🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 _ABDUL JALAL (2020)_ _Story and written by_ AISHA HUMAIRA (daddy's girl) PART 2 _PAGE 1️⃣/54_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki, da suka bibiyeni a littafi na farko, Alhamdilillah yanzuma gani na dawo domin kawo muku kashi na biyu, nagode da kulawarku, ku biyoni domin jin yadda zata kaya a cikin wannan littafi naku me farin jini. Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Gmail @ www.humaira17@gmail.com Facebook @ real humaira _MY FIRST NOVEL _ Jeje bude baki yayi yana kallon Hannah, dan yarasa meze ce mata, Hannah takuma kallon Jeje, ta nunashi da key din motarta "wannan itace magana ta karshe dazanyi da kai, nidaku dan halak ka fasa, kome zefaru sena mallaki Jalal, indai na amsa sunana Hannah" daga nan ta dauki Jakarta tai gaba abunta. Dukan tabur jeje yayi da karfi, yasa kafa yai ball da tebur din "Why, ya haka ya za a yi abubuwa su lalacemin haka, akwai matsala muddin Hannah tace zata aikata abunda ta fada. Mukullin tasa motar ya dauka shima ya bar gurin. Jalal yana gama cin Abincin sa ya mike yana hutawa, anata kiransa ana masa bangajiya, wayarsa yadakko, IG yashiga yana shiga yaci karo da hotunan birthday dinsa, abunda ya bashi mamaki, hotunan shida Jalila yafi yawa, shi akafi yadawa, fitowa yayi yakoma what's app still status din mutane hotunan ne suke yawo, shiru yayi ya kurawa hotunan ido, wani hotonsu ya tsaya akai yana kallo, yanda ta dan zumbura baki tana kallonsa, shikuma yana dariya, tsaki yayi "kalleta dan Allah se tsabar iya rashin kunya, shi mamaki yake yadda akayi tai mugun rainashi sam bata shakkarsa, kaman ba yarinyar dasuka dinga wasa da ita a zanin goyo ba, yan uwan sa mazama tsoronsa sukeji amma banda wannaan yarinyar, zuwa wani dan lokaci ya kashe wayar, ze ajiye kiran Jeje ya shigo wayarsa, kaman kar ya daga, seda ta kusa katsewa sannan ya daga "hey man kana inane?" "me zakayi min kake nemana?" "ina wajene ina jiranka" "wajen ina kenan?" "kofar gidanku mana" "ok ina zuwa" Jalal ya duba yaga Jawwad yana toilet dan haka kawai ya fito, yana fita yaga motar Jeje a kofar gidansu, karasawa yayi ya tsaya bece komai ba, jeje ya fito yana wata shu'umar dariya da wannan katuwar muryartasa yace "man of the day, our celebrity yane?" "Normal, mukarasa cikin gida" Jalal ya fada a takaice, yaiwa Jeje jagora zuwa part dinsa, suna zuwa Jeje yanemi guri ya zauna, Jalal yaje fridge ya dakko wa Jeje ruwa da lemo, ya hada da giya ya aje masa, Jeje ya dan kalli Jalal yace "J man, ya gajiyar jiya" "gajiya tabi lafiya" "good wai ya akayi ka bar gurin nan jiya, ban san ka tafi ba?" Jalal ya danyi shiru yana tunani sannan yace "gaskiya i can't recall, Hannah tabani wayne jiya, bansan meyakuma faruwa ba, ban san ya akayi na dawo gidaba, na tambayi Jawwad ma yace min ba shi yakawoni gida ba, i think ansamun wani abu a giyar nan. Dan zare ido Jeje yayi, dayaji statement din Jalal na karshe amma ya maze yace "anyway but J man, akwai wata cute baby da pictures dinku suke yawo social media, tagama haduwa babyn nan, nifa tayimin wallahi, inaso insata a harka" "wace yarinya kenan?" Jalal ya tambayeshi a takaice, Jeje ya zaro wayarsa ya nunawa Jalal hoton Jalila, tareda fadin "wallahi Jalal komai yaji ajikin yarinyar nan, zanso tayi joining insata a layi, zata kawo harka, maganar tama kawai abar sha'awa ce komai nata na birgewa ne, gaskiya ta hadu" Wani mugun hade rai Jalal yayi, ya kalli Jeje a fusace yace "Are you out of your sense, wai kai bunsurun inane da duk inda kaga mace jikinka har rawa yake, let me warn you, Wallahi3 na rantse maka, muddin wani abu yasameta sena daureka, kasan wacece? Kanwar Jawwad ce, yarinyar da yakeso, danme zaka dinga wannan kazamin maganar akanta, karka kuma fadin wani magana akanta kota arziki kota sharri akanta, wannan yarinyar ba irin jakan matan dazaka iya nasarar lalatawa bane, kaji na gaya maka take your leave now "ya nunawa Jeje hanyar fita, wani irin kallo Jeje yaiwa Jalal, amma seya daidaita nutsuwarsa yace" is ok j man bansan abunda ke tsakaninku bane, ashe kanwar kace, na dena bazan kuma ba kayi hakuri " " Naji amma for now tashi kabani guri, raina yagama baci, tashi ka tafi" ba musu jeje ya mike ya fita. Da Jawwad yafito yaga Jalal ya tafi, kawai se shima yafito, yaga Jalila cikin flours dinta tana gyarawa, ya fuskanci tanason furanni, a hankali ya karasa inda take ya zauna, ta waigo ta kalleshi, tai murmushi "Allah yatemaki yayana na kaina" Jawwad yai murmushi yace "Ameen yar baby, ya meyasa kikeson furanni ne?" "nima ban saniba, kawai dai ina sonsu ne, na gidanmu a kaduna nasan sunyi missing dina, in bana nan ummi ke kularmun dasu" sekuma tai shiru idonta yacika da kwalla, Jawwad ya nisa sannan yace "am sorry, nagane kidena damuwa kinji kicigaba da addu a muna kan nemanta har yanzu" gyada masa kai tayi tareda murmushi, yace "Yawwa babyn Yayanta" yasa hannu a aljihunsa ya dakko chocolate yabata, hannu tasa ta karba tana murmushi, tareda kokarin maida hawayenta, tai murmushi tace "Nagode Ustaz" "yaukuma nine ustaz" "Eh mana" sukayi dariya gaba daya, Jawwad yace "yawwa baby, nace wai me yafarune jiya? Ya akayi manu ya kawo Jalal gida, dazu yake tambayata ya akayi ya dawo gida" Jalila tai ajiyar zuciya tace "Hannah ce ta kaishi wani guri suka bashi wani abu, naga yafita hayyacinsa, tasaka wani yaimata gadinsa ta tafi tana waya, kawai naji ban yadda da itaba, shine na dauke hankalin wanda tasa gadinsa nasa Manu ya daukeshi ya kaishi gida" shiru Jawwad yai na dan lokaci sannan yace "thank you for your contribution my dear, hakika kintemake shi, maybe akwai abunda sukeson yi masa, narasa meyasa Jalal yakasa gane basa kaunarsa, anyway mungode sosai Baby Amma ya akayi kikasan Hannah"? "A a, ban santa ba agurin naji ana fadar sunanta, Yaya Jawwad no need kaimin godiya fa, manta kawai, amma akwai wani abu da nagani yabani mamaki" "Mekika gani?" "Wannan mutumin na rannan, da ya dinga zagin Jalal, dan kun gaisa da dansa, shima fa yaje gurin nan, abunda yakara bani mamaki shida wannan Jejen naga suna magana, shiyasa nace maka shima yana kama da yan shaye2" "Anya kuwa shi kika gani, maybe kamace kawai, bana zaton baban Faruk a irin wannan gurin, saboda yanada tsatstsauran ra'ayi, kece dai kike masa kallon ba mutumin kirki ba " "Yaya kenan shikenan tunda baka yadda ba, magariba tayi bari inje inyi salla" "to shikenan, dan Allah anjima ki dafo mana wannan tea din naki me dadi" "Hmmm yayana kwadayayye kawai" "ke kika koyamin kwadayin ai" tai murmushi ta mike ta tafi cikin gida, Jawwad kuma ya fita masallaci. Tunda Jeje yafita yake zancen zuci "lallai tunda Jalal yaketa masifa akan yarinyar nan to ba karamin matsayi take dashi a gurinsu ba, lallai dama tazomin akan wannan fitsararriyar yarinyar zan jefi tsuntsu biyu da dutse daya" Jeje ya kyalkyale da dariya, sekuma ya hade rai daya tuno da maganganun Hannah, dakuma abunda Jalila ta gaya masa ranar birthday din Jalal, "muje zuwa yan mata mu daku zanga wazeyi nasara" Bayan sallar isha'i Jawwad yasa Jalal a gaba yayi salla suka zauna suna hira, Jalal yace "Jawwad ina jin bacci, bari in tafi gida" "No karka tafi yanzu ka tsaya baby zata kawo mana tea, ka tsaya kasha seka tafi" "ok bari in jira, ina son sha, kasan wani abu" Jawwad yace "A a seka fada" "har yanzu ina mamakin me aka zubamin a giya wanda ya bugar dani haka tsawon lokaci" Jawwad yai ajiyar zuciya "Jalal shiyasa nake gaya maka tun ba yauba, hulda da mutane irin wannan be kamata ba, kasan wani abu? Jalila ce tasa aka dawo da kai gida, tunda kafita daga gurin nan, ni bansan meyafaru ba, bayan ka bugu tasa manu ya daukeka yakawoka gida" kallon Jawwad ya danyi, ya dan tabe baki irin he don't care din nan, wayar Jawwad tafara ringing, ya kalli Jalal yace masa "excuse me please" ya daga wayar "Hello My Jawwad ya kake?" Muryar Hanan ce, Jalal ya kafe Jawwad da ido, Jawwad yace "ina lafiya Hanan, ya mutan gidan" "Nifa fushi nake, ashe Jalal yayi birthday bako gayyata ko my Jawwad" "A a Hanan ba haka bane, Jalila ce ta gayamiki ko?" "A a, wannan ce zata gayamin, bata gayamin ba, hotuna nagani suna yawo a social media, kunyi kyau bama hotonta da Jalal, best couples of the year, kyanta ace wedding pictures ne" Ba Jawwad ba hatta Jalal dayake gefe yana jinsu seda gabansa ya fadi, amma yarinyar nan ta cuceshi, tarasa dawa zata hadashi se wannan fitsararriyar yarinyar Allah ya kiyaye, Hanan tace "My Jawwad ya kayi shiru ne" "bakomai Hanan, ni banga hotuna nan ba" "bari in turomaka, zaka gani sunyi kyau, idan birthday na yazo, irinsu zamuyi" Jalal yawani hade rai, Jawwad ya kashe wayar, ya dafe kai "wallahi wannan yarinyar tafi Jalila rigima" Jalal ya dan kalleshi, wa din? Kafadi son ranka dai" "ba son rai bane Jalal, hanan tafi baby rigima, banason Jalila ta gane, zataji ba dadi" dariya Jalal yayi "ganewa ta nawa sedai kar akuma, ai gara Hanan din akan wannan fitsararriyar, gara ta gane din" wani irin kallo Jawwad yai masa, ya cigaba da latsa wayarsa, hotunan da Hanan ta turo masa yake gani, wanda mafi yawa Jalila ce a jiki da Jalal, nan take yaji wani abu yazo ya tsaya masa a rai, Hanan ta turomasa "ya ka gansu, sunyi kyau sosai, sun kuma dace da juna" da sauri Jawwad ya rufe data, ya kashe wayar gaba daya yayi shiru, shikuma Jalal ya nuna ko a jikinsa, kuma yasan shima Jawwad din kishi yake, dan yasan zeji ba dadi, Jalal yai kaman besan wasu hotuna bane, ba a dadeba sega baby Jalila ta kawo musu tea, amma taga Jawwad wani iri, kaman yana cikin damuwa, ta dan kura masa ido tace "Yaya lafiya dai, yanaganka a haka, kowane abu ne yafaru" girgiza mata kai yayi "Bakomai Jalila" gyda kai tayi, ta tashi ta tafi, Jalal ya zauna ya sha tea dinsa yayinda wanda aka hada tea din dominsa yakasa sha. Bayan Jalal yagama, ya mike abunsa ya tafi gida. Daren ranar da kyar Jawwad yayi bacci, yana matukar son Jalila, meyasa hanan takeson rikita komai ne tana kokarin hada Jalila da Jalal itakuma ta maye gurbin Jalila, sam hakan ba me yuwuwa bane haka ya kwana wannan tunanin. Bangaren Jalila kuma, ta takura kwakwalwarta gun tunanin meye alakar, baban faruk da Jeje, idan har shi yana hulda da mutumin banza kaman Jeje, to mezesa yayiwa Jalal wannan muguwar tsanar haka? Waima yanzu a gurin wa zataji waye Jalal, waze gayamata tarihinsa, Jawwad sam yaki gayamata,sannan meye burin Ilham akansa, meyasa hanna ta bugar dashi haka ranar birthday dinsa? Tarasa me bata amsar wannan tulin tambayoyin, ji tayi kanta yana neman yafara ciwo, dan haka ta hakura da tunanin tayi bacci. Ya zuba mata ido yana ta kallonta tana shiryawa a gaban mudubi, dan waigowa tayi, ta kalleshi tai masa murmushi "ka dena kallona" "ta yaya zan iya dena kallon ki, kowa yana son abu me kyau, ni kekadaice abu me kyan da idanuna ke iya gani, kinga babu batun dena kallonki" murmushi takumayi masa "hmmm my cwt kenan, to nagama yi maka kwalliyar zo ka daukeni" ba musu ya mike yazo gaban mirror ya tsaya ta miko masa hannu, ya dauketa kaman wata yar baby, ta makalkaleshi tana dariya, ya nufi kan gado da ita, yayinda take kallonsa tana murmushi. A hankali JALAL ya bude idonsa, yana kallon dakinsa, idonsa ya sauka akan agogo, karfe takwas dai2, se yanzu yagane mafarki yake, wani dogon tsaki yayi, ya tashi zaune "wannan wace irin masifa ce, shikenan kullum babu mafarkin wadda zeyi se wannan yarinyar, shi a yanayin dayake ganinsu ne shida ita yake bashi haushi" tsaki Jalal ya kumayi ya sakko daga kan gadon ya tafi toilet, domin yin wanka yai salla " Karfe tara da rabi, Jalila tana ajinsu, an fara lectures, amma sam hankalinta baya kan malamin, tayi zurfi a cikin tunanin ta, gata a aji amma hankalinta yayi wani gurin, lecturer ya kalleta, cikin tsawa yace mata" Ke! Tunanin me kike haka ina lectures " a hankali ta dago ido ta kalleshi, ta maida idonta kasa, ba tareda tace masa uffan ba," ni kikewa wannan kallon ina miki magana, tashi tsaye, seda taja wasu seconds sannan ta mike, "bayanin me nagamayi yanzu?" ta daga ido, suka kalli juna itada malamin, ta dauke kanta tai masa shiru "wai ba magana nake miki ba" still dai shirun takumayi "ok get out from my class" ba musu balle bada hakuri ta dau jakarta, da wayarta ta nufi hanyar fita wasu suna kibashi hakuri, banza tayi musu, malamin yacigaba da mita "irin wannan sune jakan aji, irinsu ke kwasar carry over, se tsabar iskanci waisu yaran masu kudi" "tunda ka koreni kuma gashi na fita kacigaba da yimusu lectures din mana karka shiga lokacin su" tsit ajin yayi ana kallonta, tai ficewarta abunta" mamaki ne yacika daliban, dama tana magana haka, amma Allah yayi mata baiwar murya me dadi, sedai ana tsoron lecturer saboda masifaffe ne, da kyar in bata jawa kanta carry over ba a gurinsa, dan masifaffe ne gashi baya uzuri, yan ajin suka fara gulma, ji yadda take magana da izza, lallai wannan muguwar yar rainin hankali ce, itakam tana fita tasamu guri ta zauna ta cigaba da tunaninta Siyama ce tafado mata a rai, kwana biyu basuyi waya ba, dan haka ta dakko wayarta ta kirata, bugu biyu Siyama ta dauka "hajiya Jalila manyan kasa talaka najinku dama" Jalila tai murmushi "ke banason wulakanci fa, yakike yasu umma?" "duk muna lpy Alhamdilillah, yauba lectures ne naga kin kirani yanzu" "akwai lectures koroni akayi" Siyama tace "hali zanen dutse, har yanzu biki canza ba ko? To university ba secondary school bace, ko islamiyya, Allah sarki malam babba yanata tambayata ke" "Allah sarki malam, kice masa ina lafiya, ke ba ruwana da wata university, wani hakuri zan bashi ya riga ya koreni, hada wani wai irinmu ne dakikai" "hnm adinga hakuri dai sisy, nace ya mutuminki kuwa? " waye mutumina kuma? " " Jalal mana" siyama tabata amsa Tsaki Jalila tayi "ta yaya yazama mutumina?" "knfi kowa sani, nace yafara shiryuwa kuwa? " "tab shiriya se ta Allah, dan banga alamaba, abun se addu a, niba wannan ba ma kinsan wani abu" "a a sekin fada" "Siyama hanan ce takeson Yaya Jawwad dina, kuma fa da gaske take" "to meye a ciki, ai abun farincikine" "haba Siyama ya kike fadin haka, da wanine ba yaya Jawwad ba, se in hakura in barmata, amman kaman baki san abunda ke tsakanina da yaya Jawwad ba" "da kenan abunda ke tsakaninki da Yaya Jawwad, amma yanzu naga kin canza sheka zuwa Jalal" "mtseww, kinfiye wasa Siyama, wannan bugaggen uban me zanyi dashi" "karki rainamin hankali mana, in bahakaba me yakaiki gurin birthday dinsa kukayi hotuna, hada kallon soyayya" zare ido Jalila tayi "nidin, nasan naje gurin birthday dinsa, amma wani irin kallon soyayya" siyama tai dariya tace "kai Jalila ansan madarar gogewa mutane hadda, to a status din mutane na ganku" lecturer da yakori Jalila ne ya taho, da wasu dalibai su hudu suna binsa, Jalila tace "hmm ke se anjima, zamuyi waya" ta kashe wayarta, lecturer yazo saitin Jalila ya tsaya ya kalli daliban "kun ganiko, na koreta daga aji, memakon tabani hakuri tazo nan tayi zamanta tana waya da samari, se karshen semester yazo tasamu carry over ace bani da mutunci" ita dai shiru tayi masa, yagama masifarsa yai gaba, wani daga cikin daliban ya dawo da baya yace" yan mata meyasa baki bashi hakuri ba ai ba a haka tunda gaba yake dake seki lallaba a rabu lafiya " "akan me zan bashi hakuri, yayi kama da wanda za abawa hakuri ya hakura ne? Kuma fa dagani hakurin kuke bashi kowata alfarma kuke nema a gurinsa amma ga yadda yake wani shareku" "eh to kinsan Jami' a se hakuri, kowane lecturer da irinsa, kuma ko dan kar ya kadake, ai da kin bashi hakuri " Jalila ta kalleshi tace " Yaya na nagode da shawararka amma bazan bashi hakuri ba, kuma koda ban taba zama a lectures dinsa ba banida test banida assignment indai zan shiga exams dinsa sena ci" tana gama fadin haka ta mike, tai tafiyarta. Ji tayi yau makarantar ta isheta dan haka ta kira manu, tace yazo ya maida ita gida , befi minti shabiyar ba sega manu yazo, ya dauketa don tafiya gida, Jalila tace "Manu wai yana ganka haka, kaman mara lafiya" manu yace "ke dai bari Mamace ba lafiya an rubuta mata maganin dubu hudu, kuma ni bani dako sisi, gashi ba adade da biyana albashi ba" "Allah sarki amma meyasa baka tambayi Abba ba"? "haba Jalila, idan na tambayeshi ai ban kyauta ba, kullum cinkin yimin hidima yake, sedai inkina dashi ki aramin" "Bakomai akwai kudi a account dina muje banki, se mu tsaya in ciro in baka" "kai godiya nake uwar dakina, Allah yasa kifi haka, Allah yabaki miji nagari, ya jikan magabata, Allah ya... " Ameen nagode, godiyar ta isa haka, yi sauri muje"suna zuwa banki Jalila ta sauka ba layi sosai, dan haka bata wani dade ba ta ciro kudin ta nufo hanyar fita taji ana fadin " Yan mata adon gari, in baku babu gari, inkunyi yawa gari ya baci, amma kyawawa irinki dazasu cika garin nan, dayakara kawatuwa, barka da wannan lokaci" daga kai tai ta kall i me maganar, koda tai tozali dame maganar, take gabanta ya fadi. More Comments More typing............................. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE 2️⃣/ 55_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki, da suka bibiyeni a littafi na farko, Alhamdilillah yanzuma gani na dawo domin kawo muku kashi na biyu, nagode da kulawarku, ku biyoni domin jin yadda zata kaya a cikin wannan littafi naku me farin jini. Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Gmail @ www.humaira17@gmail.com Facebook @ real humaira Follow the group of ABDUL JALAL NOVEL FANS through this link 👇 https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL Follow me on watpad @Ayshercool7724               _MY FIRST NOVEL _ A hankali ta daga idonta, tasa a cikin nasa bata manta fuskarba dukda gani biyu ta taba yimasa, baban faruk ne, bako shakka shine, wani shu'umin murmushi yayi mata irin nasu na yan duniya "ko baki gane ni bane"? wani kallon rainin hankali tayi masa" sannan tace "dukda kasancewar kwakwalwata tana rike, tareda tuno abubuwa masu mahimmanci da suka shafeni ne, amma hakan besa na manta wannan fuskar ba" "Kenan nima inada mahimmanci a gurinki tunda har kika tunoni? " "sosai makuwa kanada mahimmanci, shiyasa na iya tunaka" wani murmushi ya kumayi "Amma naji dadin zama daya daga cikin masu mahimmanci a gurin wannan kyakyawar halittar, amma meyasa nazama me mahimmanci a gurinki" Jalila a zuciyarta tace saboda ka shigo cikin suspect dina amma a zahiri tace "saboda kasancewar ka uba nagari, me kokarin kare mutuncin dansa daga hulda da mutanen dabana kwarai ba" "kinji haushin abunda nayiwa Jalal kenan, amma inkika duba ya cancanci hakan, duba da yanayin wani irin mutum neshi" Jalila ta dan kuramasa ido, kai da ganin mutumin nan kaga rikakken dan duniya, tsabar iya barikine yasashi yake acting kaman mutumin kirki, "excuse me please komai nawa a ka'ida nakeyinsa ina da abubuwan yi yanzu se anjima" yai saurin dakatar da ita ta hanyar cewa "yi hakuri dan tsaya mana dan Allah, ina so mudinga haduwa muna gaisawa ne, in bazaki damuba ga complementary card dina seki kirani, dakuma adress dina, mutane na musamman nake bawa wannan adress din" hannu tasa ta karba ta kalli katin ta juyashi, ta dan kalleshi na wasu seconds, tsaf ta haddace lambarsa da adress din jiki, sakin katin tayi a kasa tai masa wani kallo da yakasa gane me take nufi, kawai ta juya tai tafiyarta, tsayawa yayi ya zuba mata ido, "gaskiya wannan yarinyar yar rainin hankali ce, amma kota halin yaya, seya gane wacece din Jalal, kuma se yayi yadda yakeso da ita Itakam tana fitowa ta kalli manu tace " yi hakuri manu na dan dade, muje nagama"ta shiga mota suka tafi, ta dakko kudin tabawa manu tace gashi nan, aiwa maman sannu, kuma ita kyauta ta bashi ba rance ba" manu kaman ya yi kuka dan murna se godiya yake mata. Jalila na zuwa gida, ta tarar gidan ba kowa dan haka ta tafi dakinsu ta haye gado ta sha baccinta, alhalin school ana can ana lectures, se bayan azahar ta tashi, tana tashi da baban faruk ta tashi a ranta, ras take kuma ganin katin daya bata a idonta,  kabiru Idris, shine sunan dayake jikin katin, wayarta ta dakko tayi saving sunansa da lambar sa, da adress din dayabata a jiki, duk tayi saving a wayarta, sannan ta aje wayar a hankali, sannan tace kaima ban yadda da kai ba. Ta tashi ta tafi kitchen ta hado cornflakes dan tana jin yunwa, maimakon ta koma daki seta fito harabar gidan tai zamanta a kujerun harabar gidan, ta gefen Jawwad dayake gurin akwai bishiya, ta zauna tana shan cornflakes dinta, tanayi tana karanta qura'ani a hankali, tana dan kaďa kafarta, Jalal ne ya shigo yazo ya wuce ta gabanta bata kulashi ba be kulata ba, ya wuce part din Jawwad, yana zuwa ya dau laptop dinsa da yabari a dakin ya samu guri ya zauna ya fara video call da daddynsa "My Man ka girma, naga hotuna na birthday kunyi kyau Allah yakaro tsawon rai da lafiya me inganci" "to Ameen amma ni fushi nake da kai" Daddy yai dariya "to menayi?" "Kaje ka makale a England kaki dawowa, bakayi attending birthday na ba" daddy yai murmushi "to ai nace ka daga birthday din indawo kaki, kuma abubuwa sunyimin yawa anan gakuma aikin daka sani, koka manta ne?" "ban manta ba daddy, ina fatan ana samun cigaba" "eh anasamu Alhamdilillah" "to hakan yayi kyau, yaushe zaka dawo?" "ina nan tafe next week Insha Allah" "To dan Allah ka dawo haka, inaso indinga ganinka" daddy ya dan girgiza kai "Allah sarki yarona, karka damu, nace kazo nan mu zauna tare kaki" Jalal cikin damuwa yace "Haba daddy, in taho nan in bar aminina dan uwana, kasan bazan iyaba" "Hakane Jalal, ina Dan nawane, ko yau bakwa tare?" "Yana makaranta" "that's good, Allah ya nunamin ranar da zaka koma makaranta, yanzu ka zama mutum Jalal ina fatan Allah ya shiryamin kai inmaka aure" ya mutsa fuska yayi ya kalli system din "Aure kuma? Habaa daddy yaushe aka haifeni, ni banason gayyatowa kaina matsala, mata matsalane daddy kaima kasani" ya karashe maganar kaman zeyu kuka, "ABDUL JALAL, bakowace mace ce matsala ba, in har kayi dace da samun mace ta gari, kaga hotunan birthday dinka danagani, dana ganka tareda Takwararka abun yamin daďi, senaji dama matarka ce, yarinyar tanada nutsuwa ga tarbiyya " wani mugun hade rai Jalal yayi "What matata kuma, Allah ya kiyaye, wannan kwailar, mara kunyar, na auri wannaan sedai kuzo ku tarar na kakkaryata"      A gigice Ilham ta tashi zaune, ganin hotunan da aka turomata ta what's app, ba tareda tasan waye ya turoba, hotunan dasu Jalila sukayine, a kasa aka rubutamata "Yakika gansu, perfect match, ina musu fatan Alkhairi, da fatan kasancewa tare har abada, wannan itace matar data dace da Jalal bake ba" mikewa tsaye tayi akan gadon, "What ni za ayiwa wannan rashin hankalin, lallai Jalila tayi bal'in rainamin hankali. Ba tunanin komai, taja gyalenta tai waje, Mummy tana yimata magana amma taimata banza, ta fita se gidansu Jawwad, tana zuwa taga mutuniyar tata a hakimce a farfajiyar gidan, kusada part din Jawwad, a inuwa se kada kafa take, tana ciye2 hankali kwance, bazar2 Ilham ta tunkari Jalila taje kanta ta tsaya tana huci, Jalila kam kaman ba kowa a gurin, tacigaba da abunda take. Cikin masifa Ilham tace "Wato gargadin danayi miki bakiji ba ko? Saboda kin rainamin hankali, abunda kukayi keda JALAL a gurin birthday dinsa be isheki ba ko? Hakan be miki ba seda kika hadani da wannan tsinanniyar yarinyar Hannah a gurin nan, Shine duk be miki ba sekin hada da turomin hotunanku, sau nawa ina gaya miki kifita harkata, ina tausayawa rayuwarki idan na tashi hukunta ki" Ita Jalila abun mamaki yake bata wai wace jarabar hotuna na ake damunta haka akai, ba tareda ta kalli Ilham ba tace " tunda kekika halicceni dole ki tausayawa hukuncin dazaki yimin mana, ki kasheni ki huta mana, seki tabattarmin dake kanwar Jalal ce, hakan se ya tabbatar da cewar bashi kadai yake shan giya ba" Takarasa maganar cikin ko in kula, tacigaba da watsa cornflakes dinta a baki, Ilham ta kawo iya wuya, wato Jalila takai karshe gurin raina mata hankali, idonta taf hawaye tace "Wallahi Jalila in baki fita hanyata data Jalal ba, kina daf da fadawa rijiyar sharrina, idan nasakoki gaba ruwa seya gagareki sha, Inakuma yimiki kashedi kinfara kaini bango, idan turn dina yazo bazaki ji dadi ba, ki kiyaye. Jalal ne yake tajin hayaniya, har ya basar ze kwanta seyaji hayaniyar yana kara yawa, dan haka ya yanke shawarar fitowa dan ganin meke faruwa, yana fitowa ya tsaya a kofar part din Jawwad yana kallon dramar da ake. Ilham tacigaba da cewa "waike wace irin mayyace? Mara zuciya, meye hadinki da mune, baki da alaka ta kusa ta nesa damu why do you involve yourself in our family matters, nagaya miki nakuma gaya miki Jalal nawane, wace irin mara zuciya ce ke, kishiga hankalinki harni zaki turawa hotuna, kina kece kika dace da Jalal, zakiga wacece Ilham, na daga miki kafa amma baki ganeba, zakiga me zanyi" Kamshin turaren JALAL Jalila taji, hakan ya tabbatar mata da fitowa yayi, dan haka bata kula Ilham ba ta mike tsaye, ta taka a hankali, cikin takunta na isa, kunsan fa Ummi jinin sarauta ce dan haka akwai abun  a jinin Jalila, taje gaban Jalal ta tsaya, ta kalli Jalal sannan ta kalli Ilham, ta nuna Jalal sannan tace "Wannan shine mara zuciya, mara tarbiyya shiyakamata, kigayawa bakaken maganganu bani Jalila ba, shi duk abunda yake meyasa baki ja kunnensa ba dan kina tsoronsa, kokuwa dan abunda yake ranki wanda kike boyewa, to ni bana tsoron kowa se mahalicci na, aike karamar mara kunya ce, ni idan zanyi sedai aga na aikata, bana fada, idan akabari nafadi abunda zanyi komaj muninsa sena aikata, ke alwashi nawa kika dauka kika kasa cika ko daya, Tunda ABDUL JALAL yashiga rayuwar Yaya Jawwad to a cikin rayuwata yake, shi zaki Jawa kunne ya rabu da Jawwad, in har ya rabu da Jawwad, ba ruwana da shi, bari kiji in gaya miki za ayi dayan biyune ko Jalal ya fita daga rayuwar Jawwad kokuma kudirina....  Sekuma tai murmushi ta kalli Jalal "Kagayawa wannan sokuwar yarinyar, niba abunda zanyi da kai, baka da abunda ze birgeni insoka bana cikin jerin banzayen matan da zasu zubar kimarsu da ajinsu akan namiji mara daraja irinka, wanda besan ciwon kansa ba balle yasan na wani, namijin da besan darajar iyayensa ba, namijin dabaya girmama alaka, dan da kanayi da zuwa yanzu ka tausayawa Jawwad kadena abunda kake, namijin dabe maida sabon Allah komai ba, baya kunyar sabawa mahaliccinsa agaban kowa, shikike tunanin ya cika siffa da kamalar dazan soshi a matsayin uban y'ay'a na, shi kike tunanin zan zubar da kimata ina hayagaga dake akansa "ta nuna Jalal sama da kasa da hannunta " Ilham ki canza tunani, Jalila ba irin sauran matan da kike tunani bane, duk abunda kikaga inayi i have a mission, kawai ina kokarin rama Alkhairi ne da Alkhairi, karki manta da maganar dana yimiki abaya muddin kudirina yaci karo da na wani zan rusa kudirin ko uban waye dan cikar burina" ta waiga ta kalli Jalal, da idonsa tuni yayi ja, gashi ya kasa matsawa daga inda yake kaman an dasa shi, Ilham rasa bakin magana tayi, Jalila ta kalleshi a wulakance, kaikuma ka gayamata ta kiyayeni dan muddin takuma cin mutuncina saboda kai akanka zan rama, har sena gamsar da ita cewa bawata alaka me ma'ana tsakanina da kai" tana gama fadin haka takoma ta dau Cup dinta tai cikin gida ta barsu nan a tsaye. A hankali ya lumshe ido, ya tako a hankali ya nufi hanyar fita, Ilham tai sauri tace "Yaya Jalal dan Allah...  Daga mata hannu yayi alamar baya son jin mezata ce, yai gaba abunsa, maganganun Jalila na cigaba da tafarfasa zuciyar sa. Yana shiga gida ya nufi part dinsa ya samu guri ya zauna ya dafe kai yai shiru, Ilham ta biyo shi tazo ta zauna a kusa dashi, "Dan Allah yay Jalal kayi hakuri, nibani da laifi anan, kawai ina kokarin kare alakar dake tsakanina da kaine, meyasa bazaka yadda dani a in zama wani bangare na rayuwarka ba"? Tashi tsaye yayi ya tafi bedroom dinsa ya kulle kofa ya barta a palour.   Jalila koda ta koma dakinsu, kwanciyarta tayi ta dakko wayarta, tafara chatting, ta bude pages da take advertising kayan da Maama dakuma Mummy Jalal suke siyarwa, tana kawo musu customers sosai, daga gurare daban2, wasu suzo da kansu, wasu kuma a aika musu har garin da suke, gashi Jalila ma tana harkar catering ta iya girke2, wani lokacin ta kanyi snacks ta siyar, gashi duk karshen wata Abba yana basu kudi, wani lokacin dubu Ashirin zuwa talatin, inda me bukata tayi amfani dasu, Jalila bata da wata matsala se na kewar Ummi da har yanzu yake damunta, dan har yanzu takan kulle kanta tayi kuka me isarta, tana naan tanawa Ummi Addu"ar Inda rabo Allah ya kuma hadasu. Chats dinsu da siyama ta bude taga ta turomata hotuna tana dubawa taga hotunanta ne da Jalal, wani dogon tsaki taja yanzu watakila saboda wannan hotunan Ilham tazo kanta tanamata hauka, har zata rufe data dinta taga wani sako ya shigo, tana budewa taga an mata sallama, ta duba profile din taga basuda group in Common dame maganar, amma an rubuta unique zarah, batayi reply ba ta rufe data. Da Nana ta dawo tayi mamakin ganin Jalila a gida, Manu yagaya mata ai tun goma da rabi ya dawo da Jalila gida, Nana ta kalli Jalila "Jalila ya akayi naganki a gida, manu yacemin tun safe kika dawo, kobaki da lafiya ne?" "lafiyata kalau zaman makarantar ne ya isheni, na dawo gida" dan zare ido Nana tayi to lectures dinfa? " " Kinga ki manta kawai" "Bangane in manta ba kefa al amuranki se a hankali" "A a nagaya miki gaskiya to meye na tuhumata" Nana tace "tabdijan, A haka zakiyi karatun sekin gadama zakiyi attending class in kika fadi fa" "Nana kidenamin fatan faduwa, ba abunda zekadani Insha Allah" "to Allah ya yadda amma dai banga ta yadda za aci jarrabawa a haka ba" Jalila ta dan tabe baki tace "ke kika ga haka"   Tunda Ilham takoma gida takewa Mummy kuka, "Mummy dan Allah ki gaggauta auramin Jalal, wallahi zuciyata daf take datayi bindiga in har ban mallakeshi ba, Mummy nagaji da wulakancin Yaya" Mummy ta dafata "Kiyi hakuri mana Ilham kefa macece yakamata kija ajinki, kuma ni namiki alkawarin auren Jalal" "Mummy babu wani batun aji a fagen soyayya, Mummy dan Allah kiyi wani abu" "Haba Ilham wai meye hakane, kibari daddynsa ze dawo next week Insha Allah, in ya dawo semu san yadda za'yi, tashi ki tafi dakinki ki dena wannan kukan" mikewa Ilham tayi ta tafi dakinta, tana zuwa ta rufo kofa, sannan tai kwafa "Mummy kicigaba da jamin rai akan auren danki, koki sabaki ya aureni ko karkiyi sena aureshi, sena cika burin mahaifiya ta, sekin wulakanta kin dandani bakin cikin da uwata tayi, ko zan tafi tsirara bazan bari A banza Jalal ya auri wataba bayan ni, wasan ze fara nakusa kawo karshen wannan dramar, indai na haifu se nasa bakin cikin ABDUL JALAL ya kusa kasheki, sekuma ya aureni dan zan iya halaka duk wadda tai nufin aurensa ko wacece!!!!! Share please More Comments More typing.............................. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE 3️⃣/ 56_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki, da suka bibiyeni a littafi na farko, Alhamdilillah yanzuma gani na dawo domin kawo muku kashi na biyu, nagode da kulawarku, ku biyoni domin jin yadda zata kaya a cikin wannan littafi naku me farin jini. Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Gmail @ www.humaira17@gmail.com Facebook real humaira               _MY FIRST NOVEL _ Daga nan Ilham tai kwafa, ta nufi kan gadonta, tai shiru tana sake2 a ranta. Jalal kwata2 yarasa abunda yake masa dadi, meyasa Jalila tai masa wannan muguwar tsanar haka, bata da burin da yawuce taci mutuncin sa, tabbas maganganun da take gaya masa sun fara isarsa, dole ya hukunta ta hukuncin da suka hadu seta canza hanya, hukuncin da zata dandani abunda yakeji idan taci zarafinsa, gata kanwar kanwarsa, amma ko Ilham dasuke gida ďaya bata isa tayi masa haka ba, jiyayi zuciyarsa na wani irin zafi mussaman idan ya tuna yadda Jalila take kiransa da namiji mara daraja. Dole ya hukunta ta dai2 da abunda tayi masa, Ilham ma ze gamu da ita, duk yadda yaso ya manta abunda tayi masa kasawa yayi, karshe ma yaji zuciyarsa tayi masa wani irin nauyi haka yaita juyi akan gado.   