🛥️ABDURRAHIM MATUK'IN JIRGIN RUWA NE🛥️ (RENEW) 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori, Page 1 Tafiya ta ke yi da ga gani sauri takeyi,idan ka kalli fuskarta zakaga ta nuna yanayin damuwa. Matashiyar budurwa ce da bazata wuce shekara goma sha takwas ba. Wani ma dai-dai cin gida ta shiga. Zaune ta iske su sun sa Mahaifinsu a tsakiyar su suna ai kinyi mai sannu.Na'ima da shigowarta kenan kallan Mahaifinta tayi dake kwance cikin wani hali ta ce "Sannu Baba ya jikin?." "Yauwa Na'ima ,ina Hassan d'in? " Cewar mama kafin ta bata amsa Hassana yayi sallama ya shigo, da saurinshi yak'ara in da malam Yahaya yake kwance." Sannu baba ya jikin naka?" Yauwa Hassan jiki alhamdulillah" Baba jikin ne ya sake ta shi? ". Mama ce ta amshe maganar ta hanyar cewa" Hassan dan Allah salanke zaka ka amso mai magani yanzu, adafa mai ko Allah zai sa jikin ya lafa"Tom mama amma wallahi bani da kudi ko na mota balle na maganin". kafin mama tayi magana malam Yahaya ya ce" Mariya ya d'auki buhun masarar da ya yi saura ya saida shi sai yayi kud'in motar da su ya amso maganin. " Cikin minti goma Hassan ya kai buhun masarar kasuwa ya Saida yahau motar salanke. Dayake tsakanin sabon yalwa da salanke bawani nisa bane can-can cikin awa d'aya Hassan yadawo, cikin sauri mama ta amshi maganin ta wanke tasa jar kanwa ta d'ora maganin a wuta. Cikin yardar Ubangiji malam Yahaya yana shan maganin yaji dama-dama so sai yaji jikinshi duk ya sake bakamar daba. Masha Allah cikin kwana uku jikin malam Yahaya yayi sauk'i Sosai. Malam Yahaya zaune yake da iyalansa suna fira Sosai yana basu labaran duniya Hassan yayi sallama ya shigo, goye da jakar goyo abayansa, gefan malam Yahaya ya zuk'unna bayan sun gaisa ne Hassan ya ce "Baba yau ne tafiyarmu,kasan nacema exam d'in da mukai sunana yafitu tom yau ne suke nemanmu muje dan ganinmu"Masha Allah Hassan naji dad'in jin maganar nan, Allah ya tai maka Allah yayi maka albarka Allah yabaka Wanda zai mayema gurbin uba kamar yadda kamaye min gurbin d'a, nagodee Sosai da kulawarka gare......." Sallamar da yaji ce ta hana shi k'arasa abinda yake son fada..... Yayyan malam Yahaya ne su hud'u su ka yi sallama suka shigo. Malam Yahaya da fara'arshi ya tarbi 'yan'uwanshi ya ce " A'a yaya Jimmai kune barkanku da zuwa ,yaya Rabi'u ,yaya Ya'u ku zauna mana ga guri ya shimfid'a musu tab'armar kusa da shi ". Bayan sun Zauna ne anyi gaishe-gaishe jimmai tace" Ya'u Ka fad'ama Yahaya abun da muke tafe da shi. Wanda akakira da Ya'u kara gyara zama yayi sannan ya kalli Yahaya ya ce" Yahaya game da auran Na'ima ne tom mun yanke shawarar k'arshan watan nan za a d'aura auran Na'ima da gali kamar yadda muka sanar da kai akwanakin baya. Ba Na'ima ka d'aiba hatta malam Yahaya da mama idan ka kalle su zakaga tsantsar furgici a fuskar su. "Munji shiru Yahaya kai muke saurare "cewar Rabi'u. Numfasawa Malam Yahaya yayi sannan ya ce "Dama ni yaya Rabi'u wani hanzari ba gudu ba nace dama inda ita Na'imar tadage bata son gali mai zai hana abashi w........ "K'arya kake wallahi dama ba ra'ayinka kona Na'ima mukazo ji ba a'a mun zo ne muce muku ku shirya k'arshan watan nan zamu d'aurama Na'ima aure da gali" Mahaifin Na'ima numfasawa yayi sannan ya ce " Yaya Rabi'u ina gudun abun da nasani ne nan gaba shi yasa bawani abu ba ind...." Hannu Rabi'u ya d'aga mai yace " Ya'isa hakanan!,Yaya jimmai ku tashi mu tafi " Cikin hanzari Na'ima ta kama k'afar jimmai tace" Gwaggo dan Allah ki taimakan wallahi nayarda zan auri koma waye amma bana son yaya ga......" marinda Ya'u yawanka ma ta ne yasa takasa karasa abinda tayi niyya cikin wata kid'ima da rawar jiki ta kama kafar Rabi'u tace" Baba Rabi'u kataimakan karku aura min......."Wata in giza Rabi'u yayima Na'ima wadda mahaifiyar Na'ima batasan sanda taje da sauri zata rik'e taba amma ina sai datakai kasa cikin wahala da azaba Na'ima ta fasa wata uwar kara kafin kace me sai ga jini na zuba abakinta. "Aunty jimmai,Yaya Rabi'u, yaya Ya'u ku yi hak'uri bazan iya aurar da Na'ima ba agun Wanda bata so" cewar malam Yahaya mahaifin Na'ima. "K'arya kake aure dama bakai ka had'a ba Allah ne yahad'a dan haka kamar anyi angama ne" cewar yayar su jimmai tana kai wa nan ta ce "ku muje Rabi'u " . Allah sarki malam Yahaya daya rasa abunyi sai ya fa she da kuka cikin kid'ima Na'ima da sauran k'annanta suka karasa wajan babansu, Hassan ne ya zaunar da shi yace dan Allah kabar kuka baba yawuce. Na'ima kallan Mahaifinta ta yi da ke kuka ta ce" Baba dan Allah kabar kuka ni na yarda zan auri yaya gali" kai mahaifin Na'ima ya girgiza ya ce" A'a Na'ima bazaki auri gali ba" Mahaifin Na'ima ya fad'i maganar yana mai d'aukar butar dake kusa da shi yanufi hanyar bayi tari ne ya turnik'e shi ya fad'i gurin, da sauri Na'ima ta karaso gun tarik'eshi ganin yadda yake tarin ta ce" Baba dan Allah ka kwantar da hankalinka ni na yadda zan aure shi ". Mahaifin Na'ima Kiran sunan Na'ima yayi har yanzu cikin tarin yake ya ce "Na'ima indai ni ne mahaifinki tom bazaki auri gali ba" " Amma baba kaji yadda su gwaggo jimmai suka ce" Kai Manaifin Na'ima yake girgiza mata magana yake son yi amma tari yahanashi yi, mahaifiyar Na'ima ya yafito da hannu, da sauri tak'araso inda yake. Cikin rawar murya mahaifin Na'ima ya fara magana kamar haka " Ma.ri. ya ko bayan raina banyarda Na'ima ta auri ga.. li ba" cikin sar kewar harshe yake maganar, tarinda yaci k'arfin shine yasa basa jin abinda yake cewa sai kalmar shahadar shi sukaji, cikin gigita mama ke girgiza shi ganin baya nunfashi. Cikin kuka mahaifiyar Na'ima ke girgiza shi tana cewa" Malam dan Allah kar kai mana haka dan Allah katashi. " Kullunafsin za'ikatul maut rai ya riga yayi halinshi. Kukan su Na'ima ne ya shigo da mak'ocin su......... 🛥️🛥️ABDURRAHIM MATUK'IN JIRGIN RUWA NE🛥️🛥️ (RENEW) 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori Page 2 & 3 Allah sarki duk mai rai mamaci ne, haka akayi zana'idar malam Yahaya aka kai shi gidan shi na gaskiya. Ranar sadakar bakwai haka 'yan'uwan Malam Yahaya suka taru akai addu'ar bakwai. Bayan mutane sun tafi ne Yayyan marigayi suka nemi suna son magana da Mahaifiyar Na'ima da Na'ima, bayan sun nemi gune sun zauna suka sake yima mama gaisuwar rashin Mijinta,sannan wan mariyagin ya fara magana kamar haka "Mariya yau ne akai addu'ar bakwai na d'an'uwan mu Masha Allah, Allah ya jaddada rahamarsa agaresa" Yacigaba da cewa" Mariya nasan kin sanda maganar auran Na'ima da gali ko?" Mahaifiyar Na'ima dai bata ce mai ko mai ba. Yaci gaba da cewa "Tom kamar yadda mu ka tsaida k'arshen watan nan ne auran Na'ima da gali, tom yana nan yadda yake bazamu d'agaba, yanzu zamu d'auki buhun dawar shi uku da yayi saura mu saida kud'in mu had'a mu yi ma Na'ima kayan d'aki dasu, ina fatan haka ya yi mi ki? "Ya tambayi mahaifiyar Na'ima. Allah sarki Mahaifiyar Na'ima rasa abinda zata ce mai tayi, kai kawai tad'a ga mai. " Tom ai shike nan inda hakan yayi mata ku tashi mu tafi yace ma sauran abokan tafiyar nasa, " Yau saura kwana goma d'aurin auran Na'ima kamar yadda yayyan Mahaifinta su ka ce. Na'ima zaune kusa da Mahaifiyarta so ta ke tayi mata maganar auranta da gali ganin lokaci nata gabatowa amma tanajin ba kinta yayi nau yi bazata iya ba, can dai ta daure ta ce" Mama!" Kai mahaifiyar Na'ima ta d'ago tana kallan ta alamun inajinki.Na'ima kuwa cikin rawar baki ta fara magana kamar haka "Dama mama ni bawai auran Yaya gali bane bana so, a'a wallahi na hak'ura kawai dai ina duba maganar da baba yayi ne yana gab da barin nuniya beyarda ko bayan ranshi in auri Yaya gali ba, amma naji kin yi shiru da maganar gashi lokaci sai tafiya yake" Tom Na'ima wallahi ba wai nayi shiru bane ,a'a rashin mafitane ya sani yin shirun dole, amma Na'ima ya kike gani zanyi ki fad'amin? ". Mahaifiyar Na'ima kamar zatayi kuka tai maganar. Na'ima shiru ta yi sannam ta ce "Mama ko gidan nan zamu saidane mu tashi mu koma inda basu sani ba?" Da sauri mama ta d'ago kai tana kallan Na'ima,ta ce "Na'ima mu saida gidan nan mu koma ina da zama ga tarin k'annan ki? " Na'ima za tayi magana ne sallamar Hassan ta hanata. Mama ko da murnarta ganin Hassana ta ce " Kai-kai sannu da zuwa maraba Hassan kai ne yau agarin, lallaikam ,Na'ima shimfid'a mai tabarma" Hassana ckin dariyar shi ya ce " Wallahi mama ni ne kin ganni sai yau, naso in zo ayi addu'ar bakwai dani amma Allah be nu faba" Bakomai Hassan "cewar mama. Hassana kallan Na'ima yayi ya ce" k'anwata ya akaine naga ba akulani ba tun da nashigo?" Mahaifiyar Na'ima ce taba Hassan amsa da cewa"Na'ima nacikin damuwa Hassan ko ince munacikin damuwa,naji dad'in dawowarka wallahi muna cikin damuwa sosai Hassan Nida Na'ima"Nan dai mahaifiyar Na'ima ta kwashe halin da suke ciki tafada ma Hassan kaf. Hassan shiru yayi yana nazarin inda za'abulloma lamarin dan yasan halin 'yan'uwan mahaifin Na'ima kaf, bayan dogon nazarin da Hassana yayi ya kalli Mahaifiyar Na'ima ya ce "Mama yanzu ke yadda za ki yi kina gani zasu aurar da yarinyar nan agun Wanda bata so, ba abinda zaki yi akai?"Tom Hassan ya zanyi?, Kana gani shi kan shi mahaifin yarinyar nan nuna mai suke kamar sun fishi iko da ita, tom bare kuma ni da basu d'aukan bakin komai ba " Hassana kallan Mahaifiyar Na'ima yayi ya ce "Idan kin yarda mama ni zan d'au Na'ima in kai ta gurin gwaggona ta Kaduna? " Mahaifiyar Na'ima kallan Na'ima ta yi ,sannan ta maida kallanta ga Hassan batare da shakkuba dan ta yadda da Hassan sosai ta ce"Badamuwa Hassan nasan bazaka kai Na'ima gurin da kasan zata cutu ba, na yarda na amince ka kai ta, amma tunanina d'aya ne in suka zo me zan ce masu?, ina zan ce masu na kai Na'ima Hassan?" "Tom mama ni dai yan zu sai in ga kamar wannan ita ka d'ai ce mafitar mu mafi sauki " Shiru mama tayi nawani lokaci ta ce "shikenan Hassan Allah yasa haka shi ne abinda yafi alkairi"Da ameen suka amsa. Wa she gari da wuri mama suka shirya tafiya kaduna kai Na'ima gurin gwaggon Hassan kamar yadda suka tsara, kasan cewar banisa tsakanin sabon yalwa da cikin garin kaduna yasa cikin awa (hour) daya suka k'arasa kaduna dan ma motar haya ce, Hassan yayi masu jagora har gidan gwaggonshi,kasan cewar Na'ima sun san juna da gwaggon cikin mutunci ta tar besu, bayan ta basu ruwa sun sha aka gaggaisa Hassan ya zayya ne ma gwaggo abinda yake tafe da su game da barin Na'ima da suke sonyi . "Allah sarki mutuwa kenan me to nan asiri bako mai karkiji ko mai zan rike Na'ima har izuwa lokacin da yayi muku " Godiya sosai mahaifiyar Na'ima ta yima gwaggon Hassan. "Haba ai anzama d'aya" cewar gwaggon Hassan d'in. Nan su kai sallahma suka tafi su ka bar Na'ima da gwaggon Hassan tare. Haka mahaifiyar Na'ima suka dawo sabon yalwa cikin fargabar abinda zata cema yayyan mijinta duk sanda suka zo game da d'aurin auran Na'imar. Yau kwanan Na'ima biyu kenan awajan gwaggon Hassan ,duk wani aiki kusan Na'ima ta d'auke ma gwaggo shi ,hakan yasa Na'ima ta shiga zuciyar gwaggo sosai. Yanzu haka Na'ima Zau ne ta ke tana wanke-wanke koda ta gama cigaba tayi da zama wajan wanke-wankan tayi tagumi hannu biyu, tunanin Mahaifiyarta duk ya da meta yadda zata k'arke da 'yan'uwan Mahaifinta in sunzo. Sannan asaninta basu da sauran abincin da fawa ko ya suke yi. Gwaggon Hassan dafa kafad'ar Na'ima tayi ta ce" Cire tagumin nan dan Allah bashi da kyau kinji Na'ima" Tom gwaggo wallahi abun ne yayi min yawa ga tunanin koya mama zata k'arke da yayyan babana ga tunanin kome suke ci oho, wallahi gwaggo harma narasa wane tunani zanyi"Gwaggo shiru tayi sannan ta ce "Na'ima za ki iya aikin cikin gida irin Wanda nake zuwa?" Sosai ma kuwa gwaggo ai nama samu abinda zan rika tai makamasu da shi" "Shikenan dama matar da nakema aiki tace in samarmata 'yar aiki k'awar ta na naima, inkina so sai in mata magana ki fara zuwa?" "Aiko inaso gwaggo nagodee "Cewar Na'ima cikin murnarta. Ai ko gwaggo na zuwa gidan da take aiki ta fada ma hajiyar gidan tasamu 'yar aikin da tace ta samar mata, take hajiya ta kira k'awar ta awaya ta fad'a mata tasamu 'yar aikin. Godiya k'awar hajiyar tayi ta ce "zata iya fara zuwa aiki gobe " Aiko koda gwaggo ta dawo gida ta sanar da Na'ima ta hada kayan ta gobe zata fara aikin, kuma acan zata zauna, duk da Na'ima bata so zaman can ba bata nuna ma gwaggo ba godiya tayi mata sosai. Washe gari gwaggo tare da Na'ima su ka tafi gidan da take aiki, suna zuwa ko hajiya suwaiba tasa yaran aikinta yaraka Na'ima gidan hajiya Rahina wadda zata yima aiki, koda ya kaita a palon ya ce ta Zauna ta jira hajiyar kafin ta sakko tasan da zuwan ta" Na'ima ta dad'e sosai kafin hajiya Rahina ta sakko, amma abin mamaki hajiya tazo ta wuce ta ga ban Na'ima amma bata saniba "keeeee!" Hajiyar takira su nan Na'ima amma Na'ima ta shiga duniyar tunani bata jiba. Ciikin tsawa hajiya Rahina ta sake cewa "keee bakya ji ne?" Cikin furgici Na'ima ta tawo daga duniyar tunanin da ta fad'a ta ce "Wallahi banji bane yi hak'uri dan Allah ina kwana?" Shiru hajiya tayi tana kallan Na'ima nawani lokaci sannan ta ce" Lafiya ,yasu nan ki?, 'yar nan kaduna ce ke? " "Sunana Na'ima muna Zaune ne a sabon yalwa kusa da jaji" Kai hajiyar ta jinjina ,sannan ta ce "Kinnsan aikin da za ki min ? "A'a bansani ba" "Ok zaki rika min Shara da goge-goge sai wanke- wanke, zan rika baki dubu sha biyar duk wata yayi miki? " "Nagodee sosai yayi mommy " cewar Na'ima. Yau kwanan Na'ima uku da fara aiki kuma yau yake saura kwana uku d'au rin auran ta da gali kamar yadda yayyan babanta suka sa, hakan yasa hankalin Na'ima yata shi sosai duk Wanda yaga Na'ima ko be son taba kallo daya zai mata yagano cikin damuwa take. Can ko sabon yalwa fad'in damuwar da Mahaifiyar Na'ima take sai Allah ,ta yi bak'i taramai sosai kullum cikin zullumi take na zuwan 'yan'uwan Mijinta, yanzu haka Zau ne take akan dadduma ta idar da sallah, sallamar su binta ce tadawo da ita daga tunanin da ta ke ciki. Bak'aramin furgici mama ta shiga ba ganin su Ya'u, amma sai ta danne suka gaggaisa , bayan sun gama gaggaisawa ne, Binta ta ce "Tom Mariya ga kayan lefan Na'ima nan mun kawo" bud'e akwa tin Binta tayi tana nuna ma Mahaifiyar Na'ima kayan, atamfofi ne guda shida d'aya ce cotton amma sauran duk roba ne Sai ta kalmi d'aya hijab d'aya. Bayan Binta ta gama nuna ma Mahaifiyar Na'ima ne ta ce " Gashi nan Mariya ku yi hak'urin abunda babu in ta shi ga yayi mata kin san de yaran nan basana ace gare shi ba "Yayi ma k'okari" cewar ya'u. Binta ko taji gaba da cewa " Yaya Jimmai ta ce ace maku daga an d'aura aure za azo atafi da amarya kin san hanyar tamu Sai ahankali..." Mahaifiyar Na'ima dai ta kasa cewa komai,ganin haka Binta ta ce "Mariya baki ce komai ba?" Mahaifiyar Na'ima dai bata tankaba dan batasan me zatace ba. Ya'u Wanda mahaifin Na'ima ke bimawa ya ce "Rabu da ita Binta, ko tayi magana ko kar tayi mude mun bada sa k'on da akabamu akace mubada ku tashi mu tafi" Binta da bataga Na'ima kallan Mahaifiyar Na'imar ta yi ta ce "Mariya wai In Na'imar ne Banganta ba ?" Mahaifiyar Na'ima nan ma banza tayi da su. kwafa Ya'u yayi ya ce" ku mu je" Yau juma'a kuma yau yakama ranar d'aurin auran Na'ima da gali kamar yadda akasa, haka ko ta kasance anadawowa sallar juma'a aka d'aura auran Na'ima da gali, bayan gama d'aurin auran ne badadad'ewa ba masu d'akko amarya suka kamo hanya zuwa d'aukar Amarya. Mahaifiyar Na'ima na zaune cikin fargaba da tashin hankali dan yaune d'aurin auran Na'ima kamar yadda suka ce. Mahaifiyar Na'ima na nan zaune cikin fargabar yadda zasu kaya da Iyayan Na'ima masu d'aukar amarya suka shigo............ 🛥️ ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE (RENEW) 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori Page 4 & 5 Da bud'ar su su ka shigo gidan. Mahaifiyar Na'ima cikin fad'uwar gaba tafito daga d'aki. D'aya daga cikin masu d'aukar Amaryar ce ta ce "Tom Mariya yau dai Allah yayi Na'ima ta zama matar gali, afito mana da amarya sauri muke kin san hanyar tamu". Mahaifiyar Na'ima shiru tayi,sannan ta Binta ta ce"Binta d'an shigo daga ciki muyi magana."Binta binta tayi batare da tunanin komai ba tashiga. Bayan Binta ta shiga d'akin Mahaifiyar Na'ima ne, Mahaifiyar Na'ima ta kalli Binta ta ce" Binta banfa san inda Na'ima take ba" Wani uban ashar Binta tayi ta ce" wallahi Mariya tun daga ni sai ke ki fito da Na'ima kafin su yaya Ya'u suji maganar nan!" Wani banzan kallo Mahaifiyar Na'ima tayi ma Binta ta ce "Kowa zaki fad'amawa ki je ki fad'a mai Binta nace miki bansan inda Na'ima takeba". Tana kai wa nan tajuya tayi tafiyar ta. " Binta waya ta d'auka ta kira jimmai uwar ango ta fad'a mata abinda Mariya tace. Uwar ango wanda take amazaunin yayyar mahaifin Na'ima,cikin fushi ta ce "Binta ku jirani ganinan zuwa"Daya ke banisa tsakanin tudun malam da sabon yalwa hakan yasa cikin k'ank'anin lokaci jimmai ta iso." Tun kafin Jimmai ta k'arasa shigowa gidan take fad'in" ke Mariya duk inda kika kai Na'ima kiyi gaggawar d'akko ta kafin in shigo, dan wallahi in har na shigo banga Na'ima ba sai kin san dani ki ke, dan Yahaya ma bai isaba bare ke karan ka'da miya" Allah sarki da yake Mahaifiyar Na'ima bata saba rigima ba, jikinta kota ina rawa yake. Jimmai ko na zuwa ta shak'i wuyan Mahaifiyar Na'ima ta ce"Mariya wallahi ko zaki mutu ba zan sakeki ba sai kin fad'a min ina ki ka kai Na'ima?" Wujijjiga Mahaifiyar Na'ima Jimmai take da duk k'arfin ta, masu hankali ne daga cikin wa inda suka zo d'aukar amaryar sukaga in sukabar jimmai zata yima mariya illa, in abun yazo da k'arar kwana ma ta kashe ta. Dak'ar aka b'anb'are Jimmmai daga jikin Mariya, dan bada wasa ta shak'e taba. "Dan Allah ku bar ni da ita."A'a yaya Jimmai ki b'arta, mu bata nan da kwana biyu mugani "cewar Binta. Jimmai da kallan Mahaifiyar Na'ima tayi ta ce "Mariya kwana biyu na baki wallahi duk inda ki ka kai Na'ima ki kawota kafin nan da kwana biyu, in kuma bahaka Hmmmm". 