dukiyar sa haka kuma yayi alƙawarin kulawa dasu tare da basu dukkan soyayya har zuwa ƙarshen nunfashin sa. "Time for sleep babies". Ya fada yana miƙa musu hannu, ajiye dolls din su suka yi suka ƙarasa tare da bashi nasu hannun, be yi sanya ba ya ɗauke su zuwa dakin sa a karo na biyu Hajiya salma na zaune. Sabanin jiya yau kam se ba taji ko ɗigon na bakin ciki ba se ma farin ciki da jin dadi hadi da tsananin girman sa da taji sun mamaye mata ruhi....................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 024 [ 12/11/2022 12:58 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                     Paid page 024 _________________________📖 Yau kam bata fita raka su ba shi ya kai su har class sannan ya je wajen principal Wanda bata san me yace masa ba, taga dai sun fito tare suna magana sannan sukai sallama ya dawo mota. Yau tun kan su kai office ta zare abayar jikin ta tare da gyara zaman ƙaramin hijab din ta ta saka rigar cikin jaka. Kusan tare suka fito daga motar lokacin da yayi parking, kwana biyu da bata zo ba se take jin matukar kewar companyn kamar an canja shi dan tun da ta fara aiki in ba hutu akayi ba bata taɓa fashin zuwa aiki ba. Rufe kofar sa yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da zama kan nata kujerar da ta gama goge wa duk da tasan kullum se an share an goge komai dake cikin office din. Aiki ta fara dan ma taga ba'a ajiye mata ayyuka sosai ba dan bata tarar da files ɗin da ta tafi ta bari ba wanda kashegari ya kamata ta tashi aiki a kan su se kuma bata samu zuwa ba. A hankali ta ɗago kan ta dake kan screen din laptop ta kalli Haisam tare da amsa kiran da yayi mata "Na'am, Good morning sir". "Morning Salma, ya jikin angel". "Ta warware dan suna ma school". "Allah ya ƙara lafiya ya tsare gaba, dama ina ta neman ki dan ina so muyi discussing a very important issue". "Ayya in zo office ne?". "Eh when you less busy ki shigo Ina jiran ki". "Insha Allah sir". Daga haka ya ƙarasa officer ɗin Abu Aulad ita kuma ta cigaba da aikin ta without giving much attention kan issue din da yace zasu yi magana akai dan a nata tunanin it's a business issue. Bata sami saukin ayyuka ba se after zuhr dan haka daga masallaci da tayi sallah se kawai ta wuce office din Haisam. Zaune yana ta fama da takardu ta tadda shi amma tana shigowa ya ajiye tare da ture su gefe ya nuna mata kujera alamar ta zauna, zaman tayi tana sake gaida shi ya amsa mata cikin sakin fuska kamar yadda ya saba. Dan shiru yayi cikin tunanin ta inda ya kamata ya fara kafin ya nunfasa ya ɗago ya kalle ta "Ashe mijin ki ya sake aure kuma?". Bata san me yasa ba amma se da taji wata yar faduwar gaba duk da kuwa ta sani "Eh wallahi, Allah ya nufa". Shiru ya dan sake yi se kuma ya zuba gaba ɗaya hannayen sa kan table ɗin sa "Naji an aura masa shuraiha yar aminiyar Hajiya Babba". Oh ashe yar aminiyar ta ne, to ita ina ta sani ba dan ya faɗa ba, shiru tayi masa dan bata san ne zata ce ba, tun da ya sani meye na tambayar ta kuma. "Tun kafin maganar auren ta fito na so na samu lokaci muyi magana se kuma Allah be nufa ba, yanzu kuma da akayi auren se maganar ta mafi muhimmanci akan da, magana ce nake so muyi akan mijin ki, ina nufin Abdallah". Jin sunan Abdallah yasa ta sake bashi attention din ta sosai "Auren ku da Abu Aulad aure ne da yazo cikin wata siga da ba haka aka saba gani ba, aure ne da ya wanzu bisa tsarin ubangiji, baki taɓa sanin Abdallah ba se da kika fara aiki dashi haka shima be san ki a wani matsayi ba face na ma'aikaciyar sa sedai tashi ɗaya Allah ya canja komai bisa hikmar sa ya juya lamura yada ba'a taɓa zato ba yanzu ga ku a matsayin mutane mafiya kusanci da juna, wato ma'aurata, shin salma kin taɓa tunanin yaya rayuwar mijin ki kafin yanzu?, Ma'ana kin taɓa sanin tarihin mijin ki?, Waye shi?, Yaya rayuwar sa take tun daga yarinta har zuwa bigiren matashi ko ince magidanci da yake kai?". A hankali salma ta girgiza kan ta alamun a'a. "Ba zance mijin ki be tashi cikin farin ciki ba, ba zance mijin ki be ji dadin rayuwa a baya ba sedai Zan ce mijina yanzu mijin ki na yin wata bahaguwar rayuwa ne da babu ki dison farin ciki a cikin ta, babu kwanciyar hankali balle ayi maganar jin dadi. Mutane ko ince makiyan dake kewaye dashi sun haddasa masa wani ciwo a ransa, ciwon da yasa rayuwar sa take tafiya a baibai, ba komai ban face ciwon rashin yarda wanda shekaru biyar baya be yi girman na yanzu ba sedai faruwar wani al'amari ne girma ya sake juya rayuwar sa zuwa matakin da yake kai yau, mijin ki be yarda da kowa ba ciki kuwa har da Ni, so da yawa yakan yi kamar ya yadda sani sedai in yayi wani abun se ki ga akasin haka. A halin da ake ciki ba shida wata rai mafi kusanci dashi da ta sanshi ciki da bai kamar ni sedai yardar dake tsakanin mu ba wai ta kai ta kawo bane, a baya nace miki baze ci abincin ki ba yanzu dan be gama sanin ki ba sedai ba haka bane, be yarda da kowa bane balle har ya aminta ya ci abinda ya fito hannun ki. Wani sa'in yakan bani haushi sedai in na zauna nayi nazarin irin rayuwar sa da mutanen da ke zagaye dashi se inga be yi laifi ba, kar in jaki da nisa a yanzu zaki san wane ne mijin ki ABDALLAH ABDULSALAM GAMJI. kamar yadda kika ji na faɗa yanzu wannan shine cikakken sunan sa, mahaifin sa Alh Abdulsalam haifaffen gari ko ince local government ɗin Gamji ne dake garin nan. Tun ainahin kakannin Abu Aulad masu rufin asiri ne ko ma ince masu kudin da ne dan suna da arzikin su sosai wannan yasa magidan su ba ɓoyayyen gida bane, ko yanzu kika tari ne napep kika ce masa gidan Ahmad Gamji har kofar gidan za'a kaiki duk da babu kakannin nasa se yan uwan su dan duk sun mutu. Abdulsalam Gamji baban Abdallah dan kasuwa ne cikakke wanda ke tafi da kasuwancin nasa da zamani dan tayi ilimin sa har matakin Masters, tun yana matashin sa sunan sa yayi fice a garin nan dan a lokacin babu matashin da yakai shi kudi da suna. Be yi aure ba se da yakai shekaru talatin da hudu saboda tsaikon da aka samu, manya da yara a lokacin ba wanda be san irin so da kaunar da Abdulsalam ya gwada wa Fahima ba wato mahaifiyar Abu Aulad dan a kan hidimar ta barin komai yake yaje gare ta, be yadda ta shiga motar haya ba haka be yarda da samar nata drivern ba, shine yake tuka ta duk inda zata ya kuma maida ita gida. Tsaikon da aka samu ba komai bane illa Hajiya Rahma babar sa wato kakar Abu Aulad da ta yi tsalle ta dire tace Bata San zance ba dan ta baze auri wadda ba'a san asalin ta ba dan Fahima marainiya ce dake rayuwa cikin gidan marayun garin nan, duk yadda Abdulsalam ze yi dan ganin mahaifiyar sa ta sauka daga kan ra'ayin ta yayi amma ta ki, mahaifin sa Ahmad ba mutum ne me zafi ba shiyasa kullum tsakanin sa da haka Rahma nasiha ce amma hak ta kafe taki sauraren kowa inda a ƙarshe se hakuri mahaifin nasa ya bashi kan yayi wa mahaifiyar sa biyayya. Hajiya Rahma da kanta ta nemo wa Abdulsalam aure a can dangin ta, duk da Abdulsalam be so ba haka ya hakura ya aura Safiyya dake amsa sunan Hajiya Babba a yanzu, auren Safiyya da Abdulsalam seda yayi kusan shekaru huɗu amma bata taɓa ko batan wata ba balle a sa rai da samun ciki, wannan ya tashi hankalin Hajiya Rahma ta fara nuna ita fa ta gaji da jira kawai ya ƙara aure, anyi tashin hankali sosai inda Hajiya Babba ta murje idanun ta ta fesawa Hajiya Rahma rashin kunyar da ba wanda ya taɓa zaton zata yi wanda hakan yasa Hajiya Rahma ƙudure niyyar se ta nuna mata tana da cikakken iko da ɗan ta. Bisa wannan alwashi nata Hajiya Rahma ta bawa baba izinin auren masoyiyar sa Fahima, dake abinda dama zuciyar sa bata taɓa fidda rai ba ne baba be bata lokaci ba wajen tunkarar shugabannin gidan marayun dan har lokacin Ummu wato Fahima bata yi aure ba. Cikin kankanin lokaci aka yi komai da ya kamata ciki har da daurin aure Ummu ta tabbata mata ga baba, hajiya Babba bata raina kan ta ba se da Ummu ta tare, irin rawar jikin da baba yake a kan ta dole ya tabbatar wa duk wanda ke kuwa irin matsanancin so da kaunar da yake mata hakan kuma shi ya assasa matsanancin kishin Ummu a ran Hajiya Babba kishin da ya dinga rikidewa har ya koma tsananin tsana da ƙiyayya. Tsananin ƙiyayyar da Hajiya Babba ke wa Ummu yasa ba abinda take burin gani face mutuwar Ummu sedai dake Allah ba'a masa dole kullum Ummu kara lafiya take yi dan ko ciwon kai bata taɓa yi ba har ta shekara a gidan. Shekara daya da rabi ciki ya wanzu a jikin Ummu, cikin da ya siyo mata matsananciyar soyayya da ƙauna wajen Hajiya Rahma dan ba abinda take burin gani face zuri'ar dan ta tilo wato baba. Afuwan a farko ban sanar dake ba, baba su biyu ne a wajen mahaifin su, shi daga wajen Hajiya Rahma se baffa wato Usman daga wajen abokiyar zaman ta. Irin yadda kowa ke so da daukin cikin Ummu yasa seda Hajiya Babba tayi iya yinta wajen ganin yabi rariya ma'ana ya bare, bakin cikin da ahalin suka shiga saboda barewar cikin bane bayyana bane. A takaice dai tun daga wannan cikin Ummu seda tayi bari sau uku a jere wanda a karshe likita ya bayyana musu ai a abinci take cin maganin zubar da cikin, bincike na sosai baba yayi inda daga ƙarshe ya gano ba kowa ne da wannan aikin ba face Hajiya Babba. A bisa wannan dalilin har sakin ta baba yayi , seda tayi watanni biyu a gida kafin ya dawo da ita bisa umarnin babansa Alh Ahmad dan iyayen ta kullum se sun kira shi suna bada haƙuri. Komawar Hajiya Babba gidan be sa ta rage komai na bakin halin ta ba sema karuwa da yayi, sedai ba kamar baya ba yanzu tana ɗan ɓoyewa. Dawowar ta da yan watanni ta samu ciki, abinda ya dadada mata kenan dan lokacin Ummu shiru kake ji ba labari. Duk wani iyayi da feleƙe da take yi Ummu bata taɓa ko kallon ta ba balle ta kula ta sema taya baba kulawa da ita tare da nuna son abun dake cikin da tayi hakan yasa daraja da kimar ta karuwa a idanun baba. Cikin ikon Allah ciki yakai watan haihuwa inda ranar haihuwa nayi ta haifi yar ta mace me tsananin kama da ita , sam Hajiya Babba batayi wani murna da haihuwar Saudah ba dan ita kam ba mace taso haifa ba namiji taso yadda zata mulki kowa yadda take so tun da ta haifa magajin family. Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya Saudah na girma har ta fara tafiya kafin ciki ya sake ɓullo wa jikin Ummu, irin murnar da baba yayi zaka ce ba'a taba masa haihuwa ba, bakin cikin Hajiya Babba ya dawo sabo domin tun fitowar cikin Hajiya Rahma ta sa baba ya dawo da Ummu wajen ta dan tace ba zata kuma yadda a salwantar mata da jika ba. Allah Al- baseer se ya bawa Ummu haihuwar namijin da Hajiya Babba ke kulafucin haifa, yaron ya zo da tsananin kyau da kwarjini kamar baban sa, farin jini kuwa se wanda ya gani dama kun san jarirai da farin jini to nasa kam na daban ne. Seda Ummu tayi arba'in kafin Hajiya Rahma ta yadda ta koma gidan ta inda ta cigaba da kulawa da Abdallah, soyayyar da baba ke nunawa Abdallah a fili take kuma a bayyane, fita dubu shiga dubu se ya kawowa Abdallah tsaraba, magana dari in se yi se kaji sunan Abdallah hamsin, son kuma ya samo asali ne da yadda yaron yake tamkar photocopy din sa, ga kuma kula da yake samu daga mahaifiyar sa Ummu da yasa yayi bulbul kullum cikin ƙamshi da ado. Lokacin da Abdallah ya shekara biyu kuwa se ya zama duk inda baba zashi Abdallah na tare dashi, hatta office kuwa da Abdallah yake tafiya, ko da Ummu ta faɗa wa Hajiya Rahma dan tayi masa magana ba ta yin ba se ma Ummun da ta rufe da fadan in be fita da ɗan sa ba wa ze ɗauka ya fita da, dole haka Ummu ta hakura ta zuba ido. Baba be daina fita da Abdallah ba se da ya kai minzalin shiga makaranta, shima kuma kullum shi ke kai shi driver Kuma ya ɗauko shi, in aka dauko shin maimakon gida sedai a wuce dashi wajen sa a office, a wannan karon kam Alh Ahmad ne yayi magana ya tsawata masa kan hakan da fadin ya bar yaro yayi karatu sosai. Wannan shine sanadin da Abdallah ya daina zaman office din Baba, shaƙuwar dake tsakanin Abu Aulad da baba ba karama bace dan kafin ya kira sunan Ummu so daya ya ambaci baba so goma, haka shima baba duk ya dawo daga office ba ya taba wucewa sashen sa se ya shiga sashen Ummu yaga Abu Aulad inda yake bata lokaci sosai a wajen sa. Wannan abun ba ƙaramin ciwa hajiya rai yake ba dan a ganin ta baba ba yasan yar ta saudah dan bata kasance namiji ba shiyasa baya kulawa da ita, tun tana shiru har se da ta kai ta magantu dan ta kasa riƙe abun a ranta. A lokacin kallon ta kawai Abba yayi sannan ya murmusa kana cikin halin miskilancin sa wanda shi Abu Aulad ya gado ya bata amsa "Ni ban fi son wani daban ba cikin yarana, dukkan su ina jin su a raina tun da jini na ne, ban fifita Abdallah kan saudah dan nafi son sa ko dan shi namiji ne ba, ina masa komai ne dan shi ɗin photocopy nane, halin sa irin nawa ne haka ma kamannin sa shugaban yasa nake ganin sa kamar ni sanda ina yaro, amma ki kwantar da hankalin ki zan gyara". Tun da ga wannan lokacin baba yake shiga sashen Hajiya Babba dan ganin saudah sedai babu wani shaƙuwa tsakanin su sosai dan ita saudah akwai dafar uwar ta da girman ta amma bata yarda baba ya ɗauke ta sedai kallo daga hannun babar ta..................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 023 [ 12/10/2022 11:01 AM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* Paid page 023 _________________________📖 Tattare musu kayan wasan tayi ta hade su takai daki kana ta canja kayan ta zuwa na bacci, tana zaune tana addu'a se gasu sun shigo kowanne su sanye da kayan baccin su iri ɗaya hatta ko da kala. Zama suka yi gefen ta har ta karasa ta shafa musu ta shafa wa kan ta "Ya akayi yaran Daddy basu kwanta bacci ba har yanzu?". "Momma ni na cewa Daddy a wajen ki zamu kwanta yau kar kiyi fushi irin na ɗazu". Kallon Ibty da tayi maganar tayi cikin rashin jin dadi, se taji bata so yarinyar ta faɗa masa haka ba, bayan duk wahalar da yake yi dasu ai be cancanci ta nuna masa kamar be isa dasu ba. "Maza ku koma wajen Daddy ku kwanta, yau momma bata so a dame ta". Kallon ta suka tsaya yi bare ma Ibty, suna son zuwan sedai basa so tayi fushi "Come on darlings, come and hug momma, ayi min good night hug". Ta faɗa tana buɗe hannayen ta dan tayi cheering din su, aikuwa da gudu suka shiga jikin ta suka rungume ta, da ɗaiɗaya ta bisu ta musu peck a goshi da kunci kana ta sake su "Oya maza a tafi Daddy yana jira, and acewa Daddy momma tace Masa goodnight". "Okay Mom". Suka fada suna ficewa da ɗan gudu, ajiyar zuciya ta sauke tare da komawa ta kwanta tana latsa madannin wutar dake gefen bed din ta, take duhu ya cika dakin hakan yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da yin luff a gadon. Ita kanta bata san me yasa tace a ce masa goodnight ba, kawai ta tsinci kan ta da son yi masa sallamar, tun da kuma baya kusa shine ta bada sako. Yau ma da kyar bacci ya ɗauke ta dan dagaske bata saba bacci ita daya ba tun da yaran suka shigo rayuwar ta. Bata yi gigin cewa zasu school ba dan a yadda taga uban yana ji da ƴaƴan sa tasan baze bari suje yau ba duk da jikin Iftyn ya warware tas, maybe dai gobe ya iya cewa suje. Breakfast ta hada musu traditionally, kunun gyada da kosai wanda yaji hadi yayi sutu sutu dashi gwanin kyau da burgewa, tana gama wa ta koma tayi wanka abinta ta shirya sannan ta fito gyaran falo. Bata neme su ba dan tasan se ya gama shirya su zasu fito, a yadda ta ga ya sa musu sababbin kayan bacci ya tabbatar mata siyayya yayi musu dan haka tasan akwai kayan da zasu iya sawa a dakin sa base yaje dauko musu ba. Kamar kuwa ta sani shirye suka fito yau kam zam ƴaƴan larabawa, Arabian gowns ne na yara da suka sha adon stones se walwali da ɗaukar ido suke yi gaba dayan su bakake, ita kanta da ta gan su seda tace masha Allah saboda tsananin kyan da ta ga sun yi. Cikin ranta kuwa wani sabon daraja a girma Abu Aulad ɗin ke karawa, dama an ce me da wawa, to haka ne ga salma, ba tun yanzu ba ita duk me son yayan ta yakan zama masoyin ta bare shi da ya karɓe su hannu bibbiyu yake kulawa dasu wanda a ganin ta ko mahaifin su ne iya soyayyar daze gwada musu kenan. Ita har yanzu fa mamaki yake bata, mamakin ta ba na komai bane illa yadda taga ya iya kula da yara, wankan su da shirya su, gashi ba ya'ya maza ba balle tace ai simple shiri ne Yanzu kalli dai yadda yayi wa yaran nata rolling, ko iya mace haka zata yi dan wata ma ba zata iya gyara shi yayi kyau haka ba. Tunanin ta ya katse ne lokacin da Ifty ke jan hannun ta wai suje suci abinci, bata Musa mata ba ta biya kamar raƙumi da alaka har gaban table ɗin, kujerar gefen Iftyn ta zauna wanda suka saka Daddyn nasu a tsakiya, ita tana gefen dama Ibty na hagu. Kallon plate din gaban sa kawai yake yi cikde da wani irin daɗin da ya tsaya iya ran sa be bayyana kan miskilar fuskar sa ba, ya manta rabon sa da ya karya da kunu da kosai, ze iya cewa tun ma kafin Ummu ta rasu dan ita bata shiri da kosai, sedai ta kan daure tayi masa tun da ta fahimci yana so. Manyan oily and sexy eyes din sa ya waina kafin ya kai hannu ya ɗau guda daya ya nufi bakin sa dashi bayan yayi bisimilla, irin yadda taste ɗin ya ratsa harshen sa ya wuce zuwa jijiyoyi jikin sa zuwa kwakwalwar sa ya tilasta masa dakatawa daga taunar da ya fara na tsawon sakanni kafin ya cigaba da ci, ita kam salma ganin ya tsaya da ci se take tunani ko bai yi masa daɗi bane?, Sedai kuma ganin yadda ya buɗe zuciyar sa yake ci da sauri da sauri se ya share mata tantama. Kafin kace me ya cinye na plate din gaban sa duk da ba laifi da ɗan yawa ta sa masa, flask din da yaga ta ɗebo a ciki yasa hannu ya buɗe da niyyar karawa sedai wayam babu komai se ƙamshin kosan dake tashi. Be san me yasa yaji haushi ba amma har se da ya ɗago ya wurga mata harara lamarin da ya sa salma zaro ido tare da buɗe baki tana kallon sa, hararar ta ya kuma yi tare da janye idanun sa se kuma ya sauke ganin sa kan plate din ta dake ɗauke da kosai kusan bakwai da bata kai ga cinye wa ba, be tsaya wani tunani ba yasa hannu ya janye shi zuwa gaban sa ya cigaba da ci, tagumi kawai salma tayi tana bin sa da ido har ya cinye mata kosan a gaban idanun ta, tissue tas aya goge bakin sa sannan ya wuce ta zuwa falo dan tuni twins har sun Gama nasu break ɗin. Zama yayi cikin su suna maganar da bata san meye suke cewa ba sedai tana hango yadda yaran ke dariya tare da sake shigewa jikin sa, a lokacin itama ji tayi kamar taje ayi maganar da ita sedai sanin she's not welcome yasa bata ko daga daga kujerar ta ba har suka gama ya mike bayan yayi musu peck sun masa , hannu ya daga musu tare da nufar ƙofa alamun ze tafi aiki. Se lokacin ta samu damar kallon shi dan in Yana zaune ko tsaye kuma yana fuskantar ta bata iya daga kai ta kalle shi dan ji take yi gana ɗaya ya cika wajen har bata iya shaƙar iska sosai. Dark blue din Armani suits ne a jiki sa da suka karɓe shi kamar dama dan shi aka kirkiri kayan, daga yadda ya juya ya na tafiya kallo ɗaya zaka masa ka tabbatar ya cika cikakken namiji dan iya takun sa ya shaida maka hakan. Taki ne yake yi cike da karfi da jarumta hadi da isa ga kuma yar sassarfar da yake yi kaɗan da ta kara ƙawata tafiyar tasa da har tasa salma shagala wajen kallon sa batare da ta sani ba se neman sa tayi ta rasa, ya fita!. Hannu yasa ta shafa fuskar ta tana ɗan jujjuya kai kafin kuma ta tallafi haɓar ta cikin tunani ..'meke damun ki ne salma?'... Haka ta tambayi kanta, eh mana dole ta tuntubi kan ta dan daga juya zuwa yau gaba ɗaya indai zata kalle shi se yanayin ta ya sauya, duk ƙarfin da ta tashi dashi se taji ya zagwanye kasa ta lulluɓe ta, ita kuwa in bata tambayi kanta meke damun ta ba wa zata tambaya. Yau kam su Ifty kawai ta bari suka yi wasan su su kaɗai batare da aya shiga cikin su ba dan gaba ɗaya ji take kamar bata da lafiya, hakan yasa ta wuni a kwance har bacci ya sadado ya sace ta. Ba ita ta farka ba se dab da magriba, sosai ta rude da tambayar yaran me suka ci suka ce mata sun sha fresh milk hakan yasa hankalin ta dan kwanciya. Da ruwan zafi sosai tayi wanka dan ta watsar da kasalar baccin da tayi kana ta saka Pakistan ruwan kasa ta wuce kitchen bayan ta ɗaure kan ta da mayafin kayan dake siriri ne baze yafu ba. Yau kam tayi daren girki dan haka farar shinkafa ta dafa musu da jar miya, salad ta duba a freezer se taga babu , dole haka ta hakura ta yanka ita cabbage da carrot ta haɗa musu coslow dan cin farar shinkafa tsura se dole. Wanka tayi musu dan sun bata kayan jikin su, guntun wando da ya wuce cinya da kadan ta saka musu se shimi wanda a cikin kayan da Daddyn su ya siyo Ifty ta dauko. Se da ta gama jera komai sannan hankalin ta ya kwanta ta koma ta sake kwanciya cikin sofa sedai wannan karon ba bacci take yi ba, sunna Tv ta kunna se ta tadda sun saka karatun Alkur'ani dan haka ta rufe ido take bi ƙasa ƙasa. Yau be dawo da wuri ba dan a waje tayi isha, ganin dare nayi yaran har suna neman yin bacci basu ci komai ba se ta zuba musu suka ci, addu'ar bacci tayi musu bayan sun gama kana tace su tafi dakin Daddy su kwanta ita kuma ta cigaba da zama. Se ƙarfe tara da kusan rabi sannan ya shigo falon, coat din sa a hannu yar cikin ma ya ɓalle maɓallayen saman, dukkan alamun gajiya su gama nuna kan su a tattare dashi. Sannu da zuwa tayi masa ya amsa ta ta hanyar daga hannu ya shige ɗakin sa, hararar kofar tayi ganin yadda ya wani daga mata hannu kamar kurman da be da bakin amsa mata. Shiru shiru taji fitowar bawan Allahn har ta haƙura ta cire rai, abincin ta taje taci ta bar masa nasa cikin warmer da tunanin in yazo ci ya zubawa kan sa. Ko da ta tashi da asuba ta a idar da sallah abincin ta fara dubawa dan dashi ta kwana a ranta, ganin be wani ci da yawa ba se bata ji dadi ba, haka dai ta kwashe ta kai kitchen ta shuga hidimar haka breakfast, tana aikin ya dawo daga masallaci, yadda hankalin ta ya dauku ga aikin yasa bata na ji shigowar saba se maganar sa da taji daga bakin ƙofar kitchen din "A hada musu basket zasu je school". Kai ta gyada masa alamun amsawa ya juya ze fita "Ina kwana an tashi lafiya". Ta gaida shi, yau ɗin ma dai kamar kullum da lafiya ya amsa mata ya fice ita kuma ta cigaba da aikin ta. Kamar yadda ya faɗa haka ta haɗa basket ta shirya dining sannan ta wuce da niyyar zuwa shirya su sedai tsaf ta tarar dasu cikin gogaggen uniform din su da clean white neat socks din su ƙafafun su sanye da white canvas din su me kyau. ..'lallai Daddyn su Ibty matar sa tayi Sa'a'... Ta faɗa cikin ranta se kuma ta ɗan yi turus lokacin da wani sashe ya tuna mata ..' wace matar tasa kuma bayan ke?'