Jawwad kam be dawoba se bayan la'asar ya gaji matuka, dan haka benemi Jalal ba se bayan, sallar magariba, yaje gidansu ya duba dakinsa yaga baya nan ya duba bedroom dinsa se yaji shi a rufe, be kawo komai a ransa ba yakoma gida, yai trying lambar Jalal amma shiru baya dagawa, haka ya hakura ya nemi abunda zesawa cikinsa, dan yasan maybe Jalal ya tafi nasa yawon, amma ya damu da rashin daga wayarsa da Jalal beyiba. Nana tana kwance tana waya da saurayinta, Maama ta shigo dakinsu tace dan Allah in tayi salla taje ta karbo mata laces a wajen Mummy dan in anjima hajiya Jamila zata turo yaranta su karba, dan bata fuska Nana tayi "Maama dan Allah ki aiki Jalila baby ne zezo fa, Maama ta dan bude baki" Lallai Nana, wato saurayinki yafi aikena ko? "" murmushi Jalila tayi tace "Allah ya shiryeki Nana, bari inyi sallar magariba ni se in karbo miki Maama" dan gyada kai Maama tayi ta fice Jalal kam yanajin wayarsa na ringing yai banza dan tunda ya kulle kansa a daki be fito ba, banda jujjuya kalaman Jalila ba abunda yake, ga yunwa yakeji yanzu yana fita Jawwad ya ganshi a haka ze dameshi da tambayoyin me yake damunsa danhaka ya yanke shawarar ya shiga cikin gida yasamu abinda zeci base yaje gurin Jawwad ba. Ya mike daga kan gadon ya fara yin alwala dan sallar asuba kawai yai, gashi yanzu magariba akeyi, yayo alwala yazo yai sallar azahar da isha'i, seyaji ya gaji dan haka ya mike yace yayi magariba da isha'i anjima kokuma gobe da safe, ya bude dakinsa ya fito, cikin gida ya nufa yana shiga palour Mummy suna kallo itada Ilham bebi takansu ba ya nufi kitchen ya zubo Abinci, ya dakko madara ya fito, abun mamaki yabawa Mummy dan kwanan nan yadena cin Abincin su, Mummy ta kalleshi tace "Jalal zo mana" waigowa yai ya kalleta kaman kar yaje kome ya tuna, kawai se yadawo yasamu guri ya zauna a palourn, yafara cin Abincin sa ba tareda yace komai ba, Mummy takuma tattara hankalinta ta kalleshi "yanaga kana cin Abincin mu yau?" Jalal be dago ya kalleta ba yace "Dame gidan yakawo Abincin yace banda nine? Yabata amsa ba tareda ya kalleta ba ajiyar zuciya Mummy tayi " A a ni banceba kokunyi faďa da Jawwad ne? " " No, yau abincin gidan mahaifina nakeson ci" "Hmm hakan yayi kyau dan nima bana jin dadin kauracewa abincin mu dakayi dukda tarin dukiyar mahaifinka amma ace sedai kaci Abinci a wani guri. shi Jalal mamakin yadda taketa lallabashi yakeyi, ya sha madarar sa sannan yace "Serious ashe bakya san hakan, hmm amma kinsan wani lokacin abun hannun Jawwad ya fiyemin abun cikin gidan mahaifina" Mummy tace "kaga ba wannan ba, daddynka ze dawo next week" "munyi waya, yagayamin" yabata amsa a takaice "Yawwa dama sonake in yadawo ayi maganar aurenka, tunda lokaci yayi dayakamata ace daga kai har Jawwad din kunyi aure, aure shine cikar mutum" Bayan Jalila ta idar da sallar magariba ta fito karbowa Maama aikenta, kaitsaye gidansu Jalal ta nufa ta tsaya suka gaisa dame gadinsu sannan ta wuce, tana zuwa ta tura kofar palourn ta jiyo hargagin Jalal yana masifa " wakike tunanin ze auri mutum irina, wakike tunanin yabani 'yarsa, ko sokike in auri wadda zata soni dan dukiyata? Ta aureni dan ta kasheni ta mallaki abunda nake dashi, Wace yar mutuncin ce zata auri ďan da kikayi sanadiyar lalacewarsa da kanki, lalatacce dan giya kamarni Mummy kozanyi aure a rayuwata se wadda zata soni dan Allah badan wani abu nawaba, wadda bazata kyamaci rayuwar da nake ba, meye damuwarki da dole senayi aure, ai aure ba dole bane" Da sauri Mummy ta katseshi ta hanyar cewa "A a Jalal abun duk be kai haka ba, baga Ilham nan ba, itace me sonka tsakani da Allah meze hana ka aureta ai kanwarka ce" wani mugun kallo yayiwa Mummy "Au Ashe kinada wani ďan da kika haifa bayanni ai ban saniba se yanzu" Mummy ta kalleshi cikin rashin fahimta tace "kamar yaya?" "inba wani ďan ne dake bayanni ba ai kinsan ba amin dole ko? Ya kalli Ilham" Ke! A tsorace Ilham ta waigo ta kalleshi "tunda muke na tabacewa ina sonki" shiru tayi ba tace komaiba, ya kalli Mummy cikin masifa da tsawa yafara mata magana "wai dan Allah yaushe zaki fara playing role dinki na uwa, kimin adalci a matsayinki na mahaifiyata, ba kya tunanin in shiryu, se kokarin kuma rusa rayuwata domin wanke laifinki a idon wanda kikayiwa, yakamata ki tausayamin ko sau dayane yakamata ki barni na huta haka, please Mummy ki tausayawa rayuwata haka, a matsayina na tilon danki" karo na farko da Jalila taji ya kira mahaifiyarsa da Mummy, itakam tana son sanin tarihin Jalal da mahaifiyarsa, amma waze gaya mata. Jalal kam yana gama fadin haka ya tashi ya bar palourn ya fito fuuuu kaman guguwa, yana fitowa be kula da Jalila ba a gurin ya wuceta, a hankali tabi bayansa, yana zuwa motarsa ya nufa, yana zuwa ya shiga motarsa yana kokarin kunnata,  seya fasa kunna motar ya jingina da kujera yayi shiruu, gefen motarsa taje ta tsaya tai knocking glass din, a hankali ya sauke glass din motar kawai yai tozali da fuskar Jalila. Kokarin kunna motar yake, saboda yasan in har ya tsaya ze iya illata yarinyar nan, dan yasan yanzunma ci masa mutunci zatayi, hannu tasa ta dafa window din motar saitin Jalal tana kallonsa, tana iya juyo yadda yake numfashi, "ABDUL JALAL kaji tsoron Allah kaji, karka mutu mahaifiyarka tana jin haushinka, kome tayi maka kabata matsayinta na uwa, Annabi salallahu alaihi wassalam se da yafadeta sau uku yace abita sannan yace uba, kaji tsoron Allah kadinga yafiya mana, ka tausaya mata kaimata biyayya, kaji dan gidan daddyn sa, ba daddy kawai keda hakki akanka ba, nasan yanzu mashaya zaka tafi, dan ba kunya ce da kaiba naga baka da alamar zaka dena shan giya, kayi a hankali da duniya, sannan ka kiyayi miyagun abokai, u have to focus, ka kiyayi JeJe da Hannah da sauran miyagun abokanka, basa komai banda rusa maka rayuwa, basa nufinka da alkhairi ka kiyaye, jeka Allah ya shiryeka" manyan idanunsa da suka sauya zuwa launin ja ya zuba mata, cikin idonta ya saka nasa, dukda akwai duhu se hasken fitilu be hanashi ganin fararen idanuwan taba masu kama da tana jin bacci, ji tayi kaman an daureta takasa motsawa tabar gurin, itama ta kura masa ido, ji tayi idonta yayi nauyi, ga Jalal yamata wani irin kwarjini, kamshin turarenta duk yacika masa hanci, daurewa yayi, yai mata wani mugun kallo me wuyar fassara, sannaan ya dauke kansa yace "ki kiyayi haduwata dake, zanyi maganin wannan shishshigin naki, sekinyi dana sanin shigowa rayuwata, zan baki mamaki, bari in tuna miki alkawarin dana taba yimiki, zan maida ke abun kwatance irina, matsa ki bani guri ko in takeki da mota. A hankali ta motsa bakinta, tafara magana a hankali cike da rainin hankali tace "zaka iya ai, inbaka takeni da mota ba ba sunanka ABDUL JALAL ba, ni bazan fasa fadan gaskiya ba, kome za kayimin, Kuma bazan taba zama abun kwatance irinka ba, dama kwatancen kirki ne da sauki, Allah ya tsareni zama abar kwatance kamar dan giya" "Haka kikace?" "baka da kunne ne?" Ajiyar zuciya Jalal yayi, ya kunna motarsa, Jalila ta ja dabaya ya ja motarsa da gudun tsiya, Jalila ta juya zata shiga gidansu Jalal, taga Ilham a tsaye a bakin kofa tana mata wani irin kallo na tuhuma, fuskarta na dauke da tsantsar bacin rai, dakuma tsanar Jalila, dan tana hangen abunda yafaru, tsakanin Jalal da Jalila, a hankali Jalila ta karaso, kota kan Ilham bata biba, ta tureta gefe ta wuce cikin palourn, ta tarar da Mummy a palour ta fada mata sakon da aka aikota, Ilham ta shigo palourn taji zuciyarta tana raya mata taje ta dakko  wuka ta kashe Jalila ta huta, itako Jalila ko kallon Ilham batayi ba, tacigaba da abunda take. Jalal kam kaman yadda Jalila ta fada, mashayar sa ya tafi, amma yana tafe tunani kawai yakeyi, yana ta nazarin mezeyiwa Jalila wanda ze bata mata rai, soyake ya bata mata rai yadda zataji zafi sosai fiye da yadda take masa, manyan mutane ma suna shakkarsa, saboda kwarjinin sa, amma yarinya karama tana caza masa kai, wani abun takaicin jinsa yake duk jikinsa ya mutu, kamshin turarenta kawai yakeji, yai kwafa zeyi maganinta ne. Yasamu guri yai parking Ya fito daga mota Guri yasamu ya zauna, yai shiru dayake ansan abunda yake bukata customer ne sosai, aka kawo masa giyar dayake sha, befi minti shabiyar da zuwansa ba, sega Hannah tazo , dan an kirta a waya an sanar da ita Jalal yazo, guri ta samu ta zauna tana fuskantar Jalal, "Jalal ina kashiga haka, babu ko waya nadena ganinka kwata2 tun a gurin birthday din ka bankuma ganinka ba gashi inason ganinka, nayi niyyar zuwa gidanku amma bani da lafiya ne" kallonta ya danyi yayi shiru ya cigaba da shan giyarsa. Kallonsa Hannah ta kumayi "Jalal ya kayi shiru, kayi magana mana" "mezance miki, inajinki" ta numfasa tace "Jalal dan Allah menene alakarka da wannan yarinyar me iyayin tsiya, ta fadamin sunan ta amma na manta, a zatona itace Ilham amma ranar ta nunamin Ilham tace ita ba itace Ilham ba" ajiye cup din hannunsaa yayi ya kalleta "meyasa kike tambayata wacece?" "ta damu dakai sosai" "hmm ya akayi kikasan hakan?" "Alamu nagani" "yayi kyau" shine amsan da Jalal yabata, "Jalal dan Allah wacece ita a gurinka" a fusace ya kalli Hannah yace "ke kin isheni, ki kyaleni dan Allah" "meyasa zakace in kyaleka bayan saboda kai nazo gurin nan, Jalal wata alfarma nake nema a gurinka" kura mata ido yayi sannan yace "ina jinki" "Jalal tuba nakeso nayi, na dena abunda nakeyi, dan Allah so nake ka aureni, aurenka ne kawai ze iya cetoni daga halakar danake ciki please Jalal. " Aurena ze cetoki daga halakar dakike ciki, nikuma ze janyomin halaka, ke kina tunanin zan zabi mace kamarki a matsayin matar aure, Hannah banason yarana suyi irin rayuwar danayi, dan haka uwa tagari zan zaba musu, ina miki murnar shiryuwa da kikayi, naso dan Allah kika shiryu, amma ina miki fatan alkhairi Allah yabaki miji nagari "yana gama fadan haka ya tashi ya tafi. Hanna ji tayi kaman ta fasa ihu, duk tsawon lokacin nan dasuka dauka tare ammaa ace babau soyayyarta a zuciyarsa, anya JALAL mutum ne kuwa? Aikuwa ko karfene a zuciyarsa seya soni sena aure shi, tana cikin wannan tunanin Jeje yazo, yasamu guri ya zauna a kusa da ita ya kalleta "Hannah manyan kasa, mekuma kikazo yi nan?" "meya dameka dame nazoyi, oppression na fito, na fito farautar abunda zuciyata ke so, kuma zanyi iyayina inga nasamu" "Hannah kenan dazaki zubar da makamanki ki dawo mucigaba da aiki tare gurin ganin munyi nasara akan Jalal" "Jeje meyasa kanka baya jane, ban gayamaka cewar bazan kara maka aiki ba, kaina nakewa aiki yanzu, kafita daga harkata ko inyi maganinka wallahi" ta dau Jakarta tai tafiyarta, bayanta Jeje yabi da kallon mamaki, gaskiya Hannah ba karamar mara mutunci bace, betaba zaton zata juya masa baya ba, dole yai taka tsan2 da ita dan yasan halin Hannah sarai, inta sawa ranta samun abu setayi duk yadda zatayi ta sameshi, dole yai wani abu akanta. Koda Jalal ya dawo gida, Gaba daya yau angama dagula masa lissafi, mussaman Jalila, yau an hada masa zafi sosai duk ransa a bace yake, yarasa me zeyi ya huce, kalmar namij mara daraja da Jalila takira shi dashi se yaji wani mugun bacin rai ya kamashi, yayi tunani sosai mezeyiwa Jalila ya huce haushinsa, gani yai yana kara batawa kansa lokaci, dan haka zuwa yayi ya kuma daukan giya Ya sha me isarsa, seda fita hayyacinsa ya fadi a gurin yana bacci. Share please More Comments more typing.......................... 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  57_ 4️⃣ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680               _MY FIRST NOVEL _ Yauma Jalila seda sukayi fada da wani lecturer dinsu, saboda dalibai biyu sunyi laifi ya kori daya yabar daya, dayake wadda yabari din sameera wata muguwar fitsararriya ce, ba dalibai ba har malamai tsoronta sukeji, babban abunda yake bakantawa Jalila be wuce, yadda wasu daga cikin yaran talakawan nan kemata shishshigi ba don samun gurin zama, itakuma taita hantararsu tana musu tsawa, tana zaginsu ko haushi basaji kusan duk ajin suna shakkarta, kaf ajin nan aminiyarta dayace wadda batayiwa wannan rashin mutuncin wato saleema, tun zuwan Jalila ta lura da halin kowa, ita saleema itama babanta yana da rufin asiri yanada kudi amma ba kaman Samira ba, sedai yadda Jalila ta kula saleema ba karamar yar iska bace ba kowa ke gane hakan ba saboda ta iya takunta. Yanzuma samira ce takewa, wata yar gefen seat dinta magana zahra, zahra ta bada attention dinta sosai akan lectures dinta, koda lecturer ya juyo, samira ya gani tana magana amma ya kori zahra sannan yace bata da attendance dinsa na wannan semester gaba daya, ya kyale samira be koreta ba, har ya juya ze cigaba da lectures Jalila tace "Excuse me sir" ya waigo yana kallon Jalila, yace mata "Ya dai?" "Sir meyasa ka kori zahra, ba ita tayi magana ba, bakaga ba ita take magana ba, kamata yayi ka koresu su biyun, koka kyalesu duka, amma bekamata a kori wata abar wata ba, amma am sorry idan na fadi ba daidai ba" juyowa yan ajin sukayi suna kallon ta, zuwa yanzu sunfara gane halin Jalila, ba karamar kwalluwar mara mutunci bace, yayinda take birge wasu, saboda iyayinta, da fadar gaskiya, malamin yai saroro yana kallonta ya hade rai yace "waye lecturer tsakanin nidake?" kanta tsaye tace "Sir wannan ai amsace a bayyane kaine lecturer, nikuma daliba" "dan me zan yanke hukunci kiyi challenging dina? Ke wacece? Ido kika fini banga abunda yake faruwa bane, ke har kin isa inyi magana ki kalubalanceni a gaban students dina, are u out of your sense" nan fa ya dau zafi ze farayiwa Jalila masifa ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, yace ta tashi ta barmasa ajinsa, yauma babu batun ta bada hakuri ta dau jakarta zata kara gaba, shikuma yacigaba da zage2 hardace mata mara tarbiyya aikuwa a take tace "Excuse me sir, daga fadan gaskiya zaka fara min fada hada cemin mara tarbiyya, am just your student not your daughter, am sorry for what i did, kayi hakuri in har na bata maka rai, amma karka manta fadar Manzon Allah ne salallahu alaihi wassalam, duk wanda yaga ana aikata abunda be dace ba, ya kawar da hannunsa, in ba ze iyaba yayi da harshensa, in baze iyaba yaki abun da zuciyarsa wanda shine mafi raunin imani, sir be kamata aji tsoronka aki fada maka gaskiya ba, tunda Allah ne kadai abun tsoro, dan kana shugaba ko malaminmu baze hana a fada maka gaskiya ba, duk wanda ya shigo aji ba dan me kudi dana talaka, kayi treating dinsu equally, yazakaji in zahra yarka ce aka hukunta ta akan laifin wani, kasani wannan hukuncin dakayi mata ranar alkiyama sekun tsaya a gaban Allah, wannan abunda kayi mata ya isa ya toshe maka hanyar arziki a rayuwarka, kudena raina daukar hakkin dalibanku ku dinga ganin ba wani abubane ba dan Allah yabaku dama, bekamata kace gaba daya batada attendence din wannan semester dinba, but with do respect sir this is against our Islamic teachings, da na kowame" daga nan ta juya taana wannan takunnata na kasaita tafita waje, koda Jalila ta fito ta tarar da zahra tasamu guri ta zauna tana kuka, kusada ita Jalila taje ta durkusa ta dafata, "Kidena kuka kinji, Insha Allah komai zezama dai2, kidena zama inda wannan yarinyar take kinga ta cazami ki an koreki" zahra ta kalli Jalila dan ko sannu bata taba hadata da Jalila ba a hankali zahra tace "kema ya koreki ne" "Eh korata yayi" nan Jalila tagaya mata abunda yafaru, zahra tace meyasa kikayi masa magana, rannan ma an koreki daga aji, karki jawa kanki matsala "Jalila ta danyi murmushi tace" babu wata matsala, indai ka dogara da Allah ta ya isar maka, be kamata ya kyaleta keya hukuntaki ba akan laifinta, waima tukuna me kikayi mata naga alamun ta takuramiki" tsit ajin yayi, aka rasa me cewa wani abu, shiru lecturer yayi na wani dan lokaci, sannan ya kalli wani dalibi yace yaje waje ya kirasu Jalila, aikam ya kirasu sukazo, yace sunemi guri su zauna, sukakoma gurin zamansu, bekuma cewa komai ba yacigaba da gabatar da lectures dinsa, koda yafita haka wasu suka cigaba da surutai akan Jalila, samira ce da yan group dinta tace "ina son sanin waye uban yarinyar nan da take wannan gadarar, harni zata kalla tace a hukunta, tasan waye uabana a kasar nan" saleema tace "kedai bari, amma dagani ba yar talaka bace yanayinta kawai zaki kalla kisan hakan, kuma motar da akekawosu ma babba ce, da alama itama babanta wanine, babyn tama hutawa" tsaki samira tayi "duk kudinta tayi na ubanane, saleema inaso ayiwa yarinyar nan warning, sannan kota halin yaya ina bukatar zahra" sameera tai murmushi "yadda kika dama haka za a sha yar masu kasa, sanan kizuba ido kiga wannan yarinyar carry overs din dazata kwasa a school din nan" suka kwashe sa dariya, Jalila ta kalli zahra, "Zahrah baki gayamin ba, meye hadinki da samira ta takura miki haka, kekuma kinkasa daukar mataki" ajiyar zuciya zahra tayi tace "Jalila ina cikin matsala, ni kinga babana bakowa bane ba a garin nan, ni yar talakawa ce, kinga samira da salima yaran masu kudine sannan kuma... Setayi shiru" inajinki cigaba mana wata ajiya zuciya Zahrah takumayi "Jalila samira da saleema, ba kawayene kawai ba yan iska ne, tun suna yara suke tare, daga maza har mata ba wanda basa nema, wannan yan group din nata dayawansu yaran talakawa ne, amma tasasu a wannan harkar tana basu kudi masu yawa, dayawa lectures sun santa, ba wanda ya isa tasa kara ya tsallake, saboda babanta dan siyasa ne suna da kudi, koda anyi niyyar yimata wani abu a makaranta se tayi amfani da alfarmar mahaifinta, in bata gadamaba setasa a kori mutum, da kike ganin ta haka hatta a hukumomin tsaro taana da mutane, kuma harkar da takeyi har wajen kasar nan, mu amalarta hada manyan masu kudi, itada saleema suke wannan abubuwan, shine tace wai tana sona" zahra ta karashe maganar da hawaye, kallonta Jalila tayi labarin ya daki zuciyarta, amma ta dake tace "to kekuma kikace mata me?" "shine nace mata a'a shine taketa bibiyata take takuramin, tace setasa an koreni a makarantar nan, nikuma inajin tsoro saboda, inason inyi karatu" ta karasa maganar tana zubar da hawaye, Jalila tayi tsaki "kekuma saboda wannan shashancin naki dole ta takuramiki, kin nuna kina tsoron ta, tashi muje muyi salla, semuga ya za ayi" suka tashi suka nufi masallaci, a hanya suka ci karo dasu Samira amma, ba wanda ya kula wani, Samira ta kalli saleema tace "sweet heart, bi yaran can, bana son ta shiga tsakanina da zahra, dan haka ki kiramin ita kice ina kiranta" "bakida wata damuwa, bari inje" kafin saleema taje su Jalila har sun kai masallaci, tana zuwa masallacin taga Jalila ta cire hijjabinta tana alwala, tsayawa saleema tayi tana kallon Jalila, yanzu takekuma ganin kyawun Jalila, parkistan ne a jikinta wando da riga, se dogon gashinta irin na fulani, tana tsugune tana alwala, tubarakallahu komai yaji a jikin Jalila,  koda Jalila ta idar tai ido hudu da sameera, tsaki tayi tasaka hijjabinta, suka shige masallaci, haka samira tacigaba da jiranta seda ta idar, saleema ta karaso gaban Jalila ta zauna ta kalleta taimata wani murmushi irin na rikakkun yan isaka tace "baiwar Allah dukda kasancewar, ajinmu daya amma bansan sunanki ba, aikoni akayi gurin ki, samira ce takeson ganinki" shiru Jalila taimata ta dauki jakarta tana saka wayarta, ta kalli kalli zahra tace "zahra taso muje department dinsu Nana, muje capteria muci abinci, saleema tace tab lallai wannan yar rainin hankali ce, saleema tace" baiwar Allah, magana nake fa, samira tace tana son ganinki " Jalila ta kalli samira tace " bani da lokacin kowace kucaka a school din nan amma zuciyata zata iya canza ra'ayi " Daga nan taja hannun zahra suka fita daga masallacin, koda sukaje gurin cin abinci zahra tana ta bawa Jalila labarin halin su saleema. Koda suka gama cin Abinci suka koma aji, lecturer be shigo ba, samira ce ta shigo da mukarrabanta, se wani shan kamshi take, tazo seat din Jalila ta zauna a kusa da ita, ta kalleta tace "dukda bansan wace ce keba, hakan baze hana kisan wacece niba, kuma yar wace niba, kisani ba amin shishshigi, baki isa inyi wani abu kice zakisa a hukunta niba, tunda na shigo makarantar nan, naga yadda kanki yake rawa, to kitsaya a iya matsayinki, nan fada tace duk wanda yake ajin nan a karkashina yake, dan haka kitsaya a matsayinki" samira ta mike zata tafi Jalila batace komai ba, sema murmushi da tayi "yaro be san wuta ba seya taka, baki sanni ba ne, amma muje zuwa" Ana haka lecturer ya shigo wanda yasa kowa nutsuwa, tunda lectures suke shigowa sau dubu inzakayiwa Jalila tambaya shiru zatayi tace bata saniba, hakan yasa aka fara gulmar ko dakikiyace se tsabar fitsara da izza a cikinta, dasuka fito daga lectures, tay8 sallama da zahra tai tafiyarta gida saboda Manu direba bezoba, Nana kuma basu gama lectures ba, Jalila ta tafi gida tanata tunanin labarin da zahra tagaya mata akan su saleema, lallai dole wasu iyayen su hana yara mata neman ilimi, katura yarinya makaranta amma ta lalace saboda abun duniya. Haka Jalila taje gida a gajiye, tanata tunani daban2 kanta har yafara ciwo, gida ta shiga, tana tura kofar palour taci karo da yaya mairo da Naja da Maama a palour suna hira, seda jikin Jalila yayi sanyi ganinsu a gidan nan, dan ta san bacin rai zata sha yau, sallama tayi ta shiga, ba wanda ya amsamata se Maama itama a ciki ta amsa, Jalila ta ce "ina wuninku" yaya mairo tai saurin cewa "ke dan Allah ki wuce ni banason kinibibin gaisuwarki, wuce kibani guri" Naja tai saurin cewa "tsabar kinibibine wai ita dole ace ta Allah" Jalila batace komai ba ta wuce dakinsu, tana shiga nan ma ta tarar da sa'ada kwance akan gadonsu tana danna waya gefe ga kwanon abincin dataci da jarkokin lemo da ruwa akan gadon duk ta bata gadon, ta zubar da abinci akai, kallo daya Jalila taiwa sa'ada, ta dauke kanta kaman bata ganta ba, ta ajiye jakarta da hijjabinta, ta dau towel ta shiga wanka, tagama ta fito ta zauna a gaban dressing mirror tana shafa mai, sa'ada ta dago kai ta kalli Jalila ta tabe baki "tabdijan anzo an samu guri, se murjewa ake ana yadda aka gadama, Allah ya rufa asiri ba a girma a cikin arna ba da yanzu ko ana gona hakan doya da goyon shege kokuma anayiwa   coci hidima" Ware gashinta tayi tana tajewa, ba tareda da tayiwa sa'ada magana ba, Naja ce itama ta shigo, ta haye kan gadon gefen sa'ada tana tauna cingam, ta kalli Jalila tace "Allah sarki, mukam mungode Allah da yayimu a musulmai, ba arna ba" haka suka ding a yiwa Jalila rashin mutunci suce wannan suce wancan, amma taki kulasu, ta dauki doguwar riga tasaka, halima ta shigo dakin da sauri ta Rungume Jalila, Jalila ta kalleta "leemart saukar yaushe?" halima tace "dazun nan na dawo akace kina makaranta, Aikena akayine se yanzu na dawo" "Allah sarki ya kika baro mutan garinnaku" "kowa lpy kalau Alhamdilillah, nayi kewarki sayyada Jalila" murmushi Jalila tayi "nima nayi missing dinki da hirarki me ban dariya" Naja tace "Ke halima meye haka kike wani rungumeta, kokema kin hada iri da arnan ne, ko kyamarta ba kyaji" saroro halima tayi tana kallon Naja, Jalila tace "leemart dan Allah hadomin madara da sugar a cup ki hadomin da spoon ina son zansha goldenmorn" halima ta gyada kai ta fita, sa'ada tace "tabdijan wayaga basa banba ansamu guri se abunda akeso a keci sekace a gidan ubanki, lallai Allah ya temakeki wai, da yanzu ana can anacin teba a kauyen su tsohuwa, ko ana gona ana bauta" Jalila kam gaban mirror takoma ta shafa turarurrukanta, ta dau mayafin rigarta ta daura akanta, halima ta kawo mata madara, ta karba tayi godiya, seda tagama shirinta tsaf, sa'ada da naja suna gayamata bakaken maganganu, a hankali Jalila tazo gaban su ta tsaya sannan tace "nan gidan ubanane, inada ikon yin abunda nakeso inci abunda nagadama inyi yadda nakeso, kufa meye matsayinku a gidan, se abunda yakawo ake diba a baku, kokuma ayi amfani da abunda aka farauto a bariki" da sauri Sa ada ta kalli Jalila, Jalila tacigaba da cewa "kukiyayi cimin zarafi kyaleku kawai nakeyi, ranar dana tashi nuna muku ainihin kalata, zakuji babu dadi, a kiyaye" tanagama fadin haka ta tashi ta fito takoma harabar gidan tai zamanta, a inuwar data saba zama, amma me tunani ya addabi zuciyarta, ga tunanin yadda zata sami tarihin waye Jalal, taya ya zata samu mafita akan al amuransa, ga tunanin labarin da zahra tabata akansu saleema, jikinta yana bata wani abu akan su, amma takasa gane menene? Kai ita wace kaddarar ta kawota kano, tana zamanta cikin kwanciyar hankali da umminta, kaddara ta kawota kano tunani kaman ze haukata ta, ga jarabar dangin mamansu Jawwad dabasa kaunar ganina"Allah sarki Ummi na, Allah ya bayyanamin ke" a hankali ya rike hannunta "Yar babyna, tunanin me kikeyi hakane, da alama kin gaji sosai kuma akwai damuwa a tareda ke, kinkasa cin abincin naki, kuma ga hawaye a kwance a idonki, abunda nafi tsana ganin hawaye a idonki, gayamin tunanin me kikeyi? " Jawwad ne a durkushe a gaban Jalila ya hada hannunta da kofin ya rike a nasa, a hankali kwallar dake idonta ta gangaro, Jalila ta dake tareda kakaro murmushi taimasa " Yaya kadawo ashe? " " naki wayon gayamin meyake damunki? "bakomai fa nagajine kawai" "amma kika kasa cin abinci" ya karbi cup din hannunta ya debo goldenmorn din ya nufi bakinta dashi "bude bakinki" dauke kanta tayi, ta rike hannunsa "A'a yaya Jawwad, karkashiga matsala, kasan su Yaya mairo suna gidan nan, kar ayimaka fada" Kallonta yayi "Baby, ni ban damu da hakan ba, bana fargabar kome ze faru indai akanki ne, nasan maybe zuwansune ma yasa sukayi miki wani abu daya bata miki rai" "A a basuyi min komai ba" "Baby hakan be kamata ya dinga damunki ba, kome za ayimin zan iya jureshi indai akankine, komai tsanani ina tareda ke Jalila, bazan iya rabuwa dake ba, nasan Abba ze bamu goyon baya, ina sonki Jalila " dan tsura masa ido Jalila tayi a ranta tace "Allah sarki yayana, goyon bayan uwa shine, nasan indai dasu yaya mairo to bazasu barmu tareba" murmushi tayi masa "yaya ka tashi ka zauna akan kujera mana" "A a sekin gayamin kema kina sona tukuna" rufe idonta tayi tana dariya Jalal ne ya turo gate ya shigo ya tunkaro inda su jalila suke Share please More Comments More Typing............................. [09/04, 12:29 PM] Ayshercool: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  6️⃣/59_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Abun takaicin, ya kwanta da bacin ran Jalila, zuciyarsa har wani tafasa take dan bacin rai, amma abun takaicin yauma kwana yayi yana mafarkin Jalila, cike da shaukin soyayya da kauna, a yanayi irin na ma'aurata, mafarkinsa na karshene me ban tsoro, ya firgita kwarai ganinshi yayi wasu mutane sun daureshi akan dutse, maza da mata suna saransa da wasu dogayen wukake, Jalila ta bullo daga wani guri ta taho da sauri ta rungumeshi, tana tare masa saran, yayinda sukuma mutanen suka dinga saranta jikinta yana zubar da jini, ta rungumeshi gam itakuma jini na zuba a jikinta a hankali take kiran sunansa a cikin kunnensa ABDUL JALAL. Juyi ya dingayi yana kokarin ya tashi, A firgice ya tashi daga baccin dayakeyi, yana haki, a hankali ya daga kai ya kalli agogo karfe takwas da rabi na safe, tashi yayi zaune yai shiruu yana nazarin mafarkin dayayi na karshe, jujjuya abun ya dingayi a ransa yana tuno yadda take furta sunansa, tunani yake meye alakarsa da wannan mutanen haka suke saransa, dan gutun tsaki yayi, "komeyema na bata lokacina akan wannan shirmen mafarkin" mikewa yayi ya sakko daga kan gadon ya tafi toilet don yayi brush yai alwala kawai ya tuna se yayi wanka, sannan zeyi salla wani dogon tsaki yayi "Jarababbiyar yarinya ta addabawa rayuwata, tazomin a farke ta dameni, dan jaraba har cikin baccina ma seta biyoni, ji yanzu ga rana tayi amma senayi wanka zan salla komeye hakan oho" haka yaita mita yai wanka yafito yai sallar asuba. Bayan ya idar da sallar ya tafi cikin gida, kai tsaye part din daddy ya nufa, ya tarar daddy ya tashi har yana breakfast Shida Mummy suna hira, sallama Jalal yayi, daddy yadago yana kallonsa yafara murmushi, Jalal yaje kusa dashi ya zauna, cikin girmamawa yace " good morning daddy" ba Mummy ba har Daddy seda ya kalli Jalal, rabon da ya gaida daddy haka da safe cikin girmamawa tun kafin ya lalace dan sedai daddy ya gaida Jalal amma badai ya gaisheshi ba, dama Mummy ba a maganarta itadama baya ta tata, amma abun mamaki yau hada sallama, daddy ya fadada murmushinsa yana shafa kan Jalal yace "Morning yarona katashi lafiya?" "Lafiya kalau daddy, ya gajiyar ka?" "Ba gajiya Jalal, kayi breakfast ne? Ko Jawwad din kake jira?" "No daddy Jawwad nasan ya tafi makaranta" "taho muci nawa to" girgigiza kai Jalal yayi, "kaci Abincin ka daddy, ni zanci nawa daga baya, dama zuwa nayi in gaisheka, sannan in kalleka inajin dadi, kasan na dade ban ganka ba nayi kewarka daddy" Mummy tace "Hmm wannan soyayya haka, lallai Jalal" daddy yai murmushi yace "to ya ranki, nima kllonka yana sani farinciki yarona, idan na kalleka ina jin daďi, wannan gudan jini nane, babbar kyauta daga Allah, ina alfahari da godewa Allah dayabani kai" dan shiru Jalal yayi cike da damuwa yace "daddy yanzu har farinciki kake da kasancewata danka, kalleni fa daddy kalli rayuwar danake yi, mutane dayawa na kyamar halayena, yayinda wasu suke gudun a dangantani dasu a matsayin danginsu saboda munin halayyata, mutane kalilan ke kaunata suke son farincikina daddy kai da Jawwad bansan wani irin so kukeminba, kai mahaifina ne amma Jawwad da rana ďaya be taba kyamata ba" "Jalal ko a yaya kake kai Allah yabani, kaine nawa ko halinka yafi haka muni inamaka fatan shiriya, amma ni a haka nake sonka, sannan lamarinka da Jawwad soyayyace daga Allah wanda samunta a wannan zamanin abune me wahala, shiyasa nake maka fatan samun mace tagari, Jalal ba abunda yafi zama da wanda yake kaunarka daďi" "hakane daddy, Jawwad na musamman ne, naso a ce ciki daya muka fito dashi, amma daddy dagaske bana sauke nauyin dayake kaina a matsayin danka ko? Yadda nake treating dinka bahaka ya dace ďa nagari yayiwa mahaifinsa bako? Kayi hakuri daddy zan dena Insha Allah" "waya gaya maka haka kai yaron kirkine, kana kokarin farantamin karka damu lokacine wataran se Labari, Allah ya shirya min kai" "Ameen daddy" "Jalal ta mahifinka kawai kake, a tunaninka shikadai yake da hakki akanka, ni ko oho ko, da inyi farinciki dakar inyi baka damu bako?" hade rai Jalal yayi, yaiwa Mummy wani kallo me cike da ma'anoni, ya tashi ya fita ya bar dakin gaba daya, daddy ya dan dubeta " Hadiza sam bahaka yakamata ki dinga treating Jalal ba, ko kina manta kece me laifi a gurinsa, yakamata kiyi tunanin hakan. "haba daddy Jalal, shikenan shi abu baze wuceba a gurinsa, kullum da laifina zetamin hukunci" "hadiza ke kike ganin laifinki karamine, banga laifin Jalal ba lokacin danake jan hankalinki, baki saurareniba se yanzu data kwabe miki, seki nemi daidaito da ďanki".    Jalila tana tafe akan varander na class dinsu ta ga captain dinsu da takaddu a hannunsa, yanata sauri da alama class zeje, wanda tayi Imanin takaddun hannunsa tests dinsu ne, sauri takara ta hada da dan gudu ta tana kiran sa, tsayawa yayi ya waigo, mamakine ya kamashi yaukumashi wannan yar kwalisar takewa magana ya tsaya suka gaisa da ita "Captain wannan tests dinmune ko?" "Eh sune, me yafaru" "yawwa dan Allah alfarma nake nema, sonake kabani tawa anan" "amma meyasa?" "bakomai kawai inason kabani tawa anan ne, banaso sekaje aji" yadda ta kafeshi da ido yaga tayi masa kwarjini matuka dan haka yace  "to shikenan ya sunan naki, se in duba miki" "A a bani in duba tawa da kaina, karka damu ba ta wanda zan duba tawa kawai zan dauka" ba musu ya mika mata takaddun an faďi test din nan sosai, kuma gashi over 40 ce duk an faďi tunda test din be fadi zeyita ba, Jalila tana ganin tata ta zare, tana kokarin mika masa takaddun taga wani suna Samira Kabir Idris, Tunawa tayi Kabir Idris shine sunan dake dauke ajikin katin da baban faruk yabata a banki, mika masa takaddun tayi tace" Thank you very much " " You are welcome " tunani ta dingayi waye me irin wannan sunan a ajinsu, maybe ma kawai sunane yazo ďaya, da sauri ta tafi class taje gurinta ta zauna, Captain yana raba takaddu tanajin ya ambaci sunan Samira Kabir Idris, ta juya dan ganin kowace, wadda tai tsammanice Samira kawar saleema, se yanzu taga tsananin kamaninta da Alhaji Kabiru, kenan 'yarsa ce, ajiyar zuciya Jalila tayi, barewa bata gudu danta yayi rarrafe, ba a banza ba Allah yabashi irin wannan yar, Alhamdilillah bincikena zezo da sauki, sena gane alakarsa da Jeje, tana cikin tunanine taji captain yana cewa "Yan class kunga munyi test, ga a yadda tazo dan haka se mudage a exams, sannan muyita addu'a dan banga wanda ya ci talatin bama, amma yace yanason ganin Jalila Aliyu Imam, in taji tasan kanta taje yana neman ta, danni ban santaba" zahra ta kalli Jalila," bake ake nema ba? " "nice" "Naga ba abaki naki test dinba, ni dai kinga wai 19 na samu" "kigode Allah ai kinyi kokari, yawwa zahra dan Allah samira sunawane yan gidansu" "Su biyune kawai yayanta faruk, sekuma ita sukenan" "Kuma a gidansu ansan me takeyi? " "Gaskiya bansaniba babansu dai yana da zafi, wataran yana kawota makaranta, mamansuce dai ance ba ruwanta da tsanani akan tarbiyya" "Mene sana'ar babansu?" "Kai Jalila sekace wata lawyer wannan tambayoyi haka" "yi hakuri akwai abunda nakeson ganewa ne" "gaskiya ban saniba, amma naji kaman ance dan kasuwa ne" "shikenan nagode sosai". Bayan antashi daga school Jalila tai tafiyarta gida bataje kiran sir hafiz ba, tanata tunanin yazata bullowa lamarin Alhaji Kabiru, dan tana zargin mutumin nan sam bata yadda dashiba, wayarta ta dakko ta duba what's app dinta, taga lambarsa tayi appearing a contact dinta na wats app, dan bayan dawowarta gida ranar tasaka lambarsa a wayarta hotonsa ne akan dp dinsa tayi sa'a yana online, dan haka tayi masa sallama, seconds kadan ya amsamata, suka gaisa yace mata be gane me maganaba, rasa me zatace tayi, kawai ta kashe datarta ta ajiye wayar tai shiru tana tunanin anya haka yakamata tayi, ko kawance zata kulla da samira, amma in tayi haka itama za adingayimata kallon 'yar iska, lambar hanan ta kira amma taki shiga dan haka ta hakura.   Hanan kam tana kwance, tana trying lambar Jawwad amma a kashe, ta ajiye wayar ta dafe kanta, turo kofar dakinta, dan dago kai tayi da mamakinta setaga Siyama, zumbur Hanan ta mike tana murmushi "oyoyo Siyama matar Yaya yauke kika kawomin ziyara" murmushi Siyama tayi "yau nina kawomiki tunda kin mance dani nace bari inyi surprising dinki" "amma naji dadi" Siyama ta zauna, Hanan taje ta kawomata ruwa da lemo da snacks suka zauna sunata hira, Hanan ta kalleta "ta Yaya Abdallah gaskiya Siyama, kin rike wuyan yayana over, komai ke ni ya manta dani gayamin meye sirrine" "haba Hanan waceni rike wuyan Yaya, shiya rike nawa wuyan, wallahi Hanan Abdallah ya iya soyayya shiyake tabarani, bana tunanin akwai namijin daya kai yaya Abdallah iya soyayya da kula da mace" dariya sukayi gaba daya "Siyama ya bakyacin snacks dinne?" "A a ni snacks be dameniba dama chocolate ne" "Ahh sekace queen J, kinsan inkinaso ki birgeta kibata chocolate, gaskiya ina missing Jalila ina kaunarta har cikin raina, amma alakarmu na shirin samun matsala wanda hakan bazemin daďi ba, amma nakasa samun mafita, dama kobakizoba ina son zuwa siyama" hanan ta karasa maganar cikin damuwa, "Amma Hanan bangane mekike nufiba, kamarya alakarku na shirin samun matsala kamar yaya?" "Siyama Jawwad nakeso, da farko na dau abun wasa, inayine domin Jalila ta maida hankali akan Jalal, saboda sunfi dacewa amma yanzu nagane wallahi son gaskiya nake masa kota ina yaya Jawwad ya hadu" zare ido Siyama tayi "Hanan kin san irin soyayyar datakewa Jawwad kuwa?" "Siyama soyayyar dake tsakanin Jawwad da Jalila na yan uwantaka ne, amma da Jalal ta dace shike bukatar taimakonta, ina kaunar Jalila amma bazan iya rabuwa da Jawwad ba" Hanan ta riko hannun Siyama, idonta taf hawaye tace "Siyama babu wasa a zancena, wallahi dagaske nake inason Aliyu Jawwad, so na gaskiya, sannan ina kaunar Jalila ina jinta kaman wani tsagi na rayuwata, amma bazan iya rabuwa da Jawwad ba" Ajiyar zuciya Siyama tayi, ta gogewa Hanan hawaye "For now kiyi hakuri ki dan bani lokaci, zanyi tunanin mene mafita, amma kidena kuka" gyada kai Hanan tayi kaman karamar yarinya, daga nan suka shiga wata hirar    Seda aka kwana biyu, Jalila bataje kiran sir hafiz ba, captain ne yazo yana kuma shela a aji, danshi besan wace me sunan ba, tashi tayi ta fita tatafi offers dinsa, tana zuwa ta shiga da sallama ta tarar da shi da wasu lecturers a office din ammasu dattawane ba kamanshi matashiba, amsamata sallamar sukayi, kaman yadda yake ďabi'ar Jalila har kasa ta zube cikin girmamawa ta gaishesu, suka amsamata cikin mutunci, shi sir hafiz mamaki ma ta bashi, ya kalleta a fusace "uban mekikazo yimin office, kin fadiko? Ba abunda zanyi miki aidama seda nagaya miki fita kibani guri, dakikiya kawai kisawa ranki kin gama faduwa exams dina" batace komai ba ta juya tai tafiyarta Malaman nan suka dinga jinjina tarbiyyarta, saboda a wannan zamanin a yan matan jami a asamu me durkusawa har kasa ta gaida malamai abunda wuyar samu "hmm bakusan halinta bane, tsabar iya makircine dakikiyace gata fitsararriya, nayi test ta faďi shine takamo hanya tazo". Bayan kwana ďaya sir hafiz yakuma sawa a kira Jalila Aliyu Imam, tareda kashedin in batazoba zesakamata zero a test dinsa, kuma zuwa office dinsa Jalila  tayi, yau wasu yan matane a ciki se iyayi suke suna yauki, gani tayi bashida niyyar saurarta dan haka tazo gaban tebur dinsa tace "Sir tunda baka da lokacina karka kara turawa kace inzo, zuwana nawa office din nan kaki saurarata, bayan kaikace inzo" daga kai yayi ya kalleta, yayinda yan matan suka bita da kallo "ni nace kizo? Kizo in miki me" "bakai kace inzoba karka kara tura captain yana shelar wacece Jalila Aliyu Imam dan bazan kuma zuwa ba, kaitasamin zeron inka ga dama kasamin abscent se wani wulakanci kakemin menayi maka hakane? , in akwai abunda be kai zeroba kasamin" da sauri ya kalleta "What kece Jalilan?" zumbura baki tayi "Eh nice" "karya kikeyi" ba tace komai ba ID card dinta ta dakko ta diremasa a gabansa, dauka yayi ya karanta ya kalleta tabbas itace "Ya akayi kikacinye test dina gaba daya alhalin wani abunma banmuku ba, kaf ajinku ba wanda yaci ko 30,ko satar amsa kikayi? Kallon yan matan dake office din tayi tai ta kalleshi tace " Sir Hafiz , Never Judge book according to it's cover, bana satar amsa kuma bantabayiba, kana muzantani agaban yan aji kana cemin dakikiya, abun ba anan takeba, kayi alkalanci, idan baka yadda da wannan test dinba ka canzamin wata, amma karkayi tunanin zaka tambayeni a gaban yan aji in baka amsa" shiru ya danyi, ya kalleta yafarayi mata tambayoyi, a nutse take bashi amsa, gashi ta iya turanci matuka, ga mamakinsa har abunda be koya musuba inya tambayeta seta bashi idea dinta, ajiyar zuciya yayi "shikenan zaki iya tafiya zan nemeki" Jalila ta juya ta fita. Sir Hafiz ya dade yana mamakin kwakwalwarta, gata gentle, amma meyasa tsarin rayuwar ta daban da saura ko maganarta ma daki daki kuma a tsare, kuma ba ruwanta maganar kozatiwa wanda ta fadawa dadi ko a a seta fada kuma ko  a gaban waye. haka yaita mamakinta.   Yau weekends dan haka tun sassafe Jalila taketa gyaran wardrobe dinta, tagama tsaf seta ga qura'nin da daddyn Jalal ya taba bata, ta jujjuya qura'nin yana nan kar dashi a cover dinsa "Yakamata in dinga tilawa da qura'nin nan, Allah ya bawa daddyn Jalal ladan" tagama gyaran drower dinta, ta tafi kitchen, wainar masa suka tsiriyi itada halima, a matsayin abincin rana, seda suka gama Jalila taje tai wanka ta dawo ďaki ta zauna tana kwalliya wayarta tafara ringing, tana dubawa taga bakuwar lamba ce, bata san wayeba dan haka ta saka wayar a silent. Tunda daddy yazo garin nan Ilham take kasa kunne taji, anyi batun aurensu da Jalal amma shiru yau kwanan daddy uku da dawowa amma bataji Mummy tace komai ba, dan haka ta yanke shawarar zuwa tasamu Mummy, dakin Mummy taje bata nan, dan haka ta tafi kitchen, aikuwa Mummy na can tana hadawa daddy fruit salad "Mummy sannu da aiki" "Yawwa daughter, kin tashi daga baccin ne?" "ina wani Bacci Mummy alhalin duk ina cikin zullumi da damuwa" "akan mefa?" "Mummy maganata da Jalal mana, har yanzu naga Daddy ya dawo amma bakice komai ba fa" "Ilham kenan akwai gajen hakuri, ina nan zan gayamasa insha Allah kafin yakoma za asa ranar aurenku" Murmushi Ilham tayi "Allah yasa Mummy, dan na kagu inganni na mallaki yayana" "hmm daughter ba kunya ko" Ilham ta dan rufe ido tana dariya. Jalila tagama kwalliyarta tasaka turare, ta mike taje ta dauki Abincin Jawwad ta nufi part dinsa dashi, tana zuwa ta tarar bakowa a palour, ta ajiye abincin tasamu guri a palourn ta zauna, tana jiransa koyana wanka ne, ta dora kafa ďaya kan ďaya tana danna wayarta, hankalinta yana kan wayar sosai, tana game tanayi tana murmushi, warin sigari taji ya daki hancinta, da sauri ta ďaga kanta, tai tozali da Jalal ne ya fito daga bedroom din Jawwad, kallo ďaya tayi masa ta ďauke kanta taji tsigar jikinta ta tashi, dagashi se gajeren wando, kana ganinsa kasan yana cin karfe, a murďe jikinsa yake, ga ko ina na jikinsa lullube yake da gashi, fatarsa se sheki take, babu alamun wahala a tareda shi, ya nufo inda Jalila gadan2  zazzare ido Jalila tayi, kirjinta ya shiga dukan uku2 tanaso tayi magana amma takasa. More Comments More Typing..................... 