'Yan d'aukar Amarya ko haka aka hak'ura aka koma ba amarya. Allah sarki mahaifiyar Na'ima ranar kusan kwana tayi kuka saboda bak'in cikin abinda Jimmai taimata yaranta na tayata. Aiko washe gari dawuri Mahaifiyar Na'ima ta shirya ta nufi kaduna. bata tsaya ko ina ba sai gidan gwaggon Hassan, lokacin ita kuma gwaggo tayi shirin zuwa gidan da take aiki.Gwaggon Hassan da mamaki take kallan Mahaifiyar Na'ima ta ce "Kai Mariya ke ce da wuri haka,Allah dai yasa lafiya,amma daga ganin zuwan nan nasan banawa bane, dan haka zo muje in kaiki gidan da Na'imar ke aiki" Aiki kuma gwaggo?" Nan dai kwaggo ta fahimtar da mahaifiyar Na'ima dalilin aikin nata dan ta taimakamusu ne. mahaifiyar Na'ima bata wani damuwa ba saboda tasan gwaggo bazata kai Na'ima inda zata cutu b. Koda su gwaggo suka isa gidan da Na'ima ke aiki, mai gadin gidan sukai ma magana yakakira masu Na'ima. Na'ima ko kullum damuwarta k'ara k'aruwa take, gafargabar auran ta, tana cikin wannan tunanin ne, mai gadin gidan yazo yace meta tayi bak'i. Na'ima Cikin fargabar kosu waye ke nai manta tafita. Koda ta hangi mamar ta cikin fad'uwar gaba ta k'arasa inda suke,dan daga ganin zuwan bana lafiya bane. "Oyoyo mamana ,sannun ku da zuwa".Cewar Na'ima.Nan dai suka gama gaggaisawa,Sannan Mahaifiyar Na'ima ta kalli Na'ima ta ce"Na'ima sauri nake je ki d'auko kayanki mu tafi"Mama lafiya dai ko? "Mahaifiyar Na'ima kallan Na'ima tayi ta ce "Yi abinda nace sauri nake na baro k'annanki gida su kad'ai"Na'ima cikin rawar muraya ta ce " Tom mama amma hajiyar bata nan tafita sai dai in tadawo, kinga ni kadai ce a gidan ba zaiyuwu inbarmata gida ba ba kowa" Shiru Mahaifiyar Na'ima tayi ,sannan ta ce "Na'ima bazan iya jiran kiba, amma daga tadawo ki dawo gida yau yau d'in nan, dan jiya Iyayanki suka d'aura maki aure" Na'ima bak'aramin jarimta tayi ba dan danne damuwarta dan kar mahaifiyarta tafahimci hakinda take, amma ainihin gaskiya ita kadai tasan halin da takeciki.Na'ima kallan Mahaifiyarta tayi ta ce "Mama tom ya maganar da Baba yayi, kafin yabar duniya? " "Na'ima ki yi abinda nace kinji, Iyayanki jiya bakalar cin mutuncin da basuyimin ba"Na'ima cikin damuwa ta ce "Shikenan mama zan dawo yau d'in in tadawo, amma mama kina son auran ne yanzu?" "Tom Na'ima ya zanyi?, amma maganar so ko bazan tab'a so auranki da gali ba"Shikenan mama sai nazo" Na'ima koda tadawo gida , bak'in ciki yawa yayi mata, ga haushin abinda akai ma Mahaifiyarta ga takaicin auran da aka ce an d'aura mata da gali. Palon ta zauna tana ta kuka, har hajiya Rahina ta shi go amma bataji shigowar ta ba" Hajiya Rahima kusada Na'ima ta zauna amma abin mamaki har yanzu Na'ima bata ji motsin hajiya a polon ba, kukan ta kawai takeyi a bunta. "Ke! lafiyar ki? "Cewar hajiya Rahina.Sannan taci gaba da cewa "Nalura da ke , tun da kika zo gidan nan baki da wani aiki sai tunani, tom idan bazaki iya aikin ba zan samu wata, inda abun naki k'arak'aruwa yake, yanzu abun ya zama sai kizo ki zauna ki tamin kuka, ina Tambayar ki kuma kin min shiru kin zuba min ido, tom wallahi bazan d'auka ba" Na'ima shiru tayi tana sauraran hajiya, sannan ta ce"ki yi hak'uri dan Allah" Zama hajiya Rahina tayi tana fuskantar Na'ima sannan ta ce"Me yasaki kuka yanzu nake son in sani? " "Dama mama nace tazo yanzu tace wai duk abinda na keyi in dawo gida yau, tom ni kuma bana son komawa gidan"Saboda me?" Cewar hajiya Rahina. "Saboda 'yan'uwan babana sun min aure ni kuma bana son auran da su kai min,kuma Babana ma kafin ya mutu yace kar su auramin Yaya gali" "meyasa bakya son galin? " "Saboda babana yana gaf da mutuwa yace ko bayan ranshi be yarda ba in auri yaya gali"Na'ima hannun hajiya Rahina ta kama kamar za tai kuka ta ce "Hajiya dan girman Allah kitaimakan ki kaini, kasar nan danaji kina cewa za akawo miki kaya kuma zasu dad'e basu dawo ba, dan Allah hajiya hakane kawai zai sa in gujema auran Yaya gali da Babana ma baya so "Shiru Hajiya Rahina tayi ,sannan ta ce "Zan taimakeki amma sai naji cikakkyan tarihinki, naji dalilin dayasa mahaifinki be so ki auri d'an'uwanki?" Shiru Na'ima tayi kamar mai tunani, sannan tafara magana kamar haka. "Kakana Abdullahi yanada mata biyu Jamila da kuma Habi, Habi ita ce matar kakana ta fari dan haka ita ta haifama kakana manyan 'ya'ya, gwaggo Jimmai itace babbar yarinyar kakana sai baba Ya'u sai baba Kabiru sai autar su Binta. An haifi gwaggo binta ba dad'ewa kakana ya auro mahaifiyar babana wato kakata, kakata tun da ta haifi babana bata sake haihuwa ba, kuma ta haifi babana badadewa Allah yayi ma kakana Abdullahi rasuwa, babana yataso cikin maraicin uba dan duk wani abu da yayye sukema k'annan su tom su baba Ya'u basama babana, amma fa in dai akazo maganar aiki tom akokacin zasu ce ai shine K'arami, da kakata ta lura wahala zata kassara d'anta d'aya tilo sai ta kai shi sabon yalwa almajiranci. Bakalar fad'an da su baba Rabi'u basu yiba amma kakata ta share, bayan tafiyar babana almajiranci badad'ewa kakata ta kwanta k'aramar jinya, wadda tazama sana diyar ajalin ta, babana yayi nisa da karatu alhamdulillah, saidai kash suna cikin karatu Allah yayi ma malamin nasu mutuwa shima sakamakon k'aramar jinyar dayayi, tom daga nan ne fa Babana ya koma aikin gona ana biyan shi, ahaka ahaka Allah yabud'a mai har ya tsaya da k'afarsa, cikin k'ank'anin lokaci ya sai fili yafara gini, yana cikin gini Allah yahad'a shi da mamana,kasan cewar itama 'yar'uwar babana ce ma'ana marainiya ce babana bai wani sha wuya ba aka bashi auran mamana. Tun da su baba Ya'u sukazo bikin sukaga abinda babana yayi na kud'i tom daga nan fa duk wani Wanda da muwar kudi ta tashi mai sai ya d'aurata akan babana, in ta kai cemiki har sai da sukaga sun karya shi sannan Suka b'arshi. Masha Allah Allah ya azurta mahaifina da haihuwa dan mu biyar ya Haifa, ni sai k'anwata Aisha, sai Aminu da umar sai auta auwal. In ta k'aice miki tunda gali d'an gidan gwaggo jimmai ya fara nuna yana sona babana yahanani zuwa hidimar wajan su, dalili ko duk yarinyar da gali ya d'auka ido akanta sai ya lala tata. Yaje gidan yari (prison) yafi ak'irga amma abin sai abinda yayi gaba, dan yanzu ma har sata yake"Numfasawa Na'ima tayi sannan ta ce ci gaba da ce wa "Wannan shine dalilin da ni da babana bama son aurena da yaya gali" Nan Na'ima taitaba hajiya labarinta har izuwa auran ta da aka d'aura da gali kamar yadda mahaifiyarta tasanar da ita. Hajiya Rahina kallan Na'ima ta yi ta ce "Na'ima naji labarinki kuma koni ban goyi bayan ki zaman aure da mutum kamar gali ba, dan haka zan kira gwaggonki in shaida mata in har ta yadda tom ba shakka dake za a, sai dai fa a jirgin ruwa zakuyi tafiyar,kuma tafiya ce ta wata shida kin yadda?"Eh Mommy na yadda " Waya hajiya Rahila ta d'auka ta kira k'awarta hajiya suwaiba akan dan Allah ta turo mata da gwaggo mai ai kinta. Driver hajiya suwaiba tasa ya kawo gwaggo har gidan hajiya Rahila. Bayan sun gaisane. Hajiya Rahila ta kalli gwaggo ta ce" Gwaggo nasan zakiyi mama kin kiran ki da nayi, tom Na'ima ce tarok'eni wata alfarma atafi da ita Landon kinsan acan ake kawomin kaya"Nan dai hajiya tafad'ama gwaggo duk yadda su kai da Na'ima,ta d'aura da cewa"Gwaggo kin san HALIBIZ SHOPPING MELL tawace tom dama in dai shekara tazo tsakiya muna ai kawa akawomana kaya, kin san tafiyar ta jirgin ruwa ce, tom suna yin wata shida ahanya,tom kin aminta atafi da Na'ima ko ko?, amma fa ni badani za ai tafiyar ba......... 🛥️ ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE.(RENEW) 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori Page 6 & 7 Hajiya Rahila kallan gwaggo tayi jin tayi shiru ta ce" Gwaggo bakice komai ba, kin yarda in tura Na'ima London d'akko kayan sabuwar shekara da zamuyi ? "Numfasawa gwaggo ta yi ta ce, "Tom Hajiya bawai nayi shiru bane a'a wallahi kin san Na'ima ba yarinyata bace shine nake gani kibani nan da zuwa gobe inje in tambayi mahaifiyar Na'ima inta yarda tom." Kafin Hajiya Rahila tai wata magana, Na'ima ta yi wuf ta ce. "Ahalin yanzu mamana tana cikin k'uncin rayuwa, yayyan babana sun tasata gaba akan auran nan, tun da gwaggo kikaga mama tace sai dai in dawo gida akai ni d'akin yaya gali, tom wallahi bak'aramin furgita ta sukayi ba". Na'ima kamar za tai kuka ta maida kallanta ga Hajiya Rahina ta ce, "Hajiya kima girman Allah ki amshi tayin tafiyar nan tawa ko dan in cika burin mahaifina na rashin auran nan da har ya komama ga Allah baya son shi. " Hajiya Rahina gwaggo ta kallah ta ce, "Tom gwaggo kin ji abinda Na'ima tace,kin aminta ayi tafiyar nan da ita?"Tom, ni bawai nak'i tafiyar Na'ima bane, a'a wallahi kawai dai kin san yanzu muna wata irin rayuwa ne, sai ka yi Abu da niyar taimako nan gaba yazamarma matsala" Kai hajiya Rahina ta jinjina ta ce"Hakane gaskiya,dannima bazan d'auki Na'ima ba bada amincewar kowa ba in kaita wannan kasa mai nisa kuma tafiya ce bata yau ko goba ba." Gwaggo kallan Na'ima ta yi da ke Shirin fasa kuka ta ce, "Badamuwa Hajiya amanar Na'ima ahannu na take dama, dan haka na amince Allah yasa jin shirun da zasuyi ya zamo silar rigujewar auran" "Ameen ya Allah"cewar Hajiya Rahina,sannan ta kalli Na'ima ta ce, "Ki je gida ki shirya dan goba ne tafiyar"Kai Na'ima ta girgiza ta ce "A'a babuwani shiri da zanyima" Duk wani shiri da Na'ima za tayi tayi shi, fatan ganin gobe kawai take. Washe gari Na'ima zau ne a gaban Hajiya Rahila tagama duk wani shiri da za tayi. Hajiya Rahila kallan Na'ima ta yi ta ce, "Tom Na'ima Allah yakiyaye hanya Allah ya sauke ku lafaya, yanzu ga driver nan zai kai ki airport kaya ko mai da komai anriga angama shiryawa daga kun je sai tafowa, amma fa zaki sha sanyi yarinya, zakiyi kalar tafiyar da nake sha'awa Amma ni tsoro yahananiyi danni tsoran jirgin ruwa na ke" Murmushi Na'ima ta yi ta ce "Shekara d'aya da wata hud'u zamuyi ko hajiya?" Dariya sosai hajiya Rahila tayi, sannan ta ce "Yanzu ai a jirgin sama zaku, wajan dawowa ne dai zaku dawo a jirgin ruwa saboda kaya". Driver Hajiya Rahila ya kai Na'ima airport,suna isa ko babu da d'ewa jirginsu ya tashi. "Ikon Allah sai kallo wai yau ni ce a London"Na'ima al'ajabi duk ya isheta lokacinda ta take kwance kan kadon hotel d'in da zata kwana . Kwance take akan tafkekean gadon hotel d'in da Jamilu abokin tafiyar ta ya kamamusu. Juyi kawai take sanyin k'asar da tunanin halin da Mahaifiyarta ta ke ciki yahanata bacci. Washe gari koda Na'ima ta tashi kasa wanka tayi tsabar sanyin da take ji, Jamilu da kan shi ya kawo mata tea da wani farfesun nama. "Tashi ki k'arya dan yanzu zaku Kama hanya, Amma fa zakiyi doguwar tafiya ,dan Allah in tambaye ki mana?"Jamilu ya tambayi Na'ima. "Ina jinka"cewar Na'ima. "Dan Allah me yajawo miki wan nan wahalar haka?". Na'ima kallan Jamilu tayi da mamaki akan fuskarta ta ce "Wahala kuma tame fa?". "Ta tafiya a jirgin ruwa mana, waya fad'a maki su kaya dole sai an tsare su, ai daga anba direbobin shike nan, ba sai an had'a da mai tsaron kaya ba",Jamilu ya fad'a. "Tom nima sha'awar tafiyar ce kawai" Na'ima ta fad'a ma Jamilu haka ne kawai dan ta wuce maganar. Na'ima da Jamilu tsaye suna sallama dan yanzu jirgin su zai kama hanya. Jamilu kallan Na'ima yayi ya ce, "Tom shikenan Na'imatu Allah ya isomana dake lafiya, Allah ya karemana ke gaba da baya". "Ameen "ta amsa. Jamil bashi yabar gurin ba har sai da yaga jirgin su ya tashi sannan. Can b'angaran Mahaifiyar Na'ima kuwa bayan ta koma gida, tun tanasaran zuwan Na'ima har ta gaji, har ta fara tunanin k'ila hajiyar ce bata dawo ba sai gobe, tom Allah yasa dai goban ma tazo da wuri, kafin guyababbun Iyayanta su zo. Washe gari ma haka ya faru ba Na'ima ba dalilinta, Mahaifiyar Na'ima ganin har rana tayi Na'ima bata dawo ba abin sai ya fara bata tsoro, dan tasan tun da tacema Na'ima tadawo tom ba'abinda zai hanata da wowa. "Tom ko dai an sace tane" Haka Mahaifiyar Na'ima tai ta tik'a da warwara akan rashin dawowar Na'imar. Mahaifiyar Na'ima nanan kwance tana tunanin rashin dawowar Na'ima tajiyo sallamar su Ya'u ,cikin kid'ima Mahaifiyar Na'ima ta fito da tab'arma a hannunta tana k'ok'arin shimfid'amu su , Ya'u ne yad'aga mata hannu ya ce. "Dakata Mariya,bazama ya kawo mu ba, mun zo ne kibamu 'yarmu kuma matar d'an mu ko kuma wallahi Mariya hukuma zata rabamu da ke". "Wallahi! Wallhi!! Wallhi!!!" Sonawa narantse Ya'u?" Cewar Jimmai. "Sau uku, yaya jimmai". Kai Jimmai ta karkad'a ta ce, "Wannan shine gargad'i nak'arshe Mariya, ki fitomin da surukata in kuma bahakaba tom zaki san ruwa ba tsaran kwando bane Wallahi"Tana kai wa nan tai gaba. Ya'u kusa da Mahaifiyar Na'ima yadawo ya ce ahankali yadda Jimmai bazataji ba"Mariya ni zan tai makeki,inma baki son auran Na'imar ne, amma sai da sharad'in in kin aminta zaki auran?". Wani mugun kallo mahaifiyar Na'ima tayi mai ta ce "Ba aure atsakanina da kai amma ba abin mamaki bane dan ka fad'i haka inda nasan akwai k'arancin rashin sani atattare da kai". "Kamarya Mariya bangane ba,me kuma ya kawo rashin sani anan? " "Nufina bakasan haramun ba bakasan halaliiba". "Haba Mariya mai Ya kawo maganar haramun kuma da halali ana.... ". Maganar Jimmai da Ya'u yaji ce tasa ya canza abinda yayi niyar fad'a tahan yar cewa "kin ji dai abinda nace maki kinada damar samun mafita, in kinyarda in kuma kink'i tom ya rage naki"Yana kai wa nan yayi gaba abinsa. washe gari da sassafe mahaifiyar Na'ima ta nufi kaduna, sakamakon wani munmunan mafarki da tayi akan Na'ima. Gidan gwaggo Mahaifiyar Na'ima ta sauka. Cikin gwaggo sai da ya kad'a dan ganin mahaifiyar Na'ima da tayi, dan bata san abinda zata ce mata ba game da tafiyar da Na'ima tayi bada izinin taba, haka ma fa na d'aukar mata yarinya na kaita gidan aiki bada sanin taba,kuma koda tazo bata nunamata damuwa ba, ai ko yanzu da kunya in ce mata bata k'asar, tom inama zance mata taje. Haka gwaggo tai ta maganar zuci. Muryar mahaifiyar Na'ima ce ta dawo da gwaggo daga tunanin da ta lula. "Gwaggo ki yi hak'uri karkiga nadaimeki da sintiri ,wallahi abubuwane ne sun kacamemin gashi itama Na'imar da nace tayi hak'uri tazo a kaita d'akin mijin ta shine tak'i zuwa, ni hattasani ma afargaba, na fara tunanin ko lafiya" "Lafiya"cewar gwaggo da batasan ma abinda ta ce ba. "Alhamdulillah ,dama wani mafarkine nayi akan Na'imar mai ban tsoro, shine nazo ingani ko lafiya, daga nan kuma k'afarta-k'afata". Wani irin kuka cikin gwaggo ya yi, cikin rashin sanin abinda zatace ma ta ta ce "Tom tashi mu je gidan da take aikin". B'angaran Na'ima kuwa al'ajabi duk ya isheta wai yau ita ce acikin jirgin ruwa. Su Na'ima ba su yi tafiya mai nisa ba,suka farajin Wani irin k'ara daga k'asan jirgin kamar ana balla Abu, cikin kid'ima captain d'in jirgin ya fara sanarwa jirgi yasamu matsala, kafin kace wani abu, jirgin yafara mangar-mangar. Na'ima kuka tafarayi ganin ruwa yafara tud'ad'owa cikin jirgin. Ahankali ahankali jirgin yafara k'asa ruwa yana k'ara shigowa cikin jirgin sosai kamar ana k'ara antayo shi......... 🛥️ ABDURRAHIM 🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUW NE (RENEW) 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori. Page 8 & 9 Banda salati da kuka ba'abinda Na'ima ke iya yi. Shugaban jirgin ruwan, (captain) ya bada rigar ruwa (life jacket) ya ce Aba duk matan dake jirgin su sa,sannan ya k'ara da cewa"mu na so dan Allah kowa ya kwantar da hankalin sa, ba abinda zai faru dan mun kai sanarwa (report) ababbar headquarter ta mu, za akawomana agaji yanzun nan" cewar captain d'in jirgin. Duk maganar da yake cikin speaker yake yinta, in bahaka ba ba kowa zai ji shi ba, dan jirgin nada girma sosai balefi. Bak'aramin razana mutanan dake cikin jirgin nan su kayiba, ganin jirgin nasu saura k'iris ya nutse, gashi har yanzu basuga alamun masu ceto ba. Shikan shi captain d'in jirgin yagama sadak'arwa. B'ak'aramin rud'ani captain d'in ya shigaba, ganin b'angaran matuk'an masu control d'in jirgin gabad'ayan shi ya nutse cikin ruwan . Gudu mutanan kusa da b'angaran da ya rufta suketayi suna dawowa b'angaran da yake da dama -dama. Allah sarki kusan baka ganin mutane sai kawu nan su kakegani. Bindiga carptin d'in ya sa ya harbi kan shi, dan ba zai jure ganin ruftawar jirgin gabad'aya ba. Rabin jirgin duk ya nutse, duk wata hayaniya da mutane ke yi duk sun baryi, banda mutun uku daga cikin matuk'an jirgin da su kai saura, duk dasu tsabar amanace irin ta su ta turawa, amma su sun iya ruwan da zasu iya taimakon kansu, tom amma su turawa sunada amana duk runtsi duk wuya sai dai amutu tare badai su gudu ba, dan duk sun iya ruwa sannan ga rigar ruwa amma sai sukak'isawa suka ba matan sukasa. Allah sarki su kansu mutum ukun da su kai saura sunriga sun gama galabaita suna ji suna gani haka suka sadaukar da rayuwar su, tsabar alk'awari irin nasu, Mutum d'aya ne da shima yagama galabaita, hannu yake ta d'agawa sakamakon k'arar jirgin da yake ji yana nufo su, dan ko ba afad'a ba yasan su akakawo ma agaji. Jin jirgin nata shawagi yasa ya lalibo usir d'insa yahura yasan k'arar zata ankarar da su dan yasan sakamakom ruwan da yasha kansu ne yahana masu kawo masu agajin sugan su.Tun k'arfin shi yahura usir din. D'aya daga cikin masu kawo agajin ne yajiyo k'arar husird'in, nuna ma sauran abokan tafiyar ya yi inda yajiyo k'arar . Da saurin su su ka k'araso in da su ke ji yo k'arar hura usir d'in. Shiko Azera da yajiyo alamun tahowar su cigaba da hura usir d'in yayi yana bubbuga hannun shi aruwan da d'an sauran k'arfin da yarage mai. ta ke suka gane inda al'amarin yafaru, suka k'arasa wajan. Cikin ikon Allah su kai ta fito da mutane daga cikin jirgin da had'arin yafaru, basuyi wani wahalar fito da mutanan ba, k'asan cewar yawancin matan duk asaman ruwa suke, saboda rigar ruwa da akabasu sukasa . Sun d'au dogon lokaci suna fito da mutane acikin ruwan, inda duk Wanda aka ciro asibiti ake wucewa da su. Ikon Allah duk iya sa idona danayi banga Na'ima ba cikin muta nan da aka ciro, har suka gama cirowa, ban ga alamu da sauran mutum ba, dan har na'urorin su saida suka haska basuga komai ba, sannan suka nufi da wa inda aka ciro asibiti. Tafe yake cikin d'an ma dai-dai cin jirjin sa. Matashi wanda kallo d'aya zakai mai ka tabbatar da kwanciyar hankalin ya wadatai, dan dagani ba sai an fad'aba kallo d'aya za kai mai kagane hakan, Sauri yake yak'osa yaje gida saboda uzirin da yake da shi agidan, wani tudu-tudu yake gani na tun karo shi da alama koma meye igiyar ruwa ce ta jawo shi. Tun kafin abun ya iso kusa da shi ya tabbatar da mutun ne, parking ya yi da jirgin nasa acikin ruwan, sannan yasa wata sanda dake cikin jirgin yarika jawo abun nan ahankali, sai dai tun kafin ya iso wajan shi ya tabbatar da mutum ne, dan yaga rigar ruwa ajikin mutum d'in ,shi ne dalilin da yasa bai nutseba acikin ruwan. Cikin jirgin sa ya sata sannan ya tub'e mata rigar ruwan da ke jikin ta. Al'ajabi ne ya isheshi ya ce " ikon Allah tom wannan kuma daga ina mutum cikin ruwa kuma mace" Tafiya yake yana sake- saken yadda zai yi da ita, kai ko dai in yadda ta ne, tom in kuma fa nayadda ta kuma bata mutu ba fa?" Nan dai ya yanke ma kan shi shawara akan ya kai ta gidansa alabashi yakira alheri ta dubata ta tagani ko tanada rai. Bashi ya isa gida ba sai shida na yamma (6: 00pm) lokacin garin yafara duhu. Yana shiga gidan ya d'akko ta daga mota kasan cewar yana fita gab'ar ruwan yayi parking a inda suke aje jiragan su. Ya d'auki drop d'in mota har gidan sa." Bayan ya kwantar da ita ne nalura she Na'ima ce. Waya ya d'auka ya turama alheri sako tazo yanzu yana son ganin ta. Cikin mintina kad'an alheri ta iso gidan. Alheri kallan shi tayi damamki ta ce, "Abdurrahim wannan fa, ina kasamota?. " Banza Abdurrahim yayi da ita kamar bazai amsa mata ba, sannan ya ce ahankali kamar an mai dole "Tsintarta nayi, ki dubata mana" Alheri da mamaki take kallan Abdurrahim , so take tak'ara tambayar shi amma bataga fuskar hakan ba, dan haka taja bakin ta tayi shiru, ta fara aikin da yakawota. Alheri tad'an kwashi mintina tana dubata, sannan takalli Abdurrahim ta ce, "Abdurrahim k'alau take inajin furgicin da tayi ne yasata cikin wannan yanayin amma bari ina zuwa akwai allurar da zan mata yanzu. Cikin k'ank'anin lokaci Alheri tadawo da allura tayima Na'ima, sannan ta ce mai zata tafi gida. " Ok, thanks" Abdurrahim ya ce ma alheri sannan yazaro kud'i dayawa yabata. Alheri kallan Abdurrahim ta yi ta ce "Haba Abdurrahima ai kawuce haka aguna, kodai kana kokwanton matsayinka k aguna ne? " Kai Abdurrahim ya girgiza mata alamun a'a t"Tom nagoge" Abdurrahim ya ce mata ahankali cikin natsuwar shi da rashin son hayaniyarshi. Abdurrahim tun da yaba Na'ima awa d'aya bata farkaba kamar yadda alheri tace mai, tashi yayi ya shiga d'akin dake kusa da nata, yayi sallah ya shiga kitchen yayi makan shi abu mai saukin ci, sannan yakoma d'akin da ya kwantar da ita ya kuma dubawa ko ta tashi ,ganin bata tashi ba ya nufi d'akin shi. Cikin tsakiyar dare Na'ima ta farka, da wata irin k'ara mai rud'arwa, ihu take tana salati sai tangal tangal take ita kad'ai akan gadon. Abdurrahim jin k'arar mutum cikin furgici yafito dan shi harga Allah ya manta da wata yarinya agidansa. "Keee!,keee wata irin mahaukaciya ce" cewar Abdurrahim da kwatakwata baya son hayaniya. Na'ima ko da batason abinda takeyi ba dan har yanzu ba wai tadawo natsuwarta ba ne. Sannan jin tsawar da Abdurrahim yayi mata sai ya k'ara rud'ata. Wata uban k'aratasaki Wanda yasa Abdurrahim rufe kunnuwan sa da sauri, yana ja baya. Lura dayayi kamar ba ahayyacin ta ta ke ba yasa shi Saurin barin gurin. Dan shi mutum ne Wanda baya son hayaniya, kallo d'aya zakai mai kagano hakan. Ruwa mai sanyi Abdurrahim ya d'akko ya watsa mata.sannan Na'ima ta sauke ajiyar zuciya wadda ko ba afad'a ba kasan tadawo ahayyacin ta. Sannan ta jawa wani uban numfashi .Na'ima Abdurrahim ta k'ure da ido tana kallo, can kuma ta ce"Bawan Allah dan Allah inane nan? " Abdurrahim banza da ita yayi yajuya zai koma d'akin shi, tayi saurin sakkowa daga kan gadon ta ce dan Allah Bawan Allah ina nake?,ko na mutu ne" Harga Allah Na'ima take tambayar Abdurrahim duk da tambayar ta ta ta so ta sa shi dariya, cigaba yayi da tafiyar shi, itako tacigaba da tambayoyin ta. " Bawan Allah dan Allah ya akai