... "No bani ba, amarya dai". Ta faɗa a fili se kuma ta yamutsa fuska tare da rungume yaran ta suna gaisawa. Kan dining din ta kai su tare da hada musu tea din su tare da zuba musu chips din da ta siya da kwai ta ajiye musu bread a tsakiyar su ta maza ta koma ɗaki dan yin nata shirin. Seda ta sake wanka saboda ƙamshin girki da take yi sannan ta zura farar rigar ta da blue ɗin wando, yau kam golden din after dress ta dora kan uniform din sedai Kamar ko yaushe bata ɗauki mayafin rigar ba kasancewar da hijab din ta a jikin ta. Golden slippers me kyau kirar Dubai ta sake a kafar ta tare da ciro handbag din ta kalar sa ta zuba abubuwan da zata buƙata ta fita. Kan sofa ta ajiye jakar sannan ta ƙarasa dining, ba kowa a dining din shiyasa ta maza ta karya a gurguje ta dawo wajen twins dake zaune, Daddy fa tambaye su suka ce yana daki. Sake tambayar su tayi in yayi break suka ce mata eh dan haka itama ta zauna jiran shi. Be daɗe ba ya fito a shiryen sa kamar kullum sanye da suits sedai yau ja ne kuma ba zata iya cewa ga Companyn su ba sedai daga kallo ɗaya kasan masu tsada ne saboda yadda suke daukan eyes, ɗaga iya Ido kadai ana iya gane taushin su ga kuma yadda zaren su ya saku ya kwanta kamar haka aka halicce su ba yin su aka yi ba. Bakin cover ne a ƙafarsa dake shekin tsada da ƙyalli, gaba dayan sa kana ganin sa kaga cikakken wayayyen namiji da yasan takan duniya da kaya, ado kuwa sedai a koya a wajen shi dan ta wannan fannin shi ɗin ya zarce matakin Farfesa. Da kyar da sidin goshi ta janye idanun ta daga kanshi tana lumshe su cike da shauƙin da bata san daga ina yake tahowa ba, me ya assasa shi duk bata sani ba , abu ɗaya ta sani shine taji daɗin ganin sa cikin koshin lafiya ba dan komai ba se dan yadda shima take kula da lafiya da walwalar ya'yan ta. Ganin sun nufi kofa shi da twins da suka rike masa hannaye yasa itama ta tashi tare da daukan handbag din ta ta mara musu baya tana cigaba da kallon su yadda suka yi kyau kamar uban gaske da ƴaƴan sa. Kofar sashen ta rufe sannan ta yi parking lot din sa da ta gane nasa be shi kadai tun kwanan ta biyu a gidan, tun da ga nesa ta hango jar motar dake ta ƙyallin wanki da sabunta dan daga ganin ta ba'a wani hau ta sosai ba, tana hango yadda ya saka su Ibty a baya cikin kula da takatsantsan kamar wasu sabbin jarirai kana ya shiga side din driver ya zauna. Tana ƙarasowa ta buɗe gaban motar da bisimillan da yaji ta sosai sannan ta zauna tare da rufe motar, hankalin sa yaji yana daɗa kwanciya da ita dan yana son mutum me addini da kiyayewa wanda tun a irin tambayoyin da yake wasu Ibty kan makaranta ya tabbatar da tana da ilimi gwargwado dan komai in ya tambayi kan suka iya se suce momma ce ta koya musu. Addu'ar fita da abin hawa yayi sannan ya tashi motar ya nufi gate tare da ficewa daga gidan...........................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 025 [ 12/11/2022 1:00 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                      Paid page 025 _________________________📖 Rayuwa ta cigaba da tafiya yara na girma har Abdallah yakai shekaru shida sannan Allah ya kara bawa Hajiya Babba ciki, wannan karon kam irin addu'ar da tayi kan Allah ya sa ta haifi namiji ba kaɗan bane, sedai Allah yafi kowa sanin abinda ya dace da bayin sa shiyasa ya kuma bata mace a karo na biyu. Irin kukan da Hajiya Babba ta yi a haihuwar Nadiya Kai kace mutuwa akayi mata, yarinyar kuwa seda baba yayi mata jan ido sannan ta haƙura take shayar da ita, bori kuwa irin wanda tayi baze fadu ba, shikam baba har mamakin raunin imanin ta yake yi dan kirikiri tace wai yafi son Ummu dama shiyasa yayi mata cikin namiji ita kuma da baya son ta yake mata na maata. A lokacin be iya ce mata komai ba dan ya fahimci bata hayyacin ta, shidai yayi murna da ƙaruwar da ya samu na wannan kyauta da Allah ya bashi, ya kashe kuɗi kamar me, kayan jaririya kam kamar za'a bude store amma duk hakan be dada hajiya Babba da kasa b, ita da burin ta ta haifi namiji. Haihuwar Nadiya yasa Abdallah ya makalewa sashen Hajiya saboda Allah ya zuba masa son yara wanda tun kafin ya kai haka Ummu ta gane dan in taje barka da shi da kyar ake karbar jaririn a hannun sa dan rigima yake sawa dole se an basu sun tafi dashi gidan su. Hajiya wadda tsanar Abu Aulad ta gama ginawa a ran ta tun ta uwar sa da kuma son da baba ke.masa se ta samu damar mammake shi in ya shigo wajen Baby nadee Kamar yadda yake kiran Nadiya. Duk dukan da zata yi mishi baya hana ya gama kuka kuma ya koma anjima, tun Ummu na damuwa har ta zuba ido kawai ta ƙyale shi dan akan yara kam baya ji baya gani. Duk wani kuɗin break ɗin sa akan Baby nadee yake ƙarar dasu lokacin, daga ƙarshe saboda dukan da Hajiya ke masa se yake dauke yarinyar ya tafi da ita sashen su, haka Hajiya zata bishi ta karewa Ummu zagi ta karɓe yarta a wajen shi bayan tsarabar dukan da ze Sha Amma Ummu bata taɓa ce mata komai ba dan akwai ta da kawaici da ɗauke kai. Wata rana da yaje daukar nadiya Hajiya ta ganshi ta kwace ta tare da tankade shi har ya kai ga faduwa ya fasa kai ne Ummu ta tanka hajiya Dan seda ta sille ta tas ta kuma zane Abdallah da ya fara amsa sunan Abu Aulad tun a lokacin dan ya bata mata rai, a cewar ta da be je ba ai ba za'a ji masa ciwo a cuce ta ba. Tun daga ranar Ummu take kulle Abu Aulad a sashen su ta kuma sa baba ya siyo Masa kayan wasa na yara maza masu yawa, daki guda ta ware masa ta shirya masa su wanda hakan ya sata samu sauƙin kuncin da ya fara shiga kwana biyu. Tsakanin Nadiya da Abdulkarim shekara uku ne wanda lokacin Abu Aulad ya shiga jss one kasancewar sa yaro me kwazo yasa akayi ta masa tsallake a primary dan har se da ya zo yafi saudah aji, watan Abdulkarim biyu da haihuwa Ummu ta bar duniya salin Alin ba ciwon komai, an kwan ta da ita se tashi aka yi aka ga babu ita, daren ranar dama ita ke da baba, tana ta shirye shiryen zuwa wajen sa har ya gaji da jira ya biyo ta sanadin da basu koma sashen ta ba kenan suka kwana a nan ashe kwanan bankwana suka yi. Mutuwar ba ƙaramin dukan baba da Abu Aulad tayi ba dan irin son da baba ke yi mata se da mutane suka tausaya masa yadda ya koma, Abu Aulad kuwa miskilancin sa yasa baya da wasu abokai haka ko yan uwa ba sake wa yake dasu ba, mutum biyun nan sune shi, sune duniyar sa wato Ummun sa da baba se kuma aka tashi yau babu Ummu a duniyar tasa, hakan yasa ya sususce sosai dan da ƙyar ya dawo hayyacin sa, sedai ya sake zama miskili har fiye da da. Lokacin da Hajiya Rahma tazo da batun rufe sashen Ummu kuwa sun ga tashin hankali wajen Abdallah, dole haka suka haƙura suka bar masa sashen dan yace shi yana so a nan se cigaba da rayuwar sa. Tun daga lokacin Abdallah ya zama Maraya amma partially dan baba na tsaye a kan sa, kulawar sa kan Abdallah ta ninka da, baya fita aiki se ya tabbatar Abdallah ya shirya sun tafi tare ya kai shi har cikin school ɗin, in ya dawo aiki hankalin sa baya kwanciya se ya tabbatar yaci abinci sannan ya zauna dashi yayi ta masa labarai da fita har se yaga dariyar sa tukunna, baya har sashen se Abdallah yayi bacci. Kamar lokacin Nadiya haka ma yanzu dan Abu Aulad na warware wa ya maida sashen Hajiya Babba daily routine din sa dan kullum se ya shiga yaga Abdulkarim yayi masa wasa sannan ze tafi makaranta, in ya dawo ma haka ze shiga ya bata lokaci wajen sa, kuɗaɗen sa kuwa duk na Kareem ne, kayan wasan da ya siyawa kareem da kudin sa ba zasu irgu ba hakan yasa yaron ya saba dashi har tsalle yake daga zaune in ya gan shi. Hankalin Hajiya babba ba ƙaramin tashi yayi ba dan ko kadan bata son abinda zesa Abu Aulad ya rabi ƴaƴan ta, gashi yanzu bata da damar ganawa saboda yadda baba yake matuƙar sa ido kan Abdallah da duk motsin sa. Cikin haka rayuwa tayi ta tafiya har Abdulkarim ya shekara hudu lokacin ne kuma Hajiya tayi nasarar raba shi da Abu Aulad dan dama ragowar yaran duk ta cusa musu tsana, hassada, ƙyashi, bakin ciki da tsananin ƙiyayyar sa dan tace musu shi kadai baban su ke so saboda yana son babar sa ita kuwa saboda baya son ya shiyass baya son su ƴaƴan ta tun da in haihuwar namiji ne ai gashi nan itama ta haifa. Abu Aulad be ji dadi ba lokacin da ya fahimci yaron baya son ko bin hanyar da yabi, gashi yayi ta masa rashin kunya in guri ya ƙure suka haɗu, hakan yasa ya janye jikin sa daga Abdulkarim dan shi ɗin ya tsani raini da rashin kunya, saboda sabon halin kareem wata ran se da ya mare shi, marin da sanadin sa yasa kareem ɗin be sake gigin yi masa rashin mutunci ba. Tun daga lokacin ya koma rayuwar sa shi kadai, daga shi sai baban sa da ya zame masa uwa ya kuma zame masa uba, se ko kakannin sa da yakan je sa'i da lokaci, Hajiya Rahma ba ƙaramin so da kaunar shi take ba dan in da ta Tata ne to ita zata riƙe shi sedai yadda ya nuna gidan baban sa yake so bangaren mahaifiyar sa yasa dole ta haƙura. Cikin ikon Allah rayuwa ta cigaba da tafiya har ya kammala karatun sa wanda a shekara Allah yayi wa Hajiya Rahma rasuwa a hanyar ta ta zuwa garin su wajen yan uwan ta, dangi da kowa yaji mutuwar tun bare ma Abu Aulad da baba da suke ganin sun kuma rasa wani ginshiki na rayuwar sa, dake shi Allah babu ruwan sa ko wata biyu Hajiya bata yi ba shima Alh Ahmad ya bita da dama shi bashi da lafiya ana dai rakawa ne. A wannan lokaci ne Abu Aulad suka tabbatar da basu da kowa se junan su dan baffa Usman wato ƙanin baba ba mutum ne me zumunci ba, babu ruwan sa da su se in ta kama hakan yasa babu shaƙuwa tsakanin iyalan baba da na baffa Usman ɗin. Dawowar sa cikin estate din su kuwa baba be ya roki alfamar dashi da babar shi wato kishiyar Hajiya Rahma su dawo nan ɗin da zama dan family ɗin su su hadu waje ɗaya. Zaman su tare ne ma ya ɗan sa ake mu'amala dan matar sa Hajiya Hauwa babu ruwan ta, ƴaƴan ta ne dai suka gado baban su dan ba ruwan su da kowa rayuwar su suke yi su kaɗai. Itama mahaifiyar baffa bata wani jima ba ciki estate din ra rasu suka dai zama basu da kowa face junan su se yan uwan nesa da baba ya nemo ya saka cikin gidan su dake Gamji dan kar a rufe gidan bakowa. Hala rayuwa ta ke garawa Abu Aulad har ya fara karatun sa a nan Garin dan ba yadda baba be yi ba kan yaje wata kasar ya kiya dan baze iya tafiya ya bar mahaifin da yake ganin shi kaɗai ya rage masa garkuwa ba. A makarantar muka haɗu dashi duk da tare muka yi primary amma ba wani shaƙuwa tsakanin mu, haɗuwar mu a University department daya ne yasa har muka kai matakin da muke yanzu dan nace masa nayi na like masa tun da na fahimci shi ɗin extraordinary ne dan duk irin wahalar course a few a wajen Abdallah ba komai bane. Tun yana yakice Ni da nuna halin ko ina kula har ya hakura ya kyale ni dan duk wulaƙancin da yake min bana fushi balle zuciya saboda nasan ni nake nema, sannu a hankali har ya fara sabawa dani duk da bawai ya canja halin sa na miskilanci da Shariya bane amma haka nake jurewa. Yau da gobe ba ta bar komai ba, cikin ikon Allah muka gama makaranta cike da nasarori da dama dan a shekarar mu mijin ki shine best students na gaba daya year ɗin mu kuma shi ne overall a department din mu haka da first class ya fita. Akace me uwa a gindin murhu, cikin jin daɗi mukayi service ɗin mu muka gama ba wani tension dan baba ya tsaya mana aka bar mu a garin mu aka kuma bamu inda muke so wato Companyn baba, muna gamawa muka fara aiki da baba in da Abu Aulad ke matsayin manager ni Kuma mataimakin sa. A iya tsayin wannan shekarun gaba ɗaya mijin ki be taɓa yin budurwa ba hatta irin ta wasan nan da ake yi na yarin ta, hasalima shi any stuff related to women babu shi a ciki duk kuwa da yadda su matan ke tsananin so da bibiyar sa, a rayuwar makarantar mu zuwa gamawa ba zan iya ce miki ga adadin matan da suka so Abdallah ba dan shi ɗin mutum ne mai matukar farin jini. Kyan sa, kuɗi da kuma halin sa na miskilanci shike ruɗa yan mata suke mutuwa a kan sa, ke in takaice Miki ba iya yan mata kadai ba hatta zawarawa son Abdallah suke, wata lecturern mu haka ta mutu kan Abdallah sedai shi gogan baki be taba sanin sun ayi ba, wanda ya sanin ma je didn't give a damn, harkar gaban sa kawai yake yi shiyasa yawancin su ta hanya ta suke biyo wa kan na taimaka musu saboda tsananin kwarjinin sa yasa basa ko iya tunkarar sa. Ko da muka fara service coppers mata da suka fola masa bana iya kididdigewa, haka ma a Company, ke abin se da ya fara bani tsoro saboda yadda mata ke faɗa dashi a Companyn baba, shikan sa seda ransa ya ɓaci saboda wasu da suka yi dambe katitir a tsakiyar compound, wai duk son shi suke shine suke kishi da juna. Sallamar su da yayi tare da kafa tsattsaurar doka shi yasa muka sami saukin abin ba wai fa amma an dena bane. Nafisaaaahhhh"........ Haisam ya ja sunan yana sake numfashi kafin ya cigaba. ........"nafisah itace mace na farko da ta fara samun kusanci da rayuwar Abdallah, kusancin da bayan ita ba'a kuma samun macen da ta same shi ba se da kika shigo rayuwar sa. Nafisah da ƙanwar ta Nuriyya marayu ne da suka rasa mahaifin su hakan yasa rayuwa tayi musu wahala duk da dama tun asali mahaifin nasu bame karfi bane, be mutu ya bar musu komai ba face bashin kudin hayar gidan da suke zaune hakan yasa rayuwa tayi musu zafi dan basu da sani mai taimaka musu, yan uwa kowa fama yake da kan sa ga kuma yadda zumuncin zamani ya zama. Rashin kudin da zasu biya bashin baya su cigaba da zama a gidan yasa me gidan ya kore su, rashin wajen da zasu nufa yasa suka koma karkashin gada da rayuwa. A irin wannan yanayin baba ya biyo hanyar gadar da suke da daddare ya yi katarin ceton nafisa da wasu bata gari ke neman ɓatawa rayuwa, yadda yaji labarin su ne abin ya taba shi hakan yasa ba bata lokaci ya kira driver a waya yazo da mota ya kwashe su zuwa estate. Ɓangaren ma'aikata yasa aka sauke su suka kwana kafin washe gari ya basu sashe a gidan, tsananin nutsuwar nafisa da ya gani yasa yayi wa Abu Aulad sha'awar auren ta dan yarinya ce me hakuri, bata da hayaniya ga girmama na gaba da ita sabanin yar uwar ta Nuriyya da ta kasance me rawar kai, rashin kunya da ɗagawa sabida kyan da take dashi. Ko da baba ya tuntuɓi Abu Aulad da maganar nuna masa yayi babu mace yanzu a gaban sa yayinda shi kuma baban ya dage dan a ganin sa a shekarun Abu Aulad 28 a lokacin ya kai minzalin da ze yi aure dan yana buƙatar ganin zuri'ar sa kafin shima lokacin sa yayi. Farin cikin da Hajiya ta shiga lokacin ba kaɗan bane dan jin za'a aura masa yarinya mara galihu me kwana ƙarƙashin gada hakan yasa ta shiga zuga baba cikin kissa har se da ta tabbatar an yi auren. Rayuwar Abu Aulad tare da nafisa ba wata abar ƙarar wa bace dan be saki jiki da ita ba kasancewar tun yana University ya daina ci da shan komai na gidan nasu bisa wani al'amari da ya faru da har yau be sanar dani ba sedai abun ya taba shi sosai ya kuma saka masa rashin yarda da mutanen duniya har ma da wanda ke amsa sunan ahali a gare shi. Shekarar su biyu da nafisa batare da ya kalle ta a matsayin mata ba kafin Allah ya karkato da hankalin sa kanta ya ke mu'amalantar ta kadaran kadahan dan duk wanda ke tare dasu ze gane sam babu soyayyar nafisah tare da Abdallah, yana dai zaune da ita ne saboda baba, Shekara biyu da rabi da auren su ta sami ciki, cikin da sanadin sa nafisa ta san waye Abdallah saboda tsananin kula da tarairaiyar ta da yake yi, soyayya da kaunar da yake wa cikin tun kan yazo duniya daban ce hakan yasa ta dinga jin kamar kar ta haihu dan tasan wannan soyayyar ba tata bace ta cikin ce. Ranar da ta haihu kuwa anga fara'a da dariyar Abdallah kamar baze daina ba, karin farin cikin sa da ta haifi yan biyu duka mataaa..............✍🏻. Kwana biyu bana editing ku karba da har pls👏. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 026 [12/12/2022 11:13 AM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                       Paid page 026 _________________________📖 Tun da akayi haihuwar Abu Aulad ya tare a wajen ya'yan sa, ba ruwan sa da yan barka haka ze yu zaune a daki riƙe da ƴaƴan yayi ta kallo yana murmushi kamar wanda ya sami tabin hankali, yan barka kuwa da ƙyar yake bada yaran a kai musu wasu ma sedai suyi Barka batare da sun ga ya'ya ba suna wajen uban su. Sunan da akayi a lokacin seda duk faɗin ƙasar nan ya amsa saboda yadda ya kashe kuɗi yayi wadaƙa, sutturar yaran iya wadda ya siyo musu se an bude madaidaicin shago dan daki guda aka cika da kaya, hatta uwar yaran seda ta san ta haifi ƴaƴan gata dan akwati Ashirin da hudu yayi mata na haihuwa abinda ko a lefen ta be yi rabin sa ba. Raguna kam akori kura aka ciki da su aka dinga yankawa kawai, kar ki ce ƙananan raguna, sam irin wnada suka ci suka koshi har kamar zasu fashe dan kiba, banda shanu uku da aka yanka. Kai hidimar da Abdallah yayi a haihuwar yaran nan ba zata fadu duka ba dan se mu cinye dan Lokacin da muke dashi ban gama wassafa miki ba. Wani abin jin dadin kuma kwanan su biyu a duniya ya ajiye aikin da yake yi a Companyn baba sabida ya gama ginin nasa na kan sa budewa kawai ya rage dan hatta ma'aikata an gama diba, ranar suna mata na bikin suna a gida mu kuma muka yi namu bikin bude Company ɗin wanda ke amsa sunan A.A GAMJI CONSTRUCTIONS. Ko ban faɗa ba nasan kin fahimci wannan Company ɗin nake nufi, cikin hikima da taimakon Ubangiji muka fara aiki tukuru domin dai Abdallah bai yarda ya dauki unqualified workers ba, duk wanda kika gani a Companyn nan sai da ya tabbatar da cancantar sa kafin ya bashi aiki. Kafin kice me A.A GAMJI CONSTRUCTIONS yayi suna a faɗin garin nan saboda nagartar aikin sa, sannu a hankali ya fara zama well recognize sabida kwazon ma'aikatan, ban ga laifin wanda suke yabon Abdallah kan yadda ayyukan Company ke tafiya ba dan a rubuce yake da ba'a sami jajirtaccen shugaba ba kamar sa ko da kuwa an iya ba lallai ayi mai karko kamar yadda ake yi yanzu ba, sedai Abdallah ba me sakaci ko wasa ne akan duk abinda ya shafi aiki ba, tsayayyen mutum ne me ra'ayi da akida dan baya shakkar hukunta duk wanda ya taka doka, hukuncin da ko da kuwa kora ce ta kama dan yace duk maaikacin da yake tunanin ba za'a iya sallamar sa ko hukunta shi saboda wani baiwa nasa, ilimi ko kwarewa ba to ya gwada taka ɗaya daga cikin dokokin aiki. Da taimakon baba muka kai matsayin da Companyn yake a yanzu wato sananne a kasa baki daya domin kuwa ya shiga ya fita ya haɗa mu da manyan mutane sosai, mu kuwa kokarin mu shine yi musu aiki ne inganci ta yadda gobe su da kan su zasu bukaci service ɗin mu kuma mun yi Nasara domin hatta da shugaban kasa yana bamu kwangilar gine gine ban da kuma yan siyasa. Ina nace zan zauna lissafa miki nasarar da Companyn nan ya samu daga shekarar buɗe shi zuwa yanzu tabbas zamu iya wuni bamu gama ba sedai koma me ya zama kokarin Abdallah ne sannan a zo kan mu da ragowar ma'aikata. Nasan zaki ce me yasa kai baka nemi aiki a wani wajen ba se karkashin Abdallah bayan matakin ilimin ku daya ne haka kuma kwalin ku, ba komai ne ya zaunar da ni tare da Abdallah ba face shaƙuwa, ƙauna da kuma halin sa domin nima mahaifi na da nasa dukiyar daidai gwargwado, nasan ba zaki rasa jin As-saif motors ba, to ire iren su duk na babana ne. A haka zaki yi wa Abdallah kallon baudadden mutum, miskili mara dadin sha'ani, me girman kai da wulakanta mutane ko kuma me ɗagawa ko?, To sam wannan ba Abdallah kika suffan ta ba. Shi ɗin mutum ne me sauƙin kai, nagartacce me hakuri da kau da kai, ba shi da wulaƙanci sedai yana da miskilam ci wanda wannan kuma dabi'a ce kuma halayya tasa da har abada ba Wada ya isa ya sauya masa domin haka me kowa ya yo shi, Abdallah bashi da girman kai sedai yana da gudun wulaƙanci, ya tsani rashin kunya haka kuma yana raba hanya da duk me yin ta, matsala ɗaya a halin shi itane rashin yarda wanda zan iya ce miki ba halin sa bane rayuwa ce ta koya masa bisa tilas haka kuma in dai kika kiyaye abinda duk ze yi zargi ki ka zama me gaskiya da riƙon amana da sannu zaki rabashi da ita dan ba halin sa bane koya yayi. Mu dawo ga labarin mu salma, bayan haihuwar twins sosai budi yake sake shigowa rayuwar Abdallah dan cikin wata ɗaya da buɗe A.A Gamji constructions ya buɗe GAMJI SHOPPING MALL Wanda ake wa lakabi da GSM inji mutane, bayan shi kuma ya fara ƙoƙarin buɗe shagon sai da wayoyi sedai hakan be samu ba saboda ƙaddarar da ta faɗo rayuwar sa a lokacin, ƙaddarar da ita ce ta tafi da sauran fata, buri, jin dadi, walwala, hadi da kwanciyar hankalin Abdallah. Kamar yadda muka saba in ze yi tafiya to dole ni ya kasance ina nan saboda kula da harkokin kamfani, in Kuma Ni zan tafi to shi ze zauna. A wannan karon tafiyar tasa ce dan nine nayi ta karshe kasancewar kamar shifting muke, wannan karon in naje, next shi kuma se yaje, ba komai yasa tafiyar ta zama me mahimmanci ba sedan zeje ya gana da Companyn infinix, Samsung, iPhone, Huawei da ragowar manyan kamfanonin waya saboda shagon da ze buɗe, kar dan nace shago ki ɗauka wai ƙaramin waje ne, no babban estate ko ince miki complex muka gina wanda gaba ɗaya ze zam ba harkallar da ake yi cikin sa face wireless business, ciki shine y hada da wayoyi, computers, manyan headphone, da dai duk abinda ya shafi hakan. Wannan tafiya itace ta zame masa bakar tafiya shiyasa ko daga baya be kuma sha'awar harkar ba se ma Saida complex din da yayi. Har airport na kai su shida twins da maman su, tun da muka shiga Mota yaran na hannun sa har muka kai airport ɗin, ko da muka je ba'a fara diban passengers din da zasu tashi ba saboda ana servicing jirgin, haka ya zauna a kan kujera ya ƙanƙame yaran duka biyu a ƙirjin sa kafin ya ciro su ya zubawa fuskar su ido, kallon su yake yi ba ko ƙiftawa fuskar sa cike da wani yanayi, hakan ba bakon abu bane gare mu ni da maman yaran sabida in ze yi tafiya haka ze ta kallon yaran kamar yayi kuka dan baya son yin nesa da su ko kadan. Ko da aka fara kiran mutane be bada yaran ba har aka dinga kiran sunan sa kafin da ƙyar na amshe su a hannun sa na mikawa nafisa, idanun sa cike da ƙwalla ya juya ze shige nafisa ta kira shi cikin wani murya me rauni wadda tasa dole y dakata tare da juyowa, kallon ta ya tsaya yi kafin da ɗan sauri ya dawo wajen su ya haɗa da ita da yaran ya rungume gaba ɗaya har tsayin mintuna kusan uku kafin ta fara