🖊️ 🖊️ 🖊️ 🖊️ 🖊️ 🖊️ 🖊️ Koda yaushe bazan manta da gudunmuwarku ba ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹 🌹 🌹 inajin dadin comments dinku, sauran masoya wanda nasani da wanda bansaniba ina godiya If you want Join the what's app group via this link 👇👇👇👇👇 @https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL Or contact me via my number, i mentioned at the above page If you are not reading the novel please don't join. [09/04, 12:29 PM] Ayshercool: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE7️⃣  60_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Jalila da kyar take fizgo numfashi, nufota yacigaba dayi, yana zuwa seya wuceta yatafi gurin Tv yanata shan tabarsa, yaje yasaka wayarsa a caji, Jalila kuwa se binsa take da kallo, yagama sa cajin ya taso yakuma dawowa harya wuceta ya dawo ya zauna a gabanta ya kura mata ido, dauke nata idon tayi, "naga kina son kallona ne shiyasa na zauna kigama karemin kallo" ya busamata hayakin sigari a fuskarta, da sauri ta dago tareda toshe hanci, ta dan fara tari, "wai meye haka, Allah ya sawwake inzauna ina kallonka, kato da kai kazomana gida tube sekace dakinka" "dakin Jawwad dakina ne, dan haka ko tsirara naga dama zanyi yawo" yunkurawa tayi zata mike, ya maida ita kan kujerar ya kafeta da ido, yasa kafarsa daya a gefenta, ta kalli inda yasa kafarsa aranta tace kalli jikinsa duk gashi kaman wani dan biri, lighter ya jefomata yasa wata sigari a bakinsa, yaimata alama ta kunna masa, wani mugun kallo tayi masa ta dauke kanta "Allah ya kiyaye ya rufamin asiri, nikabani hanya in wuce, kalleka dan Allah" hannunta daya yakama cikin mugunta ya murde mata yatsu, ihu tayi saboda zafi, take tafara zufa cikin tsawa yace "Kunnamin ko tarihi ya maimaita kansa, inkuma duramiki sigari yanzun nan" jiki na bari ta kunna lighter ta mika hannunta ta kunna masa, "dan Allah ka sakarmin hannuna, yatsuna zasu cire" a hankali yasakar mata hannu, idonta har yayi ja, yacigaba da busa mata hayaki, gashi ya tareta da kafa bazata iya guduwa ba, hannu ta kai zata toshe hancinta, "wallahi kika toshe hancinki sena wanka miki mari, sena baki mamaki da hannunki zaki shata" bashiri ta ajiye hannunta yana busa mata hayaki, se tari takeyi tana dauke numfashi "gaskiya Jalal dan iskane bashida mutunci, yanzu inna matsa da rashin kunya ze iyayimin akuya" seda ya shanye tabarsa tsaf sannan yadubeta "nine Namiji mara daraja ko? Ni Jalal nikike zagi ko?" shiru tayi tana kallonsa, daka mata tsawa yayi "ba dake nake ba kike wani kallona mara kunya" cikin dakewa tace "karya nayi, aiba kadyanayi ba namiji me daraja baze abunda kake ba" "hakane Amma kin bar kari tun ran tubani, kinyi sake namiji mara daraja yamiki Illa, wadda bazaki ganetaba a yanzu, idonki kawai ya nuna a tsorace kike kar in miki wani abu, ba abunda zan miki a yanzu, amma kisani bana yafiya, bana mantuwa, sena hukunta ki akan cin mutuncin dakikemin bazan kyaleki ba, sena gwada miki abunda nakeji idan kika ci zarafina, kidena shishshigi akan abunda baki saniba" Yayi ajiyar zuciya "tashi ki tafi kibani guri kuma kar inkuma ganinki a part din Jawwad dai 2 wannan lokacin, dan kinsan baya nan inkuma kika kuma zuwa to nasan abunda kikazo gani" Sumi2 ta tashi, taje bakin kofa ta tsaya ta kalleshi "to me zanzo gani, kaikanada abun kallone jiki duk gashi ba kyan gani sekace jikin biri, kokuma wannan jijiyoyin zanzo kallo, jiki kamar dan wrestling aikai ko kyan gani baka dashi, kasa wannan katon hannunka ka matsemin yatsuna Allah yasakamin dan ban yafeba kuma duk barazanar ka bazan dena fadan gaskiya ba, sannan kayi kadan kayimin Illa ko a yanzu ko a gaba, mugu kawai "tai ficewarta, Jalal kam yana jinta tana banbaminta ko dago kansa beba balle ya kalleta. Ta wuce cikin gida tana yarfa hannu saboda zafi, tana zuwa daki taga Nana ta shirya da alama fita zatayi " Ya dai naganki kin hade rai, me akayi miki ne? " Jalila ta yamutsa fuska "Bakomai" "Shikenan dama kenake jira kizo ki rakani gidan, Yaya mairo, tace tana son ganina" "Tab amma badani Jalilan bako?" "Kamar yaya?" "kamar yadda nagaya miki mana, haka kurum ketace tana son gani baniba, dan haka ba inda zani, banje gidanta ba ma cimin mutunci take, inaga innaje mata gida, kitafi kawai, ba inda zani" "Shikenan tunda bazakiba, dama banason tafiya nikadai ne" "sauka lafiya ki gaishesu"       Bayan Jawwad ya dawo daga school suka zauna domin cin Abinci rana shida Jalal, Jalal ba karamin dadi yajiba ganin wainar shinkafa ce, sunci Abincin nan sosai, Jalal yace "Jawwad dan Allah in da sauran Abincin nan ka zubamin in kaiwa daddy, kasan yana son wainar shinkafa" "Hakane Allah yasa akwai, bari inje cikin gida in duba" Jawwad ya tafi domin dubawa koda Abincin, Jawwad na fita aka kirashi waya, Jalal ya daga wayar ya duba, seyaga sunan Hanan, Murmushi yayi ya daga wayar "Jawwad ka manta dani ko? Baka daga wayata, nashiga wani hali banajin dadin abunda kakemin" gyara murya Jalal yayi "ba Jawwad bane, Jalal ne" "Jalal kaine yakake ya gida" "lafiya kalau ya Abdallah, kodayake muna waya dashi" "Yana lafiya, Jalal kaga abunda Jawwad yakemin ko? Banajin dadin hakan, dan Allah kasa baki, Jalal inason abokin ka da wasa na dau abun amma yanzu serious nake sonshi, Jalal help me, so masifa ne, da ban yadda da hakanba se yanzu" "kinaji Hanan, kiyi hakuri Jawwad inyace baya Sonki karya yake, kawai yana duba alkar dake tsakaninki da kanwarsa, amma karkidamu zamuyi magana dashi" (🙄🙄🙄 nikam nace su Jalal dama an iya rarrashi haka) Ajiyar zuciya Hanan tayi "to nagode sosai Jalal, agaida su Ilham" Jawwad ya shigo da food flask a hannunsa, ya ajiye ya kalli Jalal, "gashi nan Abincin Baby ne tace abawa daddy, amma dawa kake waya haka a wayata" "Jawwad" "Na'am ina jinka" "Meyasa kakewa yarinyar nan hakane" "Wace yarinyar kenan?" "Hanan mana, ta damu da kai, kamanta kaikake min fada akan Ilham segashi kaima kanayi, meye marabar Hanan da waccan fitsararriyar banzan, ba gara Hanan din bama tafita nutsuwa da saukin kai" "Haba Jalal, Jalila da soyayyar ta na tashi, banason yin abunda zan bata mata rai, tarayyata da Hanan baze haifar da da me idoba, kuma Hanan da kake ganinta itama rigimammiyace, kaikewa Jalila wani kallo dan bakwa jituwa" "Jawwad yakamata kakoma hankalinka, kayi wani abu akan yarinyar nan mana, kana ganinta so classic nasan da wanine ba kaiba zata sauke ajinta tace tana sonsa ne? Kayi wani abu mana" tsaki Jawwad yayi "Ina tsawon shekaru Ilham ta dauka tana nuna maka so, kai mekayi akai" "Jawwad kasani nasani, nida Ilham bamu dace ba, kuma kasan dalili, kuma bari in sake jadadda maka, kokuma in tunamaka wani abu, mahaifiyarka bazata taba bari ka auri Jalila ba, musamman in wannan magananniyar matar tana nan, kaima kasani, kayi tunani Jawwad kafin al'amura su kwabe maka" yana gama fadin haka ya kwashi food flask din yai ficewarsa, yabar Jawwad a zaune yana tunani. Jalal yana zuwa gida ya tafi part din daddy da fara'arsa, "daddy ina fatan bakaci Abincin rana ba? " "banciba ina shirin ci dai" "Abincin daka fiso nakawo maka" Jalal ya turawa daddy flask din ba karamin murna daddy yayi ba daganin Abincin da Jalal ya kawo masa, "Jalal inaka samo wannan Abincin?" "a gidansu Jawwad" "yaushe rabon da inci masa" daddy ya dan kalli Mummy "Madam kindenamin Abincin gargajiya, mussaman favorites dina" "hmm ba gashi danka yakawo maka ba sekaci ai" daddy yai murmushi "Jalal wayayi girkin nan yayi dadi" "nima bansaniba" Mummy tace "nasan baze wuce Jalila ce tayishiba, dan Maama bata fiye yin girki ba Nana kam dama ba a maganarta akwai son jiki" daddy yace "Jalal inka koma ka turomin takwararka, kafin inkoma England inason inkuma cin irin Abincin nan" hade rai Jalal yayi "daddy waibaka san sunanta bane zaka dinga cemata takwarata" murmushi daddy yayi irin na manya "hmmm to ko in tunamaka tarihin yadda aka samata sunan ne? Dan naga kaman ka manta" "Wai daddy meyasa kake son yimin haka, abune yafaru shekaru da suka wuce kuma kuruciyace baya wuce ba" murmushi daddy yayi "kaji tsoro kenan" "niba wani tsoro danaji" "hmm Jalal kenan, a shikenan tunda kaki yadda" ganin daddy yana neman takura masa yasa yatashi ya fice, bayan fitar Jalal ne Mummy ta kalli daddy "daddyn Jalal, inason muyi magana da kaine" "to ai gani ina jinki" "Dama gani nayi lokaci yayi daya kamata mucika muradin yaran nan, ina ganin Jalal idan akayi masa aure ze samu nutsuwa, ze rage abubuwan dayakeyi" Ajiyar zuciya daddy yayi "to yanzu wace yarinyar kike gani zata auri Jalal a wannan halin dayake ciki?" "to ai Jalal yanada wadda yakeso, ga Ilham nan suna son junansu, yakamata kawai ayi magana asaka rana" "kin tabbatar da duk su biyu  suna son junansu" "Eh mana sun son junansu, yakamata ayi magana kaje kasamu baban Ilham ayi maganar auren nan" "Kina ganin ba matsala a yin hakan, sunada banbancin halayya, kaman zamansu bazeyi dadi ba" "kaga tunda dai suna son junansu a haka ai shikenan" "Amma ni Jalal be taba yimin wannan zancen ba" "to aini gana nagaya maka" daddy yayi Ajiyar zuciya, be kuma cewa komai ba". Jalila kwance akan gadonsu ta dakko wayarta ta kira Alhaji Kabiru amma be daga ba, dan haka ta sauka tafara chatting, tana what's app tana hira da zahra, setaga Alhaji Kabiru yakirata, ta daga wayar amma batace komai ba, setaji yana cewa "Jabir Nakiraka bata shiga, se yanzu tashiga, kayan sun taho daga kudu, munyi waya sunkusa karasowa kano za a sauke a gidan gonata, kaje ka karba se ka rarraba musu cikin dare, kayiwa Jeje magana shima yazo ya karbi nasu" shiru Jalila tayi, wane irin kayane wannan? ta kashe wayar , ta maimaita "Kaya a rarraba cikin dare, kuma hada Jeje" what's app ta koma da sauri tai masa sallama, amma beyi reply ba, ajiye wayar tayi tanata tunani, besan lambar waya kiraba kenan, "Allah nagode maka nafara samun hint akan mutumin nan, Allah kabani mafita" wayarta takuma dubawa setaga ya amsa mata sallamar "barka da rana, ranka ya dade yakake ya harkoki" "lafiya kalau, wake magana?" shiru Jalila tayi tana tunanin wani suna zata gayamasa, kawai setace masa "Halima ce" "Wace haliman?" "hmm duniya da gaskiya kuwa? Wadda kabawa complementary card a banki" "ohhh am so sorry, kuma seda na kawo kece dan na dau muryarki, sedai dan bansan sunanki bane, ina fatan kina cikin koshin lafiya, Gimbiya Halima" "Ina lpy" "Amma nayi mamaki, dakika nemeni, danaga kin yaga card din banzaci zaki nemeni ba, nayi farinciki gaskiya" Jalila ta biye masa suka dinga chatting, daga baya ta sauka ta rufe data dinta, Jinjina kai tayi, "lallai wannan mutumin zakayi saurin fadawa tarkona, Kuma abun mamaki, wani kayane ake rabawa cikin dare, ga sunan Jeje ya ambata, to me hakan ke nufi, wannan ya tabbatar da yana hulda da Jeje, to wace irin hulda Alhaji Kabiru yakeyi da JeJe haka, wanda yasashi zuwa gurin birthday din Jalal a boye, kai akwai lauje cikin nadi" tana tsaka da wannan tunanin still aka kuma kiranta a waya, koda ta duba tagane lambar Dan sandan nan ne, tsaki tayi harta ajiye wayar sekuma ta yi wani tunani ta daga "Salamu alaikum" amsamata yayi sanna yace "beauty barka da wannan lokacin ya kike seda ta dan tura baki gaba "Lafiya kalau" "dama cewa nayi bari inkiraki inji lafiyar ki, sannan inaso inzo gidanku in ganki" "What gidanmu kuma mezakayimin" "Meye abun tashin hankali, inasonki ne aurenki nakeso inyi, please" ture wayar gefe tayi takama dariya sannan ta maida wayar kunenta "Ni wallahi kabani kunya yar baby dani yaushe na isa aure, kuma ya za'a yi Abbana ya aura maka ni, ni gaskiya yarinya ce" yadda take shagwabar ba karamin birgeshi takeba "Haba yar baby wayace miki baki isa aure ba sannan kuma babu kunya a soyayya" "Babana bazemin aure yanzu ba kuma yariga yabadani, amma nima bansan wayabawa ba" Ajiyar zuciya yayi "bayarwa ba aure bane dan haka zancigaba da neman aurenki" "Hmm shikenan se anjima, zanyi karatu yanzu" "To Baby tunda kinki gayamin sunanki, ayi karatu da kyau, inkinki mu hadu zannemo gidanku inzo gurin Abbanki da kaina" "Sekazo" daga nan ta kashe wayarta "tab ina zan kai wannaan mutumin" Bayan sallar la'asar, Jalal yakoma gurin Jawwad, koda yaje ya tarar dashi wani iri kaman mara lafiya, Jalal bebi takan tambayar meyake damunsa ba, saboda yasan akan maganar dazu ne, "Jawwad daddy yace yana son ganin kanwarka" "wacce daga ciki?" "wadda ta yi Abincin yau" "Jalila ce tayi, Allah yasa ba laifi tayiwa daddy ba" "nima bansaniba yace dai taje yanason ganinta" "zangaya mata Insha Allah" "yayi kyau bari in tafi in kyaleka naga kana cikin damuwa tunda mukayi magana dazu, karka bata lokacinka gurin dogon tunani, maganata itace gaskiyar lamari, duk inda zaka juya kayi tunani kasani maganar dayace mahaifiyarka da yan uwanta basa som wadda kakeso kuma bazasu bari ka aureta ba, dan haka mafita kacireta a ranka ka maye gurbinta da Hanan" "Jalal tayaya wannan abun ze yuwu, ni Jalila nakeso, Kuma maganar Maama nasan zata amince ne in na lallabata" murmushi Jalal yayi "Shikenan Allah yabada sa'a, amma karka manta da batun kiran daddy" yana gama fadin haka ya fice. Tunda Jalal yafuta tunani ya damu Jawwad, wayarsa ya dauka ya kira Jalila suka dinga hira, har ya manta da abunda yake damunsa, daga nana yagaya mata daddyn Jalal yace taje yanason ganinta. Jalal yana komawa gida, kozama beyiba kiran Hannah yafara shigowa wayarsa, tsaki yayi ya ajiye wayar ya shiga sabgoginsa amma tacigaba da kiransa, takirashi yafi sau goma, a fusace Jalal ya dau wayar "Hannah kina bina bashine? Wannan kiran haka meya faru?" "Niko nake binka bashi Jalal, meyasa kake wahalar dani hakane? So seya koma kiyayya bana sukuni idan banganka ba, Jalal dan Allah ka tausayawa zuciyata, Jalal kasan Masifar So kuwa? Na tabbatar dakasani dabakaimin haka ba, Jalal ka dubi girman Allah ka tausayawa zuciyata" murmushi Jalal yai kaman Hannah naganinsa "Hannah kenan, ina mamakin sanda soyayyar da kikemin ta rikide zuwa ta gaskiya abun akwai mamaki gaskiya, but don't mind me akan abunda na fada kinji, nagaya miki gaskiya tun farko, baze yuwu ace nayi yawon club sannan ace matata ma tsohuwar yar club bace, dukda zuwa club dinmu yanada banbanci, kiduba a samarin club dinnaki kisamu wani ku daidaita amma ba Jalal ba" "Amma Jalal ai nace maka na tuba wallahi inka aureni zandena" "Ni ABDUL JALAL nafi karfin ragowar garorin bariki, ki kiyayeni" yana gama maganar ya kashe wayarsa. Daddy sam yakasa yadda da batun Mummy gameda Jalal, shidai yasan Jalal ko zancen mata bayaso ayi masa, amma ya akayi haryake soyayya da Ilham besaniba dukda yana dadewa baya nan, amma yasan da zeyi masa zancen, dan haka ya yanke shawarar kiran Jalal yaji tabakinsa.     Hanan na kwance akan katafaren gadonta, tayi zurfi a tunanin ta, taji an turo kofar dakinta, dan daga kai tayi taga mum dintace, batace uffan ba tai shiruu tacigaba da tunani, gefenta Mum tazo ta zauna ta dafata "Auta meyake damunkine, yan kwanakin nan kullum cikin damuwa kike meyake damunkine" a hankali Hanan ta tashi zaune "Mummy na ba wata damuwa, damuwar school ne kawai kinsan akwai tension na makaranta" "Hakane Hanan, amma yusuf yakawomin kararki fa" dan ya mutsa fuska Hanan tayi "Meyace miki?" "gaba daya kin canza masa yakasa gane kanki, meyake faruwa ne?" "mummy kinsan tun farko dama ni bawani yimin yaya  ba kinsani, Mummy kinsan wani abu kuwa" "A 'a sekin fada" "tun farko kinsan ba son Yusuf nakeyiba, Mum zuwana kano naga Yayan Jalila cousin dinta wanda takeso, da saboda in tsokaneta nace ina sonshi, amma daga baya abun yakomamin Gaske, Mum ina son Abunda Jalila takeso ne, kuma yazama dole tabarmin dan basu dace ba". Share please More Comments More Typing............................. Daga Alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ Comments dinku yana sani nishadi ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP ina yinku irin sosai din nan Allah yabar zumunci yabar kauna Join the what's app group via this link ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP :https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL Don't join in ka/kinsan baka karanta novel din 07063065680  🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  8️⃣/61_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Wani irin Kallo Mum tayiwa Hanan "I don't think you are in your senses, Hanan, kawartaki dukda yarinyar ba wani yimin tayiba, amma son da kike mata yasa na kyaleku tare, amma hakan bazesa inkasa gayamiki gaskiya ba, Hanan inkikayi haka baki kyautaba, hakan ba daidai bane, Jalila taana kaunarki meyasa zakiyi mata haka" kwalla ce ta taru a idon Hanan "Mummy ki fuskanceni banyi haka dan cin amanar Jalila ba, Mum wallahi makauniyar soyayya nakewa Jawwad, Mummy he is very nice and gentle, gashi salihi, Mum soyayyata da Jawwad mafita ce kuma ceton Jalila ne, inajinta a zuciyata kamar yar uwata ta jini, dan haka bazan iya cutar da itaba all i know is that inason Jawwad " "Kamar yaya kenan, tayaya kike son maida karya gaskiya" Labarin abunda ke tsakanin Jalal da Jalila tabawa Mummy, ta nisa tace "Mum ko bankuma cewa komai ba kinsan Jalal is her e destiny, ita kadaice zata iya sadaukarwa domin ceton sa, Mum mahimmanci Jalal a rayuwarta ne yasa ake mata nuni da halin dayake ciki a mafarki, Mum kibani karfin gwiwa, zanyi meyuwuwa in dauke hankalinta daga kan Jawwad, sannan zan temaketa akan rayuwar Jalal" Jikin Mum ba karamin sanyi yayiba dajin labarin da Hanan tabata, "Shikenan Auta, zancigaba dayimuku Addu'a Allah ya zaba abunda yafi Alkhairi".      Jalal cikin gida ya tafi domin samun yin hira da daddy, yana zuwa ya tarar da Ilham a babban palour da waya a hanunta tana waya, kotakanta bebi ba yanufi part din daddy, bayansa Ilham tabi da kallo "muje zuwa Jalal zakaga tsiya" Jalal yana zuwa ya tarar da daddy a  palour dinsa suna hira da mummy, daddy na ganinsa yai murmushi "dan halak kaki ambato, zancenka nakeyi a a raina karaso Dama inason ganinka dan gidan daddy" "to gani mezaka bani, Jalal yafada yana zama akan kusa da daddy" "Jalal magana nakeso muyi da kai, Mum dinka tazomin da magana nayi murna da jin hakan shine nakeson ji bakinka" Mummy tai farat tace "Ba dai maganar da mukayi dazu bane, ai mungama magana dakai, meye kuma na tada wannan zancen, kayi abunda yakamata kawai" daddy yace "A a Madam karmuyi gaggawa, dole mubi komai a sannu sannan inji ta bakin kowannensu" "A'a fa ai mungama magana wannan kawai maida hannun agogo baya zakayi"   Jalila da sallama ta shigo palourn, Ilham na palourn amma tai mirsisi taki amsawa, "Aminiya Ilham amsa sallamar ma seyazamo miki aiki, amsa sallama dabi ace ta kyakkyawan musulmi, karki zama irin yayanki nan mana" tsaki Ilham tayi tareda fadin "meye hakane wai? Ke kullum in baki shiga sabgata  ba bakyajin dadi ko? Ina ruwanki da nida danuwanane mayya" "Aini indai a irin sha'anin nan ne to nafi uwar mayya naci, mayya in akayi magani ana samun nasara nikuwa babu abunda zakiyi kiyi nasara akaina, sannan duk abunda ba'aso ni shinakeyi dan aji haushi, and the most craziest part of me is that bana riko, yanzu zamuyi fada yanzu zan manta, duk abunda na rike a zuciyata nake fushi akansa to yanada mahimmanci a gurina, dan haka nibana gaba dake Ilham dan bakikai inyi hakan ba dake, sannan kuma bazan fasa bata miki raiba in har kikayi abunda yaci karo da Ra'ayina sedai kiyi hakuri " Lallai Jalila tacika yar rainin hankali, wulakanci goma da ashirin. Duk yada Mummy tayi a wayance kar Jalal yaji zancen nemamasa auren Ilham daddy yaki, karshe a fusace Jalal yace" waini meye hakane daddy, afadamin komene mana, inbaza ayiba meye na dakko maganar agabana, nibanason irin haka fa" "Ohh ka kwantar da hankalinka yaron kirki, aiba abun tashin hankali bane, maganane me dadi akanka, maganane nacika maka burin rayuwarka, Mummy dinka tagama yimin bayani akan komai, nagame da abunda ke tsakaninka da Kanwarka Ilham, dan haka zanje muyi magana da mahaifinta asa rana, nayi farinciki da har kafara tunanin aure Jalal, cigaba yafara zuwa a rayuwarka kaga...... "Enough daddy" Jalal yai maganar a fusace, "Wannan maganar daga ina? Duk matan duniya in rasa wadda zan aura se wannan, in har farinciki kake nafara maganar aure, to da saurana, wait wai wama yagaya maka wannan maganar, kodayake base ka gayamin ba nasani," ya kalli mummy "Ke kika gaya masa nasan haka, nidake na taba cemiki ina son wannan yarinyar ne? Meyasa kikemin hakane, meyasa kikeson kuma rusa al'amuran rayuwata, ke a ganinki Ilham ta dace da zama matata, kimin adalci kiyiwa kanki mana, akoda yaushe kidena duba maslahar kanki kawai, kuma Ilham tunda Ubanta na raye se ta bar gidan nan, ai ba gidan ubanta bane ba, akanme za a dinga batamin rai haka, wallahi sena kakkarya yarinyar nan inga uban da ze tsayamata" daddy yai gaggawar mikewa da nufin tare Jalal amma Jalal ya kauce ya nufo hanyar fita, Ilham taiwa Jalila wani mummunar kallo "ai dama da ganinki base an fada ba ke mayyace, bari inkuma jadadda miki, duk maitarki kurwata data Jalal tafi karfinki haka kika ganmu haka zaki kyalemu, nidashi mutu ka raba" "to dan kincemin mayya ai ba haushi zanji ba, ko ina cin kurwa bazanci taki data Jalal ba saboda bazanci kazamar kurwa ba, kuma kina bani mamaki, dakikancinki yayi yawa Ilham bansan lokacin dazaki gane cewa niba abunda zanyi da wannan dan giyar ba, kuma kema dakike ta wahala akan se ya aureki don cikar burinki, ABDUL JALAL baze taba aurenki ba Ilham, tunda yace baya sonki baze sokiba, kuma kinsan daddyn sa yana goyon bayansa, nasan hanya dayace dake dazakibi ki aureshi hanyar sihiri kuma wannan hanyar bata bullewa" da sauri Ilham ta kalli Jalila tanaso tayi magana amma takasa, "Karya kikeyi, Yaya Jalal yana sona kuma bani da wani mugun nufi akansa, ubanwa yagaya miki saboda wani dalili nakesonshi, munafuka duk masifarki wallahi haka zaki kyalemu, dan banga uban daya isa ya hanani auren Jalal ba" "Eh kinyi mamaki ko? Ya akayi nasani, da bakinki kika fada, ba a gurin wani naji ba sannan..... " A gidan ubanwa na taba gayamiki ina sonki meyasa ba kya ganewa, sa'anki neni, mahaukaciyar inace ke dakike tunanin zan aureki? Yau zaki tattara kibar gidan nan tunda bana ubanki bane, akanme zaki dage cewar nikikeso nace bana sonki bana sonki meye haka wai, mekike nema a gurina ne Ilham" Jalal ne yakewa Ilham magana cikin fada, da sauri daddy ya fito tareda Mummy, daddy ya karaso inda Jalal yake "haba Jalal ai duk abun be kai hakaba, koba komai kanwarkace, kayi hakuri" "Daddy wace irin magana kakeyi hakane, seta bar gidan nan koni inbar muku gidan, akan me za a takurawa rayuwata, for what reason dad, ace kullum mahaifiyata batada buri se ganin bacin raina" Jalila rasa abun cewa tayi, ta kalli wannan ta kalli wannan, "Haba Jalal ya ina matsayin mahaifiyarka zakace bana son cigabanka, Aurenka da Ilham alherine ni banga aibun Ilham ba, a tunanina komai ya wuce" wani mugun kallo Jalal yaiwa Mummy duk ya birkice idonsa yai jawur "Kikace komai yawuce, karki yaudari kanki mana, kodayake son zuciya baze barki kidinga ganin gaskiya ba, nayi dana sanin kasancewarki mahaifiyata, kullum bakida burin daya wuce gayyato matsala cikin rayuwar dan dakika haifa, haka sauran iyaye sukeyi" Jalila kasa jure abunda Jalal yake tayi , wanda hakan yasa ta mike ta fice daga palourn jikinta a sanyaye, tafito ta jingina da bango tai shiru tana tunani "meyake damun Jalal ne? Dole nasan dalilinsa na cin zarafin iyayensa musamman mahaifiyarsa, ina tausayawa Jalal ya mutu yana sabawa iyayensa, zanso inji dalilin hakan kozan iya temakamasa, wulakanta iyaye ba abune me sauki ba" Ilham se kuka take, duk yadda daddy yaso ya shawo kan Jalal ya kasa, seda yai me isarsa sannan ya bude palourn ya fito a fusace, yana fitowa Jalila tana gurin a tsaye akan hanyar daze wuce, hannu yasa ya hankadeta gefe yai gaba abunsa ya nufi part dinsa, mamakine yacikata, kodayake ba abun mamaki bane kadan daga aikin giya. Jiki a sanyaye ta baro gidan, sedai me tana fitowa taga motar  Hannah a kofar gidan, ta fito tana ta kiran lambar Jalal amma yaki dagawa. Jalila a ranta tace "lallai Jalal kana cikin iftila'i" dayake duhun magariba yafara yi, Hannah bata gane wacece ba, dan haka tace "Dan Allah baiwar Allah naga kaman daga gidan kika fito Jalal na ciki ne?" Karasawa Jalila tayi gabanta "kalli da kyau baki gane wacece bane?" se yanzu Hannah taganeta "dama kece? " Eh nice, meyasa bakyajin kunyar zuwa neman Jalal ne? Mace da aji akasanta abunda kike zubarda mata kike" "Ke kome nakeyi beshafeki ba kingane bana son surutu, Jalal yana nan ne?" "Eh Jalal yana nan, amma kaman yanda nagaya miki kwanaki yauma hakanne baze zoba, huwaila kike kowa, ni mamaki kike bani meyasa bakida kunya ne, me yayi miki haka kika uzzurawa rayuwarsa" "Ke dakata, ba abunda yadameki, Ko agaban uban waye zan fada son Jalal nake, nan da kankanin lokaci ze aureni" murmushi Jalila tayi "to Ilham dinfa? Kokina tunanin zuba miki ido zatayi ki aureshi, naga kaman tafiki sonshi dan tafiki himma ina tunanin za'asa sa ranar aurensu" zare ido Hannah tayi "dagaske kike?" "nasankine dazan tsaya ina miki wasa" "Ni Jalal zewa haka wallahi basu isaba dagashi har kanwar tasa, Nikadai zan aure Jalal in rayu dashi sena lalata komai, in bahakaba sena masa sharrin da nan duniya babu wanda ya isa ya fiddashi, nayi wannan alkawarin" "kaman ba yanzu kika gama cewa kina son aurensa ba, kin dade kina cutar da rayuwarsa, ranar birthday dinsa kun shirya yimasa wani abu, ni nasaka aka dauke shi daga gurin bayan kin bashi kwaya kin bugar dashi, a wannan lokacin nakara tabattar da bakinku daya da da wannan dan iskan, sannan kisani babu wani sharri dazakiyi masa yayi tasiri akansa Allah yana tareda shi, dan haka wannan ba soyayya bace, ba kyasonsa dan Allah, ku saurari yadda karshenku ze kasance " Jalila ta juya tai gaba, da sauri Hanna tabi bayan Jalila tana mata magana akan dan Allah ta tsaya, amma Jalila taimata banza tai wucewarta zuciyarta cike da tunani. Ba karamin mamaki Hannah tayiba, gaskiya Jalila tabata mamaki ya akayi haka, dama ita tasaka aka dauke Jalal, ita ta turasa wannan shirin da suka dade sunayi, to meye manufar Jalila akan Jalal. Jalila kam Tana zuwa gida  ta tarar da Nana ta dawo daga gidan Yaya mairo, ta tarar dasu a palour Nana tana kuka, Maama tana rarrashinta, kaman ta wuce seta fasa ta tsaya "Nana lafiya kuwa" "ke bana son gulma ina ruwanki, wuce kitafi inda zaki, uwar tsegumi kawai" ba Jalila ba hatta Nana seda taji babu dadi abunda Maama tayi. Dakinsu ta wuce taje tai alwala tai sallar magariba, tafara tilawar al'qur'ani, wayarta se ringing takeyi amma bata dauka ba harseda ta idar da karatunta, tana duba wayar bakuwar lamba ce da akayi ta kiranta da ita ranan, dan haka ta ajiye tacigaba da sabgoginta, har bayan sallar isha'i Nana bata shigo dakin ba Jalila kuma bata nemeta ba, wayarta ce takuma daukar ringing, a fusace Jalila ta dauka "Wai ya hakane ankira ban daga ba kuma se kuma kira ake, haba inkuma ina wani uzurinne fa?" "Tuba nake, adon gari, nakasa samun sukuni ne amin afuwa" "waima wake magana?" "Suleman ne" "waye kuma Sulaiman ni bansan wani suleiman ba" "yi hakuri, wanda kuka hadu shekaran jiya kika bashi lambarki" seda Jalila ta dan yamutsa fuska dan ita ta manta dashi, "ohh nagane sannu yakake?" "lafiya amma ba lauba, nakira nakira baki daga ba, inata kewar muryar nan taki" "Hmm to ai yanzu gashi kaji" "Hakane nayi farinciki fatan kina lafiya" "eh lafiyata kalau" haka sukayi waya da Jalila kaman ammata dole, ita kunya ma yake bata da haushi inyayi wani abun tsoho dashi se wani tabara yake mata. Nana ce ta shigo jikinta a sanyaye, Jalila bata kulata ba taje tazubo abincin dare tanaci, bayan tagama tai shirin bacci ta haye gado tana chatting dinta, Hanan tana online, suka fara hira kaman abun arziki, har Jalila take bata labarin Alhaji Kabiru, dakuma wannan dansandan, Hanan tabata shawarwari, Jalila tagaya mata abunda yafaru yau agidansu Jalal, Hanan ta fara kunna Jalila "queen gaskiya Jalal is destined to be in your life, dan haka ki kauda wata Ilham da Hannah gefe kisa kai dan kun dace sosai, ke kadaice zakiso shi tsakani da Allah ki temaki rayuwarsa" "Ke bana son shirme Allah ya kiyaye meye abunso a gurinsa, meye abun birgewa a gurin mashayin giya" "A'a adena zakewa dai, kar nan gaba azo a gigice akan sa ehee dan bazan bawa mutum shawara ba" "Narasa meyasa kike likamin wannan sakaran, inada Yaya Jawwad ba abunda zanyi da wani Jalal" "Ke dakata, Jawwad nawane kuma ni kadai, gara ki rungumi Jalal tun lokaci be kuremiki ba, Jawwad baze aureki ba nina gayamiki" rufe data Jalila tayi, dan hartaji wani bacin rai yana tasomata" Nana ta kalli Jalila tace "Jalila bazaki tambayi meyasameni bako? Kina kallo ina cikin wani yanayi" tashi Jalila tayi takoma kusada Nana "Nana hawayen nan naki jinake kaman ni nake zubar dashi, kinji abunda Maama tace dazu, shiyasa ban takuramiki inji meyasaki kuka ba bansaniba kobe shafeniba" "haba Jalila har akwai abunda ze sameni dabe shafekiba?" "to yanzu kiyi hakuri gayamin meya faru?" Nana ta share hawayenta sannan tace "Jalila wai kiran da yaya mairo tayimin, waiso take ta hadani da Nura waiya aureni" "Waye kuma Nura" "babban danta ne, wallahi Jalila inda abunda natsani na bude ido ingani be wuce wannan Jakinba" "Amma Nana meyasa?" Wasu hawayen ne suka kuma zubowa Nana "Jalila dan dabane fa, mugun tantirine har prison yayi, ga shaye shaye na masifa, ba ilimin addini bokon ma secondary ya tsaya, wai dan zalunci shi takeso ta hadani aure dashi, wallahi akace sena aureshi sena kashe kaina, inkuwa aka kaini gidansa sena ksheshi na kashe kaina" Da sauri Jalila ta rufemata baki tareda fadi "subhanallah, Nana karki kara fadin hakan, wannan maganar tayi tsauri, amma me Maama tace?" "cewa tayi inyi hakuri, zatasan matakin dazata dauka, nikam hakan beminba kawai ajanye wannan maganar, inbahakaba gara in bar gidan nan" "Nana nace kidena irin wannan zantukan mana, kiyi amfani da kwakwalwarki, kina tunanin Abba ze yaddane, baze yadda ba dan haka kiyi hakuri, ba abunda zesa ki aureshi Insha Allah mutumin kirki zaki aura, zan tayaki addu'a kinji My Nana kidena kuka, banaso" gyada kai Nana tayi sannan tace "Saboda tsabar son zuciya irin na matar nan waishi kuma Yaya Jawwad da Naja za'a hadasu, wallahi inshi ya yadda nibazan yadda da auren dan daba ba, gara in kashe tsinanne in huta" Comments nakeso ba sticker ba, kokuma just thanks, A kullum ina alfahari daku masoya wannan novel Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  9️⃣/62_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Seda gaban Jalila ya fadi, kirjinta ya buga da karfi, amma ta dake ta maze, ta lallaba Nana suka kwanta, amma bacci ya gagari Jalila, gaba daya abubuwa sun cunkushe mata ta rasa menene mafita, dan haka ta tashi taje tayo alwala ta tada salla. Washegari da safe seda Jalila takusa sasu su makara sannan suka tafi makaranta, yauma sir hafiz yashiga ajinsu Jalila, har yayi lectures yagama hankalinsa yana kanta, ita kam ko a jikinta, abubuwan dasuka dameta kawai take lissafawa, na farko damuwar Jalal, ga abunda Hanna tace, Hanan ma ta dage akan son datakewa Jawwad tana lika mata Jalal, ga abunda Nana tagaya mata jiya da daddare, gaba daya zuciyarta a cunkushe take tanason sanin waye Alhaji Kabiru ta hanyar yarsa dake ajinsu wato saleema, kallo daya zakayi mata kasan tana cikin damuwa, sir hafiz yana monitoring din duk moves dinta sam attention dinta baya kansa, dan haka yace ta tashi tsaye, ba musu ta mike, ya dinga yimata tambayoyi amma taki kulashi tayi masa shiru, lamarin yarinyar nan ba karamin daure masa kai yake ba, daya dameta ma kawai seyaga idonta ya cika da kwalla, tana nema tafara kuka. Dan haka ya kyaleta yacigaba da lectures dinsa ba tareda yace ta zauna ba, yagama tsaf sannan yace ta biyoshi office, banza tayi masa, tanemi guri tai zamanta ta kifa kai, tarasa meyake mata dadi, hawaye tafarayi tanayi tana gogewa, zahra ta dafata tace "Kiyi hakuri kidena kuka, nikaina banajin dadin abunda lecturer din nan yake miki, nasan ba dadi amma dan Allah kidena kuka kinji" sam zahra batasan meye damuwar Jalila ba dan haka tabita a haka, zahra tace "bari inje in siyo miki ruwa kisha ki wanke fusakarki" Jalila ba tace komai ba, zahra tafita taje siyo ruwa, a hanyarta ta dawowa, Su Samira suka datseta, suka sha gabanta, samira ta kalleta sama da kasa sannan tace "A tunaninki tarayyarki da wannan dakikiyar yarinyar zesa in fasa bibiyarki ne, wallahi yazama dole ki amince da bukatata, komai kike bukata na more rayuwa zanbaki shi, amma muddin kika cigaba dabin yarinyar nan, ina tausaya miki abunda ze biyo baya, saboda rayuwar taki dakike takama da ita, ita zansa a tarwatsa yadda sekin wulakanta a idon duniya " a firgice Zahra ta kallesu, Saleema tace "Zahra dama ce a gareki kina ganin su zee da salma duk asirinsu a rufe sunata hutawa, keme yasa bazaki yadda ba, waike ta Allah ko, wallahi duk matakin data dauka akanki kekika jawa kanki, sannan yazama dole kiyi gaggawar rabuwa da wannaan dakikiyar yarinyar. Daga nan suka wuce suka batta a gurin, a hankali ta furta" Nashiga uku, Allah ka tsareni daga sharrin wadannan mugayen" jiki a sanyaye tafara motsa kafarta "Ke! Ke!!" taji ana mata magana a baya, tsayawa tayi ta waigo, setaga sir Hafiz, "kigayawa kawarki kice mata bataji kiran danayi nata bane" jinjina kai kawai tayi, ta tafi aji ta kaiwa Jalila ruwa ta sha ta wanke, fuskarta Jalila ta kalleta, a sanyaye zahra tace "sir hafiz yace meyasa bakije kiran da yayi miki ba" jin maganar zahra a sanyaye yasa tace "lafiya naganki wani iri, me yafaru" zahra bata boye mata komai ba tagaya mata, "Jalila inaga dole mudena hulda tunda suka sakoni gaba, inacikin tashin hankali" ran Jalila ba karamin baci yayi, ta kalli zahra "har yanzu babu uwar datayi nakuda ta durkusa ta haifi wata shegiya dazata sa inyi wani abu ku indena wani abu dan ina tsoronta, dan haka nasiyi wannan rigimar koni kosu, musamman Saleema, bada ita zanyiba sa makyankyashinta zanyi" mamakine yacika zahra kaman ba Jalilan da take kuka ba yanzu abun tausayi amma yanzu itake masifa haka "Jalila meye kuma makyankyashi?" "ba ruwanki, kuma bazan dena hulda dakeba sedai kibar department din nan, in yaso ba tarwatsawa ba in sunga dama susakawa rayuwartaki bom, ba abunda ya shafeni bane tunda kedai bakida wayo bakusan yancinkiba, seki zauna wasu yan kwaya suna raina miki hankali saboda bukatarsu" tanagama fadin haka tatashi ta dau Jakarta tabar ajin, tabar zahra baki bude. Office din sir hafiz ta tafi, tana zuwa su samira na fitowa, kallon Samira tayi ido cikin ido tace mata "Kiki yayi shiga hurumina, karki yadda kisanni a ainihin kalata" ta juya ta nufi office din, tayi knocking yace ta shiga, yana zaune yana breakfast yana shan tea, dan kuramata ido yayi ya dauke kai yacigaba da abunda yake, har kasa ta durkusa ta gaisheshi dan dagowa yayi ya amsa mata, bata jira izininsa ba ta haye kujerar dake fuskantarsa ta maze hada jujjuyawa, aransa yace "Ikon Allah wanna yarinyar ba dai mulkiba" seda yagama abunda yake yayinda still yanzuma tunani take tanayi tana kokarin maida kwallar data taru a idonta, ya dan dubeta yai nazarinta nawasu seconds sannaan yace "Wayabaki damar ki zauna?" bata kalleshiba tace "bana son tsaiwa dazu ma daka tsayar dani a  aji kafata ciwo take" "Kodayake bakiyi kakar wahala ba, amma Meyasa kike kokarin boye baiwar da Allah yayi miki, meyasa kika zabi kidinga dizga kanki agaban yan ajinku? Kika fi maida kai akan tunani kullum?" shiru ta danyi idonta taf hawaye tace "ai kai ka janyomin, nagaya maka kadena tambayata agaban yan aji amma kullum seka tambayeni danka wulakantani, ni bazan bada amsa agaban yan ajiba, bana son sa ido" "Wayece miki dan in wulakantaki nake tambayarki?" "Zuciyatace tagayamin" murmushi yayi "tagayamiki ba dai dai ba, amma meyasa kike boye baiwar da Allah yayi miki, ga yawan tunani a class, you are too young ace kina tunani dayawa?" "Akan me zan nuna ni watace? A hakanma wasu sun tsaneni a ajinmu nibansan menayi musu ba," "Suwaye suka tsaneki?" "Samira da gangs dinta mana, kuma wallahi in basu fita sabgata ba senayu maganin yarinya " Kallonta yayi "I like your confidence, amma kidena wannaan maganar, yarinyar nan tanada manya karki sa kanki a matsala kinada kwakwalwa me ban mamaki, ba ruwanki dasu kiyi karatunki kawai" Jalila a zuciyarta tai murmushi "tab aikuwa bazan bar gurin nan ba senaji Labari sosai akansu, bari inbi da mutumin nan a sannu" Dan zumbura baki tayi "ni ina ruwana da wasu manyanta akan me zata takuramin, nima inada Allah kuma babana yana sona dan haka ba wanda zemin komai" "No bahaka bane, yarinyar tasan manyan yan siyasa, gata fitinaniya har yan daba ne da ita karkije tasa a miki Illa" Zare ido Jalila tayi ta lura yanajin dadin hirar dasuke dan haka tace "to sir amma aka kyaleta a cikin school din nan haka kawar nan tata tafi tsanata taana cemin dakikiya fa, They are terrorist in har mace za'ace tanada yan daba tazama hatsari a society" "Hakane amma ya zamuyi, hukumar makaranta bata dau mataki ba ance babu kwakwkwarar hujjar data tabattar dahakan kinga se hakuri, dan haka ba ruwanki dasu kiyi karatunki kawai kidena wannan tunanin" "To nagode sosai Insha Allah zan kiyaye, amma tunani yazamemin dole, anyway am very grateful with your advice nagode, Allah ya jikan mahaifa" murmushi yayi yace "Nima nagode Allah ya wuce mana gaba" ta dakko Jakarta ta fito. Jalal jiyake kaman inyayi kykyawan yunkuri zuciyarsa zata