nafita daga cikin ruwan nan?." Abdurrahim agogon hannun shi ya nuna mata, sannan ya kwantar da fuskar shi akan hannuna shi yanuna mata gadon da ya ajeta alamun taje ta kwanta .Duk da Hannu yake mata kwatancan, kamar dai yadda kurame ke yi. Ba yadda Na'ima ta iya haka takoma gadon ta kwanta da tunanin yadda za ta iya magana da kurma in gari ya waye. "Kai Allah dai kasa a Nigeria nake ma, shikenan yanzu inaji ina gani zan kwanta gidan wani kuma d'aki d'aya, tom ai kamar d'aki d'ayan ne inda daga yafito zai ganni aiko bazanyi bacci ba ma, dan ba'abinda natsana kamar wani yaga kwanciyata" Duk ita kadai ke maganarta cikin zuciya, ahaka dai bacci ya kwasheta ga wata bala in tattar yunwa da take ji. Washe gari Abdurrahim yagama duk abinda zaiyi amma bata farkaba. Alokacin da Na'ima tafarka lokacin shi kuma Abdurrahim yagama abinda zai yi har yafita aikin shi.Gidan ko rufe abin shi yayi kamar yadda yasaba in zai fita aiki. Da wata irin yunwa Na'ima ta farka dan cikin tama har gefe daya na rike mata, zama tacigaba dayi akan gadon tun tana tunanin fitowar Wanda tagani jiya har ta kasa jurewa ta tashi taje kusa da k'ofar d'akin shi,sai dai da alama yafita saboda tatura k'ofar taji arufe take. Kasa daurewa tayi ta fita daga d'akin ,kitchen ta shiga Allah ya tai maketa tasamu wani tea da yasha ya rage sai dai ya huce sai wainar kwai itama da alama yaci yarage ne,ta d'auka ta cinye tass sanna ta d'an ji sauk'in yunwar, sai dai me tana gama ci amai ya biyo baya aiko taita kwarashi agun. Rasa abinda zata kwashe aman tayi ta shiga tolait d'in d'akin nan ma bata ga wani alamun abunda Zata goge ba ko ta share, komawa tayi ta zauna duk da duk atsorace take agidan dan bata saba zama guri ita ka dai ba. Abdurrahim kamar yadda ya saba dawowa ya dawo gidan, har ga Allah ya manta da wata Na'ima sai da ya tun karo gidan ya tuna. Zaune take duk tata kure jikin ta, kallo d'aya za kai mata kagano atsorace take. Tanajin an bud'e k'ofa zumbur ta mike daga zaunan da take tana zare ido. Kallo d'aya Abdurrahim yayi mata ya dauke kan shi, kitchen yanufa dan haka d'abi'arshi take daga yadawo aiki bazaiyi komai ba har sai yasamar ma kanshi abinda zaici, dan shi bai iyacin abincin siye ba tsabar kyankyami irin nashi. Na'ima na nan zaune Abdurrahim ya fito ta ce "Bawan Allah dan Allah ina kasamoni tana mai maganane tana nuni da hannu kamar tana magana da kurma ,dan ita duk atunanin ta kurma ne. Wani banzan kallo Abdurrahim yayi mata ,tare da mamakin maganar da take mai da kurame. Banza yayi da ita ya shiga kitchen dan samarma kanshi abinda zai ci. Yana shiga kitchen d'in yaci karo da aman da Na'ima tayi mai aciki ,da ta rasa abin kwashewa tab'ar shi agun. Da sauri yadod'e hancinsa yadawo baya da sauri, kallanta yake rai abace ya ce" Kee, amma dai ke baki da hankali ko,kuma inajin asalinki talaka ce ke, dan su ke aikata rashin hankali irin wannan, kuma ke ko atalakar bagidajiyar talaka ce"Abdurrahim nuna Na'ima yayi da hannu yaci gaba da cewa, "wallahi nabaki minti d'aya ka cal ki goge min wan can k'azantar, sannan kuma ki zo ki bar min gidana yanzu-yanzun nan........ 🛥️ ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE.(RENEW) 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori. Page 10 & 11 Wata uwar tsawa Abdurrahim yayi ma Na'ima ya ce"ba ki ji ne?, ki je ki goge min wannan k'azantar da ki kai min a kitchen, sannan kuma ki bar gidan nan yanzun nan." Na'ima ko tsabar al'ajabin maganar da Abdurrahim ya ke yi ce tasa takasa tashi, dan ita duk atunaninta Abdurrahim kurma ne. "Keeee!,wai ba ki ji ne"Abdurrahim ya sake nanatawa ganin Na'ima ta tsaya tana kallan shi. Da sauri Na'ima ta tashi ta shiga kitchen d'in amma still bata ga tsumman da zata goge aman ba, dawowa palon tayi tace cikin rawar muryar" Banga tsumma ba ne shi yasa tun d'azu ban goge ba"Banza Abdurrahim yayi da ita ya ciro wayar shi yayi Kira alheri. "Hello alheri ki zo yanzu please" bejira amsar ta ba ya kashe wayarshi. Cikin k'ank'anin lokaci alheri ta shigo gidan, kasan cewar tasan indai Abdurrahim yakirata ba lafiya ba, dan tasan baya kiranta hakanan kawai da wuya.Cikin damuwa dan ita duk atunanin ta ko be da lafiya ne, tak'arasa inda yake tsaye da waya yana dannawa. "Abdurrahim lafiya ka kirani ,gani nazo amma bakace min komai ba? " "Kitchen d'ina zaki d'anyi min mopping" Koda alheri ta shiga kitchen d'in taci karo da amai da sauri tayo baya dan adduniya ba abinda take kyama kamar amai, bata goge ba dan jikinta yabata ba aman Abdurrahim ba ne. Alheri kallan Abdurrahim ta yi da ta fito ta ce "Abdurrahim baka da lafiya ne naga amai a kitchen d'in ka? " " No, bani ba ne yarinyar nan ce. " Sai alokacin alheri ta tuno jiya Abdurrahim yakirata ta duba wata yarinya. Alheri kallan Abdurrahim ta yi ta ce "Ita ce tai aman?" Kinga idan bazaki goge ba zaki iya tafiya. " Alheri juyawa tayi ta shiga d'akin da ta duba Na'ima jiya. Zaune ta iske ta ta tusa kanta tsakanin cinyoyinta tana kuka. "Keee,tashi ki je ki goge k'azantar da ki kai ma muta ne" Na'ima d'agowa tayi tana kallan alheri,sannan ta ce " Dama babu tsumma ne shiyasa bangoge ba"Tom yanzu ansamu tsumman tashi ki je ki goge" "Na'ima yi tayi kamar bazata tashi ba dan idan akwai abinda tatsana bai wuce arika mata magana ba cikin isa. Na'ima tashi tayi tabi bayan alheri,suna shiga kitchen d'in alheri ta mik'a mata mopper d'in. Amsa Na'ima tayi tafara aikin gyra kitchen d'in. Cikin kankanin lokaci Na'ima ta goge shi tass dan bawai aman da tayi ba kawai ta goge sai da tabi lungu da sak'o ta goge, alheri duk tana tsaye tana kallanta, kiran da akai matane awaya yasa ta tafiya, Abdurrahim ta kalla tace zanje gida amma zan dawo" kai Abdurrahim ya girgiza mata alamun karta dawo, sanin halin shi da alheri tayi yasa bata wani jaba tatafi. Wacece alheri? . Alheri ainuhin sunanta kenan ,karatu ne ya kawo su zama London kasan cewar ita 'yar gata ce awajan babanta, primary da secondry d'inta duk a Nigeria ta yi su. Bayan ta gama secondary ne suka dawo London inda taci gaba da karatu, atak'aice dai yanzu haka tana aiki ne a wata private asibiti da ke k'asar. Alheri sun had'u da Abdurrahim ne sanadiyar ciwan ulcer ya kaishi kwanciya a asibitinsu, kasan cewar Abdurrahim baya son kwanciyar asibiti yasa ya naimi abashi wanda zai rik'a zuwa gida yana duba shi, shine fa doctor ya had'a Abdurrahim da Alheri, tom daga nan ne fa Alheri tazama likitan shi, ahankali-ahankali shakuwa tafara shiga tsakanin su,inda yakasan ce Abdurrahim bashi da aminin da ya wuce kamar alheri. abotarsu ya sa Abdurrahim ko da lafiyar shi lau zai iya kiran Alheri tai mai wani abun ita kuma daga ya girata zatabar duk uzirinta taje. Sai dai ita alheri anata b'angaran so mai tsanani takema Abdurrahim, dan akwai lokacin da ta taba fada mai tana son shi, shi ko ce mata yayi iyayan shi bazasu bari ya auri christian ba.Wannan kenan haka dai sukaci gaba da ta rayya har izuwa yau Abdurrahim yak'i ba Alheri damar nuna mai kalar son da take mai,dan shi bata ita yake ba. Wannan kenan. Na'ima nagama mopping d'in kitchen d'in tazo ta wuce tagaban Abdurrahim, ba abinda yafi da mun Na' ima kamar zan manta ba d'ankwali agidan dan daga ita sai doguwar rigar dake jikin ta, kanta ba d'ankwali, d'ankwalin yacire ne alokacin da Abdurrahim yake ciku-cikun cire mata rigar ruwan da tasa,ga gashinta atsefe yake. Na'ima na nan zaune a d'akin da take , Abdurrahim yazo ya wuce ta ya shiga dakin shi, yunwa takeji sosai dan har cikinta yafara k'ugin yunwa , tashi tayi taje kitchen d'in bata ga ko mai ba Wanda zata sa acikinta gashi har wani yunk'urin amai takeji saboda yunwa, idonta ne ya haska mata wata leda da sauri ta k'arasa gurin ledar tana bud'ewa taci karo da farfesun kaza sai zuba uban k'amshi yake, zama Na'ima tagyara taci gaba da cin namanta. Shiko Abdurrahim wanka ya shiga yi yazo yaci ferfesun shi , sannan ya kalli wasan kwallo dan shi ma abocin kallon kwallo ne sosai, sai dai duk wasan kwallon da zai kalla bai zuwa ko ina ya kalla sai agidansa dan shi kamar mace yake daga dare yayi shikenan shida fita kuma sai gobe, ko dan ba mai abokai ba ne ohoho, bashi da k'awar da tawuce alheri dan har mommyn shima tasan da ita. Da saurin shi yafito cin namanshi dankarya huce, amma wazai gani, Na'ima zaune tana tand'e hannu dan har tagama cinye farfesun. kallanta Abdurrahim yake da mamki nuni yayi mata da hannu alamun ta zo, bamusu Na'ima taje dan talura bashi da mutunci inda yau kwanan ta biyu amma bai tab'a bata abinci ba saidai Wanda tagayarage take d'auka taci, so takema tace mai tana son taje gida amma takasa mai maganar, garashin kayan canzawa duk da dai tunda tazo ba tai wanka ba ne, dan ma farin mutum ba acika gane k'azantarshi ba ajiki. Zuk'unnawa Na'ima tayi nesa da shi. Abdurrahim yadad'e yana mata kallan wulak'anci abinda yake saurin tafasa Na'ima kenan tatsani kallan raini.Abdurrahim ko sai da ya gama mata kalllan raini acewarta sannan yace ahankali dan bawanima jin abinda yakecewa tayi ba" Ke wata irin bagidajiya ce, bakida hankali ne?, Abincin da nasa akaimin shine zaki zauna ki cinye min?" Abdurrahim harya k'ari maganarsa Na'ima batace komai ba, bare kuma tace yayi hakuri. Abdurrahim takaici ya isai daga tai mako. kallanta ya kuma yi ya ce " bargunnan " Na'ima yau gaba d'aya ita kanta kyankyamin kanta takeji so take tai wanka amma bata san kayan da zata Saba, inda bata da kaya, haka take wuni kullum ba d'ankwali akanta gashi yau har kwananta hud'u agidan bawanka, kai inda dai mutum min nan bada wuri yake da wowa ba mai zai hana inyi wanka da ganan in wanke rigata, tom wana zani zan d'aura? Take tambayar kanta, yauwa basai in d'akko rigassa ba wadda nake rufawa in benan inzanyi sallah insa kafin rigata ta bushe, yauwa aiko haka zanyi bari in rufe gidan kar inje yadawo, duk da rufe ni ya keyi tom nima bari in rufe ta ciki. " Rufe gidan Na'ima tayi, sannan ta dawo ta cire rigarta ta wanke ta sa ta Abdurrahim,sannan ta shiga wanka, tana cikin wankanne tarika jin buka k'ofa da k'arfi, bak'aramin razana Na'ima ta yi ba , dan tasan ba kowa bane sai mai gidan, kai aiko bazan bud'e ba inda rigata bata bushe ba, kuma inyaganni da rigassa korata zaiyi kuma bansan kowa ba, haka d'inma Nagoge masa taimakona da ya yi, saidai fatan Allah ya kawo yadda zan bar kasar" Shiko Abdurrahim wasu takaddun kayan da zasu d'auka ya manta yazo sauka gashi jiran shi akeyi, tunyana tunanin ko bacci takeyi harya bara tunanin anya lafiya, cigaba da buga k'ofar yayi amma ba alamun za abude. " Na'ima ko kasa k'arasa wankanma tayi saidai ta watsa ruwan kawai, koda ta tab'a rigarta kamarma yanzu ta shanyata, jin bugun k'ofar yayi yawa Na'ima ta yanke shawarar taje tace mai ta wanke kayanta ne tayi wanka, gudin kar yaji shiru ya koreta in ta bud'e kuma. Shawarar zuciyara tabi, cikin tsoro da addu'ar da duk tazo bakinta tak'arasa jikin k'ofar.Sai dai ko da taje kusa da k'ofar kasa magana tayi tarasa abinda zatace , ringing d'in wayar shi da taji ne yasa ta saurara danjin abinda zaice, ji tai yana cewa"Kayi hauri nad'an samu matsala ne agidan amma yanzu zan kawo in aha Allah. " Na'ima ko jin haka ta ce"Uhmm dan Allah ka basu hak'uri n...." Abdurrahim bai bari tak'arasa abinda take son cewa ba ya ya ce, "Keee,bud'e k'ofar mana"Ka yi hak'uri bazai yuwaba ne shiyasa. " Abdurrahim mamaki yasa yama kasa cewa komai,ga bak'incikin fad'an da ogan shi zai mai.Shi da gidanshi daga taimakon magidajiyar yarinyar nan tana naiman jaza mai aiki, jin wayar shi na ringing yasa ya ce, "Kee ,dan uwarki gidan ubanki ne da zaki kulle ki hanani shigowa?" "Ka yi hak'uri nawanke kayanane kuma ba kaya jikina shiyasa" Ita ko Na'ima bala in tsoran Abdurrahim yaganta da rigassa ne yasa tak'i bud'e mai k'ofar . "Keee, ki bude k'ofar nan nace!!" Abdurrahim ya fad'a cikin tsawa. "Ka yi hak'uri bakaya ne jikina shiyasa. "Ki bud'e naceeee!!!" Na'ima shiru tayi,dan ita gani take sai yafi hukunta ta in ya ganta da rigarsa ajikinta. Abdurrahim ko jin Na'ima shiru babu alamun zata bud'e k'ofar ya ce, "Shikenan bari in kira aballe min k'ofar inda ba zaki bud'e ba............. 🛥️ ABDURRAHIM 🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE.(RENEW) 📚📚🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚📚🖊 Na Fadila Sani Bakori Marubuciyar👇🏻 1 SO NE SILA 2 IN DA RAI 3 RAYUWAR HAIDAR 4 OGA HABIB 5 DAGA ALLAH KO D'AURA MA KAI 6 MENALLYN DADDY 7 ABDURRSHIM MATUK'IN JIRGIN RUWA NE Page 12 & 13 Abdurrahim ko jin Na'ima shiru babu alamun zata bud'e k'ofar ya ce "Shikenan bari in Kira ab'alle min k'ofar inda bazakaki bud'e ba". Na'ima jin Abduurahim yace zai Kira a b'alle mai k'ofar,yasa ta fara zare ido tana tunanin yadda zatai tana cikin tunanin ne taji Abdurrahim yana waya yana Kiran aturomai mai b'alle k'ofar,yasa Na'ima jikinta narawa ta bud'e k'ofar. Gefe guda ta rakub'e tana zazzare ido tana jiran hukunci. Abdurrahim ko da yake sauri yake kallan Na'ima kawai yayi ya girgiza kai ya shige ciki batare da ya ma lura da jallabiyarshi da ke jikinta ba.Cikin sauri ya d'akko takaddun ya juya zai fita. Sai dai Kiran da ya shigo wayarshi ne na manager ya d'auka da sauri yana mai cewa"Ga shinan na d'akko ina...."Manager da katar da shi yayi ta hanyar cewa" Abdurrahim gashi nan sabo da sakacinka kajamana asarar milyoyin kud'i dan haka mun da katar da kai aiki na wata uku" Abdurrahim watsarar da takaddun hannunshi ya yi yana jan tsaki sobo da buk'atar takaddun da akace anayi yasa ko karyawa betsayayi ba ya fita tsabar sauri ne ma yasa ya manta takaddun,sai kuma Na'ima da ta dad'e bata bud'e mai k'ofa ba. Na'ima ko tsabar tsoran da take ji ne yasa takasa tashi daga inda take,tana nan zuk'unne taji abu na d'iga akanta dubawar da za tai jini ne ke d'iga awajan da ta bige lokacin da Abdurrahim ya turo k'ofar da k'arfi ta bigeta. Na'ima cigaba da zama tayi agun ga yunwa da take ji inda yau beyi abin kari ba (breakfast) balalle tasamu in yarage taci, gawani basifaffan ciwan kai da kanta ke mata, kukan ma dak'ar takeyin sa, gakan nata jinin yaki daina zuba, tashi tayi ahankali tana daddafa bango saboda jirin da takeji yana nai man kadata. Abdurrahim ne yafito zai shiga kitchen dan nai man abin da zaici, ko kallan inda Na'ima take beyi ba, ita ko Na'ima Ahankali- Ahankali ta shiga d'akin da yazama kamar nata takwanta. Tea Abdurrahim yahad'a makanshi, zama yayi falon amma duk inda idon shi ya kalla jini yake gani d'igo-d'igo agun, tashi yayi yana bin duk inda jinin ya d'iga da kallo, hankalinshi ya ji yafaratashi dube-dube yafarayi yana nai man inda zaiga Na'ima amma bai ganta afalon ba da sauri ya nufi d'akin da ya ke tunanin zai ganta acan. Kwance ya hango ta takawa yayi ya k'arasa inda take ya Kira ta da "Kee"amma Na'ima shiru dan azuwa yanzu yunwa take ji sosai. Hannu Abdurrahin yasa ya d'agota, rik'e take da cikinta ga inda ta kwanta duk ya b'ace da jini sakamakon buguwar da tayi da k'ofar lokacin da ya turo. Cikin rud'ewa Abdurrahim gake kallanta ya ce "Kee baki da lafiya ne?" Na'ima dai shiru ba amsa,Abdurrahim jin Na'ima tayi shiru ya ciro waya yakira alheri. Kira d'aya ta d'aga tana d'agawa ya sanar da ita tazo gidanshi yanzu. Cikin mintinan da basu wace goma ba alheri tazo gidan, ko da taga yadda jikin Na'imar ya yi lokaci guda cema Abduurahim tayi sai dai suje asibiti da ita. Abdurrahim kallan alheri yayi ya ce " ki dubata anan mana" badan alheri ta so ba ta koma ta d'akko duk wani abu da zata buk'ata ta ta dawo. Bandage tasa mata a inda ta buge dan buguwar sosai ce.Maganar ciki ko da take ta rik'ewa ko da ta aunata ba abin da ke damunta wanda ya wuce ulcer . Alheri kallan Abdurrahim tayi ta ce"Abdurrahim wai zaman me yarinyar nan take agidan nan ne ,me yasa baza ka barta ta koma gidansu ba ? " Abdurrahim shiru yayi Kamar ba zai ba alheri amsa ba sannan ya ce"cemiki akai ni na rik'eta? ni ma da zata tafi da nafi son haka"Tom shikenan yanzu dai serious ulcer ke damunta, amma gaskiya Abdurrahim ka kuri yarinyar nan karta jawoma wata wahalar gashi yanzu ma sai jama muta ne wahala take"Okay" Abdurrahim yace. Alheri zama tayi tana kallan Abdurrahim sannan zuwa can ta ce "Abdurrahim wai ya managanar aurenmu ne Ka yi shiru ko kana nufin har yanzu kana kan bakar iyayanka bazasu bari ka auri christian ba ne?". "Alheri nariga nafa'da maki daddyna ko zai bari in aure ki tom k'ila sai in nayi aure, kinga ni kuma yanzu bantashi yin aure ba ma. " Fuuuu alheri ta d'auki jakar ta tab'ar gidan tsabar b'acin ran maganar da Abdurrahim ya fad'amata. Na'ima ko bacin ta ta shi daga baccin wahalar ciwan da taji tana tashi yunwa ma tace gatanan,Na'ima tashi tayi ahankali ta nufi falon. Zaune ta iske Abdurrahim da waya yana chart da mommyn sa Na'ima ta shigo falon kallo d'aya za kai mata zaka fahimci halinda take ciki na yunwa. Na'ima kallan Abdurrahim ta yi ta ce "Ummm dan Allah bakarage abinci ba"tana rike da ciki take maganar, kitchen ya nuna mata da hannu alamun taje can akwai. Na'ima ko da taje kitchen d'in bataga komai ba, dan haka dawowa falon tayi dak'ar take magana sakamakon rikewar da cikinta yayi ta ce" Dan Allah ka tai makamin yunwa na ke ji zan mutuuuu... "Na'ima ta fad'i maganar da k'arfi sakamakon aman da takeji yana tasomata. Kallan ta Abdurrahim yayi sai yaji ta bashi tausayi dan shima yasan yadda ulcer take rike ma mutum ciki. Abdurrahim tashi yayi yaje kitchen d'in ya had'o mata tea mai kauri, inda yabarta azuk'unne anan yasame ta. Abdurrahim mik'amata tea d'in yayi tana sha cikinta ya k'ulle Abdurrahim duk yana nan zaune yana kallan Na'ima da dake juyi tana faman rike cikinta tana cewa "Dan Allah ka taimamin Wayyo cikina da marata " Abin da Na'ima bata fahimta ba ba wai cikin ne kad'ai ke mata ciwo ba hadda mararta lokacin period d'in ta yayi sai ya had'e da ciwan cikin' duk watan nuniya haka Na'ima keshan wuya. Cigaba da malele kuwa tayi agun dan ko tea d'in ma kad'an tasha. Abdurrahim da yarasa yadda zai yi da Na'ima alheri yakira amma wa yatta akashe. Abdurrahim kallan Na'ima kawai yake yamarasa taimakon da zai bata,magungunanshi na ulcer ya kwaso mata ya bata ya ce" Ki tashi ki sha ga magani nan" Na'ima ko kallanshi batayi ba tsabar azabar da take ji,jin yadda mararta ke mata yasa tafara tunanin abin da ke damunta. "Ki tashi kisha maganin" Abdurrahim ya sake mai-mai ta mata. Na'ima da ta fahimci abin da ke damunta cikin cije baki ta ce "Bazan sha ba ba cikina kemin ciwo ba ai. "Tom me ke mi ki zuwo? "cewar Abdurrahim. Na'ima kamar zatai kuka ta ce "Ni dai ka taimakamin"Abdurrahim da ranshi ya fara b'acewa cikin d'aga murya ya ce"Ke da'allacan da me zan taimake ki ,indai bazaki magana ba Wallahi zan rabu da ke ?" Na'ima sotake tacema Abdurrahim ya siyo mata panties da always da kuma maganin ciwan mara amma kuma tana jin kunyar fad'a mai " Abdurrahim da yaga bata da niyar magana tashi yayi yabatta agun. Na'ima har dare tana gun zaune takasa tashi kuma har yanzu bata da niyyar tashi dan ciwan yanzu ne ma yake cinta sosai. Na'ima jin azaba tayi azaba dan gaba d'aya tama rasa wana yanayi take jin yadda marar kaba d'aya ta k'ulle mata tashi tayi ta nufi d'akin da Abdurrahim yake,tana zuwa ta fara bubbuga k'ofar tana nishin wahala tana cewa............ 🛥️ ABDURRAHIM 🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE.(RENEW) 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori. Page 14 & 15 Na'ima jin azaba ta yi azaba dan gaba d'aya tama rasa wana yanayi take jin yadda marar gaba d'aya ta k'ulle mata ,tashi ta yi ta nufi d'akin da Abdurrahim yake.Tana zuwa ta fara bubbuga k'ofar tana nishin wahala tana cewa"Wayyo cikina ka taimakamin zan mutu Wayyo Allah na, haka Na'ima tai ta maimaitawa tana cikiga ba da bubbuga k'ofar, abin ne yayi mata yawa gaciwan cikin ulcer, ga kuma na mara na period. Abdurrahim cikin barci ya jiyo bugun k'ofar da Na'ima ke yi, tashi yayi da sauri ya fito daga d'akin kasan cewar be san jikin k'ofar Na'ima take ba da k'arfi ya tura k'ofar ya nayin shi kamar arud'e ya fito.Wata irin k'ara N'aima tayi dan ba kad'an ba k'ofar ta buge mata kai ba, dafe kan ta yi tana jijjuya yashi, wajan da alheri tasamata bandage ya famamata turo k'ofar da yayi da k'arfi. Da sauri Abdurrahim ya k'arasa inda Na'ima ta ke hannu d'aya dafe da kan d'aya kuma dafe da marar.Abdurrahim ya d'an da d'e atsaye yana kallan Na'ima sannan ya ce"Ke wai me ke damunki ne?". Na'ima tsabar azabar da kanta da marar ta kemata yasa ko amsa bata iya ba Abdurrahim. zuk'unnawa ya yi kusa da ita ya d'an ruk'ota kad'an kamar mai kyamar tab'ata ya ce"Yanzu me ke mi ki ciwo?"Na'ima kanta ta nuna ma Abdurrahim da mararta da ta k'ulle mata. Hannu Abdurrahim ya kai wajan kan na ta, zafi rau ya ji kan."Sai me kuma?" ya sake tambayar ta. Na'ima mararta ta sake nuna mai. Abdurrahim kallanta yayi ya ce "cikinki ke ciwo?". kai Na'ima ta girgiza mai alamun a'a, shiru ya yi sannan ya tashi daga zuk'unnan da yake kusa da ita, waya ya d'akko ya kira alheri ,cikin barci alheri ta ji wayarta na ringing, kamar karta d'auka ganin Abdurrahim be tab'a kiranta ba kamar wannan lokacin yasa ta d'auka. Abdurrahim naji alheri ta d'aga ya ce" Hello Alheri ulcer dama tana sa ciwan mara ne? "dan shi duk a tunin shi ulcer ce tasata ciwan mara,gashi shima bai da ciwo sai ulcer amma bai san tanasa ciwan mara ba. Alheri cikin muryar bacci ta ce"A'a gaskiya ulcer ba ta sa ciwan mara sai dai ko in lokacin period d'inta ne ya yi" Period" Abdurrahim ya mai-mai ta." Eh menstruation ba"Shiru Abdurrahim yayi sannan ya ce " Tom me ye maganin shi? " Tom ka ga dai yanzu dare yayi, amma first aid d'in da zaka ba idan akwai suga kasamata a tea dayawa tasha zai rage mata kafin safiya. Yadda alheri tace ma Abdurrahim haka yayi, kitchen ya je ya d'aura mata tea d'in sannan ya zuba ma ta suga mai yawa a tea d'in kamar yadda alheri tace, bayan ya gama had'a mata tea d'in ya kai ma Na'ima yace"Ga tea d'in tashi ki sha "Tofa anzo wajan dan Na'ima intana ciwo bata son cin abinci. "Wayyo cikina ni bazan iya sha ba "Cewar Na'ima."ke Wallahi biki'isa ba daga taimako ki zo ki zamanmin wahala ked'in banza, ina barcina kin tadani natashi na kuma had'amiki tea ance zai miki magani dan kin maidani wani sakarai ki ce min ba za ki sha ba, tom wallahi bazan iya ba yazam dole ki b'ar min gida" Duk b'ab'atun nan da Abdurrahim ke yi Na'ima najin shi sai dai ahalin da take ciki ta ciwanta take yi dan Allah ne ka d'ai yasan yadda take ji. Abdurrahim jin Na'ima shiru bata amshi tea d'in ba zuk'unnawa yayi kusa da ita ya jawota da k'arfi dan har sai da tayi 'yar k'ara hannunta ya rik'o ya dank'a mata kofin ahannu ya ce" Da Allah malama amshi ki sha" Na'ima cikin cije baki ta amshi kofin tea d'in ta d'aga ta shanye duka. Abdurrahim kallan Na'ima yayi ya ce"Ki tashi ki je ki kwanta"Dan shi ji yake duk ta zamar mai wani kaya. Na'ima tashi ta yi tana rik'e ciki ta k'arasa kan babbar katifar ta mai kamar gado wadda wasu ke Kira da gado huta. Ahankali-ahankali Na'ima ta ji ciwan marar nalafamata ahaka har barci b'arawo ya kwashe ta. Can b'angaran Abdurrahim ko yana ganin Na'ima ta tafi ya koma ya kwanta, yana kwanciya barci ya kwashe shi. Washe gari Na'ima kasa tashi tayi dan tana jin kunyar Abdurrahim yaga halin da take ciki, dan zanin gadon yab'aci sosai da jini, sai dai Alhamdullh ta ji sauk'i sai dai ciwan da kanta yake mata kad'an-kad'an marar ko Allah ya taimake ta kwana d'aya take mata tana ciwo dama. Kasan cewar Abdurrahim hutu yake na dakatar da shi aiki da akayi hakan yasa be tashi da wuri .Lokacin da ya tashi ko da ya fito daga d'akin shi kallan inda Na'ima take kwance yayi na 'yan seconds Kafin ya juya ya shiga kitchen ya had'a ma kan shi abin kari, bayan ya kammala Karin ne, yaciro wayar shi ya ci gaba da chart da friend's d'in shi. Na'ima ko tarasa yadda zatayi ta tashi sabo da rigar ta duk tab'aci da jini,dama kuma idan menstruation d'in mutum ya zo ya sha tea ko kunu da suga da yawa haka yake zubar jini sosai. Na'ima da tarasa yadda zatayi komawa tayi taci gaba da kwanciyarta tana nan kwance Abdurrahim har ya dawo ya shiga d'akin shi yayi wanka ya fito, da alama fita zai yi da Na'ima ta tabbatar in bata cire kunya ba taima Abdurrahim magana ya tafi batasan ya zata yi ba.Naima kallan Abdurrahim ta yi ta ce "Ina kwana"Lafiya,ya jikin naki?"Abdurrahim ya fad'a ba tare da ya kalle ta ba."Na ji sauk'i dan Allah ka taimakamin da pants da always"Abdurrahim be amsa ma Na'ima ba yaci gaba da tafiyar shi gidan alheri ya je ya bata ATM card na shi ya ce"Ga shi ki siyo min kayan mata na sawa da duk wani abu da mace ke amfani da shi"Alheri kallan Abdurrahim tayi ta ce"Nasan yarinyar nan zaka sai mawa ta gidanka ko? "Kai Abdurrahim ya d'aga mata alamun eh, tun da na ke da kai baka tab'a min kara ba ka sai min wani abu, haka da birthday d'ina baka ban ko mai ba duk ban damu ba amma gaskiya yanzu na damu. Alheri kallan Abdurrahim ta yi ta ce "Abdurrahim ya ka ke da yarinyar nan,ka fad'amin gaskiya?"Bansanta ba na ce miki" Tom shikenan, bakasanta ba ka ce ko? "Alheri ta ce. Kai Abdurrahim ya d'aga mata alamun eh, shikenan bari inje in suyo mata ka jirani ina zuwa. Alheri bacin ta suyoma Na'ima duk wani abu daya kamata, takama hanyar zuwa gidan Abdurrahim, dan ace warta sai ta tanbayi yarinyar taji ta bakinta akan alk'arta da Abdurrahim d'in. Na'ima ko tana ganin Abdurrahim ya fita ta tashi ta cire rigar da ke jikin ta ta d'akko ta Abdurrahim da ta tab'a sawa tasa inda ita duk atunanin ta ya tafi aiki ne. Na'ima zaune take tana shan sauran tea d'in da yarage dakyar ma take shan tea d'in sabo da ya huce. Alheri ko da ya ke tana da key d'in gidan Abdurrahim yasa tana zuwa ta bud'e ta shiga zaune ta iske Na'ima tana shan tea abin ta. "Keee alheri ta kira sunanta da gurb'atacciyar hausar ta ta ce"Wayasaka kasa wannan rigar? " Shiru Na'ima ta yi dan ba ta san amsar da zata ba ta ba. Alheri jin Na'ima tayi shiru ta kuma cewa"Kai na ce ubanwa ya saka kasa wannan rigar? " Na'ima da duk ta gama daburcewa sai cewa tayi"Shima ya ganni da ita rannan bai ce ko mai ba kuma d...... " Marin da alheri ta wankama Na'ima ne ya hanata k'asara abin da tayi niyyar fad'a cikin tsantsar b'acin rai Na'ima ta ta shi rik'e da kunci ta ce"Bai war Allah mai ne miki zaki maran ko shima mairigar da ya ganni da ita ai bai cimin komai ba" Na mare ka dan ubanka" cewar alheri. Na'ima ko cikin jin zafin zagin mahaifinta da akayi ta ce" ka da ki sake zagar min ubana yana kabari" Uban ka na ce na ce ubanka-ubanka" wani uban kukan kura Na'ima ta yi ta afka ma alheri, da ya ke alheri irin manyamanyan matan nan ce Wanda zaka gansu ga tsawo ga k'iba yasa ta rik'e Na'ima tai ta duka ,da taga abin bai ma ta ba shak'eta ta yi ta ce"Dan ubanka ya ka ke da Abdurrahim?"Ba dai ubana ba" cewar Na'ima. Janta alheri ta ci gaba dayi ta ce"Inda bazaka fad'amin yadda kake da Abdurrahim ba, tom yanzun nan zakabar gidan nan dan ubanka" janta alheri tai ta yi har zuwa hanyar fita falon, Na'ima kuma sai cijewa take da d'an k'aramin k'arfin ta.Alheri ta ce"Dan ubanka gidan na ubanka ne Da bazaka fita ba? " ke ma gidan ai ba na ubanki ba ne"Ai alheri jin Na'ima ta zageta itama rud'ewa tayi tai ta bugun Na'ima tun k'arfin ta. Abdurrahim ko yana can gidan alheri yana jiranta ta dawo, da ya ji shirun yayi yawa kiranta yayi awaya amma bata d'auka ba,rufe mata gidan ta ya yi Shikuma ya yo gida. Tun kafin ya gama parking motar sa yake jin hayaniya da saurinsa ya k'araso cikin gidan alheri ya iske tana tura Na'ima waje had'e da kai mata duka, tana sai ta fita inda gidan bana ubanta bane, ita kuma tana cijewa tana cewa bazata fita ba inda gidan banata ba ne. Wata uwar tsawa Abdurrahim ya bugama alheri ya ce"Wa ya saki? " Alheri ko da ranta ya b'ace jin abin da Abdurrahim yace mata ta ce" Haka zaka cemin ko wayasani ,tom na rantse da d'unbun son da na ke ma yau sai ta b'ar gidan nan ,waya ce ma yasa ma ka riga" da ya ke haka take hausarta namiji ta mai dashi mace mace ta mai da ta namiji, itako Na'ima ta rakub'e gefe bak'inciki yasa sai kuka take yi, alheri kuma nuna Na'ima tayi da ke kuka ta ce"Kab'ar gidan nan nace" Allah sarki Na'ima ko kallanta batayi ba taci gaba da kukan ta, tun kud'ata alheri tayi tun karfinta Na'ima sai da ta bugu da get d'in dake gidan sannan tatafi taga-taga kamar zata fad'i wani k'arfe da ke kusa da Na'ima Na'ima ta d'auka ta yi kan alheri da shi alheri da taga bata da wani abu da zata kare kanta rugawa tayi sai dai duk inda tayi Na'ima binta take yi da gudunta ita ala dole sai ta bugamata alheri shi. ihu alheri ke yi Na'ima ko bata fasa bin ta ba. Abdurrahim da yaga indai ya kyalesu Na'ima zatai ma alheri rauni indai ta bugamata ,dai-dai ko Abdurrahim zai amse k'arfan Allah yaba Na'ima sa'a ta bugama alheri shi, dan ma Allah yasa ahannu ta same ta ba akai ba, wata uwar k'ara alheri ta yi ta zuk'unna agun tana rirrik'e hannun ta re da alkawarin sai taci uban Na'ima. Da kyar Abdurrahim ya lallabi alheri ta tafi gida, ita kuma Na'ima tana ganin wucewar alheri ta kama hanya zata koma gidan hannu Abdurrahim yad'aga mata ya ce"Kar ki sa ke ki koma min gida" ya na kai wa nan ya shige ya b'arta agun. Waiwaiye adon tafiya inji Hausawa,can kaduna ko gwaggo jerawa su kai da Mariya mahaifiyar Na'ima har'gidan da Na'ima take aiki kasan cewar me gadin ya gane gwaggo yasa ya barsu suka shiga kai tsaye, alokacin Hajiya Rahina tana waya da k'awarta Hajiya Suwaiba matar da gwaggo ke aiki a gidan ta,Hajiya Rahina ganin su gwaggo najiranta yasa ta katse wayar ta cema Hajiya suwaiba zata kirata anjima tayi bak'i ,sannan ta juya tana kallan su gwaggo ta ce " sannun ku da zuwa gwaggo" nan dai suka gama gaggaisawa, sannan gwaggo ta kalli Hajiya Rahina ta ce"Hajiya wannan da kike gani ita ce mahaifiyar Na'ima, na kawota ne in fad'amata yadda mukayi da Na'ima agabanki dan kar'ta zargan da cin amanar yarinyar ta" gwaggo ta ci gaba da cewa"Mariya bayan kin zo kinsanar da kina son Na'ima ta dawo gida sabo da auran da aka d'aura mata, tabbas agabanki Na'ima bata nuna komai ba, tom ammafa bayan kin tafi ga Hajiya nan itace sheda, Na'ima ta zauna sai rusamana kuka take tana rokan Hajiya akan dan Allah kasar da za'a d'akko ma Hajiya kaya za ai tafiyar dogon zango ta roki hajiya aje da ita wai kafin lokacin k'ila asamu mafita dan ita bazata auri mutumin da mahaifinta yabar wasiyar kar ta aura ba, hajiya tace ma Na'ima ita bazata d'auketa ba ta kai ta doguwar tafiya batare da amincewar ko wa na ta ba, sai dai ta fad'a ma mahaifiyar ta in ta amince, Mariya in tak'aicemiki magana Na'ima tazo tasamin kuka akan sai dai in amince aitafiyar da ita. Tom Allah yasani tausayin Na'ima yasani amincewa ,kin ji yadda akayi wallahi" Kiran da akaima Hajiya Rahina ne awaya yahana mahaifiyar Na'ima magana, cikin furgici Hajiya Rahina ta tashi tsaye ta ce"Accident , kana nufin jirgin ruwan da ya d'akko kayan mu yayi accident?" Banji me akacemata ba daga can b'angaran naji tana cewa"Innalillahi'wa ina ilaihirraj'un, kana nufin ba aga Na'ima ba?" kashe wayar Hajiya Rahina tayi ta dafe kai tana karanto duk addu'ar da tazo bakinta. Tun kafin Hajiya Rahina tayi masu gwaggo k'arin bayani suka fahimci duk abinda yafaru. Kuka mahaifiyar Na'ima takeyi sosai tana fad'in "Allah sarki Na'ima ashe haduwar da mukayi itace ganawar mu tak'arshe" Dukkansu Sunyi kukan su san rai dan bamai ba wani hak'uri, sai da mijin Hajiya Rahina ya dawo yayi masu nasiha akan shi komai da kuka gani muk'addarine daga Allah tunrar gini tunrar zane, nan dai alhaji yayi ta masu nasiha har Allah yasa jikinsu duka yayi sanyi bakamar maman Na'ima ba, saidai ita kad'ai tasan irin rad'adin da takeji acan k'asan zuciyar ta, Alhaji da kan shi yad'auki mama amotar sa shida Hajiya Rahina da gwaggo suka rakata har gida, bayan sun isa ne Alhaji yak'arayima ma mahaifiyar Na'ima nasiha sosai, sannan yaciro kud'i masu yawa yabata. Kafin kace me mutuwar Na'ima takauraye duka sabon yalwa, koda labarin mutuwar ya isa kunnan dan gin baban ta, har gida su ka je sukacima mama mutumci sannan suka ce mata sunanan suna jiran dawowar Na'ima duk inda ta kaita," k'aryar banza in mutuwa ta yi dagaske kamar yadda ki ka ce ina gawar ta? " Cewar jimmai mahaifiyar gali Wanda aka d'aura auran sa da Na'ima. Can b'angaran Na'ima ko tana ganin Abdurrahim yayi shigewar sa cikin gidansa ta na kuka ta fita daga gidan.......... 🛥️ ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE. 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori. Wannan shafin gaba d'ayanshi na sadaukar da shi ga 'yar'uwata barrister Hassana Sani,Allah ya taimakeki yabada sa'ar jarabawa🙏🏻🙏🏻 Page 16 & 17. Na'ima ko da ta fita daga gidan ja tai ta tsaya tana kuka dan bata san inda zata ba gashi duk inda zata waiga masu ja-ja yan kunne kawai take gani suma jefi-jefi turawa kenan. Na'ima na nanan tsaye sai ga wani bak'in kare yana kewaye unguwar yana zaro harshe, duk dare Wannan karan shike gadin unguwar, Na'ima ganin karan nan na tunkarota yasa tafara ja da baya ganin karan da gaske gunta ya yo yasa ta juya ta shige gidan Abdurrahim da gudunta, tana shiga taja k'ofar ta rufe, amma duk da haka jikinta be dai na rawa ba dan ta matuk'ar tsorata da karan, cikin tsoro Na'ima ta samu can gefe agidan ta rakub'e tana mai addu'ar da duk tazo bakinta. Na'ima na nan zaune agun har wani wahalallan bacci ya kwasheta. Can b'angaran Abdurrahim ko sai bayan ya shiga gida ya ke jin abin da yayi ma Na'ima bai kyauta ba dan dagagani yarinyar batasan inda zata ba, "Tom ai garama da yayi mata haka dan yarinyar tana bashi haushi gashi tak'i fad'a mai dalilin zuwanta garin "Tofa in ban da abin ka Abdurrahim ba sai ka tambaye ta zata fad'ama ba"inji wani tunanin nashi kenan. Abdurrahim tunawa da yayi be rufe gida ba ne yasa ya tashi ya nufi wajan get d'in dan rufe gidan, torch light d'in wayarshi ya haska ya rufe gidan dan shi daga dare yayi Yake kashe hasken gidan.Bayan ya rufe gidan ne ya juyo sai ya ga abu kamar mutum ya k'udindine awaje d'aya kusan mutuk'an jirgin ruwa basu da tsoro k'arasawa wajan yayi amma abin mamaki Na'ima ya gani kwance agun ta k'udindine jikinta tana barci abun ta. Bak'aramin tausai Na'ima ta ba Abdurrahim ba ji ya yi tausayinta gaba d'aya ya cika zuciyarshi. Abdurrahim ya dad'e atsaye akan Na'ima sannan ya lallab'a yadda ba zata tashi ba ya d'akko ta kamar k'aramar baby ya yi cikin gidan da ita, d'akinta ya kwantar da ita ya ja blanket ya rufe ta sannan ya je d'akin shi shi ma ya kwanta. Abin mamaki washegari Abdurrahim har ya yi abin da zaiyi na karyawa (breakfast) amma Na'ima bata tashi ba, har ya gama danne-dannan wayarshi ya je ya watsa ruwa,sannan jin shirun yayi yawa ya je ya k'ara dubata, still bata tashi ba, tunani ya farayi anya ko lafiya dan yau satinta uku ke nan agidan amma bata tab'a kai haka tana barci ba. Abdurrahim shiryawa yayi ya fita gidan dan zuwa ganin yadda alheri ta kwana ya duba hannun ta da Na'ima ta ji mata ciwo kafin tai mai k'orafi. Na'ima kamar jira ta ke Abdurrahim ya fita yana fita ta tashi, kallan d'akin ta farayi tana tunanin ya akai ta dawo nan,"Kai sai dai in dawo da ni akai" Na'ima ta dad'e tana tunanin yadda akai ta dawo d'akin amma bata samo ba, daga k'arshe tai tunanin k'ila bacci ne ya kwasheta shikuma da yazo rufe gida yatadata ta shigo, kai amma wani irin nauyin barci garan haka, tom amma in haka ne yayi min hak'uri ne inda yakoran daga gidan, nan dai takasa gano amsar ya yi mata ha'kuri ko kuwa daga k'arshe ta tashi ta shiga toilet tai wanka ta cire rigar Abdurrahim dake jikinta ta mai da tata data wanke, tom nan fa yunwa tace itama gatanan zuwa. falon Na'ima ta koma, tananan zaune yunwa nak'aracinta Abdurrahim ya dawo gidan, Na'ima tashi tayi daga kwancen da take da sauri ta ce "Ina kwana" Lafiya ya jikinnaki ?"Abdurrahim ya fad'i maganar yana kallanta da kulawa." Na ji sauk'i sai dai,,,,,,,, "shiru Na'ima tayi takasa k'arasawa. Abdurrahim kallan Na'ima yayi jin tayi shiru,kamar yayi banza ya rabu da ita sai kuma yaji bazai iya ba dan ahalin yanzu yarinyar tausai take ba shi.Abdurrahim kallan Na'ima yayi ya ce "Sai dai me?" Na'ima cikin jin nauyi ta ce "Dan Allah in karage abinci ina jin yunwa"Meyasa bik,,,,," banko k'ofar da alheri tayi ne yahana Abdurrahim k'arasa abin da yayi niyya kallan shi alheri tayi sannan tace"Abdurrahim kana ganin abin da yarinyar nan tayi min jiya amma bazakazo dubani ba ko?" Ke da Allah malama nazo dubaki kin tafi yawanki" Shiru alheri tayi dan tabbas bad a gida take ba.Alheri kallan Na'ima tayi da ke tsaye da alamun magana suke da Abdurrahim ,alheri ta ce" Tom shikenan, amma jiya ai naji kace kakori yarinyar nan ya akai ta dawo?"Abdurrahim batare da ya kalli alheri ba ya ce" Sabo da bata da inda zata shiyasa ta dawo " Shiru alheri tayi sannan zuwa can ta ce " Yanzu kana nufin ta dawo nan dazama kenan? " Abdurrahim da yagaji da tambayoyin alheri banza yayi da ita . Alheri ko jin Abdurrahim yayi banza da ita ga kishin zaman shi da Na'ima da ke damunta sai cewa tayi"Shikenan ni ma yau-yau d'innan zan dawo nan gidan da zama, dan banyarda da zamanka da wannan yarinyar ba"Abdurrahim batare da yana mai ci gaba da danna wayar shi ya ce batare da ya kalli alheri ba" Amma dai kinsan ba ni da d'aki ko?"Sai muyi manage hakanan" cewar alheri. Abdurrahim shiru yayi yana tuna alherorin da alheri taimai ,hakan yasa yakasa hanata amma acikin zuciyar shi bayason zamanta gidan. Alheri ko bata saurari amsar Abdurrahim ba ta ce " Bari inje in kwaso abubuwan amfanina" Abdurrahim ko kai kawai ya iya d'agama alheri. Bayan fitar alheri ne Na'ima da ke nan tsaye har yanzu ta kalli Abdurraahim ta ce" Dan Allah in karage abinci ka taimakamin"dan zuwa lokacin Na'ima yunwa take ji sosai. Abdurrahim d'aga kai yayi ya kalleta ya ce "banrageba,amma ki je kitchen akwai komai sai ki had'a ko tea ne ma " Ai ban iya kunna abun da kuke girkin bane" Muje in gwada " Abdurrahim nuna ma Na'ima yayi yadda ake amfanin da duk kayan Wutan sannan yace mata duk lokacin da take da buk'atar abinci ta dafa duk abinda zata iyaci. godiya sosai Na'ima tayi mai amma bai tankamata ba yawuce abinsa. Kamar yadda alheri tace haka ko akayi dan duk wani Abu na amfaninta tadawo dashi gidan, d'akin dayazaman na Na'ima nan alheri takai kayanta ta jera, koda Na'ima taga haka gudun rigima kayan da Abdurrahim yabata Wanda alheri tasiyo kwaso kayan tayi daga d'akin duk da basu wani burgetaba dan duk k'ananun kaya ne sai dogayan ruguna guda uku sune ma masu dama-dama akayan,a falo Na'ima ta dawo da kayanta. Shiko Abdurrahim tun da yafita sai dare ya dawo gidan, dan juwan alheri gidan sai yaji abun duk ba dad'i. Ko da ya dawo a falon yaga Na'ima kwance, bece komai ba dan yasan alheri ce zatasata tadawo nan, ko inda alheri take be kallaba yawuce ciki abinsa, alheri tashi tayi tabi bayan shi har izuwa bedroom d'insa, kusa dashi ta zauna ta mai d'aura kanta akafad'ar shi ta ce"Abdurrahim kamar baka murna dawota kusa da kai ,Shine kazo koma ka kallan kai wucewarka ko? " Banlura da ke ba ne,amma meyasa kika kori yarinyar can ta koma falo bayan kuma ita kika iske awajan?"Alheri cikin jin haushin abin da Abdurrahim yace ta ce "Sabo da nafita iko da komai nagidan nan shiyasa , i swaer Abdurrahim indai kak'ara nunamin yarainyar nan kamar tafi matsayi awajanka ranar sai ta bar gidan nan ko kuma in b'atar da ita baki d'aya" Alheri na kawai nan ta tashi cijin jin zafi tabar wajan. Washegari ranar ne yakasan ce Abdurrahim zai koma wajan aiki, yanagama shirinsa yafito zai fita kenan ya iske alheri itama ta shirya zata fita, tare suka fita, Na'ima najin duk wani motsun su tashi ne kawai da batayi ba tana jin fitar su ta ta shi ta gyara gidan duk wani abu mai k'ura saida ta goge shi sannan ta d'ora makanta abin kari. Na'ima na nan zaune tana karyawa alheri ta shigo da kukan ta, ko inda Na'ima take bata kallaba tai gaba cikin mintina kad'an sai gata ta fito da jakar kayanta, kallanta Na'ima takeyi damamaki ba damar tambaya dan abun da take tunani Abdurrahim ne ya koreta agidan. Kamar yadda Abdurrahim yasaba dawowa haka yadawo, zaune ya iske Na'ima a falon yana zama wayar shi nayin ringing, da mamaki ya bi number da kallo ganin number k'anin shi ,cikin mamaki ya d'aga kiran damamki ya d'auka dan sunfi magana ta WhatsApp basu cika waya ba.Abdurrahim,da mamaki ya ce jin abin da mai Kiran wayar yace ya ce" Inzo in bud'e maka gida kuma" cikin rud'ewa da mamaki yayi maganar, kallan Na'ima yayi itama shi take kallo yace mata" k'aninane yazo yanzu yazanyi idan ya ganki kuma inajin zai dad'e betafi ba dan yadad'e yana son zuwa"Wani kiran ne yak'ara shigowa wayarshi da sauri ya tashi yafita Na'ma ta bi shi da kallo. "Kai broz ai na yi tunanin bazaka fito ba ne? " kai Abdurrahim ya d'an sosa alamun rashin gaskiya ya ce"Ina can inama k'anwarka fad'a batayi girki ba" k'anwata kuma?" Cewar Hafiz da mamaki.Abdurrahim cikin tabbatarwa ya ce "K'nwarka kuwa, ai nayi aure bada sanin ku ba, tom dole ce tasa haka dai yarinyar marainiya ce"Hafiz da tsatsanin mamaki ya kuma cewa "Aure kuma broz? "Eh aure ka ga na huta da surutun su mommy ko, sannan kuma nayi surprise d'inku" Hakane" cewar Hafiz dan shi yayarda da maganar yayan nashi. Itako Na'ima kafin su shigo tabar falon dan ta lura b'ako yayi kuma bayason yaganta shiyasa tayi shigewarta ciki bayan sun shigone Abdurrahim yace ma Hafiz yana zuwa , d'akin da Na'ima ta shiga ya shiga zaune ya isketa tayi ta gumi, kallanta Abdurrahim yayi nad'an lokaci haka nan sai yaji yanajin nauyin fad'amata abin da ya ko son fad'a,sannan dai ya daure ya ce" kee ya sunan ki? " Na'ima kallan Abdurrahim tayi sannan ta ce" Na'ima" Yauwa to nayi bak'o k'aninane yazo uwarmu d'aya ubanmu d'aya, tom akwai damuwa yaganmu tare kuma ke baki da inda zaki, ko kinada inda zaji?" kai Na'im ta girgiza mai alabun bata da shi.Abdurrahim yaci gaba da cewa " Tom nace mai ke matata ce, dan haka sai kirik'a behavioural kamar matata kingane ko........... Ayi hak'uri da wrong typing 👏 🛥️ ABDURRAHIM 🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE. 