janye wa jin ana sake kiran sa, hannun sa yasa ya riko fuskar ta karo na farko ya fara share mata hawayen da ke gudu kan kuncin ta sannan yayi pecking goshin ta "Na yafe miki mom twins". Ya faɗa dan yasan se ta nemi tafiyar sa dan haka take masa duk lokacin da ze yi tafiya, lumshe ido tayi hawaye na sake gangaro mata "I love You Abdallah, ina son ka Daddyn twins". Numfashi ya sauke me nauyi kafin karon farko again ya furta mata kalaman da bata taɓa tsammanin jin su ba daga bakin shi, kalaman da ta sawa ranta har abada ba zasu taɓa fitowa daga bakin Abdallah zuwa kunnen ta ba. "I love You too Mom twins, so very much, pls take care". Yana fadar haka ya juya da sauri ya shige, haka muma muka juya na maida su gida. Ban san me ya faru ko ya akayi ba, kwana biyu da tafiyar sa ya kira ni a rikice wai ina nafisa, me ya sami yaran sa, sam se ban gane inda kalaman sa suka nufa ba, da kyar yayi min bayanin wai yana ta kiran ta tun jiya da dare har zuwa yammacin yau amma be same ta ba. Haka yasa na tafi estate din dan duba masa su, sedai abinda aka sanar dani yasa naji jiri na shirin jefar da ni da dole na nemi waje na zauna ina ambaton Allah a raina. Wai nafisa ta fita unguwa tun jiyan da rana amma har yau ba ta dawo ba, an bi bayan ta gidan kawar ta da taje yiwa barka tace ai tun jiyan suka yi sallama ta koma. Yanzu dai an sanar da jami'an tsaro kuma suna kan aikin neman su amma har yanzu ba'a gan ta ba, abin tashin hankalin wai gaba ɗaya cikin gari ko alamar motar ta babu balle kuma su. Ban iya na fadawa Abdallah wannan bakin labarin ba domin bani da karfin halin hakan, ina ji ina gani na kasa daukan duk kiran da yake min wanda ya kira nin yafi so hamsin daga ƙarshe ma se kashe wayar nayi. Kashegari kawai se ganin mutum muka yi ya shigo lokacin muna estate din nasu muna shawarar a fara bin ƙauyukan garin ko za'a dace, hankalin sa ba ƙaramin tashi yayi ba dan kwasar sa akayi zuwa asibiti ya yanki jiki ya fadi, dukkan mu bamu yi mamaki ba da likita ke sanar da mu jinin sa ne yayi mugun tashi irin wanda ba'a so na farar ɗayar nan ga kuma faduwar da yayi wanda ba dan Allah ya kare ba se ya samu stroke. Baba muka bari wajen sa muka shiga neman nafisa da yaran ta ido rufe sedai har dare ya rufa ba wani alamu na za'a gan ta, washegari na haka muka kuma bazuwa, bamu ba ba jami'an ba. Se bayan kwana uku jami'ai suka samo motar ta da kusan rabin ta ke kone a can hanyar barin gari, gaba ɗaya ita da yaran sun kone dan ba'a gane kamannin su musamman ita traces na wasu sassan jikin ta da basu gama ƙonewa ba kawai aka samu, lambar motar tata ce, wayar ta ma an samo ta amma ta kone sosai, takalmin kafar ta, mayafin ta har da ragowar atamfar jikin ta se rabin fuskar ta, yaran kuwa sun kone sosai da ba'a gane ko fuskar su, Bama su da kyan ganin da mutum ze so yi sake kallon su, haka aka yayyafa musu ruwa aka nannaɗe su cikin likkafani. Iya tashin hankali mun shiga a lokacin saboda baba dagewa yayi se Abu Aulad yazo kan gawar matar sa da ƴaƴan sa haka dole aka dauko shi daga hospital zuwa gida, sedai a kallon farko da yayi musu sumewa yayi a tsaye sedai gani akayi ya tafi ze fadi hakan yasan nayi azamar tare shi, ruwa aka dinga zuba masa da yasa yaja dogon numfashi, yana buɗe ido ya zabura tare da fincikewa daga jikina ya koma gaban gawar, ba wai mutuwar ce tasa yake neman haukacewa ba a'a irin yadda yaga yaran sa da matar sa ne yake birkita masa kwanya. Wani irin ja baya yayi kamar wanda wuta taja saboda fuskar yaran da yayi arba da ita, durƙushewa yayi ya fara fisgan numfashi saboda katsewa da yayi daga huhun sa sedai ya kasa nan take ya kuma zubewa, in takaice miki dai daga ƙarshe janye shi akayi daga kan gawar dan ba abinda yake se sumewa, suman karshe kuwa da yayi har an saddakar dashi ma ya tafi kafin ya farfaɗo, Abdallah be taɓa bani tausayi ba kamar na lokacin, gaba ɗaya ya birkice bashi da abin yi illa kuka hakan yasa jikin sa sake birkicewa dole akayi asibiti dashi, daga ƙarshe dai dole fitar dashi akayi waje saboda kullum jinin sa sake hawa yake ba sauka ba ga kuma zuciyar sa da ta kumbura, abinda ya bawa likitocin tsoro shine irin bugun da zuciyar ke yi ga kuma kumbura da take yi kullum sama da baya, watan sa uku a can kafin ya farfaɗo daga comar da ya shiga, seda ya dauki wata biyu kafin ya fara responding to maganar mutane ya Kuma fara magana, at least dai Abdallah se da ya bata shekara a kasar Jamus saboda likitocin sun rike shi, da taimakon Allah da taimakon addu'ar baba da ta masoya ya fara dawowa daidai saidai duk sanda abin ya dawo masa haka idanun sa ke yin jajir kamar su fitar da jini, kan sa kuwa ya dinga tsananin ciwo yayinda ƙirjin sa ma ke amsawa, dole ba yadda likitoci zasu yi su hana shi tuna bayan sa hakan yasa muka tattaro muka dawo tare da tulin magungunan da aka dora shi akai. Dawowar mu muka tarar da wani sabon tashin hankali domin dai wata karuwa ce da tayi suna da kuma fice ta makalewa baba, duk yadda baba yaso yakice ta daga jikin sa ta kiya gashi har duniya ta fara sanin shi da ita dan duk ƙasar da yaje tana biye dashi, ko ina bin sa take shi kuma baban ya kasa mata rashin mutuncin da zata bar shi ko kuma ya haɗa ta da security, lokacin da Abdallah ya tunkare shi a batun budar bakin sa se cewa yayi son ta yake, wannan furucin ya sake sa Abu Aulad cikin wani hali dan gaba ɗaya baba ya Fara bata musu reputation, ba wai yana biye mata suna sabon Allah bane, ba kuma kama su akayi tare ba haka ba ganin su a kayi a gurin da bai dace ba sedai kasancewar sa babban mutum sananne kuma nagartacce yasa ganin ta tare dashi ya zama abin surutu ga jama'a tare da zargi da sharri ga maƙiya. Shekara kusan biyu ana abu ɗaya kafin daga ƙarshe baba ya aure ta wanda shine ya kawo karshen wannan rikicin, se sabon matsala da ta bullo tsakanin Abdallah da amaryar baba wadda ba zan ce miki komai akai ba domin wannan magana ce tsakanin ku, shi zai miki bayanin komai duk da bana tunanin nan kusa amma nasan ko be miki ba tabbas watarana idanun ki zasu gane miki. Shigowar Hajar wato amaryar baba rayuwar estate din ta Fara canja salo dan kam iya shegen ta take salo salo, Hajiya babba ba ƙaramin wahalar ta tasha ba dan cikakkiyar yar bariki ce da ke juya baba cike da kissa da kisisina ta hanyar da bazai taba ganin laifin ta ba, salon ta be dore sosai ba tashi ɗaya muka ga baba ya dawo se abinda Hajiya Babba ta ce masa yake aikatawa, duk kuwa abinda tace me kyau ko akasin sa to fa wajen baban me kyau ne tar...........................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 027 [ 12/12/2022 11:29 AM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK* Paid page 027 _________________________📖 Tun daga lokacin Abu Aulad ba shi da wani sakat dan komai yayi cikin laifi yake wajen baba haka zata zuga shi yasa shi a gaba da faɗa da zagi, akwai wani lokaci da tace yayi mata rashin kunya haka baba ya sashi gaba da zagi da cin mutunci har dasu mari abinda kaf a rayuwar sa tun daga yarinta har zuwa girman sa baba be taɓa daga hannun sa ya kai jikin sa da sunan duka ba. Hatta Ummu watarana da ta taɓa marin shi haka baba yasa ta gaba da faɗa kamar ze ari Baki dan ban da Allah ya rufa asiri Abdallah dan ta ne ba da har rama masa ze iya cewa ze yi, se gashi da kan sa ranar ya daga hannu ya kai fuskar Abdallah da sunan mari wanda a lokacin shekarun sa na haihuwa 34 ne. Rayuwar Abdallah ta sake yin zafi dan yanzu bashi da wajen da ze raba yaji daɗi, kullum cikin damuwa da tunani yake ga kuma Hajar da ta sako shi gaba itama da nata sharrin hakan yasa dole ya kaura ya bar musu estate din ya koma ɗaya daga cikin gidajen sa da rayuwa. Barin sa gidan ma be tsira ba dan haka Hajiya ta zauna ta tsara baba kan ya koma gidan sa ne dan su daina sa masa ido yayi irin rayuwar da ya ga dama, wai an faɗa mata ya fara biyewa abokan banza yana bin mata shiyasa ya gujewa idanun su haka kuma shine dalilin da yasa yaki aure har yanzu. Irin cin mutuncin da baba yayi wa Abdallah a lokacin maƙura ne dan ko makiyin sa iya jifan sa da mugayen kalaman da ze yi kenan, ranar se da ciwon sa ya tashi amma baba ko a jikinnsa haka ya tsallake shi ya bar shi kwance baya ko cikin hayyacin sa. Jin shiru be zo ba bayan yace min akwai takardun daze kawo min yasa na bishi gidan shine fa na tarar dashi cikin wannan halin har na nemo likita ya duba shi. Bisa umarnin baba dole ya rufe gidan ya koma estate da rayuwa inda Hajiya Babba ta kuma ɓullo da sabon jidalin auren shuraiha da take so yayi. A karo na farko da Abdallah yayi wa baba turjiya ya rufe idanun sa yayi musu rashin m dan ya fahimci wannan baban ba baban sa bane na da wannan baban wani ne daban da aka sauyo shi, wannan baban ba me son shi bane, wannan baban wani remote control ne na Hajiya dan se yadda tayi dashi kawai shi kuma be shirya sakin ragamar rayuwar sa ga matar da ta nuna masa tsantsan ƙiyayya da tsana ba tun yarinta har zuwa girman sa dan ko da mutuwar twins da maman su ba ta masa gaisuwa ba balle jajen halin da yake ciki hakan yasa ya yarda duk duniya ba shi da makiyi sama da ita domin ta sha faɗa masa ba so daya ba baso biyu ba ta tsane shi, bata son shi bata son bude idanu taga yana rayuwa. Kamar maganar shuraiha kar ta mutu baba ya dinga kawo masa tallan mata wanda duk zaɓin Hajiya ne dan yace dole se yayi aure baze lalata masa suna a banza ba, sedai ko so daya Abdallah be taɓa bude idanu ya kalli matan ba hasalima da aka kai shi karshe gar da gar ya faɗawa baba be shirya aure ba, kuma ko ya shirya baze taɓa auren matar da ta fito daga tsagin makiyar sa ba. Kiran Hajiya Babba da yayi da makiyar sa yasa Abdulkarim cike da rashin kunya ya taso wai zai yi faɗa da Abdallah sedai yayi babban kuskure musamman a lokacin da zuciyar Abdallahn ke kusa dan bas ya balla masa hannu bayan ya sharara masa marin da yasa yayi mutuwar wucin gadi. Kukan da hajiya Babba ta fashe dashi yasa jikin baba ya shiga mazari tun bare da take ambatar ya karya wa Abdulkarim hannu, mari mafi kaskanci baba yayi wa kuncin Abu Aulad ma'ana on both cheeks, be iya cewa komai ba se kafe baba da yayi da idanun sa da suka yi mahaukacin jaa kamar wanda aka watsawa dakakken barkono a ciki, irin kallon da yake yi wa baba yasa jikin baban yin sanyi yayinda can cikin zuciyar sa ke masa zafi na ganin tashin hankali da damuwar gudan da mafi soyuwa a zuciyar sa hakan yasa ya ɗago hannun da ya mari Abdallahn Yana kallo fuskar sa cike da wani yanayi me kama da rashin jin dadi. Juyawa Abu Aulad yayi ya fita zuciyar sa na bushewa da komai ma in da yasha alwashi kome baba ze yi baze taɓa yarda da matar da zata fito ta hannun babbar makiyyar da yake tunanin kaf duniya bashi da kamar ta ba. Tun da lokacin suke cikin wannan takun sakar wanda ana cikin haka ne kika shigo rayuwar sa, am sorry to say amma na dade ina bibiyar rayuwar ki domin tun a satin ki na farko a ma'aikatar nan na shaida ke ɗin daban ce hakan yasa na shiga bibiyar ki da duk wani motsin ki domin kuwa zuciya ta na faɗa min zaki iya fitar da abokina daga halin sarkakiyar da rayuwar sa ke ciki, ina me baki haƙuri domin kuwa nine na dauki wannan