fasa kirjinsa dan bakinciki da bacin rai, daren ranar kasa bacci yayi, yasha giyar amma batayi masa komai ba, haka Jawwad yazo yasameshi da safe, juyin duniya yaki kula Jawwad balle yagaya masa meyake damunsa, haka Jawwad ya hakura ya kyaleshi ya tafi makaranta, yana nan zaune a palour yaji bacci ya sace shi, kira'ar Karatun Jalila ya dingaji a mafarki, wadda yagani a gidan telabijin shekarun baya koda ya farka daga baccin se yaji babu damuwar a taredashi, yai ajiyar zuciya yai shiru yana tunani wayarsa ce take ringing, kallon wayar yayi, sunan Hannah yagani, tsaki yayi yaki daukar wayar. Ilham hankalinta yagama tashi jin abunda Jalal yace jiya, kwana tayi batayi bacci ba, aiko sama da kasa zata hade bazata bar gidan nanba ba tareda ta samu abunda take soba, dan haka da sassafe ta tafi dakin Mummy, Kuka sosai tasakawa Mummy, "Mummy kingani ko, baya sona kinga wulakancin dayayumin, betabamin goriba se jiya dan kawai ance asa ranar aurenmu nikam nashiga uku Mummy, wallahi inban aureshi ba mutuwa zanyi" "Ilham meye hakane, kibi komai a sannu mana, kiyi hakuri bazaki bar gidan nan ba shima bacin raine yasashi fadin abunda yafada amma kiyi hakuri zan shawo kan matsalar" "Mummy nan da yaushe to? Nifa gaskiya na damu, bantaba tunanin Yaya Jalal zemin haka ba, anya kuwa ze yadda da aurena"? "Nace kiyi hakuri nasan abunda zanyi, aure keda Jalal ba fashi, kigoge hawayenki kidena kukan haka ya isa, tashi muje palour" Ilham ta goge hawayenta suka fito itada Mummy. Hannah tarasa meyakemata dadi, dagaske Jalal za'asamasa ranar aure da Ilham, aikuwa da Ilham ta tafka mafi girman kuskure a ratuwarta, to amma Jalila fa meye nata manufar, amma yakamata in gayawa Jeje wadda ta rusa masa shiri, amma yakamata inyi magana da Wannan yarinyar yana da kyau insan meye manufarta, wayarta ta dauka tayiwa Jalal message Jalal ya shiga yai wanka, message ne ya shigo wayarsa, ya dauka ya duba "Wallahi Jalal inbaka amince da aurena ba, narantse maka sena nuna maka ni cikakkiyar yar bariki ce, wallahi sena maka sharrin da harka mutu ba wanda ze yadda bakai kayi ba, ka rubuta ka ajiye gara tun wuri kanemamana mafita karka kuskura kayi ganganci auren wata, dan wallahi bakai ba kwanciyar hankali "Hmm bakida hankali" Jalal ya furta a hankali, yafito ya tafi cikin gida dan yunwa yakeji, a palour yaga Mummy da Ilham, be kulasu ba yaje ya dakko abunda ze dakko ya nufi part din daddy, Ilham ta zata yanzuma zemata masifar yace tabar gidan amma taga be kulata ba, yaje part din daddy ya zauna yaci Abincinsa suka sha hira, a haka daddy yaita masa nasiha akan hakuri dakuma yadena kyamar Ilham, se Jalal yaji kaman yai masifa danshi baya son adinga dangantashi da Ilham wai ya aureta, se ya tuno abunda Jalila tagaya masa akan baya yiwa mahaifinsa biyayya, haka yayi shiru daddy yaitai masa nasiha, Jalal yana gama cin Abincin sa ya kalli daddy "daddy kaga naji nadena, yanzu inason in dan fita ne" Daddy yace "ba dai kasaon fadan danake maka Seka dawo Allah ya kiyaye" "Ameen" ya tashi yabarwa daddy kwanukan Abincin a palour, Ilham tanata fargaba da Jalal yafito amma taga still be kulata ba ya fice daga palour, dakinta ta koma ta dauki wayarta takira yaseera, bugu biyu ta dauka "Hello yaseera kinajina?" "ina jinki Ilham lafiya naji muryarki a haka" "Yaseera ina cikin matsala" "matsalar me kuma?" Nana Ilham ta gayamata dukkan abunda yafaru jiya akan ance za'ayi maganr aurensu da Jalal. "tabdijan lallai Ilham akwai katuwar matsala, gaskiya yayan nannaki akwai taurin kai, dole musake shiri amma kunyi waya da ummane?" "A'a yaseera amma zanje anjima, wallahi banaso ingaya mata ne hankalinta ya tashi banaso ta karaya akan bazan iya cika mata burinta ba, gani nake bazam gayamata ba, gara mubari ranar Sunday muje gurin malam" "to shikenan yadda kika gani, amma abun da damuwa wallahi, ace duk wani kissa taki tasiri akansa sekace ba namiji ba, anya ba mata maza bane ba Ace mutum zuciya kaman karfe" "Hmm kema dai kyafada yaseera, bari ranar ki shirya da wuri muje" "to shikenan Allah ya kaimu" "Ameen yaseera nagode sosai". Y'an kwanakin nan, Jalila ta dan sakewa Sulaiman suna gaisawa saboda tasamu damar daze temakamata, amma sam taki yadda yazo gidansu ko susake haduwa, dama ba koyaushe yake zama a kano ba se lokaci2 yake zuwa, aikinsa yafi a Lagos, anan yake gayamata shi kakakin rundanar yansanda ne na jihar Lagos, amma iyalalinsa suna kano, suna hira sosai da Jalila yana bata labarin nasarori da hatsarin ayyukansu, amma daya dakko batun daya shafi soyayya seta kashe wayarta, hakama Alhaji Kabiru Jalila ta sakar masa sosai gani yake kaman sonshi takeyi, a nan takara tabattar da Saleema yarsace ta cikinsa itada faruk. Yanzuma waya suke da Alhaji Kabiru "sweet heart wai yaushe zaki farantawa masoyin kine, kinki yadda mu hadu" "tab waikai bakajin kunyane yarka fa daka nunamin hotonta zata girmeni kawai sesuga ka auri yar yarinya?" "to meye a ciki gidanki daban zan ware miki, ita Saleema tanacan karatunta tanagama karatu zan aurar da ita, Faruk yana ABU, sukenan yarannawa fa, kuma basuda damuwa da aurena, please my sweet kibari mu hadu mana, yakamata kinunamin soyayya ina Sonki fa" shi sam besan Jalila tasan Saleema department dinsu dayaba, Jalila aranta tace me mutumin nan yake nufine? Amma ta maze tace "yaushe zakazo ku gaisa da Abba na?" "Ai wannan ba wani abun damuwa bane, kibari mugama fahimtar juna mana kinki bari inzo gidanku balle mudan dinga fita chilling din nan, bakya wani nunamin soyayya" "Banda wannan danake maka wacce kakeso kuma?" "yakamata ace kinkawomin ziyara gidana mu gaisa mana" "haka kurum matarka ta zaneni" "wayace miki nan zakije, gidana danake ganin special guest dina zakizo" murmushi Jalila tayi "hmmm special guest, ashe nima special ce" "sosai makuwa please my sweet yaushe zakizo?" "karka damu kabari in mungama exams zanzo, ba dai zuwa kawai zanyi shize tabattar maka da inasonkaba karka damu" "Kai amma naji dadi sweet, Allah ya kaimu kugama" "Ameen se anjima" koda sukayi sallama Jalila ta kalli wayar ta takunna recording gaba daya wayar datakeyi tana recording dinta, tana saving a Gmail dinta "Azzalumi kawai, shiyasa abunda kakeyine yasa yarka take can take watsewa a makaranta bakasaniba Jaki kawai, zakuga abunda zan muku kaida yartaka sena kunyataka agabanta in nuna mata nafita iya rashin mutunci". Sosai Zahra ke gudun cigaba da mu'amala da Jalila sedai ta waya saboda kashedin dasu sameera sukayimata, gashi suncigaba da uzzuramata akan lallai ta amince da bukatar sameera, tarasa inda zatasa kanta abun ya isheta, dan haka ta samu Jalila tagayamata halin da take ciki, "Zahra yazama dole ki amince da batun su Sameera" "haba Jalila so kike rayuwata ta tarwatse ne yazakice haka?" "basonake rayuwarki ta tarwatse bane, taimakonki zanyi" "to tayaya Jalila, kinsani nasani dukkansu ba mutanen arziki bane da sharri suke nufina" "Nasani ai tarko zamuyi musu nasan yadda zanyi dasu" Saleema ce tazo har inda su Jalila ke zaune ta kalli zahra "wato zahra bakiji kashedin da Sameera ta miki bako? Har yanzu kina biyewa wannan yarinyar ko" "Ke wai dakata, suwaye dinta ku, ana dolene ko angaya muku kowa sakaraine dabba irinku" "Ke shiga hankalinki, bana son shishshigi muna daf dasawa amana maganinki yadda ko hanya muka hada sekin kauce" "Allah ko? Dama waze hada hanya da kazamai jakuna marasa tsoron Allah, aini base kunsa anyi maganina ba, nizanyi maganinku daga ke har kawartaki ba sameera ba ko langa ce kukiyayeni musamman ke" ta nuna Saleema, "Asararu ko kunya bakwaji kaf school din nan kowa yasan mekukeyi" kafin Saleema tayi magana Jalila ta dau jakarta tayi gaba tabarsu Zahra a gurin. Kwanci tashi ba wuya a gurin Allah su Jalila suka fara exams din first semester, kowa yana abunda yaga ze fisheshi, wasu sun dukufa karatu, wasu ko sharholiyarsu kawai sukeyi, itakam Jalila ta maida kaine akan lissafin yadda zata bullowa al'amuran ta dasuka dameta, Yau karfe tara zasu shiga exams, ita Nana sun gama tasu Jarrabawar dan hutu ma sukeyi, gashi Manu direba baya nan Maama ta aikeshi, da karambani Jalila tasaka Manu yakoya mata mota, da mukulli na nan da dakanta zata tafi yau, dan haka ta yanke shawarar tafiya ta hau napep, Tana fitowa daga gidataga Daddy da dansa Jalal a jikin motar Jalal, durkusawa Jalila tayi "daddy ina kwana?" "Lafiya kalau Jalila makaranta za'atafi ina direban naku?" "daddy baya nan, napep zanje in hau karfe tara zamu shiga exams" "kai Masha Allah, Allah yabada sa'a, takwarar Jalal, Allah ya temaka" Jalal ya tsani yaji ance takwarar nan tasa, yawani hade rai, "Ameen daddy nagode sosai Allah yasaka da alkhairi bari in tafi kar in makara" "A'a tsaya, dama Jalal fita zeyi, Jalal kuje seka ajiyeta a makarantar tunda duk hanyace" kallon daddy yayi, ya kalli Jalila ya dauke kansa I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣0️⃣/63_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Ita kanta Jalila setaji kaman tace A'a amma taji nauyin yin hakan, daddy yakuma cewa "Jalal maza kunna motar ku tafi karta makara" Jalal kaman yace bazashi ba amma yasan yana fadan hakan tasamu abunyi, bece komai ba ya bude motar ya kunna, Jalila ta tafi ta bude gaba ta shiga, "yawwa Allah yayi muku albarka sekun dawo" Jalila ce kawai tace Ameen, Jalal ya kunna motar yajata da gudun tsiya, yadda yake gudu yasa Jalila ta kalleshi "ni gaskiya in wannan ganganci za'ayi da rayuwata ka saukeni, akanme inkasaba kasada da rayuwarka to badaniba" banza yamata yacigaba da tukinsa, yadda yake ratsa tsakanin manyan motoci yasata runtse ido tana ambaton Allah, kallo daya yayi mata ya dauke kansa, "dan Allah ka tafi a hankali koka tsaya in sauka" jitayi an tsaya hakan yasata bude idonta, gani tayi yayi parking, yasa hannu ya yana dakko taba yana kokarin kunnawa, "kutmelesi meye haka ne?" banza yayi mata ya kunna tabarsa, sakin hayakin yayi fuuu a cikin motar, juyawa tayi zata bude kofar motar amma taji a kulle gam, yasa lock ta kalli agogon hannunta ta makara sosai ana daf da shiga exams, "wai meye haka dan Allah nika budeni in tafi zan makara, ga warin hayaki ya isheni" Shiru yakumayi ya kwanta sosai a jikin kujerar yana busa hayakinsa, ji tayi kaman ta wanka masa mari, yanajinta amma yayi banza da ita kamar wani itace, dafe kanta tayi, wayarsa tafara vibration ya dauka yaduba message din Hanna ne danhaka ya ajiye wayar tareda fadin "wasu matan are just useless" Jalila ta dago ta kalleshi, "ai Useless din ba iya mata bane hada maza, dan gara mata da wasu mazan dabasa jin magana" wani dan guntun murmushi yayi, wanda shikadai yasan yayi shi, gani tayi ya shanye sigari kusan uku yakuma kunna wata, hannu tasa ta fizgeta ta jefa waje "wallahi baka isaba, akanme ina zaune zaka dinga shan taba ka cikani da hayaki salon inje aji a dauka ninasha tabar, ka budeni in tafi in yaso kaima kazama tabar, batareda ya kalleta ba yace " warin taba ai kin dade kinayinsa, ba iya taba ba harda na giyama kinayi, kece baki saniba amma nakusa dake sun san hakan" kallonsa tayi alamar bata fahimta ba "ya za'ayi nida bana shaye2 indinga warin giya, Allah ya kiyaye" "bakiyi addu'ar a inda ya daceba, dan kinriga kin makara, kuma ba lallai sekina sha zakidinga warinsu ba" hannunta ya kamo, ya nunamata "a jininki abun yake, akwai jinin yan giya a jikinki dan haka sekidena cika baki" ita Jalila sam batagane inda maganganunsa suka dosa ba, wayartace taketa ringing tasa hannu ta dakkota Alhaji Kabiru ne akan screen din wayarta, screen din Jalal ya tsurawa ido yai shiru kaman me nazari, ya kalleta ya kalli wayar, kashe wayar tayi ta mayar cikin jakarta, kallon tuhuma yayi mata na wani dan lokaci, sannan ya dauke kansa, "hmm Jawwad za aci amana, hakan yafi ai, dan baki dace dashiba gara ya auri mutuniyar kirki, dan duk jarabarki bazaki auri dan uwana ba, Jawwad da salihar mace ya dace ba irinkiba" kallonsa tayi sannaan tace "nice ma kai, aigarani da kai, kaima kasan hakan kuma duk bakin cikinka sedai kayi, dan nafi karfin ace za'a kyamaceni a matsayin mata, dan nasan nafi wannan doluwar kanwartaka" "Hmmm meye kuma nasakota a wannaan zancen? " "kaika sani, nikawai ka budemin in fita" banza yayi mata yacigaba abunda yake, wasa2 kusan mintunansu talatin a tsaye Jalal yaki tafiya, hannu takuma sawa zata fizge tabar bakinsa cikin zafin nama ya hada da hannunta ya rike, ya juyo yana kallonta, wani mugun kwarjini yayi mata ta kasa magana ta sunkuyar da kanta kasa, "karki kuskura, bar ganin na kyaleki dazu" sakar mata hannu yayi, yacigaba da abunda yake, karfe tara hada rabi, amma Jalal yaki kaita makaranta, tarasa mezatayi kawai tafara kuka, seda Jalal yaga dama sannan yaja motar yacigaba da tafiya, wannan karon kuma a hankali yake tafiya kaman bayaso, hannu yasa ya kunna radio motar inda karatun Al qur'ani yake tashi, Jalila aranta tace "Tab dama yanajin karatun qur'ani" bata gama tunanin ba taji Jalal yanabin karatun a hankali, juyowa tayi tana kallonsa, danta tabattar anya kuwa shine yakeyi, sosai yakebin karatun cikin suratul Ibrahim, dan tabe baki tayi tana jinjina lamarin dama Jalal ya iya karatu haka, amma koda wasa bata tunanin ko bismillah ta tabajin yayi, se masifa da wake2, tana cikin tunanin taji yayi parking, "inkin gama kallon nawa seki fita" " Baka da abunda zan tsaya ina kallo, ko Meye amfanin zuwanama, tunda dai na makara nasan ba lallai inyi jarrabawar ba, kaida Allah in abunda kayimin dai2 ne, kodayake baka san darajar jarabbawa ba shiyasa kamin haka kuma Insha Allah se" "Ke!!!!" ya dakamata tsawar data tilasta mata yin shiru "wallahi duk randa bakinki yai kuskuren yimin muguwar Addu'a akanki zata kare, gobe in ankuma cewa kibi namiji mara daraja irina sekikuma biyoni, fitarmin daga mota, inbahakaba na kunna motar nan senaje gida zan tsaya, kyasan yadda zakiyi" bude motar tayi tanata kunkuni gashi ta hade rai sosai, ta fice tabar motar a bude tai tafiyarta, ankai ruwa rana sosai kafin abar Jalila tashiga hall din exams saboda ta makara, Jalila ji take kaman tana komawa gida takama Jalal ta shakeshi seya suma, haka tai exams din ta fito cike da takaici, Tasamu guri ta zauna a karkashin wata bishiya, ta zauna babu dadewa Zahra ma tazo gurin "Jalila ya akayi kika makara haka yau?" dan tsaki Jalila tayi "kedai bari, wani ne yajamin wallahi, kuma ze gauraya dani" "hmm Jalila kenan me jama'a, Amma ke sir Hafiz fa yace ince miki kije, nifa nakasa gane meke shirin faruwa tsakanin ku" Jalila ta kalleta ta dauke "ki goge zuciyarki tsaf kidena bari tana kawomiki wani tunani" zahrah ta jinjina kai "ke ba wannan ba Jalila, ina mafita anawa lamarin? Ina cikin damuwa wallahi" "Nasani Zahrah, amma abubuwan dasuke kaina dayawa ga wannan jarrabawar ga sauran abubuwa" "to nidai kitemaka Jalila, karsuyi nasara akaina" "Ai yazama dole in temaka miki, sabida indai nayi nasara kikayi yadda nace to nikeda riba, zangaya miki yadda zamuyi, amma banason gaddama da taurin kai, duk abunda nace kiyi, bazan bari kiyi abunda zaki cutu ba" "to shikenan inajinki" Jalila ta gyara zama "zaki Amince da bukatar su Sameera" zaro ido Zahra tayi "Amma meyasa?" Nan Jalila ta tsarawa zahra yadda abun ze kasance, zahra ta yadda da abunda Jalila tagaya mata. Zahra ta tashi ta dau wayarta zata tafi, Jalila ta dakatar da ita, ta dakko wayarta tasaka ta a tsakanin litattafan Zahrah daga sama, sannan ta kalli zahra" harkije ki dawo karki sake ki tabamin waya, jeki dawo ina nan ina jiranki"zahrah ta gyada  kai ta tafi, inda tasan zata samu su Sameera, tai sa'a kuwa suna gurin, tana zuwa tasamu guri ta zauna a kujerar opposite din su Sameera ta kalli Sameera tace "Sameera gurinki nazo" Sameera tamata wani mugun kallo sannan tace "fatan kinzo ki sanar dani kin Amince da bukata tane?" "A'a zuwa nayi in rokeki alfarma dan Allah dan annabi kirabu dani kiyi hakuri wallahi iyayena zasu shiga damuwa insuka gane gurbatacciyar hanyar dana fada" Saleema ce ta katseta "Ke saurar bama son shirme , kekinfiso aita nanata magana ko? To bari kiji bata sauya zaniba, koki yadda kokarki yadda bazaki kubucemana ba sannan sekinso iyayenki zasu san abunda kikeyi, abunda kezaki amfana kudi fa zaki dinga samu" Sameera ta dagawa Saleema hannu alamar tayi shiru, ta kalli Zahra "idan baki amince da bukata ta ba, wallahi kartin yan daba zansaka suyi miki fyade" A razane Zahra ta kalli Sameera "yes and i mean it, fyade na wulakanci na tozartawa kuma duk garin nan babu wanda ya isa yayi wani abu, inada yan daban dabakowa ke iya hayarsu ba, sannan inada manyan dasuka tsaya min, babu wanda ze gane ninasaka akayi miki haka balle adau mataki, bakida gatan da za'a iya kwato miki hakkin ki, kinga tarwatsewar rayuwa tagama, karatu ya kare se zaman gida jiran ajali danko waje baki isa ki fitoba saboda gudun kyamar da mutane zasuyi miki" da kyar zahra ta hadiye mugun yawu "shikenan dan Allah kar abun ya kai haka na yadda, na amince amma bana son mutane su gane" Saleema ta kyalkyale da dariya, "ashe bari ba shegiya bace yarinya da wata garan gara wata" Murmushi Sameera tayi, "kin temaki kanki" zahra ta share hawayenta "A ina zamu hadu?" nan Sameera taimata kwatancen wani gida, zahra tace "zanzo Insha Allah, sannan kibani lambarki incase ko zan bata" ba tunanin komai Sameera tabawa Zahrah lambarta, sannan ta karbi ta Saleema ma" har zahra ta mike zata tafi ta dawo ta zauna tace  "Amma dan Allah kujawa yar seat dina kunne, nayi2 tadena shiga harkata taki" Saleema tace "banni da ita zanyi maganinta" zahra ta jinjina kai ta wuce yayinda sukuma suka kyalkyale da dariya, zahra takoma inda tabar Jalila, tana zuwa tana niyyar labartawa Jalila abunda yafaru, Jalila tasa hannu ta zare wayarta, sannan ta kalli zahra "shikenan semunyi waya ina sauri zan koma gida" "Amma baki tsaya nagaya miki yadda mukayi dasu ba" "karki damu mu hade ta what's app" cikin mamaki Zahrah ta kalli Jalila "to amma meye amfanin..... " Shhhhh semun hade "Jalila tayi gaba abunta. Tana zuwa gida yaya Jawwad yana tsaye shida Abba, karasawa gurinsu tayi" Abba yana ganka a gida iyanzu? "yan makaranta ya jarrabwa" "Alhamdilillah Abba harka dawone?" "A'a tafiya ce takamani, zanje Lagos" dan hade rai Jalila tayi "Abba da tafiya zakayi ba sallama" "to ai gashi munyi sallamar" Jawwad yace "Abba muje karka makara, wannan babyn taka bazata bari ka tafi ba" "Nima zan biku Abba" Jawwad yace karatun fa? Naga kuna exams " " Eh ai bakomai dan Allah ni zan biku" Jawwad yace "rigimammiya yanzufa kika dawo baki gajiba" "bangajiba Allah" Abba yai murmushi "taho mutafi shalelena, ai rakiya zakiyi min" da murnarta ta hau motar suka tafi raka Abba airport, suna tafe suna hira itakuma ta dakko wayarta tasaka earpiece tana kallon video, dazu wayarta data saka a agaban jakar zahra video ta saita ta kashe flash din wayar, duk wani magana dasukayi yayi recording, wanda ita kanta zahra bata Sani ba, aciki Jalila taji kwatancen gidan da akayiwa zahrah a dan bare, ita Jalila bata san ma inane dan bare a kanoba, hiding video din tayi a wani app ta ajiye wayar, suka raka Abba airport, seda Jawwad yabiya ya saimata ice-cream da tarkacen chocolate suna tafe suna hira har sukazo gida. Suna zuwa suka tarar da Maama a harabar gidan, kallon tuhuma takeyiwa Jalila da Jawwad "daga ina kuke?" Jawwad yace "dama Tafiyace takama Abba zeje Lagos kuma bakyanan shine muka rakashi airport" "in kayi salla kazo ina son ganinka" "to Maama insha Allah zanzo" Maama ta juya takoma cikin gida, Jawwad yajuya ya kulle mota, yaga Jalila a tsaye abayansa bata tafiba "ya dai?" "bangaji da ganinka bane" murmushi yayi mata "Babyna kenan, aini nakine zakita kallona sekin gaji" "bazan taba gajiya da kallonka ba, jekayi salla kazo kiran Maama" "to shikenan see u later" daga nan yafita ita kuma ta shige gida, a cikin gida bataga Nana a dakinsu ba, san haka tashiga tayi wanka tai salla. Tana ninke sallayar taji wayarta na ringing Alhaji Kabiru ne wani uban tsaki taja Ta daga wayar suka gaisa, haka ta dake ta boye damuwarta suka sha hira kamar gaske, Alhaji Kabiru ya matsa matuka akan se Jalila taje gidansa, taita lallabashi tana bashi hakuri daga baya ta kashe wayarta, fiowa tayi palour domin taje kitchen tasamu Abinda zataci, gani tayi anyi bakuwa a palour da alama gurin Maama tazo, suka gaisa da Jalila tace "bari inje in kira miki ita inaga tana daki" Jalila ta tafi dakin Maama danyimata magana Jalila ta jiyo kukan Nana tana cewa "Wallahi Maama gara in mutu da in auri Nura, wallahi yaya mairo kozata kasheni bazan aureshi ba" "nima ban goyi bayan hakanba, bazaki Auri Nura ba, amma yazama dole Jawwad ya auri Naja, intaga Jawwad ya auri Naja zata hakura inyaso kesekice ba kya sonsa" "Maama saboda me shima yayan ze auri Naja yakamata ayi masa adalci abarshi ya zabi wadda yakeso" "ke rufamin baki, dole ya auri Naja saboda bazan bari ya auri wannan yarinyar ba, indai ina raye baze auri Jalila ba saboda bana kaunar uwatta itama bana sonta dana baze auri yar Arniyaba karuwa" Jalila ji tayi kaman ansoka mata mashi a zuciyarta, tura kofar dakin tayi kaman bataji komaiba tace "Maama kinada bakuwa" hade rai Maama tayi "to naji jeki ina magana da yata" juyawa Jalila tayi ta fice tafasa cin Abincin, tafasar da zuciyarta take tasa takasa komai, ga hawayen yaki zubowa balle taji sanyi aranta, a hankali taketa karanto addu'oi domin zuciyarta tayi sanyi, gani tayi inta cigaba da zama bacin raine ze dameta gara ta fita ta rage wasu abubuwan dan haka ta dau hijabinta tasaka ta dau nikab da Jakarta ta fito palour, Maama tana gaisawa da bakuwarta "Maama dan Allah zan dan fita bazan dade ba zanje siyo kayan cake" "sekin dawo" shine kawai abunda Maama tace mata, tana fitowa harabar gidan Manu ya taso "A'a uwadakina ina zuwa haka daga dawowarki yamma tayi sosai" "Manu key zakabani na mota zanfita" "Ahh ai yayi wuri kifara tuki da kanki bakigama kwarewa ba kinsan tuki a kano se kwararren direba" "karka damu ba nisa zanyiba" Manu direba yabata key din mota, ta fita sannu a hankali take tukin da tambaya hartaje unguwar danbare inda su Saleema suka kwatantawa zahra sukace acan zasu hadu, abakin layin tayi parking ta fito sanye da nikab ta shiga layin, layin shiru ba mutane sosai, har kofar gidan taje ta tsaya daga baya, tana nan tsaye sega wata mata tazo wucewa, Jalila ta tare matar suka gaisa sannan Jalila tace "baiwar Allah dan Allah tambaya nake?" "ina jinki Allah yasa nasani" "Dan Allah ke yar anguwar nance" "meyasa kika tambayeni?" Jalila tace "kinga ba cutar dake zanba wasu yan tambayoyi kawai zanyi miki" matar tace "ina jinki" "dan Allah waye me wancan gidan" Jalila ta nuno mata gidan "hmm wanna gidan da kike gani wai yan makaranta ne a ciki, kuma bawani yan makaranta taron yan iskane maza da mata bawanda basa zuwa gidan, ke kawaima gidan karuwai ne da yan shaye2 " "Amma kuke zaune dasu a anguwar ina hukuma" "wace hukuma aiko ankamasu se an sakosu saboda ita ainihin me gidan wata yarinya ce, tanada manya a sama ba wanda ya isa yayi mata komai samfirin yan mata samari da yan daba babu wanda babu, har wasu manyan mutanen ma suna zuwa nan" "Nagode sosai yar uwa, da amsamin tambayoyina" matar tace "bakomai amma fa koda wasa karki sake kice nina gayamiki danba ruwana" "karki damu babu mejin wannan zancen". Daga nan Jalila tayi godiya ta nufo gida, anata kiraye kirayen sallar magariba, tana komawa gida ta nufi cikin gida "wallahi Jawwad da raina bazaka auri yar arna ba, ko ka auri Naja kokasamu wata ka aura amma ba wannan yarinyar ba, Naana dai zanyi yadda zanyi bazata auri nuraba amma kai kam sedai kayi hakuri bazaka aureta ba wallahi" "Maama dan girman Allah kiyi hakuri Jalila batayi miki laifin komai ba, wallahi Maama ina sonta dan Allah karki rabani da ita, ina sonta dan Allah wallahi bazan iya auren Naja ba" "Au har ina fada kana fada Jawwad, nagama yanke hukunci, sedai ka mutu dan bana kaunarka da yarinyar nan baze yuwu jikokina su fito daga tsatson arna ba, wannan fitsararriyar yarinya mara tarbiyya to baka isaba ni na haifeka dan haka na isa da kai, bazaka aureta ba, tun kuna kanan akan uwatta ba irin wulakancin da ban fuskanta ba, ubanku yayi min shi Aliyun yayi min rashin mutunci akan uwatta dama shiba mutunci yacika ba, dan halinsa ta dakko, ga kakarku kowa ya hademin kai Allah ka dai yasan me tayi ta shiga ta fita ta rabani da dangin mahaifinku, suka tsaneni se yanzu kakuma jawomin jaraba baze yuwuba, zamanta a gidan nan ma ba yadda zanyi ne, amma bana kaunar ganinta kusada ku" sunkuyar da kai Jawwad yayi ya dafe kansa da karfi Jalila ta bude kofar palourn gaba daya suka juyo suna kallonta Daga Alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ I don't want stickers or just thanks, comments nakeso, dan shike bani karfin gwiwa, ina Alfahari daku ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣1️⃣64_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Kallo daya tayi musu ta dauke kanta ta wuce cikin dakinsu, itakanta Maama seda tasha jinin jikinta dan gani take kaman Jalila taji abunda tace, tashi Jawwad yayi ya fice, yayinda Nana da sauri itama ta mike da nufin bin bayan Jalila amma Maama ta hanata, "Ina zaki? Karki sake Kibi ta mayya" haka Nana ta hakura tafasa bin Jalila, Jalila tana shiga dakin tai jifa da jakarta da hijabinta akan gado ta zauna ta fashe da kuka me tsuma zuciya, dama tsanar da Maama take mata harta kai taci mutuncin mahaifinta haka shida baya doron kasar tsawon shekaru, ga kazafi datakeyi wa uwata, menayiwa wannan matar hakane meyasa ta tsaneni, banda albarkacin Abba dasu Nana da matar nan itada zuri'arta suka ganni se sun canza hanya, "zamana a gidan nan baze yuwu ba, bazan cigaba da jure cin zarafin iyayena ba musamman uwata ba dan kawai tubabbiya ce gara inshiga duniya, to amma inna tafi Jalal fa? Tabdijan wallahi matar nan tahana Jawwad aurena bata isa ya auri wata Naja ba, in ita Maaman bata san wacece Najaba to nina sani, Jawwad kuma dan uwana ne, intace baze aureniba baze auri Naja ba wallahi, bazan zauna a kasheni da bakin ciki a biyeba, ta karkashin kasa zan fara ramawa nagaji" "Enough!!!!" Jalila tafada da karfi idonta duk hawaye, guri ta nema ta kwanta hawaye na cigaba da bin gefen idonta to Jalal dinme ma? Nagaji tafiya zanyi sena bar gidan nan wallahi nagaji da wannan abun da akemin, hijab dinta tasaka ta mike. Nasihar ummi ta dinga tunowa wanda take yawan yi mata akan hakuri da rayuwa dakuma karbar kaddara, komawa tayi ta zauna ta fashe da kuka me ban tausayi. Jiki a sanyaye Jawwad yayi sallar magariba, gaba daya yarasa abunda yake masa dadi, Jalal ne ya shigo dakin da sallama, amma sam Jawwad bejiba hankalinsa baya jikinsa, dafa shi Jalal yayi cikin damuwa yace "Jawwad lafiya kuwa? Meyake damunka kake tunani haka?" Ajiyar zuciya Jawwad yayi, ya danyi shiru na wani lokaci sannan yace "Jalal ina cikin damuwa, narasa meyakamata inyi" "gayamin meya farune?" Nan Jawwad yagaya masa komai sanna ya dora da cewa "Jalal babban damuwana shine cin zarafin da Maama tayiwa iyayen Jalila ina kyautata zaton Jalila taji abunda Maama tace, amma ban tabbatar ba, data shigo ba wanda ta kula a cikinmu, wallahi bana zaton zan iya auren Naja bazan iyaba wallahi" Shiruu Jalal yayi, "Jawwad a duk lokacin da aka ci zarafin Ummi, har cikin zuciyata nakeji, raina yana baci, bana manta Alkhairi Jawwad, idan har a matsayinmu na hausawa zamu cugaba da aibata wanda suka karbi Addinin musulinci daga baya to tabbas wanda ba musulmi ba zasu dinga kyamatarmu da addininmu, Jawwad kayi hakuri, amma mahaifiyarka da yan uwanta basa kyautatawa, dukda ina gefe ina fadar rashin kunyar yarinyar nan bazan mata sharri ba tanada matukar biyayya wadda wanda dayawa aka haifa a musulincin basuda ita, kuma itama ai a musulinci aka haifeta, Ummi mace ce me karamci da ilimi riko da Addininta yasa ta baro iyayenta gidan jin dadi dau shekaru ba tareda ta waiwayesu ba, soyayyar datakewa mijinta da yan uwansa ce tasa nima naci Albarkacinku, Jawwad mahaifiyarka bata kyauta ba, kuma zigata akeyi amma kasani gara wanda ya tuba daga baya akan abunda yar mahaifiyarka take aikatawa"da sauri Jawwad ya kalleshi yana kokarin yayi magana, Jalal yace "karka tsananta tambaya dan bazan gayamaka komai ba amma lokaci zenuna komai, mahaifiyarka zatayi nadamar abunda tayi, kayi kokarin ganar da ita, tun kafin tasamu kanta a halin datawa mahaifiyar take ciki, nima da datawa damuwar nazo maka amma bari in kyaleka ka huta, kacigaba dayaimana addu'a kaji dan uwana, banason damuwar ka ina kaunarka dan uwana kadena damuwa" Jalal ya dan daddaki bayan Jalal alamun rarrashi, daga nan ya tashi ya fice. Jalila yadda taga rana haka taga dare, se tufka da warwara kawai takeyi, gashi tunda ta dawo Nana ko dakin bata shigaba, Maama ta hanata Nana bata kwana a dakin ba a can gurin Maama ta kwanta. Bangaren Jawwad ma hakane, juyi kawai yakeyi, ya daga waya zs kira Jalika yaga inya kirata ma mezece mata, tunda be tabbatar Jalila taji abunda Maama taceba. Washegari Sam Jalila bata nuna da wani abu a ranta ba, sedai ko karyawa batayiba ta fita domin tafiya makaranta, a kofar gida tasamu Manu yanata goggoge mota, suka gaisa takoma gefe tana jiransa yagama su tafi, Jalal yana cikin motarsa a kofar gida, zeje wani guri, daga cikin motarsa yana ganin yadda ta rame, da ganin idonta kaman bata samu bacciba ta kwana cikin damuwa, lokaci2 tana goge idonta da handkerchief, Jalila tanada yawan fara'a bata fiye hade raiba, musamman in ta samu abun tsokana, amma yau fuskarta sam babu annuri, setayi kaman wadda ta dade tana jinya, har cikin ranaa seyaji babu dadi ganinta a haka, haka manu ya dauketa ya kaita makaranta. Hannah abun duniya ya dameta tarasa ta ina zata bullowa lamarin Jalal, amma tanason sanin matsayin Jalila a gurinsa, yazama dole taga Jalila, amma kafin taga Jalila kokuma bari in bari tukuna, amma bari inje gurin wannan garan sena hadu da Jeje, Hannah ta shirya tsaf ta dau mota, ta tafi inda tasan Zata hadu da Jeje, Jeje na ganin Hannah yafara murmushi yana tafa hannun sa "barka da dawowa Gimbiya Hannah" daga masa hannu tayi alamar bata son surutu, guri ta nema ta zauna tana facing din Jeje, Jeje ya rigata magana ta hanyar cewa "dama nasani Hannah zaki dawo, zaki cigaba da aiki damu kin temaki kanki da kika gane hakan, don Jalal baze taba aurenki ba, ni kaina yau rabon da Jalal yazo mashaya ya dade, shiyasa wani shirin muke sakeyi akansa zuwanki a yanzu kinzo akan gaba" "kaga dan Allah kayi shiru kaji meyake tafe dani se surutu kake, kai ka isa inyi magana in janye saboda wani banzan me gidanka baku isaba wallahi ka tsaya ka saurareni, nazone in gaya maka wanda yasa aka dauke Jalal ranar birthday dinsa ba kowa bane face wannan yarinyar data  kawo cake" a razane ya kalleta "are you serious?" "sekaje kayi bincike, da bakinta tagayamin haka, sannan kasani in har tana raye to baka isa kuyi nasara akansa ba, seku sake shiri sannan nima bazan bari kuyi nasara akansa ba saboda aurensa zanyi, mataki ya rage ku dauka akan wannan yarinyar, danni nafi karfinku kasani" "Amma hannah........" kaga ni na riga nagama magana" ta mike ta bar gurin, jinjina kai Jeje ya dingayi yana tuna abunda Jalila tagaya masa daren da yafara ganinta akan Jalal, tabdijan yazama dole ya dau mataki akan yarinyar nan. Yazama dole anjima inje gidansu Jalal da kaina, inbahakaba akwai yuwar wannan yarinyar tamayar mana da aiki baya, bazan bari oga KB yaji wannna zancen ba mara dadi" Anfito daga exams Jalila tana tafiya kaman wadda kwai ya fashewa a ciki, daka ganta kasan bata cikin walwala, gani tayi an sha gabanta tana daga ido taga saleema, matsawa tayi da niyyar wucewa, takuma shan gabanta "Ke magana zanyi dake" Jalila ta kalleta "ina jinki" "Kashedi na karshe zanmiki akan Zahrah, ta kawo mana kararki dan haka ba ruwanki da rayuwar da takeso tayi, dan haka kidena mana shishshigi, bake ba zahra" Jalila ta dakko wayarta tana dannawa sannan tacewa Saleema "tsakanin nida zahra wakika haifa da kikemin wannan kashedin?" "haka kikace to kicigaba karki fasa zakiga abunda ze biyo baya" "bazan dena ba, mekika isa kiyumin meze biyo bayan?" cikeda da gadara saleema tace "Abunda ze biyo bayan abune mafi muni da bakinciki a rayuwarki abu mafi kunya da asara" murmushi Jalila tayi "shikenan ina jira, nabaki nan da yan kwanaki in har abun da kika fada be faru daniba to ke ze faru akanki, sha3 kawai" binta da kallo Saleema tayi, yayinda itakuma ta wuce, office din sir Hafiz taje, yanata marking, ya kalleta "hmm Gimbiya yar senaga dama se yau kikazo kiran danayi miki" shiru tayi batace komai ba "well ya exams din" "lafiya kalau Alhamdilillah" "meyake damunkine? Naganki kaman bakida lafiya" "lafiya ta kalau" ta bashi amsa a takaice Mikewa yayi ya tattare takardun gabansa yasaka a drower yace mata "biyoni" ba musu tabi bayansa, sun danyi tafiya me nisa sannan sukazo bakin wani office, Sir hafiz ya bude kofar yamata alama yace "bisimillah" Jalila ta kalleshi "fara shiga zanbiyoka abaya" murmushi yayi "kina zaton zan cutar dakene anyway biyoni a baya" suka shiga office din, office din babbane sosai ya hadu matuka, se kamshi da sanyin Ac ne ke ratsa ko'ina a cikin office din, kallo daya tayiwa mamallakin office din yana kashingide yana dannan laptop dinsa, sallama sir hafiz yayi, da fara'a wanda ke danna laptop ya dago tareda amsa sallamar, musabiha sukayi da sir hafiz suka gaisa, ita dai Jalila kallonsu kawai takeyi Sir hafiz yace "kalleta ina fatan ita kake nufi" mutumin ya kalleta "eh itace Hafiz nagode sosai Allah yasaka da alkhairi" suka kuma gaisawa sir hafiz ya kalli Jalila yace "to game son ganin naki nan" batace komai ba sir hafiz ya juya ya fice, mutumin ya kalleta "bisimillah ga kujera nan kizauna mana" ya mike ya yaje fridge ya dakko mata ruwa da lemo ya ajiye a gabanta, "wai meyasa kake nemana, ni dai ban sankaba menayi maka" murmushi yayi ki kwantar da hankalinki dolece tasa na nemeki saboda naganki da abunda na dade ina nema " kallonsa tayi irin ban fahimta ba "dan Allah a ina kikasan ABDUL JALAL, meye alakarki dashi?" kallonsa tayi cikeda mamaki sannan tace "waye kuma hakan?" "Naganki a motarsa jiya yakawoki school shiyasa na tambayeki" "kai mene alakarka dashi?" "Abokina ne, mun dade bamu hadu ba sena ganku tare, shiyasa na tambayeki saboda akwai wani muhimmin abuna a tare da shi?" "shiya kamata ka tambaya alakar dake tsakanina dashi tunda abokinka ne, kokuma inbaka lambarsa seka tambayeshi" "to shikenan bani lambar tasa" mikewa tsaye Jalila tayi sannan tace "Sena tambayi izininsa tukuna" ta juya tai ficewarta daga office din tana zancen zuci "wannan wane irin abune kawai kawani fara tambayata waimeye alakata dashi mtseww" wata Jalila ta tsayar ta tambayeta sunan me office din, tagaya mata sunanshi malam Sagir Ahmad, Jalila taimata godiya ta tafi, Koda ta fita tsaki yayi, ya dauki wayarsa, ya dan daddana sannan yasa a kunnensa "hello, ke gaskiya yarinyar nan tanada matukar wayo, taki yadda tacemin komai a game da alakarta Da yayanki" Ajiyar zuciya Ilham tayi "kai duk dabarar naka da iya maganar amma ka kasa" "lallai Ilham, yarinyar tana da lissafi batacemin komai ba akan alakarsu" "shikenan nagode sosai" "yawwa to se anjima" Ilham ta aje wayar ta jinjina kai "shikenan tunda kinki fada, bari in je gurin malam inji meze cemana, Allah ya kaimu goben" yauma seda Jalila tasa nikab taje dan bare gidan dasu Saleema suke sheke ayarsu, ta tsaya daga waje, maza da mata ba wanda baya zuwa gidan nan, seda ta tabbatar su Saleema suna zuwa gidan nan kuma babu kalar yan iskan da babu. Ta dau lokaci a labe tana kallon masu shiga da fitaa a gidan sannan ta tari abun hawa takoma gida. Ko a gida ma tunani taitayi, ko Jalal zatayiwa zancen wannan Sageer din cab toma tayaya zan tari wannan jarabbabben da wannan maganar ko ina, tana cikin tunanin ne Nana ta shigo dakin da fara'arta tace "kindawo ashe?" "Eh na dawo Nana" "yaya Jarrabawar" "Alhamdilillah" "Jalila taso zomuje ankawo sabon order na laces da turaruka, zomuje mu zaba" "kai Nana wane irin lace kuma? Duk kayan damuke dashi" "to Ai Abba ne yayo waya yace muje" "to bari indakko hijjabina" "kai Jalila ingo mayafin nan dora, banaso wasu su rigamu zuwane a zabe abarmu" Jalila ta karbi mayafin hannun Nana ta yafa, ta kalli Nana "Nana gaskiya mayafin nan yai kadan dubi kayan jikina fa?" "wallahi watakila har muje mu dawo bazamu hadu da kowaba taho kawai" Nana taja hannunta suka tafi gidansu Jalal, Mummy bata babban palour dan haka sukaje part dinta, tana palourn ta tana kallo, Ilham tana kwance tana gyara dogayem faratan ta cikin girmamawa suka gaisheta ta amsa, Ilham bata kulasu ba, Nanace taitayiwa Ilham korafin ta dena nemanta yanzu zumuncinsu ba kamar da ba, nanma Ilham batayi wani responding ba a zuciyarta tace "kina tareda babba makiyata zan dinga sauraranki, taanar danake mata yanzu ai harda ke" Nana tace "Mummy anuna mana kayan mu zaba tun kafin azo a