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila sani Bakori Page 18 & 19 Shiru Na'ima tayi tsabar al'ajabin maganar Abdurrahim,Abdurrahim kuma jin Na'ima tayi shiru ya kuma cewa "Wai bi ki ji ba ne? Nace kirik'a behavioural kamar matata idan ba haka ba da akwai damuwa idan Hafiz yaje gida ya sanar ina zaune da mace kin ga dole zasuyi wani zargin da bahaka ba ne ".Kai Na'ima ta d'agama Abdurrahim alamun ta gane. Shiru Abdirrahim yayi sannan ya ce"Yauwa kin iya girki ko? Kinga munyi bak'o kuma yanada buk'atar abinci"Nan ma dai Na'ima kai ta d'aga ma Abdurrahim alamun Eh."Oh"Abdurrahim Yace ya ce " Kirik'a amsamin da bakinki mana" Tom"Na'im tace ahankali. "Yauwa tom yanzu bari in koma falon kar ya jini shiru" 'Hafiz mutanan England" cewar Abdurrahim da fitowar shi falon kenan. Hafiza da fara'arshi ya ce dan shi mai fara'a ne"Broz Allah maganar auran nan taka ta d'aure min kai, dama zaka iyayin aure ba da saninsu mommy ba? "Kabari kawai Hafiz yarinyar auran tausayi nayi da ita bawai so ba ne, yanzu haka sonake Idan nagama shirina in kaita mahaifarsu"Hafiz da mamaki ya kalli Abdurrahim ya ce "Mahaifarsu kuma? Tom auran fa? " Tom Hafiz ina tsoran karsu mommy su k'i aminta da auran ,gara idan nai musu bayani suka aminta sai inje garinsu in kaita nan wajansu" Shiru Hafiz yayi yana kallan Abdurrahim bai ce komai ba,Abdurrahim kuma yaci gaba da cewa"Nasan kanada surutu saura inji maganar auran nan bakin mommy dan nafi so in sanar da ita da kaina, kaji dai abin da nacema ko? "Insha Allah broz bazataji ba,inda baka son ta sani abakina" Nan dai kowa yayi shiru da tunanin da yake ,sai zuwa can Hafiz ya kalli Abdurrahim ya ce " Tom ita Auntyn ta wa bazata zo mu gaisaba ne? " Kai Abdurrahim ya sosa ya ce"Bari inje in fito da'ita" Na'ima na kwance tanajin motsin alamun shigowa tai sauri ta ta shi ko inda take Abdurrahim be kallaba ya ce" So ki ke ki ruguzamin plan ko? Tom rugujewar plan d'in nan dai-dai yake da barinki gidan nan duk inda zaki kije babu ruwana, yanzu in kiga dama ki zo ku gaisa"Abdurrahim na kai wa nan yafita abinsa. Bayan shi Na'ima tabi da k'ak'aro murmushin dole na tarbar bak'o tana zuwa falon ta ce"Snnu da zuwa"Tana fad'i maganar tana mai zuk'unnar da kai kamar wadda tayi k'arya asirinta yatonu. kallanta Hafiz yayi mai makon ya amsa gaisuwarta sai cewa"Wow broz your wife she is very very beautiful, gaskiya ka'iya zab'e" Sannan ya maida kallan shi ga Na'ima ya ce " Auntyna kin ganki kuwa? kamar ke kikayi kanki, dan Allah ki na da k'anwa ina rik'o" Da ya ke Hafiz irin mutanan nan ne masu b'arkwanci. Abdurrahim kallan Hafiz yayi yad'an harareshi dan shi atunaninshi jawo rainine hakan na kod'ata d'in da yayi. Sai zuwa can Abdurrahim ya ce dan katse Hafiz d'in "Tom malam idan kagama zub'ar sai katashi karakani inyoma cefane aimaka wani abun kaci"Kai broz nagaji fa, kawai taimin simple food ya'isa" kafad'a Abdurrahim ya d'aga irin ko ajikin shi, kallan Na'ima yayi yace" Tom kinji ki mai abu mai sauk'i kwai" Na'ima bata amsaba ta juya ta shiga kitchen d'in ,rasa abin da za tai mai tayi. Abdurrahim ko sanin hakan zata iya faruwa yasa yabiyo Na'ima kitchen d'in, tsaye yasa meta tayi tagumi daga gani tayi nisa aduniyar tunani, table d'in dake kusa da ita ya d'an buga, ya ce" Dafa mai ruwan zafi yasha tea sai ki soya mai k'wai kawai" Na'ima kai ta d'ama Abdurrahim,Abdurrahim harararta yayi ya ce "Ki natsu bawai kirik'a abu kina duk'ar da kai ba kamar wadda asirinta yatonu tayi gulma ba" kai Na'ima ta kuma d'aga mai alamun tom.Abdurrahim kuma juyawa ya yi yabar kitchen d'in. Cikin minti goma Na'ima ta gama had'a mai tea d'in ta soya mai kwai ta ta d'ora a plate ta kai mai. yauwa sannu da aiki Auntyna, murmushi Na'ima tayi mai ta ce"kai sai kace wani aiki mai yawa"Wow broz kai mai sa'ane voice d'in mai kwantaccan sanyi irin yadda kake so,Allah da gaske nake broz ina kamun k'afar k'anwarta dan karma arigani"Ita dai Na'ima murmushi ta yi dan taji dad'in yabata d'in da Hafiz ya yi gashi yana bata dariya. Abdurrahim ko hararar shi yayi bai tanka mai ba. Bayan Hafiz ya gama shanye tea d'insa ne, Abdurrahim yaja shi suka fita su kai sallah daga nan suka shiga gari duk da Abdurrahim bawani mai yawan dare bane basu suka dawo gidan ba sai 11:20 pm alokacin Na'ima ta dad'e da yin barci,rashin sanin inda zata kwanta yasa ta kwanta a falon inda gidan 2 bedroom ne . Hafiz ko da suka shigo yaga Na'ima kwamce a falo ya ce " kai! Kai!! Kai!!! broz yau ka yi laifi fa? "Abdurrahim cikin rashim fahimtar Hafiz ya ce"Laifin me? "Hafiz Na'ima ya nuna ma Abdurrahim da ke kwance tana bacci abin ta dan daga ganin barcin kasan tayi nisan kiwo. "Broz kalli inda amarya ta kwanta fa daga gani kai take jira ,ni karka jamin tabar ban abinci kafin in wuce"Banza Abdurrahim yayi da shi dan shi dama baya iya ma surutun Hafiz, kallan shi Abdurrahim yayi ya ce"Inkagama zubar sai kazo innunama inda zaka kwanta"A'a broz kyau kafara kai Auntyta taci tukun" Kai Abdurrahim ya sosa ya ce"Kai bataso in ta yi barci atadata barta anan kawai in ta tashi ta shiga ta kwanta" Haba broz daga gani fa zaman jiran mu take gaskiya ya kamata katadata taga dawowarka dan k'ilama da fushinka tayi barci"Kai bana son shirme kazo mu je ka kwanta". Hafiz da yake irin mutanan nan ne masu naci sai cewa yayi "Broz gaskiya bazataji dad'i ba ta tashi ta ganta a falo kwance zataka kamar danni ne ka juya mata baya kuma kaga laifina zata gani kasa tabar banu abinci"Hafiz ya k'arasa maganar da barkwancinsa. Abdurrahim gaba ya yi yana mai cewa"Inkashirya kwanciya ka kashigo ka kwanta ni nayi nan inda kai naga alamar bakajin barci magana kake jin yi"Hafiz bin Andurrahim yayi yana dariyar maganar Abdurrahim d'in. Inda Na'ima ke kwanciya Abdurrahim ya kai Hafiz ya kwanta. Washegari Na'ima koda ta ta shi fuska kawai ta wanke kasan cewar ba sallah take ba, Kitchen ta shiga tana tunanin abin da zatayi ma bak'onsu, nan dai tayanke shawarar d'ora ruwan zafi ta had'a mai tea inda bawani abu su ke da shi ba sai ya siyo kamar yadda taji yace jiya. Na'ima bayan ta kammala ne ta koma Falon ta gyara bayan ta gama gyara falonne ta koma kitchen d'in shima tana gyarawa,tana cikin aikin ne Abdurrahim ya leko ya ce"Sannu da aiki"Yauwa" Na'ima tace cikin girmamawa dan Na'ima akwai ladabi daganin mutumcin Wanda yake sama da ita. Hafiz ko da yatashi sai da yayi wankanshi sanna yafito falon alokacin Na'ima na zaune tana shan tea, shi kuma uban gayyar yana zaune nesa da ita yana danna waya. "Good morning Auntyna " cewar Hafiz yana murmushi. Na'im ma murmushin tayi mai sauti sannan ta ce"Barka da safiya, ka tashi lafiya, ya gajiyar tafiya?" Lafiya klau Auntyna, ina'iya zama?"Sosai ma kuwa"Na'ima ta ce tana mai murmushi. Zama Hafiz yayi d'an nesa da Na'ima. Banyan sun gama karyawa ne dan har Abdurrahim sai da yasha tea d'in dan yalura da yarinyar batada k'azanta sannan ya ce" tom kai sai ka ta shi mu je asiyo abubuwan buk'ata na dafawa, na sanka sarkin jin yunwa ne kai" Dariya Hafiz yayi sannan ya tashi suka fita. Na'ima na ganin fitarsu ta tashi ta shiga toilet d'in da ta saba shiga tayi wanka tasa d'aya daga cikin dogayan rigunan da Abdurrahim ya ba alheri ta siyo mata. Na'ima na gama shiryawa yayi daidai da da dawowarsu Hafiz. Hafiz cikin tsokana yake Kiran Na'ima ya ce "Auntyn gashi angonki yace yau ki yi girkin da yafi na kullum dad'i"Na'ima fitowa tayi tana murmushi ta amshi cefanan da sukayi ta shiga kitchen d'in. Tare da Hafiz suka shi ga kitchen d'in hatta aikin tare sukayi tun Na'ima na d'arid'ari da Hafiz har tasaki jiki suna aikinsu tare suna hira dan tafahimci Hafiz mutum ne mai sauk'in kai bakamar yayan shi ba. Abdurrahim ko dama suna dawowa cefanan ya tafi wajan aiki bashi ya dawo gidan ba sai dare. Hafiz ko ganin yadda Abdurrahim ya dad'e ya ce"Auntna wai dama haka broz yake da d'ewa?" Shiru Na'ima tayi dan yaune yayi haka,sai zuwa can ta ce" Gaskiya yana dawowa da wuri k'ila wani abunne yarik'e"Hafiz numa Na'ima agogon hannunshi yayi ya ce kalla 9pm fa? " Shiru Na'ima tayi dan itama tafara tunanin ba lafiya ba dan aiya zamanta da Abdurrahim ta lura shi ba irin mazannan bane masu firar dare awaje. Hafiz ko jin Na'ima tayi shiru ya ce "Aunty Amarya kin yi shiru?" Nima na fara tunanin k'ila ba lafiy,,,, " Turo k'ofar da akayi ne ya hanata k'arasa abin da tayi niyyar cewa. Abdurrahim zama yayi kusa da Hafiz ya ce" kaji na dad'e ko? "Kai Hafiz ya d'aga mai alamun Eh. " Kabari kawai wallahi bansan me ya faru ba yanzu ake yawan samun accidents d'in jirgin ruwa ba 'yan kwanan nan, kwanan nan fa ba afi wata d'aya ba akayi wani akarasa ran mutum da dama amma ikon Allah kaga yau aka sake yin wani" Wai gaskiya broz kuna aikin gan-ganci, ni me yajani in rasa abun da zanyi sai tukin jirgin ruwa wai!,sannunku" murmushi Abdurrahim yayi yace "Badamuwa ai tawani b'angaran aikin taimako ne, haka kwanaki fa na tsinci wata yarinya igiyar ruwa ta jawo acikin ruwa ,sai dai nayi parking cikin ruwa na d'akkota "Na'ima da sauri ta kalli Abdurrahim dan ta ji ajikinta bawata bace ita ce dagaji, aiko zata gwada tambayarshi taji itace" Hafiz cikin al'ajabi ya ce"Amma broz ta mutu?"A'a bata mutu ba"Abdurrahim ya kauda maganar da cewa" Kai nagaji sosai" Hafiz kallan shi yayi ya ce "Broz asama abinci ko?"No nak'oshi, sai da naci abinci na k'oshi sannan nadawo" Abdurrahim tashi yayi ya shiga ciki dan bak'ad'an ya gajiba, ya yi ma Hafiz saida safe ya shige ciki yabar Na'ima da Hafiz agun. Hafiz kallan Na'ima yayi yace"Auntna Allah bakyakulawa da broz sosai fa amma ki tsaya yanga wata ta kwace broz, duk da naga shima kamar irinki ne,ko dai dan kunganni ne?, amma idan har kina ganin kamar auran tausayi yayi dake yasa kikakasa bashi kulawa gaskiya shawara nake baki ki canza ki kula da mijinki da kyau kafin wata ta rigaki" Shiru Na'ima tayi tana sauraran Hafizs ji tai kamar ta fad'amai gaskiya ita ba matar Abdurrahim bace, amma tana jin tsoran kar Abdurrahim ya koreta gidan kuma batasan inda zata ba. Hafiz ko ganin Na'ima ta shiga tunani ya ce" yanzu dai duk ba wannan ba" ki ta shi ki je ki kula da mijinki" Na'ima cikin inda-inda ta ce "Gaskiya ni nan zan kwana" Haba Auntyna me ya sa ki ke yin haka ne mijinki ne fa!" Na'ima ba ta jin dad'i in taji yace wai Abdurrahim mijinta ne. Hafiz ko haka ya tasa Na'ima da naci da magiya sai da ya turata d'akin Abdurrahim. Na'ima ba dan taso ba sai dai ta rasa yadda zata zillema Hafiz haka ta hak'ura ta shiga d'akin da sand'a dan kar Abdurrahim yaji zuwanta,inda Allah ya taimaketa Abdurrahim yayi barci dan ya gaji sosai kamar yadda yace. Na'ima daddumar sallarshi ta d'akko ta shimfid'a ta kwanta ak'asa , sai dai kasa bacci tayi sabo da sanyin k'asan haka taita juye-juye ,asubar fari talallab'a kafin Abdurrahim ya tashi tai saurin barin d'akin. Yau satin Hafiz d'aya da zuwa kenan,shak'uwace sosai ta shiga tsakanin Hafiz da Na'ima kuma har yanzu Hafiz bai san Na'ima ba matar Abdurrahim bace, kullum Na'ima tare da Abdurrahim suke kwana d'aki d'aya sai dai Abdurrahim bai tab'a sanin Na'ima d'akin shi take kwana ba, sabo da ba ta shiga d'akin sai yayi barci haka zataitajan Hafiz da fira dan Abdurrahim yayi barci kafin ta shiga ,bata yadda ya tashi ya ganta zatayi sammakon barin d'akin. Dan Hafiz ba ya yadda ya kwanta sai yaga shigar Na'ima sannan. Yauma kamar kullmum Hafiz Ya ce" Auntna yau kije ki kwanta da wuri dannima barci nakeji" Na'ima k'in tashi tayi haka taita jan Hafiz da hira har sai ta ta tabbatar Abdurrahim yayi barci sannan tayima Hafiz sallama ta tashi ta shiga cikin sand'a kamar yadda ta saba, saidai me tana shiga taga Abdurrahim.............. Ayi hak'uri da wrong typing👏🏻 Masu naiman Abdurrahim matuk'in jirgin ruwa daga farko basu samu ba zasu iya magana ta numbar nan 08063830828 🛥️ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE. 🔔📚 *JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚* Na Fadila Sani Bakori. Afuwa kwana biyu shiru🙏🏻🙏🏻 Page 20 & 21 Zaune Na'ima ta iske Abdurrahim yana daddan na wayarshi,bak'aramin shock ta ji ba gashi yaganta bare ta koma dan saida ya d'ago kai ya kalleta sannan ya yacigaba da danna wayar. Tsayuwa Na'ima tacigaba dayi abakin k'ofar dan takasa k'arasawa.Abdurrahim bai tankamataba cigaba da danna wayarshi yayi ita kuma da alama bata gaji da tsayuwar ba. "Lafiya? "Abdurrahim ya tambayi Na'ima. "dama Hafiz ne yadaman saidai in zo nan in kwanta" Inda ki ke kwana fa?" Shiru Na'ima tayi tana najarin abin da za ta ce ma Abdurrahim inda dai duk kwanan da ta ke yi d'akinshi bai sani ba. Na'ima cikin rashin sanin mafita ta ce "tom kullum haka yake min ai sai ya rako ni dole"Abdurrahim da bai gane maganar Na'ima ba ya ce "Ina ki ke kwana na ce? "A nan!" Na'ima taba Abdurrahim amsa kai tsaye. "Anan kuma?"Abdurrahim ya mai-mai ta, kai Na'ima ta d'aga mai ,Abdurrahim da mamaki ya bar abin da ya keyi ya tsaya yana kallan Na'ima ya ce "Wato sai nayi bacci ki ke lallab'owa ki shigomin d'aki ko? "Na'ima kanta ak'asa tana wasa da yatsun hannunta ta ce"Hafiz ne ke takuramin amma bada son raina ba" Banzan Abdurrahim ya yi da ita yagama danne-dannan wayarshi ya kwanta yana jiran yaga ina take kwanciya in ta shigo. Na'ima ko ci gaba da tsayuwa tayi sai da ta kintati lokacin da take tunanin Abdurrahim yayi bacci sannan ta lallab'a ta hau gadon ta d'akko addumar sallarshi ta shimfid'a ta kwanta ak'asa, saidai Na'ima batasan duk abin da take ba da ido d'aya👁️ Abdurrahim ke kallanta,Abdurrahim ko yana nan yana tunanin yadda zai b'illoma Hafiz akan haka har bacci kwashe shi. Kamar yadda Na'ima tasa ba tashi haka ta tashi ta shiga kitchen ta had'amasu abin kari suka karya kamar yadda suka saba. Bayan wata d'aya. Wata irin shak'uwa ce ta shiga tsakanin Hafiz da Na'ima yanzu haka yau satin shi hud'u kenan a k'asar.Duk lokacin da Na'ima zasu zauna suna fira da Hafiz sai taji kamar ta fad'a mai ita ba matar Abdurrahim ba ce ko Allah zai sa ya tausayamata ya mai da ta k'asarta, saidai daga ta tuno da auran gali dake kanta sai taji kwata-kwata bata sha'awar komawa k'asarta, lokuta dadama tunanin mamarta da k'annanta na damunta gashi yanzu hattayi wata d'aya da sati biyu kenan ak'asar . Na'ima na nan zaune tana ta tunane-tunananta Hafiz ya yazo bata sani ba,Hafiz ganin haka ya ce"Amaryar big bro lafiya kuwa? Tunanin wa ki ke haka ne?" Murmushi Na'ima tayi ta ce" Hafiz kenan tunanin wa zanyi Wanda yawuce na....." Kafin Na'ima ta idasa Hafiz ya rigata da cewa"Na Yayana ko?" . Dariya Na'ima tayi tace"kusan haka"Aunty Amarya yafa kamata yau mu je ki kaini inga gari tun da nazo sau biyu fa ki na gani mijinki ya fita dani" itama Na'ima dama ta gaji da zaman gidan dan haka da saurinta ta tashi ta ce"aiko tashi mu je kaga dama ni ma ina sha'awar fitar"Na'ima d'an kwalin rigar dake jikinta ta yafa suka fita a motar Abdurrahim. Yau da wuri Abdurrahim ya dawo gida, sai dai Yana tura k'ofar rufe yajita gam, tunani yafara tom ina suka je lallai Hafiz rawar kanka ta kai, da yagaji da jira number Hafiz d'in yakira gashi tana ringing amma ba ad'auka ba, yakira yafi ak'irga amma ank'iyin picking call d'in, hankalin shine yafara tashi yace karfa inje yarinyar nan fa ta fad'ama Hafiz gaskiyar lamarin yadda nake da ita.Abdurrahim yana nan tsaye bakalar tunanin da bai yi ba, yana nan tsaye sai ganin motarsu yayi tayi parking . Kallo d'aya zakaima Abdurrahim kasan rashin ab'ace yake. Hafiz da sauri ya k'araso wajanshi ya ce"Yi hakuri brother mun ma laifi, Wallahi kaga wadda tasanan muketa yawo"Hafiz yanuna Abdurrahim Na'ima yana mai ci gaba da cewa "gashi abin haushi ma tasa na manta...." tasssss! Ka ke ji Abdurrahim ya d'auke Hafiz da mari ya ce" Da Allah rufe min baki dama na lura baka da hankali kwata-kwata waya baka izinin fita da ita?" Zuk'unnar da kai Hafiz yayi yana dafe da gun da Abdurrahim ya maraishi. Abdurrahim ko yaci gaba da cewa" tom daga yau har kabar k'asar nan nahanaka magana da ita baki d'aya kaji ko?" Kai Hafiz ya d'agama Abdurrahim yana tunanin tsafin rai irinna Abdurrahim d'in. Shiko Abdurrahim bakomai yasa yayanke tarayyarsu ba sai tsoran kada Na'ima ta tona mai asiri danyaga shak'uwarsu kamar wa inda suka dad'e da sanin juna ne. Abdurrahim mai da kallanshi ga Na'ima yayi ya ce" daga yau kar insake ganin ku tare Ke ma zamanki na d'an lokacine ki kiyaye "yana kaiwa nan ya fusge key d'in dake hannun Na'ima ya bud'e gidan ya shiga yabar su agun a tsaye. "Mu je "Hafiz ya ce ma Na'ima, shiga su kai suna shiga Hafiz yayi hanyar bedroom d'in shi Na'ima tace"abinci fa?" kai Hafiz girgiza mata yawuce ciki. Ba wanda yaci abinci ya kwanta dan gidan kowa ranshi abace yake ,shi Hafiz bawai marin da Abdurrahim ya yi mai bane yab'ata mai rai a'a cewar yahanasu magana da Na'ima shine abin ya bashi haushi, itama b'angaran Na'ima hakane maganar d'aya ce hanasu Magana da Abdurrahim yayi ne yab'ata mata rai. B'angaran uban gayyar ko ko ajikinshi dan shi dad'in ma haka yaji dan dama kullum tunanin shi kar Na'ima tayi gigin fad'ama Hafiz gaskiya. Na'ima kwanciyarta tayi a falon ganin Hafiz ya shige ciki dama shike takura mata taje d'akin Abdurrahim ta kwana. Hafiz ko wayarshi ya manta hannun Na'ima yazo amsa yasan zatayi tunanin aje mai a falon,sai dai sai yana zuwa yaga Na'imar kwance a falon, Hafiz hannun kujerar da take kwance ya bubbuga bud'e idonta tayi tana kallanshi Hafiz ya ce "Haba Aunty amarya ba dai sabo da kina fushi da Yayana ba ne yasa kika gudo nan ki ka kwanta? Dan Allah tashi kawai ki shiga ki kwanta" Na'ima sanin nacin Hafiz da tayi ne yasa ba tai mai gaddama ba taje ta kwanta. shigo Abdurrahim alokacin yayi nisan tafiya a duniyar bacci. Cikin dare Na'ima tafarka da matsanan cin ciwan mara dama tunda wata yazo k'arshe kullum cikin fargaba take, juyi takeyi a d'akin gaba d'aya tafita hayya cinta, wayyoo Allah na zan mutu, wani irin nishi takeyi na wahala cikin bacci Abdurrahim