hotunan lokacin da kika nemi faduwa ya tare ki, ban yi dan bata miki suna ba illa na son hada alkhairi sedai bani da wata mafita da ta wuce hakan domin ko nace Abdallah ya aure ki baze taɓa yarda ba dan yace sam babu mace a gaban shi, shi da mace har abada, shiyasa na ɓullo masa ta hanyar da na san dole ze haƙura domin shi ɗin me tausayi ne ba ze so sunan ki ya ɓaci saboda shi ba. Jaridar duk da kuka gani shiri ce domin makudan kudade na biya aka buga min iya adadin da nake buƙata, ni na aikawa baba da ita haka ni na kawo ta office din Abdallah har guda Ashirin saboda in ɓatar Masa da hankali dan in ya ganta kaɗan yana iya darsa wani abu a ransa domin be da yarda ko kadan amma da ya ganta da yawa ko da zai yi karar gidan jaridar se da nasan yadda nayi na bashi haƙuri tare da bukatar ya bar komai a hannuna zan sa a hukun ta su sedai ba abinda nasa akayi masu dan BA SU DA LAIFI, Ni na zauna na nuna masa faidar auren ki domin ze zamo makamin da SIRRIN BOYE ze bayyana kasancewar akwai abubuwa da yawa da muke zargi a mutuwar nafisa, dole akwai abinda ya faru dan haka kawai ba abinda ze sa nafisa tafiya hanyar barin gari balle har tayi hatsarin da ya dau ranta dana ƴaƴan ta, a yadda akayi reporting motar tayi bindiga ne sedai ko da aka kawo motar gidan manta a rufe yake, ga kuma warin fetur da take yi shaidar akwai wani abu a ƙasa, abubuwa dai da yawa da se yana da aure ne komai ze bude. Bayan auren ku da na tabbatar nayi nasarar kulla shi na kona jaridun dan amfanin su ya kare dan haka ki cire komai a ranki duniya babu kallon da take miki domin ba wanda yaga hotunan nan. A takaice dai wannan shine tarihin rayuwar Abdallah, wannan itace rayuwar mijin ki salma!". Shiru salma tayi kan ta na kasa, kallon agogo Haisam yayi tare da dan zare ido ganin yadda lokaci ya tafi sosai "Shin kin shirya taimakon mijin ki salma?, Kin shirya daidaita rayuwar mijin ki?, Kin shirya dawo masa da farin cikin da ya rasa na tsawon shekaru biyar?, Kin shirya damarar yakar makiyan dake zagaye dashi?, Shin zaki taimaka masa ya gano BAƘIN ƘULLIn (my next book 💃) dake sarƙe da rayuwar sa? Kin shirya sama masa nutsuwa, kwanciyar hankali da amincin ruhi?, Kin shirya zaman aure da Abdallah salma?, Ki bani amsa salma?, Kin shirya yin yaki domin mijin ki ko a'a?". Hannun ta dake rawa ta kai kan table ta yagi tissuen dake ajiye ta shiga share hawayen tausayin rayuwa Abdallah da suka kasa tsaya mata, wani irin kwarin gwiwa take ji, wani irin zumma take ji, tausayin sa na ratsa mata zuciya, burin ganin sa cikin farin ciki na dabaibaye nata ruhi haka kuma tsananin zafi da jin haushin Hajiya babba da duk wani makusancin ta na cika ranta, tabbas kome ne ne zata yi akan shi, rayuwar shi da ta ta na kamanceceniya sedai tasa ƙaddarar tafi tata tsauri, ita tasan dukkan iyayen ta mutuwa suka yi, duk da mutuwar da maman ta tayi ba me daɗi bace amma Gara ita akan shi da ya kalli gawar iyalin sa daidai har uku kwance a lokaci daya, bayan babban rashin bango kuma jigon sa da yayi wato Ummu ga kuma WATA ƘADDARAR (shamsiyya manga) ta bangaren baba, lallai yaga jarrabawa shima a rayuwar shi. "Na shirya ya Haisam, na shirya yin komai da ka ambata dama wanda baka lissafa ba, tsananin tausayin sa da nake ji a raina yasa naji zan iya yin komai a kan sa, ban damu da za'a cutar dani ba, ban da mu da kome ze faru ba, abu ɗaya zuwa biyu na sani shine ina buƙatar farin ciki a rayuwar Daddyn twins haka bana buƙatar duk abinda ze taɓa min yarana, shin ya zan yi?". Ta faɗa tana rushewa da kuka, ada yaran ne kawai rayuwar ta amma a yanzu tana jin ba zata iya rayuwa me kyau batare da Daddyn su a kusa da ita ba, bata ce ya kalle ta ba, bata ce ya so ta ba, bata ce ya kula ta ba ita dai in dai za ta dinga ganin sa to bata da wata damuwa ko kadan. "Ya Isa salma, kiyi shiru ki daina kuka kinji ko, naji daɗi da naji wannan kalaman daga bakin ki haka hankali na ya kwanta na tabbatar na sakawa Abdallah Alkhairan da ya dinga yiwa rayuwa ta ta hanyar sama mishi uwar yaya ta gari. Batun ƴaƴan ki insha Allah babu abinda ze same su, kina musu addu'a kullum kina kuma kula dasu, na kuma tabbata a yadda na ga Abdallah na son su ze fi ki sa ido akan dukkan lamuran su dan haka hankalin ki ya kwanta insha Allah ba abinda ze Sami babies din mu". "Allah yasa yaya Haisam, yanzu yaya zan yi kenan ina nufin wace rawa zan fara takawa dan ganin na hau matakin nemo wa Daddyn twins farin ciki?". "Babban mataki a yanzu shine ki samu kusanci dashi, duk wata hanya da kika san zata kusan ta ki dashi ita zaki bi salma, duk da nasan hakan is not easy dan nasan waye Abu Aulad amma in kika dage kika kiji kika ki ganin duk abinda ze miki na rashin kirki tabbas zamu yi Nasara, dan ko a yanzu haka ina hango ta dan ban yi zaton ze ci abincin ki so soon haka ba". Sanyi jikin salma yayi da ta tuna yadda yake tsare ta ta fara cin kome ta dafa kafin yaci "Ai ba dan ni yaci ba, Ifty ce ta dage shiyasa ya hakura yaci kuma se da yasa naci dan ya tabbatar ban zuba komai ba tukunna". "Ki manta da duk wannan ki maida shi ba komai ba domin nasan yana da dalilin hakan, baze yi dan tozarta ki ko wulakantawa ba sedan yana da ƙwaƙƙwaran hujja, na faɗa miki tun yana University ya daina cin komai na gidan su sedai ya dafa ko yaci kayan leda, duk da be faɗa min dalilin ba amma dole nasan yana da alaka da rashin yarda da cin abincin ki, amma ko ba komai mun yi nasara, abinda nake so dake yanzu shine ki kwantar da hankalin ki ki koya wa kanki rashin ganin laifin sa ko da kuwa laifin yayi dan hakan ne zesa zuciyar ki ba zata dinga zafi ko daukar fushi ba balle har ki ji kina son fasa aikin dan kuwa Abu Aulad na da kayan ban haushi kashi kashi da dole se kin kautar da kai. Abu na biyu kuwa shine dole ki mu'amalanci mutanen estate din haka kuma cikin ma'aikatan kowane ɓangare ya zama kin ja wasu a jikin ki ta yadda zamu dinga bugar cikin su dan jin wani abu game da mutanen dan muna zargin kashe nafisa da ƴaƴan ta akayi ba wai hatsari ne na Allah ba, dan Allah salma ki taimaka mana mu cimma abinda muke fata dan hakan wani babban fata ne na dawo da ko kaso daya ne na farin cikin mijin ki". "Na riga na amsa zan yi ya Haisam haka kuma bana jin akwai abinda zesa na dakata dan haka ka kwantar da hankalin ka insha Allah komai ya kusa zuwa karshe, shi kuma zan jure ko me ze yi tunda ni nasa kaina, ai sa kai yafi bauta ciwo". Ta faɗa tana ɗan murmushi, shima murmusawa yayi yana mata godiya "Bari na koma bakin aiki na lokaci ya tafi sosai bamu lura ba". "Ga kuma mafadacin mijin ki a kusa dan ma ba ruwana kun fi kusa kin san yadda zakiyi dashi in ya fara fadan sa da ya saba, haba mutum kullum aiki kamar wani inji". Ita dai bata ce komai ba se murmushi da take yi ta fita shikuma ya cigaba da ƙananun mita kan halin Abu Aulad na son aiki kamar wasu saƙaguna. Ko zama bata yi ba wayar kan table ɗin ta ta shiga ƙara, seda gaban ta ya ɗan fadi ganin code ɗin office din sa dake yawo kan karamin screen na landline din. "Ki shigo yanzu ki same ni". Tsam tayi jin abinda ya faɗa batare da ya amsa ko sallamar da tai ba, da alama dai ya san bata nan duk da ta riga ta gama ayyukan ta amma dai tasan fadan da ze yi baze mata daɗi ba dan yana bala'in girmama duk wani abu da ya shafi aiki. A hankali ta tura ƙofar ta shiga kanta a ƙasa tana tafiya kamar ba zata yi ba dan haka kawai taji wata shakkar sa ta cika mata rai. Tafi minti goma a tsaye be kalle ta ba balle ya nuna yasan Allah yayi ruwan ta a wajen, tun tana tsayuwa da daɗi har ƙafafun ta suka gajiya ta nemi jikin bango ta jingina, seda ya gama signing wasu tulin takardu dake gaban sa kafin ya ɗago ya kalle ta lokacin akalla tayi minti fiye da talatin a tsaye a wajen......................✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel:                       Paid page 028 _________________________📖 "Since when kika tashi a aiki?". Ɗagowa tayi ta kalle shi cikin rashin fahimtar me yake nufi, "Don't lemme repeat myself". "Sir ban yi closing ba tukunna, it's not yet time". "Then we're have you been for the past one hour?". Shiru tayi dan bata fiya son yin ƙarya ba in ba guri ya ƙure mata ba domin sabo da karya nasa ko yaushe a dinga wa mutum kallon makaryaci ko da kuwa gaskiya ya fada. "I'm with sir Haisam, we discussed about something". "Something?". Ya fada with an interrogative tone "He let me outta the dark akan issue ɗin wasu takardu dana kasa fahimta" Shiru yayi na wasu sakanni kafin ya nuna mata hanyar ƙofa alamun ya sallame ta. Seda ta sauke wani makalallen numfashi da take riƙe dashi tun da ta shiga office din kafin ta saka hannu ta dafe ƙirjin ta, kai gaskiya kwarjinin mutumin nan yayi yawa, magana take amma cikin ta juyawa yake saboda kar ya gane ba gaskiya ta faɗa masa ba duk kuwa da cewa da gaske he unmasked everything to her yadda zata fahimta amma ai ba takardu bane. Haka ta cigaba da zama cike da tunanin labarin Abu Aulad tana jujjuya komai a ranta tare da sake yi masa fashin baki ta yadda zata kara fahimtar komai da kuma yadda zata ɓullowa kowa. A yanzu kam ta fahimci ware kanta da take a part din ta baze yiwu ba dole ta shiga cikin ahalin ayi da ita ya kuma zama dole ta jure duk wani wulaƙancin su sedai ba zata yi shiru gaba ɗaya ba kar a raina ta fiye da wanda aka yi mata. Abu ɗaya da ya tsaya mata a rai shine taya zata fara samun kusanci da Abu Aulad?, Wannan shine tambayar dake ta yawo a kwanyar ta amma har yanzu ta kasa gano hanyar da hakan ze yiwu. Ta san dai kawai dole ta ringa kasa shisshigi kenan ko, eh to shisshigi mana tunda tun farko ya nuna ba ya bukatar ta kusa da duk abinda nda ya zama personally nasa ne amma gashi zatai crossing limit din ta. Lokacin tashi na yi ta tattara komai ta aje inda ya kamata kana tayi signing out ta fice, yau ma a parking lot na company ta tadda drivern ta yana jiran ta, ba bata lokaci ta shiga yaja suka fice daga building din tare da nufar makarantar su Ibty. Wanka tayi musu ta canja musu kaya zuwa na shan iska sannan ta baje musu kayan wasan su a bedroom ita kuma ta Fito ta shiga aikin gidan. Komai da ya kamata se da ta gyara a part din dan har zaman kujeru seda ta juya tsarin, se falon yayi kamar wani sabo, ƙamshi kuwa ko kai waye wajen hassada dole ka sara mata dan har ya kama gurin a dan zaman da tayi wanda yau ta cika sati. "Huh". Ta fitar da numfashin gajiya dan aikin nan mutum ɗaya ba sauki, dakin sa ta kalla wanda tun ɗazu take san shiga ta gyara sedai ta rasa courage din yin hakan, yanzu kam runtse ido tai ta dake ranta tare da karfafawa kanta gwiwa ta nufi ɗakin. Hannu na rawa ta murɗa handle din take kuwa dakin ya buɗe, seda ta ɗan yi jim a tsaye kafin tayi summoning courage ta shuga da salma a bakin ta duk da tasan babu kowa a ciki. Kusan wannan shine karo na farko da ta fara shigowa dakin dan wancan zuwan daga bakin ƙofa ta tsaya yanzu kuwa ga ta a tsakiya. Dakin na da girma sosai dan yafi nata fadi da zurfi, a wadace yake dan san babu natsuwa acikin sa, ƙaton bed din sa da ya ci kusan ɗaya cikin ukun dakin se wardrobe din sa da ta mamaye bangon gurin da take, dressing mirror ɗin sa dake