💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 PROMISE OF THE HEART 💔 ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.hausanovels001.com.ng Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** ✍🏻M SHAKUR 1️⃣ ~UK~ Tundaga nesa take leke babban building din datake dumfara tana bin uban tulin cars din wajen da kallo kaman akwai abinda take nema kafin daga bisani idanuwanta su sauka kan wata white Bentley car, gashinan kar kar ko alamun a single dust babu ajikin motan, ajiyan zuciya tasauke ahankali murya chan kasa tace “Alhamdulillah he’s still around” sanan tashiga sauri takarasa gaban wajen da ake kira da Cozy, harzata saka hannu tabude kofan tashiga tadanyi jim tsaya kafin ahankali tabi jikin ta da kallo tana sanye dawani white jeans daya kamata tsam dawata yar dark blue top mai shegen kyau wacce da kadan tasauka daga kan cibiyanta, saidan gyalen data yana kanta white shima dayamata kyau sai gashin kanshi dakenan kusan rabi awaje anmata kalaba da attachment kanana dayamata kyau shima, hannunta rikeda wasu books guda biyu dakuma phone nata kirar iPhone 13, sai wata yar karaman jakan datake rataye da ita, ajiyan zuciya takara saukewa kana ganinta kasan she’s nervous sanan ahankali tasa hannu tabude kofan wajen tashiga ciki. Hadaden eatery ne and bar mai shegen kyau, babu wasu mutane dayawa awajen wayanda suke wajen yawancinsu turawa ne fararen fata maaikatan wajenma fararen fatane hakan yasa zaka gane wajen na bature ne, ahankali take tafiya tanabin wajen gabaki daya da kallo da gefen idanunta, kafin takarasa gaban kanta taja kujeran wajen ta zauna sanan tasauke books dinta agabanta da wayanta, daidai baturen Bar attendant din yakaraso yana kallonta yace “what can I get you miss” dan waigawa tayi kaman tana neman abu awurin tace “Pierre Zēro Rosé please, two shot” ganin duk tana maganan ne batare datama kalleshi ba yasa yace “gotcha” sanan yajuya yakoma yadauko wine din datai order yazuba mata a cups guda biyu sanan yadawo gabanta ya ijiye yace “here we go” dan juyowa tayi da sauri takallai sanan tasauke jakanta da sauri tadauko kudi taba shi tace “keep the change” kafin ma yay magana tasake juyarda kanta tana bin mutanen wajen da kallo one after d other….. “Kai Zayn look” wani hadadden chocolate guy daga tachan karshen babban falon wajen da aka cikada kujeru ne kowa na zaune yana abinda yake yataba wani kyakkywan thick farin guy dake zaune kan kujera ya lumshe idanu pipe din shisha na bakinshi yana zuka yana fitarda hayakin ta hanci, yana sanye da riga da wando both black na LV, farine shi kal yanada cikan jiki dayake rigan dayasa short sleeve ne hakan yafito da kakkauran murdadden hannunshi, irin guys dinan ne masu manyan gabobi dakuma murdadden jiki, dudda idanunshi a lunshe but idan ka kalleshi bazaka so kadauke idanunka ba dan yanada wani irin kyau kaman mace, lips dinshi sunyi wani kalan masifan ja kodan shishan dayake shane oho, yanada dogon hanci siriri dayazauna akan fuskanshi gwanin ban sha’awa, sai gashin giranshi baki sidik kuma acike yanada tabon salla agoshi sai gashin kanshi baki sidik shima dake kyalli sun nannade kaman na buzu sanan gawani kwantaccen saje a fuskanshi Masha Allah, koda ace shiyay kanshi bazaiyi kanshi da wanan kyau dinba ballema bashi yayba. Ganin baida niyyan amsashi yasa Mamu ya fizge pipe din shisha dake bakinshi yace “kafara ko ina maka magana kamin banza” ahankali yabude idanunshi dasuka wani lumshe sukai yaushi da idanda zai kalli mace dasu sai lissafinta yarikice sanan yazubasu kan Mamu kaman ance yay magana dan dole yace “what”? Dan murmushi Mamu yayi da hannu yamai alamu yace “look over to the counter ga budurwanka chan, stalker dinka tazo sai kallon ka take wlh, haba Zayn kaiko bazakaji tsoron Allah ka kula yarinyar nan koda sau daya bane tunda dai ta kasa maka magana for morethan 2months yarinyar nan kullum binka take tana stalking naka tana kallonka u know she really really likes u waikai maisa kacika wulakanta mata ne eh? Anyway I don’t blame you ni wlh in mace ne banmaga abin so ajikinka ba mutum dukgaka nan kalan asibiti farin fata kalan cuta, duk baku da karfi” dan murmushi yayi dan yasan Mamu so kawai yake yajashi suyita surutu this afternoon shikuma baida time dinan, hannunshi yamikamai alamun yabashi shishi shi, ijiye pipe din shishan Mamu yayi kan table din gabansu yace “Ya isheka hakanan gashinan duk idanunka sun chanza launi, munada lectures yanzun nan fa I think in the next 5min” dan tsaki yaja yasa hannu yadauki pipe din shisha yacigaba dasha abinshi yana daddanna wayanshi yana hura hayakin ta hancinshi batare dayama daga kai ya kalli inda Mamu yacemai yarinyar nan takeba Mamu nabinshi da kallo yarasa yanda zaiyi yaraba Zayn da shisha, shima bawai bayasha bane no but occasionally yakesha, shiko Zayn zai iya wuni yanashan shisha hakanma yasa baya iyacin abinci sosai, ganin yasake lumshe idanu yasa Mamu yaja tsaki yamike tsaye yace “dalla Malam wuce mutafi” bude idanunshi yayi dasuka dan kankance sukaija sanan ya watsama Mamu harara kafin ahankali ya ijiye pipe din yamike tsaye dogon namiji ne nagaske, budadde sanan kuma cikakke irin mazan nanne da ake kira da burin mata, car key dake kan table din yadauka yana rikeda wayanshi yay gaba abinshi batare daya cema Mamu komi ba yay hanyar kanta. Tundaga nesa ta hangoshi ya dumfaro gaban kanta, duk taku daya dazaiyi saita jishi har kirjinta yana amsawa, tun kafin ya iso wajen wani kalan kamshin dayakeyi dayake neman sata ta haukace sabida sonshi ya lullube mata hanci ganin ko’ina najikinta yadau kyarma yasa ahankali tasa hannu tadauki cup na drink dinta takai bakinta still tana kallonshi ta gefen idanunta daidai ya iso ya tsaya dab da ita dasauri bartender din yazo yace “u done sir” bai amsashi ba yasa hannunshi a wandonshi yaciro wallet dinshi yabude yana kokarin zaro kudi ko kadan batasan drink din yamakai saman hancinta ba tsabagen yanda take kallonshi kawai numfashin dazata shaka ta shaki wine din wani irin mahaukacin shakewa tayi dabama tasan lokacin data saki cup din akasa ba tana wani kalan mahaukacin tari wine nabin hancinta suna fita idanunta sunyi ja kwalla yacikasu dawani kalan sauri daga Bartender din harshi suka juyo suna kallonta dasauri Bartender din yataho ta saitin gabanta yace “sorry Miss” dudda tarin datake kokarin danne tarin take tana kakalo murmushi dan wanan kwafsin haka har ina baki tabude zatai magana wani tarin yakara sarkaketa wine din na fitowa daga bakinta yana diddiga akan white wandonta duk yay staining sabida Jan wine ne, kaman daga sama taga wani clean white handky agabanta kamshin da ajikin mutum daya tall a duniyan nan takejin kamshi taji yana fitowa daga hanky ahankali tadago kanta sama tanabin Tundaga handkerchief din dakallo harzuwa white hannun dake rikeda shi zuwa kan fuskan Zayn dake kallonta in the eyes, wani sabon bugawa zuciyanta yashiga yi hannunta har rawa yake tasa takarba zatakai kan fuskanta dan sharewa shikuma yajuya ya ijiye kudaden dayariga yaciro daga wallet dinshi yadaura kan kantan yajuya yawuce batare daya kara bata second look ba, ahankali ta janye handky dagakan bakinta tabishi da kallo harsaida yabace ma ganinta sanan tasauke ijiyan zuciya kafin ahankali tasauke kanta tana kallon handky din ko kadan tama manta inda take rungume handky tayi akirjinta tana murmushi sosai. 💫 PROMISE OF THE HEART 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💔 ✍🏻M SHAKUR 2️⃣ Murmushi Bartender din yayi inda sabo yasaba yasan yanda yarinyar nan ke crushing on that guy like hell, not just her da many other ladies ma, sabida guy dinan cinikin dasukeyi yanzu a eatery dinan is mind blowing, dazaran ansan yana ciki yammata zasu fara tururuwa suna shigowa from no where so koshima he’s happy for her at least yau yakulata, he hope suyi relationship dudda guy din dumping yammata yake anyhow kaman trash kuma ko ajikinshi dan yasan yanda suke binshi, he just hopes wanan will not be one of his victims, dan yana using babes kaman yanda yake using pen na rubutu idan yagaji da wanan ya yar yadauki sabo. Tadade awajen ita kadai sai murmushi take tana daddaura handkerchief din akan fuskanta tanajin dadi daga bisani wayanta yashiga kara, dasauri ta kalli wayan ganin Juliana Munari ke kiranta yasa dasauri tadauka tana murmushi sosai tace “Hi Babe ya” daga tachan bangaren wata yarinya tace “ina apartment dinki amman bakinan Ayshu where are you? Ba tundazu muka gama lectures ba” murmushi tayi sosai tace “ina Cozy” dan jim Jully tayi tace “for Godsake Aisha when will u get sense? Eh, look at the way Kabeer ke binki Ayshu yaron nan loves you like a mad man amman kina nan kina stalking wanan heartbreaker da the worst part baimasan kina existing ba” dasauri Aysha tai fari da ido tace “says who, wayace miki baisan ina existing ba? Wlh yasani infect right now ma yanzu haka handkerchief dinshi nake kallo a hannuna it feels warm and smells succulent, OMG it smells just like him wlh, I feel kaman Zayn dina ne anan wajen” shiru Jully tayi saikuma chan tace “Ayshu I am ur friend and I will always tell you the truth, forget that guy he’s nothing but a dream and face the reality face wanda ke sonki ba wanan ba da kowa in our university sunsanshi ba wajen using yammata yay dumping nasu, Ayshu enough of this stalking, sabida yaron nan kin chanza gida kin dawo apartment din dayake, kin biya kudi double of the normal amout sabida acire tenant din dake zaune adakin dakenan directly opposite nashi kinyi parking kin koma compund din, Aysha sabida yanda kike stalking guy dinan kinsan karfe nawa yake tashi, karfe nawa yake fita gym, karfe nawa yake shiga school, sau nake yake da lectures kinsan all his spots, grades dinki kullum low suke karayi sabida soyayyan wanda baisan dakeba ke gabanki kum…” “Jully please enough, allow me to leave my life, ana so by force ne banson KB ki rabudani da maganan shi, kuma zaki gani Zayn will notice me and I will date him” dasauri Jully tace “dating Ayshu bakince min Islam dating babu kyau ba” dan yatsine fuska tayi tace “Jully is because bakisan guy dinan bane saisa, irinsu idan kika basu kanki ne kawai zasu zauna dake, dan gayu ne nafitina kaman ba muslim ba, boko tashigeshi, I want him to be addicted to me kaman yanda yakenan addicted to shisha, I am ready to give him anything, wlh Ina bala’in sonshi, just wait for me, ki dafa mana abinci gani nan zuwa” tana maganan ta katse waya shiru Jully tayi, at this point zubama Ayshu ido zatayi dan Allah yama Ayshu taurin kai batajin shawara, kuma yaron nan will only break her heart, she will only chop breakfast a hannunshi a nothing will happen yaron da har lecturorin su mata crushing suke akanshi, anyway she just hope for the best. Wuraren 6 ta shigo gidan, kana ganin gidan kasan na mugun yaran masu kudi ne, elevator ta shiga zuwa floor dinsu sanan tawuce Dakinsu tana kallon nashi dakin datana gani tasan baidawo ba daman baya dawo da wuri kullum sai 11 ko 12 nadare kuma kullu yaumin bata iya bacci saitaga dawowanshi wata rana tai kuka duk randa zai dawo da mace wata tana kuma tai murmushi, the truth is baifiye neman mata ba, wani zubin zaiyi 2month baidawo dakowace mace ba wani zubin kuma saiya dawo da mace zasuyi kusan kwana uku ko hudu tare saikuma shikenan bata kara ganinta dudda batasan dalili ba but kawai haka take gani, kuma baka taba ganinshi da babe din dabataci sunanta babe ba, duk tana tunanin nan tana tafiya ne tana kaiwa gaban Dakinsu tabude kofa tashige ciki tana ihu kitchen tafada tawani irin rungume Jully tana nuna mata handky tace “Jully look” murmushi Jully tayi tana kallon handky sanan tace “Ya akayi yabaki handky shi” nan tabata labarin from A to Z tana murna, murmushi Jully tayi tace “nidai jeki wanka kizo muci abinci dan Jerry zaizo yadauken” gira daya Aysha tadaga mata tace “Iyye love birds” tai maganan tana wucewa bedroom nata tashiga sanan ahankali ta ijiye handky kan pillow dinta tareda shafawa sanan tawuce ta shiga wanka agurguje tana fitowa tazo sukaci abincin tare sanan Jully ta shirya ta wuce abinta, komawa tayi ta kwanta kan gado tadauki handky tana kallon shi kafin ahankali tace “Zayn! I love you so very much Zayn” rungume handky tayi akirjinta tsamtsam tanaji kaman shita rungume, ahaka bacci ya kwasheta 11 dot na bugawa ta bude idanunta tsam shi kanshi gangar jikinta yasaba da stalking nashi, fitowa falonta tayi tai hanyar window ta ta tsaya dayake wutan dakin akashe ne ta tsaya tana kallon kofarshi tana tsaye awajen kam wajejen 11:30 saigashi ya shigo yana tafiya nan cikeda isa akuma hankali tundaga wajen saida kamshin dayake yadaki hancinta bude kofanshi yayi ya shiga sanan ya maida yarufe kafin ya kashe wutan falon, murya chan kasa tace “good night My love, asuba tagari” sanan ahankali tasauke window blind din tajuya takoma daki ta kwanta saikuma kaman wani abu yafado ranta dasauri ta tashi tadauki handky tafada bayi ta wan ke shi tsaf sanan ta shanya tafito tazo ta kwanta, shida dot tabude idanuwanta agurguje tafada bayi tadauro alwala tafito sallan ma agurguje tayi bama ta tsaya cire hijabin ba tafito ta daga window blind ta tsaya jikin window dan 6:30 dot yake fitowa tafiya gym, tana tsaye saigashi yafito cikin kayan workout gajeren wando da singiletin Riga da safa da canvas, cinyanshi tabi da kallo amunmurde kaman na yan wrestling sanan yaja kofan dayake da pin suke bude kofan yawuce yana jogging yatafi abinshi murmushi tayi ahankali sanan tace “good morning baby na” sanan tajuya handkerchief din tadauka tai ironing nashi, sanan ta shiga wanka tadade sosai abayin sanan tafito tana ganin 8 saura da sauri tawuce wajen window Wuraren 8 yashigo yana zufa murmushi tayi dasauri tajuya tashiga ciki wani hadaden short gown ta saka daya sauka daga guwiwabta da kadan pink yamata kyau Wanan Karan batasa dankwali ba sai turaren data feffesa sanan tai parking gashin ta in a stylish way sanan ahankali tadauki handky tana kallon kanta agaban madubi ahankali tace “Ya Allah kadaurani akanshi” sanan ta zura slippers dinta tawuce tafita falo ahankali tabude kofa tafito daga flat dinshi sanan kaman wacce abi yafashewa aciki tai hanyar dakin shi kirjinta na daukan uku uku tawuce gaban dakinshi tadade atsaye kafin ahankali ta danna door bell, ankai kusan 5min kaman bazaa budewa farat aka bude kofan gabadaya dasauri tadaga kanta suka hada ido wani irin faduwa gabanta yake tana kallonshi yana daure da bathrobe ajikinshi kirjinshi duka abude gashin kirjinshi akwance ruwa nabi sai karamin towel a hannunshi yana goge kanshi da alamu daga bayi yake, da mamaki yadan kalleta batare datai magana ba, lips dinta har rawa yake sanan ahankali tadaga hannunta dake rikeda handkerchief din murya chan kasa tace “ahhhhhmmm dama, dama, I brought your handkerchief back ne” tai maganan tana wani irin nishi sama sama kaman numfashinta sai dauke, kirjinta nawani irin racing, this is the first time take ganinshi ahaka, ganin still kallonta yake ba yabo ba fallasa kuma bai fasa abinda yake ba wato sharekanshi da karamin towel din dayake rikedashi, yasa taji wani bala’in fargabanshi na cikata jin baice komiba dakyar tadaga hannunta tamai pointing kofan dakinta dake kallon nashi tace “actually that’s my flat, yanzun nan naganka shine nace uhmmm bari nakawo ma” dan yatsine fuska yayi amugun wulakance ya kalli handky datake mikamai tundazu har hannunta na neman sagewa yace “I don’t need it, discard it” yaja kofan zai maida yarufe da sauri tace “uhmmm wait please” chak ya tsaya yana kallon fuskanta da fuskanshi dababu alamun rahama akai face dinshi looking kaman zai maketa, tagefenshi taleka tana kallon indomie da taga yafito dashi zai dafa yacika ruwa a babban pot yazuba albasa aciki ya fasa kwai aciki ruwan na kumfa sosai, dan murmushi tayi cikeda shakkanshi tace “are you trying to cook indomie”? Yana kallonta still a bala’in wulakance yace “uhn” kaman dole akace yay maganan, murya chan kasa cikeda shakkan abinda zatace tace “that’s not how to, lemme cook it for you p…..please” wani kalan wahalallan tsaki yaja ko kunyanta baijiba yace “banso” sanan yay slamming door din on her face batare dayama jira maitake shirin cewaba, kuka taji yazo mata wuya tadaure tahanashi fitowa tadade ahaka awajen sanan ahankali tajuya tawuce takoma dakinta zama tayi tana kallon handkerchief din tama rasa meke mata dadi, tunda take bata taba shakkan wani namiji ba sai wanan menene shi? Jibeta fa tanada kyau babu namiji da bazata iya daukemai hankali ba shi waye, enough of all this, tashi tayi fuu tai kofan tabude tafice sanan direct tai dakinshi ta danna door bell baa wani dauki lokaci ba wanan karan tabude kofan koyana expecting wani ne oho, churus ya tsaya ganin yarinyar dazu, wani irin faduwa gabanta yayi ganinshi dagashi sai dogon wando na Jean da Riga a hannunshi dabai Riga yasaba yanada wani irin broad chest ga cikakken shoulder parts garai, kasa magana tayi saiwani kalan kallon kirjinshi datake lips dinta na rawa tana kallon dark aroelas dinshi, ahankali tace “l…..l….ove……you…..Z….Zayn” Tundaga sama har kasa yake kalleta sanan yace “ke kikama kanki” wanan Karan wani slamming kofan yayi on her face saida yataba goshinta ahankali tajuya kaman an kashe mata yaran ciki tawuce side nata ta zauna dirshan akasa, tana zaune awajen taji fitowanshi yafice, kiri kiri kasa zuwa class din datake dashi tayi sabida yanda komi baya mata dadi. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 PROMISE OF THE HEART 💔 ✍🏻M SHAKUR 3️⃣ ~Nigeria~ Wata babbar mace ce doguwa chocolate skin tsaye cikin wani lafiyayyen hadadden kitchen ginin zamani, tana sanye dawata doguwan rigan Atampa mai kyan bala’i ga kallabi daure akanta da kana gani kasan daura dankwalin kawai tayi amman hakan baihana kwantaccen black gashinta dake gauraye da farare lekowa ba, tana tsaye agaban wani hadadden babban gas a kitchen tanama wata yar aiki dake juya basmati rice a tukunya dawani wood spoon magana sukaji wata zazzakan murya dake ratsa zuciya na y’a mace ta kwala ma matar uban kira. “Mama nadawo, nakawo miki wasu kawayena ki gansu” wani irin kwashewa da dariya yar aikin dake juya abinci a tukunya tayi takalli Matar da aka kira da Mama datai tsaye kawai tama rasa ta cewa tace “Hajiya wlh tun ina iya kirga yawan kawayen Khairy harna bace a kirgan” kwafa kawai Matar da aka kira da Mama tayi tace “karasa juya abincin sai ki kwashe a warmer Ladid…..” bata idasa maganan ba aka kara rangadamata kira da wanan zakakkiyar muryan kaman ana busa sarewa. “Mamaaaa kina ina zoki gansu” dafa goshinta Matar tayi cikeda takaici tace “Allah nagode maka dakabani wanan yarinya, ina ganin Ummulkhairy ce zata bani hawan jini aduniyan nan” tai maganan tana fitadaga kitchen din ta hanyar bude kofa tafice, tana fitowa dining tai kicibus da yammata kusan su tara a zazzaune kan lafiyayyun kujerun falon suna maganganu suna hira suna kallon lafiyayyen hadaden falon dayaji Cubana furnitures, ganin Matar da kallo daya suka mata suka gane itace mahaifiyar Khairy yasa duk suka zubo daga kan kujerun cikeda girmamawa duk suka gaidata. “Mama ina yini, Mama barka da rana, Mama ina gajiya” lafiyayyen murmushi ta sakin musu tana karasowa tsakiyan falon tana bindi da kallo daidai tace “Masha Allah sassannunku da zuwa yammata yakaratu”? Kafin subata amsa wata kyakkyawan budurwa yarinya chocolate skin color, yar doguwa bachan sosai ba dabazata wuce 20yrs, skin dinta nawani kalan glowing fuskanta babu ko kuraje guda, tanada dan dogon hanci yet kuma dan karami dan diss afuskanta but fitacce, tanada manya manyan pure white eyes, idanunta are very big sunada wani kalan adorable spherical shape that is just damn gorgeous, dan kana kallonta the first thing dazasu fara daukan maka hankali a fuskanta are her big white eyes, ga eyelash dinta dogaye bakake cikakku, hakama gashin giranta, tanada goshi wanda kusan yarabu biyu ne rabi duk gashi ne dayake nan baki sidik sun kwanta daya karama fuskanta wani kalan kyau dan zaka dauka buzuwa ce sai dayan rabin kuma fatarta ne dayataho har gira, tana sanye da dogon rigan atampa itama da dan kwalinta akanta, tawani buga uban ihu da saida falon ya amsa gabadaya. “Mamaaaa” yanda ta kwala mata uban kiran nan yasa mahaifiyar nata tadago da kanta tareda juyowa ta zuba mata idanuwanta kurii irin na jama’a yaya zanyi da wanan yarinyar ne? Wani irin washe baki Khairy tayi cute saitin white teeth dinta suka bayyana tashiga saukowa daga stairs din dagudu kaman ba ita Mamar kema kallon zaki ganeba kawai tawani irin fada jikin Maman nata tana ihu sosai tana rawa ta kankame Maman kamkam. “Wayyooo Mama wlh nai missing naki, inata nemanki nadauka kin fita ne har hankalina yatashi ashe kina kitchen, Mama tun safe yau banganki ba awa nawa yanzu bansaki a idona ba karfe biyar fa, nai kewanki Maman mu, Mamana, I miss you Mommy Ummulkhaiyr” tai maganan tana kara kankamet Mama cikeda tsananin murna, dudda yanda Mama ke mugun kule da ita saida tai murmushi har cikin ranta duk cikin yaranta babu wanda ke sonta kaman yanda Khairy ke sonta, idan Khairy tadawo gida batanan wani zubin har zazzabi takeyi, Son da Khairy ke mata dabanne, gabaki dayan kawayenta baki suka sake suna kallon Khairy yanda ta kankame mamanta cikeda murna tana rawa kaman wata yar karaman yarinya, murmushi kawai Maman takeyi ganin yanda kawayen ke kallon Khairy sabida wayan nan wasu new set ne basu saba ganin haukanta agidaba yasa Mama tace “ke dalla cikani kije kitchen kitaya Ladidi ku kwaso abinci kiyi serving friends naki kuci” sakin Mama tayi ahankali tana murmushi dake bala’in kara mata kyau tana kallon Mama tace “tom Mama” sanan tawuce kitchen da ihunta ta shiga kitchen din. “Ladi kwas kwas!” Tsabagen yanda Ladidi tafirgita batasan lokacin data saki cokali data rike a hannunta kasa ba, kwashewa da dariya Khairy tayi ganin yanda Ladidi tafirgita, Ladidi ta watsa mata harara tana dafa kirjinta da hannu jin yanda yake bugawa tace “aniyarki tabiki Khairy bani zaki sawa bugawan zuciya ba wlh” dariya Khairy tayi tadauki spoon tazo kusa da ita tana kallon tukunyar tana murmushi tace “uhmm smells good, let’s have a taste” abincin tadeba takai baki tana lumshe ido, harara Ladidi tabita dashi tana kallon long full lushy eyelash dinta dazakaji kaman ka cire kasama naka sabida kyau, dan murmushi tayi tace “yayi dadi Khairy? Kinga nasa coconut milk dakikace nadinga sawa” bude idanu Khairy tayi ta kalleta sanan ta yatsine fuska tace “yayi dadi ba laifi amman ba kaman nawa ba” batarai Ladidi tayi hakan yasa Khairy tafashe da dariya tace “ki zubamana nida kawayena kizo ku gaisa” hararanta Ladidi tayi tace “Malama ki tsaya ki dauki abincinku ki kaimusu ba inda zani nagaji da gaisawa da kawayenki, nibansan ko kamfani gareki na kawaye ba” turobaki Khairy tayi tace “bakinciki kikemin kinga inada kawaye masu sona ke bakida kawa ko daya” dasauri Ladidi tanuna kanta tace “ni Khairy bakin ciki ana zaune lafiya, kawayenki sunfi dari, ni idan Allah yabani kawaye ko sama da biyu ne bansan yanda zanyi dasu ba” hararanta Khairy tayi tadauki Baban tray da Ladidi tajera musu different abinci akai a different plate guda 5 tafita dasu taje takai musu sanan tadawo ladidi na kallonta tace “yanaga kin dawo” akufule tace “su tara ne plus ni goma, kuma is just 5 plate of food nafita dashi” kasa magana Ladidi tayi kawai tashiga zuba wasu sababbi tass abincin yakare Ladidi tace “yayyinki suka dawo maizasuci” “oho” ta amsata akufule tafice abinta takaimusu abinci suka shiga ci suna hira shaaaa kakeji sun cika falon da hayaniya kadauka biki ake kowani liyafa aka hada, lekosu Ladidi tayi daga kitchen kwafa tayi tace “yo wlh ban kara daura wani girkin barima kiga tafiyata zanyi, masu gida nakema aiki ba kawayenki ba, yarinya kowani kare da doki kawayenki ne, mijinki zai sha fama Khairy” tai maganan tana komawa ciki, hada yan kayanta tayi a handbag dinan sanan tabi takofar kitchen tafice abinta daman inhar tagama aikin yamma indai Hajiya na sama tafiyanta take saidai in tana kasa ne saitaje tamata sallama tawuce. Sai wuraren 6 sanan kawayen nata suka fito bayan takaisu sama sunma Mama sallama har compound tarakosu inda sukai parking motocin su duk suka shishiga, daya daga cikinsu taleko bayan tama motarta benz key tace “wai Khairy yaushe zaki farajan mota kine eh? Gamu duk mu munaja ke kadaine kullum driver ke kawowa” kaman zatai kuka tace “ba su Mama bane da Baba wai tsoro suke su barni nafara tuki wai nacika rawan kai kumafa na iya wlh Paddy” dariya dukansu sukayi wacce ta kira da Paddy tace “ke da karfin hali zakisa su barki kifara tuki wlh daukan mota kawai zakiyi wataran ki fice, Babe magrib tayi bari muwuce see you tomorrow at school” hannu tadaga musu tace “see yah girls” gateman dinsu yabude musu gate suka fice motoci biyar daidai kuma motocin yayinta na shigowa gida na Baban su biyeda su, washe baki tayi tana tafi ahankali tana kallon motar Baban su dake shigowa last tace “oyoyo Baba” motan na parking tai wajen motan da gudu batare databi na yayyinta da kallo bama. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 PROMISE OF THE HEART 💔 ✍🏻M SHAKUR 4️⃣ Kafin ma Baba yabude kofa tasa hannu tabudemai kofan jikinta har rawa yake tanajin dadi. “Baba oyoyo, Baba sannu da zuwa” wani magidancin mutum ne babba sosai yana sanye da babban riga yanada gemu dayacika da furfura, ga kuma katon ciki irin na manya wayanda suka manyanta dinan, exactly idanunsu iri daya da ita manya saidai nashi daya soma kankancewa sabida tsufa, wani kalan kyayataccen murmushi yasakin mata, cikin kamilallen muryanshi irin na magidantan nan yace “yarinyar Babanta” yay maganan yanajan dan hancinta, murmushi tayi sosai tace “sannu da zuwa Baba” fitowa daga motan yayi yace “to akwasomin kaya akai ciki” gyadamai kai tayi tace “to Baba” yawuce yana kallon yaranshi maza su uku da duk suke tsaye suna jiran fitowanshi, Manaf wanda yake Babba yanada 27yrs, sai Mu’az shima 27yrs twins ne shida Manaf saidai ba identical twins ba ko kadan ma basuyi kamaba idan baa gayamaka yan biyu bane bazama ka yardaba, Manaf na kama da Mama, Mu’az na kama da Baba, sai Maheer dakenan 24yrs, dukansu sun gama makaranta duk a company Baba suke aiki yanzu. Gaida Mahaifin nasu sukayi cikeda girmamawa kana ganinsu kaga yaran dakeda tarbiya dakuma natsuwa. Cikin so da kauna ya amsasu yana tambayan kowa ya aiki sanan suka wuce masallaci, itakuma kayan Baba su files da wasu yan tarkace tafito dasu daga motan sanan tai cikin gida. Sama tayi direct zuwa lafiyayyen hadadden falon Baba, ijiye kayan tayi sanan tajuyo tabude kofa ahankali, ganin Mama tsaye abakin kofan kaman ita take jira daman yasa takarasa fitowa tareda maida kofan tana rufewa tana kallon fuskan Mama dake kallonta tana murmushi, harara Mama ta watsa mata tace “ba murmushi nace kimin ba, quietly go to that kitchen kidafa sabon abinci wanda za’aci agidan nan this night tunda wanda aka dafa dake da kawayenki kun cinyeshi tatas” dan turobaki tayi dan wlh tagaji ahankali kaman zata rushe da kuka tace “Mama maisa Ladidi bata dafa wani ba wlh nagaji school fa naje” cikin fushi sosai Mama tace “are you stupid Umma? Inba so kike na makeki ba kiwuce yanzun nan kafin raina yabaci kije ki daura abincin daza’aci this night, I am talking to you kina gayamin Ladidi tadafa, kin zaci sabida ke nadauki Ladidi aiki kokin dauka jakace ita batasan ciwon kanta ba dazata zake tai girkin gida keda kawayenki kuzo kutasa abincin agaba ku cinye tas, yanzu ina gayamiki kije ki daura wani kina neman kawomin gabli da ba’adi, to the kitchen my friend!” Mama tadaka mata tsawa kaman zata kurma ihu tawuce hawaye sun cika idanunta tass tai kasa, harara Mama tabita dashi sanan takada kai kawai tawuce tashiga dakinta. Kitchen din tashiga tamaida kofan da mugun karfi tarufe kaman zata Balla kofan sanan ta jingina da kofan tana maida numfashi takai kusan 5min sanan tawuce ta kwaso kayayyaki tashiga shirin hada girki. Saida akai Isha’i sanan Baba da su Manaf suka shigo gida, afalo suka tarda Mama zaune gaidata duk sukayi, Mama ta gaida mijin nata zama duk sukayi, Maheer yace “Mama me aka dafa yunwa nakeji” ahankali Mama tace “Khairy na kitchen tana girki, itada kawayenta suka cinye duka abincin da aka dafa tass shine yanzu dannace taje tadafa wani abincin take kumbure kumbure” dan murmushi Baba yayi yana duba wayanshi ganin yanada miss call, cikeda kufulewa Maheer yace “wlh Mama Allah zan zane yarinyar nan, duk randa takawo kuchakun kawayenta tashiga kitchen tamusu girki da kanta ba abincin muba” cikin fushi shima Mu’az yace “ni I don’t even know wani kalan brain Khairy keda shi, ni tunda nake bantaba ganin wacce takai Khairy yawan kawaye ba, kawayenta sunfi dari biyu, tamaida mana da gida nanne majallisar kawayenta ai gobe Saturday Allah sa takawo mana wata gidan nan wlh daga ita har kawar saina kakkaryasu” Baba daduk ke jinsu yana taba wayanshi wayan ya ijiye yakalli Mama yana murmushi sanan yakalli su Maheer yace “ku kyale yarinyar nan she’s just a small girl, idan making friends makes her happy so be it, abincin gidan banike siyaba taita kawo kawayenta sunaci is no big deal, and you wife” yajuyo yakalli Mama yace “idan abincin gida da kawayenta keciki ki kara yawan abinci since kinsan yarki mai mutane ce, ta yanda zasuzo suci su koshi sanan muma muzo muci okay” tabe baki Mama tayi tace “daman babu wanda ke bata yarinyar nan saikai kacigaba” Mama tai maganan da fushi dan murmushi Manaf da tuntuni baice komiba yayi ganin yanda ran Mama yabaci yace “Mama kudena making issue out of this small thing please bagashi yanzu tana kitchen tana dafa mana wani ba, is just friends ta tara bawai wani bad hali ko dabi’a takeyi wanda yaran yanzu sukeyi ba Mama, please ku kyaleta, she’s still a small girl, inda ace bata gama secondary school dawuri ba da har yanzu bamata shiga university ba ballema tazo hartana final year, ku barta please Mama ahankali zata gyara” murmushi sosai Baba yayi yanajin maganan da Manaf keyi, Manaf nada dabi’unshi sak, ga hakuri ga iya tafiyar da gida gashi da halin manyanta halin Baba, amman Mu’az da Maheer jin kansu suke kaman sa’onnin Ummul Khairy. Baki Mama tabude zatai magana aka bude kofan kitchen din aka fito Khairy ce tadauko wani hadaden warmer, ko kallonsu batayi ba sai uban turo baki take tawuce zatakai warmer dinning Baba yace “zo kawo kulan nan Umma anan falo zamuci” ahankali tajuyo tazo Mu’az da Maheer sai uban ballamata harara suke tana karasowa ta ijiye kulan Baba na kallonta yace “yauwa sannu da aiki Yanmata na” Maheer dake kallonta yace “yi sauri kije ki kawomin plate dina da fork” dasauri ta kalleshi da manya manyan idanunta harara ta watsamai wani irin mikewa tsaye yayi kaman zaiyo kanta dasauri tai baya tareda dan sakin ihu. “Wayyo Ya Manaf kaganshi ko” hararanshi Manaf yayi batare dayay magana ba hakan yasa Maheer yakoma yazauna yana kwafa, Manaf yakalleta yace “go and bring the plate and serve us” gyadamai kai tayi tajuya tana turo baki daga Baba har Mama suka bitada kallo, bata wani dade ba tafito dauke dawani babban tray da plates spoons, bottle water da drinks ke kai sanan takawo tsakiyan falon, sanan tabude kulan wani kamshi ne yadaki hancinsu tadafa wani lafiyayyen taliya da nama, zuzzubama kowa tayi sanan ta tashi, Baba yace “ina zaki zauna kici naki” ahankali tace “nakoshi naci shinkafa dazu, wanka zanje nayi Baba nagaji” “jikiyi yarinyar kirki” wucewa tayi sama sukuma sukahau ci, saida Maheer yajuya ganin hartama shiga dakinta yasa yajuyo yace “at least she’s good in one good aspect, wato girki” murmushi Baba yayi yakalli Mama yace “akwai wacce zata zauna da Wife bata iya girki ba ballema yarta” murmushi kawai Mama tayi batacemai komiba, saida suka gamacin abincin tsaf sanan Maheer ya kwashe komi yakai kitchen kafin su tashi suma iyayensu sallama suka wuce side dinsu. Tashi Baba yayi yana kallon Mama datai shiru yace “please kidena sa zancen shirmen Khairy aranki, is just like what Manaf said at least friends kawai ta tara bawani mugun hali ba” dan ijiyan zuciya ta sauke sanan ahankali tace “Alhaji still yawan kawaye basu da amfani wlh” ahankali Baba yace “I promise duk randa nai sensing wani bad behavior kokuma wani abu nida kaina zan rabata dasu, please this matter of her friends shouldn’t be an issue again ok” Ahankali Mama tace “ai shikenan dama kaine ke bata Umma ai” Mama tai maganan tai gaba abinta binta yay abaya yace “wifeyyy common” bata biyemishi ba tabude kofar dakinta ta shige, murmushi yayi kawai aranshi yace “I will handle u later” sanan yay hanyar dakin Khairy, knocking yayi ahankali tareda kiran sunanta. “Umma” jin shiru yasa ahankali yabude kofan dakin, dakine nai kyau dakana gani kasan dakin Yar gata ne anyimai Fenti pink dakuma design na flowers everywhere, tana kwance kan lafiyayyen gadonta mai kyau tana sanye da dogon gown na bacci tana bacci hankali kwance ga dakin uban sanyin AC tachure alamun sanyi takeji, karasowa gaban gadon yayi yace “Umma Umma, mamar ki dake fada ita batasan rashin jin maganan ta kika daukoba” yay maganan yanajan bargon gadon yarufa mata sanan yadau remote don AC yarage AC sosai kafin ahankali yajuya ya kashe wuta sanan yarufe mata kofan yawuce dakin matarshi!!!! 💫 PROMISE OF THE HEART 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💔 ✍🏻M SHAKUR 5️⃣ Da asuba kafin Baba yawuce masallaci yashigo yatadata wanda hakan yakeyi kullum. Da farinciki ta tashi yau sosai kaman ba itane ta kwana da fushi jiyaba, murna take sosai sabida yau zataje bikin kawarta Zainab. Saida tai salla tai karatu sanan ta gyara dakinta tsaf tafito kasa ta sauka a kitchen ta tarda Mama tsaye zata fara aiki dawani irin gudu taje ta rungume Mama. “Mama good morning” murmushi Mama tasakeyi this is another aspect na halin Umma datakeso ko kadan batada riko, tureta Mama tayi tace “waike karyani kikeso kiyi” dariya tayi tace “Mama dadi nakeji yau bikin Zainab Kawata, Beaty wacce nai ankon ta kin tuna”? Baki Mama ta tabe tace “ina zan tuna wata Besty Bestotin kin sunfi dari, keda kullum cikin bikin kawayenki ake, idan babanki ya shigo kije ki tambayeshi izini baruwana da zuwa bikinki, bani tukunya nidai kiga” dasauri tadaukoma Mama tukunyar nan suka shiga hada breakfast tanama Mama surutu wuraren 8 suka gama komi suka jera a falo daidai nan su Baba suka shigo gidan duka zama sukai a falo suka shiga kari sai bayan an gama ta kwashe komi takai kitchen sanan tadawo da saurinta tazauna kusa da Baba, fuskanta kadai yagayamai dawani abu hakan yasa yace “Ya akayi Khairiyya?” Murmushi tayi tace “Baba yau bikin Zainab kawata shine nakeso nagayamaka” idanu Baba yazuba mata yace “amman kinsan yau yakamata kije gidan Baffan kiko” gyadamai kai tayi dasauri ahankali tace “Baba gobe zanje gidan tunda yau inada biki please naje Baba”? shiru yayi sai chan yace “ok kije, but by 4 kidawo gidan nan ban yarda kije kai Amarya ba” murmushi tayi tace “Baba ai daman bazanje ba itada za’akai Kano, kumama ana daura aure wai zaa tafida ita kaga kenan kafin 4 nadawo ma” jinjina kai Baba yayi yace “duk kincikani da surutu, okay to adawo lpy, ki kama kanki banson kula maza okay” dasauri tace “to Baba, bari naje na shirya to” tai maganan tana tashi tai sama, tashi Manaf yayi yace “bari naje na kwanta Mama” binshi Mama tai da kallo yawuce yafita shikuma Maheer da Mu’az Kwallo suka kunna a falon suna kallo abinsu, Baba kuma na duba wasu files dayasa Mama tadaukomai daga dakinshi. Wanka tasakeyi sanan tashirya cikin wani hadaden ashobe, skyblue, dogon riga aka mata daya kamata daidai ita ya bala’in mata kyau, yabi jikinta sosai, zama tayi gaban madubi tana kallon kanta, dan tsaki tayi takai hannunta tana shafa siman rigan da akabi da net da kana iya hango tudun saman boobs dinta ahankali tace “I hate style like this dake nuna jikina, I will use gyalena narufe Mtsww” tasake jan tsaki sanan ta zauna tai wani lafiyayyen dauri dazaka dauka make up artist ce tayi, kwalli ta zizara sanan tadau wani lipgloss tasaka dayasa lips dinta shining pink din jiki yafito sosai dazaka dauka janbaki pink tasaka, wayanta dake gaban mirror kiran samsung note 22 ta dauka, ganin 10miss calls yasa tace “OMG guys gani nan zuwa kunata kirana” ganin battery ta yay ja yana nuna 10% left yasa takara jan tsaki tace “ohhh namanta bansa chaji ba” arayuwanta babu abinda take kiwuyan sawa irin chajin waya wani zubin sai wayan ya mutu russ ne shine zata dauka ma tasa a chaji, jefa wayan tayi a shinning handbag dinta dake ijiye kan mirror sanan tajawo wani hill na dolce gabana tasaka sanan tamike tsaye, dan karamin gyalenta tadauka ta warware sanan ta yafashi ta gaba tsaf yarufe mata kirji sanan tadauki turarukanta ta feffesa kafin ta maida komi yanda yake tafito lokacin 12:48PM. Saukowa tashiga yi daga Mama sai Maheer afalon yana kallon wrestling shima Mu’az yatafi ya kwanta, kamshin dayaji yasa yajuyo ganin Khairy yasa yasaki baki yace “ke kece amaryan Wanan kwalliya haka, Wanan ko ranan aurenki banjin zaki irin wanan kyan ba” hararanshi tayi takalli Mama dake binta da kallo tace “Mama kin ganshi ko” hararan Maheer Mama tayi hakan yasa yay shiru itakuma takaraso wajen Mama tace “Mama zan tafi ina Baba?” Ahankali Mama tace “Ya kwanta, ga kudi ya ijiye miki” tanuna mata bandir na yan 200 dasauri tadauka tana murmushi tace “Allah sarki Babana he’s the best, Mama natafi” tai maganan tana wucewa zatai kofa, Mama tace “ke” dasauri tajuyo takalli Mama dake kallonta, Mama tace “kindaiji abinda Baban ki yace ko, 4 tamiki agida Umma, kuma ki kama kanki, baruwanki da maza ko abokan ango, saura kuma naji kin wuce wani gantalin daban, wlh kika saba any of them bikin dazakije na karshe kenan ban kara barinki fita” dasauri tace “Mama I promise, nida keda bukukuwa I will not jeopardize that Mama, bye, Mama zan kawo miki alkaki” hararanta Mama tayi tace “banso, wuce Direba na jiranki” kofa tabude tafice, Already Adamu Direba harya shiga cikin motan ita kawai yake jira, wata lafiyayyen bakar Benz tabude baya tashiga sanan tace “gidansu Zainab zamu Adamu” “to Hajiya” yay maganan yana tada motan yaja, saida sukahau kan titi sanan taciro wayanta dake nuna 9% yanzu sabida uban kiran dasuke mata, kafin tama danna wayan wani kira yashigo da suna Zainab, daukan kiran tayi tana dariya tace “Amarya kinsha kamshi da turare, kuma wani gida ne gani ahanya” shiru tayi sai chan tace “Okk” sanan tace “Adamu suna gidansu Amal wai” ahankali tace “to” dan babu gidan wata kawarta dabaisani ba, tafiya kai nisa sukayi sanan suka shigo wani hadadden estate daya cika da mutane kana gani kAsan biki ake wani Layi daban ya shiga sanan yay parking agaban wani hadadden gida, murmushi tayi tace “yauwa, Adamu bani key motan narike” dasauri yajuyo ya kalleta, ganin kaman yanaso yaganota yasa tace “zan taimaka musu dashine, ana kwaso one or two things dazamuyi amfani dashi, idan zan dawo zan kiraka saikazo mutafi” tai maganan tana mikamai hAnnu, ahankali yazari key motan yabata karba tayi tace “yauwa katafi to dan sai yamma zan kiraka” tai maganan tana fitowa daga motan shima fitowa yayi sanan tarufe motan ta danna lock tawuce cikin gidan abinta shikuma yawuce yatafi zuwa bakin titi ya tsaye abin hawa yahau. Tun kafin tashiga gidan takejin tashin kida, murmushi tayi ta shiga gidan an gyara anyi decorating ga yammatan Amarya sai rawa suke suna hangota aka wani hau ihu. “Khairy, Khairy ta iso, ke join us” wani irin murmushi tayi kaman abinda take jira kenan dasauri tai dance floor din, DJ yasakan musu wani mad song rawa sukahau yi suna ihu suna hotuna idan kaga Khairy zaka dauka taje dancing school ne, suna haka saiga Amarya tafito wani mahaukacin ihu sukasa aiko tashigo itama sukahau rawa kaman mahaukata, Amaryan ta rungume Khairy tana mata magana a kunne, hakan yasa taciro wayanta tana video ganin wayan na nuna mata 1% yasa tai tsaki ta maida bag sanan taciro kudi tana ihu yara sai kallonsu suke taba manna ma amaryan. It was fun she love her friends and she loves wedding har buri takeci irin na shagulgulan da zaayi idan bikinta yatashi. 💫 PROMISE OF THE HEART 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💔 ✍🏻M SHAKUR 6️⃣ Wajajen 3 aka wuce da Amarya Kano, ita kanta Khairy saida tadanyi kuka cus Besty tabata tausayi, bayan an wuce da ita tama Maman su sallama tawuce dan zuwa chan gidan dasukai party inda motanta yake a pake, ahankali take tafiya ta bala’in gaji sabida rawan dasuka sha, ita kadai kemagana tace “yanzu inda Baba yabarni da hardani za’akai Zainab Kano, gashi akwai more event a Kano” dan murmushi tayi ita kadai tace “Allah kaimu bikina wlh 2 weeks zaayi ana event hmm” dan murmushi tasakeyi tace “nidako saurayi banda shine nake planning biki na” ahankali ita kadai tace “saikace wata mara farin jini, inada samari dayawa but duk mazan Nile ne, basu hadu ba gasu yan rainin wayau saisa i don’t even talk to them” tai maganan tana murguda baki daidai lokacin ta iso wajen motan, ahankali tace “I want to marry hadadden namiji, classic , handsome, miji dat will make mata jealous of my catch” tsayawa chak tayi takalli motan gabanta yadan fadi, saikuma chan tace “don’t be scared Khairy you have to show Baba u can drive sabida yabarki kidinga jan motarki” tana maganan tabude gaban motan tashiga tazauna tana sauke ajiyan zuciya sanan tamaida kofar motan tarufe kafin ahankali tace “Ohhkay let’s see” sitbelt tasaka still gabanta nafaduwa bata taba tuki bafa kawai tasha ganin yanda akeyi sanan Maheer idan tashiga mota dashi yana nuna mata yace “kihaka kihaka this and that” ahankali tace “Bismillahir Rahmanir Raheem” sanan ahankali takunna motar gently gabanta na dum dum tashiga yin reverse kadan kadan kana gani kasan wacce bata iya tuki bane acikin motan nan sanan ahankali taja motan tana tafiya ahankali wani irin murmushi tayi cikeda jin dadi tace “see ba gashi nan na iya ba ina tuki perfectly like a pro” Ahankali takejan motan feeling a bit too sad sabida su Mama basu Bari takai Zainab ba ahaka hartakai gate din estate din tasa kan motarta tafice tana kalle kallen main road din gabanta na faduwa, ganin motoci kowa na zuba gudu na wucewa yasa sabida irin karfin hali irin nata tasa motan ta shige cikin titin sanan tafara gudu Adan hankali, ganin tana gudu kan titi smooth babu wani tangarda yasa tai murmushi tace “wlh na iya” sanan tawani kara uban gudu tana murmushi, ko kadan bata lura dawani keke napep dake bullowa daga wani layi da mahaukacin gudu ba kawai danno kan keken shi yayi batare dayama kalli titin ba rawa jikinta ya dauka dudda da akwai tazara kadan tsakaninta dashi amman sabida yanda jikinta ke rawa tanason takara kara rage gudun datake kawai ta danna sauri before the blink of an eye jikake kwarap!! Motanta yadaki bayan keken da bala’in karfi tacigaba da tura keken gaba jikinta nawani irin rawa tama kasa taka burki. “Innalillahi wa innailaihi raji’un” tafadi arude kaman walkiya sanan ta ci wani mahaukacin burki dayasa dabata saka sit belt ba data buga kanta a siteri, ganin motan ya tsaya chak yasa dawani irin sauri ta murza key ta kashe motan gabaki daya tana wani irin sauke ijiyan zuciya da sauri dasauri tana kallon keken dake manne da gaban motanta zufa nawani irin keto mata daga goshi takasa ko motsi still in shock. Dawani kalan sauri direban keke napep din yafito yaci Kwalli a idanunshi yana sanye da Yar singileta daya koma brown tsabagen datti da jeans passengers shi maza biyu suma dake baya duk suka fito yana kallon yanda bayan keken shi yay condemn, sauran motoci sukuma sunata wucewa abinsu tunda dai Allah yakawo sauki hatsari ne da babu wanda yaji ciwo to su karata chan anata wucewa ta gefensu. Saida mai keken yagama duba kekenshi tass yakalli yanda duka kwan fitilan dake bayan keken suka faffashe sun fadi akasa sanan ahankali yadaga kanshi yakalli glass din gaban motan ranshi amugun bace yana kallon Umma dahar lokacin takasa motsi sai numfashi datake maidawa ita kadai tasan yanda cikin jikinta ke rawa, kafinma mai keken yay magana daya daga cikin passenger yace “durun uwanchan amman matar nan yar bala’in rainin wayau ce Auwal, muna tuki abinmu lami lafiya tazo ta dakan mana keke tamana Wanan uban asaran sanan ta zauna hankali kwance a motanta batama fitoba balle ta duba asaran datayi mana ba”…….. Wani hadadden hilux baka dakana ganinta zaka gane da security personnel ne ke gudu akan titin, ganin titin is congested go slow yasa yashiga rage gudu yana kalle kalle, wani kyakkyawan saurayi ne ke tukin motar yana sanye da kayan yan sanda, daya bala’in haska farin fatan jikinshi, ahankali yake tuki yanabin titin da kallon ganin yanda motoci suka cika hanya tam ga daga chan gefe gefen titi haka ya hango accident akayi tsakanin keke da wata mota dayaba iya ganin cikin motan cus tinted glass ne, ga masu keken sun fito suna duba keken su uku kana ganin yaran kasan irin rascals dinan ne, dan tsaki yayi ahankali sanan ya gangara gefe yay parking motan shi, murya chan kasa tace “I hate this job Dad!” sanan ya kashe motan yafito yanadan yatsine fuska tareda maida kofan motan nashi yarufe..….. Cikin wani kalan bakan zuciya mai keken da aka kira da Auwal da idanunshi sukai jajir danshi kadai yasan wuyan dayasha kafin yasami keken nan mezaicema mutanen dasuka bashi haya, cikin fushi ya nuna Umma dake kallonsu kuri ta glass din gaban motan da yatsa, irin warning dinan yama kasa magana tsabagen zuciya, hakan yasa ahankali Umma takai hannunta ta zare sitbelt sanan tabude kofan motan tafito ahankali jikinta na rawa tana kallon gaban motanta itama dayama bare yay kacha kacha saikuma bayan keken dashi ma ya baci wutan duk ya mutu sun faffashe sun fadi, sanan takaraso ta inda suke tsaye nesa dasu zata bude baki tai magana Auwal mai keken ya tare mata numfashi yace “ke dan ubanki dame kike takama agarin nan dazaki min condem din adaidaita sanan ki zauna cikin motarki batare dakinma fito kin duba barnan dakikayi ba balle kibani hakuri..” sosai kirjinta kewani kalan dukan uku uku hakuri tai niyyan tabashi amman yanda yazagi Babanta yasa taji ranta yabaci, cikin fushi tana kallonshi itama right in the eye tace “karka karayin kuskuren zagin ubana again inba hakaba wlh saina wanka maka mari, besides ma kai agidanku ba’a koyamaka kaduba hanya kafin kashigo ciki ba eh”? Cikeda wata kalan bakar zuciya Auwal yana kallonta da idanunshi da ita kanta taga bala’in dake cikinsu yace “ni kike gayama magana?” Dakewa tayi dudda kirjinta kaman zai tsage tace “ai kai kafara, dama ance idan Yaro bai koyi tarbiya agida ba zai koya a titi, dan haka from today karka kara ganin mutum kai kuskuren zaginshi ko iyayenshi” kafin ma Auwal dake dunkule hannu yay magana passenger sukace “ke wai kinada hankali kuwa kin bugemai keke kinmai asara bazaki bada hakuri ba” wani mugun kallo tamusu tace “kune marasa hankali bani ba, kuma hakurin bazan bayarba kuyi yanda zakuyi” tai maganan zata juya jitayi an wani irin fizgo bayan riganta fut tadawo baya hartana turgeda kafa sabida heel din data saka, wani irin bari jikinta yadauka tana kallon Auwal daya fizgota ganin yadaga hannu zai kaimata mari yasa tawani irin kwala ihu tareda kai hannayenta biyun tana kare fuskanta, shiru taji batare dataji saukan Marin ba akan fuskanta, hakan yasa ahankali kaman wacce tai sata ta shiga janye hannunta daga kan fuskanta tana nishi sama sama sanan tabude idanunta da kyau tana kallon gabanta inda su Auwal mai keken suke, wani mutum tagani dogo fari kal sanye da kayan yan sanda yasha gabanta yana rikeda hannun Auwal daya kawomata mari ya murde, dudda bataga fuskan mutumin ba dan yabata baya but she could see yanda bayan shi keda fadi, gawani kalan bakin suma dake kanshi sun kwanta suna kyalli sosai zuwa shi wajen yasa wajen yadauki kamshin dayakeyi. Daga Auwal har passengers din duka tsurewa sukayi suna mutumin, cikin wata kalan kakkausan murya yace “how dare you raised your hand zaka daki mace akan titi, are u mad!” Yadakamai tsawa yana murde hannunshi da kyau ihu Auwal yayi jin azaba yace “officer dan Allah kayakuri bazan karaba, wlh bugemin mota tayi opisa” cikin muryan nan nashi nabawasa yace “and u dare to lift your hand up zaka daketa, cause she is a woman, and she is helpless, alone! Inda kanwar kace fa? U deserve to sleep in jail dukan ku the three of you” sosai suka shiga bashi hakuri, tun tana kallonsu tanajin mesuke fadi har taji kanta nawani irin juyawa kaman tanajin jiri, bugawan da kirjinta keyi yay multiplying da kusan dari hakan yasa gently tajuya tana daura hannayenta akan kirjinta tana kokarin ta saita numfashinta dake mata wuyan kamawa tana kokarin tafiya kawai tafiyan taji ya gagareta wani irin zubewa tayi jikin motan, Karan faduwanta da bugewa da motan datayi yasa dawani irin sauri dagashi harsu suka kallo inda take, ganin yanda take nishi tana beating chest nata tana kokarin numfashi at the same time tana kokarin tashi tsaye yasa dawani irin sauri yasaki Auwal yay inda take. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 ✍🏻M SHAKUR 7️⃣ Ganin Officer yasaki Auwal yay wurin yarinya datake abu kaman mai aljanu yasa suka juya da gudu suka shiga cikin keken su suka ja suka bace atitin saurama kadan sukara wani hatsarin Allah ya kiyaye. Ahankali ya tsugunna agabanta yana kallonta from head to toe, this is the first time yake kallon fuskanta ganin yanda take fitarda numfashi da kyar yasa yashiga bin jikinta da kallo kota bugene koko tai sustaining any internal injury ne,or something else but babu any sign ajikinta, ahankali yasake maida idanunshi kan fuskarta yana kallon yanda take breathing not knowing exactly what to do, da kyar ta iya bude idanunta tana nishi kaman zata mutu, dishi dishi take gani sosai but she could see mutum akanta yana kaman yana kokarin karantan wani abu, gently taga pink lips dinshi na motsi kaman magana yake mata amman batajin komi, tashi yayi da sauri ganin kaman something is stopping her from breathing maybe tanada blockage a airways dinta, bude gaban motan yayi ya cire jakanta dake wajen ya wurga kujeran mazaunin direba sanan yadawo inda take zaune akasa, ahankali yasa hannunshi yakamo kafadunta sanan gently yadagata yadauketa yakai ta gaban motan yasata aciki yamaida kofan yarufe sanan yazaga ta dayan bangaren direba da sauri daidai ana kiran sallan magrib yabude kofa yana kallon yanda take wani irin dambe da numfashinta da kyar ta iya bude idanunta ta kalli jakanta daya wurga mazaunin direba dayake kokarin daukewa zai zauna ganin haka yasa dasauri yadauki jakan yashigo motan tareda bude jakan cikin zafin nama yashiga ciro abubuwan ciki, kayan shafa, kudi turare wayanta sai daga dan lungun jakan yaga inhaler. Ganin inhaler yasa dasauri yadauka yana kallon jikinshi sai chan yadaga kanshi yakalleta, ganin yanda take mimmika tana juya idanu yasa yacire Marfin inhaler dasauri yamika mata ahankali yace “You are asmatic” yanda take nishi yasa tama kasa karban abun da hannunta ganin haka yasa yakai bakinta yamakala mata yana kallon fuskanta cike da tausayi cikin muryanshi dabakaman ta dazuba very soft dashi yace “try and breath in, gently” yay maganan yana kallon idanunta dakokadan basa buduwa da kyau dudda hawaye baya gangarowa but dogayen eyelash dinta were completely moist ga gajerun hawaye dasuka tsaya wajajen idanun kana ganinta kasan tana wahala, ganin eyes dinta nakokarin closing rup gashi takasa jan inhaler yasa ahankali yakai hannunshi kan soft cheek dinta ya bubbuga sau biyu yace “ke open your eyes” dan kadan tabude idanunta ta kalleshi dudda bamata ganeshi sosai sama sama taji muryanshi yace “breath in, breathhhh” kaman wani abu yashigeta wani kalan karfi taji yazo mata taja inhaler, jin wani sanyi har kasan kirjinta yasa dasauri tadaga hannunta bamatasan tadaura akan nashi ba tawani irin kama inhaler da hannunshi da kyau tana shaka da sauri sauri. Har cikin brain dinshi yaji wani yirrr jin hannun yarinyar akan nashi, ahankali yake kallonta tana shakan inhaler tana sauke ijiyan zuciya tana dan natsuwa idanunta a lumshe har lokacin kaman tai bacci. Almost 10min sanan numfashinta ya daidaita tadena motsi jikinta ko’ina yay relax, ahankali yashiga yunkurin janye hannunshi daga nata gently tabude idanunta, dudda garin yay duhu but baihanata ganin fuskanshi ba sabida hasken motocin dake gittawa ta gefensu, ganin dan sanda wanda she is sure wanda yay saving nata from those guys ne yasa dasauri tasaki hannunshi hakan yasa shima ya janye hannun nashi yakoma mazaunin direba yazauna da kyau, ahankali yace “how are u feeling now”? Ahankali tajanye inhaler, kafin murya chan ciki datai sanyi sosai sabida yanda batada karfi ajikinta tace “I am okay” kallonta yasake yi ganin yanda take zufa tundaga goshinta har wuyanta, calmly yace “can you drive back home”? Batare data kalleshi ba ta girgizamai kai tanajin wani abu na tokaremata wuya she try to swallow it takasa sai kawai tadaura hannayenta kan fuskanta tashiga kuka sosai mara sauti jikinta ko ina narawa, cikin kuka sosai tace “I can’t drive” bata tabajin tsoro kaman nayau abinda ma yasa tai having attack kenan, Binta da kallo yayi yanda take kuka tarufe duka fuskanta da hannun yace “call your family to come and pick you up then” yay maganan yana mikamata wayanda daya cirosu daga jaka dazu, ahankali ta hadiye kukan sanan tasa hannunta ta share fuskan nata tass kafin ahankali tajuyo tasa hannunta takarbi wayan dayake bata, taba wayan tayi ganinshi amace yasa ahankali kaman mai tsoron magana tace “banida chaji tamutu wayan” shiru yayi yana kallonta, yanabin hannunta datake fidgeting da kallo, yadade ahaka sanan gently yakai hannunshi ya murza key ya kunna motan batare daya kalleta ba yace “where is your house”? Kallon hanya tayi dudda gabanta nafaduwa amman hakanan taji takasa kin fadamai, ahankali tace “Wuse” dan juyowa yayi yazubamata idanunshi dasauri tasauke kanta kasa tana kara kankame inhaler dake hannunta, murya chan kasan makoshi yace “where at wuse” ahankali tace “Ademola adetokunbo way, gidanmu nakan hanya” jan motan yayi da bala’in gudu dayasa taji wani kalan mugun tsoro yashigeta yana sharara uban gudu akan titi kaman babanshi ne mai hanyan, har sukakai wuse din, zuwa layin sanan tanunamai wani dankareren gate din wani gida, karasawa yayi yay horn, lekowa mai gadi yayi ganin wata rubabbiyar mota da duk gabanta tai dameji yasa yafito daga gate din yazo wajen motan ta side din direba daidai police man din na saukar da glass din motan kasa kafin ma yay magana hango Khairy yasa dawani irin sauri cikin farin ciki yace “Khairy!” Dawani irin gudu yakoma cikin gida daganan gate sukaji muryanshi yana ihu yace “Alhaji tadawo ga Ummulkhairy nan” yay maganan yana bude gate din da duka karfinshi tsabagen murna, wani irin mahaukacin lafiyayyen gida ne mai bala’in kyau, ga mutane wanda kallo daya yamusu yasan iyayenta ne duk a tsaitsaye, barinma matan wanda ya kyautata zaton itace mahaifiyar yarinyar ce idanunta sunyi ja, saiga yayyinta daduk yagani rikeda waya a hannunsu da alamu ita suke kira, yanayin yanda yaga damuwa tattare dasu kuma duk motan suke kallo yasa baimayi wajen parking space din dayaga an tanada a compound din gidan ba yayi gabansu inda duk suke tsaye sanan ya kashe motan, duk suna tsaye suna kallonsu kafin ya Manaf shiya fara motsi dasaurinshi yakaraso bangaren mazaunin direban yabude kofan yana kallonta, ahankali yabude motar yafito yana kallon su Baba, cikeda girmamawa yakaraso gaban Baba dake kallonshi kuri batare dayay motsi ba dagashi har Mama cikeda natsuwa yace “Barkanku da dare Alhaji, nadawo da yarku gida ne, she had an accident akan titin Apo itada keke napep, ina cikin mota ganin hold up I had to step out naga what’s happening nan naga hatsari akayi motanta yadaki na keke napep ga masu keken su uku about to beat her because she couldn’t apologize, I step in nahana su, I was about arresting them naji faduwanta akasa breathing somehow, I had to let go off the keke guy and reach out to her, at first nadauka ciwo taji kafi daga baya nagano she’s asmatic bayan naga inhaler ajakanta, bata dade da regaining senses nata ba, ganin she can’t drive, I try to make her call family ta but wayanta akashe I had to ensure her safety dan yarinya ce kuma is not safe for her tadawo gida dakanta, saisa nadawo da ita, here is the car key” tunda yake maganan daga Baba har Mama da yayyinta da ita kanta Khairy da Manaf yafito da ita daga mota kanta nakan kirjinshi tai lamo kallon police man dinan dako rufamata asiri baiyi ba take, like babu an atom of lie a maganan shi. Kafin Baba yay magana cikin tsananin bacin rai da damuwa Mama tace “Alhaji kaga abinda Khairy keyi ko, wai Khairy kadai na haifa aduniyan nanne da ita kadai kebani ciwon kai, ga maza yayyinta har uku da sune yama kamata suyi rashin ji amman basuyi sai ya mace ce keyi, yanzu inda wanan bawan Allah this kind hearted officer ya ceceta ba da Allah kadai yasan mezai faru, Allah kadai ne zai sakamai da alkhairi, inda ace bai taimaka mata ba kunsan kalan dukan da masu keken nan zasuma Umma eh, wlh……” dasauri Manaf yace “Mama please we are not alone here” cikin fushi sosai Mama tace “abinda kukeyi kenan dagaku har mahaifinku saisa Khairy duk ta baci haka, zaki gamu dani Khairy” tama Khairy wani mugun kallo taredayin kwafa sanan tawuce ciki fuuuu cikeda bacin rai. Dan murmushi Baba yayi sanan yasa hannu yakarbi car key dayake bashi anatse yakai hannunshi yakama na officer cikeda murmushi yace “thank you, nagode nagode, I can’t even thank you enough, Allah yamaka albarka for saving Ummulkhair, nagode officer, Allah yamaka Albarka” gyadamai kai ahankali yayi yace “saida safen ku bari natafi” dasauri Baba yace “bari Mu’az yakaika wajen motanka please is late” dasauri yace “a’a Alhaji, dare yayi, yazauna agida I can manage, saida safen ku” yay maganan yana juyawa zai wuce dasauri Baba yace “youngman, I mean officer” jin Baba yakirashi yasa ya tsaya tareda juyowa yakalli Baba, ahankali Baba yace “baka fadimin sunanka ba” dan jim yayi yana kallon Baba kaman bazaiyi magana ba sai chan yace “sunana ASP Aliyu Hydar Zango” gyadamai kai Baba yayi yace “Allah maka albarka Aliyu Hydar” murmushi kadan yayi tareda juyawa yana tafiya one one kaman Gwarzo yawuce yafita daga gidan. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 ✍🏻M SHAKUR 8️⃣ Ajiyan zuciya Baba yasauke sanan yajuyo da kanshi yazubama Khairy idanunshi da kallo daya tamai kawai tafashe da mugun kuka, duk duniya babu wanda take tsoro kaman mahaifinta, Baba is the best father amman not just her kowa tsoron fushi Baba yake agidan nan sai Mama dan idan Baba ya burkice ko ita bata iya taroshi, tsugunnawa tayi awajen tana kuka sosai tace “Baba dan Allah kayakuri wlh wlh bazan karaba please I am so sorr…..” baima jira sauran maganan ta ba yawuce ciki shima fuuuu, cikeda tashin hankali takalli yayanta tace “Ya Manaf na shiga uku daga Baba har Mama fushi suke dani” cikin fushi Mu’az yace “da murna kikeso suyi dake sabida bakida hankali do you know how worried they were, saida akasa direba yakoma gidan bikin nan amman baaa ganki ba wai kintafi, Khairy tunda kike arayuwan ki kintaba tuka mota ne dazaki fara yau inda kinje kin kashe kanki ko kinjima kanki ciwo da yaya kikeso muji eh, kawai gakinan ne girma kawai kike amman bakida hankali ko kwara daya stupid girl” yawuce yajuya yay flat dinsu, hararanta Maheer yayi dudda tabashi tausayi yace “babu abinda ta iya sai rashin kunya da tara kawaye, inda police man dinan bai ceceki ba dakin gane shayi ma ruwane, fitsararra kawai” shima yajuya yatafi, ahankali Ya Manaf yasa hannu yadagota yace “stop crying muje kije change this clothes shower kici abinci and sleep” yay maganan yana sakinta yakoma mota ya tattara kayan jakanta yahada mata ya rike sanan yazo yakama hannunta suka shigo falon, Baba kadaine zaune a falon yana rikeda jarida hakan yasa sukai hanyar stairs, cikin kakkausan murya Baba yace “kawomin wayan ki nan” wani irin fashewa da kuka tasakeyi sosai jikinta har rawa yake ta karbi jakanta daga hannun ya Manaf ba musu hannu tasa taciro wayan sanan ahankali tana sheshekan kuka takaraso wajen Baba tabashi wayan, karba yayi ya ijiye gefenshi, sanan yajuyo yakalleta yace “Ummulkhair” muryanta har shakewa tayi tace “Naam Baba” cikin kakkausan murya yace “I ban you from going outside this house for a whole week” zubewa tayi agabanshi tana girgizamai kai tace “Baba please I am sorry dan Allah” cikeda fada yace “nabata ki dayawa, nabaki freedom dayawa kullum your Mum is complaining yau nagani da idanu na, dan haka bazaki saka kafa kifita daga gidan nan ba dagayau har zuwa kwana bakwai, ba school ba islamiyya, sanan ko friend naki guda daya nazo nagani kokuma aka gayamin tazo saina kulleta, i will even tell the gateman koda wasa yabar kawayenki suka shigo cikin gidan nan abakin aikinshi dan haka duk wacce tazo yacemata ma bakinan kowani abun I don’t care” sosai take kuka tana girgizamai kai Baba baitaba mata Wanan kalan punishment dinba tsawa yadaka mata. “tashi daga gabana!” da sauri ta tashi tawuce sama da gudu tana kuka Ya Manaf yabita da kallo yay jim sanan ahankali yadawo falon zama yayi kusada Baba ahankali yace “Baba please kayakuri, punishment dinan yay tsauri dayawa, Khairy batada hankali har yanzu Baba, mudena kallonta kaman wata Babba sabida tana final year a school, Baba she is just 20, yanzu shine lokacin her growth, lokacin datake feeling she’s capable itama takai matsayin ahankali zamu nuna mata this and that, but Baba hanata fita, hanata zuwa school, karbe wayanta, dakuma Hana kawayenta zuwa wajenta I feel is too much Baba, she will be depress” wani mugun kallo Baba yamai yace “Manaf koyamin tarbiyan yara kake?” Cikeda girmamawa yace “a’a Baba” cikin kakkausan murya Baba yace “to tashi daga nan wajen” ahankali yatashi zaiyi sama Baba yace “barin flat din nace kayi katafi naku” ganin ran Baba abace yake sosai yasa baiyi gardama ba ya sauko yazo yajuya yafita daga falon. Waya Baba yadauka yakira wata number, ko 10min baa daukaba wani doctor magidanci haka yazo, tashi Baba yayi sukai sama, afalon sama Baba yanunama Dr kujera ya zauna sanan yawuce dakin Khairy saida yafara knocking sanan yashiga tana zaune kan gado ta chanza doguwan rigan jikinta tasa wata na Atampa simple tasa hula akanta idanunta sunyi jajir sundan kumbura, tana ganin Baba dasauri ta kwanta, ba Yabo ba fallasa yace “fito adubaki” yay maganan ya tsaya yana kallonta tashi tayi ahankali sanan tasaka slippers juyawa Baba yayi tabishi abaya suka taho falon gaida Dr tayi sanan tazauna, dubata yayi yamata yan tattanbaya tana bashi amsa sanan yabata wasu magani guda biyu kafin yakalli Baba yace “shikenan Alhaji” kallonta Baba yayi yace “wuce kitchen kije kici abinci kisha magani” gyadamai kai tayi sanan yajuya shida Dr suka fice, saida sukakai waje wajen motanshi sanan Baba yace “are you sure Dr she’s okay?” Dan murmushi yayi yace “eh, ai Asmanta yaragu sosai bakaman da ba datake having constant attack, I am telling u abinda ma yatada nayau was mugun tsoratan datayi saisa numfashinta yafara mata wuyan kamawa, wlh she’s very lucky tasami wanda yataimaka mata she would’ve lost….” Dasauri Baba yace “Alhamdulillah she’s fine” gyadamai kai Dr yayi yace “yes, bari idan anything change call me, but for now let her relax and rest system dinta yahuta, magungunan dana bata zaisata bacci sosai” gyadamai kai Baba yayi suka gaisa yashiga motanshi yaja yawuce. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 ✍🏻M SHAKUR 9️⃣ Wuraren 5 Baba ya shigo da kanshi yatadata don sallan asuba, da kyar ta tashi saida yaga tashiga bayi sanan yajuya yafice, tana idar da salla da kyar ta iya lallabawa takoma gado sai wani baccin. Wuraren 11:30 ta tashi daga bacci, ita kanta wani dadin jikinta taji taji, ahankali ta tashi zaune tasauke kafanta kasa tana kallon dakin, dakinta very clean and very fine kana ganin dakin kaga dakin wacce akeji da ita, tashi tayi ahankali dagakan gado tai wajen window dakinta bude window tayi haske yawani daki fuskanta lumshe idanu tayi kafin ahankali tabudesu starring into compound dinsu that is very fine idanunta suka sauka kan motar ta da ake pake agidan, faduwa gabanta yayi ganin yanda gaban motan yay completely baci, maida labulen tayi tarufe window feeling sad sai yanzu ta tuna abinda yafaru sanan tawuce tashiga bayi, wanka tayi tafito daure dawani pink towel, karasawa tayi gaban madubi takalli kanta kodan tayi bacci sosai ne gani tayi tana wani kalan sheki, fatarta nawani kalan glowing and sparkling, yatsine fuska tayi sanan tawuce tadauko kaya a wardrobe tasaka wani pink half gown na cotton, batama tsaya daura dan kwali ba tasaka slippers kawai tafito gabanta na dukan uku uku tsayawa tayi wajen bene taleka falo ganin Mama bata falo yasa ahankali tajuyo tai gaban dakinta, tsayawa tayi sanan tasauke ijiyan zuciya ahankali tasa hannunta tai knocking ahankali, jin baaa amsaba kuma ta tabbatar Mama naciki yasa ahankali tabude kofan dakin tadan leka tana shiga ciki, hada idanu tayi da Mama dake zaune kan couch na dakin tana karanta wani Littafin zikiri dake hannunta, babu ko alamun wasa akan fuskanta tace “fitan min daga daki Ummulkhair” dan rau rau tayida idanunta kaman zatai kuka murya chan kasa kaman na Yar baby amugun shagwabe tace “Mamaaa sorrry please, kinj….” “Get out of this room Khairy” gyadama Mama kai tayi ahankali sanan tajuya tana tafiya kaman wacce ke koyon tafiya tana tunanin abinda zatayi Mama tahakura kaman daga sama Mama kawai taji Khairy taja wani uban nishi tana bubbuga kirjinta tayi baya zata fadi, wani kalan salati Mama tasaki tawani ijiye Littafin kan kujera ta taso dasauri ta tareta da hannayenta tace “Subhanallahi Khairy, Khairy, ina inhaler ki”? wani kalan dadi taji ya lullube ta ganin yanda Mama harta tsorata ta taso, kawai Mama gani tayi yarinya ta kankameta tafashe dawani sangartaccen kuka ajikin Mama tace “Mama please kiyakuri wlh wlh bazan kara abinda nayi jiyaba I promise Mummy, kikai fushi dani ina zansa kaina eh kinaso in mutu ne da ciwo? U are my best friend Mama, u are my happiness kika shareni I will be shattered, Mama dan Allah kinji smile for me haba my world best, best of the best, bestest, the best Mama in the world, Mama dan Allah kiyafemin” tai maganan tana kara kankame Mama kaman wata yar yarinyar da baa dade da yayewa ba, dudda yanda ran Mama yake abace amman saida jikinta yay sanyi sosai, ahankali tadaga hannayenta taciro Khairy daga jikinta ta tsare fuskanta da idanu hardan rama tayi ga hawaye sun cika idanunta, Mama takai hannunta ta share mata idanu sanan takama hannunta tajata zuwa bakin gadonta zaunar da ita tayi sanan tazauna agefenta tana kallonta ahankali tace “Ummulkhair bakiji, ba fushi nake dake ba I am only trying na nuna miki kuskurenki, ke y’a mace ce bazaki dawwama agidan mahaifinki ba dole zakiyi aure kije gidan mijinki, i want to teach you not just life but how to live life Khairy, inaso nakoya miki rayuwa dakuma yanda ake zaman duniya lafiya, ke mace ce Baban ki da yayyinki cannot teach you abinda ni mahaifiyar ki mace zata iya koyamiki, akwai mutuwa, akwai ciwo, akwai kuma tsufa any of the two can happen to me Khairy yaya zaki kare eh? Kin taba tunanin, wanan kawayen yau baki bikin wanan gobe baki bikin wanchan kene aganki achan gidan bikin kina tika rawa ko achan birthday kina tika rawa ko Micheal Jackson yaganki kina rawa saiya baki fili yarinya saikace rainon dujal, what are all this behaviors Khairy? Sabida ana cewa ke yarinya ce kinsan yara nawa wanda ma kin girmesu sukai aure suka hayyayafa eh? Yanzu abin haryakai kija mota dakanki ki shiga titi da daddare Ummulkhairy idan da wani abu yasameki how do you want me to cope? Kasheni kikeso kiyi da damuwa?” Dasauri ta girgizama Mama kai ahankali tace “Mama bazan karaba wlh” Ijiyan zuciya Mama tasauke ahankali sanan tai murmushi tana kallon yanda idanunta sukai zuru zuru long kalaban kanta duksun barbaje sun sauko fuskanta, hannun Mama takai ta gyara mata gashin sanan ta shafa fuskanta tace “ke kadai ne y’a mace da Allah yabani aduniyan nan Ummulkhair, inaso ki natsu, wisen up, anything can happen to me, and I want you to be able to take care of yourself, su Manaf, Mu’az da Maheer, you will be their Mum, kindaiga banda kowa, I told dukanku labarin nan agidan marayu Baban ku yaganni ya auroni ina gidanshi nai karatu, bansan any family naba dazance yau idan bani inada wata danasan zata rikeminku tsakani ga Allah so I want you to take after me kinji, ki natsu and know what you are doing” fashewa da kuka tayi ahankali duk zuciyanta namata nauyi da duhu, bayan hannunta takai ahankali ta share idanunta sanan cikin sheshekan kuka tace “Mama maisa duk idan namiki laifi saikitamin magana kaman zaki mutu eh? Wlh Mama bazan karaba na rantse da Allah kinji, dan Allah kayakuri kuma kawayena zan ragesu, Mama I love you a lot please kidena fushi dani kuma kidena magana haka kinji, Mama you will leave long har yarana zaki goya” murmushi Mama tamata she just wish zata iya daina mata magana hakan, kumatunta taja cikeda so tace “oya stop crying inba hakaba I will snap your face natura a group dinku na nunama friends naki sugan cewa the famous Khairiry dinsu is a crying queen agida” dasauri tasa hannu tashare fuskanta ta washe jerin white teeth nata kananu dakeda bala’in kyau tace “Mama nadena” dan dariya Mama tayi tace “oya je bude drawer nan nawa ki kawo comb da kipiya ayi wanan tsifan” da sauri tasauka dagakan gadon tai wajen drawer dakin Mama tabi bayanta da kallo wani irin girma Khairy keyi da batasan ina zatada girma ba ga shape kaman ita tai kanta, daukowa comb da kifiyan tayi tajuyo Mama tabi damemmen cikinta da kallo tace “wuce kidebo breakfast kidawo” tai maganan tana karban comb din hannun nata, juyawa tayi tafita daga dakin koba komi ta lallashi Mama tahakura saura Baba shikuma da Baffa zata hadashi simple. Dinning taje, plate tadauka tana bude kula, chips tadeba da sausage batare data taba kwan wajenba sanan takada tea tajera komi a tray tadawo dakin Mama, ganin Mama na rubutu da pen a dairy dinta wanda inda sabo tasaba ganinta tana yan rubuce rubuce aciki yasa tai murmushi ijiye abincin tayi anan kasan carpet sanan ta taso tazo inda Mama take tana kallon abinda take rubutawa da sauri Mama tarufe dairy tadago kanta tana hararanta tace “lpy” turo baki tayi ashagwabe tace “Mama handwriting dinki nake kallo fa, wlh Mama handwriting dinki yafi harna Baba kyau, inama nine nakeda fine handwriting haka, amman rubutuna kaman tafiyan tsutsa” hannu Mama takai ta dakamata duka a kafa tace “kincikani da surutu wuce kije kiyi breakfast kizo namiki tsifan” wucewa tayi tana dan dariya sanan tazauna tanacin abincin tana wasadashi kaman wata yar yarinya Mama kawai ta tasata agaba tana kallo, saida tagama sanan ta kwasa tafita dasu kafin tadawo Mama tahaumata tsifan kan. ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? ************************** 💫 ALKAWARIN ZUCIYA💫 ✍🏻M SHAKUR 🔟 For those asking me how to subscribe Dan shiga group din danake posting all you have to do is pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na. Dan magana dani directly click on this link wa.me/+2347012181461 ******* Free page UK Karan wayanshi yatadashi daga dan gajeren baccin dayake yi mai dadi sabida shishan dayasha harya bugar dashi, ahankali yasa hannunshi da kyar yajawo wayan sanan yakai gaban fuskanshi yakalli screen din ganin Dad yasa duka baccin idanunshi suka washe da sauri yatashi yana gyara zama ya matsar da shisha pot din gefe sanan yadaura wayan nashi akunne cikeda girmamawa yace “Abba ina yini” daga tachan bangaren cikin muryan dattaku irin muryan daba na yaraba dinan kanaji kasan na Babba ne yace “Zayn naji muryanka wani irin lafiyanka kalau”? Dan yatsine fuska yayi yarasa maisa Abba always gets him, kafin yadan saki murmushi yace “Abba bacci ne daman yadan kwasheni amman nariga natashi, yasu Ammi Abba?” murmushi Abba yayi mai dan sautin ta wayan yace “Ammi dakowa duk suna lpy, Matar kaninka Hafiz tahaihu ansami y’a mace” dan ware idanunshi yayi cikeda mamaki dakuma farinciki sosai yace “Masha Allah, Allah ya raya mana” anatse Abba yace “Ameen ya rabb, when will you be rounding up PHd dinan Son”? Ahankali yace “nan da 2months Abba In sha Allah” “Uhmm” Abba yafadi yana gyara murya yace “Masha Allah Allah yasa kagama lpy Allah ya sanya Albarka acikin sa” ahankali yace “Ameen Abba” dan gyaran murya Abba yayi yace “Zayn tunda kataso bama kai kadai ba duka yaran dana haifa aduniyan nan I always give you all abubuwan dakukeso, I support dreams dinku with all I can, Zayn tunkana yaro dan kankani na lura kai yaro mai kwazo ne sanan gason karatu, I supported you sabida inaso kai leaving dreams dinka, bantaba complain ba dan buri na shine kagama duka karatun dakake, Hafiz yana gama masters dinshi yanuna shi aure yakeso I supported him as well da sauran kanninka mata, burina amatsayina na mahaifi shine naga yarana na cikin farin ciki sanan suna rayuwa yanda sukeso madaman bai sabama koyarwan ma’ikin Allah ba tsira da amincin Allah su tabbata agareshi, dan haka Zayn dazaran watan nin nan biyu dakafadi mini yanzu sun cika, inaso ka tattaro yinaka inaka kadawo nan naijeriya, kafara aikin ka anan sanan kai aure kaima ka natsu kanajina” ahankali yace “eh Abba” yanadan yatsine fuska me a aure please da all this Nigeria’s father values it so much, aure is problem, damuwa ce kawai tacika aure, shifa baijin zai iya rayuwan da he will cater for someone ba, ko babes dinshi whenever he’s honey he feed on them idan yagama ya tashi ke kikasan yanda zaki da kanki, ina zaiwani iya aure dashi zai dinga kulada wata, lallai! “Zayn kanajina” yaji maganan Abba dasauri yace “eh Abba” Abba yacigaba yace “kaine Babban d’ana, tsufa yazo Zayn inaso tun yanzu da raina da lafiyana nahada kan yarana agari guda, yau da wani abu zai sameni kaine babba kaine zaka rikemin gida, dan haka nasanka da natsuwa Zayn dakuma tsoron Allah amman bazan gaji da gayamaka ba kadingajin tsoron Allah aduk inda kake sanan ka kiyayi abokanai marasa kyau, Allah maka albarka, idan na ijiye wayan nan zan aika maka da kudi kaji” dasauri yace “Abba no, inada kudi kamanta ina musu aiki anan ana biyana duk wata” anatse Abba yace “kudin aikinka daban kudin na ni mahaifinka daban as long as bakai aureba baka da iyali naka na kanka nine komi naka Zayn Allah maka albarka” murmushi yayi har cikin ranshi yanason yanda Abban shi ke sonshi, kobakasan komi nagidansu ba dazaran kashigo gidan kagansu duka kasan Abba yafison shi kan duka yaran daya haifa shi kanshi baisan mesa ba, kowan nan zancen haihuwan he’s sure yanaji yakirashi before Ammi kanta takirashi Abba yakirashi sau dubu, Karan alert dayaji yasa yakalli wayanshi, $10,000 dollars yagani, murmushi kawai yayi ya ijiye wayan yatashi yaje yay wanka yasan nan bada dadewa ba shima Hafiz zai kirashi. Wanka yayi ya shirya cikin wani dan gajeren wando mai bala’in kyau black sai farin riga, feffesa turare yayi sanan yasaka wani black crocs na designers dayama white kafanshi kyau sosai kaman kafan bature, kana ganinshi kaga irin yaran yan gayun nan yan hutu kuma yan iska at the same time sanan yawuce akan table yadauki car key nashi yabude kofa yafito yanadan yatsine fuska ganin rana yafito yau sosai, ciki yadawo yadauki sunglasses dinshi yasaka kafin yafito yaja kofan nashi yarufe sanan yasauka kasa, motanshi yabude yashiga sanan yafice daga gidan yana mahaukacin gudu abinshi waka natashi daga motanshi. Tana ganin fitanshi zama tayi dirshan anan wajen window jikinta ko’ina narawa kaman zata haukace inda ace zaa gayamata Zayn yamata magani ne da wlh zata yarda sabida wani wutan sonshi datakeji azuciyan ta is another thing, ganin kaman zuciyanta na neman daina aiki yasa ta tashi tadauki wayanta akan dinning tai dialing number Jully, ringing daya Jully tadauka kafin ma Jully tai magana tahau mata magana kaman wacce tazare. “Jully if u ever love me Jully please help me, Jully zan mutu, soyayyan Zayn is about to kill me, I was sent to school amman nakasa komi na school I keep stalking yaron dabaimasan inayi ba, wayyo Allah na wlh zuciyanta kaman ta kumbura sabida son Zayn I just want him, I want him so bad sosai, I want him to hold me, hug me kiss me And tell me he loves me, i am loosing my head my mind and my whole soul, ina tsoron kar watarana ki tashi kiga na mutu because of Zayn, nagayamai yau ina sonshi all he did was slam the door afuskana, Jully help me please” bakaramin tausayi Ayshu tabata ba jitayi kaman tamata kuka, murya chan kasa tace “Ayshu calm down, I am coming don’t do anything just give me 5min u will see me kinji” gyadamata kai Ayshu tayi kaman tana ganinta sanan tacire eayan daga kunenta ta ijiye akasa itama takoma kasa gaban dinning ta zauna idan kaganta zaka dauka ta haukace tana zaune awajen taga wayanta yahau ringing Mommy tagani amman takasa dagawa, wajajen 10min tana zaune awajen saiga Jully tashigo tana sanye da Riga da jeans, da handbag dinta a hannu ganin yanda Ayshu tazauna akasa idanunta sunyi jazur sun chanza launi tsabagen damuwa yasa dasauri tai inda take zama tayi kusada wajen tana kallon fuskanta tace “Ayshu look at you My baby, Ayshu you need help I think we should go see a Doctor” girgiza mata kai tayi cikin wani kalan yanayi tace “Jully I love him, I am madly inlove with…..” “someone that doesn’t even know about your existence Ayshu, yaron nan never loves any woman ke u are an eyewitness yanda kike stalking nashi kina ganin yanda yake chanza babes, kina ganin yanda yake rayuwa, and u still love him kinason ki karake like all his other women” ga mamakinta gyadamata kai Ayshu tayi tace “eh, as long as he will be with me, smile with me, hold me lemme feel his warm soft skin akan nawa and those his succulent lips while he stares into my eyes dawayan nan sexy eyes din nashi dat always look kaman yanajin bacci I want, his eyes use to make my body cringe,Jully I want Zayn” kallonta kawai Jully take dan kawarta is obsess, one a scale na 10, Ayshu is even more than 10 dawanan fitinannen son datakema yaron nan, ajiyan zuciya tasauke tana kallonta tace “Ayshu I want you to define the terms in your own way, sama da kowa kinsan cewa yaron chan is not the love type kinsan cewa bala’in dan iska ne shi, f**k boy and a play boy, Ayshu tell me what do you exactly want from him tunda kinsan shi waye shi” shiru Ayshu tayi tana kallon Jully kafin ahankali tace “I want to sleep with him! I want to know him in and out, I want to have koda one single memory nawa da shi wanda I will always dwell akanshi, I want to share something da Zayn Jully….” Ajiyan zuciya Jully ta sauke tasan menene so amman harga Allah bataso kawarta taso Zayn ba she prefers her Kabir dakenan kaman zai zare akanta amman tace sai Zayn, jakanta tabude sanan taciro wani dan karamin white kwalba dawani blue liquid abu ke ciki tamikama Ayshu, kallonta Ayshu tayi sanan takalli kwalban abin batare data karba ba tace “what is this”? Dan murmushi July tayi tace “this is ur problem solver u have no idea nawa na kashe yanzun nan kafin na iso wajen nan kafin yaran nan su saidamin da abin nan, yanzu dai not that bakince kinsan password din kofanshi ba” dasauri Ayshu ta gyadamata kai, murmushi Jully tayi tace “perfect, u see this serum is for shisha acikin shisha ake zubawa nasanshi kuma he always take shisha, zaki shiga dakinshi get his shisha pot kibude ki kwara serum din aciki” dasauri bakinta har rawa yake tace “mezai faru idan ya kunna shishan ya sha to bayan najuye” hararanta Jully tayi tana murmushi tace “u don’t wanna know” cikeda kosawa tace “please tell me Jully” ahankali Jully tace “this serum dakike gani will turn dat guy to a beast, ke he can even cry for you and beg you kibashi yaci inba hakaba zaiji kaman zai mutu” wani kalan tashi Ayshu tayi da sauri tana karban abin daga hannunshi tace “bayanan Bari naje nasaka” kafinma Jully tamata magana hartai kofa tabude tafice Jully kawai tai shiru bata taba ganin so irin na Ayshu ba tsabagen yanda take monitoring activities nashi har password na kofanshi tasani, she just hope this satisfy whatever crave it is dayake zuciyanta ko tayi concentrating a school tana zaune a inda take saiga Ayshu tadawo da empty bottle din tana dariyan jin dadi sosai tace “done” dariya Jully tayi tace “to mutafi school munada lectures” make kafada Ayshu tayi tace “what if yadawo anjima basai dare ba, kedai kitafi ni yanzu ma Mommy zan kira ta kirani dazu ban amsa ba” tashi Jully tayi tace “natafi” bye friend….. Tana zaune all ranan a falo bai dawo gidan ba as usual sai wajajen 1 nadare yashigo gidan, sai addu’a take karya dawo da wata, ganin shi kadai yadawo yasa taji zuciyanta yamata wani dadi daki yawuce yay wanka sanan yafito da boxer as usual tana ganin inuwanshi ta madubi, dauko shisha pot dinshi yayi ya kunna sanan yazauna kan kujera yana tattaba wayanshi kafin taga yamika hannu yadauki pipe din wani tsallen dadi tafara tana yes yes take it, zuka yayi yana tattaba waya sanan yafito da pipe din ya busoda hayakin waje kaman zata haukace sabida dadi rawa tafara sosai. Comfortably yakeshan shisha shi yana streaming online kafin chan yaga message na Hafiz yaturomai pictures dasauri ya shiga watsapp din yabude hotMunan yana dubawa na baby ne yanadan murmushi he love babies. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 ✍🏻M SHAKUR 1️⃣1️⃣ For business advert or promotion chat me up directly on watsapp by clicking on this link : wa.me/+2347012181461 Dan lumshe idanu kadan yayi yabudesu da sauri tareda ijiye wayan tsigan jikinshi nawani kalan tashi gabanshi na mahaukacin tashi da baida control of , maranshi na murdawa yanajin wani irin bukata dashi kanshi baisan daga ina tazo ba , shishan yashiga sha da sauri da sauri kozaidan bugar dashi yasakashi bacci yanadan tsaki cikeda kulewa yace " shit ! " He don't even know ko shishan karamishi yake oho jiyayi his world is clouding and going sideways , ahankali yasaki pipe din shishan yawani fadi akasa yana cizan lips idanunshi na kankancewa sosai yana sauke ijiyan zuciya kadan kadan , hannunshi yamika yadauko wayanshi daya yar agefenshi da kyar dayan hannunshi kuma yana kaiwa kan boxer cus he's having mad pains , wayanshi yabude amman bayama gani da kyau ko kadan dazaima iya kiran daya daga cikin yammatan shi , kofanshi yaji anbude anshigo dasauri yajuy o da jajayen idanunshi yakalli wajen , Ayshu ce tashigo tasaka wani red rigan bacci very transparent dababu abinda baya gani ajikinta , tasaki braids dinta kasa tai wani kalan kyau lips dinta na shinning na red janbakin data saka , wani kalan ijiyan zuciya yasauke jijiyan kanshi na fitowa waje tsabagen jaraban dayakeji dakewa yayi yana cizon lips dinshi da kyar ya iya tattaro karfinshi gabaki daya yace " what are you doing here " ? wani kalan murmushi tayi dan yau farin ciki takeji takaraso har inda yake tsugunnawa gaban kujeran itama tayi dab dashi tana kallon fuskanshi da kirjinshi dakenan very very huge ga fadin bala'in gawasu sexy hair dakenan akwance lup lup kamshin nan nashi da ko daga mafarki aka tadata zata iya cewa shine na shiga hancinta yana penetrating azuciyanta , ahankali takai yatsanta dake rawa tsabagen yanda take shakkan shi amman tadaure tace " I come to sleep here don't u want my company " yanda take yAwo da yatsanta akirjinshi kafin tai landing akan nipples dinshi tawani murza nipples din yasa yasaki wani kalan kara . " Mmmmmm " murmushi tayi bata taba sanin she can see Zayn like this ba looking so vulnerable yana pleading with his eyes ma har body sabida yanda yakebin kirjinta da kallo da idanunshi dasuka kankance , janye hannunta tayi daga kan nipples dinshi , ganin yanda yake kallonta without action and ita action takeso yasa ta mike tsaye tana wani irin tafiya tana juyamai ass dinta dayake ganin komi ta rigan tadan waigo ta kalleshi tace " come nabaka abinda kakeso , it's all yours " saida takai daidai hanyar bedroom nashi sanan ta tsaya tajuyo takalleshi ganin har lokacin kallonta yake kaman wani maye she can see yanda eyes nashi suka nuna how badly he wants her , rigan jikinta tawani cire tayar anan gaban kofan bathroom din sanan tawani juyo tana shafa yan matsakaitan boobs dinta tana lashe lips tana kallonshi , wani kalan tashi tsaye yaye ita kanta saida gabanta yafadi ganin yanda boxer jikinshi yatashi kafin tagama tunani jitayi anwani fizgota kaman rago yaaaaa kawai taji ya yaga pant na jik inta kafin yabude kofan bedroom din kawai taji yawani wurgata kan clean royal gadonshi ...... Ahankali take bude idonta dasuka mata bala'in nauyi , ko'ina najikinta yay wani kalan tsamin gaske , ijiyan zuciya tasauke tanabin gadon datake da kallo tana kara lumshe idanu kaman karta tashi takeji , kawai sotake tacigaba da shakan wannan kamshin turaren datakeji nashi komi. najiya da daddare nadawo mata she is just sure sumewa tayi , oh my God anya akwai namiji kaman Zayn aduniyan nan kuwalman that guy is fire in bed . Ahankali tana cizan lips dinta ta tashi zaune tana kallon agogo dake gefen side drawer nashi 11:30 nasafe , dakinshi tabi kallo dakin is so clean very neat , babu datti kodaya , wow ! Da kyar ta iya saukenta a kasa sanan tamike tsaye komawa tayi dasauri tazauna dan pains din datakeji ko lokacin datai sex d first time da KB bataji irin wannan ba , tadade ahaka sanan tadaure takara tashi tana kallon bakin kofan bedroom din datagani abude ga riganta na. jiya akasa inda tacire tanarshi nan yake karasawa tayi ahankali ta tsugunna tadauka sanan tasaka kafin tadau pant nata daya yaga yake kasa shima tadukunkune tarike a hannu sanan ahankali kanta na kasa tafi falon tana tafiya kadan dan batason ta nunamai ragonta ko wani gazawa nata ko gajiya. , yana zaune akan kujera dagashi sai towel a waist nashi yana video call dawata baturiya awaya dan kallo daya tamai ta hango baturiyan a screen nashi , sai kiranshi baby baby take yana murmushi while sipping kofi hankalishi kwance , gefenshi yan bandur bandur na dollars guda uku ne , kasa jure kin kallonshi tayi tadan juyo tana binshi da kallo kozAice mata wani abu amman kaman baimasan dawata a falon ba magana yake ana tse ayangance yana sipping kofi abinshi , daurewa tayi ta wuceshi tai hanyar kofa harta bude kofar zata fice daga sama taji muryanshi yace " you , Hey " danshi harga Allah he don't even know her name , dan rike tayi jin yana kiranta takalleshi ahankali lips nata narawa tace " mu... me ? "Maida kanshi yayi kan wayan yace" excuse me babe just a sec " sanan yadaga kanshi yakalleta yana nunamata sarakuna gefenshi yace " come get this ur pay " wani kalan kallo tamai her pay yadauka ita Yar iskace kaman sauran karuwanshi komene , rike tayi dasauri zata fice daga dakin jin zagi da dan graded ." dont ! "Yafadi babu alamun wasa kan fuskanshi , juyowa tayi yakalleshi jitayi zuciyata na buga fast hakan yasa tama kasa motsi kawai ta tsaya inda take kaman jira take yabata , kudin yadauka hankalinshi nakan wayan jin yarinyar Namai magana sanan yajuyo yakalleta yajefamata yace " u can throw su tafi waje but just get them from my room okay , is ur fee " yana gama maganan yacigaba da video call din dayake abinshi tadade tana kallonshi kaman bashine yake ihu kamar zai haukace akanta jiyaba kafin ahankali ta tsugunna tashiga kwashe kudin ita kanta batasan Mesa ba. take daukan kudin ba abinda ta sani bataso ta batamai rainin hankali sabida wutan sonshi dake cinta arai amman batada abinda zatai da kudin nan cus she missing nothing . sanan ahankali tajuya tafice idonta sunyi jazur , dakinta tabude tashiga Jully tagani zaune ganinta yasa Jully ta mike tana binta da ka llo tundaga sama har kasa tace " how far Ayshu" wani irin kuka Ayshu tafashe dashi dake kunshe da farinciki bakin ciki dakoma wani kalan emotion tarungume Jully ahankali tace " Jully thank you , u are the best friend in this world " murmushi Jully tayi tace " je ki shawa ki daina gode min, u look terrible " dan dariya tayi tasake tana fuskantar tawuce tana tafiya ahankali tai daki Jully tabita da kallo ganin yanda yakusan kasheta , girgiza kai kawai tayi ance idan abinda yafi karfinta da bakada abinda zaka iyayi sai ka girgiza kai , kitchen tawuce tanada mata tea lafiyayye da chips sanan tazuba komi tai arranging a tray , tanada paracetamol tasamata akan tray din , tai bedroom dinta , akan gado taganta zaune tasaka wani simple english gown , karasowa Jully tayi ta dije tray kan gado tana kallonta. tace "ka tabbata lafiya"? murmushi Ayshu tayi tace " kinga yakusan kasheni ko , me zan iya cewa zayn dabba ce " tai maganan tanadan lumshe idanu sanan tabude takalli Jully tace " wlh Jully Kabir ba haka bane. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 ✍🏻M SHAKUR 1️⃣2️⃣ 17 Free page Nigeria Tuntuni Baba yadawo saida yagamajin maganan datama Khairy tsaf sanan ahankali ya sauke ijiyan zuciya daya nuna tsantsan damuwa sanan yawuce yashiga dakinshi , manyan kayan jikinshi yarage dama sabida Mama yadawo yasan fushi take , koyaya yafita bayan yasan tana fushi to baida kwanciyan hankali , ahankali yazauna kan wata lafiyayyen kujera dake dakin nashi na massage ya mikar da kafafunshi tareda daura hannu dayakan daya yana sauke ajiyan zuciya mai sauti sanan ahankali ya lumshe idanunshi jin kujeran tafara massaging jikinshi sama sama yanajin surutun Khairy datake ma Mama dake mata tsifa , yana zaune awajen yaji Mama tace " taje ta taje kan " sanan yaji karan bude kofa wanda yasan Khairy ce . Yadade zaune ahaka sanan yaji karan an bude kofan dakinshi hakan yasa ahankali yabude idanunshi ganin Mama ce tana sanye da doguwan rigan atampa mai kyau ta daura kallabi tai kyau sosai tana kallonshi cikeda so da kauna yasa cikin tausasshen look yasakin mata annurin fuskanshi sanan yamika mata hannunshi alamun ta iso gareshi , murmushi tayi ta maida kofan tarufe sanan takaraso ciki table din tsakiyan dakin tajawo gefen kujeran sanan tazauna kusadashi ahankali tace " ina kwana " hannunta yabi da kallo dayasha jan lallen salatef sanan yasaka hannunshi yakama hannunta nata yarike gam yanajin dumin hannun kafin ahankali yadaura hannun kan kirjinshi sanan yasake sauke ijiyan zuciya yana kallon fuskanta cikin tsantsan muryan so yace " ina sonki Maryam , karki kara fushi dani kinji " murmushi tamai sanan takai dayan hannunta tadaura kan saman nashi tana kallon fuskanshi tace " bazan taba iya fushi dakaiba , sabida irin karfin soyayyan danake maka Baban Manaf " murmushi yamata sanan yazare ha nnunshi yakama duka hannayenta biyun yakama yakai bakinshi yamusu kiss sanan yamaidosu kirjinshi yanabin fuskanta da kallo ganin damuwa aciki , ahankali yace " menene " dan shiru tayi tana kallonshi tace " inaso kajanye hukunci dakama Khairy kabarta takoma school gobe ta tafi , banson daidai dasau daya Khairy tasan inada wata mu'amala da asibiti kuma kaga gobe zamuje muga Dr " shiru yayi yana kallonta cikin yan sakanni idanunshi taga sun koma sunyija , murmushi tadanyi sanan ahankali tazare hannunta daga nashi sanan takai duka hannayen tana shafa fararen gemunshi cikin wani irin kulawa tace " baka sake cemin komi kan maganan kara Auren dana maka ba ? " Hannunshi yasa ya kabar da hannayenta dake kan gemunshi sanan yajuyar da fuskanshi yakalli gefe alamun he's not interested in maganan , kukan datakeji ta dage ta danne tana kallonshi kafin ahankali takai hannunta takama hannunshi tarike ahankali tace " Baban su Manaf , nidakai we've been married for morethan 40yrs today , Alhamdulillah I get to give u beautiful kids ga yan biyun mu nan Manaf da Mu'az , ga Maheer gakuma Khairy mu , kasan dalilin dayasa na roki wanan alfarman agareka I am doing this for yaranmu , barinma Maheer da Khairy wanda sune kanana , i want them to start learning rayuwa da wata daban amatsayin mahaif ...... " " ya isheni maganan nan Maryam ! " Baba yay maganan da tsawa still batare daya juyo ya kalleta ba , yace " naji Khairy will go to school tomorrow , na janye punishment din , but this should be the last time dazakimin maganan kara aure " murmushi tasaki wacce babu komi cikinta sai kunci da daci , ahankali takai hannunta tajuyo da fuskanshi yana kallonta idanunshi sunyi jajir hancinshi tadanja tana murmushi tace " why are you being stubborn eh " ? Dan runtse idanunshi yayi cikeda ciwo zuciyanshi namai zafi yanamai radadi sanan gently yabude idanunshi yadaurasu akanta yace " Maryam you are the stubborn one here , kinki accepting treatment , babu yanda banyi dakeba dagani harsu Manaf da Baffan su , akwai wanda baimiki magana ba but kinki , ba kin gwammace ki ..... " hannunta tadaura kan bakinshi tana murmushi da duk idan tayi yasan sanyayamai zuciya ahankali tace " yau shekaruna 57 aduniya , na aureka tun inada sha shida , nayi rayuwan aure dakai na shekaru arba'in da daya , and look at me I still look 30 kaman banyi aureba " tai maganan tana dariya tanamai fari da idanu , sanan calmly tace " I am not greedy after enjoying wayan nan shekarun idan Allah yace lokaci yayi sai ince baiyiba ? Baban Manaf kasan meke damuna sama da kowa , treatment dinan bata lokaci ne kawai , sanan karasa cinyeka ma yake , I want kullum idan Ummulkhairy tadawo tundaga compound tana kwalamin kiran nan nata tashigo nabata abinci tanaci tanamin surutu , I want to use the little time daya ragemin to be with all my children , inamusu girki , ina tareda su da karfi na ina musu murmushi , banson nazama burden kan yarana yazamto suna kallona da pity , Khairy na final year yanzu inaso tagama school in peace tasami good grade , you know how Umma take tun tana yarinya idan tadawo gidan nan bananan , b a treatment din da a asibiti zan karake da zamaba nadawo kaman agwai , I rather stay here kullum tadawo taganni , kullum yarana maza suka dawo suganni , I want to die here in this house gidan aurena , taredakai dakuma yarana , please kabarni " wasu gajerun hawaye taga sun gangaro daga gefen idanun Baba yana kallonta yanadan . sakin huci mai zafi , dasauri takai hannunta ta sharemai sanan ahankali tadaura kanta akan kirjinshi hannayenshi yakai kan bayanta yana shafawa murya chan kasa yace " I hate movies tun ina yaro , amman for the first time in my life Maryam sabida ciwon ki I wish I was a super man kokuma inada wani supernatural powers dana ciremiki Wanan ciwon " dan dariya tayi tanakan kirjinshi tana danne kukan datakeji tace " wayace maka bakada supernatural powers din ? Soyayyan ka da kulawanka is what keep me stronger , is what keep me going tun bayan anyi diagnosing dina da wanan ciwon har izuwa yau Baban Manaf , baka taba bacci baka bani magunguna na , kafin kafita aiki dasafe kabani , da rana ko kana office u call , ko katuro any of our boys suzo har gida subani na rana what more can I ask for ? U are my Superman , my superhero , my wonderman , mijina rakena " tai maganan hawaye na gangaro mata da sauri ta share da hannunta tana murmushi . Tana daukan hula tasaka tafito tadawo dakin Mama ganin Mama bata daki yasa tadauki wayan Mama dakekan gado tafito da sauri tai dakinta tana shiga maida kofan tayi tarufe sanan ta shiga bayi , zama tayi a kasan clean bayin nata sanan tashiga contact din Mama number da akai saving da Baffa tai dailing , ringing daya biyu ana uku aka dauka cikin muryan wanda ya manyanta sosai akace " Maryama " dasauri ashagwabe tace " Baffa nine , Khairy ce " cikeda wasa yace " diyar arziki Khairiya kece , yau kuma mekikayi " ? Kaman zatai kuka tace " Baffa wai dan nadauki mota shine Baba yace bazan kara fitaba har tsawon sati daya kuma ba school , sanan Baffa ya kwacemin wayata sanan yahana kawayena zuwa , Baffa kasan kai kadai Baba kejin maganan shi , Baffa please ka kirashi kasa ya janye " anatse yace " kimin . alkawari bazaki kara daukan mota dakanki ba idan lokaci yayi koninan saina koyamiki da kaina kidinga ja " wata kalan muguwan dariya tayi kaman tana magana da tsaranta tace " kai Baffa kaida kaima tukaka ake chab , saidai Ya Hafiz yakoyamin wth ni bazakaje ka maidani gurguwa ba " dan dariya Baffan yayi yace " Matar Hafiz ta haihu munsami mace , yanzu kinzama Anty " wani kalan ihu data tsandala da sauri Baffa yace " jama'a zata hudamin dodon kunne " taushe bakinta tayi da sauri tana dan dariya tana kallon wayan ganin Baffa ya katse tace " su Ya Hafiz andawo Dady , finally nazama Anty , Baba please give me my phone back nakirashi lyye zanje naga Baby " tai maganan tana tashi sanan tafice taje ahankali tabude kofan taleka dakin ganin Mama bata dawo ba ta shige ciki da sauri sanan ta maida wayan tafito takoma nata dakin . Bayan sallan