yajiyo nishin Na'ima.Abdurrahiim tashi yayi da saurin shi ya kalli inda ta ke ta malele kuwa ak'asar tana rik'e k'asan cikinta,tana cewa "wayyo Allah na" haka Na'ima ke ta maimai tawa dakyar-dakyar. Abdurrahim sakko wa yayi daga kangadon da sauri yayo kanta dan bak'aramin tsoro ta bashi ba ganin yadda takeyi, jawota yayi yana girgizata ya ce " ke me ke damunki ne ? "Yayi mata tambayar da alamun tsoran ganin halin da take ciki . Na'ima cikin cije baki ta ce mai"Marata ke ciwo" irin na rannan?"Abdurrahim ya tamayeta."Eh irin shi ne"Abdurrahim sakinta yayi yafita yahad'omata tea da suga dayawa kamar yadda alheri tace mai wancan karan yayi mata. Cikin mintina k'alilan Abdurrahim ya had'o tea d'in yaji suga sosai yakawoma Na'ima, sai dai ko kallan shi batayi ba ta ci gaba da juyinta tsakar d'akin tana mai k'ara tamke marartata. Abdurrahim kusa da ita ya matsa ya tadota ya d'an jinginata da jikinshi irin yadda akema yara, sannan ya d'akko cup d'in tea d'in ya kai shi bakinta, Na'ima hannu tasa ta ture cup d'in dan ji take bazata iya shaba , turewar da za tai ko tea d'in ya kusa barema Abdurrahim ajiki,hakan yasa Abdurrahim ya tunkod'eta da saurinsa ya ce "ke ki ka sani kuma daga wannan watan bazakisake min wannan ciwan agida ba daga Hafiz yatafi kema za ki san inda dare yayi Maki ke ma, dan kin samu ma tsabar samun guri zaki ture cup d'in ki zubar da shi a k'asa ina jin bacin na kaucema da ajikina za ki zuba min ke ki ka sani" Yana kai wanan yabar mata d'akin ya koma falo ya kwanta, sai dai ko da ya kwanta sai yaji duk ba dad'i abin da yayi mata,azuciyarshi ya ce Allah ya baki lafiya ki samu ki bacci inda kin zubar da maganin.Duk yadda Abdurrahim yaso bacci ya kwasheshi kasawa yayi sabo da tunanin halin da Na'ima take, dan gaba d'aya tunanin halin da Na'ima take ya hanashi sukuni gashi ya kasa zuwa dubata tsabar haushin zubar da tea d'in da tayi. Abdurrahim Sai da yayi sallar a suba sannan ya shiga d'akin dan ganin halin da Na'ima take ciki, Masha Allah bakamar jiya ba sai dai abin da be sani ba yanzu abin yafi na jiya dan yanzu ko juyin ma yagagareta , takure take guri d'aya ga rigarta duk ta b'aci da jini. Abdurrahim matsawa yayi kusa da Na'ima ya kirata ahankali amma Na'ima shiru bata amsa ba kuma tanajin shi motsin ne bata son yi,Abdurrahim ko jin tayi shiru matsawa yayi kusa da ita da sauri ya sa hannu ya ya d'an bubbugata yana mai cewa"Kee"Abdurrahim jin Na'ima shiru ga idonta arufe yake sai yaji kamar d'ayar take jan numfashi ma d'agota yayi sai yaga kad'an-kad'an take fidda shi tsabar tagama galabaita. Abdurrahim tunanin kaita asibiti yayi karta mace mai anan, saidai koda ya duba duk ta b'ata rigar jikinta da jini, batare da tunanin komai ba yakama rigarta zai cire, cikin d'an sauran k'arfin da yaragema Na'ima ta rik'e hannun shi,Abdurrahim ko cikin tausaya mata ya ce"Ki yi hak'uri taimakonki zanyi riga zan canza miki in kaiki asibiti" Abdurrahim na fad'in haka ya kama rigar ya zare mata ita ajikinta, sannan ya je inda yake tunanin kayanta ne ya d'akko mata wata rigar zaisamata sai asannan idon shi ya kai ga halitarta,rin tse ido Abdurrahim yayi yana mai son sa mata rigar kuma kasan cewar idonshi arufe yake ya kasa,dan gaba d'aya wani irin kasala da sanyi ya rufe shi,haka dai ya daure cikin sanyi jiki da mutuwar gab'b'ai ya zura mata rigar sanna ya shiga d'akin Hafiz.Zaune ya iske Hafiz d'in alamun bai da d'e da idar da Sallah ba, Abdurrahim kallan Hafiz yayi ya ce"Hafiz zan kai yarinyar nan asibiti batada lafiya" "Subhallah me ke da munta?" Wai lokacin menstruation d'inta ne yayi tom tana shan wahala. Hafiz kallan Abdurrahim yayi ya ce"Brother kamanta aikina kenan abin da nake karanta kenan? bari da akwai magungunan da zan rubuta ma ka amso mata zata samu sauk'i insha Allah dama wasu haka yake musu"Hafiz rubuta ma Abdurrahim magungunan ya yi. Abdurrahim na amsawa yaje ya siyo mata. Cikin ikon Allah Na'ima na shan maganin ciwan yalafa ma ta bacci yayi awan gaba da ita. Ko da Na'ima tatashi jitai kamar anzare mata ciwan baki d'aya. Na'ima koda ta fito Hafiz ya jiki kawai yayi mata yayi shiru inda Abdurrahim ya hanasu magana, in kaga Na'ima suna magana da Hafiz tom Abdurrahim baya nan daga yadawo shikanan ,hakan sai yasa Hafiz yaji jaman duk ba dad'i ya isheshi. Ranar da Hafiz yacika sati shida da zuwa ranar ya shirya tafiya kamar yadda yafad'ama Abdurrahim, saidai ita Na'ima bata san da maganar tafiyar Hafiz d'in ba saidai ta gan shi da kaya, sallama Hafiz yayi ma Na'ima sannan yabata number shi ko da Abdurrahim ya sai mata waya acewarshi. Na'ima bataji da'in tafiyar Hafiz ba ko kad'an dan bak'aramin sabo tayi da shi ba, bayan Hafiz yatafine taji gidan duk ba dad'i cire kayanta ta shiga wanka ko zataji dad'i.Bayan Na'ima tafito wankane tana cikin shiryawa Abdurrahim ya shigo d'akin , k'ara Na'ima tasaki tai sauri tajawo rigar da ta cire ta d'akko ta kare kirjinta da ita .Inda Na'im take tsaye Abdurrahim yanufa, Na'ima kai take girgizama Abdurrahim alamun karya k'araso inda take amma shikan shi Abdurrahim besan dalilin k'arasawar ba umarnin zuciyarshi kawai ya ke bi da gangar jikinshi,yana kaiwa kusa da Na'ima y........... Ayi hak'uri da wrong typing🙏🏻🙏🏻 🛥️ ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUW NE 📚📚🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚📚🖊 Na Fadila Sani Bakori Page 22 & 23. Kai Na'ima ke girgiza ma Abdurrahim tana cewa"dan Allah karka k'araso inda nake" amma ina Abdurrahim bai fasa ba yana zuwa yasa hannu ya jawota jikinshi "Wayyoo Allah na dan girman Allah ka sake ni" cewar Na'ima da duk ta furgice."Sheeet" Abdurrahim yace ya ce mata "Uban wa ya ki tsaya min gida ahaka?, nan gidan kune?" Kai Na'ima ta girgiza ta ce"Wanka nayi Wallahi yanzu haka kaya ma zansa ka gama kayan nan na ciro " duk cikin furgici Na'ima take fad'in duk abin da take fad'a. "Tom d'akko kayan kisa"cewar Abdurrahim har yanzu yana rik'e da ita ba wai ya saketa bane, "tom ka sakeni dan Allah"sakinta Abdurrahim yayi yana maimamakin kanshi da abin da ya aikata, Na'ima ko na ganin Abdurrahim yasaketa tai saurin d'akko rigar da tacire tamaidata ,tana gama sawa tayi saurin juyawa zata fita d'akin, hannunta Abdurrahim ya jawo ya ce" Ina kuma zaki?"Dan Allah ni gidanmu nake son komawa" cewar Na'ima da duk tagama furgita da Abdurrahim dan ita da kallan mutunin kirki take mai shiyasa tasaki jiki tai zamanta agidan. Shiru Abdurrahim yayi sannan ya ce"Gida kuma?" Kai Na'ima ta d'aga mai alamun Eh. Shiru Abdurrahim yayi yana mai rik'e da hannun Na'ima har yanzu ,kamar yana tunani sai zuwa can ya ce" Me ya sa ki ke son zuwa gidan? " Na'ima kanta ak'asa ta ce "Sabo da bana son abin da kayimin yanzu ya sake faruwa"Abdurrahim kallan Na'ima yayi ya tab'e baki ya ce"ina ne gidan naku ?" kaduna sabon yalwa "Na'ima ta bashi amsa." ki na da kud'in jirgi ne?" Abdurrahim ya tambayi Na'ima. kai Na'ima ta girgiza mai alamun batadasu"tom shikenan sai ki bari duk radda ki ka samu kud'in jirgin Sai ki tafi" Na'ima fusge hannunta tayi daga ruk'on da Abdurrahim yayi mata dan in batsabar rainin hankali ba inazata samu kud'in jirgi, dazai ce wani innasamu kud'i ta tafi. Abdurrahim ko bin bayan Na'ima yayi da kallo, yana tunanin me ke damunsa,yarasa gane takamaimai abin da ke damunshi akanta,tun radda yayi ido biyu da halittun jikin Na'ima yarasa natsuwarshi, ko baccin kirki kwana biyun nan baya samu daga yarufe ido ta yake gani, yanzu haka ya dawo daga rakon Hafiz ne shine ya dawo gida ya huta ya kuma to zali da halitarta da ta kasa fitar mai a ido tai mai tsaye a cikin sak'on tsakiyar gwagwalwar kanshi ,hakan sai ya k'ara da gulamai lissafi ,tom shi ne fa baima san ya isa gurinta ba dan da tayi gangancin yin shiru........ Masha Allah Na'ima sun dawo zama da Abdurrahim kamar yadda suke da, magana batacika had'asu ba dan sai tayi kwana biyu bata gan shi ba sai dai motsin shi da take ji na fitarshi da dawowarshi. Sai dai shi Abdurrahim ana shi b'angaran abin yayi mai tsanani gaba d'aya halittun Na'ima sun hana shi sukuni,dan yanzu ko tsayuwar kirki bai iya wa tsabar ciwan da mararshi ke mai, yanzu haka yau kwanan shi biyu agida bai fita ba dan tsayuwa nanaiman gagararshi yadda yake jin marar na k'ulle mai. Na'ima zaune tayi shiru tunanin duniya duk ya isheta, dan ita yanzu bata da burin da ya wuce taganta agidansu gaban mahaifiyarta dan ahalin da take jinta yanzu har auran galin ma zata iya hak'ura dashi ta zauna dashi ta amshi k'addararta na auranshi. Na'ima na nan zaune tunanin Abdurrahim ya fad'o mata,tana tunanin abin da ya hanashi fitowa kwana biyu,dan yau kwana biyu ke nan Na'ima batasa Abdurrahim a idonta ba. Tunani tafara yi ko ta je ta d'an lek'a tagani lafiya,Na'ima tashi tayi tana tafiya ahankali-ahankali kamar wata b'arauniya cikin sand'a Na'ima ta tura d'akin da Abdurrahim yake kwance,ciki ta hango shi akwance dafe da mararshi dan yanzu ko abu zai d'auka sai dai da rarrafe yake zuwa yad'akko.Kallo d'aya zakai mai kagane ciwan banawasa bane dagaske yake, cikin tausaya mai dan Na'ima akwai tausai ta k'arasa inda yake kwance tace"Sannu, bakada lafiya ne ?" Kai Abdurrahim ya d'agamata, dan ganinta da yayi sai ya ji ciwan nak'ara yun k'uro mai. Na'ima cikin tausayawa ta ce"Ayyah sannu" juya mata baya Abdurrahim yayi dan gabad'aya ji ya yi yana nai man sumewa ganinta da ya ke yi tsaye akanshi, itako Na'ima da batasan dalilin juyawar ba d'ayan b'angaran ta koma tace"ko in kawoma abincine ? "Nan ma banza Abdurrahim yayi da ita yasake juyawa inda ta baro. Allah sarki Na'ima ganitake tsabar ciwone yasashi juye-juyan, ai bata gaji ba sake binsa tayi d'ayan b'angaran tace"Sannu in kawoma abinc..." maganar kakarewa tayi sakamakon jawota d'in da Abdurrahim yayi. Na'ima cikin furgicin jin yadda Abdurrahim ya fusgota ta ce"Kai ma girman Allah kasake ni" dan Na'ima sosai ta tsorata da ruk'on da Abdurrahim yayi mata, Abdurrahim cikin sanyayar murya irin ta Wanda ya gama galabaita ya ce "ba abin da zan miki ,dan Allah ki taimakan zan iya rasa rayuwata ,kuma Kinga kema bakisan ina zaki zauna ba "duk maganar nan da Abdurrahim yake yana rik'e da Na'ima. Na'ima cikin rawar baki ta ce "tom ni mai zanma?" Tace mai tana yunk'urin tashi daga jikin shi ,shi kuma yana k'ara riketa.Abdurrahim kallan Na'ima yayi irin ki tausayamin ya ce "nan d'inki kawai zan tab'a" yanuna mata kirjinta, cikin kid'ima dajin kalaman shi Na'ima ta dage ta fusge daga ruk'on dayayi mata taruga dagudunta falo ,sai dai kafin ta zauna ta ga Abdurrahim agabanta,Abdurrahim be tsaya wata-wata ba ko jin abin da Na'ima ke cewa d'akkota ya yi cak tana ihu tana rikon shi dan son da ya ke ma iyayan shi kar ya yi ma ta komai, amma ina Abdurrahim be saurari Na'ima ba sai da ya kaita har d'akinshi.Na'ima na ihu tana rok'on Abdurrahim amma ina.... Cikin lokaci k'alilan Abdurrahim ya keta mutunci Na'ima. Wasu irin hawaye ke zuba a fuskar Na'ima masu zafi gaba d'aya gani takema rayuwarta bata da amfani, take tunanin auran da aka d'aura mata ya fad'o mata arai ,yanzu mai zata cema gali, kai cona danakasa yin hak'uri da abin da 'yan'uwan mahaifina suka zab'amin, mahaifiyata ta hak'ura mai yasa ni ban yadda da auran gali kaddarata bace ,ashe wanna munannan k'addararce tasa nakasa hak'ura na ta kura hajiya sai anyi fatiyar nan dani. Na'ima tuntana kuka ahankali hatta dawoyi da k'arfinta, Abdurrahim ko yana jinta amma yagaza cemata komai duk da maganganun da tayi acikin zuciya tayisu bajinta yayi ba. Abdurrahim yakasa cema Na'ima komai girgiza mata kai kawai yakeyi alamun tayi shiru, amma kamar yana k'ara zigata Abdurrahim bayan Na'ima ya dawo yana bubbugawa kad'an-kad'an,dole tasa Na'ima tayi shiru bawai dan tayi niyar shirun ba.Gashi tayi tayi Abdurrahim ya barta ta sauka akan gadon yak'i haka ta hak'ura dole ta kwanta ba dan ta soba ahaka har bacci b'arawo ya d'auketa. Washegari Abdurrahim har ya ta shi Na'ima bata ta shi ba, lallab'awa yayi yasakko daga kan gadon gudun kar ta tashi, wanka yayi agugguje dan so yake ya gudu kafin Na'ima ta tashi,dan nauyin had'a ido yakeyi da ita. Abdurrahim yafita da jimawa sannan Na'ima ta ta shi, koda ta tashi Na'ima ta tuno abin da ya faro da ita kuka ta fasa ta koma takwanta tsabar bak'in cikin halinda taga kanta ciki, tayi kuka kamar ba gobe har tagaji ta lalla shi kanta tayi shiru ta lallab'a ta ta shi taje tatsarkake jikinta. Gaba d'aya bata jin dad'in jikinta gawani irin tsanar zaman gidan da take ji. Abdurrahim kamar yadda yasaba dawowa haka yadawo, kwance ya isketa a falon kanta na kallan sama iya tausai Na'ima taba Abdurrahim, k'arasawa yayi inda take kwance, Na'ima naganin shi tayi saurin d'auke kanta cikin fad'uwar gaba, kallanta Abdurrahim yayi yace"Tabbas ni mai lefine wajan ki, dan girman Allah kiyi hak'uri ni kaina bantab'a aikata zina ba wallahi sai akanki" Na'ima cikin kuka ta ce "insha Allah sai Allah ya sakamin ,haihuwar fari da za kai insha Allahhu mace zaka haifa kuma insha Allah sai Allah yasa ammata fiye da abin da kai min "Na'ima na kaiwa nan ta tashi tabar mai gun ta shiga d'akin da yake ama zaunin na ta. Fita Abdurrahim yayi dan siyo ma Na'ima wani abun ko allah zaisa tayi hak'uri ta yafemai ,dan ya girgiza da addu'ar da tai mai.Tsabar saurin Abdurrahim yake ne yasa yamanta bai rufe gidan ba ita kuma Na'ima jin fitar shi datayi yasa ta dowa falon amma da mamaki sai taga k'ofar falon abud'e bai rufe ba. alhamdullilah tace dan tun d'azu taso barin gidan taji k'ofar a rufe. Na'ima da hanzarinta ta tashi ko kayanta bata tsaya d'auka ba ta fita daga gidan da saurinta ,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,, 🛥️ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUW NE. 📚📚🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚📚🖊 Na Fadila Sani Bakori Page 24 & 25 Cikin sauri Na'ima ta bud'e d'an ma daidai cin get d'in ta fita. Sauri kawai ta ke yi ko gabanta ba ta gani sosai so ta ke kawai taga tafita daga Unguwar gabad'aya. Abdurrahim na cikin wata plaza yana siyayya ya hango Na'ima sai sauri ta ke, banza yayi da ita saida ya gama abin da yake yi amma duk yana han gyanta daga inda yake.Bayan Abdurrahim ya gama biyan kud'in siyayyar da yayi ne ya kin kimi kayan da ya siya yasa su a mota. Abdurrahim bin Na'ima ya rik'ayi abaya -abaya, ita ko Na'ima zuwa yanzu ta fara gajiya dan gabad'aya ba ta jin k'arfin jikinta ga yunwa inda bata ci komai ba, tafiya Na'ima ta ke tana haki dan wani irin amai take jin yana zuwa mata tsabar yunwar da take ji kuma tsabar naci ta dage sai tafiya take yi wadda bata san inda zata ba, duk inda yayi mata nan take bi. Abdurrahim ko parking d'in motar shi yayi yana han gyanta daga inda yake inda tafiyar kad'an-kad'an take yi, wani bak'in kare Na'ima ta hango ai tun kafin ta gama tantance babbane ko k'arami ta juya da gudunta ta koma baya. Abdurrahim ko duk yana zaune a cikin mota yana han gyanta, shi ko karan bin ta shi ma yayi da na shi gudin,ihu Na'im ke yi tun k'arfinta da sauri Abdurrahim ya bud'e mata murfin matar ta shiga, dan ita bata san koma waye ba tana ganin ceto kawai ta afka. Ayyah Na'ima inda ki ka fito ki ka koma😅. Ciki gigin tsoran da Na'ima ta ke tace" dan Allah ka taimaka min wallahi ban san ina zani ba" tom badamuwa"Abdurrahim yace cikin k'asa da murya gudin kar ta gane shi, aiko da ya ke Na'ima ba cikin isassar natsuwarta take ba ba ta ga ne Abdurrahim d'in ba har sai da suka shiga gidan ya bud'e mata murfin motar ya ce "fi to"Sannan jin muryar shi da Na'ima tayi yasa tayi saurin d'aga kai ta kallai tace"kai ne dama ? Tom Wallahi bazan fi to daga Motar nan ba ai na riga na gama zaman gidanka inda kai baka da amana ba zan tab'a komawa ba har abada". Abdurrahim zamanshi yayi a Motar, ya da d'e yana kallan Na'ima ita kuma sai kau da kai take alamun bata son kallan da yake mata, cikin natsuwa Abdurrahim yafara magana kamar haka "Na ji ba za ki koma gidana ba yanzu ina zaki tom? "Ba bu ruwanka da inda zani" Cewar Na'ima. Shiru Abdurrahim yayi sannan zuwa can ya ce" Shikenan za ki iya tafiya, sai dai ki sa ni nan ba Nigeria ba ce abin da ya fi abin da naimiki zai iya faruwa da ke, sannan za ki iya had'uwa da masu yan kar kai dan mu nan da ki ke gani akwai restaurant d'in farfesun naman mutane amma in kin ga za ki tafi tom badamuwa za ki iya tafiya"Shiru Na'ima tayi tana tunani sannan zuwa can tace"dan Allah ana yanka mutane da gaske anan? Ka fad'a min gaskiya"Kin ga ne je ki kawai, ni da ma taimakonki naso yi dan kar nukan garin nan da ki ke gani zasu iya cin ye ki ma kafin ki had'u da masu yanka muta nan"Abdurrahim na kai wa nan ya bud'e murfin mutar zai fita, da sauri Na'ima ta kamo hannun shi tace" dan Allah tom zan koma gidan naka wallahi ina tsoran kar nukan garin nan da masu yanka mutane dan Allah zan bika amma dan Allah ba za ka sake cin amanata ba?" Kai Abdurrahim ya d'aga ma Na'ima alamun Eh, "yauwa tom na gode,nama kusa yafema k'ila" Cewar Na'ima. "Tom na gode" Ta re suka shiga falon gidan, kayan da Abdurrahim ya siya ma Na'ima ne ya d'akko ya aje mata a gabanta ya ce"Ga kaya nan na siyo mi ki ki ta sawa abin ki" Na'ima kallan kayan ta yi tace"Ni dai ba kaya nake so ba So nake ka taimaka ka mai da ni garinmu dan Allah"Na'ima ta ida maganar tana zubar da hawaye. Shiru Abdurrahim ya yi na d'an lokaci sannan ya ce"Ki bari k'arshen watan nan ne zan je gida ba kin ce Kaduna ki ke ba? " Kai Na'ima ta d'aga ma Abdurrahim alamun Eh.Abdurrahim yaci gaba da cewa" tom ki bari sai mu wuce tare" A'a ni dai ina so in fara wuce wa" Cewar Na'ima, "Shikenan sai kin dawo in ki na da kud'in Jirgi" Abdurrahim na kaiwa nan ya tashi yayi shigewar shi ciki ya barta. Na'ima ma tashi tayi ta shiga kitchen ta sa mar ma kanta abin da zata ci. Yau Sati hud'u ke nan da faruwar abin da yafaru tsakanin Abdurrahim da Na'ima.Alhamdulillah ko hannun Na'ima Abdurrahim bai sake ta b'awa ba, sai dai zaman nasu ya canza salo, dan yanzu sukan sauna suyi hira bakamar da ba, hakan ya d'an rage ma Na'ima abin da ke damunta dan wani lotun in ta gaji da zaman gidan har addu'a take Abdurrahim ya shigo tasamu abokin hira. Yanzu haka zaune suke suna hira duk da yawancin hirar Na'ima ke yin ta. Na'ima kallan Abdurrahim ta yi tace"yauwa dan Allah me ya sa ka kori alheri a gidan nan? "Kallanta Abdurrahim ya yi ya ce"Na koreta kuma?". "Tom banaga ta zo tana kuka ba ta kwashe kayanta"Oh! Babanta ne yarasu" Ayyah shi yasa ta ta tafi..." Bugun k'ofar gidan da suka ji ana yi ne yasa su kai shiru ,Abdurrahim yana mamaki dan ba wanda su ka zai zo wajan shi, tashi yiyi ya je ya bud'e k'ofar cikin mamaki ya ke kallanta dan shi ya ma manta da ita, kallan shi alheri tayi tace" dama irin damuwar da ka ke cewa kayi dani kenan ko? Daddyna ya mutu amma so d'aya ka kira kai min ta'aziya me ya sa?" Abdurrahim hannun alheri ya rik'o ya ce"Yi hakuri zo mu je ciki in fad'a mi ki dalilin rashin kiranki da banyi ba" Hannunta Abdurrahim ya kamo har Falon, haka nan Na'ima sai ta ji ba ta ji da d'in hannun alheri da Abdurrahim ya rik'e ba. Alheri ko zama tayi tana wani cicin magani ganin Na'ima da tayi dan ta d'auka tsawan wannan lokacin ta wuce. Abdurrahim ko kallan alheri yayi ya ce "kin gane ko abin da yasa ban kiraki ba na yarda Wayana ne tom shi ne fa narasa number ki"Shikenan ba damuwa"Cewar alheri.Alheri nuna Na'ima tayi tace" Abdurrahim wannan yarinyar tana nan kenan?"Kai Abdurrahim ya jinjina ma ta.Alheri ta ce"Ta'iya girki? "Shiru Abdurrahim yayi kamar ba zai bata amsa ba sai kuma yace"in ta'iya ya akai?" "Dama na gajine isowata kenan ta d'an dafamin ko indomie ce"Abdurrahim kallan Na'ima yayi ya ce "Na'ima je ki dafa mata indomie taci kin ji yanzu ta iso" Haka nan Na'ima sai ta ji ranta ya b'aci sa ta d'in da Abdurrahim yayi ta yi ma alheri girki . Ba dan Na'ima ta so ba ta shiga kitchen ta soya ma ta indomie ta kawo mata. Tun daga ranar yazamana Na'ima ita ke masu girki dukan su, tsakanin ta da alheri ko sai dai harara, amma magana ko gaisuwa bata had'asu, tsakanin