nan kamar na wata sabuwar amarya saboda yadda yake a tsare shaƙe da mayuka da turaruka kala kala. Carpet din da ya fara tun daga bakin bed din zuwa ragowar filin dakin, rug ne me tsananin taushi dan tun shigowar ta taji kafar ta ta nitse a ciki, sam dakin sa babu kazan ta sedai kuma ba a tsare yake yadda ya kama ta ba. Kayan sharar hannun ta ta ajiye ta ta shiga gyara masa dakin, gaba ɗaya ta sauke mayuka da turarukan sa daga kan mirror ɗin ta goge sa tas har se da ta ga yana ƙyalli sannan ta maida ta canja musu tsari. Ita kanta seda mirror ɗin ya bata sha'awa sedai bata tsaya ba ta nufi bed din, tana daga duvet din sassanyan ƙamshin sa ya shige hancin ta, tsabar daɗi da kaunar da take wa turaren seda ta lumshe idanu kafin ta matse duvet din a ƙirjin ta tana jin wani yanayi me daɗi na ratsa ta, seda ta shaki ƙamshin iya son ranta sannan ta cire shi daga jikin ta ba dan ta gaji da shi ba sedan aikin dake gaban ta dan ko girki bata yi ba. Tsayawa kawai tayi tana kallon gadon da ta dame da sabon saitin bedsheet da ta dauko cikin wardrobe Wanda se da tayi mamakin ganin yawan bedsheets din sa, wnn ko mace ma se wadda tayi dace ta zo ita daya a gidan masu kudin da suka amsa sunan su dan fa seda ta tsaya ta irga su ganin kamar suna mata gizo, bedsheets har guda Ashirin da huɗu, tab lallai masu kuɗi nayin yadda suka ga dama. Yadda ta tsara gadon ta jera komai yadda ta gani ana yi a wasu vedio, da kyar ta kau da kan ta daga gadon ta shiga sharar dakin, carpet din kuwa gaba ɗaya ta daga shi ta bubbuge duk yadda yake da nauyi haka ta daure sannan ta ajiye shi a gefe ta share marbles din tare da yin mopping sannan ga maida ta shimfida rug din. Se a ta huta dan gaskiya da gajiya sannan ta shiga toilet ta wanke masa ba tare da ta tsaya kallon ya tsarin sa yake ba dan ta fahimci in bata yi wasa ba gaba ɗaya a dakin nan zata lalace, boxers ɗin sa biyu da singlet da ta gani ta wanke masa su tas tare da busar dasu da na'urar busar da kaya kana ta sa masa a wardrobe wajen undies da ta gani. Tana murna ta gama komai se saka turare kawai se kuma ta ankara da wata ƙofa dake gefen wardrobe din wadda bata lura da ita ba se yanzu, tana buɗe ƙofar ta saki baki gaba ɗaya tana bin ko ina da kallo. Da sauri ta fito ta buɗe wardrobe ta shiga daddaga kayan da hannu, se lokacin ta lura da cewa wai ashe undies ne kaɗai a cikin wardrobe din se jallabiyas, se Kuma bedsheets din sa, jiki a sanyaye ta koma ɗakin ta shiga bin jerin kayan sa dake tsare da kallo, gaba ɗaya dakin an mai dashi dressing room ko closet zan ce ne dan cike yake da kaya nau'i nau'i kala kala, kama daga kan suits, coats, traditional Attires, ƙananun kaya zuwa kan sleeping dresses, gaba ɗaya dai dakin cike yake da kaya iya ganin ka dan gasu nan lodi lodi, gefe ɗaya kuwa wajen takalman sa ne da suna wasu shirgi ne na daban, huluna, belts, da ragowar tarkace. A hankali ta shiga gyara arrangements din takalman wada shine kawai ya birkice amma komai na dakin neat yake. Tana gamawa ta jona burner ta saka turare sannan ta fita main bedroom din Shima ta saka, seda ta jira yayi yadda ta ke so sannan ta zare socket din tare da fitar da burner falo shikuma bedroom di ta sake fesa sassanyan air freshener me ƙamshin berries. Alas a kitchen tayi birki ta shiga ƙoƙarin haɗa dambun shinkafar da take son yi, sam girki be bata wahala shiyasa cikin kankanin lokaci ta kammala komai tare da jerewa bisa dining, da gudu tayi daki jin ana kiran magrib, wanka tayi tare da shirya wa cikin straight skirt pusha Pink se rigar sa milk, rigar bata da hannaye se igiyoyin da ake ɗaurewa a kafada, ba ƙaramin kyau tayi ba kamar a sace ta a gudu, gyara gashin ta tayi tare da saka hula ta tura ta can baya ta yarda gaban kan ta dake ɗauke da kwantattun gashi masu taushi da santsi ya bayyana, turaren ta me daɗin ƙamshi ta fesa sannan ta zura tattausan room slippers din ta me taushi kamar jikin mage ta fito falo inda ta tarar da yaran ta na wasa, haɗe kayan tayi ta mayar sannan ta saka suka yi alwala suka yi sallah ban da ita da ta cigaba da kallon ta dan yau tana fashi. Se da ya tsaya yayi isha ya shigo gidan yau ma a gajiye, ba abinda yake bukata a lokacin kamar wanka se kuma abinci dan wuni guda ba abinda yaci. Suna falo gaba ɗaya lokcin yaran na yin homework din su ita kuma ta maida hankali ga kallon citrus TV da ake hada wani smoothie, gaba ɗaya hankalin ta na can dan duk abinda suka yi ko zuba tsab kwakwalwar ta ke riƙe shi. Ihun yaran ne yasa ta juyo dan ganin me ya faru se kuwa tayi arba dashi rungume da yaran da suka ruƙunƙume shi har yana yar da ƴar saman suit din sa, cikin bawa kanta kwarin gwiwa tana faɗa wa kan ta she's on a mission ta tashi ta karasa inda suke durƙushe ta ɗauke masa rigar sa dake kasa kana ta juya zuwa ɗakin sa. Be lura da inda tayi ba abinda ya sani ya ji ƙamshin ta daf dasu sedai ko da ya ɗago daga pecking twins tuni ta bar wajen shima be kuma maida hankali kan ta ba ya cigaba da biyewa yaran duk da gajiyar dake tare dashi dan when it comes to children he's more than simple haka kuma yana iya barin komai dan ya saurare su. Ita kuwa a can har wani ajiyar numfashi tayi ganin be biyo ta ba ta maza ta kai masa suit din closet sannan ta koma toilet ta haɗa masa ruwan wanka, wajen zuba turaren wanka ne ta shiga al'ajabin ganin su kala kala a jere cikin wani cupboard kamar za'a bude karamin kan yi banda su shower gel, shaving creams da shaving stuffs, haka dole ta janye idanun ta ba dan ta gama kallon toilet din ba sedan sanin a kowane lokaci me dakin ka iya shigowa. Seda ta fito masa da kayan zaman gida da taga yafi amfani dasu wato three quarter da t-shirt ta feshe su da turaren sa sannan ta fita, lokacin kam dafi'an yana gyarawa yaran inda suka yi ba daidai ba a homework din su, wuce su tayi zuwa kitchen ta ciro sassanyan kunun gyadar da tayi daga fridge ta Kai dining tare da ɗebo tumblers din da za'a yi amfani dasu ta aje. "Sannu da zuwa Daddy". Ta fada lokacin da ta lura ya gama koya musu yana kallon yadda suke yi, batare da ya ɗago daga kallon littafin ba ya amsa mata da yauwa. Bata damu da yadda ya amsa ba dan dama tun zuwan ta gidan amsar gaisuwar ta lafiya ce haka ma sannu da zuwa yauwa ne in ma ya ga damar amsawar kenan. Seda yaran suka gama gaba ɗaya sannan ya tattara musu litattafan yasa musu a jaka yace sukai daki kana ya tashi zuwa nasa dakin, tun da ya bude kofar ya tsaya kawai yana kallon dakin ba tare da ya shiga ba, ganin yadda yake wa dakin wani irin kallo yasa gaban salma faduwa dan tun da ya nufi ɗakin dama take cikin fargaba haka kuma idanun ta na kansa cikin son ganin reaction din sa. Da sauri ta maida kanta kan wayar hannun ta ta shiga shafawa batare da ta san me take yi ba dan juyowa yayi gaba ɗaya ya zuba mata mayatatttun idanun sa masu matukar kaifi da kwarjini da yasa take gudun jinin ta ya karu ga kuma wani zafi da taji yana ratsa jikin ta da bata san daga ina yake ɓullowa ba haka kuma kusan duk AC biyun dake falon a kunne suke. Iya dauriya tayi wajen ganin ta hana kan ta ɗagowa ya kalle shi dan bata don ma kallon idanun sa balle da tasan ba kallon arziki zata samu daga cikin su ba, tsawon minti biyu yana hukuntata da kaifafan idanun sa kafin ya janye ya juya ya shige ɗakin nasa cike da takun sa dake daya daga cikin abinda salma ta fi so a tattare dashi. Wayar ta ajiye ta shiga yiwa jikin ta fita da hannun dan se lokacin taji iska ta fara ratsa jikin ta haka kuma gudun jinin ta ya fara raguwa, "Ya ilahil Alameeen". Ta faɗa tana sakin ajiyar zuciya akai akai kamar wadda tayi tseren gudu. Anya kuwa zata iya wannan aikin alhalin de dinga tsare ta da wannan idanun nasa da bata taba jin tasirin wani ido akan ta kamar yadda take jin nasa ba, minti ɗaya baya kafin ya janye idanun sa ji take gaba ɗaya tayi rauni, gaba ɗaya ya hallaka dukkan wani karfin hali da kwarin gwiwa da take dashi da kallon da yake mata, a lokacin ji tayi ba abinda take so face ta fashe da kuka kawai dan har idanun ta sun fara tara ƙwalla se kuma ya janye, ta tabbatar da be janye ba ba abinda ze hanata fashewa da kukan da bata san ma'anar sa ba ko kuma dalilin yin sa. Jiki ba ƙwari ta tashi domin tuni ya raunana ta yayi tafiyar yaji da dukkan wani kuzarin ta, a sanyaye ta bude kofar dakin ta ta shiga ta wuce toilet direct, ruwan sanyi ta kunna tare da saka hannun tana tara ta a watsawa fuskar ta wai ko ta samu ta dawo hayyacin ta. Tsayin lokaci kafin ta koma ta jingina ajikin bangon toilet din hannun ta dafe da ƙirjin ta ta rufe ido, 'Karki karaya tun yanzu, zaki iya salma, tabbas zaki iya, ki daure domin wannan yakin ba gudu ba ja da baya a cikin sa, yaki ne da dole nasara kike bukata a cikin sa domin faduwa ki na nufin cigaba da rayuwar Abu Aulad cikin kunci ko ma ki rasa shi gaba ɗaya, domin ina aka cigaba da tafiya a haka zuciyar sa ka iya gazawa daga nan kuma kin rasa shi, rashi na har abada'. Da sauri ta buɗe idanun ta tare da kallon mirrorn toilet din ta shiga girgiza kai saboda wannan maganar da wani sashe na zuciyar ta ya mata "No, baze yiwu ba, baze taɓa faruwa ba, ba zan rasa shi ba, zan rayu dashi zan kuma mutu dashi dan haka baze tafi ya bar ni ba, am more than ready to protect him, zan yi yaki domin shi, ba kuma zan ja da baya ba har se nayi nasara da izinin Ubangiji". Tana fadar haka ta ji gaba ki daya kuzarin ta ya dawo har ma fiye da da, taji ba idanun sa ba ko hannun sa ze sa mata zata jure zata dauka in har zata yi galaba dan haka tayi saurin fitowa daga toilet din taja hannun twins zuwa falo.................... Ouummey✍🏻. Ouummey 📚✍🏻. [12/13, 10:37 PM] Maman kalisat Novel: Ouummey 029 [ 12/13/2022 8:48 PM ] ★★★ *ANJANE* ★★★ (Rashin sani) ★★★★★★★★★ _*PAID BOOK*_ Story/written by Ouummey. Wattpad @ouummey. From The author of: *HAƘORIN DARIYA* *ƘASAR MU A YAU* *BA NI DA LAIFI* *SARAKI (the accused prince)* *ABOTA CE KO SOYAYYA* *And now.......ANJANE (Rashin sani) PAID BOOK*                       Paid page 029 _________________________📖 Kamar ta aika Ifty ta kira shi se kuma zuciyar tace mata take da kanta kawai hakan ma wani abu ne. Knocking tayi har so uku kana ta tura ƙofar tana faɗa wa kanta kusan minti talatin da something din da yayi a dakin yaci ace ya gama shiryawa. Kan sofa ɗaya ƙwal dake dakin ta gab shi zaune da waya a hannun sa gefen sa kuma laptop ce da alama ya ajiye ta ne ya huta ko kuma ya gama aikin da ze yi da ita. Yaji Knocking din da tayi amma ba maida hankali ba a tunanin sa twins ne yasan kuma zasu shigo shiyasa ko yanzu be ɗago ba yayi magana "Angel din Daddy ce ko kuwa prettyn Daddy ce?, Oya come and tell me what and what you did at school". Jin abinda yace yasa tasan be san ita bace so se ta buɗe baki "Ehm Daddy abinci is ready". Surprisingly ya ɗago kansa zuwa inda yaji Muryar ta, take kuwa sukai four eyes dan bata tsammaci ze ɗago ba shiyasa take kallon sa ganin be saka kayan da ta fito masa dasu ba. Itane ta ɗauke nata da wuri dan bata shirya ya sake raunana ta ba, shikam duk ya kalli kwayar idanun ta sha'awa da burge shi suke yi shiyasa baya ko yunkurin janye nasa, kamar zeyi magana se kuma ya fasa ya