isha tana zaune gaban madubi tana kallon gashinta yanda yawani kwanta kaman tasa shamfo taji Baba ya kwalamata kira wanda tuntuni take jiran kiran , tashi tayi tadau hulanta tasaka sanan tawuce 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 ✍🏻 M SHAKUR 1️⃣3️⃣ WARAKA TEMPLE gidan maganin kowacce irin cuta da izinin Allah Karin niima da dadi Karin dandanonki da duminki Matsewarki ki dawo yar Sha shida Gyaran nono Sa megida sambatu Sa kyauta Maganin Sanyi Da sauran magungunan damuwar da ke addabar mata zaku samu a waraka temple ku tuntubemu a no waya ko Instagram. Don magana dasu directly click on this link wa.me/+2347042419516 Yau dayake Monday sunada lectures 9:00 wuraren 8:00 tasauko ta sanya wata Dubai gown sky blue dayama skin nata bala’in, sai uban sheki fuskanta yake ka kalleta saika juyo kabata second look, yau flat shoe tasaka baki sanan tadauki black bag shima, tana tafiya tana duba jakanta taga ko tasaka komi dan lecturer su na safen nan shege ne ajinshi you must jot inba hakaba yakadaka waje yace “you are not ready for school” Tundaga stairs take kallon Mama dataga tana zaune dinning takife kanta a table which is not like normal Mama, dasauri takarasa wajen dinning din takai hannunta ta taba bayanta tace “Mama” dasauri Mama ta tashi zaune idanunta sunyi ja irin name mugun zazzabin nan kafinma tai magana Khairy tarigata tace “Mama bakida lafiya ne jikinki zafi” dan zaro idanu tayi takai hannunta tana taba jikinta tace “bawani zafi daga AC kika fito Niko dana gama da kitchen ba dole kiji jikina yay zafiba, zo zauna kiyi break kitafi school” kujeran kusada Mama tazauna ahankali tana kallon fuskanta dan bata yardaba, Mama ta tashi tareda daukan plate tace “kici masa sabida yarikeki” tai maganan tana zubamata sanan ta tura gabanta tace “Oya Oya eat” fara ci tayi tana kallon fuskan Mama data daure iya daurewa, ahankali ta hadiye masan bakinta tace “Mama nakawo miki paracetamol kisha kinga kar zazzabin ya kwantar dake” dan shiru Mama tayi tana kallonta ganin dukta damu yasa ahankali tace “to naji zansha amman dakaina zan dauka Nasha ke yanzu kici abinci kitafi school yi maza ina kallonki” murmushi tayi sosai har ranta tace “yauwa Mama, world best Mama, har hankalina yatashi, wlh Mama ko tari banso naji kinayi balle ciwo sai inji komi bayamin dadi” dan dariya Mama tayi tanaji kaman zatai kuka amman ta daure tace “Malama eat bance kitasani agaba da surutu ba, Ummulkhairy aku” dariya tayi bata kara cewa komibaharta cinye kafinma tai motsi Mama tamikamata ruwa a cup, kallon fuskan Mama tayi sanan tai wani kalan murmushin dadi tace “Mama ya akayi ki kasan ruwa zan dauka” bata kofin Mama tayi tace “sabida ni Maman kine, angayamiki just like that naci wanan sunan world best nabakin ki” wani kalan washe hakori Khairi tayi sanan ta shanye rawan ta tashi tazo kujeran Mama rungumeta tayi tabaya tace “Mama natafi, I love you kinji, Mama karki je ko’ina please, koma zaki fita ki jirani nadawo saina rakaki mutafi tare” murmushi Mama tayi tadaga hannunta tashafa kanta tace “naji, a dawo lpy, banda rashinji, banda kula maza Umma, banda rashin kunya” sakin Mama tayi batare data amsaba tafice daga falon da sauri ganin 8:30, Mama na zaune inda take tana kallonta ta window harta shiga mota mai gadi yabude gate driver yafice da ita. Ajiyan zuciya tasauke ita kadai tasan metakeji ajikinta, jin tafiyan Baba datun bayan yay breakfast yatafi sama shiryawa dan yau ba aiki zashiba asibiti zaikaita yasa tadaga idanunta takalleshi, hada idanu sukayi dawani kalan sauri ya shiga saukowa daga stairs din yace “wife, ur……Han…..hancinki” yay maganan yana karasowa gabanta ganin jini na gangarowa daga hancinta, dasauri tace “hanci na” takai hannunta ta taba jin abu na gangarowa kafin tadawo da hannun gabanta ganin jini yasa tace “laaa banma saniba” cikeda karfin hali tamike tsaye wani irin mahaukacin jiri yadibeta tai baya dawani irin sauri Baba yatarota tafado jikinshi a sume, daidai lokacin Manaf da Mu’az na shigowa falon cikin shirin zuwa office, ganin Mahaifiyarsu yasa dasauri sukai wajen kafin ma suyi magana Bana yace “Manaf daukomin mayafinta afalo mutafi asibiti, Mu’az get the car” dasauri Mu’az haryana bigewa da centre table yafice waje shikuma Manaf yay sama, har gaban flat din Mu’az yakawo motan sanan yadawo ciki atare dukansu suka dauki Mama sukai mota da ita bata Baba yashiga da ita, Mu’az da Manaf suka shiga gaba sanan suka fita gida. Wani Babban private hospital sukaje, suna shiga aka karbe Mama sanan akasasu tsayawa awaje, zama Baba yayi da kusan yamafi yaran nashi damuwa, ahankali su Manaf suka zazzauna kusada shi babu iyacema wani kala idanunsu sunyi jajir, suna zaune awajen na kusan 2hrs sanan saiga Dr wanda yake abokin Baba yafito, Baba dagashi harsu Manaf na ganinshi duk suka tashi, kallonsu Dr yayi sanan yace “Alhaji follow me” binshi Baba yayi yay tafiya kusan biyu sanan yajuyo yakalli su Manaf dasukai zuru zuru yace “let’s go” dasauri suka biyoshi abaya har zuwa office na Dr, zama Dr yayi sanan yanunama Baba sit ya zauna sukuma su Manaf duk suka taaitsaya kowa kallon Dr yake with hope koma yayane abasu goodnews, lumshe ido yayi ahankali sanan yabude yace “Alhaji ayanda kuke kallona dagaku har yaranka I wish zan iya gayamuku abinda nasan har cikin ranku shi kukeso kuji, I am sorry I don’t have that sai akasin haka, condition din matarka has become worse da ayanzu riketa a asibiti yama kamata muyi muna bata yan taimakon dazamu i……” kasa jiranshi Baba yayi yakarasa sabida yasan menene zai fadi, cikin wata kalan tsinkakkiyar murya dake cikeda sanyi jiki dakuma lack of hope yace “how long does my wife have?” Kallonshi Dr yayi dan baiji Baba nason yaji Wanan amsan tambayan ba amman ganin kalan kallon dayakemai na ya shirya ji yasa ahankali yace “less than a month” hawaye Manaf yaji yazomai dasauri yajuya yafita daga office din, bayanshi Mu’az yabi da sauri yana goge hawayen dayazubomai, shiru Baba yayi kafin ahankali cikin wata kalan karyayyiyar murya yace “kasan dai kai ba Allah bane ba ko likita dazaka gayamin matata nada less than a month to leave” shi kanshi Dr ya bala’in tausayama Baba cus idanunshi sunyi jajir, cikeda lallashi yace “Alhaji listen to me, niba Allah bane, Allah shine masanin gaibu, kawai ina maka discribing lokutan datake dashine base on science, cells dinta sun soma shutting down daya bayan daya, I am just preparing you ne for the worst, you have to be strong ma yaranka, sabida ayanzu they’re looking up to you, ka dake sanan ka koyamusu sudake, kanunama matarka so da kauna sama da da, karku dinga kuka agabanta koku dinga nunamata damuwa, hakan zai saukaka mata abubuwa da dama, ganinku cikin damuwa da rashin walwala shi zai karamata damuwa da zafin ciwo, dan haka Alhaji I am giving you Wanan chance din cry as much as u want now, after yanzu baka kara kuka ko nuna rashin kwazo sabida yaranka” kaman jira Baba yake ahankali hawaye suka shiga kwararowa daga idanunshi, tissue Dr yadauka yabashi karba yayi dasauri yakai kan idanunshi yana sharewa cikin wata kalan murya dake sosarai yace “I don’t want Maryam to leave me, naso mu tsufa tare sanan mu mutu tare, why are you doing this to me now Eh Maryama diyar albarka” saukan da kanshi las Dr yayi yana sauraron Baba yakai kusan minti 15 ahaka sanan ya share fuskanshi tass da tissue Dr yanunamai bathroom yashiga ya wanko fuskanshi yafito yama Dr sallama yafice zuwa dakin Mama ganin su Manaf tareda ita tana bacci ana mata Karin wani abu kaman yellow madara yasa yafito, zama yayi a kujeran gaban dakin sanan yaciro wayanshi number dayay saving da Amini yay dialing, ringing daya aka daga cikeda barkwanci irin na manya yace “badai kahanamin yarinya zuwa makaranta ba” dan murmushi kadan yayi sanan yace “jikin Maryam yatashi muna asibiti Baffa” anatse daga dayan bangaren akace “Subhanallahi, turn d car Bala muje asibiti” kawai aka katse wayan. Yana zaune awajen ko cikakken 10min ba’a dauka ba, wani Babban mutum da akalla shida Baba zasuyi sa’onni ya shigo cikin asibitin yana gyara Babban riganshi, farine mutumin sol yanada kiba dan yamafi Baba, shida wani dan saurayi dabazai wuce sa’an su Manaf ba dayay kama dashi dukansu fuskokinsu yanuna damuwa sosai, yana karasowa dafa kafadan Baba yayi yace “be strong my friend, Allah yabama Maryama lafiya, Allah yatashi kafadunta, Allah yasa kaffarane” tashi Baba yayi yanadan murmushi sanan yakalli yaron dake gaidashi yace “su Baban Baby girl Hafiz, Allah ya raya” ahankali yace “Ameen Baffa” sanan suka shiga ciki, har lokacin bacci take, da idanu Baffa yama Baba alamu su fito, suna fitowa yace “bazamu fitada ita wajeba ko har yanzu tanakan bakanta”. I will talk to her idan ta farka, ahankali Baba yace “Allah yasa ta yarda” kara komawa sukayi wajen Dr ko akwai wani solution amman babu, dudda haka Baffa saida yakira some of the best Doctors dayasani a Abuja but is still same thing hakanan suka hakura. Wajajen 3:00 na rana tafarka, dakin tabi da kallo kafin ahankali tafara yunkurin tashi dasauri Manaf da Mu’az suka dagota, ahankali Mu’az yace “kinajin yunwa Mama mezakici” dakin asibitin tabi da kallo kafin ahankali tasauke ijiyan zuciya tadanyi murmushi ganin duk sun damu tace “ya akayi bakuje aiki ba yau, laaaa is that Hafiz” tai maganan tana kallon Hafiz dake zaune kan kujeran gaban gadon yana kallonta cikeda tausayi, cikeda murna tace “zonan zoka nunamin hoton jikata nagani” dan murmushi yayi yataso yazo, wayanshi yaciro yafito da picture cute baby girl dinshi yabata karba tayi tace “Masha Allah tubarkallah, Allah ya rayamana kaga yarinya kaman Babanta Yan biyu” tai maganan tana nunamusu hoton kafin idanunta ya sauka kan time din wayan ganin karfe uku har da minti goma yasa dasauri tamikamai wayan takalli Mu’az tace “kiramin Dr yasallameni inkoma gida, Khairi takusan dawowa daga school” tana maganan saiga Baba da Baffa da Dr sun shigo tare, Baffa na ganinta yace “ya jiki Maryam” murmushi tayi tace “Alhamdulillah Baffa, ya ji kalle inasu Hajiya Asiya” kafinma taji amsanshi tace “Dr zokai discharging dina natafi gida” ahankali Dr yakaraso wajen yace “Hajiya kibari mu dubaki na kwanaki tukunna saimu sallameki” kallon Baba tayi sanan takalli Dr rai Adan bace tace “sallameni yarana banaso su dawo Bana gida Dan Allah” kallon Baba tayi sanan ahankali tace “daman Wanan ne shirinka idan ka kawomi asibitin arikeni” dasauri Baffa yazo wajen anatse yace “Maryam kalleni nan” ahankali tajanye idanunta dagakan Baba dake kallonta kuri takalli Baffa, anatse Baffa yace “Maryam kiyakuri ki zauna likitocin nan su cigaba da baki gudunmawa, zamanki agida zai karasa ciwon yazama worst ne, dan Allah maryam inhar kinajin magana ta” lumshe idanunta tayi sanan tabudesu ahankali tace “Baffa tun ina yarinya kasanni ban taba cemaka no ba, kome kacemin inayi dan haka yau Baffa dukanku anan zan rokeku alfarma, dagayau dan girman Allah kome zai sameni karku sake dawodani asibiti, Baffa nasan kalan chutan danake dashi, nasan metake nufi, da inzauna anan allurai da maganinsu yakarasa cinyeni gwara in koma dakina, I want to die adakina tareda yarana dakowa, I hate hospital and zaman asibiti shizaifi kasheni dawuri sama da komi, please Baffa dan Allah, idan baka yarda ba naji zan zauna, amman rokonka nake please Baffa” kowa na dakin saida jikinshi yay sanyi har Baffa, ahankali Manaf yakalli Baffa yace “Baffa please grant Mama wish, let’s just take her back home ko Hafiz” gyadamai kai Hafiz yayi da idanunshi sukai jajir, hakama Mu’az, ganin Baffa da Baba sunyi shiru dan su sunfiso tazauna a asibiti tasami lafiya yasa ahankali Dr yace “Alhaji kubarta takoma gida, idan anything come up ku kirani ni zandinga zuwa nadauki Wanan nauyin” ahankali Baffa yakalli Baba dakokadan baisoba, kallon kayakuri takoma gidan, hakan yasa ahankali Baba yace “shikenan” murmushi Mama tayi sosai nan da nan aka zaremata drop din sanan Dr yarubuta mata magunguna suka saya sanan suka dawo gida gabIaki dayansu. 💫 ALKAWARIN ZUCIYA 💫 ✍🏻M SHAKUR 1️⃣4️⃣ Free page Wuraren 8:50Am sukakai school. Adamu na parking wajen parking tafito da saurinta bama ta tsaya mai sai anjima ba tashiga sauri cus 9 dot mutumin nan ke shiga aji gashi baya wasa da attendance, tana cikin tafiya zuwa class saiga wasu yammata su hudu sun taho tunda suka ganta sukahau ihun murnan ganinta Khairy nada wani irin farin jini naban mamaki wajen mata, tareta sukayi. “Khairy how far”? Murmushi tayi dake karamata bala’in kyau tace “lpy lau wlh, yanaga zaku waje daban ba class garemu ba yanzu” yatsine fuska sukayi, daya daga cikinsu tace “wlh dabaki wani wahalar da kanki ba wajen class din Mr Okeme ba ba’a taba ganewa ba, ke saurayinki Ahmad celebrity yazo nemanki fa” hararanta Khairy tayi tace “Malama niba saurayina bane kidena hadani dashi, na wuce class nidai” tai gaba abinta ranta abace, daya daga cikinsu ne ta daga murya tace “idan yakadoki meet us a garden chan mukayi” daga murya itama tayi tace “that’s not gonna happen Ladies” tana tafiya wasu another set na yammata na tareta bamata tsaya sauraransu ba tace “I will see u later ladies inada class now” tahau tafiya gudu gudu sauri sauri, duk inda tabi ana kwalamata kira Khairy Khairy waving mutane kawai take tawuce benen dazai kaita ajinsu tana kaiwa yana shiga tana tsaye yana kallonta yaja kofanshi yarufe, ahankali ta yatsine fuska murya chan ciki tace “this wicked man cannot make heaven” sanan tajuya tana kallon kasa daganan bene yanda student kowa na takanshi sanan ta fuzar da iska ita dai ko itace allazi boko bazata taba tsayuwa jikin window har agama 2hrs class ba, tashi tayi abinta tafara tafiya tawuce tana sauka daga staircase abinta tanadan turo baki ita kadai tana kunkunai. Sabida yanda ranta yake abace taji bamatason tabi normal hanya friends nata suyita tareta da magana hakan yasa tabi ta parking space dan taje garden daga wajen, ahankali take tafiya ita kadai a parking space din tana cikin tafiya a parking space din taji an kwala mata kira. “Khairy” dan tsayawa tayi jim batare data juyoba jin muryan namiji ne ke kiranta, tunani tafara acikin kanta muryan waye wanan sai chan taja wani kalan annoying tsaki tacigaba da tafiya abinta gani kawai tayi ansha gabanta wasu maza guda biyu sunshamata gaba suna sanye da kananun kaya sun bubbude hannuwa irin suna tareta dinan, wani kalan daure fuska tayi babu ko alamun wasa akai tace “me haka” dan dariya sukayi daya daga cikinsu yace “listen to Ahmed mana Khairy yasan bazaki tsayaba saisa yace mutareki” yay maganan suna nuna mata bayanta, juyawa tayi cikeda masifa wani black skin guy ne da dududu bazai wuce mate nata ba in age maybe 20 ko 22yrs haka yake, yana sanye cikin rugget kayan yan iska dinan, crazy baggy jeans da wata babbar baggy riga yayi dying gemunshi zuwa blond color kana ganinshi kaga irin yan iskan yaran nan gashinan very popular aciki school nasu, wani kalan mugun kallo tamai da manya manyan idanunta tace “kai da boys dinka Ahmad should get out of my way” wani kalan murmushi yamata tareda daura hannunshi akan kirjinshi yana shafawa yace “auuch! I love it when you look at me like that Khairy with those ur big big lulu white eyes, Baby my heart only beat for you” spitting miyau tayi agefenta sanan tajuyo takalleshi tace “you disgust me Ahmad, nagayamaka time without numbers stop wasting ur time on me, you are not my type of guy, idan maza irinkane suka cika duniyan nan I rather die banyi aure ba dana aureka, I don’t like you an taba soyayya dole ne” dan takowa sahu daya yayi zuwa gabanta, tsayawa chak tayi tareda kama waist dinta kirjinta na bugawa fat fat, wani mayen kallo yabita dashi barima kirjinta dayaga yacikamai idanu tunba yauba tunda ya lurada yanda Khairy keda boobs yaji yakara haukacewa akanta, dan hucin zafi Ahmad yayi yana kallonta still sanan yanuna kanshi yana bude kafafunshi da tsabagen effizy sun koma kaman boleg yace “look at me kinsan how many babes anan School namu ke kiyamun laili because of me eh? Look at me Khairy, I have money, I was born in wealth, banda haka I am a hip hop rapper number 1 a arewa, yaro mai zamani, har rap nayi da sunanki natura miki a watsapp u don’t even open my chat balle kiji how much I love you, Khairy tell me mezan miki dazaki soni eh, kinga we are the only ones here, just tell me babu kowa don’t be shy Khairy, baki sona don’t u wish to be mine, don’t u wanna make matan makarantan nan jealous ace Kece tawa, I want you to be my Choima while I become your Davido, lemme make you famous, lemme make u a star gurl, what will I do to make you mine baby na? Don’t u want all of this” all maganganun dayake mata jitake kaman tai amai bala’in kyaman Ahmad take bawai he’s dirty bane, kawai dai yanayinshi yanda yake dressing yana shiga kaman wani su wizkid yayi coloring gemunshi da halinshi na waka ita kawai he’s not her spec, yana mata magana yana wani wawware fingers kaman yana rapping yana kama tsakiyan baggy wandonshi, ko kiranshi amatsayin boyfriend nata ma bataso ta tsani taji anyi, bakin ciki da haushin shi yamasa tama kasamai reply kawai tajuya ta gefenshi zata wuce dan sometimes idan abu is really annoying agareki rasama abinda zakace kake, kawai ji tayi yariko hannunta “don’t go baby wait” wani irin juyowa tayi batai wata wata ba kawai ta daukeshi da mari jikake tass! Wani irin ihu abokanenshi sukayi suna waige waige ko there’s anyone there dayaga Marin datama Ahmad dan zai zama abin kunya ance wata tamari hiphop rapper. “Ke celebrity kika mara” fizge hannunta tayi tana kallon yanda yadaura hannunshi kan kuncinshi yana wani irin kallonta da idanunshi dasukai jajir dan marin ya shigeshi, rawa jikinta yafara da sauri tajuya Ahmad daya bala’in zuciya yace “ku bita” jin haka yasa ta kwasa da bala’in gudu acikin parking space din dababu kowa tana kalle kalle, kaman ance takalli right side dinta, hango wani dogon mutum tayi yabata baya Awani lane na motoci yana tsaye jikin wata suv waya a kunenshi da alamu waya yake, wani irin kwana tayi tana gudu tai lane din dayake batai wata wataba tana kaiwa daidai inda yake batai wata wataba tawani zaga ta gabanshi ta shige kirjinshi at once tana boye fuskanta akirjinshi jikinta ko’ina narawa sosai sabida tsoro yanda maza har biyu komatace uku suka biyota, cikin Yar siririyan muryanta that is trembling sosai tace “please save me…..plss…….I’m sca…….” tana maganan tana nishi da sauri da sauri dayake jinshi harcikin fatan kirjinshi don fuskanta gabaki daya na wajen ne, daidai lokacin daga boys din Ahmad din har Ahmad din dukansu sunzo wajen sun tsaya agabansu suna maida ijiyan zuciya sabida gudun dasukayi, One by one mutumin ke binsu da kallo batare daya furta ko a word ba har lokacin wayan nakan kunneshi bai cireba, faduwa gaban Ahmad yayi ganin fuskan mutumin dake kallonsu, ahankali yajuya sadaf sadaf daso samune ko takalmin shi da kasan wajen karma suyi motsin nuna alamun yana moving sanan ya yafito abokananshi da hannu yace “let’s go guys” dasauri sukace “marinka fa tayi Boss” da saurinshi kaman ana hankadashi yawuce yace “shikenan nidai natafi ku ku tsaya” ganin yanda yake tafiya da saurin bala’i tun bayan yaga fuskan mutumin yasa suma sukasha jinin jikinsu suka juyada sauri suka wuce. “Eh Gwaggo ina jinki sorry ba shareki nayiba, Abban nake jira nariga nakawo shi…” ahankali tashiga dagoda kanta kaman wata mara gaskiya cikeda kunya jin mutum na wayanshi ta tsokano fada tazo tafada jikin shi, kanta akasa ahankali sadaf sadaf tashiga fitowa tana matsawa baya kafin gently kanta nakasa batare data kalleshi ba tace “thank you” sanan ahankali tajuya tashiga tafiya har lokacin gabanta nafaduwa sosai. “You!” Taji kaman daga sama mutumin yakirata chak ta tsaya batare data juyoba, “turn around” taji muryanshi anatse yet with authority batasan mesaba amman kasa ketare abinda yace tayi tayi hakan yasa gently tajuyo sanan ahankali tadaga fuskanta takalleshi, wani dogon saurayi ne fari sol dashi kaman balarabe yana sanye da jumper na farar shadda bugaggiya kanshi babu hula gashinshi akwance baki sidik sai kyalli yake hannunshi rikeda iPhone 13 yazubamata idanu dababu alamun wasa daidai da digi acikinsu, hakanan jitayi takasa jure kallon mutumin dataga kaman ta sanshi amman ta manta a ina ta sanshi ta sauke kanta kasa, anatse yace “the next time I will see you making trouble I will arrest you!” dasauri tadago kanta ta kalleshi saida yafidi kalman arrest sanan police din ranan yafado mata arai, dauke kai yayi daga kallonta sanan yabude kofar motan daya tsaya jikinta ya shiga ciki tareda rufe marfin motan da sauri dayadan firgitata sanan ahankali tajuya tacigaba da tafiya ahankali. Samin kanshi yayi da binta da kallo ta madubin motan, yanda take tafiya ahankali har lokacin bata dawo daidai ba, sanan ahankali yadauke kanshi daga kallonta jin wayanshi na ringing again screen din yakalla ganin Grandma yasa yabude motan yafito yace “this woman will not allow me leave in peace”. Garden din takarasa tun daga nesa kawayenta dasuka hangota suka kwalamata kira hakan yasa takarasa zuwa inda suke zama tayi sanan tadauki bottle na ruwan dake gaban Farida tabude takai bakinta ta kwalkwale duk kallo suka bita dashi, saida ta shanye goran ruwan tass sanan ta ijiye tana sauke ijiyan zuciya, Farida tace “daga ina kike haka duk kinyi zufa kaman kin fito daga yaki” dan yatsine fuska tayi kaman bazatai magana ba ganin yanda suke kallonta yasa tace “Ahmad na mara shine yabiyoni and someone…..” tadanyi shiru kafin ahankali tace “wani mutumi yataimakeni” atare dukansu all the 5 friends sukace “wani mutumi” shiru tayi sai chan tace “oho nima ban sanshi ba” dukansu dariya sukahau yi dasauri takallesu tace “me” hada baki sukayi sukace bakomi, sharesu tayi kawai cus she doesn’t even feel okay batasan mesa ba, duk suna zaune wata kawarsu tashigo eatery dagudunta tana haki tace “kufito kugani yan sanda sun shigo school dinan anzo ana kwashe su Ahmad da Gang dinsu” dasauri Farida tace “ke haba let’s go video it musashi a internet” dukansu tashi sukayi itama ta tashi tabisu suka fice daga cikin garden din, van suka gani na police gaban wani eatry dake kusada garden din dasuke ciki, dasauri suka karasa gaban eatry din student sun cika wajen suna kallon Van din police, suna tsaye wajen dayay cha da mutane sukaga an fito da Ahmad da akasamai handcuff a hannu an sashi a van din sai abokanen shi na dazsu dasuka biyota guda biyu saikuma wasu guda biyu daban yan sandan sun fito dasu ana sakasu a van din saiga police man dinan shima yafito daga eatry har lokacin yana sanye da kayan dazu farin shadda waya a kunenshi still, hada idanu sukayi batasan mesaba jitayi gabanta yafadi dasauri ta sauke kanta kasa tareda juyawa ahankali tamabar wajen bata kara juyowa ba kawai tai hanyar class nasu, daidai lokacin ana shirin fara wani lecture kujera tasamu atsakiyan ajin ta zauna sanan tabude jakanta taciro note nata da pen aka fara lecture ko kadan takasa concentrating batasan mesa ba she just keep seeing police man face din da what happen today, gabaki daya all through da day har yamma ita kanta tasan yau ba school tazo ba takasa natsuwa tunanin shi da komi yacika mata kai, wuraren 5 na Yamma Adamu direba yazo daukan ta shiga motan tayi ahankali tace “Adamu please kafara kaini Coldstone nasayi ice cream nasha saimu wuce gida” cikeda girmamawa yace “to Miss Khairy” daura kanta tayi akan kujeran tajuyar da kanta tana kallon hanya tareda fuzar da ijiyan zuciya, she just hope tanashan ice cream dinan sanyin shi zaisa brain nata yay sanyi tadena all tunane tunanin datakeyi tun safe. Agaban wani Babban joint na coldstone Adamu yay parking hakan yasa tabude motan tafito ta shiga ciki, daidai wani Babban Jeep na shigowa wajen parking yayi kusa da Benz da Adamu ke ciki, bude gaban motan yayi yafito ahankali wanan karan yana sanye da kayan yan sanda Rolex din dake daure a hannunshi yakalla shidda saura, sanan yazaga zuwa boot din jeep din yabude keken guragu yaciro ya ijiye ya maida boot din yarufe sanan yadawo bangaren baya yabude motan wata kyakkyawan tsohuwa ce fara sol kaman balarabiya zaune abayan tasaka Riga da zani irin na