Na'ima da Abdurrahim ko sun dawo kusan 'yar gidan jiya hakan yasa Na'ima sai ta ji duk haushin su ta ke ji gashi yawan cin 'yan kwanan nan bata jin k'arfin jikinta ga wani irin ciwan kai da ke damunta ga yawan fad'uwar gaba da ke da munta ,hakan yasa yau ko girkin ma ta kasa yi ta had'a tea ta sha tai kwanciyar ta . Na'ima na nan kwance alheri ta shigo gidan wacce dawowarta kenan daga aiki, ko kallan ina Na'ima take alheri bata yi ba, wayarta ta d'akko tana danne-danne sai zuwa can tace" kee ina abincina?" Banza Na'ima ta yi da ita, alheri kallan Na'ima ta yi da mamaki wai wannan abarce take ma magana tai banza da ita, Alheri cikin d'aga muraya tace"kee ba da ke na ke ba, ina abincina na ce?"Na'ima gudun fitina dan ba k'arfin jikinta ta ke ji ba yasa tata shi zata bar ma alheri falon. Fusgota alheri tayi sannan ta turata tun k'arfinta zuwa hanyar kitchen d'in.Da yake Na'ima ba k'arfin jikinta ta ke ji ba yasa ta fad'i gun ta ciki,wata uwar k'ara Na'ima ta yi wadda sai da ta ba alheri tsoro, ko da alheri ta duba Na'ima sai taga kamar suma ta yi, sauri alheri tayi ta bar gidan. Fitar alheri kamar da minti goma Abdurrahim ya shigo gidan, kwance ya ga Na'ima kamar ba rai cikin gigita Abdurrahim ya idasa gurinta yana jijjigata yana kiran sunan ta amma ina batasan yana yi ba tashi yayi da sauri ya shiga kitchen d'in ya d'ebo ruwa ya yayyafamata .Wata doguwar ajiyar zuciya Na'ima ta sa ki ta bud'e idonta tana kallan shi sai kuma tasa kuka, Abdurrahim jawota yayi yajikin shi ya rungumeta yana tambayar ta me ya sa meta, banza Na'ima tayi dashi ta ci gaba da kukan ta, ga kanta da ya ke wani irin jijjuyawa ma ta ga cikinta tana jin ya k'ulle ma ta. K'ok'arin tashi tayi daga jikin shi shi kuma yana k'ara riketa, ya ce"Lafiya wai me ya samekine haka?" Na'ima cikin sanyi ta ce " Ka sakan d'aki zani" Abdurrahim sakin Na'ima yayi yana kallanta, taku bai fi biyu ta yi ba ta yanke jiki ta fad'i agun, da sauri Abdurrahim ya matso ya d'auketa yayi motar shi da ita, a mota ya sata ya kaita wani k'aramin asibiti da ke kusa da su, aiko yana kai ta aka amseta, cikin k'ank'anin lokaci likitan ya gano abin da ke damun Na'ima. Likitan takardar scanning d'in ya ba Abdurrahim da magunguna yace "ko wana lokaci in ta farka zasu iya tafiya" Abdurrahim ko bai tsaya duba ta kardar scanning d'in da likitan ya bashi ba yace ma doctor zai d'auke ta tafarka agida sabo da yana sauri ne" likitan bai mu sa mai ba. Abdurrahim ko da suka shiga gida bedroom d'in shi yayi da Na'ima ya kwantar da ita, tsayawa yayi yana k'aremata kallo haske yaga ta yi mai sosai sai 'yar k'iba da ta d'an yi,Abdurrahim kwanciya yayi gefan Na'ima shima ya jawota jikin shi yana shafa kanta sosai yake jin Na'ima na burge shi ,haka Abdurrahim ya yi ta wasa da sassan jikin Na'ima ,haka ya tsinci kan shi cikin nishad'i,Abdurrahim matse Na'ima ya kuma yi sosai ajikin shi rigarta ya d'aga dan ba abin da ahalin yanzu yaji yana son gani kamar k'irjinta sosai shaid'an ke k'ara k'awata mai ita. Ita ko Na'ima da bata san abin da ke faruwa ba k'ara shigema Abdurrahim tayi jin d'umin jikinshi sai yayi mata dad'i. Abdurrahim ko jin Na'ima nak'a shige mai ai sai yak'ara kaimi wajan abun da yakeyi mata, bakinsu ya had'e guri d'aya yana mata zazzafan kiss,haka Abdurrahim yayi yadda ya ke so da Na'ima . Bayan komai yalafane Na'ima ta fara jin yungurin amai tashi tayi dakyar tashiga toilet d'in shi tai ta kwara amai. Alheri da dawowarta kenan gidan ta kardar scanning d'in da ta gani da magunguna ta k'arasa ta d'akko tana dubawa. "Ciki"Alheri tace da k'arfi, Abdurrahim ko dama Na'ima na shiga toilet d'in shi ya fita daga d'akin ya shiga nata toilet d'in da sauri yayi abin da zai yi dan so ya ke yayi ya kintsa jikinshi dan lokacin sallar magriba yayi, yana fitowa yazira jallabiyar shi yafita falon, alokacin kuma alheri ta d'auko takardar scanning d'in Na'ima tana gani, dai-dai lokacin da take cewa" ciki" Abdurrahim ya fito ya kuma ji abin da ta ce. Abdurrahim Kallan rashin fahimta yayi ma alheri ya ce" Ciki kuma?Wa ke da cikin?" Yarinyar da ka ke tare da ita mana, yarinyar da ka ce wai taimakonta ka ke yi ita ke d'auke da cikin shege na tsawan wata d'aya ga shi nan likita ya rubuta muku baku gani bane........... A yi hak'uri da wrong typing 🙏🏻🙏🏻🙏🏻 NI NA YI NAN DAN NAGA ABDURRAHIM YA TSORATA DA JIN LABARIN CIKIN NA'IMA🏃‍♀️🏃‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️ 🛥️ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE. 📚📚🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚📚🖊 Na Fadila Sani Bakori 1)SO NE SILA 2)OGA HABIB 3)IN DA RAI 4)DAGA ALLAH KO D'AURA MA KAI 5)RAYUWAR HAIDAR 6) MENALLYN DADDY 7) ABDURRAHIM MATUK'IN JIRGIN RUWA NE Page 26 & 27 Cikin rud'ewa Abdurrahim ya fusge takardar hannun alheri yana karantawa, wata irin zufa Abdurrahim yaji tana keto mai kota ina, kallan alheri yayi ya ce" alheri ban yarda ba zo ki dubata dan Allah wannan ma ai shirman banza ne yaza ai ma ce wai tana da ciki akan me?" Wani irin kallo alheri ke ma Abdurrahim, Abdurrahim ko hannun alheri ya kamo ya ce"dan Allah mu je ki duba yarinyar nan danni ban yarda ba Wallahi ace wai tana da ciki" cikin masifa alheri ta fusge hannunta tace" bazan duba ta ba d'in!" tana kaiwa nan ta d'au wayarta tafita daga gidan gabad'aya. Abdurrahim zagaye d'akin ya ke ta yi dan ya ka zama, ana cikin wannan yanayin ne sai ga Na'ima ta fito falon dan samar makanta abin da zata ci dan wata irin yunwa take ji, garashin k'arfin jiki da ke damunta. Ko inda Abdurrahim yake Na'ima bata kalla ba kitchen ta shiga ta had'a tea tai zamanta kitchen d'in tasha,abin da ya ba Na'ima mamaki duk dad'e war da tayi a kitchen d'in haka ta dawo ta iske Abdurrahim yana ta kewaye falon da takardar scanning d'in ahannun shi inda ita Na'ima batasan ya kai ta asibiti ba inda har yakaita ya dawo da ita bata cikin hayyacinta. Kallan shi Na'ima ta yi ta gefan ido ta tana tunanin ta kardar da ya ke ta faman juyawa ko ta meye ,juwa ta yi zata tafi ," keeee! " Abdurrahim yakira ta, juyowa Na'ima tayi tana kallan shi dan raban da yayi mata irin wannan kiran harta manta. "Wai dagaske ne ki na da ciki?"Abdurrahim ya tambayi Na'ima yana mai k'ureta da ido. "Allah yarabani yin ciki dama fatan da ka ke min kenan? Tom Wallahi bazan tab'a yin ciki ba" cikin kuka Na'ima ta idasa maganar tana kaiwa nan ta juya zata shige bedroom d'inta , da sauri Abdurrahim ya rik'o hannunta ya ce" ke duba nan ki gani" yana nuna mata takardar scanning d'in , zaro ido Na'ima tayi tace"tom ai bani Na'imar ba, wannan bakaga Na'ima Abdurrahim akasa ba? Ni kuma Na'ima Yahaya sunana, kuma ni akan me ma zan yi wani ciki"Na'ima ta fad'i maganar tana turo baki ta ci gaba da cewa "San nan ni ban je asibiti ba" "Zauna "Abdurrahim yace mata. Zama Na'ima ta yi kamar yadda ya'umar ce ta. Shiru Abdurrahim yayi yana kallan Na'ima sannan ya ce"Kin san dai bana miki wasa ko? "Kai Na'ima ta d'aga mai alamun Eh, " Yauwa tom, jiya ba ki da lafiya kika fad'i anan gun ki ka suma na d'auke ki na kaiki asibiti tom shi ne bayan an dubaki suka ban takardar scanning d'in nan da kike gani" zin bur Na'ima tayi ta ta shi tace" Ni wallahi k'arya suke min banda wani ciki!"cikin kuka Na'ima ta fad'i maganar.Shiru Abdurrahim ya yi nad'an lokaci yana tunanin maganarta fa kamar gaskiya ce, yaza ai ace tana da ciki , kallan ta Abdurrahim yayi yace "dai na kuka ni ma da ma banyarda ba"Amsar takardar scanning d'in Abdurrahim ya yi daga hannun Na'ima ya yayyagata ya ce" tom ki dai na kuka kin ga ma na yayyaga takardar ko dan in tabbar masu da k'arya suk dan haka share hawayan kinga dai na yaga takardar ko?" Kai Na'ima ta d'aga mai, "yauwa tom yanzu ki je kiya sallah abinki kin ji?" "Tom "Na'ima tace, sannan ta ta shi ta shiga ciki. Na'ima cikin kwanciyar hankali taci gaba da gudanar da komai nata dan ita bata yarda tana da wani ciki ba kamar yadda shi ma Abdurrahim bai yarda ba. Yau kwana biyu kenan dayin maganar cikin Na'ima kuma cikin kwana biyun bawani zama gida Abdurrahim ya ke ba, lokacin da zai dawo Na'ima kuma ta yi bacci. Yau ta kama weekend Abdurrahim na gida tun safe yake falon dan so ya ke kawai yaga Na'ima , jin shirun ta yi yawa yasa Ya lek'ata yaga ko ta ta shi amma still akwance ya iddata, matsawa Abdurrahim yayi ya d'an bubbugi k'afarta, ido Na'ima ta bud'e tana kallan shi ya ce"Ya dai ? Na ji shiru baki tashi ba" "ban da lafiya ne"Na'ima tace mai." Me ke damunki?" Abdurrahim ya tambaye ta, "jikina ko'ina ke min ciwo, dan Allah yau she zaka k'asar ku d'in? Na k'osa in koma gida ina son ganin Mamana" Shiru Abdurrahim yayi sannan ya ce"tom tashi ki yi breakfast sai muyi maganar zuwa gidan", cikin sauri Na'ima ta sakko, kitchen ta shiga ta samarma kanta abin da zataci dan haka nan sai taji yau tagaji da tea d'in,haka yasa ta dafa taliya, saidai be fi loma uku taci ba ta ji amai nataso mata, da sauri ta ta shi ta k'arasa toilet sai da ta amayar da ita duka. Abdurrahim shiru yayi yana tunanin In ba zai mantaba ya tab'a jin mommyshi nafirar daga tasamu ciki duk abin da taci sai tayi aman shi. Bayan Na'ima ta fito daga toilet d'in ne Abdurrahim ya kalleta ya ce" Shirya mu je asibiti" Cikin k'ank'a nin lokaci Na'ima ta shirya. Wani baban asibiti Abdurrahim yakai Na'ima , yayi ma doctor bayanin abin da suke so, wata roba doctor yabashi yace taje tayi fitsari takawo mai. Abdurrahim inda yabar Na'ima yaje yakai mata rob'ar yanuna mata toilet yace taje tayi fitsari takawo mai, amsa Na'ima tayi taje tayi fitsarin takawoma Abdurrahim shi kuma yakaima doctor, wani d'an ma dai-dai cin d'akin dake cikin office d'in doctor yashiga yayi aune aunan da zai yi sannan ya kawo ma Abdurrahim wata takardar Wanda ke d'auke da bayanan abin da ke damun Na'ima,Cikin fargaba Abdurrahim ya bud'e takardar, sai dai abin da waccan takardar ta fad'a mai ita wannan ta fad'a mai. Abdurrahim cikin zuciyar shi yake mai-mai ta innalillahi'wa inna ilaihirraj'un! Abdurrahim ya dad'e zaune dafe da kai yana tunanin mafita, doctor ya tambaya za'a iya mata theater acire cikin, magani doctor yabashi yace inda cikin baiyi kwari ba yabata tasha zai zube, kud'i dayawa Abdurrahim yaba doctor yakoma inda yabar Na'ima wadda batasan me ke faruwa ba. Abdurrahim suna cikin mota suna tafiya ya kalli Na'ima ya ce" dama maganar da doctor nan gaskiya ne ashe?" Wata magana?" Na'ima ta tambaya. "Maganar ciki mana" "Wayyo nashi ga uku ! , Da gaske ka ke?" cewar Na'ima idonta har ya kawo ruwa. Abdurrahim kai ya jinjina mata ya ce"da gaske ne mana ,amma ki kwantar da hankakinki Allah ya kawomana mafita ga magani nan likitan ya bamu yace daga kin sha cikin zai zube" Ai Na'ima ko jin shi bata yi ba kukan ta kawai take yi, banza Abdurrahim yayi da ita har suka isa gida, Abdurrahim da kan shi ya je kitchen ya d'akko mata ruwa yakawo mata yace"amsa ki sha daga kin sha likitan yace cikin zai zube"Na'ima ko kallan Abdurrahim ba tai ba bare yasa ran zata amshi maganin daga hannun shi, kukanta kawai take yi mai tattare da nadamar biyema shawarar zuciya da tayi, dan tasan da tanaimi izinin mamarta bazata bari ta zo k'asar ba bare abin da yafaru da ita har ya faru da ita. Na'ima kukanta taci gaba da yi tana cewa"wayyo ni ya zanyi in koma gida? Wayyo dan Allah ka tai makamin!" Maganin Abdurrahim ya k'ara mik'a ma Na'ima ya ce" na ce mi ki ki amsa ki sha zaki rabu da cikin yanzu-yanzun nan daga kinsha"Wayyo ni wallahi bazan sha ba sanadiyar mutuwar Jamila kenan, ni kam inajin tsoro inje in mutu!" Abdurrahim kai ya girgiza ya ce " ok ,ashe ko zaki haifi cikin agidanku ,daga nan kuma sai ki naimo Wanda yayi maki cikin!"Abdurrahim na kai wa nan yabar mata gidan ma gabad'aya. Inda Abdurrahim ya bar Na'ima nan yadawo yasameta, kamar ya wuce sai kuma ya fasa ya dawo, gefanta ya zauna ya ce" Yau she ki ke son komawa gida?" Shiru Na'ima tayi da kukan da take tana kallan Abdurrahim.Shi kuma jin tayi shiru ya kuma cewa" yau she ki ke son koma gida na ce!?" Ni dai ba zan koma da ciki ba gaskiya mamana saita kashe ni, sai dai in da Kaga kai ne kai min ta k'arfi in za ka zo muje ka fad'amata gaskiyar yadda akai in da kaga ni dai ba laifina ba ne" kallan baki da hankali Abdurrahim yayi mata, sannan yace" Ni aina fita hak'inki in da na kawomiki magani kin k'i sha,amma in ki na so in rakaki tom kisha maganin nan sannan"Ni dai gaskiya bazan sha ba wallahi inje in mutu" kafad'a Abdurrahim yamak'e alamun ko ajikin shi, sannan ya tashi ya ce "ki shir ya cikin satin nan zaki koma" yana kai wa nan ya juya yayi tafiyar shi.Na'ima ko cikin kuka ta ce" Ni Wallahi ba zan je gida ba da wannan cikin"Okay, zamu gani "cewar Abdurrahim. Da daddare koda Abdurrahim ya kwanta kasa bacci yayi dan yana tunanin anya kuwa in ya bar Na'ima ta tafi da cikin nan nan gaba baza asamu matsala ba inda tabbas yasan cikin shi ne, kai gara dai ya matsa mata koda tsiyane ta sha maganin cikin ya zube zai fi samun kwanciyar hankali, nan dai yayanke makan shi shawarar koda tsiya da safe sai ta sha maganin. washegari Abdurrahim zaune a falo ya gama breakfast yana zaman jiran Na'ima tata shi, yana nan zau ne sai gata ta fito." Ina kwana"Na'ima tace mai "lafiya" Abdurrahim yace. Kitchen Na'ima taje ta had'o makanta tea dan shi ne kawai abin da take iya sha bata amayar ba, in ba shi ba komai ta ci sai tayi aman shi . Tea d'in Na'ima ta d'akko ta zo falon ,Abdurrahim rik'e da wayarshi yana daddannawa amma kallan Na'ima ya ke afakaice har ta gama shan tea d'in. "Kin gama shan tea d'in?" Abdurrahim ya tambayi Na'ima, kai Na'ima ta d'aga mai alamun Eh. "Am sa ki sha"Abdurrahim yamik'a mata maganin, amsa tayi tace"Maganin me ye?" "ki sha magani ne" cewae Abdurrahim.Na'ima juya maganin tayi a hannunta tana kallo ta ce " ni gaskiya bazan sha maganin da bansan ko maganin me ye ba" Abdurrahim cikin jin haushin maganarta ya ce"Maganin zubar da cikin jikinki ne kuma dole ki sha wallahi!" Ni wallahi bazan sha ba" cewar Na'ima tana turo baki, Abdurrahim tashi zaune yayi daga shin gid'an da ke ya ce cikin muryar daga ji kasan ba wasa, "Sha maganin nan na ce!" Idon Na'ima ruwa yafara kawowa ta ce"Ni dai dan Allah bazan sha ba" fusgota Abdurrahim yayi tadawo kusa dashi, kuka Na'ima ta fasa dan taji zafin musgowar da yayi mata. Abdurrahim zare ma Na'ima ido yayi ya ce"sha na ce!" Na'ima k'ara rik'e maganin tayi da k'arfi tace ni dai wallhi bazan tab'a sha ba". Abdurrahim rik'e Na'ima yayi ya b'anb'are maganin ahannunta da k'arfin tsiya,sannan ya bud'e bakinta da tsiya ya tura mata magnin ya d'akko ruwa ya tsiyaya mata irin yadda ake ma yara d'ure ya matse hancinta,,, ,,,,,,,,,,,, AYI HAK'URI DA WRONG TYPING 🙏🏻 🛥️ ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE 📚📚🅙︎𝗮𝗿𝘂j𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚📚🖊 Na Fadila Sani Bakori. Page 28 29 Na'ima cikin fitar hayyaci jin yadda Abdurrahim ya matse mata hanci ta fusge kanta ta furzar da maganin daga bakinta. Abdurrahim kallan ta yayi cikin b'acin rai ya ce"ba za ki sha ba Sabo da kina son cikin ko?" Kai Na'ima ta girgiza mai tace cikin jin wahalar matsar da ya yi mata" Ni Allah tsoran sha na ke kuma ni bana son cikin" Abdurrahim tsabar takaici rasa abin da zaice ma Na'ima ya yi, kawai sai yayi banza da ita yafita gidan, Na'ima ko d'akinta ta koma tana kukan ta kai cin cikin, gashi harga Allah tana tsoran zubar da cikin. Abdurrahim kamar yadda yasaba dawowa haka ya dawo, zaune ya iske Na'ima a falon tayi tagumi, takardar hannun shi yawurga ma ta ya ce"Gashi nan ticket d'in jirgi ne gobe zaki tafi da safe dan haka ki shirya" Abdurrahim na kaiwa nan yayi tafiyar shi yabar Na'ima agun, Na'ima kamar za tai kuka ta ce "Ni wallahi bazan tafi da ciki ba" Abdurrahim yana jinta yayi banza da'ita. Washegari da wuri Abdurrahim ya tashi dan shi ya matsu ya ga Na'ima tabar gidan dan jin cikin jikinta yake kamar wani kaya ne agun shi.Abdurrahimda kan shi ya shiga kitchen ya had'ama Na'ima abin kari (breakfast) amma shiru-shiru ba'alamun Na'ima zata fito, gashi har 9:15 Am, Abdurrahim tashi yayi da niyar zuwa ya tada Na'ima sai gata ta fito , dan dolece ma tasa ta fitowa amma batayi niyar tashi ba sai lokacin da yace mata ya wuce dan ita wallahi ba taga abin da zaisa ta koma da cika ba acewar ta,Na'ima ko inda Abdurrahim yake bata kalla ba dan ita ala dole wai fushi takeyi da shi, hanyar kitchen ta nufa Abdurrahim yace" Ga shi nan na had'ami ki" yana nuna mata tea d'in da ya had'amata, dawowa Na'ima tayi ta zauna tana sha kad'an-kad'an, " ki yi sauri ki gama lokaci zai k'ure" cewar Abdurrahim da yafad'i maganar ba alamun wasa." tom ni ai nace bazan je ba ko?"cewar Na'ima. Abdurrahim tashi yayi daga kishin gid'an da ya ke ya ya kalli Na'ima ya ce" tom sai dai ki ne mi gurin zama amma Wallahi ba dai gidan nan ba, lokaci ya kusa k'urewa dan haka ki yi sauri Malama!"Na'ima ganin babu wasa a fuskar Abdurrahim yasa tace"tom bari in d'akko kayana dama nayi wanka"ko kallanta Abdurrahim be yi ba bare ta sa ran tanka mata, Na'ima na shiga d'akin ta sa key ta rufe k'ofar, Abdurrahim da mamaki yake kallan k'ofar dan be tab'a tunanin zata yi haka ba da sai dai ta tafi ahaka. Abdurrahim tashi yayi yaje yana bubbuga K'ofar kamar zai b'alla ta ya ce"Na'ima ki bud'e k'ofar nan kar ki sa inyi asarar kud'in ticket d'ina, ki bude!" banza Na"ima tayi da Abdurrahim sai da ya gaji da bugawa dan kan shi sanna ya hak'ura. Yau kwana biyu kenan da Na'ima ta rufe kanta a d'aki tak'i bud'ewa, Abdurrahim sai dai a falo ya ke kwana, jiya ma sai dai a plaza yaje ya sai kaya, inda tarufe d'akin da kayan nashi suke, tunanin yake tom inama take samun abinci dan yalura kamar cin abincinta yak'aru sosai, murmushi yayi dan tabbas yasan hasashan shi gaskiya ne, wayo ta ke yi sai taji futar shi sannan take fitowa tasamarma kanta abinci, tashi yayi yabud'e k'ofar falon da k'arfi sanna ya maida ya rufe batareda ya fita ba ya koma kitchen ya b'oye. Na'ima ko dake d'aki taji alamun fitar Abdurrahim fitowar ta daga wanka kenan daga ita sai k'aramin towel tafito falon, kitchen ta nufa direct tana zuwa Abdurrahim ta gani tsaye a kitchen daga gani kasan jiran shigowarta yakeyi, Na'ima naganin Abdurrahim tajuya da gudu zata koma inda tafito amma ina gudu ba d'aya ba befi taku biyu tayi ba Abdurrahim ya cabketa, kara Na'ima tayi tana bashi hak'uri ta ce" ka yi hak'uri Allah zan tafi yau-yau d'in nan ma" Abdurrahim banza yayi da'ita ya d'auke ta cak yayi d'akin shi da ita duk irin hak'urin da Na'ima ke ba Abdurrahim be saurareta ba saida yayi yadda yaga dama da'ita, bayan komai ya lafa ne yace mata "Wallahi ko ki shirya ki tafi gobe ko kuma kullum sai nayi yadda naga dama dake zab'i yarage naki, kuma tun da nabiya miki kud'in jirgi ki ka sa nayi asararsu yanzu sai dai ki nemo me biya mi ki"Na'ima banza ta yi da Abdurrahim ta ci gaba da kukan bak'in cikin kusantar ta da yayi. Abdurrahim ko a halin yanzu yana son zama da Na'ima saidai cikin jikinta yake tsoro inda yayi da ita tasha magani ya zuge tak'i ,kuma shi ma yanzu tsoran tasha maganin ma yakeyi kar aje asamu matsaka ta mutu kamar yadda tace,hakan yasa yake ganin gara kawai ta tafi. Can cikin dare Abdurrahim ya jiyo kukan Na'ima dan tun abin da ya faru tsakaninsu ta ke kuka har yanzu tak'i yin shiru, Abdurrahim ji yayi kamar ya shareta amma jin har yanzu kukan take yasa yatashi ya zura jallabiyar shi yafito, zaune ya isketa ta ta tura kanta tsakanin cinyoyinta tana kuka, kusa da'ita Abdurrahim ya zauna ya tafata, amma ko d'ago kai bata yi ba bare yasa ran zatama saurarai, d'ago kanta Abdurrahim yayi ya ce"yi hakuri ki daina kukan nan dan Allah baki tsoran kanki yayi ciwo, haba kukan yayi yawa mana, yanzu fad'amin me ye damuwar ki atafiyar? "Shiru Na'ima tayi tana nazarin abin da zata cema Abdurrahim, sai zuwa can ta ce " Ni mamana na ke tsoro"tom yanzu ya ki ke so ayi? "Shiru Na'ima d'an yi sannan ta ce" So na ke dan Allah muje tare da kai sai ka fad'a ma mamana balaifina bane kaine ka yi min dole, dan Allah ai