kwashesu" murmushi tayi tace "to hajiya Nana, dankuwa kinsan akwai costumer da Jalila ta hadani dasu sunce zasuzo da sun rigaku zuwa da sun kwashe" Jalila tai murmushi "Mummy ashe har yanzu suna zuwa" "muna hulda sosai suna siyayya a gurina, Jalila maza shiga bedroom dina ki dakkomin mukullaye acikin wardrobe dina, se muje a bude store ku gani" Jalila tana mamakin yadda Mummy batajin komai take turata kan kayanta, Ilham seda ta dago ta kalli Mummy, Mummy ta dauke kai, meyasa Mummy bata yadda da ita akan irin wannan lamuran nata, tsabar haushi Ilham ta tashi takoma baban palour, Jalila taje ta dakko keys, sukaje store suka gama ruwan idonsu suka dauki kaya" Mummy tabiyosu sun fito babban palour sega Daddy ya shigo shima suka gaisa daddy yace "Jalila na kuwa tura Jalal nace masa yace inason ganinki sega faduwa tazo dai2 da zama" murmushi tayi "ai bansaniba Daddy dana zo" yace hakane ya kalli Mummy yace "yan borno zasuzo next weekend Insha Allah" A razane Mummy ta kalleshi, Ilham ma seda ta tashi zaune, Mummy tace "yan barno kuma? Meza suzo suyi?" "Zumunci mana, dan haka Jalila naga kin iya wannan kayan dadin Abincin naku na yan zamani da irin namu na yan da, dan Allah inban takuramiki ba inaso za'ayimin zamuyi baki ne nasan Madam bazata iya ba ita kadai" Jalila ta dan rusuna "bakomai Daddy Insha Allah ba damuwa za'ayi" Nana tace "daddy dama Abincin hada wani na kwadayi" murmushi yayi "Eh mana Nana irin naku na zamani ba" Jalila tace "amma wani irin Abincin kakeso ayi musu sannan su nawane"? "Yawwa takwarar son, nagode sosai, yanzu kije gida kiyomin list din Abunda za'a bukata, kiyi musu kawai Abinci me dadi, nasan zasuzo da dan yawa ina jiranki kiyo list din, wanda muke dashi shikenan in babu se a siyo, inkin tashi kizo kiyi anan karki bata muku gida " "to Daddy bari inje yanzu zan kawo maka Insha Allah" Su Jalila suna futa Mummy tace "dan Allah dagaske kakeyi koda wasa!" "daga snake shiyasa ban takuraki nace kiyi musu girkin dazaki karbesu ba gara nasa na waje suyimin tunda ke ba lallai kiyi ba, bayan shekaru yan uwana zasuzo sukawomin ziyara" daga haka ya wuce part dinsa, dafe kai Mummy tayi tanemi guri ta zauna ita kanta Ilham kanta ya kulle, Jalila tana zuwa gida, ta zauna tayi list din abunda take bukata ta fito domin kaiwa Daddy, amma tundaga kofar gida taci karo da motar Jeje, "Wannan annamimin mayen yazo kenan" tana shiga taga Jalal da Jeje a harabar gidan, suna zaune akan fararen kujeru suna hira, suna shan wata irin taba me girma sosai dan tafi wadda Jalal yake sha girma, zuwa tayi ta wucesu cikin gida, Jeje da kyar ya iya dauke idonsa akan Jalila, saboda karamin mayafine ajikinta gashi doguwar rigarta cif jikinta Share please Daga Alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ I want Comments not stickers or just thanks what's app only 👇👇👇 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣2️⃣65_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ "Waime kake kallo hakane?" Jalal yaima Jeje tsawa cikin inda2 Jeje yace "ohhh am sorry J, nothing, dan samomana kayan washi mana, tunda kwana biyu bamu hadu ba" Jalal yace "to jirani ina zuwa" Jalal ya mike yaje part dinsa ya kawo musu kwalaban giya da wayne cups ya ajiye akan table din"Jeje yace "yauwwa nace meyasa kadena zuwa club, friends nata tambayarka yane? Ga beb dinka Hannah duk tana cikin damuwa irin sosai kagane eh" "kai bari kawai, haka nan bana son zuwa club din nan, a gida nake dura duk abunda nakeso normal ne ai nan da can" "A'a akwai banbanci, nan  ba wasu zafafan mata, bawani sauti me ratsa kunnuwa, kodayake bebs din dake ratsawa a gidan nan naku ma sun isheka kallo, especially wannan zazzafar baby girl din, komai nata me kyaune," hade rai Jalal yayi, a fusace yace"kamanta kashedin danayi maka abaya ko" Jeje ya sauri yace "ohh No am sorry bazan karaba Insha Allah, yanzu kaga dakkomin wani product din wannan ta isheni, kusan kullum ita nake sha, nasan bazaka rasa na manyan kai ba, dan Allah kabani wani product din" "bazanje ba sedai karka sha" "please am sorry nasan kanada masu tsada dan Allah ka dakkomin" banza Jalal yaiwa Jeje, sekuma can jumawa ya tashi ya tafi dakko masa wata giyar Jalila ta shiga palour bakowa, Seta jiyo sautin maganar Mummy a bangaren daddy, kaman sa'insa sukeyi, dan girgiza kai Jalila tayi, be kamata taje musu a yanzuba, tana jiyo muryar daddy yana "yan uwanane gurina zasuzo ba gurinki  ba, insunzo sedai kibar gidan" "Amma kamanta abunda yafaru ne? Har kake wannan tunanin?" "ni ba abunda ya faru tsakanina dasu sedai tsakaninki dasu" Jalila juyawa tayi tafito da sauri dan karma su fito su ganta su gane taji sa'insar da sukeyi. Koda ta fito harzata tafi, ta juyo Jeje cikin wannan muryar tasa mara dadin ji  yana cewa "hi beb i like your confidence, akwaiki da fada da cikawa, " tsayawa tayi cak ba tareda ta juyo ba, yacigaba da cewa "kin fada kuma kincika, kinyi nasarar batamin aikina na wannan rana wanda na dora raina akaki, amma ki saurari hukuncin dakuma abunda ze biyo baya" juyowa tayi ta kalleshi, kawai taga kwalaben giya akan tebur, take taji ranta yabaci koya daddy zeji in yafito yaga dansa yana shan giya a cikin gidansa, shida wani dan iska ta kalli Jeje "ai fada da cikawa baka ga komai ba, se randa sharrin ka yakoma kanka, se ranar dana ga karshenka, asararrae dan wahala, kalle ka sekace karen arna tir da kai da halinka, kuma shi zalunci in abunyine kacigaba, nima bazan gajiba" "Jalal, shike kama da kare amma ba dainiba shike kama da karnuka, kuma kisa ido, zakiga yadda ze koma ke, zakiga yanda zan maida shi, senacika alkawarin da na daukarwa me gidana, se Jalal ya lalace fiye da tunaninki seya kare rayuwarsa a prison a wulakantacce, ke asuwa naganin bayana karya kikeyi, dukda bangane meye nufinki akansa ba amma zanyi maganinki wallahi, senamiki tabon da harkibar duniya bazaki manta ba" "Shikenan naji nakuma yadda, koni ko kai duk wanda yasamu dama yaga bayan dan uwansa, sena wulakantaka daga kai har megidannaka, ainasan waye megidannaka zaka gani, banda ai sam Jalal be dace da tarayya da tababbe irinka ba tunda kaikayi sanadiyar yazama haka, ka cutar da rayuwar sa, sannan kacigaba da wargaza masa rayuwa, nikuma zancigaba da bashi kariya dayi masa addu'a har zuwa numfashina na karshe kuma insha Allah seka wulakanta kafin in bar duniya, sanna kasani........ Shiru tayi ganin Jalal yafito da wata katuwar kwalbar, yaje ya zauna, tana tsaye tana kallonsa ta gefen flours Jeje yaimata wani shu'umin murmushi, Jalal sam be kula da itaba, saboda tana bayan inda yake a zaune, Jeje ya bude giyar ya zuba, sannan ya zubawa Jalal a cup ya mika masa, Jalal ya karba ya kai bakinsa ze sha, Jeje kuma idonsa na kan Jalila, yanaso yaga yadda zatayi da hanzari ta kaaraso inda suke, Jalal ji kawai yayi an kwace kofin hannunsa ta kalli fuskar Jeje ta watsa masa ruwan giyar nan a fuskarshi , gaba daya suka bita da kallo, ta kalli Jeje cikin zafin rai tace "Asararre tababbe mara zuciya, wallahi inbaka ji tsoron Allah ba, mushen jaki seyafi karshenka kyan gani, saboda rashin mutunci a cikin gidan mahaifinsa zaka biyo shi kuyi shaye2" ta kalli Jalal tuni idonta yacika da hawaye "kaima saboda rashin zuciya Jalal mahaifinka na cikin gidan nan kana nan kana sha masa giya a gida, kowane lokaci ze iya fitowa yazeji in yaganka a haka? Memakon ma kuyi a dakinka amma kake shan giya a bainar jama'a ko kunya bakaji, kodayake bakaji kunyar Allah ba sena mutane, bakaji dadin halinka ba wallahi" Jalal sam ba abunda Jalila tayi bane ya bata masa rai illa irin kallon maitar da Jeje yakemata, ta juya ta hankade tabur din da giyar take kai, suka fadi kwalaben suka fashe, tana kuka tana fadin "Jalal kaji tsoron Allah, Allah ya tsinewa me shanta, da duk me ta'amali da ita, amma giya a cikin gidanku, gidan mahaifinka"  ta kalli Jeje "kafita kabar gidan nan, wallahi bantaba tsanar mutum a rayuwataba kamarka, idan na ganka jinake kaman naga shedan natsaneka wallahi, kallon nan danake maka kaman zuciyata ta fashe haka nakeji, in baka bar gurin nan ba sena maka illa da kwalba" ta durkusa tana kuma fasa kwalaben dabasu fashe yadda takeso ba, Jeje ya kalli Jalal "J man, anya yarinyar nan ba mahaukaciya bace ba, kalli fa abunda takeyi" kafin ya rufe bakinsa tafasa hannu da kwalba, da sauri Jeje ya durkusa ze tabata, cikin zafin nama Jalal ya janyeshi, "meye haka kake kokarin yi" Jalila gaba daya ta hargitse kaman mahaukaciyar, Jeje yace "haba J kalli yadda beb din nan takeyi inta illata kanta ba karamar asara za'ayi ba, kallon Jeje yayi,"get out from here" da mamaki ya kalli Jalal "me kake nufi?" "kafita ka tafi yanzu ka bar gidan nan" "Amma Jalal...... " kafita nace bakaji menaceba ne, kosokake seta illata kanta" Jeje ji yayi gaba daya duniyar tamasa zafi jiyake kaman ya mutu ya huta yau shi Jalal yakewa wannan tsawar saboda mace, ya juya ya fice daga cikin gidan, da sauri Jalal yasa hannu dago Jalila daga durkushen da take, ya jinginata a jikin bango sannan yasa hannunsa ya dafe gefe da gefe, ya kalleta yace "baki da hankali ko?, sekinyiwa kanki Illa tukuna, ji yadda kika yanke hannu meye amfanin hakan da kikeyi ne? Ina ruwanki dani dolene sekin shiga shirgin rayuwata" idonta duk hawaye tai masa wani irin kallo, shima kallonta yayi daga sama har kasa, ya karewa rigar jikinta kallo sannaan ya kalleta "Idan kika kuma bari naganki da kaya irin wannan sena bata miki rai, sena yaga kayan ko agaban uban waye, sena miki rashin mutincin da bakya tunani" idonta duk yayi ja tace "au yanzun meya hanaka yagamin rigar, tunda baka da hankali, Jalal baka da hankali na fada kuma zan fada ko agaban waye baka da hankali, ai daka sani ga yagamin riga seka tabbatar min lallai giyar daka sha tafara aiki, yanzu kagama cemin ina ruwana da rayuwar ka, nima ina ruwanka datawa rayuwar, kanwarka wace irin shigar ce batayi seni zaka dingayiwa shouting haka, ko tsirara zan tafi ba ruwanka dani, in kafasa yagamin kaya baka kaunar Allah, sannan ka gayawa abokinka zan gauraya dashi, dagani kabani guri in wuce ko in hankadeka akan kwalaban nan, koka mutu banda asara" banza yayi mata ya cigaba da kallonta, "Nine banida hankali ko? "eh baka da hankali, ka matsa in wuce nace ka tsaya kana karemin kallo, duk ka cikani da warin giya, da kaurin hayaki, kaman zanyi amai. Jitayi kaman wani abu yana shanshana mata kafa, dubawatayi taga menene, ihu tayi, ta rungume Jalal tana" wayyo Allah na mene wannan" dubawa Jalal yayi seyaga ashe dan karensa dayake cewa bobby ne  kiwata shiyake  a part dinsa ya bar kofa a bude shine yafito, karen dan guntune da kadan yafi mage tsayi, ga jikinsa buzu2 da gashi gashi kato sosai amma ba tsawo, daga England daddy yakawo masa shi, Jalila bata taba ganin kare irin wannan ba, kuma batasan dashi a gidan ba. Ilham se kiran layin Maminta takeyi ta labarta mata abunda yake faruwa a gidan, amma wayar taki shiga ba network, dan haka ta yanke shawarar bari ta fito waje kozata samu network. Koda bobby yaga Jalila ta tsorata sekara zuwa kusada ita yakeyi, yana shanshana mata kafa, sosai take ihu tana kara shigewa Jalal, hmm dariya ma tabashi tagama zaginsa kuma yanzu abun tsoro yazo ta rirrikeshi, dan haka ya kyaleta Bobby se zagaye mata kafa yake, "Nashiga uku, Dan Allah a temakeni, wani abu ze cinyemin kafa, waimeye haka bazaka hanashi ba banaso, dan Allah banason mage fa" duk ta yamutsa masa kaya gashi ta goge masa jinin hannunta duk a rigarsa, janyota yayi ya tsayar da ita "meye haka? Kare ne fa kalli" itadai bata taba ganin Kare a haka ba, Jalal ya dago bobby a hannunsa yana nuna mata, aikuwa Bobby yai tsalle yakoma jikinta, ihu takumayi tana nema fita a hayyacinta, tana kokarin cire Bobby a jikinta, dan tsoro yakebata, sosai takuma rike Jalal tana ihu, Jalal ya riketa ya dauke Bobby a jikinta, Abunda Ilham tagani ne yai matukar tayar mata da hankali, tarasa idonta biyune kokuma mafarki takeyi, Jalila ajikin Jalal, abunda bata taba ganin yayi ba, nan take taji kirjinta ya buga da karfi, tama rasa me zatayi, ta juya takoma cikin gida da gudu. A hankali yacewa Jalila "Nutsu mana is just a dog, ba abunda ze miki, kalli yadda kike nema ki firgita kanki, duk tsiwar taki kalli yadda kika rikice akan kare, seki dagani ai, tunda ba jikin Jawwad bane, jikin makakke ne mara daraja, kokindena kyankyamin gashin jikin nawa" tsaki Jalila tayi ta juya, girgiza kai Jalal yayi, Jalila tai tafiyarta gida. Nana tazo ta zauna a kusada Jalila tace "Jalila kamshin wani turare kikeyifa" "kamar ya?" "kamar yadda nagaya miki, kamshin me dadi" "turare na dai dayane kuma kinsanshi sekuma me?" "hmmm bakomai, yaushe zamu kai dinkine?" "ko yaushe ne kikaimana, ni har yanzu bamu gama jarrabawa bane" "to shikenan" Daren ranar Ilham ko na minti daya bata rintsa ba ta dau wayarta ta kira malaminta "hello malam ina cikin damuwa fa, yarinyar nan da alamun soyayya suke da Jalal, tashin hankali na ma kar inje Aikin da akayi masa ya karye" "Aikin da akayi masa har yanzu yana jikinsa, amma kibari zuwa gobe kizo" "to shikenan nagode zanzo goben" sukayi sallama, saboda tunani da bacin rai, tarasa meyake mata dadi, sabida abunda idanunta suka gane mata yau amma gaskiya Jalila tacika yar rainin hankali taita nuna ita batason Jalal dan munafunci ashe soyayya da suke harta kai ta rungumeshi, taita nuna ita ta Allah ce amma abun bahaka yake ba, Allah2 kawai take gari yawaye ta tafi gurin malamin nan ayi duk me yuwuwa ayita ta kare!. Jawwad har ya shirya ze kwanta, Hanan ta kirashi, kamar ya share ta sekuma ya dauka "barka da dare abun kaunata fatan kana lafiya" "lafiya kalau hanan yaya mutanen gidan?" "duk suna lafiya kalau Alhamdilillah, kwana biyu ko nemana bakayi meyasa" "bakomai Hanan abubuwa ne sunmin yawa kawai, gashi muna daf dagama school" "Allah sarki nayi murna sannan inamaka fatan Alkhairi, Allah ya sanya Albarka a ilimin ka yasa al'umma su amfana" "Ameen Hanan naji dadin Addu'arki nagode sosai" "No bekamata kayimin godiya ba, tunda ina sonka zanso duk wata karuwarka Jawwad, amma na lura kaman ina takuramaka ni kadai nakesonka nasan kana guduna saboda Jalila, amma nima yakamata ka tausayamin Jawwad, Abunda kakeji game da Jalila shinakeji game da kai, bazanso incigaba da takurawa rayuwarka ba, bazan so saka ka a cikin damuwa ba, zanso ka kasance a cikin farinciki koda zezama ni narasa nawa" "Hanan yakamata ki......" "A'a Jawwad base ka gayamin komai ba, karka damu, amma kasani bazan dena sonka ba har karshen rayuwata, inasonka Jawwad, amma Insha Allah wannan shine kira na karshe da zanyu maka, bana son rusa maka farinciki, tunda na fuskanci ina takuramaka, ka gaishemin da masoyita kuma yar uwata" kafin yayi magana ta kashe wayarta, jiyayi daga karshe kaman kuka take, seyaji sam beji dadin hakan ba, dan haka yai kokarin bin layinta amma a kashe haka yaita trying har ya hakura. Da wuri Jalila ta shirya dan tafiya makaranta, sam bata jin dadin jikinta, ta kwana da ciwon kai wadda tasan damuwa ce datayi mata yawa, kallo daya zakayi mata kasan tana cikin damuwa dan duk ta rame, tana fitowa ta tarar manu yana goge mota, suka gaisa ta shige gaban mota ta kifa kanta, tana jiran manu yazo su tafi, har ya shigo ya kunna motar bata dago kanta ba, seda taji gudun yayi yawa ba tareda ta dagoba tace "Manu mutafi a hankali mana, kaina ciwo yake sosai, wannan gudun kaman zamu bar gari" shiru be amsaba kuma be dena gudun ba, dagowa tayi kawai taga Jalal ke tuka motar ba manu ba "kaiii meye haka kuma? Ina manun?" shiru yayi yacigaba da tuki "magana fa nake maka, yauma ka dakkonine don kamin wulakanci, inkuma makara wallahi baka isaba ka ajiyeni kawai in sauka" still bekuma cewa komai ba "wai baka jinane? Nika ajiyeni, bana son adinga gani tareda kai kar wannan shashan yan matan naka su dinga min hauka, gashi har wani yafara titsiyeni sena gaya masa alakar dake tsakanina da kai ni ka ajiyeni" "Ke!!!" seda ta tsorata, saboda yanayin da yayi maganar "idan na ajiyeki duk abunda yasameki kika sani, ba cewa kikayi kanki yana ciwo ba, amma se surutu kikeyi, wallahi kika kuma magana sena baki mamaki, in an ganmu tare duk wanda ya tambayeki kigayamasa abunda kika gadama" ba shiri taja bakinta tayi tsit, ko minti biyar beyi, da wannan maganar da Jalal yayi ba, wata mota tasha gaban tasu motar a guje, wanda ya tilastawa Jalal yin parking. I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 Daga Alkalamin Aysha cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE 1️⃣3️⃣ 66_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Jalal bai fita daga motar ba,  dayake motar tint glass ne, da mamakin Jalila motar data sha gaban tasu, Jeje ne a ciki da wasu manyan karti suka fito, suka tinkaro inda tasu motar take, knocking sukayi a side din direba, a hankali Jalal ya sauke glass sukayi ido hudu da Jeje, rikicewa Jeje yayi, cikin inda inda da mamaki yace "J man kaine da kanka, huh ya gida amm... "shut up please" Jalal ya katseshi, "nasan za'ayi haka ai, shiyasa na shirya hakan, Jeje baka da amana, baka da mutunci, kobataci darajar kowaba taci darajar yayanta amininane, amma saboda baka da mutunci shine ka shirya cutar da ita, kuma duk abubuwan data fada akanka karyane? Ba karya bane ba, Jeje inaso in maka kashedi, koda makamancin wasa ba kai babu ita, idan nakuma fuskantar ka shirya wani abu akanta na cutarwa, you know what am capable of doing, ka kiyaye " " haba Jalal kai ka dauki abun a haka amma ni banyi niyyar yimata wani abuba... "Enough malam, kayimin blocking way, ku janye motarku zan wuce" cike da bakinciki Jeje yasa aka janye motar, ya shirya ya dauke Jalila yaketa mata haddi, saboda abunda tayi masa, ya dauki fansa akan abubuwan datayi masa, ya akayi Jalal ya gane shirina haka, dukan motarsa yayi da karfi, yayiwa kartin umarnin su shiga mota. "kinga Abunda shishshiginki ya nemi ya janyomiki ko? Da kin bari kin taho ke kadai da wani zancen ake ba wannan ba" ya karasa maganar cikin fada, kallon Jalal tayi, ta dauke kanta "waman yatawwakallu alallahi fahuwa hasbuh, dan haka be isa yayi min wani abu ba, kuma kaima baka isa ka kareni daga komai ba, ba gudu ba ja da baya wallahi koze kasheni seyayi nadamar niyyar dayayi akaina, kar ya fasa, zan nuna masa wacece ni duk Abunda nasa gaba Allah yana bani sa'a kansa, bana alwashi in kasa cikawa, duk wanda ya takaleni da sharri senaga bayansa, kodame yake takama, dan haka ba kaika kareni ba Allah ne, kuma ka gaya masa zamu gauraya dashi dan haka kadenamin tsawa" Jalal yakara jinjinawa Jalila akan taurin kai, betaba ganin mace me taurin kai kamanta ba, bata da tsoro bata son raini, kuma abun mamakin she has a luck, kota gangamo rigima se Allah ya kwaceta. Kallonta kawai yayi yai shiru bekuma cewa komai ba yacigaba da tukinsa, suna zuwa kofar gate yayi parking, "Fita" "aiko bakace in fitaba zan fita, komeye nayimin gadara aiba motarka bace, kuma bani nace ka kawoni ba dan haka karka kara yimin tsawa" harzata bude motar, setaga wannan lecturer da Sir Hafiz ya kaita gurinsa wato Sir sagir yazo wucewa, da sauri ta kalli Jalal "Yawwa kasan wancan mutumin?" Kallo daya yayiwa sagir yagane shi, cousin din baban Ilham ne, shikuma meye hadinsa da ita oho, amma yace "ban saniba kifita nace"  "to kayiwa kanka dama sako yabani in baka, tunda kace haka shikenan" ta fice abunta Jalal ya girgiza kai yatafi. Karfe tara na safe Ilham tana kofar gidansu Yaseera ta kirata awaya ta fito suka tafi gidan malamin nan. Suna zaune agabansa kaman masu neman gafara, ya kalli Ilham yace "kunyi sake gaskiya, saboda aikin baya tasiri akansa yanzu sosai kaman a baya, amma yanzu mekikeso ayi" Ilham kaman ta fashe da kuka tace "Malam har za'ayi maganar aure bawan Allah nan yaki yaita min wulakanci, amma katsam naganshi da wannan yarinyar da nake gayamaka rungume a kirjinsa, hankalina ya tashi matuka" "to aina gayamiki Asiri baze tasiri a jikinta ba, yarinyar bahaka take zaune ba tayiwa Al'qur'ani kyakyawan riko, tanada ibada danhaka sedai ayi Amfani da kissa, da dabarunku na mata akanta badai sihiri ba" ya dakko wata kwalba da ruwa a ciki ya mikawa Ilham, yace "gashi nan ki tabbatar kinzuba mai wannan ruwan a Abinci ko Abun sha kin bashi da hannunki yaci, daga nan kome za'ayi baze kuma yinkurin hana Aurenku ba" Yakuma dakko wani turare, ya mika mata tasa hannu ta karba sannan yace "shikuma wannan ki tabbatar kinyi amfani da wannan turaren, kinshafa kafin kibashi Abinda kika zuba wannan maganin" Ilham ta gyda kai, yaseera tace "to amma malam kana ganin auren nasu ze yuwu kuwa?" "in har tayi yadda nace, komai zewuce ze aureta, kiyi a hankali, kikula da kyau muddin aka samu kuskure to komai ze iya lalacewa, danba karamin hadi nayi ba, karki bari wannan damar ta wuce" sukayi godiya Ilham ta bude jaka ta debo kudi fal ta bashi, sannan suka fito suka tafi, "Yaseera wallahi bansan ya zanyi inbashi Abu yaciba, haushina yakeji sosai, ko kallona bayayi balle yaci abun hannuna" "aikuwa haka zaki dage ki kokarta har bukatarmu ta biya, kiyi iya kokarinki kiga kin aiwatar, sannan yazakiyi da wannan yarinyar" "banni da shedaniya aini harnaga abunda zan mata kyaleta kawai" akazo inda yaseera zata sauka sukayi salkama. Ilham tana karasawa gida taga mota a bakin layinsu, rabawa tayi da niyyar ta wuce aka kuma biyota da motar, ta ja ta tsaya, Hannah ce tafito daga cikin motar, tasha gaban Ilham, kallo daya Ilham tayi mata ta ganeta, Ilham ta hade rai sosai, Hannah tacire glass din fuskarta tace "nasan kin ganeni, babu bukatar inmiki bayanin waceceni, kashedi ne nazo miki dashi, wanda sabawa kashedina daidai yake da rusa duk wani farincikin ki" "inajinki fadi abunda kikeso" "Naji labarin za'ayi miki baiko da Jalal, dan haka nazo miki da kashedin kiyi gaggawar janye batun ayimuku baiko, inbahakaba banki in salwantar da rai ba, dan haka kishiga hankalinki, kiyi tunani" mamakine yakama Ilham, wannan maganar kuma daga ina amma ta dake tace "Kinyi kadan wallahi, sedai muyi asarar rayuwarmu gaba daya amma kome zakiyi, wallahi indai ina numfashi baki isaba, aurena da Jalal se anyi shi" "haka kikace ko?" "bakida kunne ne, dalla matsa ni kibani guri in wuce" Ilham ta bangaje Hanna ta wuce, Hanna tace "zaki gani kuwa" Ilham tai tafiyarta gida, Hannah ta shige motarta, itama ta bar gurin. Yausu Jalila suka kamalla first semester exams dinsu, su sameera se kuma bibiyan zahra suke akan su tabattar data amince da bukatansu, yayinda gefe daya suke tayiwa Jalila barazana kala kala. Da Jalila takoma gida ma sabgoginta ta shiga yi, Suleman ne yakirata, ita mutumin nan yafara isarta, ta daga wayar suka gaisa, yaita mata magiya tabarshi yazo gidansu, "dan Allah kayi hakuri babana ya bawa wani, inkazo gidanmu zega kaman ina kokarin bijirewa umarninsa ne" "subhanallah kiyi hakuri, baki gayamin da wuri ba, bazanso kisamu sabani da mahifinki ba, amma naso ace na sameki a matsayin matar aure ina sonki sosai, a tarayyata dake ya nunamin kinada nutsuwa da ilimi, dan haka ina son mudinga gaisawa kafin kiyi aure" murmushi Jalila tayi aranta tace "gaskiya mutumin nan akwai saukin kai" a fili tace "karka damu insha Allah zamu dinga gaisawa" sukayi hirarsu sannan sukayi sallama. Yana kashe wayar taga tests din Alhaji Kabiru akan wai tana wulakantashi tsawon lokaci yanzuma ya kirata wayarta busy tama waya da wani, in bazata yadda dashiba ze hakura" murmushi tayi sannan tace "hmm kiris ya rage zaka gane baka da wayo" ta kirashi a waya ta dinga lallabashi tana bashi hakuri tayi masa alkawarin zasu hadu ranar juma'a, haka ya yadda yaita murna. Takira Zahrah a waya tace mata tacewa su sameera zatazo gurinsu ranar juma'a, zahra ta yadda. Jalila tace "Allah yasa abunda na shirya yatafi dai2". A yammacin ranar ta shirya tasa nikabinta ta tafi hisba, taje takai report akan wannan gida da su sameera suke sheke ayarsu a ciki, sukayi mata alkawarin insha Allah zasu kaiwa gurin sumame, Jalila tace tanason ganin mataimakin commnder personally, yace bakomai sukaje wani office din Jalila tace "ranka ya dade gurin nan sonake kuje ranar juma'a misalin karfe hudu na yamma" "Amma meyasa?" "saboda a lokacinne manyan lalatattun suke zuwa, abun haushin hada manyan mutane" "karki damu Insha Allah zamuje" "to shikenan nagode sosai ranka ya dade" Jalila ta taho gida cike da farinciki tareda fatan Allah yasa su afka tarkonta, sesun kunyata tun a duniya, daga nan ta taho gida, tana zuwa gida Jalila tasamu Nana tace "Nana kece me sauraran radio, dan Allah inaso kibani lambar wani gidan radio inkina da ita wanda kikasan in Labari yajemusu se duniya taji" Nana tace "ikon Allah yaukuma me za'ayi da lambar radio, Allah yasa dai ba wata rigimar kika kwaso mana ba" "ke haba dai, nima sonake indinga jin radio yadda nima zan dinga kira inji muryata a radio" Nana tai murmushi "to shikenan na dauka wata rigimar za'a kwaso mana ne" Jalila Allah 2 take asabar tazo taga yazata kaya. Ta kaiwa daddy Jalal list din abunda take bukata na girkim da zatayiwa bakinsu. Jalila tagayawa zahra cewar tacewa su Sameera karfe hudu na yamma zatazo gidansu. Ilham duk wata hanya data san zatabi domin janyo hankalin Jalal hartasamu damar bashi wannan maganin amma yaki, dan wani mugun kwarjini ya kema ta gashi ko san ganinta bayayi, gefe guda tsanar Jalila na karuwa a zuciyarta, kiris take jira tasamu damar dazata yiwa Jalila abunda se kowa ya tsaneta. Haka nan Jawwad yakejin tausayin hanan a ransa, yana ganin kaman be kyauta ba, amma duk yadda za'ayi shi Jalila yakeso, kuma yana fatan ze aureta. Yayinda bangare  Jalila tana kokarin yin baya2 da Jawwad musamman idan Maama tana nan, sabida batason tashin hankali sam, dan zuciyarta na rayamata yiwa Maama rashin mutunci wataran, shiyasa ko Abinci ta dena kai masa sedai halima ta kaimusu, iyakacinta da shi ta waya, sekuma in anyi sa'a ya shigo cikin gida kokuma sun hadu a harabar gidan. Ranar Alhamis Jalila taje gidansu zahra, Zahra tayi murna sosai da ganin Jalila, tayi wa ummanta introducing din Jalila suka gaisa daga nan suka wuce daki, Jalila tace "ke ba zama nazo yiba, ya ake ciki kingaya musu gobe in Allah ya kaimu zakije?" "Eh nagaya musu, zanzo karfe hudu" "yawwa zahra to yanzuma wani abu nakeso kiyimin" "me kenan?" Jalila ta dakko wayarta tasaka wani sim din a ciki, sannan ta kalli zahra, lamba zankira yanzu, inason kicewa mutumin nan kinaso ku hadu a wannan gidan ranar juma'a, kinuna masa kaman kinsanshi a baya amma bazaki gaya masa wacece ba" Jalila taima zahra bayanin abunda takeso tayi, zahra tace "Amma Jalila..." kinga babu batun amma kawai kiyi hakan" "to shikenan" Jalila tai hiding lamba takira Alhaji kabiru tabawa Zahra, bugu biyu ya dauka sannaan yace "Hello wake magana" zahra tace wata baiwar Allah ce, kadai kacemin baka dau murya ba" "gaskiya bangane ba, wacece dan Allah?" "nikuma kaga naganeka ba amma in duniya da gaskiya be kamata ka kasa gane wace ba, a cikin yan matanka ne" "to aikinsan abunne dayawa" "hakane kam, amma in ka ganni zakaji kunya akan cewar baka ganeniba" "ko? To nidai ki gayamin" "bazan gayamaka ba sedai in munhadu a gidana zaka gane" washe baki yayi, "gidanki wanne kenan" ta kwatanta masa gidan dasu Sameera suke zuwa, "kazo ranar juma'a karfe hudu, semu hadu ko?" "aikuwa zaki ganni dan zanso sanin wacece?" zahra tai murmushi "to shikenan nagode se anjima" zahra ta kashe wayar, ta kalli Jalila, Jalila ta jinjina mata "weldone dear kinyi yadda nakeso, zan barmiki sim din nan a gurinki, kucigaba da waya har Allah ya kaimu gobe juma'a, komai yazo karshe" "Amma Jalila shi waye wannan?" "ba ruwanki kedai kawai kiyi abunda nace inkuma akasamu kuskure kece a ruwa baniba" Jalila taimata sallama tai tafiyarta. Yau juma'a shine ranar da Jalila take sa ran su Sameera su fada trap dinta, kuma gobe ranar asabar bakinsu Jalal zasuzo dan haka ta rarraba hankalin ta kashi2, tun sassafe take up and down, taje kasuwa tayo siyayyar abubuwan dazata bukata na aikace2 da zatayi, karfe uku da rabi ta shirya tasa hijjabinta da nikab ta dau jakarta, Nana ta kalleta "Jalila ina zaki hakane kiketa sauri?" "banisa zanyiba yanzu zan dawo" amsar da Jalila tabata kenan tafito, tanata sauri a harabar gidan taci karo da Jawwad, "Baby ina zuwa haka da ranar nan? " "Yaya zan dan fitane gidansu wata kawata" "in hanya ne muje se in kaiki" "Aa kayi tafiyarka kawai, yanzu znadawo bazan bata ba kaji sweetheart" ta kashe masa ido tai waje murmushi yayi ya girgiza kai, Jalila ta tafi layin gidan, can karshe tasamu guri ta zauna, tana nan zaune motarsu Sameera tazo suka shiga itada Saleema, sunyi wata irin shiga ta fitsara abun babu kyan gani, ga wasu manyan karti  maza suna shiga suna fita daka gansu kaga manyan yan duniya, dan basu da maraba da yan daba. Jalila takira zahra a waya "ke ya akeciki kunyi waya yatahone?" "Eh ya taho, yacemin yana hanya, yanzu su Saleema suka kirani, wai ina inane, nace musu nakusa zuwa" Jalila tace "good kice masa ya hanzarta inbahakaba zaki fita" "to shikenan" Ba'ayi minti goma ba da waya dasukayi da Zahra sega Motar Alhaji kabiru a layin gidan yayi parking dai2 kofar gidan da su  Saleema suke ciki, yana zaune a cikin mota be fitoba, zahra takira Jalila, "Jalila yacemin waigashi a kofar gidan" "kice masa yashiga kansa tsaye" Jalila ta katse wayar tanata addu'a Allah yakawo yan hisaban nan da gaggawa, tana kallo Alhaji Kabiru yafito daga mota ya doshi gidan nan, Jalila tana ganin ya shiga gidan, takira gidan radio ta sanardasu cewar hisaba sunzo kame a  unguwar dan bare kuma akwai wani gagarumin abun kunya dake shirin faruwa, "Innalillahi wa inna ilaihi raji un" shine abunda Alhaji ya dinga maimaitawa ganin yarsa ta cikinsa Saleema da shiga rabin tsirara akan cinyar wani kato, suna shan shisha, gefe ga wasu sunata aikata badala ciki hada Sameera, a takaice dai gidane na manyan karuwai da yandaudu I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 ..🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣4️⃣66_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Koda Saleema ta dago tai ido hudu da mahaifinta a gigice ta mike daga cinyar wanda take zaune, tana zazzare ido, gaba daya sukayi cirko2 suna kallonsa, koda ya duba yaga waye Saleema take kan cinyarsa ba kowabane illa Jeje, a gigice Alhaji Kabir yace "Saleema abunda kike aikatawa kenan, kin cuceni kin cuci kanki Allah ya isa tsakanina da ke" ya maida idonsa kan Jeje "nizaka ciwa amana, karasa da wadda zakayi lalata se yar cikina, duk halaccin danayi maka a rayuwa wallahi seka ga karshenka sekaga abunda zanyi maka, sena dau mummunan mataki akanka" Jeje rasa mezece yayi gaba daya ya rude, daga gefe wani tsageran matashi yace "wai dan Allah meyakawo ka nan gurin, kake wannan maganganun ne, nina dauka harka kazo, kaima fa ana kaimaka matan nan guest house dinka to meye dan anyiwa yarka, abunda kakewa yayan wasu nefa" seda Alhaji Kabiru ya duba sosai sannan ya gane matashin, tabass suna kaimasa karuwai yana biyansu kudi. A fusace Alhaji Kabiru ya dau wata kwalba ya nufi inda matashin yake, Saleema se kuka takeyi, jin ance itama ga abunda mahaifinta yakeyi, yana zuwa ya bugawa matashin a ka, sauran matasan sukayo kansa, duk wanda yazo seya kaimasa suka da fashashiyar kwalba. Itako Jalila koda taga Alhaji Kabiru ya shiga cikin gidan nan ta kuma kiran yan jarida, tana gama wayar sega motar "yan hisba, tareda yan sanda, sukayiwa gidan dirar mikiya, suka kewaye shi, sannan wasu suka shiga cikin gidan, babban abun kunya da asara shine kama uba da 'ya a gidan karuwai, nan aka tarkata kansu tsaf, Alhaji Kabiru se rantse2 yake, ga wadanda yajiwa ciwo da kwalba, Saleema banda aikin kuka ba abunda takeyi, kan Jeje se zubarda jini yakeyi,'yan sanda suka caje gidan inda akasamu miyagun kwayoyi, da kayan shaye2 kala2, kafin a tafi dasu yan jarida suma suka karaso, suka rufawa motar yansanda baya dan zuwa daukar rahoto, ba karamin farinciki Jalila tayiba, rasa inda zatasa kanta tayi dan murna, batasan lokacin dataji hawaye farinciki nabin fuskarta ba "Allah kai kabani wannan dama, Allah kaikabani nasara ba dabarata da wayona ba, Allah nagode maka, nagode da ni'imarka da kariyarka, Allah kasa sanadiyar shiryuwar bawanka ce tazo" hanyar titi ta nufo tana sauri, yamma tayi sosai, ta tafi gida gida cike da murna da farinciki. Takoma gida tanata murna, tana zuwa ta tarar da sa'ada tazo itada Naja wai a gidan zasu kwana biyu, Jalila ko takansu bata biba, murnarta kawai takeyi, Nana tace "Baby meye sirrin wannan fara'ar da murmushinne haka?" "Nana nima ban saniba ina murna ne kawai" "Hmm kyama fadi gaskiya" "gaskiyar kenan Nana" sukayi dariya gaba daya. Kan kace me Labari yafara yada duniya cewar an kai sumame gidan karuwai, inda aka kamo hada wani uba da 'yarsa tareda yaronsa a gidan" nan da nan zance yafara zaga social media, da sauran kafafan watsa labarai, inda ake ta tir da Allah wadaran akan Alhaji Kabiru. Nana takira Jalila a waya "Jalila Allah yasaki a Aljannah, kinceci rayuwata da sauran rayukan dasu Saleema sukaso lalatawa, Allah yabiyaki da mafificin Alkhairi, Allah yabaki miji nagari me kaunarki" "ba komai Zahra, Nagode sosai nima Allah ya amsa mana bukatunmu" Alhaji Kabiru yashiga cikin matsanancin bakin ciki, yarasa msyake masa dadi, wai yarsa yakama da wanda ya amincewa wato jeje, abun bakincikin ankamoshi da yarsa a gidan karuwai, gashi ba'asan ainihin me yafaru ba amma zance yanata yada duniya, nan yashiga tunanin waima wacece wadda takirashi tace yaje gidanta ne, in akajima ya tuna yadda yaga yarsa da jeje, se ransa yakara baci, ya kalli Jeje yace "Jabir (shine ainihin sunan jeje) Allah ya isa tsakanina da kai, duk halaccin danayi maka a rayuwa amma ka lalata min yarinya" "dama can lalatacciyace, kuma halaccin dakayimin aiba kyauta kaimin ba aiki nake maka, shekaru nawa nayi inamaka bauta" "Au hakama zakace ko, zamu fita ai zakaga abunda zanyi maka, kasanni kasan halina" Jeje ya kalleshi "kabari kaga munfita lafiya tukuna, aisena bari munfita lafiya zaka samu damar yimin wani abu, dan haka sena fadi komai" zazzaro ido Alhaji Kabiru yayi, "me kake nufine wai?" inbaka ganeba seka bari sena aiwatar zaka gane".    Duk yadda su Sa'ada sukaso bakantawa Jalila rai bata kulasu ba dan karma su bata mata farincikinta, tabar musu dakin takoma na halima ta kwana a can, tun sassafe tai salla, sukayi aikace2 dazasuyi itada halima a cikin gidan, sannan ta tafi gidansu Jalal itada Halima, tunda Ilham tai arba da Jalila takejin kaman ta dau wuka ta kasheta, suka gaisa da Mummy ta nuna mata kitchen Jalila suka shiga suka fara abunda yakamata, aka jima Nana itama tabaro wasu sa'ada gidan ta tabiyosu Jalila a ranar suka hada snacks din dayakamata, sukabar aikin dabasu gama ba zuwa gobe, kafin bakin suzo sesu karasa, Nana da halima suka koma gida, Jalila ta tsaya tana jarasa gyara kitchen din, Jalal ya shigo da katon kwando cike da fruit ya ajiye yai waje abunsa, ta zauna ta shiryasu a fridge sannan ta tafi. Wahsegari da safe Jalila ta dawo, bata tashi halima ba daga bacci saboda taga alamar tagaji sosai jiya, ta dama kunun gyada, ta dibi nata a dan karamin flask ta tafi dashi. Jalila tayi busy sosai a kitchen, dan bata samu ko karyawa tayi ba, dogon wandone a jikinta da rigarta har gwiwa me dogon hannu, ta daure kanta da dankwali, amma karshen gashin ta yafito, taji alamun ana kallonta, bata waigaba ta basar tacigaba da abunda take, cikin kitchen din ya karaso ba sallama ba komai yakama dube2, bata kulashiba tacigaba da aikinta ya jijjiga tea flask bakomai a ciki, tsaki yayi ya bude fridge yana kallon arrangement din datayiwa fruits din, still ya rufe fridge din, Jalila ta fuskanci yunwa yakeji, ta kalleshi "wai meyene?" "bansaniba" "karka sani din" yaje ya duba kettle yaga akwai ruwan zafi a ciki, ya dakko ya zuba bako lipton, ya dakko madara da sugar yana kokarin antayawa, ita Jalila ma dariya yabata, ta dakko flask ta zuba masa kunun gyada a cup, ta zubamasa samosa, ta mika masa, bako kunya ya karbe, yanemi guri kan kujera a kitchen din yai zamansa yafara ci, itakuma tacigaba da aikinta, wayarta tafara ringing, sunan sweet hanny shine akan screen din wayar, tadaga wayar tasa a kunnenta "Hello sisyna ya kike" hanan tace "Hmm ba fada meyakawo gaba Baby, kin yadani, kin manta dani ko?" "A'a hanan ban manta dake ba, ko zan manta komai bazan manta da yar uwata ba" "Anya kuwa Jalila? Kina guduna saboda inason Jawwad ko? Karki damu hakan baze shafi zumuncinmu ba, amma yakamata kikawomin ziyara, in duni6da gaskiya bekamata ace tunda kikabar kaduna baki kuma zuwa ba" Kwalla ce ta taru a idon Jalila, cikin muryar kuka Jalila tace "Hanan bazan iya zuwa kaduna, bazan iya zuwa anguwarmu ba, Hanan hakan ze tayarmin da hankali, inzo unguwarmu ummi bata nan, bansan inda take ba, kiyi hakuri Hanan, amma kina raina daks da sauran mutane masu mahimmanci danake dasu a garin" takarasa maganar hawaye nabin idonta, "Jalila na fuskanci abunda yake damunki, inajin damuwarki a zuciyata, kiyi hakuri mucigaba da addu'a kinji, kidena kuka" gyada kai Jalila tayi kaman tana gaban Hanan, sannan tace "Nagode Hanan, kigaida kowa da kowa mussaman babana" "zasuji Insha Allah yar baba" ta kashe wayar, duk kokarin da Jalila tayi ta cigaba da aikinta amma takasa, tanata kokarin daurewa ta hadiye kukanta amma takasa hawaye ketabin idanunta, sosai Jalal yaji tausayinta ya kamashi, yaji inama ace shima zeji wannan kaunar da shaukin da y'aya sukeji game da iyayensu mata, har fuskar Jalila tayi ja. Tasowa yayi yazo bayanta ya tsaya yana kallon ta, dagowa tayi ta kalleshi suka hada ido, "Meyasa bazaki karbi kaddara a duk yadda tazo miki ba, memakon kiyi addu'a amma kike kuka, hakan bekamata ba, kizama jaruma mana" dauke kai tayi takuma fashewa da kuka wannaan karon hada sheshsheka, sunkuyowa yayi daf da ita a hankali yace, "Ummi tana raye, kuma zaki ganta very soon, jikina yana bani" da sauri ta kalleshi ya jinjina mata kai, yai mata alama  tasa hannu ta goge hawayenta, "da mutum yana da ikon sauya kaddararsa, kokuma kuka yana canza wani abu, da mutane dayawa sun fita daga matsalolin dasuke ciki, wani lokacin mukanyi kuka ne don samun sassauci a cikin damuwar da take damunmu, amma ta wata fuskar kukan yana karamana matsala ne da damuwa, ummi tayi rayuwa me tsayi ba tareda yan uwanta ba, kuma hakan besa wani abu yafaru da itaba, dan haka kema addu'a zakiyi kicigaba da hakuri " yana gama fadin hakan ya mike ya kai hannu ya juye sauran kunun gyadan nan ya juya ya fice, Jalila tabi bayansa da kallo, tai ajiyar zuciya tacigaba da aikinta jikinta a sanyaye. Wajen karfe shadaya na rana mummy ta shigo tanayiwa Jalila sannu da aiki, Jalila tace yawwa" Mummy barka da safiya" "Yawwa barka ya aikin?" "lafiya kalau Mummy nakusa kammalawa ma" "to masha Allah" Bayan Mummy tafita ba dadewa Jalila taje gida ta dakko wasu spices ta dawo, ta windowa kitchen dake harabar gidan taga Ilham tana zukar wani abu a kwalba da syringe tana tsirawa ruwan a jikin wani jan Apple, Jalila ta tsaya tana kallonta, tana gamawa ta maida shi cikin fridge ta rufe ta fita ba tareda ta lura Jalila ta ganta ba.  