tsofaffi anmai dinkin Bubu kafafunta da hannayenta sunsha lalli, hannunshi yamikamata batare dayace mata uppan ba hararanshi tayi tana kama hannun nashi tamike tsaye da kyar tana masifa tace “idan kaga dama kai gaba dani dagayau har jibi Ice cream dai saika kaini nasaiwa jikoki na ja’irin yaro kawai” ko kala baice mata ba da taimakonshi ya daurata akan keken sanan yamaida kofan bayan yarufe da karfi tace “kama balla motan baban karfi, ubanka zai sayamin wata Alhamdulilah Allah yamai arziki rufin asiri danasha takaici” cikeda masifa yace “wlh Goggo in baki shiru ba anan zan barki na shiga ciki nasayo” wani kalan murmushi tayi tamaka bakinta tace “yo ai nadauka gaba kake dani to muje nadena” dan murmushi kadan kawai yayi sanan yashiga turata zuwa gaban entrace din dakenan divided into 3, staircase ne gefe da gefe sai tsakiya a bit sloppy floor dazaka haura ka shiga cikin shagon, daidai lokacin security na budewa Khairy kofa tana fitowa rikeda paper bag na ice cream din dakuma handbag dinta rataye a shoulder dinta, saiga wasu yara su biyu maza dabazasu wuce 8yrs ba suna guje guje kowanne rikeda ice cream dinshi dayan kawai ya mamayi brother shi ya fizge ice cream din hakan yasa brother yay ihu yabi dan uwanshi da gudu Khairy dabude mata kofa kenan tasa kafa tafito zata fara sauka daga staircase din kawai yaran suka fito suka mugun bangajeta dayasa ita kanta tasaki wani irin ihu kafanta ya gicce abunku da tiles kawai ta kifo zata fadi da mugun sauri Gwaggo tace “Subhanallahi” dawani irin sauri yasaki wheelchair Gwaggo daidai kanta zai daki dakaIUlin stairs din… 2️⃣1️⃣ Free page Saida tai sallan isha’i sanan tacire hijabi kayan bacci taciro tasaka tana tunanin abinda yafaru dazu itada Aliyu, dan murmushi tayi sanan ta kashe wutan dakin ta kwanta. Batasan mesaba tadade kwance rikeda wayanta tana kallon wayan every minute deep down she wish to hear his voice amman kuma bamataso tana tunanin what she wish for din akanshi abin is so so new for her she’s not just use to it, ahaka bacci yay awon gaba da ita wayan nakan kirjinta this is the first ever time in her life da waya ke bacci akan kirjinta. Wuraren 12 nadare wayan nata yahau ringing afirgice tafarka tana daukan wayan daga kan kirjinta tana danna gefe dan yadena ringing yay silent, sanan takalli screen din da kyau ganin Aliyu Hydar batasan mesaba faduwa gabanta yayi, ahankali takai yatsanta dake dan rawa ta danna wayan na gab da katsewa takai kunnenta, murya chan kasa dake nuna alamun bacci tace “Hello” shiru yayi yana sauraron muryanta da bazaiyi karyaba tunda yake baitabajin macen da muryanta yamai dadi kaman nata ba, dan gyaran murya kadan yayi cikin wata kalan murya dashi kanshi baisan yanada itaba yace “Khairy” ahankali kaman wata Yar karaman baby tace “Uhm yajiki? Kasha magani?” dan murmushi yayi jikinshi namai wani iri jin muryanta like that so naked sabida baccin data fara, sanan har ranshi yaji dadin yanda ta tambayeshi yajiki koyasha magani, ahankali yace “yeah, Abba yamin allura” kaman zatai kuka dan ita harga Allah tanada tausayin mara lafiya tace “auuch that must have hurts, I hate niddles, sorry ko!” murmushi yayi ya gyadamata kai yace “thanks, you are sleepy”? Gyadamai kai tayi tace “Uhm” ahankali yace “alright good night, make sure you plug in your phone sabida yasami chaji, and say your prayer before sleeping okay” gyadamai kai tayi ahankali tanajin wani iri azuciyanta kaman tacemai sucigaba da magana karya tafi tadenajin baccin tace “okay night” tai maganan batare data cire wayan daga kunnenta ba shima bai katse wayanba sunkai kusan 10min ahaka sanan murya chan kasan kasan makoshi yace “I love you Ummulkhair okay” gyadamai kai tayi ahankali tanaji hawaye nazuwan mata dabama tasan na meyeba but ko Allah yasani she just feel damn connected to him and vulnerable around him kaman ba itaba, katse wayan yayi hakan yasa taciro wayan daga kunnenta tarungume wayan hawayen na gangaro mata daga idanu, karan message dataji yasa taciro wayan daga kirjinta dasauri tabude wayan ganin message from Aliyu Hydar, bude messege din tayi da sauri. “Maisa nake sonki Ummulkhair? Well who am I to question faith? All I feel right now is I wanna spend my eternity with you, gud night Khairy” Takaranta message din kusan sau biyar sanan ta danna reply tai shiru tana kallon blank space din bamatasan mezata rubuta maiba, saikuma chan tashiga typing . “I feel vulnerable and free around you, my heart beat whenever I hear your voice, duk sanda na rufe idanuna kai kadai nake gani, is that love?“ Yana ganin message din yay mata reply. “time will tell Khairy na❤️” Wani kalan murmushi tayi ganin yakirata da Khairy na sanan ta tashi zaune USB takamo dake jone da wall socket ta saka wayan nata kaman yanda yace tayi sanan takoma ta kwanta tadade kafin bacci yay awon gaba da ita. Da asuba Baba yashigo yatadata saida yaga tashinta dan Khairy nada nauyin bacci sanan yawuce yatafi, bayi tashiga tadauro alawala tazo tai salla, koda tagama karatun Al Qur’ani tayi yau sosai wuraren 6 ta tashi, hijabi tacire yau ita keson yimusu breakfast tunda bazata school ba hakan yasa ta tashi tafice daga dakin tasauka kasa kitchen tashiga tana murmushi tace “idan matarchan tazo yau zataga na hutashe ta” lafiyayyen breakfsat tahada musu dan sinasir tayi da farfesu sai kunun Gyada dasu fried chips, saida tagama tsaf sanan tashiga fito da komi falo ganin Mama zaune afalo kusada Baba yauma sanye da kayan sanyi yasa ta ijiye kulan a tsakiyan falo ta tashi tana kallon Mama dataga tamata haske sosai Mama datake nan baka but tai wani irin haske, kafinma Mama tai magana Baba yace “ke wuce ki kawo mana abinci ga yayyinki nan zuwa” dasauri tajuya tana murmushi tace “Baba naga Mama tai haske ne takara kyau” kitchen tashiga takarasa fito dakomi takawo lokacin su Manaf sun shigo suma zama duk sukayi Baba da kanshi yadebo ma Mama Sinasir yana bata abaki, murmushi tayi tana kallonsu tana taba Ya Manaf, hararanta yayi yace “dalla kauyus” cigaba dacin abinci duk sukayi kowa yay shiru Baba da Mama ne suka fara gamawa sanan yakalli Khairy yace “Maman ki tace zaki saloon ko” gyadama Baba kai tayi tace “eh Baba, gyadamata kai shima yayi yace “yau rabonki da gidan Baffan ki kwana nawa” dan ajiyan zuciya tayi ganin yanda Baba ke kallonta sanan ahankali tace “an dade Baba” jinjina kai yayi yace “kije ki shirya kitafi saloon yanzu ana gamawa kije gidan Baffan ki ki gaidasu sanan kije gaida Matar Hafiz” ahankali tace “to Baba” “tashi kije” tashi tayi tai sama Baba yacigaba dayima Mama hira yau yanaso yakaita asibiti kotaki kotaso dan kwata kwata this days bata iya baccin dare ga kurajen nan kara fesowa suke ajikinta bana wasaba. Tana shiga dakinta zama tayi kan gado sanan tadauki wayanta dahar lokacin bata cire daga chaji ba tabude message din Aliyu tagani around 5 na asuba. “it’s time for subhi, wake up”. Murmushi tayi sosai sanan ta ijiye wayan tawuce bayi wanka tayo tafito direct gaban wardrope dinta taje wani riga da skirt na wani paper lace dinta tafito dashi da akamata dinkin jumper rigan yakai mata har gwuiwa sai skirt shikuma straight skirt daidai jikinta, mustard color ne lace din sai aka ni kayan dawasu bakaken stone, murmushi tayi taje tadaurasu kan gado sanan tazauna gaban mirror tadauki manta tana shafawa tana kallon fuskanta amadubi tana tunanin Aliyu, saida tagama shafawa sanan ta saka kayan dasuka mata bala’in kyau sosai, murmushi tayi black veil tadauka ta feffesa turare sanan tadauki handbag dinta ta jefe wayanta aciki tasa flat slippers yau tafito, afalo taga Baba kan doguwan kujera yana duba jarida Mama kwance tayi filo da kafanshi tana bacci yarufamata bargo, ganin Khairy yasa yadaura hannunshi akan lips dinshi yace “karki tadamin da matata tana bacci” turo baki Khairy tayi ashagwabe tace “Baba yanzu kafisun Mama dani Yar Autan ka” dan dariya tayi yamika mata wasu kudade yace “gashi Adamu na jiranki kije saloon kina gamawa ki wuce gidan Baffa” gyadamai kai tayi ta karbi kudin sanan takalli fuskan Mama dake bacci tace “Baba natafi” adawo lpy. Saloon suka wuce direct baa wani bata lokaci ba wanke mata kan akayi sanan aka mata kalaba yan manya manya within one hour tagama tafito tashiga mota Adamu yatada motan zuwa gidan Baffa, dan tsaki tayi ahankali kawai dan babu yanda zatayi ne dabataje ba bata wani don zuwa gidan Baffa dudda tana bala’in don Baffa da duka yaran gidan, da Mum amman Ammi kwata kwata jininsu bai hadu ba batasan mesaba, tana cikin yan tunane tunanen ta ta iso gidan, Babban gida ne katoto, gidansu Babba ne but Gidan Baffan su is X2 nasu, mai gadi na ganinsu yahau murmushi yace “oyoyooo Khairy” murmushi itama tayi Adamu na parking tabude tafito dasauri mai gadon yazo wanda yake bayaro ba yace “munyi fushi wlh” dariya tayi tace “Baba Bala wlh school yaboyeni” tai maganan tana ciro kudi a jaka tamikamai 5k cikin kudin da Baba yabata karba yayi yace “nagode Yar albarka, Khairy mutuniyan kirki” murmushi tayi tajuya tana kallon cikin gidan, dankara dankaran flat ne guda uku agidan haka ajere, na farko wanda shizaka fara isa kafin kaje sauran yafi sauran biyun girma saina biyun dana ukun girmansu daya, da sauri saurin ta gudu gudu take tafiya wuce flat na farkon tayi tayi na biyun bude kofa tayi tana ihu. “Mummmmmm Mum” bin falon tayi da kallo daya hadu sai kamshin turaren wuta yakeyi stairs tayi da gudu tai sama daidai wata mata dazata kai 45 kefitowa daga wani daki cikin shiga na alfarma ta harari Khairy tace “ai nayi fushi wlh Khairy” wani murmushi Khairy tayi batayi wata wata ba taje dagudu tafada jikin Mum tana juyida ita cikeda murna tace “Mum I am sorry kinji, wlh school yahanani zuwa, Mum kinyi kyau iyyeee, ina Batool” turata Mum tayi tana nishi tana dafa kujera dan jiri taji tanaji tace “jama’a na shiga uku yarinyar nan zata kassarani” dariya Khairy tayi tajuya tai hanyar wani daki tace “nasan yarinyar nan tana bacci to baki isaba nazo” binta da kallo Mom tayi ganin kullum kara girma Khairy keyi, tana bude dakin taga wata yarinya da atleast zasu iya zuwa mate kokuma yarinyar tabama Khairy 1 zuwa 2yrs haka ta tashi zaune sanye da kayan bacci tana hamma tana hararan Khairy, yarinyar kamansu daya da Mom, wani tsalle Khairy tayi tafada kanta akan gadon yarinyar ta kwasa ihu tace “Mum kinga Khairy ko ni dagani ai wlh fushi nake dake konai chatting naki up baki dubawa kuma baki daukan calls” sakinta Khairy tayi tace “wlh Batool ni taba waya ma wahala yakemin balle responding to calls or chat har gwarama kamin text message ina gani zan reply, but rabona ma dana shiga watsapp harna manta wlh” baki Batool tabude zatai magana Mom ta turo kofan dakin tashigo hakan yasa duk suka kalleta, Khairy takalla tace “kinje kin gaida Ammi Khairy”? Dan zaro idanu Khairy tayi sanan ta girgiza mata kai ahankali, daure fuska Mum tayi babu alamu kan fuskanta tace “Oya tashi kije ki gaidata, fast” tashi tayi kaman ruwan jikinta ya shanye, jakanta ta ijiye kan gadon Batool sanan tawuce tafito Mum tace “duk idan kin shigo gidan nan always ki shiga flat nata ki gaidata kafin kizo nan” gyadamata kai Khairy tayi sanan tawuce ta sauka kasa kafin tabude kofa tafice. Ajiyan zuciya tasauke tana kallon kofan sanan gently tasa hannu tabude kofan wani lafiyayyen kamshin turare namata sallama ahanci, Babban falo ne sosai dayamafi na Mom girma, zaka dauka dakin wani president ne ko gwamna sunji kujeru da kayan gayu, wata Babbar mace ce mai kiba sosai a falon, kana ganinta you don’t even need to ask twice kaga Hajiya irin cash HajiyUoyin nan. 2️⃣2️⃣ Free page Fara ce tass kana ganinta kaga bafulatana dan tanada mark na fulani a gefen fuskanta taci gayu na alfarma tana sanye dawani stone gown na exclusive mai pattern, kunenta zinare wuyanta ma haka yatsun hannunwanta guda biyu ne kawai babu zoben zinare ajiki manyan yatsun hannunta sune babu but sauran 4 4 fingers nata duka da zinare tana zaune akan kujera ta hakimce gawani iPad na Apple agabanta tadaura kan wani very very fine stool tana video call dabata iya ganin kowaye a screen din tunda ita daga waje take, hannunta matan rikeda wani white transparent bowl da ita kanta Khairy basuda irinshi agidansu an yanyanka strawberries da kiwi fruits kanana tanaci da fork, kokai waye kaga matan saika shiga taitayinka like duk rawan kanka irin matan nan ne da they don’t even needs to show u su waye kana ganinsu kasan they’re no nonsense powerful woman saisa haryau itadai Khairy bazata iya cewa ta tsani matan bane but kawai bata sonta, hasalima ita tsoronta ma takeji ko haukanta take agidan dazaran Ammi tazo wajen natsuwa take kaman ba itaba kodako da Baffa take magana, kuma agaban kowa ko agaban Baffa ne Ammi zata iya rufe kowa da fada baruwanta saidai in bakayi ba daidai ba. Kallo daya tama Khairy ta dauke kai, ahankali Khairy tajawo kofan falon ta maida tarufe sanan takaraso cikin falon ta nemi waje ahankali akasa tazauna kanta akasa tana sauraron maganan datakeji na namiji daga iPad din ashagwabe data rasa na waye dan tasan muryan duka yaran gidan nan banda Babban yayansu da akace yana UK. Ashagwabe yace “Ammi please niki kyaleni I will get the food nafita jibi fa yanda kitchen dina yadawo” hararanshi Ammi tayi tana kallon screen din tace “My friend dauki egg din break it ingani” cikeda gajiya kaman zai fashe da kuka yace “I don’t even know why I called u ki koyamin yanda ake soya egg ma” dan dariya Ammi tayi da saida Khairy dake zaune tadan saci kallonta dan bata taba ganin Ammi ko taji Ammi tai dariya haka ba lallai waye wanan itakuwa. “Good boy Zayn, tom add a pinch of salt” Zayn! Zayn Zayn! Itako a inama ta tabajin sunan nan Ohhkay kaman shine sunan yayan nasu dake kasan waje ko yayan su Hafiz, tatabaji Baba da Baffa suna maganan. Maganan Ammi ne yadawo da ita daga tunanin datake tace “bagashi nan ba kagama soya egg din amman da u are being lazy” dariya yayi sosai yace “Ammi nataba gayamiki u are the world best Mommy? No not just best you are the bestest Mom in this world Ammi na” dan murmushi Khairy tayi dan maganan yasa ta tuna da Mama haka take cema Mama world best, kiss taji yasakin ma Ammi ta wayan yace “love you Ammi bye” murmushi sosai Ammi tayi tace “I love you too Son, speak later, make sure u put on jacket kafin kafita dan u are having cold” “who am I to say no to this fine woman, Ammi this egg taste delicious bye” dasauri Ammi tace “kaci ahankali karka kwar…..” kafin takarasa maganan ya katse wayan murmushi tayi sosai kafin takalli bowl don fruits din hannunta ganin tacinye yasa ta kwalama mai aikinta kira. “Karima” da gudu mai aikin tafito daga kitchen jikinta har yana bari dan inhar Ammi takiraka sau biyu to kora ne, cikeda girmamawa tace “Hajiya gani” bowl din Ammi tamika mata tsugunnawa tayi sanan ta karba tace “akawo miki wani abune Hajiya”? Girgiza mata kai tayi tamata alamu da hannu ta tafi, wucewa tayi tawuce kitchen falon yarage daga Khairy dake zaune akasa ta takure waje daya saikuma Ammi data dauki wayanta Z-flip tana daddannawa kaman batasan da mutum awajen ba. Ahankali kaman ba Khairy ba tsabagen yanda ta natsu tace “Ammi ina yini” batare da Ammi takalleta ba kota daina abinda takeyi da wayaba tace “yanzu kikaga daman shigowa gaida ni Ummulkhairy” girgiza mata kai dasauri Khairy tayi gabanta nafaduwa da kyar tace “Ammi kiyakuri bansan kin…..” “stand up and get out of this room!” Ammi tadaka mata tsawa dan she finds it insultive ace itace Babba agidan nan ko kare yashigo gidan nan yasan itane Babba an dole ne abata wanan girman balle Wanan Yar karaman yarinyan nan da aka haifa agabanta tashigo gidan nan saita fara zuwa ta gaida kishiyanta sanan zatazo nan, itafa Ammi is like that bata daukan raini kona waye gatada fada, komin girmanka zata iya daga hannu ta kwasama mari. Tashi tayi jikinta har rawa yake itafa adai rayuwanta yanzu this woman is the only woman datake shakka aduniyan nan, duk iskancin ka baka iya kallon fuskan Ammi kace zaka mata rashin kunya kozaka maida mata da magana wlh bazaka iyaba Allah yariga yabata Wanan haiba da kwarjinin nanne, gabanta nafaduwa sosai idanunta sunyi ja tace “Ammi I am so……” “out!” Ammi tai maganan tana nuna mata kofa dasauri tai kofa zata bude aka turo kofan hakan yasa kofan yabuge mata hannu, baya tayi tana yarfe hannun dasauri idanunta sunyi ja Hafiz ne yana sanye da jeans da riga ganin Khairy yasa yace “Khairy kene agidan” hannunta yabi da kallo yace “ohh no sorry nabuge miki hannu ne” murmushi takakalo tana maida hannun baya tace “Ya Hafiz welcome ina yini” sanan tabi tagefenshi tafice dasauri yabita da kallo kafin ya kalli Ammi dake danna wayanta abinta, maida kofan yayi yarufe yazo kusa da Ammi ya zaune yace “Ammi yaushe Khairy tazo” batare data kalleshi ba tace “maiya hanaka tambayanta kake tambayana” shiru yayi baice komi ba, saida tagama abinda zatayi sanan ta ijiye wayan takalleshi tace “how’s my granddaughter”? Murmushi yayi yace “she’s fine” “tafara shan nonon”? Gyadamata kai yayi yace “tafara Ammi, bata barin mu bacci, koda yaushe shan Nono take bata barin Moon tahuta” dan dariya Ammi tayi taharareshi tace “idan naga granddaughter na tarame dagakai har matarka will have to answer me I am very very serious Hafiz, anyway anjima idan yan suna sun watse akwai kayan dazaka tafi musu dashi” Gyadamata kai yayi yace “Ammi kinsan irin uban kudi da Ya Zayn yaturomin wai nabama Moon da Little niko sule biyar bai baniba bayan ni namafi mai jegon wahala” dariya Ammi tadanyi saikuma tai shiru kaman mai tunani ahankali tace “I can’t wait to see yaran Zayn shima” dasauri Hafiz yace “Ammi ai nagayamiki Zayn nadawowa kurikeshi kumai aure dan wlh Ammi Ya Zayn bai shirya yayi aure ba” shiru Ammi tayi batace komi ba, kallon fuskanta Hafiz yayi ganin tai nisa a tunani yace “Ammi kema u believe what I am saying ko” “stop talking about ur brother Hafiz” shiru yayi saikuma chan yatashi yace “ina zuwa Ammi” baijira amsanta ba yawuce yatafi, awaje yaga Khairy gaban tap na wajen flower tana wanke fuskan ta da ruwa, bamata lurada shi ba yana zuwa ya tsaya agefenta yace “after all this years haryau baki gane halin Ammi ba kullum kikazo sai kinyi kuka common my friend, je daki ki dauko gyalenki keda Batool na kaiku gidan suna kowa nachan banda ku” murmushi tayi tajuya da dan gudunta tashiga dakin Mum, basu wani jimaba itada Batool suka fito datai wanka taci gayu motanshi suka shiga sai gidaUnshi. 2️⃣3️⃣ Free page Gidan Ya Hafiz yacika makil da mutane sabida suna, duka yaran Baffa na wajen, Yaran Baffa takwas, Ammi ta haifi hudu duka maza, Zayn ne babba, sai Hafiz, sai yan biyun da Ammi ta haifa maza da Hassan da Hussain, dukansu manya duk sun gama makaranta suma aure yau ko gobe, dan Ammi da Baffa sunyi aure tun suna yara, haihuwan yan biyun yazo mata da complication da dole aka cire mahaifanta gabaki daya data haifi sama da haka, itakuma Mom yara hudu ta haifan ma Baffa, mata biyu Batool da Zara’u wacce itace auta dan maza biyu kebin Batool kafin Zara’u, Abdulhamid da Abdullahi sai Zara’u, Zara’u ce kadai ke primary school su Abdulhamid yanzu suke SS1 boarding school, Batool itace ke university, dayake ana hutu dukansu suna gidan ga mamakinta harda su Ya Manaf da Maheer, dukansu sun hadu dasu Ya Hassan suna gaggasa raguna, mantawa ma tayi tayi kuka suka shiga shagalin suna ga Matan Ya Hafiz badai kirki ba sunan Moon yabita hakan yasa kowa Anty Moon yake cemata. Sai Bayan sallan isha’i sanan suka baro gidan itadasu Ya Manaf, tagaji iya gajiya bacci ma tasoma abayan motan tadaura kanta kan kafadan Ya Maheer, bai tadata ba ganin tagaji yacigaba da danna wayanshi abinshi. Bude musu gate akayi ganin motocin su Baffa yasa daga Ya Manaf har Mu’az din kowa yasha jinin jikinshi, parking sukayi hakan yasa tabude idanunta jin tsayuwan mota ta tashi zaune tana kallon compound dinsu sanan tabude kofa suka fito zata wuce Ya Manaf yace “ke ina zaki”? Dasauri tajuyo takalleshi kafin ma tabashi amsa yace “kibi Maheer kuje flat dinmu su Baffa sunzo magana akeyi” batai musu ba danta gaji tabi Maheer sukai flat dinsu shikuma da Mu’az sukai flat dinsu Mama da saurin su, bude kofa sukayi suka shiga sunabin kowa na falon da kallo, Baffa ne da Baba zaune kan kujera daya, sai Ammi da Mom zaune tareda Ammi akasa da fuskanta ya kukkumbura kaman ba ita suka Bari this morning fuskanta looking normal ba, Mom na rikeda handky tana share idanunta dan takasa rike kuka itakuma Ammi idanunta sunyi ja dan ciwo is something dako enemy naka don’t wish it on him, duk wanda yaga Mama saiya koka mata, kallonsu Mama tayi lurada kaman magana takeso tayi yasa Manaf yakaraso inda take hannunta yakama yarike yace “na tura Maheer da Khairy chan side dinmu Mama” ahankali yace “Mama meke miki ciwo”? Kafin ma wani afalon ya iya magana aka bude kofa aka shigo Dr ne, rikeda wata karaman Leda a hannu yana zuwa allura yahada yazo wajen hannun Mama yakama yamata alluran a jijiya sanan yakalli Baba da Baffa dake kallonshi yace “can I talk to you sir in private”? Girgiza mai kai Baba yayi yace “likita duk duniya banda family daya wuce Wanan circle din dakake gani anan u can say anything, I think we are ready to hear kome zakace right wife” gyadamai kai Mama tayi kaman ba ita ke wahala ba, huci Dr yayi yakalli Mama yace “alluran nan zai saukar da kumburin fuskan nan da wuyanta, but at this point all I can say is make ur wife as comfortable as possible dan koda ankawota asibiti babu abinda zamu iyayi kuma, daga yanzu kome zaku gani kawai hakuri zakuyi har Allah yayi ikon shi dan komi na hannunshi, just make her comfortable and happy, please kudena kuka agabanta kowani abu dan Allah, that’s all bari nakoma hospital” tashi yayi yafita babu wanda ya iya cemai kala, Manaf yayi yayi yarike kukan nashi but yakalli Mama yaga yanda tadawo but dudda haka she’s still faking smile musu kawai yaji zuciyanshi yay breaking, fuskanshi yakifa akan kujera kusada Mama sai kuka yake da Mu’az dahar lokacin shi yama kasa shigowa cikin falon yana wajajen kofa, ahankali Mama tasa hannu takamoshi wani irin rungumeta yayi sanan tamikama Mu’az hannu alamun yazo zuwa yayi shima kuka wiwi ajikinta babu wanda ke iya magana cikinsu har Maman dan kumburin da fuskanta da wuyanta yayi yasa bata iya magana. Ranan dukansu suna zaune a falon nan babu wanda ya iya motsi har asuba sanan tai bacci, daki suka Kaita suka keantar da ita sanan Baffa ya kwashi iyalinshi suka tafi gida, suna shiga alwala yadauro kawai yawuce masallaci. Wuraren karfe 8 nasafe yafito daga masallacin, gida yawuce dayake yana dakin Ammi ne nan yayi bata falo yasan ta kwana hakan yasa yay sama zuwa dakinshi, zama yayi kan wata kujera ta musamman dayake da ita adakin nashi datake nan kaman gado shiru yayi yana tunani, ahankali yamika hannunshi yadauki wayanshi yay dailing number dayay saving da Zayn dayake nan international number, wayan na gab da katsewa yadauka anatse yace “Abba” dan ajiyan zuciya ABBA yasauke anatse shima yace “Zayn nasan is late ko wajenku” gyadamai kai Zayn yayi yana ture shishan dake gabanshi yatashi daga wajen yay bedroom dinshi zama yayi kan study chair nashi jin muryan ABBA somehow couple with the fact Abba baima Saba kiranshi da night ba most time da safe ABBA ke kiranshi ko darana, ahankali yace “Abba what is it are u okay”? Ajiyan zuciya Abba yasauke yace “Zayn Maryam matan Baffan ku batada lafiya, she’s seriously ill, inaso kome kakeyi yanzu kabarshi find any available flight dazaka samu dazai taho naija gobe be it PJ ko normal flight ne kadawo gida” tunda yafara school that’s tun lokacin dayake degree Abba baitaba demanding yadawo gida ba sai this time hakan yasa ahankali yace “okay Abba, but meke damun Mama”? Zayn yay tambayan ahankali dan yanason Mama she’s one humble woman da he admires alot dudda he’s not that close to her shi aduniyan nan ma only Ammin shi ne he’s close too. Ahankali Abba yace “she has blood cancer! Just few days takeda shi left inji Doctors, anyway just come home kayi few days Saika koma tunda baka fara finals dinka ba, good night son” “night Abba” yay maganan ahankali feeling down, yadade ahaka sanan yatashi. Wuraren 8:00 na safe tabude idanunta ganinta adakin yayyinta saida abin yabata mamaki, murmushi tayi ta tashi zaune sanan ahankali ta sauko daga gadon lallai tagaji ko lace din jikinta bata chanza ba tai bacci, jakanta tadauka tawuce tafita daga dakin tana tafiya ahankali, flat dinsu tashiga babu kowa a falo sama tayi dakinta tashiga alwala tayi tai salla tukunna sanan tacire kayan wata doguwan rigan bacci ta tasaka sanan tafito direct hanyar dakin Mama tayi bude kofan tayi tace “Mama tun jiya nan ganki ba adakin su Ya Manaf na kwana” akan gado taga Mama ta jingina da hango ta sanya sweater tai fayau da ita da hulan sanyi akanta batasan mesa ba but gani tayi Mama tamata wani iri a idanu, karasowa tayi gaban gadon saikuma ta tsugunna takai hannunta tai tagumi tana kallon Mama, hararanta Mama tayi da kyar ta iya dagewa tabude bakinta tace “me haka”? Ahankali tana kallonta still tace “Mama wlh kin chanza, lips dinki are so dry, Mama wai bakida lafiyane kike boyemin kinyi wani iri eh sabida kinsan zan damu, bazan damu bafa Mama ai yanzu na girma saima na kula dake” dan shiru tayi tana kallon Maman dake kallonta tanaso tai magana amman azaban datakeji awuyanta yasa takasa, dasauri Khairy tace “zan damu kadan but zan kulada ke bakid lafiyane Mama” tai maganan idanunta na rau rau dan she’s really believing Mama bata da lafiya, ganin haka yasa Mama tamikamata hannu sanan tahadiye duk wani azaban datakeji tace “lafiyana kalau kawai gani nayi my little Khairy has grown so sooo big, yarinya na tai girma she can even take care of her Mama come here” dasauri ta tashi hannun Mama takama sai kawai tasaki hannun tafada jikin Mama ta kankameta sosai ahankali tace “Mama wlh ina bala’in sonki, without you bansan ya zan kasance ba, Mama ko idan na kalli wasu yaran ko sai inga they are not lucky sabida bakene Maman su ba, Mama u are the best Mama I the world, u are the coolest Mom, the softest, the sweetest, bakida fada, gashi kina sonmu, we are ur everything Mama, Mama kinsan menene” girgiza mata kai Mamantayi, Khairy tace “all mothers are mothers, but not all mothers are like Mamana, cus Mamana tafi takowa dadi, Mama kinga duk girman dazanyi I will always be ur baby, Yar autan ki, kinga na gama school nafara aiki zan dinga miki komi, Mama nasan kinje makka but zan kaiki makka da kudina da aka biyani albashi wajen aiki” dariya Mama tahauyi sosai dayasa Khairy wani kalan murna, sanan tace “Mama yauma ni zan miki breakfast mezaki ci na dafa miki” ahankali tace “fate nakeso” wani tashi tayi tasauka daga gadon sanan tai juyi tace “then fate it is bari naje” tajuya dasauri tai hanyar kofa hartasa hannu zata bude kofan ahankali Mama tace “Ummulkhair” faduwa taji gabanta yayi hakan yasa ahankali tajuyo takalli Mama tace “naam” dakai Mama tamata alamu tazo dasauri taje gaban gadon, hannu biyu Mama tasa tai cupping face nata tana kallonta kafin ahankali takai goshinta saitin bakinta sanan ahankali ta manna mata kiss a goshin, murya chan kasa tace “I love you Ummulkhairy, Allah yamiki Albarka, Allah ya haskaka rayuwanki, Allah ya tsaremin ke” ahankali tana kallon fuskan Mama tace “Ameen Mama” takasa tashi, ganin kaman she’s trying to read something from Mamas face yasa Mama tace “Oya tashi kije kimin fate na yunwa nikeji Madam kokin fasane tunda kin tasani gaba kaman kin sami talavijin” da sauri ta tashi tana dariya tafice daga dakin. Bana tagani agaban dakin murmushi tayi tace “good morning Bana natafi yima MaUma fate”. 