dai balaifina bane ko? " Na'ima ta tambayi Abdurrahim,kai Abdurrahim ya d'aga mata ,Na'ima tace "tom dan Allah za ka je kai ma Mamana bayani ?"Eh zan zo in mata bayani ince mata balaifinki ba ne laifina ne" Allah sarki Na'ima cikin jin dad'i ta ba Abdurrahim address d'in inda suke. Abdurrahim ko tabbatar ma Na'ima yayi da ya na nan zuwa,sannan ya tashi ya ce "tom ki kwanta ki yi bacci dan Allah kinga dare yayi kuma gobe da wuri zaki wuce"tom ba kace bazaka biyamin k'ud'in jirgi ba?" cewar Na'ima tana goge hawayan da ya zubo ma ta, Abdurrahim cikin jin tausayinta ya ce "wasa na ke mi ki zan biya mi ki" nan dai Abdurrahim ya lallashi Na'ima tare da tabbatar mata da in taje zai zo daga baya sannan yabarta ta kwanta. Washegari Abdurrahim da kan shi ya shiga kitchen ya had'a ma Na'ima tea ya soya mata kwai anufin shi duk dan kar taji yunwa dan shi tausai yanzu ta ke ba shi. Bayan Abdurrahim ya gama komai ne ya tada Na'ima. Bayan Na'ima tayi wanka ne tasa sabuwar rigar da Abdurrahim ya siyo mata wadda bata ta b'a sawa ba ,bayan ta gama shirin ta ne tafito falon, kallanta Abdurrahim yayi nad'an lokaci dan sai ya ga batatab'a mai kyau ba kamar yau ba. Bayan Na'ima ta gama shan tea d'in ne tabar mai kwan shi agun, kallanta Abdurrahim yayi yace"me ya sa baza ki ci k'wan ba? "Amai zai sani" "Okay"Abdurrahim yace. Abdurrahim dakan shi ya d'auki Na'ima ya kaita har airport. Abdurrahim hannun Na'ima ya ruk'o lokacin da zata sauka daga motar ya ce" Tsaya mu yi sallama mana,Na'ima dan Allah kar ki bari ki haifi cikin jikinki kin ji?"Abdurrahim ya fad'i maganar cikin sanyi ahankali, dan ji yake jikin shi duk yayi sanyi na rabuwar da zasu yi, sannan yaci gaba da cewa" kin ga gida zaki dan Allah in ki ka je kiyi k'okarin zubar dashi acan kinji?" Kai Na'ima ta d'aga ma Abdurrahim.Abdurrahim kuma cikin sanyi ya ce"kin yi min alkawari za ki zubar ?" Nan ma dai kai Na'ima ta k'ara d'aga mai," ki yi magana da bakinki sannan in yarda"cewar Abdurrahim. Na'ima cikin sanyi itama ta ce" na yi alkawari zan zubar insha Allah" ta fad'i maganar tana share hawayan da ke zubar mata. Wata leda Abdurrahim yamik'a ma Na'ima ya ce"gashi nan da akwai wata takarda aciki in kinje gida ki karanta kinji? "Amsa Na'ima tayi still tana goge hawayan da ke zubar mata. Abdurrahim kallanta yayi ya ce" me ya sa ki ke kuka? " "Ni ma bansan ina yin kukan ba" Hannunta Abdurrahim ya kamo ya ce" Allah ya k'addara saduwar mu" yana kaiwa nan yabud'e mata murfin motar ta fita. Abdurrahim na nan tsaye yana kallan Na'ima yaga ko zata waigo,amma Na'ima har ta shiga jirgin bata wai goba.Abdurrahim ta da motarshi yayi ya tafi. Jikin Abdurrahim asanyaye ya koma gida. Na'ima basu suka sauka gida ba sai cikin dare, direct Na'ima gidan hajiya Rahina ta nufa tad'au drop din mota,suna zuwa tai ta bubbuga gidan, mai gadin cikin tsoro ya matso kusa da get d'in ya ce"waye?" Baba ni ce" cewar Na'ima."ke ce wa?"Mai gadin ya tambaya. "Baba Na'ima ce" Ai Baba mai gadi najin haka ya matsa kusa da get d'in cikin wani sabon tsoran dan shi asanin shi ance Na'ima ta mutu a accident d'in da su kai na Jirgin ruwa har kayan hajiya suka hallaka, wayar hajiya Rahina Baba mai gadi yakira. Hajiya Rahina cikin bacci taji wayarta na ringing dubawa tayi taga number baba mai gadi, d'auka tayi tace"Baba lafiya? "Hajiya Wallahi ba lafiya ba, bubbuga k'ofar gida ake na tambayi waye ne akacemin wai Na'ima ce yarinyar ta akace ta mutu" Hajiya Rahina ma cikin kid'ima ta sakko tayo wajan mai gadin, tsaye tagan shi can nesa da get d'in, ita kuma Na'ima har yanzu bata bar bugawa ba tana cewa"Baba ni ce ban mutu ba Wallahi" Ai Hajiya Rahina najin haka tace"Baba bud'e Na'ima ce wallahi ga muryar ta nan wata biyar ai bazai sa inkasa gane muryar ta ba" bud'e get d'in mai gadin yayi, Na'ima ciki tashigo tana goge hawayan da batasan takamaimai na me ye ba, na murnar dawowarta mahaifarta ne Ko ko na bak'in cikin dawowa da cikin shege ne, Hajiya Rahina rungume Na'ima ta yi tana cewa "alhamdulillah dama Na'ima baki mutu ba ? Alhamdullilah!" abin da Hajiya Rahina ke cewa ke nan.Hajiya Rahina dakan ta ta rik'e kayan Na'ima suka shiga cikin gidan, d'akin da aka tanada dan bak'i Hajiya Rahina takai Na'ima,sannan ta kawo mata tuwan shinkafa. Na'ima ko yunwa take ji amma ta san ko da taci aman shi za ta yi dan haka ta kalli Hajiya Rahina tace"Mommy da dai akwai tea ne da shi na sha" dariya Hajiya Rahina ta yi tace "Allah sarki anyi doguwar tafiya ko ciki ya cin ku she"Shiru Na'ima tayi Hajiya Rahina kuma da kanta ta Had'o ma Na'ima tea d'in ta kawomata tai mata sai da safe dan ta huta washegari sa zanta. Bayan Na'ima ta gama shan tea d'in ta ne ta d'akko ta kardar da Abdurrahim yabata ta bud'e ta fara karantawa kamar haka, "Ki yi hak'uri Na'ima bazan iya zuwa gidan ku ba, hasalima address d'in da ki ban namanta shi, sannan ki taimaki kanki ki zub'ar da cikin da ke jikinki, ga kud'i nan ki yi hidimar zubar da cikin dasu. Bissalam. 🛥️ ABDURRAHIM🛥️ MATUK'IN JIRGIN RUWA NE 📚📚🅙︎𝗮𝗿𝘂𝗺𝗮𝗶 🅦︎𝗿𝗶𝘁𝗲𝗿𝘀 🅐︎𝘀𝘀𝗼𝗰𝗶𝗮𝘁𝗲𝗱📚📚🖊 Na Fadila Sani Bakori. MARUBUCIYR 1)IN DA RAI 2) RAYUWAR HAIDAR 3) SO NE SILA 4) OGA HABIB 5) DAGA ALLAH KO D'AURA MA KAI. 6) ABDURRAHIM MATUK'IN JIRGIN RUWA NE 7)MEENALLYN DADDY Page 30 & 31 Bayan Na'ima ta gama karanta letter da Abdurrahim yabata dafa kanta tayi tana kuka sosai tana cewa" Wayyoo Allah na na ba ni wa zan ce ya yi min cikn nan Allah na rok'eka ka d'oramin cikiwan da zai zubar da cikin nan ba tare da na sha magani ba" Na'ima ta dad'e tana kuka har ta samu bacci b'arawo ya sace ta. Washegari da wuri Na'ima ta ta shi ta tayi wanka kasan cewar yanzu saurin jin yunwa gareta yasa tafita ta ga ko hajiya Rahina ta ta shi in da da kan ta ta ke girkin ta bata da 'yar aiki, Na'ima ce ka d'ai wadda ke mata aiki ita ma kuma share-share ne kawai da wanke-wanke .Na'ima a kitchen ta hangi hajiya Rahina tana ta aikin had'a abin kari( breakfast) Na'ima har ta shiga kitchen d'in ta fito da sauri k'arnin k'wain da ta jiyo dan bata shiri da k'arni, tun kafin Na'ima tak'arasa shigowa hajiya Rahina ke kallan Na'ima ganin irin yadda ta yi k'iba tayi haske, bak'aramin mamaki hajiya Rahina ta yi ba ganin Na'ima tafasa shigowa ta koma tana dod'e hanci," Yarinyar nan lafiya kuwa?" Cewar hajiya Rahina, bayan hajiya Rahina ta kammala had'a kayan Karin ne ta Kira Na'ima ta bata nata. Na'ima tea d'in kawai ta d'auka tabar doyar.Na'ima d'auka ta yi zata shiga d'akin da yake mazaunin nata hajiya Rahina ta ce"zauna ki sha anan mana, nakira hajiya Suwaiba na ce mata ta turomin gwaggon ki Allah bashi sai ki fad'a mana halin da ki ka kasan ce bayan tunanin kin mutu da mu ka yi"Na'ima cikin sanyi ta ce" tom mommy ba damuwa Allah ya kawota lafiya" Bayan Na'ima ta gama shan tea d'in da shi ka dai take iya sha, ta share falon ta goge duk wata k'ura da ke falon.Bayan ta gama ne ta na nan zaune gwaggo ta yi sallama ta shigo falon.Da gudu Na'ima ta ruga ta rungume gwoggo ta na kuka." laaa ka gamin shirman banza, me ye kuma na kuka ke da za ki yi farin cikin dawo da ki kai cikin danginki da Allah ya yi"Cewar gwaggon Na'ima. Hajiya Rahina ce ta fito jin shigowar gwoggo da tayi.Bayan sun gama gaggaisawa ne hajiya Rahina ta ce "dama gwaggo na kiraki ne dan ina so ko mai Na'ima zata ce game da b'atanta ta fad'a gabanki inda ni ke ce nasani amatsayin mahaifiyar Na'ima" Hajiya Rahina kallan Na'ima ta yi ta ce"Na'ima mun shi ga rud'u jin bacewarki kwata-kwata inda duk wa inda suka rasa ransu anga gawarsu, amma ke ba ki ba gawar ki, ina ki ka shiga Na'ima har tsawan watanni biyar ko shida? " Tun da hajiya Rahina ta fara magana gaban Na'ima ke fa'duwa, shiru Na'ima tayi dan tarasa ta inda zata fara. "kin yi shiru Na'ima?" Cewar hajiya Rahina. Na'ima cikin sanyi ta ce "Ni ma Wallahi ta ka mai-mai Ban san ya akai ba Wanda ya taimakan ya taimakeni,dan betab'a ban labarin ba ,abin da dai na sani bayan faruwar hatsarin Jirgin mu na farka na ganni agidan wani bawan Allah ba haushe ne kuma kuma musilmi anan naci gaba rayuwata na tsawan wata shida da na yi har Allah yasa ya biyamin kud'in Jirgi na dawo"Cewar Na'ima tana share hawayan dake zibar mata. Hajiya Rahina kallan Na'ima tayi ta ce"takardar fa da na gani waya baki ita ?" Hajiya Rahina ta ciro letter da Abdurrahim ya ba Na'ima tana nunama Na'ima ita. Ita ko Hajiya Rahina ta ga takardar ne lokacin da ta shiga d'akin Na'ima ita kuma lokacin Na'imar bata ta shi daga bacci ba,anan taga takardar ta d'auka ta karanta. Gaba d'aya Na'ima ta gama rud'ewa kuka ta fasa tana cewar"Wallahi gwaggo ba da yarda ta haka ta faru ba da..."Gwaggo tare Na'ima tayi dan ita basan me ya ke faruwa ba,ta kalli hajiya Rahina ta ce" wai hajiya mai me ke faruwa ne ,takarda me ye ne ki ka gani ?" Shiru hajiya Rahina tayi dan tarasa ta inda zata fara yi ma gwaggo bayani ,sannan ta ce"tom gwaggo abi sa ga alama dai Na'ima da ciki ta dawo"Wata irin zabura gwaggo ta yi ta ce"Ke 'yar nan ki rufa min asiri ciki kuma! Kamar ya? " Na'ima ko ta dage kukan ta kawai ta ke yi. Hajiya Rahina ta ce"tom Na'ima ta kuka kuma ai ta k'are in da aikin gama ya gama, amma taya haka ta faru Na'ima? Bayan kin san da aure kanki Na'ima!" Cikin kuka Na'ima ke cewa"Wallahi mommy f'yade ya yi min bada son raina ba ne"Daga hajiya Rahina har gwaggo shiru ka wai su kayi dan dukkansu sun rasa abin cewa, gwaggo ko kuka ta fasa tana cewa"Na'ima ya zanyi da mahaifiyarki? Me zance mata Na'ima? Da wa na ido zan kalleta?" Na'ima cikin kuka ta kuma cewa"Wallahi gwaggo ba da son raina b,,,,,,,,,,," Ke da Allah can yi min shiru yaza ai ki je ki zauna gida daga ke sai Namiji,wanda ba muharraminki ba ba d'an'uwanki ba ba dangi iya ba na baba balle ya kalliha" Cewar gwaggo. Hajiya Rahina ta ce "Haba gwaggo tom ita da ba 'yar k'asa ba ina ta sani ai aikin gama yariga ya gama yanzu tashi zata yi mu je aima mahaifiyarta bayani"Gwaggo kai ta jinjina ta ce"Wallahi hajiya ba zan iya had'a ido da Mariya ba ince mata 'Yarta na d'auke da ciki, ina ba zan iya ba" Cewar gwaggo tana nai man tashi."ai hak'uri za ki yi gwaggo ta inda aka hau ta nan ake sauka dan haka dole da ke zamu ayi ma mahaifiyar yarinyar nan bayani" Gwaggo ba dan ta so ba sai dan ba ta da yarda zata yi.Haka suka d'unguma a motar hajiya Rahina suka nufi sabon yalwa gidan su Na'ima. Na'ima kuka ka wai take yi dan ita kanta batasan da idanun da zata kalli mahaifiyarta ba, Na'ima na cikin tunane-tuna nanta sai dai ta ji hajiya Rahina na cewa "mu je ko Na'ima, sannan ki goge hawayan nan na ki" Mahaifiyar Na'ima na d'aura ma yaro manja da yake itace sana'arta yanzu tun jalin da mijin hajiya Rahina ya bata ta saro manja da su kuma alhamdullilah sana'ar ta amsheta, dan tana ciniki sosai kuma da ita suke ci da sha da k'annan Na'ima.Mahaifiyar Na'ima da fara'arta ta shimfid'a ma su gwaggo tabarmar Na'ima ta kalla ta k'ara kallo ta ce"gwoggo wa na ke gani kamar Na'imata? "Ita ce Mariya ba gizo ta ke miki ba ita ce wallahi" Cewar gwaggo. Na'ima rugume Mahaifiyarta tayi tana kuka, Allah sarki ita ma mahaifiyar Na'ima kukan ta ke, saida suka gaji suka yi shiru dan kansu ba wanda ya hanasu daga gwaggo har hajiya Rahina, ita mahaifiyar Na'ima sun san na murnar dawowar 'yarta ce, ita ko Na'ima sun san kan zancan kukan na ta. Mahaifiyar Na'ima zaunar da Na'ima ta yi ita ma ta zauna tana mai cewa"Ku yi hak'uri hajiya ban baku ruwa ba mun tasaku gaba muna muku kuka" Murmushi hajiya Rahina ta yi ta ce"Wallahi hajiya banga laifinki ba"Mahaifiyar Na'ima tashi tayi tasamu yaro awaje ta ba shi kud'i ya siyo musu pure water. Bayan angaisane ansake gaisawa hajiya Rahina ta kalli mahaifiyar Na'ima ta ce"Maman Na'ima kin ga ikon Allah ko ya dawo mi ki da Na'ima alokacin da kin riga kin hak'ura da ita, haka ake so duk abin da yasamu bawa yayi hak'uri ya fawwala ma Allah, Allah na san bawansa mai yadda da k'adddara ko wata iri ce shi ne cikakkan musulmi. Kin ga da ki ka bar ma Allah ko mai duk da dai mun zaci Na'im ta mutu ne sai Allah yadawo da ita alokacin da ba muyi zato ba ,ashe Na'ima ba mutuwa ta yi ba duk da tace Wanda yatsince ta bai fad'a mata yadda akai ya tsinceta ba, tom Na'ima gatanan dai agabanki bata mutu ba, wani bawan Allah ne yatsinceta yakaita gidan shi yaci ga ba da riketa har izuwa lokacin da Allah yanufa ya biyamata kud'in jirgi ta dawo garemu.Maman Na'ima kin san duk indai namiji da mace suka kad'aita shaid'an ne yake zama cikon na ukun su, tom Cikin k'adddarorin da Allah ya rubuta mi ki ke da Na'ima gashi nan Allah nata nuna mi ki su d'aya bayan d'aya dan ko auran Na'ima da gali kin san k'adddara ne amma sai kuka nuna bazaku amshesa ba, tom haka Allah ke ikonsa da Na'ima ta nuna bazata amshi k'addarar auran gali ba sai Allah ya musanya mata da ciki yaga ita zata amshe ta Ko ko itama zata butulce mai ne.Maman Na'ima atak'aice dai ina so ince mi ki yarinyarki Na'ima na d'auke da ciki"Wata uwar k'ara Mahaifiyar Na'ima ta yi wadda saida ta rud'a su hajiya Rahina, balle kuma uwa uba Na'ima, dan ita take ta fasa kuka. Mahaifiyar Na'ima ta shi tayi ta shi ga d'akinta da gudu kamar sabuwar mahaukaciya ta d'akko tab'arya tayo kan Na'ima da ita da sauri hajiya Rahina su ka rirrik'e Mahaifiyar Na'ima.Mahaifiyar Na'ima kuma cikin b'acin rai ta ce "Hajiya ki sake ni ina jin kunyarki!"Ki yi hak'uri maman Na'ima na san da ciwo ,amma dan Allah ki yi duba da hankalinki kin san wacece Na'ima in ba k'addara ba kin san halin yarinyarki" Ina Mahaifiyar Na'ima bata saurari maganar hajiya Rahina ba,sai dai duk yadda mahaifiyar Na'ima ta so sub'arta ta bugu Na'ima abin yaci turo, ganin baza su saketa ba ya sa Mahaifiyar Na'ima cikin b'acin rai ta ce" Hajiya k'un k'i saki na ko? Tom shikenan gaku ga Na'ima nan dan Wallahi Na'ima sai saidai tasan inda zata zauna ba dai gidan nan ba, kuma in dai ni ce mahaifiyar Na'ima tom na cireta aciki 'ya'yana da nahaifa bani babu Na'ima,ki fita in bar ganinki wallahi kafin in mi ki baki, dama abin da ki ke son yi kenan shi yasa kika ce kar afad'a min zaki tafi ,Shikenan ki fitarnin agida na ce ko!, hajiya dan Allah ku fita baki d'aya ku fita bana son ganinku dukkanku abin da ku kai min Allah ya sa kamin kun had'a kai kun kai min yarinya ammata ciki dole za ku zo ku yi min dad'in baki ku fita dan Allah !!" Cikin wata irin razananniyar tsawa Mahaifiyar Na'ima tai maganar. Allah sarki Na'ima ko ta had'a kai da gwiywa sai kuka take, Hajiya Rahina jawo hannun Na'ima tayi tasa ta mota ta shiga suka tafi. har suka je gida Na'ima batayi shiru ba. Bayan sun shiga falon hajiya Rahina ne sun zazzauna, gwaggo ta ce"Hajiya yanzu ya za ai da Na'ima da cikin jikin ta? "Tom Na'ima dai sanadiyata wannan k'addarar ta fad'a mata ,dan haka za ta ciga ba da zama wajena, ciki kuma k'addararta ce dan haka zata raini abin ta"Wayyo ni dan Allah ku tai ma ka min azubar k'il in aka zubar ita ma mamana tayi hak'uri dan Allah ku tai ma ka min " Allah sarki da yake hajiya Rahina macece mai tsananin tausai jawo Na'ima tayi ajikinta ta ce"ki yi hak'uri Na'ima zubba ciki laifine babba, shi musulmi ana so duk k'adddarar da tasamai ya amsheta hannu bibbiyu ya gode ma Allah, sai ki ga Allah ya kawo mai mafita cikin sauk'i sabo da Wanda Allah ya nufa da alkairinsa shi ne yake jarabta, in ma yaran ne ko yarinyar in ki ka haifa ni nayi alk'awari zan rik'eta" Nan dai hajiya Rahina tai ta lallashin Na'ima, dak'ar Na'ima tayi shiru sannan hajiya Rahina ta kawo ma Na'ima abinci, Na'ima k'in ci ta yi hajiya Rahina matsama Na'ima tayi akan dole taci abinci,Na'ima cikin kuka ta ce " bana iya cin komai sai tea " Tea d'in Hajiya Rahina ta had'o ma Na'ima mai kaurin gaske, nan dai suka yi sallama da gwaggo bayan taci abinci ta tafi. Duk wata kulawa da ake ba mai ciki hajiya Rahina ta na ba Na'ima ita, game da mahaifiyar Na'ima ko hajiya Rahina tace ma Na'ima tambari sai ta haihu sunje su sa ke samunta dan har yanzu tana cikin takaicin cikin. BAYAN WATA TAKWAS: Cikin Na'ima har yafito dan a lissafin su koda yaushe Na'ima za ta iya haihuwa. Yau Na'ima ta ta shi da wani irin ciwan mara, Allah yasa hajiya Rahina ta na gidan, amma kuma tana ta shirin zuwa airport d'auko d'anta da ya gama karatu dan yama kirata suna gaf da sauka, zata tafi kenan d'akko shi ta shiga tai ma Na'ima sallama ta isketa cikin halin da ta ke ciki. Hajiya Rahina cikin rud'ewa ta shiga d'akin tana kamo Na'ima tana mata sannu,waya hajiya Rahina ta d'akko zata kira wata likita sai dai ganin yadda Na'ima ta zama lokaci guda yasa hajiya Rahina ta kasa kiran. Cikin kin ikon Allah da taimakon hajiya Rahina Na'ima ta haihu,dai dai lokacin ne kuna yaron hajiya Rahina ya shigo gidan yana mamakin jin kukan jinjiri agidan nasu, har zai shiga d'akin da ya ke jin kukan sai kuma yafasa ya zauna falon ya na jiran fitowar mommyn shi. Gajiya yayi da zama ya tashi ya shiga ciki ya watsa ruwa ya sakko k'asa samama kan shi abin da zai ci, karo su ka yi da hajiya Rahina da cup cike da tea ahannunta ,hajiya Rahina rik'e baki tayi ta ce"Kai-kai son afuwa Allah saura kad'an in manta da kai" mommy lafiya dai ko? Ina kuma ki ka samo b'aki ? Dan naji kukan jariri ina shigowa" "kai dai ka bari in mik'a mata tea d'in nan inzo in baka abinci da labari"Tom hajiyata afito lafiya"Hajiya Rahina tea ta ba Na'ima ta ce " yi ma za ki sha yanzu nan yarona ya dawo" murmushin K'arfin hali Na'ima ta yi dan bata jin dad'in jikinta gabad'aya. Hajiya Rahina falon ta dawo ta ce"Ayyah my son fushi bai ma kyau ba,gara kayi murmushinka ya fi ma kyau" Haba mommy tun d'azu nazo ba ta ni ki ke ba ta wata can ki ke wadda ban san ina ki ka samota ba"Dariya hajiya Rahina ta yi ta ce"ina yarinyar nan dana ta b'a baka labari wadda aka je d'akko mun kaya da ita lokacin da Jirgin kayanmu yayi accident na ce maka ta mutu?" Eh na tuna mommy"Tom wallahi ashe ba ta mutu ba wanda ya tsince ta ne kuma yayi mata ciki kasan mutane, mahaifiyar yarinyar kuma tace bazata rike ta ba shi ne fa ni na ke rik'onta,,,," kukan babyn da Hajiya Rahina tajine ta ce"ka ji ko yarinyar na kuka ina zuwa na bar mai haihuwa ita kad'ai"Hajiya Rahina ko da ta shiga Na'ima na gefe d'aya rik'e da mara saimalele kuwa take babyn kuma sai kuka take, Hajiya Rahina batabi ta babyn ba ruwa mai sanyi tasamo ta yayyanka allbasa taba Na'ima tace taci zai mata sauk'in ciwan marar, ganin tarasa yadda zatayi dasu ga Na'ima sai malele kuwa take tak'i shan maganin ga kuma babyn itama sai kuka take, babyn hajiya Rahina ta d'auka ta fita da ita ta ce"son dan Allah jijjiga min yarinyar nan inji da uwarta" Amsar yarinyar yayi yana jijjigawa, ita kuma ta koma ta d'au maganin da kanta ta ba Na'ima abaki . Shi ko sai jijjiga yake ita ko baby ta dake sai kukanta ta ke. Hajiya Rahina jin yarinyar tak'i shiru ganin ciwan Na'imar ya lafa ta ce "Son kawo min ita" Da sallamar shi ya shi ga sai dai kasa idasa salkamar yayi yana nuna Na'ima itama Na'ima ba ta san san da ta ta shi ba daga kwancan da take tace "Hafizzzzz kai ne?"Wanda Na'ima ta Kira da Hafiz shi ma cikin mamaki ya nuna Na'ima ya ce "Aunty Amarya ke ce!?" Hajiya Rahina kallan su ta ke yi ganin irin kallan da su kema juna na sani, gabantane yafad'i kardai ace Hafiz shi ya yi ma Na'ima ciki tunowar da tayi Hafiz ba a England ya ke karatu ba yasa hankalinta yad'an kwanta,ta kalli Hafiz ta ce "Hafiz kasan Na'ima ne dama?" Mommy matar brother Abdurrahim ce,,,,,,,,, ABDURRAHIM MATUK'IN JIRGIN RUWA NE daga nan free pages ya k'are 'yaruwa ki na buk'ar ci ga ba ? Dan samun ci gaban Abdurrahim matuk'in jirgin ruwa ne cikin sauki za ki transfer ta account d'in nan Account number 2111619333 Account name Fadila Sani Bank name zenith Bank za ki yi transfer 500 Kacal ko katin MTN number 08063830828 idan kuma biyu ki ke so ABDURRAHIM MATUK'IN JIRGIN RUWA NE da MEENALLYN DADDY za ki transfer 900 only 👌🏻 ko katin MTN ta number nan 08063830828 Dan nai man k'arin bayani za ki iya magana da marubuciyar kai tsaye ta number nan 08063830828 . Dan Allah idan ba siye za ki ba kar mu b'ata ma juna lokaci🙏🏻🙏🏻🙏🏻