Se wajen karfen daya Jalila ta karasa girkin Abincin tareda taimakon Nana data biyota daga baya. Sun kammala komai sun gyara kitchen din kaman ba'ayi amfani dashi ba, suka fito itada Nana, daddy yana palour "Sannu da aiki yaran kirki, nasaku wahala ko?" Jalila tai murmushi "ba wani wahala daddy mun kammala komai ma" "Masha Allah, Allah yayi Albarka" Nana tace "Ameen daddy, amma ni gaskiya nagaji" "Aidama ke lazy ce Nana" sukayi dariya, daddy yace "Jalila amma in sunzo aizakizo kiga yan uwan yayanki ko?" murmushi tayi ta jinjina kai, daga nan suka fita suka tafi gida. Jalila ta gaji dan haka wanka tayi, Naja tana kan gadon ta baje, Jalila ta haye gadon ta kwanta itama, Naja ta kalli Jalila "malama meye haka? Bakiga nice a kwance agurin ba" "Eh banganiba, babu a house ko?" A fusace Naja tace "amma kinsan karyane kicemin babau a house ko" "in akwai a house ai dabakiyi wannan shirmen ba, kodayake aiba mamaki a sha rashin hankalin nono" "kut me kike nufi?" "inkika bari, nakuma bude baki da nufin mayar miki da martani sekinyi kuka, dan haka kiyi abunda ya dameki bacci zanyi" Jalila ta kwanta abunta, tabar Naja tana kallonta, can cikin bacci Jalila taji Nana tana cewa "Ke Jalila ki tashi, bakinku sunzo fa?" A hankali Jalila ta bude ido "wane bakin kuma?" "Bakinsu Jalal mana, ki tashi yau zakiga yan uwansu, masu irin hancinsa" Jalila takuma juyawa akan gadon tace "ni dan Allah ki kyaleni mana" "Ke Jalila kinada matsala wallahi, dan Allah ki tashi muje, akwai wanda nakeson gani a cikinsu, inajin kunya inje ni kadai" Jalila ta bude ido ta kalli Nana, "ikon Allah, Nana kinda damuwa, wallahi nikam ki kyaleni" Nana tace "kar Allah yasa kije" "eh bazaniba" har Jalila tafara bacci, ta tuno Apple din nan, kartaje Ilham takuma zuba wani abu, zumbur ta mike, ta bude drower tasaka kayanta, tafito da sauri ta tafi gidansu Jalal, harabar gidan duk motoci, tundaga varrender take jiyo hayaniyar mutane, ta bude kofar palour a hankali, dayawansu kamansu daya da Daddy Jalal, duk haka suke da dogon hanci sosai aranta tace "tab wannan ko bata sukayi da wannan hancin nasu za'a ganesu" se yare sukeyi, ga Jawwad ma a cikinsu, shima se yaren ake dashi, tanaji daya yana tsokanar Nana, da wata irin hausarsa yace "gaskiya Nana kin girma kin ganki kuwa, waike yan mata tunoki nake lokacin kina dan karamarki" Nana ta dan zumbura baki "kajika Kaima ai da bahaka kake ba, ji yadda ka wani tara gemu, waikai dole ka girma" dariya sukayi gaba daya, daddy yai murmushi yace "Nana yaushe zaki dena surutu ne, bakinki baya mutuwa" kallo daya zakayiwa Jalal kasan yana cikin farinciki, fara'a yake sosai, 'yan uwansa duk nutsatstsu, amma shi yafita daban a cikinsu dan gashin kansa ba kyan gani, ga kallo daya zakayi masa kasan lips dinsa yana shaye2, setaji hakan ba dadi, a hankali ta sulale ta shiga kitchen ba wanda ya ganta, Tana tsaye a kitchen din Ilham ta shigo taci kwalliya sosai, gashi tasa wani turare me karfi, wanda sam bashida dadi, wani banzan kallo taiwa Jalila sama da kasa a wulakance, "Aikin banza jaraba da maita, tunda kingama abunda akasaki aisekikoma inda kika fito ko, ko yanzunma wani munafuncin zakiyi, shine kika dawo" "Aini bana munafunci kaina tsaye nake abunda nakeso, Aikinne ban gama ba, nazo nakarasa wanda aikin da nakarasa yafi kowanne mahimmanci, na bata aikin wasu dan gyara nawa, kamar yadda nasha fada muddin aikin wani yashigo nawa, sena bata shi" kallon Jalila tayi cike da mamaki wannan karon kuma me take nufine, kwafa Ilham tayi tawuce ta  fara daukar kayan Abinci tana fita dasu, alhalin lokacin da Jalila take aikinta ko dauraye spoon Ilham bata tayata ba, Jalila ta tsaya tana kallonta tagama fita da kayam Abincin, ta dawo ta bude fridge tafara jera fruit a tray, tana kallon Ilham ta dakko Apple din nan tai masa guri na musamman akan tray din, tayi waje, Jalila tabiyo bayanta ta tsaya a window tana kallonsu, Ilham sewani iyayi take tana kwarkwasa, Jalila tayi mamaki da bataga Mummy ta fito ba, bakin su biyar ne maza hudu se mata uku, duk daka gansu kasan yan uwan daddy ne, Ilham cikin iyayi tace "bari kufara da fruits kafin kuci Abincin ko" cikin bakin daya shima me matukar kama da Jalal yace "Eh hakane gaskiyanki Ilham" tafara binsu daya bayan daya tana basu Apple, Jalila tana kallonta ta dauki Apple din nan ta mikawa Jalal, ya mika hannu ya karba shima kamar kowa dayake Apple yana daga cikin favorite fruit din Jalal. Jalila tana ganin irin kallon da Ilham kewa Jalal, Ilham na ganin Jalal yaci Apple din nan tafara murmushi. dawowa Ilham tayi da tray din ta ajiye a kitchen, har zata fita Jalila tace "bar murna karenki yakama zaki kinyi mantuwa" waigowa Ilham tayi tana kallonta, kawai taga Jalila tana jefa Apple sama tana cafewa "Ilham kinsaba lamba, saboda na canza Apple din" a razane ta kalli Jalila, Jalila ta karaso gaban Ilham, ta kamo hannunta ta doramata Apple din, duba da kyau wannan shine Apple din dakika zubawa magani ba wanda yaci ba, ko baki gayamin ba nasan abunda kika zubawa Apple din nan na asiri ne akan Jalal, Ilham shi so ba'asiyan sa kuma sihiri be isa yabaki soyayya ba koya soki na lokaci kadanne, in abun ya barshi shikenan, yanzu meye ribarki a cikin cutar da dan uwanki? " .. I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣4️⃣66_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Koda Saleema ta dago tai ido hudu da mahaifinta a gigice ta mike daga cinyar wanda take zaune, tana zazzare ido, gaba daya sukayi cirko2 suna kallonsa, koda ya duba yaga waye Saleema take kan cinyarsa ba kowabane illa Jeje, a gigice Alhaji Kabir yace "Saleema abunda kike aikatawa kenan, kin cuceni kin cuci kanki Allah ya isa tsakanina da ke" ya maida idonsa kan Jeje "nizaka ciwa amana, karasa da wadda zakayi lalata se yar cikina, duk halaccin danayi maka a rayuwa wallahi seka ga karshenka sekaga abunda zanyi maka, sena dau mummunan mataki akanka" Jeje rasa mezece yayi gaba daya ya rude, daga gefe wani tsageran matashi yace "wai dan Allah meyakawo ka nan gurin, kake wannan maganganun ne, nina dauka harka kazo, kaima fa ana kaimaka matan nan guest house dinka to meye dan anyiwa yarka, abunda kakewa yayan wasu nefa" seda Alhaji Kabiru ya duba sosai sannan ya gane matashin, tabass suna kaimasa karuwai yana biyansu kudi. A fusace Alhaji Kabiru ya dau wata kwalba ya nufi inda matashin yake, Saleema se kuka takeyi, jin ance itama ga abunda mahaifinta yakeyi, yana zuwa ya bugawa matashin a ka, sauran matasan sukayo kansa, duk wanda yazo seya kaimasa suka da fashashiyar kwalba. Itako Jalila koda taga Alhaji Kabiru ya shiga cikin gidan nan ta kuma kiran yan jarida, tana gama wayar sega motar "yan hisba, tareda yan sanda, sukayiwa gidan dirar mikiya, suka kewaye shi, sannan wasu suka shiga cikin gidan, babban abun kunya da asara shine kama uba da 'ya a gidan karuwai, nan aka tarkata kansu tsaf, Alhaji Kabiru se rantse2 yake, ga wadanda yajiwa ciwo da kwalba, Saleema banda aikin kuka ba abunda takeyi, kan Jeje se zubarda jini yakeyi,'yan sanda suka caje gidan inda akasamu miyagun kwayoyi, da kayan shaye2 kala2, kafin a tafi dasu yan jarida suma suka karaso, suka rufawa motar yansanda baya dan zuwa daukar rahoto, ba karamin farinciki Jalila tayiba, rasa inda zatasa kanta tayi dan murna, batasan lokacin dataji hawaye farinciki nabin fuskarta ba "Allah kai kabani wannan dama, Allah kaikabani nasara ba dabarata da wayona ba, Allah nagode maka, nagode da ni'imarka da kariyarka, Allah kasa sanadiyar shiryuwar bawanka ce tazo" hanyar titi ta nufo tana sauri, yamma tayi sosai, ta tafi gida gida cike da murna da farinciki. Takoma gida tanata murna, tana zuwa ta tarar da sa'ada tazo itada Naja wai a gidan zasu kwana biyu, Jalila ko takansu bata biba, murnarta kawai takeyi, Nana tace "Baby meye sirrin wannan fara'ar da murmushinne haka?" "Nana nima ban saniba ina murna ne kawai" "Hmm kyama fadi gaskiya" "gaskiyar kenan Nana" sukayi dariya gaba daya. Kan kace me Labari yafara yada duniya cewar an kai sumame gidan karuwai, inda aka kamo hada wani uba da 'yarsa tareda yaronsa a gidan" nan da nan zance yafara zaga social media, da sauran kafafan watsa labarai, inda ake ta tir da Allah wadaran akan Alhaji Kabiru. Nana takira Jalila a waya "Jalila Allah yasaki a Aljannah, kinceci rayuwata da sauran rayukan dasu Saleema sukaso lalatawa, Allah yabiyaki da mafificin Alkhairi, Allah yabaki miji nagari me kaunarki" "ba komai Zahra, Nagode sosai nima Allah ya amsa mana bukatunmu" Alhaji Kabiru yashiga cikin matsanancin bakin ciki, yarasa msyake masa dadi, wai yarsa yakama da wanda ya amincewa wato jeje, abun bakincikin ankamoshi da yarsa a gidan karuwai, gashi ba'asan ainihin me yafaru ba amma zance yanata yada duniya, nan yashiga tunanin waima wacece wadda takirashi tace yaje gidanta ne, in akajima ya tuna yadda yaga yarsa da jeje, se ransa yakara baci, ya kalli Jeje yace "Jabir (shine ainihin sunan jeje) Allah ya isa tsakanina da kai, duk halaccin danayi maka a rayuwa amma ka lalata min yarinya" "dama can lalatacciyace, kuma halaccin dakayimin aiba kyauta kaimin ba aiki nake maka, shekaru nawa nayi inamaka bauta" "Au hakama zakace ko, zamu fita ai zakaga abunda zanyi maka, kasanni kasan halina" Jeje ya kalleshi "kabari kaga munfita lafiya tukuna, aisena bari munfita lafiya zaka samu damar yimin wani abu, dan haka sena fadi komai" zazzaro ido Alhaji Kabiru yayi, "me kake nufine wai?" inbaka ganeba seka bari sena aiwatar zaka gane".    Duk yadda su Sa'ada sukaso bakantawa Jalila rai bata kulasu ba dan karma su bata mata farincikinta, tabar musu dakin takoma na halima ta kwana a can, tun sassafe tai salla, sukayi aikace2 dazasuyi itada halima a cikin gidan, sannan ta tafi gidansu Jalal itada Halima, tunda Ilham tai arba da Jalila takejin kaman ta dau wuka ta kasheta, suka gaisa da Mummy ta nuna mata kitchen Jalila suka shiga suka fara abunda yakamata, aka jima Nana itama tabaro wasu sa'ada gidan ta tabiyosu Jalila a ranar suka hada snacks din dayakamata, sukabar aikin dabasu gama ba zuwa gobe, kafin bakin suzo sesu karasa, Nana da halima suka koma gida, Jalila ta tsaya tana jarasa gyara kitchen din, Jalal ya shigo da katon kwando cike da fruit ya ajiye yai waje abunsa, ta zauna ta shiryasu a fridge sannan ta tafi. Wahsegari da safe Jalila ta dawo, bata tashi halima ba daga bacci saboda taga alamar tagaji sosai jiya, ta dama kunun gyada, ta dibi nata a dan karamin flask ta tafi dashi. Jalila tayi busy sosai a kitchen, dan bata samu ko karyawa tayi ba, dogon wandone a jikinta da rigarta har gwiwa me dogon hannu, ta daure kanta da dankwali, amma karshen gashin ta yafito, taji alamun ana kallonta, bata waigaba ta basar tacigaba da abunda take, cikin kitchen din ya karaso ba sallama ba komai yakama dube2, bata kulashiba tacigaba da aikinta ya jijjiga tea flask bakomai a ciki, tsaki yayi ya bude fridge yana kallon arrangement din datayiwa fruits din, still ya rufe fridge din, Jalila ta fuskanci yunwa yakeji, ta kalleshi "wai meyene?" "bansaniba" "karka sani din" yaje ya duba kettle yaga akwai ruwan zafi a ciki, ya dakko ya zuba bako lipton, ya dakko madara da sugar yana kokarin antayawa, ita Jalila ma dariya yabata, ta dakko flask ta zuba masa kunun gyada a cup, ta zubamasa samosa, ta mika masa, bako kunya ya karbe, yanemi guri kan kujera a kitchen din yai zamansa yafara ci, itakuma tacigaba da aikinta, wayarta tafara ringing, sunan sweet hanny shine akan screen din wayar, tadaga wayar tasa a kunnenta "Hello sisyna ya kike" hanan tace "Hmm ba fada meyakawo gaba Baby, kin yadani, kin manta dani ko?" "A'a hanan ban manta dake ba, ko zan manta komai bazan manta da yar uwata ba" "Anya kuwa Jalila? Kina guduna saboda inason Jawwad ko? Karki damu hakan baze shafi zumuncinmu ba, amma yakamata kikawomin ziyara, in duni6da gaskiya bekamata ace tunda kikabar kaduna baki kuma zuwa ba" Kwalla ce ta taru a idon Jalila, cikin muryar kuka Jalila tace "Hanan bazan iya zuwa kaduna, bazan iya zuwa anguwarmu ba, Hanan hakan ze tayarmin da hankali, inzo unguwarmu ummi bata nan, bansan inda take ba, kiyi hakuri Hanan, amma kina raina daks da sauran mutane masu mahimmanci danake dasu a garin" takarasa maganar hawaye nabin idonta, "Jalila na fuskanci abunda yake damunki, inajin damuwarki a zuciyata, kiyi hakuri mucigaba da addu'a kinji, kidena kuka" gyada kai Jalila tayi kaman tana gaban Hanan, sannan tace "Nagode Hanan, kigaida kowa da kowa mussaman babana" "zasuji Insha Allah yar baba" ta kashe wayar, duk kokarin da Jalila tayi ta cigaba da aikinta amma takasa, tanata kokarin daurewa ta hadiye kukanta amma takasa hawaye ketabin idanunta, sosai Jalal yaji tausayinta ya kamashi, yaji inama ace shima zeji wannan kaunar da shaukin da y'aya sukeji game da iyayensu mata, har fuskar Jalila tayi ja. Tasowa yayi yazo bayanta ya tsaya yana kallon ta, dagowa tayi ta kalleshi suka hada ido, "Meyasa bazaki karbi kaddara a duk yadda tazo miki ba, memakon kiyi addu'a amma kike kuka, hakan bekamata ba, kizama jaruma mana" dauke kai tayi takuma fashewa da kuka wannaan karon hada sheshsheka, sunkuyowa yayi daf da ita a hankali yace, "Ummi tana raye, kuma zaki ganta very soon, jikina yana bani" da sauri ta kalleshi ya jinjina mata kai, yai mata alama  tasa hannu ta goge hawayenta, "da mutum yana da ikon sauya kaddararsa, kokuma kuka yana canza wani abu, da mutane dayawa sun fita daga matsalolin dasuke ciki, wani lokacin mukanyi kuka ne don samun sassauci a cikin damuwar da take damunmu, amma ta wata fuskar kukan yana karamana matsala ne da damuwa, ummi tayi rayuwa me tsayi ba tareda yan uwanta ba, kuma hakan besa wani abu yafaru da itaba, dan haka kema addu'a zakiyi kicigaba da hakuri " yana gama fadin hakan ya mike ya kai hannu ya juye sauran kunun gyadan nan ya juya ya fice, Jalila tabi bayansa da kallo, tai ajiyar zuciya tacigaba da aikinta jikinta a sanyaye. Wajen karfe shadaya na rana mummy ta shigo tanayiwa Jalila sannu da aiki, Jalila tace yawwa" Mummy barka da safiya" "Yawwa barka ya aikin?" "lafiya kalau Mummy nakusa kammalawa ma" "to masha Allah" Bayan Mummy tafita ba dadewa Jalila taje gida ta dakko wasu spices ta dawo, ta windowa kitchen dake harabar gidan taga Ilham tana zukar wani abu a kwalba da syringe tana tsirawa ruwan a jikin wani jan Apple, Jalila ta tsaya tana kallonta, tana gamawa ta maida shi cikin fridge ta rufe ta fita ba tareda ta lura Jalila ta ganta ba.  Se wajen karfen daya Jalila ta karasa girkin Abincin tareda taimakon Nana data biyota daga baya. Sun kammala komai sun gyara kitchen din kaman ba'ayi amfani dashi ba, suka fito itada Nana, daddy yana palour "Sannu da aiki yaran kirki, nasaku wahala ko?" Jalila tai murmushi "ba wani wahala daddy mun kammala komai ma" "Masha Allah, Allah yayi Albarka" Nana tace "Ameen daddy, amma ni gaskiya nagaji" "Aidama ke lazy ce Nana" sukayi dariya, daddy yace "Jalila amma in sunzo aizakizo kiga yan uwan yayanki ko?" murmushi tayi ta jinjina kai, daga nan suka fita suka tafi gida. Jalila ta gaji dan haka wanka tayi, Naja tana kan gadon ta baje, Jalila ta haye gadon ta kwanta itama, Naja ta kalli Jalila "malama meye haka? Bakiga nice a kwance agurin ba" "Eh banganiba, babu a house ko?" A fusace Naja tace "amma kinsan karyane kicemin babau a house ko" "in akwai a house ai dabakiyi wannan shirmen ba, kodayake aiba mamaki a sha rashin hankalin nono" "kut me kike nufi?" "inkika bari, nakuma bude baki da nufin mayar miki da martani sekinyi kuka, dan haka kiyi abunda ya dameki bacci zanyi" Jalila ta kwanta abunta, tabar Naja tana kallonta, can cikin bacci Jalila taji Nana tana cewa "Ke Jalila ki tashi, bakinku sunzo fa?" A hankali Jalila ta bude ido "wane bakin kuma?" "Bakinsu Jalal mana, ki tashi yau zakiga yan uwansu, masu irin hancinsa" Jalila takuma juyawa akan gadon tace "ni dan Allah ki kyaleni mana" "Ke Jalila kinada matsala wallahi, dan Allah ki tashi muje, akwai wanda nakeson gani a cikinsu, inajin kunya inje ni kadai" Jalila ta bude ido ta kalli Nana, "ikon Allah, Nana kinda damuwa, wallahi nikam ki kyaleni" Nana tace "kar Allah yasa kije" "eh bazaniba" har Jalila tafara bacci, ta tuno Apple din nan, kartaje Ilham takuma zuba wani abu, zumbur ta mike, ta bude drower tasaka kayanta, tafito da sauri ta tafi gidansu Jalal, harabar gidan duk motoci, tundaga varrender take jiyo hayaniyar mutane, ta bude kofar palour a hankali, dayawansu kamansu daya da Daddy Jalal, duk haka suke da dogon hanci sosai aranta tace "tab wannan ko bata sukayi da wannan hancin nasu za'a ganesu" se yare sukeyi, ga Jawwad ma a cikinsu, shima se yaren ake dashi, tanaji daya yana tsokanar Nana, da wata irin hausarsa yace "gaskiya Nana kin girma kin ganki kuwa, waike yan mata tunoki nake lokacin kina dan karamarki" Nana ta dan zumbura baki "kajika Kaima ai da bahaka kake ba, ji yadda ka wani tara gemu, waikai dole ka girma" dariya sukayi gaba daya, daddy yai murmushi yace "Nana yaushe zaki dena surutu ne, bakinki baya mutuwa" kallo daya zakayiwa Jalal kasan yana cikin farinciki, fara'a yake sosai, 'yan uwansa duk nutsatstsu, amma shi yafita daban a cikinsu dan gashin kansa ba kyan gani, ga kallo daya zakayi masa kasan lips dinsa yana shaye2, setaji hakan ba dadi, a hankali ta sulale ta shiga kitchen ba wanda ya ganta, Tana tsaye a kitchen din Ilham ta shigo taci kwalliya sosai, gashi tasa wani turare me karfi, wanda sam bashida dadi, wani banzan kallo taiwa Jalila sama da kasa a wulakance, "Aikin banza jaraba da maita, tunda kingama abunda akasaki aisekikoma inda kika fito ko, ko yanzunma wani munafuncin zakiyi, shine kika dawo" "Aini bana munafunci kaina tsaye nake abunda nakeso, Aikinne ban gama ba, nazo nakarasa wanda aikin da nakarasa yafi kowanne mahimmanci, na bata aikin wasu dan gyara nawa, kamar yadda nasha fada muddin aikin wani yashigo nawa, sena bata shi" kallon Jalila tayi cike da mamaki wannan karon kuma me take nufine, kwafa Ilham tayi tawuce ta  fara daukar kayan Abinci tana fita dasu, alhalin lokacin da Jalila take aikinta ko dauraye spoon Ilham bata tayata ba, Jalila ta tsaya tana kallonta tagama fita da kayam Abincin, ta dawo ta bude fridge tafara jera fruit a tray, tana kallon Ilham ta dakko Apple din nan tai masa guri na musamman akan tray din, tayi waje, Jalila tabiyo bayanta ta tsaya a window tana kallonsu, Ilham sewani iyayi take tana kwarkwasa, Jalila tayi mamaki da bataga Mummy ta fito ba, bakin su biyar ne maza hudu se mata uku, duk daka gansu kasan yan uwan daddy ne, Ilham cikin iyayi tace "bari kufara da fruits kafin kuci Abincin ko" cikin bakin daya shima me matukar kama da Jalal yace "Eh hakane gaskiyanki Ilham" tafara binsu daya bayan daya tana basu Apple, Jalila tana kallonta ta dauki Apple din nan ta mikawa Jalal, ya mika hannu ya karba shima kamar kowa dayake Apple yana daga cikin favorite fruit din Jalal. Jalila tana ganin irin kallon da Ilham kewa Jalal, Ilham na ganin Jalal yaci Apple din nan tafara murmushi. dawowa Ilham tayi da tray din ta ajiye a kitchen, har zata fita Jalila tace "bar murna karenki yakama zaki kinyi mantuwa" waigowa Ilham tayi tana kallonta, kawai taga Jalila tana jefa Apple sama tana cafewa "Ilham kinsaba lamba, saboda na canza Apple din" a razane ta kalli Jalila, Jalila ta karaso gaban Ilham, ta kamo hannunta ta doramata Apple din, duba da kyau wannan shine Apple din dakika zubawa magani ba wanda yaci ba, ko baki gayamin ba nasan abunda kika zubawa Apple din nan na asiri ne akan Jalal, Ilham shi so ba'asiyan sa kuma sihiri be isa yabaki soyayya ba koya soki na lokaci kadanne, in abun ya barshi shikenan, yanzu meye ribarki a cikin cutar da dan uwanki? " .. I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 ..🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE 1️⃣5️⃣ 68_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ A razane Ilham ta cewa Jalila " Ubanwa ya gayamiki wani abu na zuba a ciki, ke bayan munafunci hada sharri a lamarin naki, ai na dade da gano sonshi kikeyi, kalleki a haka kaman ta Allah amma tsabar rashin tsoron Allah da idona na ganki kina rungume Jalal, se anyi magana kice aike basanshi kike ba, in ba sonshi kike ba uban me ya kaiki jikinsa, meye naki nasamun ido iyee, munafuka kawai" Jalila tai murmushi tace "inkika daga murya kanki zaki tonawa Asiri baniba, danni ba ruwana, sannan dan na rungume Jalal, damace nasamu kema kije ya rungumeki mana inkincika mace" Jalila takarasa maganar tana dariya, tacigaba da cewa "Ilham tsabar mugun abunkine yasa kullum idonki yake ganemiki abunda ze hanaki sukuni tsakanina da dan uwanki, amma ko makamancin so na wancan abun babu araina fatan kin gane, for now Jalal beci wannan tsafin ba sekije kiyi wani shirin kuma" tana gama fadin haka bata jira me Ilham zatace ba ta juya zata fita, Ilham tasa hannu ta janyota, ta waigo sukayi ido hudu, Ilham kaman ta fashe da kuka tace "wannan karon kinyi Nasara, amma ki saurari abunda ze biyo baya nan gaba" "Idan har Allah shine abun dogaron mutum to a koda yaushe nasara tasace, dan haka inaji ranki, sannan kisani bani kadai yakamata kigabaya ba, Hanna ma tana nan tana target akanki, sekin kara tunani kin rarraba hankalinki, dan hanna bazata barki ba," Jalila ta fizge hannunta tai gaba abunta.  Ilham taji wasu hawaye na bacin rai suna bin idonta Allah yahadata da Jaraba, mezatayiwa Jalila ta huce ne? Gani take da za'abata wuka seta kasheta, ita hannah ba barazanace a gurinta ba Jalila tafi tsayamata a rai, da Jalal yaci abun nan da yanzu anmawo karshen komai, amma Jalila ta wargaza komai, ajiyar zuciya Ilham tayi "dole in sanar da umma abunda ke faruwa, na dauka zan iya shawo kan lamarin nan amma abun yafi karfina" Jalila kam takuma silalewa ta fice ba tareda kowa ya ganta ba ta tafi gida. Koda Jalila takoma gida, sabgoginta ta shigayi, amma takan tuna nasihar da Jalal yaimata dazu, babban abunda yabata mamaki yace jikinsa yana bashi ummi tana raye fatanta Allah yasa hakane ummi tana raye, har akayi sallar isha'i sannan Nana ta dawo gida, da fara'arta ta tafi gurin Jalila ta zauna, Jalila ta kalleta "se yanzu kika dawoko? Dan kinga Abba bayanan" "Aiko yana nan baze hananiba, Allah sarki Yaya Jalal se murna yake yaga yan uwansa" "Hmm Nana ai dan uwa dadi ne dashi, sedai abun tausayin naga yan uwannasa duk nutsatsu amma banda shi" "ya akayi kika gansu bayan kina gida?" "naje naga palourn a cike bazan iya wucewa ba dan haka na dawo" Nana ta dan girgigiza kai "bari kawai Jalila, Jalal abun tausayi ne, Allah ya kyauta kawai" daga nan Nana bata kuma cewa komai ba ta tashi, ta bar dakin Jalila ta dauki wayarta ta hau internet, batun abunda yafaru da Alhaji Kabiru ya zaga duniya, hada masu kara abunda ba'ayiba, yan makarantarsu Jalila kuwa se murna suke da kama su Sameera da akayi suke, dama dayawa suna jin haushin su Saleema, sabida yadda suka gallabi makarantar, ga bata yaran mutane dasuke, se zancen ake tareda Allah wadaran da suu saleema ace ankamaka kaida mahifinka a gidan karuwai, Jalila tace dole taje station din da aka kai su Alhaji Kabiru, kuma yanzu amfanin Yallabai Sulaiman yazo. Don kuwa setayi me yuwuwa ta tabattar da ta kawo karshen Jeje da Alhaji Kabiru, taji dadi da Allah yasa aka kama da jeje a wannan kamen, Dagashi har Alhaji Kabiru sesunyi danasanin shiga gonarta, Tagama abunda takeyi tana shirin kwanciya, sa'ada tace "ya haja? Ba dakin halima zakije ki kwana ba ai dakin zaki barmana malama, mu a ina zamu kwanta" shiru Jalila taimata tana kokarin jan bargo, Naja tasa hannu ta rike bargon "malama maganafa ake miki, ki tashi ki bamu guri kitafi dakin yan aiki ku kwana a can dan bazamu kwana dake a daki daya ba" mikewa Jalila tayi a zaune, ta kalli su Naja "da Abba yake gina gidan nan gudunmuwar nawa ubanku ya bayar" bude baki sa'ada tayi "ke karki sake ki zagarmana uba wallahi, dan kika zagi ubanmu semunyi kasa2 dake" "inna zage shi mekuka isa kuyi, aiba karya nayiba, in ya kawo gudunmuwa lokacin da ake gina gidan nan ku fadi nawane a biyaku, kudena min gori, inkuma bebada ko sisi ba, kar shashar data kara cewa inje in kwana a dakin me aiki, tunda ba da gudunmuwar tsoho a gina gidan alfarma akemuku, koni nawa iyayen ba mutane bane da kuke zaginsu ? Inkun ji haushi a daren nan kukoma gidan naku iyayen, kuma wallahi duk wadda takuma yimin maganar banza sena gayamata maganar dabazata iya bacci ba" ta juya ta kwanta akan pillow tana murmushi. Haka suka hakura suka tafi dakin Maama suka kwana a can, dan Jalila ba karamin taurin kai gareta ba. Hannah duk ta rame sabida dorawa kanta masifar son Jalal dakuma kishinsa, tayiwa kanta alkawarin muddin bata aureshiba sedai ayi biyu babu, dan in har tana raye bazata bari ya auri wata mace ya zauna da ita ba, kodai ya aureta cikin dadin rai, kokuma ya aureta kota tsiya, yanzu yazma dole ta hada kai da jeje, ta yaudareshi su hada kai taga bayan Ilham, Ita Jalila nata me saukine, Ilham ce tafi tsayamata a rai, ta dakko wayarta taita kiran lambar Jeje, amma taki shiga, tayi2 harta gaji ta hakura, da niyyar gobe taje ta sameshi, (bata san ankama shi ba) Da sassafe wayar Jalila tafara ringing, cikin magagin bacci ta kai hannu ta daga wayar, muryar Jawwad taji "Am sorry baby na tasheki ko?" ya fada a hankali "bakomai Yayana, fatan ka tashi lafiya" "Lafiya kalau, hope kinyi bacci me dadi?" "Alhamdilillah yayana" "yawwa baby wata alfarma nake nema a gurinki" "fadi kanka tsaye komenene indai zan iya dole ayi shi" "Yawwa baby, kinga a gidansu Jalal na kwana muna tareda su mahmud, gari ya waye babu alamar Mummy zata basu breakfast, na shiga cikin gidan yanzun naga ta kulle kitchen dinta, daddy kuma ya fita kiran gaggawa da akayi masa da asuba ya tafi Abuja, to banason Jalal yasani, dan Allah ki dafa abunda yasamu abawa bakin nan" mamakine ya cika Jalila to meyasa Mummy zatayi haka, meye ma'anar hakan datayi, ajiyar zuciya Jalila tayi "bakomai karka damu, zan hada abunda ya sawwaka inkawo" "Yawwa Baby, Allah yayi miki Albarka" "Ameen bloody" gajiyar jiya bata saki Jalila ba. ta tashi ta tafi kitchen ta dora girki, ba a dade ba Nana ta fito taji karar kwanuka a kitchen ta leka setaga Jalila nata fama a kitchen "Jalila kekam meyasa ba kyason hutawa rankine, da sassafen nan kowa na bacci kekina kokawa da kwanuka, gashi gajiyar jiyama bata sakeki ba" Jalila ta gayamata duk abunda yafaru, Jinjina kai Nana tayi tace "Tabdijan itakam har yanzu Mummy abu baya wucewa a gurinta, to Allah ya kyauta" Da mamaki Jalila tace "meye baya wucewa a gurinta? " Nana tace "manta kawai, bari inzo in tayaki, bekamata kiyi aikin keka dai ba" Nana ta tayata suka karasa aikin, duk yadda Jalila taso Nana tagayamata wani abu, amma Nana taki ta basar da zancen. Maama tafito kitchen zata dauki plate,  Jalila tace "Maama ina kwana" "lafiya" shine amsar data bawa Jalila, ta kallesu "wai wane irin girkine da har yanzu ba'a gama breakfast ba" Nana tace "Yaya Jawwad ne yasamu aiki, mummy tahana bakinsu Abincin safe" dan zare ido Maama tayi "Are you serious, ita har yanzu bata dena wannan abunba? Itama dai Mummy by now yakamata ace komai ya wuce, kodan danta, amma Ai shikenan" Se Karfe tara na safe Suka gama aikin Abincin, suka dauka suka kai gidansu Jalal, a palour suka tarar da wata mata me fara'a, tana kama da daddyn Jalal sosai, zatayi shekara talatin da biyu,  Jalila bata santa ba amma dagani tasan yar uwar daddy ce, Nana ta santa, suka gaisheta, ta amsa musu cikin fara'a, suka tsaya suna hira da Nana,  Jalila bata da saurin sabo, gashi bakomai take ganewa a hausar matar ba, dan haka Jalila ta mike takoma gida ta dakko sauran kayan, tana dawowa tundaga harabar gidan tafara jiyo hargowar Jalal kaman a filin yaki, a ranta tace "jarababbe Allah yayi dare gari ya waye a gaban mutanen ma baze dena wannan jarabar ba" tana shiga palourn ta ganshi a tsaye a gaban Mummy idonsa jawur yana surfa masifa, wata mekama da wadda suka tarar a palour dazu tana rikeshi tana masa magana da yarensu, cikin fushi yake kallon Mummya yana cewa "Wace irin macece ke mara Adalci, ai Abincin banakibane ba dazaki hana 'yan uwan babana ci, kodaga gidanku aka kawoshi, amma kinsan ki diba har kibawa wanda basu kamata ba, akanme dan uwansu ne yake nema yakawo zaki hanasu Abinci, ke wace irin mara adalcicene meyasa kika fiye sonkanki, su basuyi fushi dakeba seke zakiyi dasu, why? Mummy why? Wace irin zuciya ce dake haka" Mummy tace "Jalal nikake ciwa mutunci agaban mutane, kake zagina a gaban mutanen daba kaunata suke ba, nikake gayawa wannan miyagun maganganun, uwarkace nifa nikake ciwa mutunci haka" takarasa maganar tana hawaye, jiyo hargowane yasa Ilham ta fito da sauri daga dakinta, don ganin meyake faruwa, ta tarar Jalal yanata baka'i "Eh nayi din, dan sunfiye minke a matsayin uwata, haifata kawai kikayi amma sam bakisauke hakkinki na uwaba meyasa kikazamo uwa a gareni, a rayuwata sam banyi dacen uwaba, kowani da yana farinciki yana murna in aka ambaci uwassa amma bandani Jalal, baruwanki da ya rayuwata zata kkasance se cikar miyagun burikanki sukikasa a gaba, har yau kinkasa yin nadama akan rayuwar da nakeyi saboda rashin kulawa irin taki, dakuma laifukan dakika aikata a rayuwarki, wallahi mahaifina da danginsa sun fiyemin ke wallahi" cike da masifa da bacin rai Jalila tafara magana "ABDUL JALAL Kaji kunya wallahi, agaban mutane kake gayawa mamanka wannan maganar, ba ladabi babu da'a ba komai, kome tayi maka tunda tariga takawoka duniya tagama yimaka komai, kalli 'yan uwanka dasukazo kowa a nutse tunda ga fuskarsu shigarsu da kamalarsu amma banda kai, ta yaya kake tunanin zaka cigaba a rayuwa da wannan wulakancin da kakewa mahaifiyarka,kana tozartata kana nunawa duniya kai baka da tarbiyya, tirr da hali irin naka Jalal, Allah ya shiryeka inme shiryuwa ne, ba yadda za'ayi kaga haske ko cigaba a rayuwarka alhalin kana tozarta mahifiyarka, tir da halinka wallahi" A mugun fusace ya juyo, ya kalleta ido cikin ido, kan Jalila yayo gadan2, itakuma taki motsawa balle ta gudu, kafin ya karaso gurinta, matar dazu dasuka tarar a palour tashiga tsakaninsa da Jalila, tana girgizamasa kai "Allah ya huci zuciyarka, kayi hakuri, ka kyaleta" Yare ya canza yana magana,ya cigaba da tunkaro su idonsa jawur cike da masifa, tareda kwalla, ya nuna Jalila yanawa matar magana da yarensu, a cikin maganar da Jalal yake taji ya ambaci sunanta, JALILA!!! Abunda tunda take bata tabajiba, sedai yace mata ke, koyace wannan yarinyar kokuma yacewa Jawwad kanwarka, Matar tacigaba da bashi hakuri da yarensu, ta kalli dayan tace "mahmud jashi kufita, kabashi hakuri" Mummy tuni tabar palourn yayinda Ilham agabanta akayi komai, Nana ma rasa bakin magana tayi, Matar nan taja hannun Jalila suka fita daga palourn, bayan gidan taja Jalila ta zaunar da ita akan wasu fararen kujeru, sannan itama ta zauna ta kalli Jalila tace "Dama kece Jalila?" Cike da mamaki Jalila ta kalleta "Eh nice, ya akayi kika sanni?" Ajiyar zuciya matar tayi tareda murmushi, "kece baki sammu ba, amma mu duk munsanki ai" "Amma naga bamu taba haduwa ba, ya akayi kuka sanni" "ba abun mamaki baneba Takwararmu, duk family dinmu munsanki, amma meyasa kikewa Jalal hakane?" da mamaki Jalila ta kalleta "me nayi masa kuma?" "duk lokacin dakika bata masa rai seya gayamun, kina yawan sakashi fushi meyasa?" dan dauke kanta Jalila tayi tace "Anty Jalal baya kyautawa abunda yakeyi, kullum yana jefa rayuwarsa a cikin hatsari, ace mutum yakai munzali kaman Jalal amma ace kullum cikin sa'insa yake da mahifiyarsa bekamata ace yana daga mata murya haka ba? Banda sauran abubuwa dayake dabasu dace ba, kema kinsani, amma meyasa bakwa zuwa inda yake maybe dakuna zuwa da ganinku zesa yarage wasu abubuwan da yakeyi, rayuwarsa ta gurbace dayawa, baya ganin girman kowa, shaye2 shine babban abokin rayuwar Jalal, be damu da ibada ba sam, ko abokan kirki bashida su sena banza, yayi shaye2 a club yayi a gida, kuma ko a gaban waye, baya ubangiji, da sauran abubuwa marasa dadi dayake aikatawa" Ajiyar zuciya matar tayi "Jalila tabbas maganarki gaskiyane, Jalal baya kyautawa duk rayuwarsa ta gurbace, amma meyasa kika damu akansa haka?" Jalila tace "nima bansaniba, kawai dai soyayyar da Jawwad yakemasa ne, dakuma kokarin dayake dan ganin Jalal ya shiryu yasa banajin dadin abunda Jakal yakeyi"? "kin taba tunanin meyasa babu soyayya da tausayi na da da uwa a tsakanin Jalal da mahifiyarsa?" "eh nayi wannan tunanin, amma nakasa samun amsa, nayi2 Jawwad yagaymin amma yaki" "meyasa baki tambayi Jalal dinba?" zare ido Jalila tayi "taya zan tambayeshi nida muke fada, ya shakeni a banza" murmushi tayi "baze shakeki ba Jalila" Jalila ta kalleta "tab lallai wallahi ze iya shakeni, har dukana yakeyi" matar tayi murmushi "Jawwad yacika dan uwa nagari, daya boye sirrin Jalal, dukda a yau zamu bar kano, zamu koma garinmu, tunda matar gidan bata son zuwanmu, amma yanzu a takaice zan baki labarin waye Jalal, sannan ya ingaya miki ya akayi muka sanki, idan nabaki labarin sekiyi masa alkalanci" Please pray for me zanfara exams, dana kammala zan cigaba da posting insha Allah Comments nakeso ba sticker ba kokuma just thanks Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 .🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE 16️⃣ 69_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ WANENE ABDUL JALAL???!!!!! Khadija munir shine cikakken sunan mahaifiyar Jalal, malam munir shine mahaifinta suna zaune a unguwar dorayi dake cikin garin kano, malam munir malamin makarantar secondary ne, sannan yana yan sana'oinsa domin rufawa Iyalansa asiri, yanada mata uku, hauwa itace uwargida, se sadiya itace matarsa ta biyu, da zulaihat itace matarsa ta uku, yanada yara goma sha uku, khadija 'yace ga sadiya matar malam munir ta biyu, khadija su ukune agurin mahaifiyarsu, itada yayyenta maza biyu, Abubakar da Aliyu, itace yarinya ta tara a gurin mahaifinsu, khadija tana da kyau daidai gwargwado, wanda har wasu suke cewa duk tafi yaran gidan kyau, dukda kasancewar ta ba fara tas ba amma tanada kyau, khadija yarinyace mara kunya, bata dagawa kowa kafa, duk wanda yayi mata duk yarintarsa duk tsufansa zeta cimasa zarafi babu ruwanta, tun yayyenta na kamata su daka intayi rashin kunya harsuka gaji suka kyaleta, saboda rashin mutuncin ta bata bar kowaba ciki harda matan babanta da yayyenta, mahaifiyarta ta sangarta ta kasancewarta ita kadaice yarinyarta mace, duk wanda ya daki khadija ranar se anyi tashin hankali da mahaifiyarta, har kirari takewa khadija cewa "ni 'yata matar manyace, se wanda yaci yatada kai zan bawa, dan khadija na ba kalar talakawa bace" hakan yasa abun yafara tasiri a zuciyar khadija tun tana yarinya, takejin cewa kota isa aure seta samu me kudi zatayi aure idan kuwa bata samu me kudiba, gara ta tsunduma ita tanemi kudin dan bazata iya auren talaka ba, kuma batason rayuwar wahala. indai khadija nason abu, kaya kona uban waye koda kudi ko a bashi, mahaifiyar khadija zata siyamata su. Saudat kanwace ga khadija sakuwarta ce khadija tabata shekara daya da rabi, ita saudat 'yace ga zulaihat amaryar malam munir, itace ta biyu a dakinsu, wani lokacin suna matukar shiri ita da khadija saboda halinsu yazo daya dukkaninsu tsagerune, Sedai Khadija tadama saudat ta shanye a tsageranci, dukda wannan shiri dasukeyi baya hana in tsiyar khadija ta motsa tayiwa babar saudat rashin mutunci a hadu aita masifa a gidan nan, makaranta da yan unguwa babu wanda besan halinta ba, karamin aikintane ta zagi malami agaban dalibai, in an koreta mamanta seta canza mata makaranta, dama islamiyya tuni ta dena zuwa, a cewarta tunda tasamu na salla shikenan, dan bazata jure wannan masu gemun kaman brush suna dukan kyakyawar fatarta da fatar bunsuru ba, abun dukan doki, malam munir yayi iyayinsa gurin ganin khadija ta nutsu amma abu yaki yuwuwa, Abinci se wanda taga dama zataci, sutura se wadda takeso zata saka, wani wanki da guga almajiri uwatta take biya yayiwa khadija, haka dai rayuwar khadija ta tashi a mugun sangarce, ga rashin tarbiyya. Tun tana jss2 tafara samari, inda a nan ne ta hadu da saurayinta Kabir, Kabir yana matukar sonta kaman yayi hauka, Kabir marayane, mahaifinsa ya rasu, dagashi se mamansa da kannensa mata biyu, shikadaine namiji gashi mahaifinsa bebarmusu wani abun kirkiba se gidan dasuke ciki, seyaje yayi aikin wahala yake samo abunda zasuci yake biyan kudin makarantarsu, tunda yafara soyayya da khadija abubuwa suka fara tabarbarewa saboda yawan bani2, yazamana da kyar yake iya morawa mahaifiyarsa da kannensa wani abu sedai yayiwa khadija haka yadinga dawainiya harta shiga sss, nan manyan mutane suka dinga fitowa suna sonta, duk cikin manemanta babu wanda yayi mata saboda ita burinta ta auri, namiji kyakyawan gaske sannan wanda ya tada kai da naira, sannan tanada burin tazaga duniya, tayi ilimi me zurfi a kasashen waje, yadda zata goga kafada da manyan mata a kasar Nigeria dama nahiyar Africa gaba daya, shiyasa duk wanda yazo indai yanada kudi zata wankeshi son ranta sannan ta sallemeshi, dan har yanzu bataga dai dai da itaba, malam munir yayi iya yinsa dayimata nasiha itada yar uwatta saudat amma abu ya gagara, ana cikin wannan haline Allah yayiwa malam munir rasuwa, mutane sunji mutuwarsa saboda mutumin kirki ne kwarai dagaske, bayan an gama makoki khadija tacigaba da tsiyarta daga inda ta tsaya, ganinda Kabir yayi masu kudi na neman aurenta yasa kara zage damtse, dayasamu kudi ko anmusu albashi dayake yasamu aiki a wani kamfani, seyaje ya kashewa khadija su, har rawar jiki yake wasu kudin sushigo yakuma kaimata, alhalin gidansu wataran se a kwana biyu ba a dora tukunya ba, se ayi term biyu ana korar kannensa saboda kudin PTA, amma baze iya basu ba sedai khadija. Mahifiyar Kabir ta zubda hawaye ba'adadi amma bayadda ta iya da wannan hali na ko inkula da danta Kabir yake musu itada kannensa, sam takasa gane kansa. In khadija ta dau wanka ta taho seka dauka wata yar hamshakin Attajiri ce, saboda 'yar kwalisa ce ga karya data dorawa kanta, khadija tayi candy amma taki cigaba da makaranta tace seta auri mekudi zataje abroad tacigaba da karatu, sabida abun kunyane a ce nan gaba intazama wata a Nigeria ace za' ayi interview da ita tace a Nigeria tayi karatu. Yauma yammace taci uban ado tana taku kamar tana taka kwai, taji anamata horn da babur amma tayi banza taki matsawa, mutumin yadinga horn amma taki ko daga kai balle tabashi hanya ya wuce, parking yayi ya kalleta yace "baiwar Allah kokurma ce ne? Inata horn kibani hanya zan wuce amma kinyi banza" wani mugun kallo tayi masa, "idanni kurma ce kaikuma mara hankali ba" zaro ido mutumin yayi saboda yasan a haife ya haifi wannaan yarinyar "nine mara hankalin yarinya?" "kwarai kaine mara hankali, ya za'ayi ina tafiya zaka isheni da horn da wannan rubabben gwangwanin naka, kana nema ka kashemin dodon kunnena, aida seka tsaya in wuce, kokuma ka canza hanya, tunda bakai ka gina hanyar ba ai" "Amma kina ganin ya dace ki kirani mara hankali da girmana da komai" Cikin tsiwa tace "to semenene? Ai abun rashin hankalin kayi" "shikenan in abunda kikayimin dai2 ne za'ayiwa mahaifinki kiji inda dadi" "to ya mutu wata uku dasuka wuce, inkuma kabarin za'abishi ayi masa se inji, aikin banza mutane suyita abu kaman wasu yan kwaya" Cikin rawar murya yace "nine kaman dan kwayan"? "kaimana da dawani nake, wayasanima ko ita kaje kasha, kake nema kayimin akuya nonsense" tayi gaba abunta, mutumin nan seda ya zubda hawaye, ya kunna babur dinsa yazo daidai saitin khadija ya tsaya ya kalleta yace "Insha Allah sekin haifi dan kwaya, sekuma ya miki abunda kikayimin" "kai kasani, koma kwayar zan haifa, shirmen banza kawai, adai dinga kula, da irin kwayar daza'asha in bahakaba a kare a gidan mahaukata" bataji mezece ba tayi tafiyarta. A fusace ta shiga gida tana ta mita, saudat na tsakar gida tana danna waya, ta dago ta kalli khadija tace "Ahh kaga manyan mata a gidan Kabir ya akayine, waya taboki kike mita?" A wulakance khadija ta kalli saudat, "waye kuma kabir, karki kara hadani da wannam matsiyacin, a tunaninki mace mai daraja kamarni zan iya auren wani Kabir, tausayinsa kawai nakeji wanke dan banza zangama, da zarar nasamu my dream hubby inyi dumping sha3 aside inyi aurena, idan na auri wannan fakirin ta ina burina ze cika" murmushi saudat tayi, "angaisheki matar manya, banga laifinkiba, nima ina bayanki wayakeso  talauci ai kudi kawai alaji, amma meya bata miki rai haka?" Nan khadija ta gayamata abunda yahadata da wannan mutumin, saudat tace "ke manta dashi, kinsan irin wannan mutanen, basa raina abun magana" "aikuwa yajawa kansa dan sedana masa rashin mutunci naji dadi a raina" sukayi shewa gaba daya, uwar gidan malam munir tana jinsu tace "khadija baki kyauta ba abunda kikayi" Khadija ta murguda baki "ai dama banyi dan in kyauta ba, kinganni ba ruwana, da kusanci, ko girman mutum ana mun nake ramawa ehee" "to Allah ya shirya" "Ameen ya shirya abunda yafi hakama". Haka rayuwa tacigaba da tafiya, khadija tana gwara kan samari, yau ta wanke wannan gobe ta wanke wancan, ba wanda yake da ikon yin Magana, gefe dan wahalarta wato kabeer yanata faman wahalta mata, uwarsa da kannensa kuma ko oho.     Yau ake sa ran za'a kawo kudin auren kanwarsu khadija, wato surayya babbar yayarsu maryam tanatayiwa khadija da saudat fada akan su tsaida miji sudena wannan shiriritar, zumbura baki khadija tayi "waike Anty Maryam akanki muke zaune ne? Duk kinbi kin ishi mutane, itakanta surayya guda nawa take za'ayi mata aure, yarinya da kuruciyarta shekara iyanzu ta haihu, ga mijin shiba kudi ba, gaba wani ilimi me zurfi duk tabi ta tsofe da wuri" bude baki Anty Maryam tayi "lallai sannu khadija, surayya ce tayi yarinta da aure, kuma shi arziki na Allah ne ai, sannan ita ya mace darajarta shine dakin mijinta, ba gararamba a layi tana tara samari ba" "eh ansan arziki na Allah ne amma ba wanda yakeson talauci ai, tara samari yanzu muka fara semun wankesu munci rabonmu mayi auren" Saudat ta kwabe baki sannan tace "batta ai ita na fuskanci so take kowama yayi rayuwar wahala kaman yadda tayi, kuma babu wannan zancen" Anty Maryam dataga abun nasu dagaske suke tace "to Allah ya baku hakuri matan masu kudi" Khadija tace "Ameen Anty Maryam, Allah yabamu mutemakamuku tunda ku baku da rabo" suka kyalkyale da dariya itada saudat. Ana haka sega surayya ta shigo dakin goye da yarinyar Anty Maryam tace "Anty kinga  humaira tayi bacci a bayana gaskiya na iya raino" Anty Maryam tace "Aikuwa dai kin iya raino, badi iyanzu in Allah ya kaimu Insha Allah kinkusa haifar naki" rufe ido surayya tai tace "gaskiya inajin kunyarki Anty maryam amma dai Ameen" dan zaro ido khadija tayi "au kekinayin auren zaki zage kiyita barin yara sekace kazar hausa" Saudat da sauri tace "ganemin hanya dai" Surayya tace "to meye a ciki yaya khadija, yara rahama ne bakasan wanda zaka huta dashi ba" "Ai seki zage kibada himma, ga auren talaka ga haihuwa, nan da nan ki ragwabe akasa banbance tsakaninki da mamanki, kinga bari in tashi in je in abunda yake gabana wannan batamin rai zatayi" khadija ta fice daga dakin, Anty maryam ta girgigiza kai "Surayya kyale wadannan sunyi nisa basajin kira, se fatan Allah ya shirya". Haka rayuwa tacigaba har akayi bikin surayya, yayinda su saudat duka dorawa ransu dogon buri musamman khadija, bata saurarawa duk wani saurayi da yashigo hannunta, duk tsiyarka duk arzikinka seta wankeka sannan ta sallemaka, amma duk da haka tana tare da Kabir, sha wuyanta kuma yana cigaba dayimata hidima iyakar yinshi, ya wofantar da mahaifiyarsa da kannensa. Kawayen saudat sun san khadija sosai, duk da kasancewarta me izza da jin kanta, ko kawayen kirki khadija bata da su se yaran manyan masu kudi, yaran masu kudin ma se yarinyar da akasan ubanta wanda ya tara dukiya sannan tayi kawance dake. Ranar wata laraba suna zaune, saudat tayi bakuwa, kai daganin yarinyar kasan kudi sun zauna, saboda ba tayi kalar wahala ba, motar da aka kawota ma a ciki ba karamar mota bace, kawar saudat din me suna Salma ABDUL JALAL Tajudden, kawar saudat ce sosai tasanta da dadewa dasuka hadu a gurin wani biki, khadija tanajin sunan salma a gurin Saudat, tana bata labarin kudin da familyn su salma ke dashi, bayan Salma sun gaisa da mutan gidan, taciro iv card a Jakarta ta bawa Saudat tace "ga iv din nan, saudat dan Allah kizo gurin bikina saura three weeks" saudat tace "Insha Allah zanzo, ashe abun yazo yama za'ayi kice bazanzo ba bayan nayi duk ankon bikinki" Salma tayi murmushi tace "Ainasan halinkine saudat, yanzu in bakiga dama ba sekice bazaki ba" "zanzo Insha Allah" "kinga bari inyi sauri, akwai guraren danake son zuwa, se anjima" har Salma ta mike zata tafi, khadija tace "Salma ni baza'a gayyaceni ba, anyway ina miki murna Allah yasanya Alkhairi" murmushi salma tayi "ni na isa, kema ga naki, ina gayyatarki yaya khadija" ta mikawa khadija iv, tasa hannu ta karba, bayan fitar Salma suka duba iv din nan, kwana bakwai cif za'ayi ana bikin nan, khadija tace "Saudat wai ita kam wannan wazata aura haka" "mhmm yaza'ayi insani khadija? Najidai ance dan uwanta ne, boyeshi take kaman ciwo batason aganshi, iya sanina da ita tana son gayen nan kaman ranta, ko sunansa bata fada, kinga jikin iv dinma sunan tane kawai, Allah ya kaimu bikin dai muje muga wazata aura haka" "Ainima dole inje bikin nan, dan naga alamar irin bikin da nake sone, dan haka dole a kece raini, muyi wanka kaman yaran senetes, inje inyi sababbin kamu" dariya sukayi gaba daya suka tafa. Kafin lokacin bikin Khadija tasa Kabir a gaba, seda yasamomata kudi kusan dubu arba'in ta sai less din dinner, ta dinga bin samarin ta, tana karbar kudi a gurinsu da haka seda ta sai komai sabo, tayi anko kafin lokacin bikin nan   Ranar da'aka fara biki, khadija da saudat sun dau wanka, kaikace sune dangin amaryar, khadija takira wani saurayinta yazo ya daukesu a tsaleleliyar motarsa, ranar kamu da bridal shower, da mother's evening duk ango bezoba, amma anci an sha, anyi barin kudade, kai dagani kasan wannan family sunci sun tada kai, naira ta koka a wannan bikin, gasu kyawawa kaman su sukayi kansu, daga mazansu har mata, gasu dayawansu ba farare baneba amma sunada matukar kyau, sunada dogayen hanci mazansu da matansu, wanda hakan ze tabattar maka family dayane, saboda suna kama da juna, khadija tayi samari a gurin bikin nan, saboda tayi kwalliya tayi kyau harta gaji, kaman uwa daya uba daya suke da amaryar, bangaren saudat ma hakane tasamu samari a gurin bikin. Ranar dinner hall ya cika taro yayi taro, manyan mutane maza da mata daga bangarorin Nigeria sun halarci bikin, Mc yabada announcement cewar ango da amarya zasu shigo, nan aka shiga yimusu kirari "Ango Alhaji Habib kamal tajudden, matashin Attajiri me ji da kansa, me gwalagwalai da zinare, Ango kayi dacen amarya hajiya salma ABDUL JALAL Tajudden, me kyautar zinare da dama hagu bata saniba, me ado da  sarkar zinare, abu naku maganin a kwabeku" haka aka cigaba da yimusu kirari tareda saka musu kida flower girls ne suka fara shigowa, se wasu kyawawan 'yan mata sannan ango da amarya a tsakiya. Amarya da ango sun hadu, sunyi kyau harsun gaji, tunda khadija tayi tozali da angon nan tarasa nutsuwarta, ya hadu karshen haduwa bata taba zaton akwai kyakywa a maza irinsa ba, da farine toda tabbas zaka iya rantsewa kace bayajin hausa, wannan shine irin mijin datake tsarawa zuciyarta tana son aure, wanda bata taba zaton ganinsa a gaske ba, Habib ta maimaita sunansa a hankali kaman yadda taji Mc yafada dazu, gumi taji yana tsatstsafo mata a goshi. Shikam ango se fara'a yakeyi cameras kota ina se hotuna akeyimusu, Saudat ta janyo hanun khadija sukaje suka dinga hotuna da ango da amarya, bayan sun dawo gurin zamansu ne saudat tace "khadija kinga wannaan bawan Allah kaman shi yakera kansa, dan Allah ga kyau, wallahi yafita kyau sosai" da kyar khadija tace "mhmm aikam dai yana da kyau" duk bata cikin hayyacinta, haka aka gama dinner din nan aka watse, a hanya khadija tacewa saudat "Sauda amma Salma ba hausawa baneba ko?" "eh to rabinsu hausa rabinsu kanuri, yan borno ne, kasuwanci yakawo wasunsu kano" "lallai kam, gasu da kyau gasu da kudi" haka suka cigaba da hira har sukaje gida,ranar khadija kwana tayi tana tunanin habib, tareda mafarkinsa. Suncigaba dazuwa gurin bikin nan har akayi akagama. yayinda kullum khadija insukaje suka dawo, soyyaya da tunanin habib ya cigaba da ninkuwa a zuciyarta. Ranar daza akai amarya, juyin duniya saudat tayiwa khadija akan suje kai amarya tace bazata ba, tun tana lallabata har itama ta hakura tace tafasa zuwa gurin kai amaryar, taje daga baya, in Salma ta tare. Ranar Khadija ta kwana da matsanancin kishin Salma, kasa bacci tayi daren ranar dan tayi mamaki yadda kaunar habib ta mamaye zuciyarta lokaci daya haka, haka ta kwana sake2 da tunani har gari ya waye. Koda gari ya wayema bata fito tsakar gida ba tana tana kan gado tana juyi Saudat ta shigo dakin tazauna gefen gadon ta kalli khadija tace "yar uwa tashi muyi wata magana kibani shawara dan Allah" khadija ta kalli saudat idonta duk yayi ja alamar rashin bacci, ta mike zaune ta dan yatsina fuska ta kalli saudat "fadi inajinki?" Saudat ta gyra zama tareda kallon khadija sannan tace "Khadija nifa tunda mukaje bikin salma, nayi ido hudu da mijinta naji wallahi inasonshi, shiyasa nazo kibani shawara yazanyi, Dan gaskiya bazan iya hakuri ba, bazan iya auren kowa ba seshi, dan Allah sister bani shawara ta ina yakamata in fara?" Gaban khadija ne yafadi, zuciyarta ta shiga bugawa da karfi, ga wani gumi dayake tsatstsafo mata a iya goshinta, taiwa Saudat wani irin kallo, sekuma tayi murmushi seda hakoranta suka fito, ta kalli saudat" Kin tabatta kinason Habib? " da sauri Saudat tace" Wallahi khadija so bana wasa bama, wallahi ina sonshi, aurensa nakesonyi" khadija ta gyada kai takuma yin wani murmushi Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣7️⃣70_ Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL _ Ta dafa kafadar saudat "bakida damuwa zanyi meyuwuwa inga burinmu yacika, amma kisani dole abu daya yafaru, ko kiyi nasara, kokuma akasin haka" "hakane amma ni nafi sa ran nasara dan kome zefaru sedai yafaru" "gara kidinga sawa ranki nasara da akasin haka, yanzu dai macigaba anjima, inada abunyi yanzu" "to shikenan bari zan dan fita dama, sena dawo" Saudat nafita khadija tabi bayan saudat dawani mugun kallo, sannan tayi kwafa "gaskiya Saudat bakida hankali, kekin isa inso abu kema kice kinaso, zakiga tsiya dake zanyi tarkon cikar burina, ita kanta Salma seta barmin Habib" ta sakeyin kwafa ta nemi guri ta kwanta. Sati daya da kai Salma gidan habib, Saudat ta shirya taje gidan Salma, ba karamin tsinkewa Saudat tayi ba da ganin aljannar duniyar dake gidan Salma, gidane na alfarma kaman ba a Nigeria ba, ga shi an kashe masa kudi da kayan alatu, haka Saudat ta sake taita kallo tana video gidan dan ta nunawa Khadija, bangaren kayan Abinci ba a magana, tasamu kyakyawar tarba daga salma, ta karramata da kayan Abinci sukayita hira Saudat tace "Salma kawo in turamiki hotunan da nadingayi miki lokacin biki" ba musu Salma tabawa Saudat wayarta, tana cikin yimata turi ta faki idonta ta dauki lambar Mijin Salma wato Habib, haka suka dinga hira se la'asar sannan saudat ta tafi, saudat taso taga habib amma bata ganshiba salma tagaya mata baya gari. Tunda saudat taje gida tana rawar jiki taje tasamu khadija tadinga nuna mata video gidan salma, gaba daya khadija ta rikice da ganin aljannar duniya, tabbas habib shine mijin daya dace da ita, Daga nan ta nuna mata ta samo lambar Habib "khadija ga lambarsa na samo ta ina yakamata in fara" Hanzarin me kike ne, ba tace miki baya gari ba, kibari se kaman  nan da sati daya mana maybe lokacin ya dawo" "anya zan iya jira har sati kuwa, nifa banki ace ko a satin nan a daura aure ba dan ba karamim so nakeyiwa gayen ba, kokuma ince nakewa dukiyarsa ba" Khadija ta jinjina kai tace "to wai yazakiyi da kawarkine, in ta gane zaki aurar mata miji" tsaki saudat tayi "wayake tawani matarsa, ai ranar biyan bukata rai ba a bakin komai yakeba, indai buri zecika, to babu batun kunya da cin amana, inma ta gane ita tasani nidai fatana in ganni a cikin wannan daukar" "hmm Gaskiyar ki yar uwata, Allah ya ida nufi" "Ameen khadija, ammafa in Salma tagane ba karamin hauka zatayu ba, dan tana masifar son gayen nan, gata da kishi kamar bala'i, amma tasamu dai dai da ita indai nice" murmushi khadija tayi "gaskiya zata taro match kishi da hajiya Saudat" sukayi shewa gaba daya. Kwana biyu da zuwan saudat gidan Salma, khadija ta shirya tun safe ta fita ashe wayar saudat ta dauka tun dare ba wanda yasani, ta fita ta cire sim din saudat tasa a wayarta ta dauki lambar Habib, sannan ta kakkarya layikan saudat ta zuba a kwata, sannan ta jefar da wayar tai tafiyarta, bata koma gida ba se bayan magariba yaje ta tarar anata jimamin wai barawo yashigo gida jiya da daddare yasace wayar saudat, ta shiga sahu akaita jajantawa saudat, saudat tabiyo khadija dakinta kaman tai kuka tace "wallahi khadija ba batan wayatane yabani haushi ba, rasa lambar habib itace ta konamin rai" "don't panic dear, karki damu, inkika canza waya seki kuma samo lambartasa, aibawani abu a ciki" "haba khadija kinsan da yadda nasamo lambar nan kuwa idan nakoma mezance mata inkuma karbar wayarta, kuma kwata2 yaushe naje gidanta dazan koma" ta karasa maganar kaman zatayi kuka "haba saudat kefa kikace ranar biyan bukata raiba abakin komai yake ba, amma kibari kaman in akayi sati biyu sekikuma zuwa, kinga ba wanda ze zargin wani abu" Saudat ta kalleta "haba khadija har sati biyu, anya kuwa zan iya jurewa" "Saudat idan kikabari matarsa ta gane zaki aurar mata miji to tabbas bazata kyaleki ba, gara kibi komai a sannu in lokaci yayi taji" Saudat tayi nannauyar ajiyar zuciya tace "kuma kinyi gaskiya khadija, shiyasa nakeson shawarwarinki nagode sosai, bari anjima Mukhtar zezo se in sashi yakawomin wata wayar" "eh hakan ma yayi kyau" "hakane nagode bari inje inyi salla" tana fita khadija tai murmushin mugunta. Khadija tasa kabir yasiyo mata sabon waya, me madannai tayi saving lambar habib a ciki, kullum safiya da dare seta tura masa zazzafan text messages da addu'oi , hakama da daddare zata tura masa  bata taba kiransa a waya ba, shima kuma betaba biyowaba balle yaji waye. Amma habib yana mamaki wacece take turomasa wannan messages haka, shidai yasan ba Salma bace bata da wannan lambar, kuma tunda sukayi aure bata yimasa tex kamana yadda take masa kafin suyi aure, amma bari ya tambayeta ko itace take turo masa, salma na gaban mirror tana taje kai, habib yana kan gado a kwance ya kalleta yace "my sweet lambobinki nawane?" kallonsa tayi "meya farune??" 'No bakomai na tambayeki ne dai" "fadamin gaskiya ko watace take kiranka ka zata nice" gabansa ne ya fadi ya kalleta, amma yakasa magana a hankali ta tako tazo ta zauna a kusa dashi tace "yanaga ka tsorata, nafada dai2 kenan" "A' a kam kinbani mamakine kawai, daga tambaya kin canzamin magana, kaman kina zargina" Tayi Ajiyar zuciya "Habib kada Allah ya nunamin ranar da wata mace zata dinga kiranka, amatsayin budurwarka, inaga a wannan ranar se zuciyata tayi bindinga, bazan iya jure ranar dazanyi sharing dinka da wata mace, inasonka habibi da'iman" seda cikin habib ya duri ruwa, amma ya dake yace "I love you too hibbaty, karki damu zuciyata kekadai ce a ciki, zan rayu dake har zuwa karshen rayuwata" yai mata murmushi tareda yin kissing dinta a goshi, ta dora kanta akan kirjinsa tanata ajiyar zuciya, message ne yashigo wayarsa, yasa hannu ya dauka ya bude message ne na nuna tsantsar soyayya da kauna da khadija ke turomasa, sauri yayi yasa lambar a blacklist, ba tareda salma ta dago ba tace "habiby waye ya turomaka message?" "Alert ne, kayan dana siyar aka turomin kudin" har cikin ranta ta yadda da abunda yace. Haka khadija takuma canza layi tacigaba da turawa habib messages baji ba gani, abunne yafara damun habib kar by mistake Saudat tagani, gashi layinsa ne dayakeso wanda huldodunsa na kasuwanci duk akai suke da se ya cire layin ya yar, besan mezece ma Salma idan taga wannan messages dinba, dan Yasan halinta da mugun kishi, yanzu se cibi yazama kari, ba dan haka ranar ya yanke shawarar yakira yaji kowacece, da safe wajen karfe goma khadija tana kwance tanata tunanin habib tana kallon hotunansa, karamar wayarta datake kiran habib da itane tafara ringing, ga mamakinta taga Habib ne nannauyar ajiyar zuciya tayi tareda yin murmushi ta rungume wayar a kirjinta tanajin ringing din wayar harcikin zuciyarta, wayar tayita ringin harta katse bata daga ba taitajira koze kuma kiranta amma be kirata ba. Kusan kwana uku bekuma kiranta ba itamuma tacigaba da turamasa, rana ta ukun da daddare yakuma kiran wayar khadija seda ta kusa tsinkewa, sannan khadija ta tattara duk wata nutsuwarta ta daga wayar, tana dagawa kafin tayi magana a fusace yace "wai dan Allah wacece haka, kina nema ki hadani fada da matata meye hakane, karki kara turomin wannan rubbish din nagaya miki" maganganunsa sunyimata zafi, amma ta dake tace "ohhh masha Allah, zanyi bacci irin wanda bantabayiba yau habib, naji muryarka Ina sonka, kayi bacci me dadi kaman yanda zanyi cike da farinciki" tunda tafara magana gaba daya jikinsa ya mutu yakasa cewa komai, itama bata jira meze ce ba ta kashe wayarta, tace "Lallai Habib bakasan wacece khadija ba bazaka taba kufcemin ba tunda kayi gangancin kirana" khadija bata taba gajiyawa ba gurin yi masa aiken zafafan kalaman soyayya. Yau sati biyu cif tacika da zuwan saudat gidan Salma, tun karfe goma na safe ta shirya, tazo tayiwa khadija sallama cewar zataje gidan Salma, ita khadija ta manta ma cewar sunyi da khadija yau zata koma gidan Salma, khadija ta dake taimata fatan nasara, bayan ta fitane ta dinga mata dariya. Koda saudat taje gidan me gadi yasanar da ita cewa masu gidan basanan sun tafi Abuja karfe 2narana zasu bar Nigeria zasu wuce Dubai, Saudat jitayi kaman ta dora hannu akai tayi ihu, tacewa me gadin "dan Allah yayana kozaka temakamin da lambar me gidan?" zare ido yayi "lallai da alamu kina da tabin hankali yadda tsaro yayi karanci zakice abaki lambar megida, to ni kaina bani da lambarsa, seta PA dinsa, se in abun me mahimmanci ne sannan ya hadaki dashi kuyi magana, inkuma bame mahimmanci bane ba yakamaki yace bakida gaskiya, indai baya gari tokomenene hakura nake"dafe kai saudat tayi takuma cewa" dan Allah kabani lambar P. A dinnasa mana" "waike wace irin mayyace ne, bar kofar gidan nan ko inyi waya azo a tafi dake wallahi" "No yi hakuri zan tafi, insun dawo senazo" daga nan ta juya ta taho gida, tareda tsinewa barawon dayasaci wayarta albarka, tasamo lamba a bagas an sace wayara haka ta dawo gida jiki a sanyaye, kallo daya khadija tamata tagane babu alamun nasara, nan Saudat tabawa khadija labarin abunda yafaru taita rarrashinta tareda bata karfin gwiwa kaman gaske. Khadija takoma daki ta tsarawa Habib text "Hayateee ashe zakabar kasarnan ba labari, masoyi masoyine ai at least yakamata in sani ai, Allah yakaika lafiya, yatsaremin kai yakareka ya kare dukiyarka, Allah ya albarkaci neman ka, ya doraka akan makiyanka, dukda ni baka damu daniba amma ni kullum soyayyarka ninkuwa take a zuciyata, gangar jikina tana Nigeria, zaka tafi da rayuwata Dubai, kaine rayuwata habib ka kulamin da rayuwata, zanyi kewarka rayuwata, Ina sonka Hayateee" Habib yana harabar hotel din dasuka sauka yaji message din yashigo koba a gayamasa ba yasan na wannan mayyar ne, yana budewa yakaranta sakon yana kuma karantawa, to ya akayi tasan zebar kasar, kiranta yayi seda taja aji sannan ta dauka "barka da wannan lokaci Rayuwata" "ke wai aina kika samu lambata kike takuramin haka, sannan wayagaya miki zan bar garine yau" "haba hayatee, kaifa rayuwata ne, yaya za'ayi inkasa sani, dukda nibani da mahimmanci a gurinka, kai kanada mahimmanci a gurina, Habib yakamata ka girmama kalmar so" tayi ajiyar zuciya, cikin kissa kaman zatayi kuka tacigaba da cewa "Habib bansan da wani kalman za gwada maka yadda nakeji a zuciyata ba" "kinga dakata, wai bakisan inada aure ba kwata 2 wata biyu kenan da yin aurena, yazaki dinga turomin messages na soyayya in matata tagani fa?" "shiyasa bana kiranka nakemaka message, kuma mata hudu Allah ya halatta maka, karkayi garkuwa da aurenka ka wulakanta bukatata" "Ke inkece a matsayin matata yazakiji idan akayi miki haka, inason matata kuma ni bazan kara aure ba mace daya Salmana ta isheni" "Habib da kaine a halin danakeciki nake maka abunda kakemin yazakaji, nafara sonka tun kafin infara ganinka" tayi ajiyar zuciya sannan tace, "shikenan Habib ka dawo lafiya Allah ya dawwamar da farinciki a rayuwar aurenka, nikuma zan dawwama cikin bakinciki har karshen rayuwa ta, zancigaba da rayuwa da soyayyar ka" takarasa maganar tana hawaye "kakula da kanka rayuwata ina sonka rayuwata Habib, i will miss you, zanshiga yanayi mara dadi habibina" kafin yayi magana ta kashe wayarta, habib yacigaba da jujjuya kalaman yarinyar, dan tabe baki yayi yakoma masaukinsu. Seda habib ya shafe wata shida bezo Nigeria ba shida Salma, suna dubai yana business dinsa suna cin aamarcinsu, sam khadija bata samun habib a waya saboda bata da lambarsa ta Nigeria, ta turamasa message harta gaji, ta bibiyi har gidansa taje tabawa megadinsa makudan kudi da zimmar duk randa habib ya dawo zekirata a waya ya sanar da ita, sannan tace masa idan har Saudat takuma zuwa gidan ya hadata da 'yan sanda, yace musu su tuhimeta, sannan ayi mata iyaka da zuwa gidan habib, ganin kudi yasashi amsawa yace yadda takeso haka za' ayi. Wannan kudin databawa megadin gidan Habib Adashin da kabir yayi ne a gurin aiki yakawo mata fiye da rabin kudin yace ta sai kayan kwalliya, shine ta dauki kusan dubu tamanin tabawa megadi dan yayi mata aiki. tsawon watanni shidan nan haka tayisu kaman mara lafiya, zazzafar soyayya da takewa habib ta wuce misali, har rashin lafiya tayi, gaba daya yan gidansu sun kasa gane kanta, juyin duniya taki gayawa kowa abunda yake damunta, ta rame sosai. Haka bangaren Saudat tayi zarya gidan habib harta gaji, kamar yadda khadija tagayawa megadi haka ya hada Saudat da yansanda, yace musu be yadda da itaba da alama, irinsune wanda yanfashi ke hada kai dasu, haka yan sanda suka kama Saudat, ranar wuni tayi a cell, yayyensu maza sukace ba ruwansu bazasu belinta ba, dama bata da kunya gara a koyamata hankali. Maman Saudat ta dinga hadasu da Allah suje sufito da Saudat sukaki, sukace "aibasu suka aiketa yawon gidan masu kudiba" Khadija da kanta takira kabir a waya tace yazo yanata rakiya, tasa Kabir agaba sukaje police station sukayi belin Saudat, yadda khadija tasaki jiki da yansanda suka dinga hira hada exchange na number ba karamin batawa Kabir rai yayi ba, tunda suka fito yake mita "haba khadija kinsan bana sonki da irin wanan abun, danmene zaki saki jiki da wasu mazan a gabana hada basu lambar wayarki" "kai dakata malam, aurena kake dazaka dinga takuramin, inbahaka nayiba kana ganin zasu sakarmin kanwata ne? Nifa banason wanan shirmen naka wallahi, inka gama mitar ka iya tafiya" tai shigewarta gida tabarshi a nan a tsaye. Tunda suka koma gida Saudat tayi wanka takasa ko cin Abinci, khadija taje kusada ita ta zauna "Saudat wai meye na damun kanki, bagashi naje nafito dake ba?" "mtsee khadija ba wanan ya dameniba, ni yanzu tashin hankali na rasa habib, wallahi khadija inason habib, zanyi duk meyuwuwa nima inshiga wannan daular in dama, kome zafaru dani a gaba sedai ya faru amma sena auri habib" "Saudat kibi komai a sannu, karkiyi gaggawa, se komai yazo miki da sauki, inkikace zakiyi garaje to zaki lalata komai ne" "hakane amma ni yazanyi zuciyata kaman ta fashene khadija, ni kawai burina inganni a wannan daular" khadija aranta tace "yarinya man kaza, niba dukiyarsa kawai nakeso ba, har shi kanshi habib din nakeso, dan haka zan cigaba da wasa da hankalinki yarinya" ta riko hannun Saudat "yar uwa, duk macen dataga habib taga dukiyar daya tara dole tasoshi amma kibi komai a sannu, in baki iya takunki ba garin wannan rawar jikin naki wataran prison za'a kaiki, yanzu abunda ze faru kidanyi hakuri kibari su dawo kasar nan semuga ya zamuyi tunda ba abunda zamu iya a yanzu tunda baya kasa" "shiyasa nake sonki khadija, kin damu da damuwata, zan bari se ya dawo kasar nan" "idan ya dawo dinma karki sake kikuma zuwa layin gidansu, kibari zansa aje a dan dinga survey din anguwar tasu da anga ya dawo za'asanar damu, Nikaina zanyi alfahari inganki a cikin wannan daular, inkika samu aina samu" rungume khadija tayi da sauri "nagode sosai, inaji dake yar uwa" "zakigane baki da wayo, bazan taba bari kikuma rabar inda habib yakeba" Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣8️⃣71 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com               _MY FIRST NOVEL_ Haka khadija tacigaba da wasa da hankalin Saudat ba tareda ita Saudat din tasan me khadija take shiryawa ba. Khadija ta karbi kudade dayawa agurin Kabir da sauran kudaden data damfara a gurin samarinta tafara business na atamfofi da kayan sawa, gurin manyan masu kudi, saboda tace in Allah yasa lokacin bikinta kece raini zatayi bazata barima azo ayi wani abu  a wannan gidan nasuba, biki za'ayi kaman na diyar sarakuna, dan jikinta yana bata zatayi galaba akan Habib saboda alamun sun nuna yanada saukin kai da tausayi. Ranar da habib yadawo Nigeria me gadinsa yakira khadija a waya yasanar mata, taimasa godiya take ta turamasa katin 5k saboda albishir din dayayi mata, shi habib har yamanta da batun me turomasa messages, se bayan kwana biyu yamaida layinsa na Nigeria messages din khadija yafara cin karodasu ba adadi, tsaki yayi ya aje wayar yashiga sabgoginsa, kwanan sa uku da dawowa yakoma gurin aikinsa, yana zaune a office aka kirashi a waya, bakuwar lamba ne dan haka beyi tunanin komai ba ya daga wayar, tana sallama ya gane wacece, amma yarasa meyasa duk lokacin dazata kirashi baya iyayimata rashin mutunci. Yana cikin wannan tunanin yaji muryarta tana cewa "Rayuwata, barka da dawowa kasa Nigeria, ina maka barka da zuwa nayi kewarka matuka, nayi rashin lafiya sosai bayan tafiyarka, ina fatan kundawo lafiya" Abun mamaki taji yace "ya jikin naki?" seda tayi murmushi ta wani lumshe ido "Jiki ina samun sauki Alhamdilillah" "me yake damunki?" takuma kashe murya "hayatee komaima yana damuna, nikaina narasa meke damuna, amma jigon rashin lafiyata soyayya ce, at least zansamu relief tunda ka dawo, bari in barka ka huta, I love you hayatee" ta kashe wayarta, tunda habib ya dawo Nigeria tafara shawo kansa saboda koyace katta kara kiransa bata fushi, kullum cikin nuna masa soyayya take, ta lura ya dan damu akan maganar rashin lafiyarta, hakan yasa tafara ji ajikinta burinta yana daf da cika. Tacigaba da kokari tana dauke hankalin Saudat daga kokarin zuwa gidan habib. Seda khadija ta lura habib yafara bata kulawa, seta dena tura masa message ta kashe wayar da take kiransa da ita domin ta tabattar da ko yafara sonta, haka ta danne zuciyarta tsawon sati biyu bata kirashi ba kuma bata turamasa message ba. Ranar da sati biyu ta cika khadija ta kunna wayarta, messages ne suka shigo wayarta, data bude duk na habib ne sekuma kamfanin layi, dayake shikadai take kira da layin, duk messages din yana tambayarta ina tashigane layinta baya shiga Allah yasa lafiya, bata san lokacin datayi wani tsalle ba tayi ihu a daki, mamanta ta shigo dakin da sauri "ke lafiya meyasameki?" "bakomai mama bansan nayibane" "to Allah ya shiryeki auta" mama ta fice khadija ta mike tsaye hada rawa a cikin daki. Bayan sallar magariba kabir ya tura yaro yace yayi masa sallama da khadija, tace yaron yace tana zuwa, ta shirya zata fita gurin kabir sega kiran Habib. Nan da nan ta tashi ta kulle kofa tazo tanemi guri ta zauna akan gado ta daga wayar cikin sanyin murya tai masa sallama, kafin ya amsa sallamar yace "ina kikashiga haka tsayin wannan lokacin?" "hayatee bani da lafiya ne fa" Cikin sauri yace "subhanallah jikinne har yanzu? Yanzu kina inane?" "ina gida naji sauki" "dagaske kinji sauki kokuma wasa kike?" "Am serious, yau naci Abinci sosai nayi wanka nayi kwalliya, i wish kaga kwalliya nan hayatee" murmushi yayi yace "dagaske?" "Eh mana nayi kyau sosai, sedai ciwon so duk ya ramar dani" "yaushe zan ganki?" "Duk sanda kakeso, a shiryenake" "kiyi fixing time, seki gayamin zanzo mugaisa" "masha Allah, hayateee harnaji na warke gaba daya" "to Allah yakara afuwa, bari zan shiga gida" cikin sauri cikin shagwaba khadija tace "haba hayatee ni wallahi bangaji dajin muryarka ba, kalli tsayin lokacin daka dauka bana jin muryarka fa" haka khadija ta dinga hilartasa suka shantake suna waya, tana masa hira me dadi har gurin goma da rabi na dare sannan sukayi sallama, Kabir yagaji da jira gashi lokacin sanyi amma khadija taki fitowa maganar duniya tayi banza taki bude kofa tacigaba da wayarta, daga baya tace ace masa yacigaba da jira inyaga ze iya tana da abunyi me mahimmanci datakeyi. Seda ta gama wayarta tace ace masa ya tafi bazatazoba. Saudat ta shigo dakinta tace "khadija wai dan Allah wani zazzafan kika samune haka kusan awa uku kina waya, naga duk saurayin dakikayi bakya yiwa Kabir wulakanci amma yau kin shuka masa dayawa fa" khadija tayi wani shu'umin murmushi tace "ai ke bar gara kawai, najefa fatsata a ruwa kuma da alamu nakamo kifi me nauyin gaske, ba kama kifinne matsalar ba, sedai zanyi gwagwarmaya kafin kifin yazama mallakina saboda akwai masu farautar wannna kifin dayawa abakin ruwan" ta kuma kallon Saudat tace "kodayake kince ranar biyan bukata rai ba abakin komai yakeba yar uwa, dan haka zan jure gwagwarmaya da kubale in mallaki kifin nan" Saudat tace "kinga ni kiyimin hausar dazan gane, se wani kwana2 kikemin, nibangane mekike nufi ba" "karki damu zaki gane very soon yar uwa" Bangaren habib kuwa, Salma ta damu matuka baya kaiwa tsawon wannan lokacin a waje, amma yau ya kai, tayi2 yagayamata dalili yace bakomai wani abune ya rikeshi haka ta hakura. Wasa2 taga ya maida hakan dabi'arsa baya shigowa gida se bayan goma, dataga bashida niyyar denawa itama ta watsar dashi tacigaba da sha'aninta, seta ajiye masa abincin sa akan dining tayi kwanciyar ta, hakan yakara bashi damar sakewa suyi waya da khadija. Ranar juma'a da yamma suka shirya zasu hadu a wani gurin shakatawa, saboda khadija bataso yazo da rana gidansu Saudat ta ganshi, yarigata zuwa gurin yana zaune yanata duba agogo har yafara fidda ran kozatazo, yana kokarin kiran layinta ne, yaji kamshi me dadi yacika masa hanci, dukda yajuya baya, amma tana kallonsa tabaya tasan shine, a hankali ta tako tazo bayan kujerar dayake ta tsaya, ta durkuso da kanta a hankali tace "Hayateee barka da zuwa" ya dago kai ya kalleta daga sama har kasa, doguwar mace ce, sannan tana da dan kiba kadan, baza akirata da fara tas ba amma tanada hasken fata sosai, tabbas khadija tana da kyau dai dai2 gwargwado, murmushi yayi mata "sannu da zuwa masoyiyar boye" murmushi tayi ta zagaya ta zauna akan kujerar datake facing dinsa, suka gaisa sun sha hira sosai sannan ya dauketa ya kaita har bakin layinsu shikuma ya tafi. Khadija tayi nasara samun zuciyar habib tana nunamasa soyayya iyayinta, haka habib yasake da khadija suke soyayya ba tareda Salma tasani ba, yakanzo gurin khadija tadi, Saudat ta fusakanci yan kwanakin nan khadija tana cikin farinciki. Bayan sun gama cin Abinci khadija ta tafi daki ta shafe kusan awa uku tana waya, a iya sanin Saudat datayiwa khadija tasan bata son doguwar waya, amma ya akayi kwanan nan take waya haka, mikewa tayi tabi khadija daki, taje ta