2️⃣4️⃣ Free page This book is 1k to join my group pay 1k into 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 Chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 Wuraren 11 tagama faten daya cika gidan da kamshi, fito da kulan falo tayi Mama tagani da Baba zaune afalo saisu Ya Manaf sunama Mama hira, tashi Maheer yayi yatayata suka fito da komi tsakar falo sanan suka zazzauna karban na Mama Baba yayi da kanshi yadinga bama Mama faten bashi kadai ba harsu Manaf sunyi mamakin yanda tasha faten dan tadena cin abinci, tass ta shanye sai dadi Khairy keji saida kowa yagama sanan ta kwashe komi itada Maheer sukakai kitchen tarema sukai wanke wanken tace “lallai yau mutanen mutuncin ka na nan kusa Maheer” hararanta yayi yawuce yafita daga kitchen din itama tabiyoshi tafito, Baba dake kallonsu yace “go and get ready Khairy malamin ki zaizo by 12” sama tawuce agurguje ta shirya tafito falo lokacin ba kowa Baba yakai Mama dakinshi, by 4 malamin yatafi su Manaf suka fita da ita basu dawo gidan ba sai around 10 tana zuwa lafiyan gado tabi. Gabaki dayan gidan yau basuyi bacci ba sabida yanda jikin Mama yay tsanani, amai tadingayi na jini both tabaki da hanci, jikinta yay zafi sai maganganu take dabama sa ganewa, saida safen nan bacci ya dauketa. 6 ta tashi tana kallon agogo mamaki ma take ya akayi take lattin tashi late this days, wayanta dataga yay haske yamika hannu tadauka 2miss calls tagani na Aliyu saikuma message dayamata bude message din tayi. “I miss you” murmushi tayi ta ijiye wayan sanan ta tashi tawuce bayi wanka tayo tareda alwala Dan yau tanada morning lectures, tana fitowa tasa kaya tai salla sanan tabude kofa tafito su Ya Manaf tagani a falon sama kwakkwance kan kujera suna bacci, mamaki tayi amman ta tabe baki tai hanyar dakin Mama bude kofan tayi zaune taga Baba kan kujeran dakin yabude Al Qur’ani yana karantawa itakuma Mama na kwance kan gado tana bacci yarufa mata bargo, saida yakai ayar sanan ya kalleta tace “Good morning Baba” murmushi yamata yace “morning daughter, Mama is sleeping jiya dukanmu bamuyi bacci dawuri ba munata hira yayyinki na nan falo suna bacci suma” gyadamai kai tayi tace “eh nagansu” Gyadamata kai yayi yace “jeki breakfast yau Monday 8 kikeda lectures i want you to be serious kigama da good grade” gyadama Baba kai tayi sanan tajuya tafita tana kallon fuskan Mama dake bacci peacefully sanan tasauka falo ahankali, kitchen taje tea tadafa musu duka sanan ta soya chips zama tayi dinning zataci amman hakanan taji takasaci jikinta yamata wani irin sanyi kodan ita kadai ke yin breakfast dinne oho, tashi tayi tawuce sama tana kallon su Manaf da still ke bacci ta shiga dakinta dan shiryawa. Shiryawa tayi tsaf cikin wani black abaya mai bala’in kyau tai rolling gyalen akanta ko kadan batai kwalliya ba but she looks kaman wata Somalian queen, jakanta tadauka sanan tafito, dakin Mama tabude takalli Baba dake karatu har lokacin tace “Baba natafi” saida ya idasa Ayan sanan yadago kudi yaciro yamika mata karba tayi tana murmushi tace “thank u Baba, kacema Mama natafi idan ta tashi bye” murmushi Baba yayi yace “to yarinyar Mama” maida kofan tayi tarufe yasauke ijiyan zuciya Noo yagaji Khairy deserve to know Maman ta is sick, he’s tired of hiding it from her, bari Maryam ta tashi zai gayamata is time sufadi ma Khairy, Khairy is grown up she can handle it. Fitowa tsakar gida tayi tana tafiya ahankali hakanan jikinta kawai yamata sanyi yasaki tarasa mesa kawai she’s feeling sad and week ma yanzun nan, karasawa wajen motanta tayi Adamu na shiga itama tana shiga baya daidai sunajin horn mai gadinsu na budewa, motar Baffan ne ke shigowa gidan Hafiz ke tuki, sai motar Ammi biyeda su da driver ke parking sai kuma motan Mom, bude kofan motar tayi tafito tana murmushi da saurin ta tai wajen motan Baffa, daidai lokacin Baffa na bude baya yana fitowa yana mata murmushi yace “yan makarantan bokoko” dariya tadanyi tace “Baffa ina kwana, Ya Hafiz Baban Baby ina kwana, Laaaa Ya Hassan da Ya Hussain harda ku akazo yau” kafinma suyi magana Baba yace “wuce tafi school karki latti” yanuna mata motarta da Adamu yatada yana jiranta shiga motan tayi tana waving Mom dake saukowa daga motanta dan har yanzu motan Ammi bama abude ba kuma bamata iya ganin cikin banda driver shima ta glass din gaba taganshi dan motan tinted ne, jan motan Adamu yayi suka tafi nai gadi yamaida gate din gidan yarufe daidai lokacin Baba da Manaf suka fito. Ahankali aka bude kofar motar Ammi, wani clean white kafane ya sauko dake sanye cikin wani hadadden sandals na Prada black, nails na kumban kafan are so fresh and white, gently yakarasa saukowa daga cikin motan yana yatsine fuska yana gyara bakin sun glasses na idanunshi na kampanin rayban, yana sanye cikin milk color yadi dayay dinkin jumper dashi daya bala’in amsan jikinshi, yanada tsayi dan wajen gabaki dayansu yafisu tsawo babu wanda baya ganin kanshi, yanada cika dakuma fadin kirji, kana ganinshi kaga Ammi kaman tai kaki ta tofar saisa yafi kannenshi kyau dansu Hafiz da Baffa suke kaman, yanada wani irin black very very dark saje dake kyalli kaman na bature, lips dinshi is so pinkish, gashin kanshi a kwance suna shinning, hannunshi ya daura agogo Rolex akai, ita kanta Ammi anytime ta kalleshi she feels proud da Allah yabata Zayn as her son, Zayn is definition na handsome guy, kyakkyawan namiji da babu macen data isa tamai yanga, ganin Baba yataho wajensu yasa ahankali yakai hannunshi yazare eye glasses na idanunshi yadan sunnar da kanshi kasa Baba nazuwa cikeda mamaki yakama hannun Baffa yace “d’ana Zayn nake gani haka” murmushi daga Baffa har Ammi da Mom sukayi, Baffa yace “da asuban nan yashigo gida” anatse Zayn yace “ina kwana Abba”? Hannu Baba yabashi ahankali yasa nashi hannun cikin na Baba, daidai sukaji muryan Maheer yana ihu. “Babaaa” Dawani irin sauri Baba yasaki hannun Zayn yay ciki Baffa da kowama suka bishi sama sukayi, dakin Mama Baba yashiga yatarar da Mu’az yarike Mama dake aman jini sosai tai lakur babu karfi kodaya ajikinta, wajenta Baba yayi yakamata daga hannun Mu’az yadau tissue yana share mata bakin ganin tadena aman, shigowa dakin Mom tayi takalli Baba tace “Alhaji bari mu chanza mata kaya” girgiza kai Mama tayi ahankali tana rike Baba gam batare datai magana ba, kallonta yayi sanan yakalli Mom yace “abarshi tukunna” karasowa gaban gadon Baffa yayi yaja kujera yazauna yana kallon Mama dabata iya bude idanunta da kyau yace “Maryam mutafi asibiti”? Girgizamai kai tayi ahankali, ajiyan zuciya yasauke yay shiru, shigowa ciki Ammi itama tayi tasami gefen gadon tazauna ahankali tana kallon Mama murya chan kasa tace “kina bukatan wani abu Maryam mezaki ci?” Girgizama Ammi kai tayi hakan yasa itama tai shiru, ahankali Baffa yajuya yakalli Zayn daya tsaya chak abakin kofa shima yana kallon Mama sanan Baffa yajuyo da kanshi ya kalli Mama yace “Maryam ga Zayn dakika ce nakira miki yazo” dan yunkurowa kadan tayi da duka karfinta, dasauri Baffa ganin haka yasa yace “Zayn come” karasowa gaban gadon Zayn yayi ahankali sanan gently ya tsugunnawa gaban gadon yana kallon Mama dake kallonshi kallon dakasan baa hayyacinta takeba yace “Mama I am here” hannunta daya tacire daga jikin Baba data rikeshi gam gam jin haka yasa Baba yatayata , kama hannun Zayn tayi hawaye yazubomata daga idanunta sanan kadan tabude bakinta dasauri Zayn da zuciyanshi ta katse yace “Mama I am here mekike so tell me” yakai kunenshi saitin bakinta, magana tashigamai a kunne wanda harta Baba dayake rikeda ita baiji abinda ta Fadima Zayn ba sanan takoma jikin Baba ta kankame shi, Maheer dataga yana kuka sosai mara sauti abakin kofan ta kalla hannu tamikamai ahankali yataso yazo kawai kankameta yayi yahau kuka sosai ahankali yace “Mama dan Allah kiwarke, Mama please karki mutu kibarmu” motsi sosai bakin Mama yafara hakan yasa Baba ya janye Maheer daga jikinta kankame Baba tasake yi takama hannunshi tarike gam gam kaman dats the only thing dake mata dadi sanan cikin wata kalan murya dabata fita da kyau dan hakoranta sun datse tace “Baffa, Ammi, Mom, dukanku yarana ina rokonku gafara ku yafeni idan nataba bata muku, idan Ummulkhair…..” wani kalan nishi tayi tana kuka sosai dabayama fitowa sosai tace “kuce mata nace tayakuri tayafema Maman ta, i hide everything sabida nasan idanda tasan banda lpy bazata dauki abin da kyau ba, Baban Manaf” tai maganan tana kankame Baba tace “ka kulamin da Khairy dan Allah, Baffa nabaku amanan Khairy da duka yarana, Khairy is fragile, and innocent please ku rikemin yarinyata amana ita nafiji araina, zanbar duniyan nan amman Khairy ce araina sabida ita kadaice diyata mace yayyinta maza ne” ajiyan zuciya Mama tasake saukewa sanan ahankali tace “idan narasu Khairy taki kwantar da hankalinta kabata Littafin nan danabaka ka ijiye mata Baban Manaf” gyadamata kai Baba yayi ahankali hawaye na taruwa a idanunshi Baffa ya bubbugamai kafa alamun karyay kuka, ahankali Mama tace “Baffa kamishi aure dazaran na rasu banson yarana su rasa uwa, Manaf kurike Matar da mahaifinku zai aura kaman ni kada kubata ciwon kai” gyadamata kai Manaf yayi, Ammi kallon Mu’az yayi dake bakin kofa tayi ya tsugunna idanunshi sunyi jajir tace “zo wajen mahaifiyar ka Mu’az” mikewa yayi tsaye da kyar shigowa yayi zuwa wajen gadon kawai yadaura kanshi kan gado yadaura hannunshi kan nata dan that’s what Maheer da Manaf duk sukayi, yanda tazo tana nishi yasa Baffa ya gyadama Baba kai ahankali Baba yasoma karanto mata kalman shahada, saukar da kanshi kasa Zayn yayi, ahankali Mama ta amshi kalman shahadan karfe 12:03 daidai tacika da imani daidai lokacin Khairy ta tashi daga kan kujera sun gama lectures zasu fita jitayi kafafunta sunyi sanyi kawai tai baya zata fadi kaman tai paralyze Rabi dake bayanta ta tareta tace “ke Khairy are u okay” ? rike Rabi tayi tana taba kirjinta tace “gabana fadi yakeyi sosai kafana ba karfi” zaunar da ita Rabi tayi tace “kinyi breakfast kuwa”? Girgiza kai tayi hakan yasa Rabi da sauran kawayenta sukai dariya tace “yunwa ce muje kici abUinci”. 2️⃣5️⃣ Almost good 10min na silent ne yacika dakin, at this point Baba jiyayi kaman shima yamutum ne dan he could feel yanda hannayenta suka sassandare ajikinshi kasa koda motsi yayi hakan yasa Baffa yay taking over, daga Baba tsaye yayi, ahankali Baba yasauke kanshi kasa yana kallonta in disbelief, yadade ahaka sanan yakai hannunshi ya kulle mata idanu kafin yaja bargon yarufeta saikawai yazauna akasa dabas baimasan mema zaiyi ba dan he’s still in shock idan ya kalli su Manaf daduk suke kuka saiyaji zuciyanshi yakara tsinkewa, kafadanshi Baffa yakama ya matsa hakan yasa ya fuzar da iska kafin ahankali yasa hannunshi yakamo su Manaf daya bayan daya duka yarikesu ajikinshi kam kam, juyawa Baffa yayi yakalli Hafiz dashima yay mutuwan zaune hakama su Hassan ahankali yace “Hafiz jeka dauko Khairy daga makaranta” Tashi Hafiz yayi ahankali yafice daga dakin tafiya yake but jiyake kaman iska ke kadashi yana tuna all memories dinshi da Mama shikenan daba danta data haifa ba balle kuma yaranta yaya zasuji. A famfon gaban flower ya tsaya saida ya wanke fuskanshi tass sanan yakarasa wajen mota shiga yayi yatada motan yana kallon yanda mai gadi ke budemai gate he just wish yanada karfin sanar da su, amman ina motarshi yaja yafita daga gidan zuwa school din su Khairy, har gaban department dinsu yaje accounting yay parking yakai kusan good 20min zaune acikin motan baida courage na facing Khairy, da kyar ya iya gyara mood dinshi sanan yakashe motan yafito yamaida yarufe yana kallon ko’ina kafin ya shiga ciki, Khairy nabashi labarin how popular she is a school so yasan ganinta bazai tabamai wahala ba, wasu yammata guda uku dasuka sauko daga bene yatare yace “hello ladies dan Allah kunga Khairy” daya daga cikinsu ce tace “yanzun nan muka rabu da ita ga ajinsu chan wanchan floor din suna lectures” thanks yace musu sanan yawuce sama zuwa gaban class din excuse yay taking hakan yasa lecturer yafito dan yana ganinshi yasan Wanan baimai kala da dalibin makarantan nan ba, dawowa cikin ajin lecturer yayi yace “Ummulkhair” dasauri Khairy dake zaune ta kwantarda kanta kan table takalli lecturer tace “yes sir” waje yanuna mata yace “ana nemanki” tashi tayi ahankali tana daukan jakanta tafito tana tafiya kadan kadan dan sosai kafafunta basuda karfi ganin Ya Hafiz yasa tabude baki cikeda mamaki takarasa gabanshi da sauri tace “Ya Hafiz mekazo yi a school dinmu”? Hararan ko’ina yayi yay gaba abinshi tana binshi da sauri yace “me zanyi a school dinan naku Baffa yace nakawo ki” dasauri tace “Allah sarki Baffa yana ina tare kukazo kenan” “yana gida” yafadi kai tsaye batare daya juyo ya kalleta ba daidai suna karasa sauka kasa tana binshi abaya tace “Ya Hafiz wani laifin nayi ne wanan da dazu dasafen nan nabar Baffa agida mekuma nayi” juyowa yayi yakalleta daidai yabude mota yay murmushi yace “yarinya laifi dayawa” zare idanu tayi cikeda tsoro tace “hala saisa gabana keta faduwa wlh” tada motan yayi tashigo ganin duktai wani irin yasa yace “common babu abinda kikayi so relax” murmushi tayi dasauri tana sauke ijiyan zuciya but dudda haka she’s not just feeling ok hakan yasa tai shiru kaman ba itaba danda tacikashi da surutu shima shiru yamata baice mata komi ba ahaka har suka shigo layinsu, tundaga nesa take hango tulin mutane ata kofar gidansu maza na alwala hakan yasa ta gyara zama tace “Ya Hafiz maiya faru a anguwan mu”? Hango gate din gidansu abude awangale gakuma mutane yasa taji kawai gabanta nafaduwa ba kakkautawa, shiga cikin gidan sukayi daga baki baki Hafiz yay parking dan compund din yacika da mutane wasu tsaitsaye wasu zazzaune hango mai gadinsu da Adamu direbanta na kuka yasa kawai taji wani karfi yazo mata tawani bude kofan taduro juye juye tafara tana juwa juwa tanabin all mazan da idanunta kan sauka akansu tana kallo, kaman daga nesa taji dodon kunenta yaji wani magana. “Itace diyar Hajiyar data rasu” kafafunta da tun dazu sukai sanyi jitayi karfi yazo mata acikinsu kawai tahau gudu tai flat dinsu dataga kofar abude tashiga uwa an jefota tanabi kowa na falon da kallo matan anguwansu ne makotansu sunci mayafai some da charbi a hannu, stairs tayi dawani kalan mahaukacin gudu kawai neman mutum daya take dan gidansu she wants to know what’s happening idanunta ma sun rufe zuciyanta na bugawa batama ganin gabanta bum! Taji sunci karo da mutum da sauri takoma baya sanan tazaro idanunta tadaga kanta takalli wanda ke gabanta kaman yanda shima yake kallonta, batasan wayeshi ba but she could see kamannin shi da Ammi wani kayatyaccen kamshi nafitowa daga jikinshi, ahankali bakinta ke motsi numfashinta na neman gagaranta yi sabida yanda kirjinta ke bugawa ba kakkautawa ahankali tace “I……ina…….ina….”? Idanunta ne suka sauka kan gawar dataga an shimfide anan falon sama da aka suturta, sai yanzu ma talura da mutanen dake falon saman, Baffa, Baba, Ammi, Mom, Ya Manaf, Ya Mu’az, Maheer, Ya Hassan da Hussain Mama ce kadai batagani, still numfashinta na bala’in katsewa tabi idanun kowada kallo barinma Maheer dake kallonta yana wani irin kuka harda majina da she just think that answers her question, gently tadaga kafanta tana wani kalan kyafkyafta idanuwanta tana dambe da numfashinta dake kokarin daukewa tana kokarin tai taking just a step forward kawai tajita blank tai baya straight, wani irin tareta yayi dawani irin sauri Baffa yataso yana kallon Zayn daya tareta yace “Zayn kwantar da ita akasa she’s asmatic, Manaf get me her inhaler” dakinta Manaf yashiga yafito da sabon inhaler dago kanta Baffa yayi yadaura akan kafanshi yakai inhaler bakinta yana bubbuga kumatunta da kyar ta shaka tai wani irin nishi tadawo Baffa takalla tashi tayi zaune kaman bata hayyacinta tace “Baffa ina Mama na”? Ganin Baffa yay shiru yakasa bata amsa yasa takalli Ya Manaf tace “Ya Manaf ina mama ya akayi banganta ba” saukar da kanshi kasa yayi, ahankali Baffa yace “Ummulkhair” wani irin gyadamaikai tayi jikinta ko’ina na ta rirrike Baffa, all this while Baffa has been mai taurin zuciyan but for the first time yaji Khairy kaman itace zata karyashi, dakewa yayi yace “listen to me Khairy, kinaji” gyadamai kai tayi jikinta har kafafunta bari suke ta rirrike Baffa wani irin zufa na keto mata agoshi, anatse yace “dukanmu anan da mazajen dakika gani a waje ke kawai ake jira domin inaso kima mahaifiyarki addu’a, Ummulkhair inaso kizama yarinya mai Imani da kaddara mai kyau ko mara kyau sanan kisani cewa kullu nafsin za’ikatul maut, i want you to calm down don’t shout and don’t cry kinga kinada Asma karkije kima kanki illa, Ummulkhairy Allah yayiwa…..” Baffa yadanyi shiru ganin yanda tazaro ta kwalalo manyan idanunta waje kaman zasu fado kasa yanda jikinta ke rawa zaka dauka ajikin injin markade take, daurewa Baffa yayi ahankali yace “Allah yayiwa mahaifiyar ki, Maman ki rasuwa Ummulkhairy”. 2️⃣6️⃣ Wani kalan shuuuuu taji kunenta nayi, itadai tasan taji koke koke, taji maganan Baba, su Ya Mu’az har maganan Ammi tasan taji sama sama kafin chan kuma taga tabude idanunta tana kallon kowa dake kanta, kala batace musu ba rarrafe ta shigayi har zuwa gaban gawan zama tayi dirshan tana kallon farin likafanin hannu tamika zatakai tabude saikuma tai shiru kafin ahankali tasa hannunta taja likafanin kasa fuskan Mama ya bayyana tai wani haske ga alamun murmushi tanayi wani kuri tayi da idanu kaman tahaukace sai kawai idanunta aukahau mata yana kaman Mama murmushi take mata dariya tayi sanan tajuyo ta kalli Maheer dake kuka tace “Ya Maheer dena kuka kaji zoka gani ga Mama nan namin murmushi, Mama bata mutu ba bacci take wlh gashinan zoka gani” babu zuciyan wanda bai tsinkeba adakin ahankali takai bakinta saitin fuskan murya chan kasa tace “Mama Mama, world best tashi kiji, Mama ai bacci kikeyi ko” tasake shiru, ganin ko motsi Mama batayi yasa tai tagumi tana kallonMama tace “zan jira harsai kin tashi kinmin magana” ahankali Baba yataho yazauna kusada ita dasauri tajuyo takalleshi kaman mai karantan wani abu akan fuskanshi, kafadan Khairy yakamo sanan ahankali yace “Ummulkhairy mamanki has been bathling with cancer for so long, blood cancer bataso kisani cus tasan abinda zakiyi kenan idan kikaji she has few days left, u will not take it likely, saisa taboyemiki all this while mamanki has been sick, seriously sick amman taki yarda kisani duk ciwon da mamanki keyi taganki she will pretend she is fine” hawaye masu bala’in dumi ne suka zubo mata dasauri tasa hannu tashare, ahankali Baba yace “karki sakawa Maman ki hakan nan Khairy inhar she’s your world best, kimata addu’a tasan tabar ya tagari aduniyan nan muje mukaita makwancinta, your mum is tired she need rest, go and pray for your mum” ahankali Khairy tasake matsawa kusada Mama she can’t believe Mama ne nan kasa addu’an tayi sai kuka ahankali tace “Mama dan Allah dagaske wai kin rasu?”, zuwa yayyinta sukayi kawai rungumeta ahankali Manaf yace “Mama tarasu Khairy pray for her” Ahankali tace “Mama Allah yajikanki Allah ya gafarta miki, Mama why did u leave me, shikenan bazan kara ganin ki ba, Mama maisa baki bari na rokeki kiyafemin ba, kullum ina cikin batamiki rai inta rashin ji, Mama Tayaya zan cigaba da rayuwa baki aciki Mama Innalillahi wa Innailaihi raji’un” tashi Baba yayi ahankali hakama Baffa dasu Ya Hassan da Hafiz dakuma Zayn zasu dauki Mama dan kaita waje salla, wani Zabura tayi zata tashi dasauri Manaf yariketa, Mom yabama ita tana wani kalan nishi hannu Mom tasa takarbi inhaler ta tace “Khairy Khairy” kaman zata haukace haka takeji da kyar ta iya kallon Mom tace “Mom na shiga uku, Mom Mama tarasu Innalillahi wa innailaihi raji’un, Mom wlh wlh ko….” kawai maganan yakakare takara suma, ruwa Mom tashafa mata a fuska tanamata addu’a, tafarfado ta sume tai having Asma attack haka tadingayi ahaka har akama Mama salla aka tafi da ita, Khairy bamatasan inda kanta yakeba tana jikin Mom, jikinta yay wani mahaukacin zafi dayasa Mom takalli Ammi dake zaune tanajan charbi tace “Hajiya kira Alhaji Dr yazo jikinta yay zafi dayawa, kuma suman nan datakeyi yay yawa” dan jim Ammi tayi sanan tadauki wayanta takira Baffa ta sanar dashi. Bayan magrib Baba yashigo gidan tareda Baffa gaisawa yayi da matan dake falo dakemai gaisuwa sanan suka taho sama tundaga stairs yake kallon Khairy dake kwance akasa gatanan gatanan ne kawai baa cewa komi, tsugunnawa Baba yayi agabanta ahankali yadagota sharaf ta taso Mom yakalla yace “tayi salla kuwa”? Girgizamai kai Mom tayi, Baba zaiyi magana kawai tasaki wani sabon kuka mai bala’in tabarai dayasa kowa na dakin yazuba mata idanu tana taba zuciyanta kaman ta mutu takeji, kaman tai hauka takeji, kaman tadawo da hannun agogo