cigaba da aikin da yake yi. Shiru shiru tana jiran taji ya taso amma ba shi da ko alamun hakan se kawai ta juya ta fita, duk da yaji fitar Tata amma be ɗago ba sedai cikin ransa wani irin jin haushin ta ne na saba umarnin sa da tsallake iyakar ta, se da ya faɗa mata kar ya kuma ganin ta a dakin sa amma dake bata da kunya shine har da yi masa wani gurgun gyaran ta da be burge shi ba sam se ma bata masa rai da yayi sannan dake ita a rashin kunyar pro ce ta kuma biyo shi daki tana faɗa masa wani abinci is ready tunda ga mayunwaci da be saba cin abinci ba, da wani bakin ta me wari a nan. Yamutsa fuska yayi tare da yin ƙwafa be ko maida bakin sa daidai ba twins suka bude kofa suka shigo, sakin fuska yayi tare da yi musu smile Yana nuna musu gefen sa, da sauri suka ƙarasa suka zauna ya ɗau laptop din sa ya ɗora kan laps din shinya shiga danne danne can ya juyo musu da ita, cartoon ne ya kunna musu, irin educational cartoons din nan, aikuwa cikin murna suka shiga kalla har dashi. Kofar ta buɗe a karo na biyu ta shigo riƙe da tray kan sa shaƙe da warmers din da ta zuba abincin, hankali kwance ta aje a gaban kujerar da suke zaune ta juya ta fita da sauri batare da ta kalli inda suke ba balle taga ita yake kalla ko cartoon din duk da yana jin slight effect na idanun sa a jikin ta. Haka ta dinga ɗebo kayan har ta maida komai dakin sa sannan ta nemi gefe kan carpet ta zauna ta shiga danna wayar ta batare da tace dasu komai ba. Shi da kansa ya kashe kallon dan yau twins sunyi daren bacci saboda basu ci abinci ba ga kuma kallo, a yadda yasan su na sati ɗaya karfe takwas ma sunyi bacci ko suna shirin yi, yanzu kuwa gasu har tara saura mintuna biyu. "Daddy muje muci abinci, momma ta dafa mana delicious ko mom?". Barin game ɗin da take bugawa tayi ta ɗago ta kalli Ifty da tayi maganar "Sosai ma kuwa Angel, har kunnen Daddy se yayi rawa". "Laaah, Daddy kaji har kunnen ka ze yi rawa, pls muje muci in gani in zeyi". Ibty tafada ido zare kana ta shiga jan hannun sa kan ya tashi, itama Ifty taya ta ta shiga yi tana faɗin "Come Daddy, zo muje muci daɗi, kasan momman mu ka the best cook fa". Haka suka dinga jan shi da dole ya tashi yana makawa salma harara jin wai har shi ne zata ce kunnen sa se yayi rawa akan jagwalgwalon ta, duk da ta ga hararar amma bata damu ba se ma murmushi da ta saki tana kau a kai daga kallon sa ta shiga serving din su dan fa yaran basu sake shi ba seda suka kai shi gaban abincin. Duk da ya gasgata batun ta na cewa se kunnen sa yayi rawa amma be bari fuskar sa ta nuna ba haka ya cigaba da cin abincin cike da jin daɗi, tabbas ya yarda da abinda Ifty tace, their momma is the best cook, ko da bata zama bestest ba yasani she most be amongst the bestest. Haka suka ci abincin ba me magana se karar cokula kawai da suke tashi, yana ajiye spoon ta jawo tumbler ta cika masa shi da kunun aya, duk yadda yaso kar yasha amma ina zuciyar sa taki bashi hadin kai dan kuwa se zillo take masa a ƙirjin sa tana faɗa masa ita tana so, dole haka ba dan yaso ba ya maze ya dauki cup din ya kai bakin sa, tun da ya lumshe idanun sa be buɗe ba har se da ya shanye gaba ɗaya , be jira ta kara masa ba yasa hannu ya jawo jug din gaban sa ya sake cika kofi ya kai baki, wasa wasa se da yasha kofi uku sannan ya ajiye tare da yin relaxing bayan sa jikin kujera yana maida numfashi. Irin koshin da yayi ya manta rabon da yayi irin sa kafin yanzu, hamadala kuwa a zuciyar sa yayi wa Allah tafi dubu, cikin jin daɗi salma ta mike ta fara kwashe kayan kwanikan zuwa kitchen, ɗaga yadda yaci abincin sosai ya kuma shanye fiye da rabin kunun ayar ta tabbatar ta sami nasarar gamsar dashi ta nan ɓangaren, hankalin ta ya kwanta da ganin yadda yake samun nutsuwa da girkin ta, in da ta dauri niyyar faranta zuciyar sa da daddaɗan girkunan ta, kai ita se ta koma catering school ko da na online ne in har hakan se dadada ran sa. Se da ta kwashe komai sannan ta gyara wajen kana ta dubi twins "Tohm, babies a wajena zaa kwanta ko a wajen Daddyn?". Da sauri kowacce ta fadi ra'ayin ta "A wajen momma". "A wajen Daddy". Dariya tayi jin kowanne ya fadi sabanin na dan uwan sa ba kamar yadda suka saba bin ra'ayin juna ba. "Ibty kizo mu kwanta wajen Daddy Kinga shi ba kullum kullum muke kwantawa a wajen sa ba irin momma". Gyaɗa kai Ibty tayi alamar ta yadda da abinda Iftyn ta faɗa "Eh momma zamu kwanta wajen Daddy". "Then goodnight". Ta faɗa tana juyawa zata tafi, da sauri Ibty ta ruƙo hannun ta tana jan ta kasa wai ta tsuguno tai mata kiss, tsugunnnawar tayi ta mata itama Ifty ta mata kana ta fice daga ɗakin. Buɗe hanci tayi tana shaƙar numfashi sosai bayan ta karasa dakin ta, duk da abinda tayi ƙarfin hali ne da dauriya dan internally ji take kamar ace kyat ta zuba da gudu dan fargaba. Wanka tayi ta sauya kaya zuwa na bacci tayi addu'a sannan ta kwanta. Karfe biyu na dare ta farka, fitsari taje tayi sannan ta ɗaura alwala kana ta dawo ɗaki ta kalli gabas ta shiga gabatar da nafilolin da ta ƙudure wa ran ta yi, cikin kowacce sujjada kuwa se ta rattaba wa Allah bukatun ta cikin kankan da kai da yakinin yana ji yan al'umma ganin ta ze kuma amsa mata. Bata kuma samu ta runtsa ba dan har akayi kiran sallan asuba tana kan praymat, tana idar da sallar subh ta fita nema musu abinda zasu ci, tana gamawa ta fitar dining ta dawo hada musu snacks dim da zasu tafi dashi school. Ba ita ta fito daga kitchen ba se wajen bakwai da minti biyar, a gurguje ta koma ɗaki tayi wanka sedai bata saka kaya ba dan kar taje shirya su Ifty ta jika kan ta, se kawai ta bar towel din da ta ɗaura ta zura hijab akai ta nufi ɗakin Abu Aulad. Da sallama ta shiga bayan ta buɗe sedai ganin su a shirye tsaf yasa ta saki ajiyar zuciya ta koma batare da ta karasa shiga dakin ba, kayan ta ta shiga sawa tana tunanin sauƙin hali irin na Abu Aulad ɗin wasu lokutan, yanzu dai dubi yadda yayi musu wanka ya saka musu kaya tsaf kau baka ce namiji ne ya shirya su ba se tashin ƙamshi suke yi, lallai matan da mazan su ke taya su hidimar guda yan gata ne dan ita yanzu da be shirya su ba ta tabbatar se sun makara. A gaggauce ta gama shirin ta fito hannun ta ɗauke da handbag din ta, kan dining ta nufa inda ta gano su zaune suna karya wa dan ko da ta karasa se ta ga har ma sun kusa gamawa, a tsattsaye itama ta karya kana ta dau jakan ta da basket din su ta fita tare da rufe sasshen ta yi parking lot dan ta san can zata same su. Cikin mamaki take kallon yadda aka gyara sashen kusa da nata yayi wani irin dau yana ɗaukar ido tsabar yadda yasha gyara yayi kyau, haɗiye mamakin ta tayi ta yi gaba tun da bata da hurumin in za'a kawo wasu se ta sani, ita zuwan yanzu yanzu dan bama zata ce ɗazu ba. Yau ma haka ta wuni a Company din tana aiki, duk san da ta samu space kuwa tunanin ta yadda zata kaddamar da aikin gaban ta dake jiran ta sedai har yanzu juya i yau ne domin dai bata samo wata mafita ta daban ba haka dole ta haƙura. Yau ma bata daddara ba se da ta shiga dakin nasa ta gyara cikin ranta kuwa mamaki ne take yi yadda be rufe ba shi da yace baya son a shigar masa, bata wani yi nisa ba ta kore mamakin ta yi abinda ya kai ta, yau kam bata bar dakin ba se da ta karewa ko ina kallo ta bawa idanun ta abinci, toilet kuwa da ta shiga sam ba wani datti kamar ma ba'a yi amfani dashi ba amma haka ta sake wankewa, yau ma bata fita ba to se da ta bade ɗakin da ƙamshin turaren ta wuta me daɗin ƙamshi kana ta bishi da sassanyan air freshener sannan ta rufe masa. Yau kam teba tayi me kyau da miyan kubewa busasshiya, bata san a ina aka siyo ba ita dai ta bawa daya daga cikin masu gadin kuɗi ta faɗa masa kubewa take so, ita a yadda ta faɗa ma danya take nufi se gashi da busasshiya ta kuwa daku tai kyau, bata Gwale shi ba ta karɓa tare da yi masa godiya. Gaba daya ƙamshin miyar ya cika gidan banda kuma farfesun cow leg da tayi wanda ya wadatu da kayan yaji da kuma magi da spices. Ta dade tsaye gaban wardrobe din ta kafin ta zaro wata bakar atamfa me golden ta warware tana kallo, doguwar riga ce amma bubu sedai an wadata ta da stones caba caba hakan yasa take ga reflecting, sawa tayi ta kalli kanta a mirror, ba tun yau ba atamfar na mata kyau sedai na yau din se ta gama kamar ya karu, ko da yake ita kanta ɗazu da safe da ta kalli kanta a mirror se taga ta canja, ta kara haske sosai ga kuma yar ƙiba kaɗan da tayi se jikin ta ya sake murjewa kyan ta ya sake fitowa. Zama tayi kan stool din mirrorn ta shiga naɗa daurin ɗankwali, cikin kankanin lokaci se gashi ta malkawada shi ya zauna a kanta cif cif yai kyau, gashin gaban goshin ta dake kwance suka kuma ƙawata fuskar tata, powder ta murza tare da wadata idanun ta da kwallin kajol, haka kawai ta samu kan ta da kara maskara kan zara zaran baƙin gashin idon nata ta kuma bi idanun da eyeliner, bakin takuwa sun sha lipgloss me danko nude color se pink lips din nata sukai wani irin sassanyan kyau me fizgar hankali. Ya subhanallah, ita kanta da ta gama gaba ɗaya ta kalli kanta se da ta zaro golden brown cat eyes din ta cikin tantamar anya ita ce kuwa, irin kyan da ta ga tayi seda ya firgitata, idanun ta a suka fi komai yin kyau a yau, wani irin ɗaukan hankali suke yi dan yadda ƙwayar cikin take ba baka ba ragowar kuwa fari ne tas hakan yasa kwallin da ta saka ya zauna daram, daga saman farar fatar idon kuwa ga nan bakar eyeliner, ga Kuma gashin idon ta da tun ainahi baki zara zara ne ya kuma sha bakar maskara se ya sake yin duhu ya kuma mike sosai. A hankali ta janye daga jikin madubin tana tasbih a ranta, wai fa komai be ki gyara ba ko, kai gaskiyar hausawa da suka ce ko kana da kyau ka kara da wanka, yanzu dai kalli ita ɗin nan ba wanda zece itace wadda taje aikin nan dazu, duk da dama da kyan ta amma kwalliyar ba ƙaramin sake fito da ita tayi ba. Falon ta zauna ta kunna wa twins dake shirye cikin gungun wando iya cinya fari da bakar riga me kamar shimi wanasha suna kallan wakokin larabawa ita kuma ta cigaba da karatun novel din da take yi na Ayusher muhd me suna A GIDANA, ba ƙaramin tafiya da ita salon labarin yayi ba, haka ma kuma jarumin ciki wato khaleed, gaba ɗaya se take ganin halin sa na mata kama da na gwarzon mijin ta Abu Aulad, yanayin miskilancin su, Shariya da iya bakar magana se take ganin kamar mijin nata aka suffan ta. Karatun take tana murmushin dramar khaleed da uwargida kuma amaryar sa zainab lokacin Bayan anyi auren su yadda yake tafiyar da ita, abin se ya ƙayatar da ita ta dinga jin dama nata mijin shima ze bata dama kamar haka duk da kuwa ita zainab ta cika son girma da bata so a ga gazawar ta balle ya raina ta a cewar ta. Tattausar Muryar sa da yayi sallama ta ratsa dodon kunnen ta ne yasa ta lumshe ido tana gyara zama kana ta ɗago ta dube shi dan har ya shigo falon, yau kam be zauna wajen su Ifty ba ya shige bayan sunyi welcoming nasa. A gurguje ya shirya ya fito, inda ya bar ta zaune nan ya same ta, "Ɗauko mayafin ki kizo, ki tahowa da yaran nan takalman su". Kallon sa tayi cikin son karin bayani sedai ganin ya tsuke baki yasa ta miƙe dan cika umarnin sa a ranta tana mamakin ina ne zasu da daren nan..................... ✍🏻. Ouummey 📚✍🏻.