baya takeji tama Mama duk abinda takeso batare datasa Mama fushi ba, duk su Baba magana suke mata amman harga Allah bata gane komi kunenta ma yadode, duk suna zaune ahaka tai kuka ta sume tadawo Dr yashigo gidan, allura kawai yamata aka samu tai bacci, Baba zai dagata Dr yace “ku kawo bargo kurufa mata, let her sleep anan” Baffa da kanshi yashiga dakinta pink bargonta da filonta yadauko yakawo Baba yakarba yasamata akarkashin kai sanan yarufa mata bargon yana kallonta yana kafin yasa hannunshi yacire rolling gyalen dake kanta ya ijiye gyalen agefe long kalaban ta suka bayyana duk akai shiru. Hayowa saman sukayi duka yaran Hafiz na rike da jakanta daya dauko daga motanshi Dan dazu amotar tabari dakinta yabude ya shiga ya ijiye sanan yafito yasamu gefe daya yazauna afalon, suma su Hassan da Manaf suka zazzauna, ahankali Zayn ke hayowa stairs din da duk yay wani irin tsayawama waje yayi yin wata waya saisa bai shigo tareda kannen nashi ba,hayowa yayi kallo daya yama Khairy dake bacci akasa da aka lullube da pink bargo yadauke kai sanan yawuce gefen Ammin shi yazauna akasa tareda daura kanshi kan cinyanta hakan yasa tadaura hannunta ahankali tana shafa kanshi, kallon yaran Baffa yayi yace “kutashi kutafi gida mu muna nan” cikinsu duka babu wanda yay motsi, ahankali Ammi dake shafa kan Zayn tace “Son tashi katafi gida kahuta yau ka dawo daga tafiya” girgiza mata kai yayi ahankali yace “I don’t wanna go Ammi” kallon Hafiz Baba yayi yace “wuce katafi gidan ka Hafiz” girgiza kai yayi shima yace “Baba ai basu kadai bane kanwarta damai mata wanka duk suna nan” addu’a Baffa yayi dukansu sanan aka shafa, aka zauna turus duk wanda yaga su Baba da yaranshi saiya tausaya musu abinda kuma yahana yaran Baffa tafiya kenan Dan idan suka tafi gidan zai musu wani iri kai mutuwa batada dadi! Baba da Baffa sauka falon kasa sukayi sukuma yaran duk suna wajen kusan ahaka bacci ya kwashe kowa daga Ammi da Mom da duk suke kan kujera zuwa su Manaf dake bacci rabi rabi falon yarage only Zayn ne baiyi bacci ba dayake tattaba wayanshi maganan da Baffa da Baba keyi akasa yanaji. Motsin da Khairy tayi cikin bacci yasa yajanye kanshi daga waya yazuba mata idanunshi kusan sai yanzu nema yake mata a very good kallo tunda yazo, hawaye yaga suna gangarowa daga gefen idanunta pink lips dinta na motsi sosai cikin bacci ta kankame pink bargon da aka lullubeta dashi tana maganganu da kana gani kasan mafarki take. “Mama Mama wai kin mutu? Ai baki mutu ba ko, bansan menama su Baffa dasukemin karya ba, Mama zansha madara, in dauka, Mama Mama Maaaaa….” Wani dogon ijiyan zuciya tasauke na kuka kalabanta daya na saukowa kan fuskanta, dauke kai yayi daga kallonta shi dabama danta ba mutuwan yajishi balle yaran data haifa, he can’t even imagine loosing Ammi God no please, Allah ya sassauta musu koma mesukeji a zukatan su. Wuraren 4 daidai tabude idanunta daga kwance datake tana kallon saman dakin da kallo, the first thing daya fado brain nata is mutuwan Mama, ajiyan zuciya tasauke tana assuring kanta cewa mafarki ne tayi, juyoda kanta tayi tabi kowa na dakin da kallo, Hafiz nakan kujera yatakure yana bacci, Ya Manaf na zaune shima kan kujera yana bacci, Ya Mu’az ma haka Maheer ne kadai akasa yana bacci, sai Zayn da kanshi kekan kafan Ammi yana bacci shima kaman wani auta, Mom dake saitin inda take akan kujera tana bacci itama ta kalla ajiyan zuciya ta sauke zuciyanta na tsinkewa but she’s still in disbelief, bargon jikinta ya yaye ahankali sanan tamike tsaye da kyar cikinta namata wani irin ciwo na yunwa dan jiya all through babu abinda tasa abaka, tadade tsaye tana rikeda cikinta kafin ahankali tafara tafiya jelan kalaban kanta na lilo abayanta tai hanyar dakin Mama, ahankali tasa hannunta tabude kofan kaman a kunnen Zayn danshi baida nauyin bacci hakanan any movement kodan kara daza’ayi yana tashinshi da sauri yajuyo da kanshi yakalli kofan tana tsaye bakin kofa tarike handle na kofan da hannu tana kallon cikin dakin gashinta na lilo. Ko’ina na dakin takebi da kallo idanunta namata gizo daga taga Mama tafito daga bayi tana mata murmushi saita ganta kan dadduma tana mata murmushi, saita ganta kan kujera tana zaune rikeda littafin zikirin ta saikuma chan taganta kan gado kwance tana mata murmushi, hannayenta duka biyun tadaga takai kan idanunta ta murza idanun da kyau sanan taciresu tasake kallon dakin amman babu kowa ciki dawani irin sauri ta shiga dakin tai bayi budewa tayi dasauri tace “Mama kina ina” ganin babu kowa abayin yasa tadawo dakin tana juye juye kalle kalle bakinta na rawa tace “Mama kina ina”? Gadon tayi ta yaye bargon kan gadon, jini jini datagani a zanin gadon wanda na aman jinin da Mama tadingayi ne yasa taji kafafunta sun kara sanyi kawai tayi kneeling awajen takifa kanta akan gado sai kuka kaman ta kwakulo zuciyanta tayar takeji kukanta sa duk wani wanda zaiji tanayi kuka yake, kowa na falon tunda tafara kiran Mama suka farka amman babu wanda ya iya shigowa yacemata wani abu abar Khairy tai kuka dan ita akama Wanan mutuwan. Da kyar Manaf ya iya tashi yashigo dakin gaban gadon yazo kusada ita yadaura hannunshi akan bayanta murya chan kasa yace “Khairy stop crying and pray for Mama, kinga tun jiya baki magrib ba balle isha’i, muje dakinki kicire rigan nan shower kiyi salla and pray for Mama, Mama tariga tarasu……” wani kalan ihu tayi da saida gidan gabadaya ya amsa. “Mama bata rasu ba, Mama batada lafiya babu wanda yafadamin, mena muku? Ni yarinya ce dazaa boyemin uwata batada lafiya, nama Mama laifi dayawa bansami dama na roketa gafara ba, nabar Mama agida natafi school nadawo kucemin Mama tarasu, babu wanda yagayamin Mama batada lpy saidai kugayamin tarasu, Mama b…….a…” maganan yasoma gagaranta sabida mugun attack na Asma daya taso daukanta chak Manaf yayi yafito da ita daga dakin yana karban inhaler da Maheer kebashi, Mom tace “please ku kulle dakin nan tadena zuwa ciki” kwantar da ita kan gadonta yayi yasa mata inhaler cus nishi take kaman zata mutu da kyar ta shaka, Mom tashigo dakin takalli Manaf dake kanta tace “tafi Manaf” fita yawuce yayi daga dakin. 2️⃣9️⃣ Free page Ganin yarinyar nan da Mamanta tarasu dayaga antaho da ita gidansu dazu dazasu dawo dan he can’t even remember her name yasa yadan ware idanu yana binta da kallo yanda take sauka daga kan staircase din gaban flat din Mom, babu takalmi akafanta babu dan kwali akanta kalaban kanta na lilo atsakiyan bayanta, daga ita saidan rigan bacci pink mai hannun taliya daya tsaya a guiwanta, ganin yanda take tafiya one one as if she’s trying to hold something yasa yadanja karamin tsaki yace “God am I a baby sitter now” jin tace Mama kijirani tai hanyar gate yasa yadanja tsaki yatashi dasauri ganin tai hanyar gate, dawani irin sauri yasha gabanta batare dayace kalaba yay folding hannunshi a chest dan ihu yaso yamata but to his biggest suprise gani yayi gabaki daya idanunta are close is she sleeping walking or what? Yatambayi kanshi daidai ta iso gabanshi babu any tazara tsakanin shi da ita tsayawa yayi yana kallonta just to feed his curiosity yaga mezatayi, wani kalan heart melting murmushi tasaki daya bala’in lobar da dimples dinta all the 2 yabayyana set na white teeth dinta, pink lips dinta nawani kalan shinning kafin ahankali takai duka hannayenta biyun tadaura kan hannunshi daya rungume a kirji takama cikin muryanta kaman na baby tace “Mama kinjirani, Mama I miss u, karki kara tafiya ki barni kinji Mama” tai maganan tana warware hannunshi daya rungume a kirji tasaukar da hannun kasa sanan gently takara tako one more step ta shige cikin jikinshi tai wrapping two hands nata around his back tawani kalan kankameshi tana sauke ijiyan zuciya dahar cikin brain dinshi saida yaji ahankali tace “Mama bacci” tunda yake in his life what he just felt now baitaba jinshi ba, sandarewa yayi hannunshi sauke akasan batare daya iya komiba yanajin saukan ijiyan zuciyanta akirjinshi yana kallon tsakiyan kanta da yanda gashinta ke lilo sabida iskan dake kadawa da yanda heart dinta ke biting each beat yana jinshi anashi heart din, yakai kusan 2min ahaka she’s still holding him tight batare data kara magana ba, ahankali yadaga hannayenshi dayaji sunyi sanyi kaman basa functioning kuma yakai saitin hannunta abayanshi zai kwance yanda tadaure hannun abayanshi, kankame hannun tasakeyi saikuma yaji tasaki kuka dabaida kara ko kadan. “Baran sakeki ba Mama, ina sakinki cemin zasuyi kin mutu, Mama nakusan haukacewa da suka fadamin haka ni nasan baki mutu ba, ni ajikinki zanyi bacci anan dakinki zanyi bacci, I will not allow u to leave me ever again and go” yanda hawayenta kebin kirjinshi yasa yaji zuciyanshi ta tsinke shifa baicika tausayin mutane ba but for the first time jiyayi yarinyar nan tabashi tausayi sosai ahankali yakomar da hannunshi batare daya rabata dashi ba, yadan dade ahaka sanan gently yadan duka tareda ita yasa hannayenshi the two yadauketa ajikinshi kankameshi tasake yi gamgan tana kara gyara zaman kanta akirjinshi yana kallon fuskanta saida tagama sanan ahankali kaman yadauki Kwai yafara tafiya har zuwa flat din Mom, shiga ciki yayi daman kofan abude yake yay stairs da ita yana mamakin yanda batada nauyi kaman yadauki paper, dakin Batool dayagani a bude ya tabbatar mai daganan tafito, shiga cikin dakin yayi dudda ko’ina da duhu but he could see sabida hasken window dake nuno compound nasu gently ya tsugunnawa kaman yanda ake kwantar da baby haka ya kwantar da ita kan gadon zai zame hannunshi yaji ta chapke hannunshi da sauri tana sheshekan kuka kaman yanda jarirai kema mamansu takai hannunshi kirjinta ta kankame sosai kaman idan tasaki hannunshi something will happen to her, wani dauuuu yaji a brain dinshi kaman an watsa acid a alkaline environment, dan gabaki daya a boobs nata ta kankame hannun nashi, he could basically feel sign na her sleeping nippy, karya fizge hannun tahau kuka ne this is middle of night a ganshi adakin nan saisa yakeyi ahankali, gently ya tsugunna jikin gado, wani kalan zufa yaji yana ketomai shi kanshi baisan mesa ba this is not the first time yake feeling boobs na mace why is hers different, why so much effect, ahankali yakai dayan hannunshi yadaura akan fuskanta yana shafa kumatunta he don’t even know what to do samin kanshi yayi da hura mata iskan bakinshi a fuskan wani irin ijiyan zuciya ta sauke tasaki hannun nashi kadan bakaman yanda ta kankame hannun a kirjinta da farko ba, ganin haka yasa yacigaba da hura mata iskan yana shafa kumatun nata dayaji yamafi na jariri taushi sanan gently yashiga janye hannunshi kafin yay nasaran janye hannun duka sanan ya dauke hannun kan fuskan nata dawani irin sauri yatashi yafice yaja kofan nasu ahankali sanan yasauka kasa yafice waje abinshi. Wuraren 6 tafarka daga bacci daga Mom har Baffa daya shigo dubasu da asuba saida sukaji dadi ganin yanda tai bacci sosai yau dan this last few days dudda ana mata allura bata tabakai war haka bata tashi ba 4 ta tashi ko 3 nadare ma. Kalle kallen data shigayi yasa Mom data shigo dubata tace “Khairy ya akayi me kike nema? Kin tashi” Dasauri zuciyanta na bugawa fast fast tace “Mama ina take?” Shiru Mom tayi tana kallonta hakan yasa tafashe dawani irin kuka tace “wlh ba karya nake ba Mom naga Mama adakin nan takwana tareda ni I was even holding hannunta sabida idan kuka tashi kugani, kuma tace bazata kara tafiya tabarni ba” hannu Mom tasa tadafa cinyanta ahankali tace “Khairy idan aka rasu an rasu kenan mutum baya dawowa, sabida rasuwan Mama na ranki saisa kike mafarke mafarke, Mama tarasu, you had a dream about her, tashi kije ki dauro alwala kiyi salla” tashi tayi ahankali tana goge hawayen dasuke zubomata tai bayi, fitowa tayi daure da alwala tai salla, da kyar tasha kunun da Mom tabata shima kadan sanan Mom tabarta da su Batool da Zara’u daketa musu surutu Khairy na kallonsu kuri kaman tazare itakuma Mom ta sauka kasa. Knocking akayi tareda shigowa dakin, Zayn ne yana sanye da kananun kaya yay kyau yana zuba wani uban kamshi, ganinshi yasa Mom tace “Zayn shigo mana zoka zauna” karasowa yayi cikin falon cikeda girmamawa yace “Mom zan tafi” dasauri Mom tace “harzaka koma” ahankali yace “eh something come up dole nakoma dama 1week naso nayi amman bazai yuba” murmushi Mum tayi tace “Allah sarki to Allah kiyaye hanya, Aida nasan yau zaka tafi dana maka su dambun nama wlh yanzu sai yaushe kenan” dan shiru yayi yana tunani sanan yace “let’s just say 2month intotal nagama komi” ahankali Mom tace “Alhamdulilah Alhamdulillah komi yay farko zaiyi karshe Allah bada sa’a Allah ya kiyaye hanya” Ameen yace yana tashi har waje Mom tarakashi Baffa dasu Hafiz suka daukeshi a mota har zuwa airpDort. 3️⃣0️⃣ This book is 1k pay into 3107021073 aisha Muhammad first bank. Saiki turomin evidence of payment ta watsapp number na 07012181461. LAST FREE PAGE Bayan 3 weeks! Yau 3 weeks kenan chip chip da rasuwan Mama, an dage sosai da addu’a akanta she’s very very much better yanzu, tadena koke koken nan she’s doing everything dakanta saidai she hardly speak, kome aka cemata saidai ta gyadakai tariga ta yarda Mama tarasu and babu abinda zata iyayi dazai dawo da ita, har yau bata iyacin abinci at all, saidai kadan kadan kuma shima liquid, once in a while Besty nazuwa har gidan Baffa dubata dan su Ya Manaf nema suka kawota gidan tasani, sanan Baba yabata number shi yanzu ma haka ance gobe zata koma school danta kira Baba next week zasu fara first semester 400 level exam sauran ta one semester tagama school hakan yasa aketa shiryamata har sababbin dinki Baffa yamata hadadun gaske Mom ma haka, just to cheer her up amman ina bin kowa take da ido dakuma kalman godiya shikenan. Yau tun safe Mom dakanta ta shigo dakin ganinta zaune kan dadduma yasa tace “laaaa yar nan Oya maza tashi ki shirya yau kinada lectures 8 kika zauna yanzu har 7 yi maza tashi ki shiga bayi” batai musu ba tashi tayi tai bayi wanka tayi tafito, gani tayi Mom tamata arranging kayan dazata saka akan gado, wasu Riga da skirt ne na atampa cikin sababbin da aka dinka mata orange color ne atampa yanada flowers yan kanana brown, sai brown gyale tahada mata jakan makarantan ta da book sai wayanta da tuntuni aka kawomata gidan bata taba tabawa ba shima Mom dukta saka mata, shiryawa tayi tsaf, Mom tashigo dakin dauke da tea da chips tana kallon yanda kayan suka mata kyau dudda tarame sosai takalli kitson kanta tace “satin nan zamu kwance kan nan ayi wani kitso Khairy” takarasa ta ijiye abincin akan carpet sanan tadauki dan kwalin kayan tamata dauri mai kyau kafin tadauki tea tabata, karba tayi da kyar ta iya shan dan kadan sanan ta ijiye, ita kanta Mom batama iya tursasata taci abinci tashi tayi tadauki jakan a hannu da gyalen ahankali tace “natafi” binta Mom tayi tace “dan Allah Khairy kiyi karatu da kyau kinga jarabawa zaku fara next week karki fadi” Baffa suka gani afalo shima wa’azi yamata sanan yakaita har mota saida tashiga sanan yama Adamu alamun yatada motan yatada suka tafi, titi kawai takebi da kallo, jitayi hawaye ya gangaro mata dasauri ta share, she use to kullum saitaga Mama take tafiya school, school sukakai Adamu yay parking ganin taki tashi yasa Adamu yace “tashi kije class Khairy” kukan datake rikewa taji yazo mata fashewa da kuka tayi sosai tasa gyalenta akan fuska tana kuka shiru Adamu yayi takai kusan 20min sanan ta share fuskan nata da gyalen idanunta sunyi jazur tabude kofa tafita tana tafiya kaman iska ya kadata tafadi tarame babu abinda yarage ajikinta sai nono da hips, su kadai ne basu rame ba but wuyanta duk kashi idanunta sun fada ciki sosai, ahankali take tafiya yan makaranta su natareta suna mata gaisuwa gyadamusu kai kawai take tana wucewa dasauri dan bataso taita kuka ta tarama kanta mutane ahaka hartakai aji da lecturer ma aciki, baa hanata shiga ba hakan yasa tashiga taje tasami chan baya karshe chan tazauna ko abu daya bata ganewa ahaka aka gama lectures din lecturer tafita by 10, basuda wani lectures kuma sai 2, zagayeta yan ajin sukayi ana mata gaisuwa gyadamusu kai take tana danne zuciyanta, ganin yanda takeyi yasa class governor dinsu yace “dan Allah kubar Khairy tahuta let’s go guys” fiffita daga ajin suka shiga yi, su Amal sukace “tashi muje cafe Khairy” ahankali tace “kuje ina zuwa” dan jim sukayi suna kallonta babu maison yatakurata hakan yasa duk suka tafi ajin aka watse ita kadai tarage aciki hakan yasa takifa kanta akan desk tahau kuka ita kanta she wants to stop the cry amman bata iyawa tadade ahaka ita kadai a class kaman aljana kanta akife akan table, kaman daga sama taji ance “Ummulkhair!!” Awani irin hankali take dago kanta daga table kafin tadaura jajayen rinannun idanunta kan Aliyu dake tsaye agaban ajin yana sanye da uniform na yan sanda yana kallonta, yarame shima idanunshi sunyi wani kala yana mata kallonda only heart dinshi zai iya sanar da mai kallon ke nufi, jitayi duniyan ya tsayamata chak duk wani bakin ciki emotions, tausayin kanta da sauransu sun taso mata sun tsayamata awuya, jikinta harwani rawa yake ganinshi dan she can’t believe shine, wani irin tashi tsaye tayi tana kallonshi kaman yanda yake kallonta kallon dayana mata zuciyanta nafassaramata dawani irin gudu gyalenta na faduwa akasa tai wajenshi kaman dama shitake jira batai wata wata ba kawai tawani kalan fada jikinshi sai kuka sosai as if she ne dama asalin wanda takeso tama kukan, ahankali ya lumshe idanunshi yana feeling kukan datake in every single bone of his flesh, hannayenshi yadaga gently yay wrapping nasu around her back kafin yakai bakinshi saitin kunenta murya chan kasa yace “I am here for you Pickle, I am here” sake kankameshi tayi sosai cikin kuka tace “Ya Aliyu Mama…..” murya chan kasa dake nuna he’s with her, he’s feeling what she’s feeling yace “I know Pickle” takai almost 3min tana kuka ajikinshi sanan ahankali yacirota daga jikinshi yana kallon yanda take kuka hannunta yakama zuwa first kujeran dake ajin zaunar da ita yayi sanan ya tsugunna agabanta still yana kallonta, jikinta ko’ina rawa yake na kuka, hannunshi yasa a aljihu yaciro clean handkerchief dinshi yakai kan fuskanta yafara share mata hawayen murya chan kasa yace “shiiiiiii” shiru tayi tana kallonshi still, tass yashare mata fuskan harda hancin sanan yamike tsaye yay inda take zaune a ajin da, tsugunnawa yayi yadauki gyalenta daya fadi a tsakar class din sanan yakarasa yadauki handbag dinta sanan yadawo har zuwa inda take a zaune, gyalenta ya yafa mata aka yasauka har kan kirjinta sanan yamika mata hannunshi yace “let’s go” kallon fuskanshi tayi kafin ahankali tasa soft hannunta cikin nashi yariketa gam sanan suka fito daga class din suna tafiya ahankali sai kallonsu ake amman ko ajikinshi har zuwa parking space, gaban motan yabude mata zama tayi tana kallonshi da jajayen idanunta sanan ya maida kofan yarufe kafin yazagayo yazauna wajen mazaunin direba yarufe motan yatada motan yafice daga school din da ita, sunyi tafiya mai nisa sannan taga ya tsaya gaban wani eatry ya shiga batasan meya siyoba yadai bude bayan motan ya ijiye komi sanan yadawo yatada motan, wani waje yakaita ita kanta duk zamanta a Abuja batasan wajen ba, duwatsu ne masu kyau ga kamshin ruwa awajen da alamun akwai water fall ciki, parking yayi sanan yakalleta yace “I am coming” fitowa yayi yabude baya yadauki ledan daya siyo musu dawani babban dadduman dayake dashi mai taushi sanan yashiga wajen baiwani dade ba yadawo, bude inda take yayi yasake saka hannu yadauki jakanta sanan yamika mata hannu ahankali tasaka nata ciki, saukowa tayi yamaida motan yarufe sanan suka shiga wajen, cikin dutse ne kaman cave sanan ga ruwa atsakiyan wajen yana gangarowa daga dutse babu kowa wajen, wajen is so serene and peaceful bakajin karan komi saina tauntaye dana karan ruwan dakuma kamshin ruwan dutse dakakeji. Zaunar da ita yayi kan dadduman sanan shima yazauna yana facing nata, ledan yabude yaciro take away na biryani rice da rosted lamb sai ruwa mai sanyi daya siya yabude, ahankali yasa spoon din aciki sanan yadebo abincin a spoon yakai bakinta yana kallonta jitayi zuciyanta yawani tsinke wani sabon kuka yazo mata ahankali tashiga reramai kukan, jaaa idanunshi yayi sanan gently ya girgiza mata kai bude baki tayi yasamata abincin taci saiyau tasan ashe tanajin yunwa, kadan tarage abincin all through harta koshi kuka take, yanabata abaki tanaci tanamai kuka sanan yadauki ruwa yabata shima sha tayi sanan ya ijiye. Ijiye komi gefe yayi sanan ya matso kusada ita ganin taki daina kukan cikin muryan lallashi da murya dake nuna asalin so da tsantsan so yace “I know! and it’s okay I am here for you okay” gyadamai kai tayi tana sauke ijiyan zuciya, hannunshi yakai yakamo hannunta ahankali yadaura hannun nata kan kirjinshi yana kallon idanunta yace “can you feel yanda zuciyana ke bugawa sabida yasan kina cikin damuwa?” Gyadamai kai tayi ahankali murya chan kasa yace “I came to your house tun ranan ban sake samin kwanciyan hankali ba because I know my Pickle is not fine, I lost sleep, I lost peace, bana iya komi sabida ke, kinason zuciyata tabuga because of you ne”? Girgizamai kai tayi ahankali tanajin maganganunshi har a bargon kashinta, murya chan kasa yace “I lost my Mom when I was 25yrs, I know what u are going through Khairy, but if anything yasameki bazan iya rayuwa ba I will die, I love you alot, Ummulkhair I Love You” wani sanyi taji ya ziyarci zuciyanta each magana dayake gayamata zuciyanshi datakejin bugunshi nakara tantance mata cewa gaskiya yake fadi, ahankali yace “when I lost my mum I was depressed but as time goes on nazo ma fahimci this is not abinda mamana keso, she wants me happy, tanaso na cigaba da rayuwana, tanaso nai fulfilling dreams dina and above all she wants me happy and praying for her, Pickle abinda kikeyi yanzu is that abinda Mama kiso”? Girgizamai kai dasauri tayi alamun aa ahankali yace “to mesa kike hakan”? Lips dinta na rawa kuka na neman kufce mata tace “because banajin magana and nasa Mama fushi dayawa, halama saisa taki fadamin she had blood cancer” tafashe da kuka tana kallonshi girgiza mata kai yayi yace “Mama taki gayamiki she’s ill ne because you are her youngest daughter Khairy u can’t handle it, and Mama wants wats best for you, that’s is the reason, trust me pickle you are not stubborn, ke y’a ce dakowani parent will wish to have, I know Mama is so proud of you, ta haifi selfless and fearless yarinya that can stand for her self a ko’ina, karki kara tunanin Mama is angry with u iyaye basa iya fushi da yaransu, and Wanan kukan dakike da rashin cin abinci shizaisa Mama tai fushi dake, cus instead of kinata addu’a kina using time din to cry and not eating zai baki wani sabon ciwo u want to be sick” girgizamai kai tayi dasauri ahankali yakai hannunshi yakama dayan hannunta yace “promise me daga yau kin chanza, u will stop all this, take care of yayyinki and your Dad, do you have any idea yanda sukeji ga rashin Mama gaki” sake girgizamai kai tayi yace “promise me you will change daga yau, u will always pray for Mama, study well and pass exam dazaku fara next week, did u promise” gyadamai kai tayi ahankali tace “Uhm I promise” murmushi yayi he feels kaman yarungumeta yasata ajikinshi and just stay like that forever” ahankali yace “smile for me i finds it healing is my therapy, smile” dan murmushi kadan tayi ita kanta tamanta the last time datai murmushi. To jama’a anan nakawo karshen free pages zan barku da tambayan nan ALIYU NE KO ZAYN NE??? Dan samin amsoshin nan kucigaba da bina awanan Littafin mai suna ALKAWARIN ZUCIYA! Dan son cigaba da karanta Wanan littafin zaka iya turo 1k ta 3107021073 aisha Muhammad first bank saiki turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding naki a group din danake posting. Dan girman Allah badan niba kubiya ku shiga group ku karanta. Support me🥰 You can chat me up directly by clicking on this link wa.me/+2347012181461 Thank you M Shakur🥰 ********************** ? ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************? ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ? ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ? **************************