tarar da ita tanata zuba shagwaba a waya, tana ganin Saudat ta shigo dakin tai maza tayiwa habib sallama ta mike zaune "Saudat lafiya kuwa na ganki haka ba zato babu tsammani" "hmm dole kice haka mana almost 3hrs kina waya, ba'a kojin mekike fada, shikam wani me nasarar ne haka? Kodai kin hadu da dream hubbyn nakine" wani kasaitaccen murmushi khadija tayi "kwarai kuwa kedai kiyitamin Addu'a" "shine babu ko Labari balle a gabatarmin dashi" 'mekikeci na baka na zuba, shida zezama sirinkinku sekin gaji da ganinsa "Saudat tace" Allah sarki Kabir yanata tsuma ze aureki " Tsaki khadija tayi " ke dalla kidenamin zancen wannan wawan, nifa badan ina tausayinsa ba da tuni na dade masa wulakanci, kodayake wulakanci na nawa, bashida zuciya ne" "Mhmmm nikam nace khadija waime ake ciki game danawa damuwar ne, wallahi khadija ko baccin kirki bana iyayi" Ajiyar zuciya khadija tayi tace "gaskiya Saudat ina tausaya miki, abun nada matukar tausayi, nikaina na kagu inga kinshiga wannan daula amma semunbi komai a sannu, bakisan iya kokarin danakeyi miki ba, yanzu haka nabada cigiyar in yadawo a sanar dani, naje har layin gidansa dakaina, amma ance an hana shiga layin ba tareda wanda zakaje gurinsa yasaniba, amma inata miki kokari " " to khadija Allah yasa adace" "zama adace kakri damu Saudat". Duk ranar da Habib zezo gurin khadija tadi sedai su hadu a gidan kanin mahaifiyarta acan suke zancen, soyayya ce me karfi tashiga tsakanunsu, duk kasar dayatafi A gaggauce yake ya dawo domin ya hadu da ita, baya jure dogon lokaci basu hadu ba. Habib da kansa yacewa khadija ze turo iyayensa ayi maganar aure, amma zeje maiduguri tukuna in yadawo seya turo, tayi murna ranar kamar ta zauce bata taba zaton a abubuwa zasu mata da sauki haka ba. Gefe guda habib yanata tunanin, yadsa ze sanarwa da Salma batun auren dayakeso yayi, dan yasanta da matukar kishi, dan haka ya yanke shawarar zefara zuwa maiduguri in magana tayi nisa yagayawa Salma. Koda Habib yajewa mahifiyarsa da zancem Aure bata bashi goyon bayaba hasalima faada takama yimasa "haba habib, yaushe kayi auren fari da har zakace zaka kara aure, yarinyar nan yar uwarkace fa, mahifinka da mahifiyarta uwa daya uba daya, hakan ze iya shafar zumuncinku, gaskiya ka hakura kozakayi aure ba yanzu ba" yakada yaraya amma mahaifiyarsa taki yarda, Habib tunda yake betaba yiwa mahaifiyarsa musuba se wannan karon, yaita mata magiya, karshe seda yaje yagayawa yayanta yazo yasa baki, badan tasoba haka ta amince, amma tace kafin aje neman auren se anyi bincike, akayi bincike amma bincike ya nuna khadija ba mutuniyar kirki bace, batada aibu, sedai rashin kunyarta da iya fitsara, yan uwan mahifin habib suka gayawa mahaifiyarsa nan ma ta dage tace baze yuwi ayi auren nan ba. Khadija yagayawa khadija halin da akeciki ta damu sosai nan ta shiga addu'a ba dare ba rana, ta sanarda mahifiyarta komai sukacigaba da addu'a habib yanakin baze iya rabuwa da itaba dan haka yacigaba da lallaba mahaifiyarsa. Habib ya canza gida, yakoma wani dankareren gida daya Gina a gadon kaya, gidane na alfarma matuka, anan ya tsara inya auri khadija ze hadasu da Salma. Bayan khadija ta tabattar da Habib ya tashi daga gidansa, taje ta samu dansandan dayake gadin rukunin quaters din dasu Habib suka tashi, tabashi kudi, ta shiryamasa abunda takeso yayi mata, sannan ta dauki Saudat sukaje tsohuwar unguwarsu Habib da nufin suje sugani yadda zasuyi kozasu samu Habib, suna zuwa dansanda dayake gadin rukunin quaters din yace musu "wakuke nemane?" khadija tace "gidan Habib kamal mukazo" Nan yagaya musu "Ai yabar quaters din nan, tunda yadawo daga Dubai bezoba" Da sauri Saudat tace "ina suka koma?" "kamarya ina sukakoma dokace, da sun yadda daku dakunsan inda suka koma dan haka kubar nan gurin" khadija tai kokarin yagaya musu amma yai musu korar kare tare da barazanar ze kullesu, khadija ta kashe masa ido alamar aikinsa yayi kyau. Habib yasha wahala sosai sannan mahaifiyarsa ta amince da maganar Aurensa da khadija, dangin mahifinsa ciki harda mahifin Salma, sukazo nema masa auren khadija gurin wan mahaifinta, sannan mahifin Salma yajawa mahifiyarta kunne kan be yadda wani yagayawa Salma Habib zekara Aure ba shida kansa ze gaya mata, dangin mahifin Habib suka kai kudin Auren Habib akasaka wata shida. Khadija jitake kaman ba itaba, habib yagaya mata ansaka wata shida ji take yamata nisa wata shidan nan, se murna take ta tafi dakinsu Saudat cikin zumudi tana kiran sunan Saudat, tana zuwa ta tarar da Saudat tana kuka, da sauri ta karasa inda take tadafata "Saudat meyasameki haka?" Saudat ta share hawayenta ta girgigiza kai tace "bakomai khadija" "A'a da komai gayamin menene?" Saudat ta dan gyara zama tace "khadija har yanzu burina becikaba, gashi ke zakiyi aurenki amma ni se gararamba nake, ba wani tsayayye wanda nake hangen yakasa samuwa, yanzu zakiyi aurenki ki barni" khadija ta riko hanun Saudat sannaan tace "Saudat dan adam be isa yasamu abunda ba rabonsa ba, indai habib rabonkime sekin aureshi, inba rabonkibane ba ba yadda zakiyi, shawarata agareki shine karki tsaya jiran Habib, ki bata lokacin ki, tun wuri kinemawa kanki mafita" "khadija kina nufin in hakura gaskiya bazan iyaba kome zefaru, kedai kiyi aurenki ni zancigaba da fafatukata, sena auri Habib wallahi" murmushi khadija tayi "to shikenan Allah yabawa me rabo sa'a" daga nan ta tashi ta fice. Habib da kansa ya shirya ya dauki Salma suka je maiduguri, yakaita gidansu da nufin tayi musu yan kwanaki, mahaifin salma yasa aka kiramasa ita dakinsa, ya zaunar da ita yayi mata nasiha sosai sannan ya sanarmata Habib ze kara Aure, ji tayi kaman mahifinnata ya watsa mata wuta, take idonta yayi jawur ta kalleshi "Aabba kan nufin Habib dinane zeyimin kishiya, kuma kake gayamin innalillahi wa inna ilaihi raji un, dan Allah Abba kacemin da wasa kake, wallahi bazan iyazamabda wata a matsayin kishiyata ba" "Ke meye hakane? Akanki aka fara, to ki nutsu, akanme mijinki yanada halin daze auri mata hudu ya kuma iya rike su danme zakice baze aure ba, karki kuskura inji kin daga masa hankali shiyasa nace nizan gaya miki da kaina, dan haka kiyi hakuri, daba a aure dakema baze aureki ba, yakamata kija girmanki tunda kece uwargida, dan haka kiyi hakuri tashi kije Allah yayi miki Albarka " da kyar ta mike tsaye tana tafe tana hada hanya ta tafi dakin mahaifiyarsu, tana zuwa ta zube a jikin mamansu takama kuka " mama dama habib ze iya yimin kishiya, ko shekara biyu bamuyi da aure ba shine ze auri wata, mama anyimin adalci kenan" ajiyar zuciya mama tayi tana dan dukan bayan Salma alamun rarrashi "kiyi hakuri Salma kinji, kuma bazamu kira abunda habib yayi da rashin kyautatawa ba tunda shima danmune, ni macece salma masan meye kishi abune me ciwo amma kiyi hakuri zakiga ribar hakurin, kiyi masa fatan alkhairi sannan karki nuna masa kin damu" "A'a Mama bazan iyaba, wallahi zuciyata zata fashe, mama bakisan menakeji ba, bantaba mafarkin Habib zemun kishiya ba, in hakanema yabari sena kwana biyu a gidansa mana, amma yaushe mukayi auren zemun haka, toni na hakura da aurennasa yaje ya zauna da wadda yakeso" nan mama taita rarrashinta tana nunamata illar cewa zata kashe aurenta. Kwanan salma biyu a gida sannan habib yazo daukar ta, iyayen salma sam basu canza masa ba, sedai Salma fuskarta sam babu walwala zakayi zaton jinya takeyi, harsukazo kano batace masa uffan ba. Bayan sunkoma gidama ta tattara tayi watsi dashi, bata cin Abinci sosai kullum cikin kuka take abun yafara damun habib sosai dan haka yaje ya sameta a dakinta yanzuma idonta jawur da alama tasha kuka sosai. A hankali ya karasa ya zauna kusa da ita yayi kokarin janyo ta jikinsa amma ta kwace, ya kalleta "habibty dan Allah kiyi hakuri, bazanyi Auren nan dan in wulakanta kiba, matsayinki yana nan a zuciyata kaman yadda kika sani, dan Allah badanniba kidena azabtarmin da kanki, kidinga cin Abinci kin rame sosai kindena bani kulawar da duk kike bani, please my Salma calm down" kuka takuma saki me ban tausayi, ya rungumeta ya dinga mata nasiha yana rarrashinta a irin kishi na salma be taba tunanin ze iya rarrashinta ta hakura ba, kusan kullum se iyayenta sun kirata a waya anmata nasiha da addu'oi hakan yasa tasamu raguwar radadin da take ji a zuciyarta. Biki nata karatowa anata shirye2 amma har yanzu yan gidansu khadija basu taba ganin Habib ba, sunyi mitar sunyi harsun gaji amma taki yadda aganshi, yayyenta sunyi fada sosai dasukaji cewar ba Kabir ne yakawo kudin auren khadija ba, amma aka barshi yana wahala, amma mahaifiyarta ta goyamata baya, hatta yan anguwa bakowa yasan khadija zatayi aure ba saboda tace ba kowane garane zezo mata gurin biki ba, mussaman ma yan unguwarsu yan bakin ciki, Habib yana sakarwa khadija kudi yadda yakamata anata shirin biki. Babban abun mamakin yadda haryanzu kabir besan khadija zatayi Aure ba yana zuwa gurinta tadi, kuma yanabata abu takarba, yauma suna tsaye tagama hira da Kabir wani makocinsu yagansu, sungama tadi ya dakko uwar leda cike da kaya yabata, nan ya jinjina kai lallai wannan yarinyar tacika yar banza, aikuwa sena gayawa yaron nan, kokuma inje har gida ina sanarwa da uwarsa dan watakila idan nagaya masa wannan makirar yarinyar tace karya nake babarsa zanje ingayawa Tirkashi Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  1️⃣9️⃣72 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ Washegari da yamma makwabcin su khadija yatafi gidansu Kabir, dayake abokin baban kabir ne kafin ya rasu, yaje gidansu kabir yai sallama mahaifiyar kabir tayi masa iso, bakowa a gidan se ita suka gaisa da mutumin, tunda mahaifinsu kabir ya rasu jefi jefi yakanzo su gaisa shima se a shafe shekara bezo ba, suna ciki gaisawa ne kannen kabir suka shigo suka gaisheshi ya amsa yana su karimane suka girma haka masha Allah, yana nan zaune yaga suna gaganiyar fita da murhu da ice waje, seda suka gama ya kalli mahaifiyar kabir yace "suwai ba waime yaran nan suke da murhu a waje" mahaifiyar kabir tace "kasan yanayin rayuwar ne se godiyar Allah, suna dam soye soyene a waje suna siyarwa, in sun siyar muke samun biyan bukatun yau da kullum da nauyin karatunsu, ga kuma batun aure na kokarin tasowa, ba mai yimana komai se Allah" "Amma ina kabir, naji ance yasamu aikin kamfani kwanakin baya, ga kuma nakan ganshi wataran a kasuwa yana neman kudi, ya akayi yake barinku har se kannensa sunfita waje suna siyarda abu" Ajiyar zuciya mahaifiyar kabir tayi "hmm lamarin kabir se addu'a inzaka yankani bansan inda yake kai kudi ba, kullum na tambayeshi se yace bashida kudi, semu shafe wata uku ko gawayin girki be saimin ba balle Insaran kayan Abinci, ficika kabir baya moramin a kudin dayake samu, haka kannensa zasu shafe tsawon likaci a gida ba makaranta saboda ba abiya kudin makaranta ba amma baze iya biyaba, tun ina magana harna hakura na zuba masa ido" "Tirkashi anya kabir nason yagama da duniya lafiya kuwa?" "to yazanyi, na hakura na kyale shi yaje in abunda yakemin ya kyauta yaje shima ze gani" "to bari in gayamiki wani abu, kimanin shekaru shida kenan kabir yake zuwa gurin wata yarinya a kusa da gidana, ita yake kashewa kudadensa, yarana suna shiga gidan suna gayawa mahaifiyarsu irin hidimar dayake mata, yanzu haka yarinyar bikinta saura sati shida, shi kabir ne saniba kuma ko jiya akan idona yabata katuwar leda cike da kaya" Zaro ido mahaifiyar kabir tayi "kana nufin dama dagaske ne kabir yana neman yarinya, a gayamin amma ban yadda ba" "Aiko yakamata ki yadda, dan yarinyar ba karamar hatsabibiyabacce ba, ya dade yanamata wahala duk abunda yasamu ita yake bawa, yanzu kuma zatayi aurenta ta barashi, gara tun wuri kisan halinda kike ciki, ni zan tafi Allah ya kyauta gaba" haka mutumin nan yatashi yabar maman kabir da bacin rai batasan lokacin data fashe da kuka ba "yanzu duk wahalar danayi daku amma sakamakona kenan agurinka kabir, ka fifita budirwa sama dani" haka ta cigaba da kuka, da magariba kannen Kabir suka dawo daga gurin sana'arsu amma suka tarar da mahaifiyarsu ranta a bace, na suka shiga jero mata tambayoyi, bata boye musu komai ba tagaya musu, karima tace "aini na dade da sanin zancen nan, banason ranki yabacine, amma yaya kabir har adashi yake yaje ya kaimata, komai yasamu ita yake kaiwa" "Amma karima shine baki taba gayamin ba" karima tace "to mama meye amfanin fadar, yanzu da kika sani meyakara inba bacin rai ba, ai ga sakayya nan, zatayi aure tabarshi kuma itama zata gani, dan Allah kidena kuka" haka suka cigaba da rarrashin mahaifiyarsu daren ranar mahaifiyar kabir kasa bacci tayi, mussaman inta tuna matsin rayuwar dasuke shiga amma Kabir baya musu komai yana can yanayiwa budurwa bauta. Yau khadija ta shirya ta tafi kasuwa bata nan, mahaifiyar kabir kasa jurewa tayi ta shirya ta tafi gidansu khadija, da taje khadija bata nan se mahaifiyar khadija ta tarar suka gaisa sannan maman Kabir tace "dama nice mahaifiyar Kabir" umman khadija tace "Allah sarki sannu dazuwa, kabir yaron kirki ya kuke ya yan uwansa" "muna lafiya kece mahaifiyar khadija?" "eh nice ya akayi ne?" "yanzu dama bazaku bashi auren yarinyar ba amma kuka dinga sawa yana kashemata kudi har tsawon shekara shida, ni ina can ina fama da maratun kannensa, kukuma ya tare a gurinku, ga wahala gashi yarinyar zatayi aurenta kunyi mana adalci kenan" takarasa maganara idon taf kwalla, umman khadija tace "to baiwar Allah ai se hakuri dama indai ka haifi namiji ai wata ka haifawa, kuma ita mace allura ce a cikin ruwa me rabo ka dauka, kuma kinsan halin yarn zamani ba'a iya musu dan haka se hakuri" "Yanzu hakan yayai daidai kenan"? "to inma beyi daidai ba aisedai kiyi hakuri" ana haka sega khadija ta dawo, batabi takan mamanta da bakuwar dasuke tareba ta shige daki abunta, mamanta ta kirata ta nunamata maman kabir tace "ke ga babar kabir nan tabiyo jin kadin ya akayi kinsan bazaki auri danta ba kika dinga ci masa kudi, itakuma baya kulada ita" kallon mahaifiyar kabir tayi tace "banda abunki aiba nina rikeshi nahanashi tafiya ba, kuma ni bance karya kulaldake ba, abunda nasani niba sa'ar aurensa bace dannafi karfin auren matsiyaci irin danki m, kidubeni da kyau  banyi kalarsa ba dan haka yaje yanemi daidai da shi baniba, sannam ze iya lissafa abunda ya kashe a biyashi konawane, zan auri miji daidaidani danki shine matsiyaci se abiyashi kudinsa sekuma me? " Bude baki mahaifiyar kabir tayi cikin mamaki "Au hakama zakice" ta juya ta kalli mahaifiyar khadija "yanzu kun kyautamin, kina kallon yarki abunda kukayi adalci ne? Shikenan kuda Allah kuma wallahi ke sekinga sakayya a rayuwarki, se Allah yabaki dan dazemiki fiye da abunda kikasa dana yaimin, kirikiri insha wahala da yayana, tun suna kanana har suka girma, amma kika kanainayemin yaro, kin hanashi ya amfanamin komai, alhalin kinsan ba aurenshi zakiyi ba, wallahi na barki da Allah" kuka sosai mahaifiyar kabir takeyi, wanda hakan ya janyo hankalin mutan gidan suka fifito tsakar gida, ita kuwa khadija tace "ai kokinki ko kinso dole kibarni da Allah dama, kabir ne naci rabona dama rayuwa ta gaji haka, kinzo se hayagaga kike mana kin taramin mutane sekace namiki sata aikin banza kawai" khadija tai tafiyarta ta shige daki haka mahaifiyar kabir ta baro gidan gwiwa a sabule tanata kuka, tana zagin khadija. Koda mahaifiyar kabir takoma gida inta tuno abunda yafaru se tayi ta kuka, da magariba kabir ya shigo gidan, yazo ya gaisheta a fusace tace "ka tashi bana bukatar gaisuwarka kabir, kaje na yafewa diniya kai na sallamaka ga yarinyar daka fifita fiye da uwarka, kabir ashe tsawon shekaru shida kanayiwa yarinya bauta itada iyayenta, amma ni wani lokacin abunda zamuci da kannenka gagararmu yakeyi kana kallo ko a jikinka, kaje idan abunda kayimin ka kyauta kaje ga duniya nan" "haba mama wacee irin maganace wanan wane munafikin ne yagaya miki haka?" "dalla rufemin baki nice munafukar, har gidansu yarinyar naje yau, suncimin mutunci ita da uwatta, kuma suka tabattar min da wani zata aura, kayi asara kabir, bazanma bakiba amma hakkina ya isheka wallahi" a sukwane kabir ya mike tsaye "bangane khadija zatayi aure ba wayagaya miki?" wani takaici ne ya tokare mata a kirji wato shi ta batun auren ne ya daga masa hankali, shiru tayi ta sunkuyar da kai tanata sharbar kuka, a sukwane ya fice yabar gidan. Be tsaya ko ina ba se gidansu khadija akayi masa sallama da ita, yau yaci sa'a ta fito, ko gaisawa basuyi ba a gigice yace "khadija wai dagaske aure zakiyi"? "injiwa? " mama tacemin tazo gidan nan, an tabattar mata aure zakiyi, khadija ki gayamin gaskiya " " nifa bana son wannan abun ds kakeyi ka nutsu mana, nibawani aure da zanyi da auren zanyi da bakasani ba, ka dinga bincike ka tabattar da abu kafin kazo kanamin surutu" "Alhamdilillah har naji dadi, khadija inna rasaki bansan ya zanyi ba" dariyar mugunta tayi masa tace "kaga zankoma gida ina aikine, adinga hakuri dan ba kullum ake kwana a gado ba, kaga dama A'ayi bikin kawata ne zanturomaka 100k a account dinka inaso asamomin sababbin dari biyar biyar" "100k dijena ai sunyi yawa, yazaki lika har hundred thousand" "bacewa nayi kabani kyauta ba, zanturomaka ne kamin canjinsu kawai" "dija samun sabon kudi yana dan wahala, amma zan duba miki insha Allah zan kawomiki karki damu" "shikenan yayi kyau, ka gaida gida" daga nan ta shige cikin gida abunta. Lokacin biki nata kuma karatowa, Salma ta rame sosai, duk tayi duhu saboda damuwa, mahaifiyar Habib da kanta tazo kano, taitayiwa Salma nasiha tanabata hakuri, sannaan tajawa Habib kunne akan ya kulada Salma, Ta hadasu tayi musu fada sosai sannan takoma maiduguri. Saura sati biyu biki Habib tafiya takamashi, akai sa'a a ranar akakawo iv din biki, yaje dakin Salma ya sameta a kwance ya zauna a kusada ita yace "Habibty anjima zan tafi, ga katin biki an bugo ko da wanda zaki gayyata" "Allah ya sanya Alkhairi" shine abunda tace masa kawai "Habibty banajin dadin yadda kike shareni, nasan namiki laifi amma horon yayimin tsanani" "dan Allah habib ka kyaleni, ka tafi karka makara" "kina korata kenan?" "niban koreka ba amma ka kyaleni" "shikenan amma kimin Addu'a mana" "Adawo lafiya Allah ya kiyaye hanya" haka ya juya ya tafi jiki ba kwari, bayan fitarsa ta dakko wayarta tana kallon hotunan bikinta da Habib tana kuka, hotunan Sauda data ganine yasataga bata kyauta ba yaushe rabon dasuyi ko waya, dan haka tasaka tshohon layinta ta kira Saudat. Ba karamin mamaki Saudat tayi ba dataga kiran Salma dan haka cikin sauri ta daga wayar "salamu alaikum" Saudat tafada, "wa'alaikum salam, Saudat yakike ya gida" "lafiya kalau Salma, Salma naje gidanki ba adadi bana samunki, daga baya aka cemin kuntashi bansan inda kikakoma ba" "eyya kiyi hakuri Saudat, kinga mun dade bama Nigeria ne, kuma damuka dawo ba dadewa munkoma gadon kaya" "Allah sarki yanzu kina gari kenan, aiko insha Allah cikin satin nan zanzo dukda munata shirin biki" Salma tace "Masha Allah, bikin waza'ayi? Amma ba gayyata" "Khadija ce zatayi Aure saura 3 weeks" "Kai kice na bugo waya a dai dai, da yanzu se ayi babuni ai yakamata inzo bikin khadija, dukda nima Habib ne zeyi Aure kusan lokaci dayane ma dana khadija" seda gaban Saudat ya fadi "A.... Au... Aure kuma, wai wani Habib din kike nufine?" "Hmm Saudat kenan, wane Habib kuwa, mijina mana, abun yabaki mamaki ko? Aure zeyi Saudat, amma Insha Allah zanzo bikin khadija ban manta dawainiyar da kukayi a bikina ba" cikin Saudat tace "to shikenan Salma se anjima, semun sake waya" ta kashw wayarta, mikewa tayi a sukwane ta tafi dakin khadija tana kwala mata kira "lafiya kikemin wannan kiran, kaman wadda kikebi bashi meye haka?" Saudat ta karaso cikin dakin tana haki ta zauna sanna tace "Khadija na shiga uku" "Kamar ta kinshiga uku, meyasameki?" "Ni narasa ta ina zanfara, Salma sun dawo Nigeria yanzu haka mukayi waya da ita tagayamin unguwar dasuka koma, wai amma Habib Aure zeyi saura 3 weeks, Khadija Aure zeyi nikam na kade, wallahi ko wacece bata isaba wallahi " "to shine kika daga hankalinki haka, kemafa mijin watane kike kokarin sekin Aura, har gara ke baki Aureshin ba, ita matarsa ma bata daga hankalinta ba seke, Saudat abun nan naki yafara yawa, you better find another solution, kidena bawa kanki wahala, inbahakaba ki mutu bakiyi Aure ba" Mamakine yacika Saudat ta kalli khadija "Au hakama zakice, dole ki gayamin haka tunda ke zakiyi Aure, to bari kiji ingayamiki wallahi kowa ze aura inze auri mata hudu seyasaki daya ya aureni, duk bala'in daza'ayi sedai ayi wallahi, matsalata tawace zanyi kokarin shawo kan matsalata inci ka burina, zanje gidan Salma sedai ai duk wacce za'ayi " Murmushi khadija tayi" To Allah yabawa me rabo sa'a, fada da aljani ba wasa ba, kije Allah yabawa me rabo sa'a" tsaki Saudat tayi ta fice daga dakin, sosai khadija take dariya tace "sha3 zakigane bakida wayo, keda Habib har abada" Duk yadda mutan gidan su khadija sukaso suga mijin dazata aura ki tayi , kome za'ayi sedai a gidan yan uwan babansu, amma taki yadda sam yazo gidan, invitation din daurin Aure ma hanawa tayi agani, saboda kar Saudat tagano, tayi mata hauka. Yau khadija ta yanke shawarar zata gayawa kabir Aure zatayi zata sallame shi, yadena zuwa gurinta yaje shuma Allah ya hadashi da rabonsa, da magariba kabir yakawowa khadija wannan kudin, lokacin saura kwana takwas biki, ta karbi kudin tayi masa godiya suka gama hira zetafi tace "dan jirani ina zuwa" ta shiga cikin gida ta dakko iv ta fito, yana nan tsaye inda ta barshi ta miko masa kati. Yasa hannu ya karba yace "wannan fa?" ba fargabar komai tace "duba kagani mana?" Kafin kabir yagama karanta katin, yaji kafarsa na rawa, fitsari yacika masa mara "khadija wannan invitation din na waye?" "bangane ba bagashi a hannunka ba kana gani, sunan waye kuwa, katin Aurena ne, saura kwana takwas dama ita duniya haka ta gada, dan haka iname baka hakuri Kabir Allah yahada kowa da rabonsa, nasamu irin mijin danake mafarkin Aure dan haka Cikin tsawa Kabir yace "Dalla malama dakata, kina nufin zaki Auri wani baniba wallahi khadija karya kikeyi, shekara shida ina wahala dake, amma kice bazaki Aureniba wallahi karya kikeyi" "dalla dakata, kai namaka kalar auren matsiyaci kamarka, wanda se ya samo da kyar, nasamu hamshakin attajiri daidai dani kaima seka samo yar talakawa wadsa zata iya da talaucinka ku daidaita, inkana ganin bazaka hakura ba, ka lissafa nawa ka kashemin kobo bayan kobo za'a biyaka hada Riba " " Wallahi baki isaba, kece babbar matsiyaciya kwadayayyiya, kije k Auri wani khadija, kin kyauta amma wallahi yadda nasa uwata kuka saboda ke, kema se kinyi wanda yafi na uwata, zan nuna miki ni dan halak ne, amma ki saurari matakin dazan dauka akanki, anta gayamin zakiyi Aure amma ban yadda ba yau kin gayamin da bakinki, wallahi sena wulakantaki a idon duniya, sena turamiki bakinciki mafi muni da zeyi ajalinki" Kare masa kallo tayi tsaff sannan tace "kai kana ganin har akwai wani bakinciki, zanyi Aure a gidan Naira, zan rayu da wanda nakeso, jeka kayi abunda kaga zaka iya, khadija ce kafi kowa sanina sha3 kawai, idan nayi Aure bazaka kara ganina bama dan wahala" ta shige ta barshi a kofar gidan Zubewa kabir yayi a gurin, yanajin kaman zuciyarsa zatayi bindiga wai yaushi khadija tabawa katin Aurenta. Salma tana gabaan dressing mirror tana shafa mai, ta kalli envelope din invitations da Habib ya ajiye mata tsaki tayi ta ture envelope din invitations din suka zube kasa, a hankali ta kai hannu ta dakko na daurin Aure tana dubawa Duf! Duf!! Duf!!! Taji kirjinta yana bugawa Khadija Munir yakasai tunani take ina tasan wannan sunan, take sunan Saudat ya fado mata Saudat Munir Yakasai, taduba inda za'ayi daurin Aure unguwar su Saudat ne layinsa Ji tayi kaman numfashinta ze dauke, wayarta ta laluba ta nemo lambar Saudat, jikinta na bari, Saudat ta daga sama2 Salma take jawo Numfashi tace "Saudat waye  ze Auri khadija?" Cikin rashin fahimta Saudat tace "lafiya kuwa Salma?" "ki gayamin wa khadija zata Aura?" Takuma tambayar cikin karaji Saudat tace "nima bansaniba amma naji tace sunanshi Habib" "INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI UN!!!!!! " Salma ta furta da karfi A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu 'oinku Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za' a fara posting din Littafin ABDUL JALAL  Facebook tundaga farko Insha Allah, za'afara posting a group din AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy's girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣0️⃣73 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ Da sauri Saudat tace "Salma lafiya kuwa? Wai meya faru ne?" Cikin kuka tace "dole kicemin meyafaru Saudat, kuncuceni ina zaman lafiya da mijina, amma ku yaudareni keda yar uwakki wallahi bazan yafe muku ba Saudat, kije da Allah nabarku da Allah daga ke har khadija" cikin rashin fahimta Saudat tace "bangane me kike nufiba Salma, dan Allah kimin bayani" "Au saboda baki da kunya har bayani kike nema inmiki, Azzalumai kawai, wallahi bazan yafe muku ba na yadda dake kun hada kai da yar uwakki kun cutar dani cuta mafi muni kuda Allah" ta kashe wayarta, ta dora hannu akai ta fashe da wani irin matsanancin kuka me tsuma zuciya "Na shiga uku ni Salma, menamuku kuka kwacemin miji, mijina mafi soyuwa a gareni shi zaku auremun Habibin nawa, shi zaku auremun na shiga uku ni Salma, meyasa nasanki Saudat" haka tacigaba da kuka tana surutai. A salube Saudat ta sauke wayar, takasa gane inda maganganun Salma suka dosa, meye alakarsu da Auren mijin Salma. Tana cikin wannan tunanine taji ana shelar ankai lefen khadija gidan kanin babansu, akwati ashirin da hudu, gida ya dau sowa da hayaniya "Akwati ashirin da hudu"? , Saudat ta maimaita, "itakuwa khadija ina tasamo Attajirin mutum haka? Waye wannan ze Auri khadija haka, shiyasa take boye shi, to tabbas idan har bansamu Auren Habib ba, sena shiga na fita naraba khadija da Auren nan koda tayishi, dan bazeyuwu tayi Aure tasamu Attajiri haka, nikuma ina gararanba ba" Tafito tsakar gida yan gida nata surutu, wasu na san barka wasu na kushewa, suna agarin kwashe2 kil dan yankan kaine, inbahakaba akwati ashirin da hudu sekace wata yar gwal, yayinda bakin mahaifiyar khadija yaki rufuwa dan murna. Khadija bata gida dan sedare ta dawo, yauma Saudat gurin khadija ta tafi "Khadija nikam dan Allah ki gayamin waye mijin nan ko a hoto ki nunamin shi, akwati ashirin da hudu dozen biyu fa, sana'ar meyake haka" "mekike ci na baka na zuba, har gidan nan zezo ranar daurin Aure kijira zaki ganshi ai, koma sana'ar meyake ni ina ruwana" "sewani Boyeshi kike kaman ciwo, zamu ganshi dai muga meye ake boye mana, nace wai yazakiyi da kabir ne"? Tsaki khadija tayi "Kabir din banza, nabashi katin daurin Aurena, yagama zage zagensa da kumfar baki, uwassa ma tayi tagama, nace yaje yai duk abunda yaga ze iya" "hmm khadija manya, amma Kabir be cancanci haka daga gareki ba, ya miki wahala be kamata ku rabu baran baran ba" "to ko zaku daidaitane keda shi?" "Allah ya kiyaye ke ki auri me kudi nikuma ki hadani da matsiyaci Allah ya kiyaye" "yo kuma ni sekiga laifina" "to abar wannan zancen dazu tela ya aiko miki da dinkinki" "Aiko ya kyauta, dama nagama biyansa kudinsa" "Khadija munyi waya fa da Salma dazu" wani mummunar faduwar gaba ta ziyarci khadija amma ta dake tace "Allah sarki" "Amma wasu magamganu ta dingayi da bangane musu ba" "kamar ya kenan" "ni kaina ban gane me take nufiba, Amma zankuma kiranta, yadda take maganar tana cikin damuwa" "Saudat duk wanda za'ayiwa kishiya ai dole yashiga damuwa, mussaman bw san da wacce kishiyar zata shigo ba, kibata shawara cewa ta mike tayi tsaye, dan duk wata mace a yanzu musamman wadda zata shiga gidan me mata toda shirinta take zuwa" "bata tsaya ta saurareniba balle in bata wata shawara, bari dai ayi bikinki agama, nikuma zan mike inyi fafatuka nima inshiga a ta uku" dariya sosai khadija ta dingayi mata "lallai Saudat yakamata kema seki dage Allah yabawa me rabo sa'a" Yau Habib yadawo daga tafiyar da yayi, dan satin biki yakama, dan gidansu khadija har sunfara wasu events din da mamakinsa koda yadawo Salma bata gida, yakira wayarta amma taki dagawa. Yasan bata da wasu kawaye ko gurin zuwa a kano dan haka a ranar ya shirya ya nufi maiduguri, aikuwa yanazuwa tana can gidansu gaba daya bata hayyacinta banda aikin kuka babu abunda takeyi, dayake shima gidansu ne be jira amma sa isoba ya shiga gidan ba kowa se ita kadai a palour a kwance akan doguwar kujera idonta duk ya kumbura saboda kuka "Salma meyasa kika taho kekadai baki gayamin ba, inata kiran wayarki kinki ki dauka hankalina ya tashifa" Banza tayi masa ta dauke kanta, "haba Salam meyake faruwa ne?" "dan Allah ka rabu dani Habib karshen wulakanci kayimin shi, karasa wadda zaka Aura se yayar kawata duk matan dake garin nan, bakasan wacece khadija ba, amma ka rubuta ka ajiye sekayi danasanin wannan auren kuma bazan koma gidanka ba nagama Aurenka Habib, am really disappointed on you " mikewa tayi zata bar palourn ya riko hannunta amma ta fizge ta wuce dakinta ta kulle kofa, jiki  a sanyaye yanemi guri ya zauna ya dafe kansa a gurin, Salma tanada mahimmanci a rayuwarsa baze taba bari kishinta ya rufemata ido ta rabu dashi ba, amma me take nufi daze auri yayar kawatta dama tasan khadija ne? Mikewa yayi ya nufi part din mahaifin Salma. Amma yana zuwa ya tarar yanada baki dan haka yajira ya gama sannan yashiga, mahaifin Salma na ganinshi yafara murmushi "Ango kasha kanshi, saukar yaushe haka ba Labari" dan sosa kai Habib yayi ya samu guri ya zauna yace "Abba dan Allah ka tayani bawa Salma hakuri, duk na rasa gane kanta, munyi sallama lafiya na tafi na dawo na tarar bata gida ta taho nan, nace tazo mukoma tace bazata koma gidana ba" Ajiyar zuciya mahaifin Salma yayi sannan yace "Mata se addu'a, ni na dauka kasani kai ka batta tazo ai, kuma mahaifiyarta batacemin yaji tayo ba, tashi muje yaudin nan zaku koma kano tare Insha Allah" Suka mike suka tafi dakin Salma, Abba yace ta bude masa shine, haka ta taso ta bude, Nan ya dirar mata da fada ta inda yashiga bata nan yake fita ba, yaimata kaca2 Cikin kuka tace "Abba kayi hakuri amma yayar kawatace fa, meyasa yaya Habib zemun haka" "ko kawartaki ce aiba haramun bane ba, kuma daba'a Aure daba a Aureki ba" daga nan ya yakoma yimata nasiha da rarrashi, ya hadasu gaba daya yai musu nasiha yai musu Addu'a, Abba be bari maman Salma ta dawo ba yace ta shirya tabi Habib sukoma Kano. Da magariba Saudat tanata safa da marwa a daki, tarasa meyake mata dadi, khadija zatayi Aure ta batta, gashi khadija tasamu me kudi itakuwa ko oho, ga Salma na wasu maganganu da bata gane kansu ba, "gaskiya yakamata inyi wani Abu, bari inji in Salma na gida gara tamin kwatancen gidanta inje inji komai, sannan inyi fafutukar haduwa da Habib" Wayarta ta dakko da sauri ta dannan lambar Salma, aiko a fusace Salma ta daga wayar "me kike nema a gurina kuma, kun kwacemin miji, hakan yayi sanadiyar samun sabani da iyayena, kun rabani da farinciki na, shine kika bugo kiji kona mutu ko? To ban mutu ba da raina" Cikeda mamaki Saudat tace "dan Allah Salma kiyi hakuri bangane mekike nufi ba" "dole kice baki ganeba, maciya Amana kin hada kai keda yayarki zata Auremin miji, Saudat kurasa wanda zaku cuta seni Habib dina yayarki zata Aura, nagode Saudat karki kara kirana a waya, kuma ko a lahira bana fatan Allah ya hadani da ireiren zuri'arku" Saudat bata karasa gane me Salma take nufi ba, dan kojinta bata gamayi ba, dan tuni ta saki wayar a kasa, kokari take ta tabattar da bacci take kokuma idonta biyu, kaman wadda aka tsinkula tayo waje da sauri daga dakin. Khadija tana kwance tana wayada Habib "Hayatee dan Allah kazo inganka mana, tunda satin biki yakama banaganka ba kuma kacenin kadawo daga tafiyar" "kiyi hakuri Dijart, wallahi Salmace duk ta birkicemin, kuma bata da lafiya dole ina tareda ita kiyi hakuri, Tana bukatar kulawa ta mussaman" "nibana bukatar kulawarka kenan? " bahakabane ba deejart, ita daza'ayiwa abokiyar zama tana bukatar rarrashi da kulawa, yawwa nace dama kinsan Salma ne? " " Meyasa ka tambayeni" Saudat ce ta fado dakin bako Sallama tayo kan Khadija, da sauri khadija ta tashi zaune ta kashe wayar "Khadija wane Habib din zaki Aura? Waye Habib din?" dama khadija tasan wannan ranar zatazo, dan haka ta mike da sauri ta rufe kofar dakin, saboda yan biki sunfara zuwa gidan da mutane, ta dawo ta kalli Saudat tace "ina jinki, mekike cewa?" Cikin fada tace "tambayata ma kikeyi? Waye Habib din dazaki aura?" Cikin dakewa tace "Habib Kamal me Gwal, mijin Salma kawarki shi zan aura" A razane Saudat ta kalleta "ke yanzu khadija bakji kunyar gayamin haka ba, macuciya Azzaluma, na yadda dake kici amanata, mijin kawata, wanda nakeso nazo nagaya miki matsalata, kikace zaki temakamin ashe cuta ta zakiyi khadija, na yadda dake amma kimin haka" "ke dalla dakata, mekikace mijin kawarki, aigara ace nina aureshi akanki abun kunyar seyafi sauki, ni abun kunya gaba na bashi ba bayaba, kekikace ranar biyan bukata rai ba abakin komai yakeba, kema Auren cin amana kikaso kiyi ai, Saudat na dade ina mafarkin Auren miji irin Habib tun ranar da naganshi naji nakamu da sonsa amma abun mamaki, kika rigani gayamin kema kina sonshi, a lokacin nan dana gayamiki ina sonsa nima toda biyu babu za'ayi, shiyasa namiki shiru, na gargadeki da kinemi wani karki tsaya jiran Habib amma kimayi bris dani, kisani mutuwa ce kadai zata iya hana Auren nan, duk wani shige da fice dazakiyi a yanzu aikin gama ya gama baki isa kiyi komai ba, dan ba karamin shiri nayi ba" Fashewa da kuka Saudat tayi tace "khadija da tun farko kin sanardani kina son Habib, dazan iya barmiki shi, da ban wahal da kaina haka ba, amma kika bari na dinga lalube kina rainamin hankali, tun tasowarmu kaf cikin yan uwana uwa daya uba daya dake na yadda, amma kinmin cutarwa mafi muni khadija!!!! Kinsa na zubda hawaye kin bakantamin rai kinmin tabo me muni da bazan manta ba, kin kwace abunda na kallafa raina aki, shikenan ki shirya ki rubuta ki Ajiye idan harni Saudat yar halak ce haihuwar uwa da uba, wallahi senamiki mummunan tabo kema ki Auri Habib ga daula nan kinsamu, amma ki saurar zakiga nima abunda zan iya" ta juya da sauri fuskarta duk hawaye zatayi waje khadija ta rikota, karo na farko dataji tausayin Saudat amma ta basar tace "Saudat ki fawwalawa Allah lamarinki, kiyi wanka da fetur, sannan ki hau risho da wandon leda yafimiki sauki akan hana Auren nan, kisawa zuciyarki salama kibi a sannu kema sekiga kin samu ko wanda be karasa Habib bane, kinfi kowa sanin hatsarina karkije garin daukar fansa kikuma ruftawa wani tarkon wanda bazanso hakan ba, har yanzu ina kaunarki yar uwata, kar abunda nayu miki ya shafi zumunci da kaunar dake tsakaninmu" Fizge hanunta tayi da karfi ta bude dakin ta fice, Ajiyar zuciya khadija tayi ta koma ta zauna tayi murmushi tace "Saudat kenan, na dade ina ankarar dake amma baki gane ba, naciki wasa se hakuri" Tundaga lokacin nan Saudat tafara rashin lafiya har akayi gama bikin khadija, tarasa nutsuwarta gaba daya, banda tunani babu abunda take, so take ta samu hanyar dazata turawa khadija bacin rai dan ta huce, tarasa mezatayi danta huce, kasa samun mafitane yasata takara shiga damuwa da halin rashin lafiya, yayinda khadija ko a jikinta hidimar bikinta kawai takeyi, anyi hidima sosai a bikin khadija anci an sha, anyi watsi da nera yadda yakamata. Kabir yashiga matsanciyar damuwa gameda Auren khadija, yayi kuka, yayi kukaba adadi, ga fushi da mahifiyarsa keyi dashi, ga basussukan mutane saboda yadda yakecin bashi yana kashewa khadija, gaba daya duniya tayimasa zafi, yarasa meyake masa dadi. Tunda Allah yasa khadija ta shiga gidan Habib komai yafara rushewa, gaba daya hankalin Habib yakoma kanta, Salma dama bata da surutu, khadija tafita baki, dan haka ta shiga hadasu fada, dama khadija bata kaunar dangin Habib tunda taji labarin basa son Aurenta, da Habib baya wata guda cikakke beje maiduguri ba amma tunda ya auri khadija seyayi watanni bejeba, Salma sedai ta zauna tasha kuka, ya shirya musu tafiyar wata daya Dubai shida Salma da khadija, Salma tace bazataba, ya dauki khadija suka tafi basu dawoba seda sukayi wata uku, gaba daya Salma ta zubawa sarautar Allah ido. Idan yan uwan Habib sukazo gidan ta dinga rashin mutunci kenan tana habaici Tunda taje dakin miji Saudat bata taba zuwa gidanta ba balle takirata a waya, hakazalika seda ta shekara guda cif sannan ta yadda tabi Habib maiduguri ta gaida mahaifiyarsa, tunda mahaifiyar Habib taga khadija taji sam bata kwanta mata ba dan sam babu alamar kunya ko kara a tareda ita, tunda ya aureta shekara guda sannan tazo ta gaishesu. Ta lura khadija a tsaye take ga Salma ta rame matuka tayi duhu, dan bata gayawa kowa meyake damunta, kota fada ba a goya mata baya sedai ace tayi hakuri kishine ke damunta. Maman Habib ta kirashi dakinta, ta dinga masa fada, akan yadinga adalci tsakanin matansa, in bahakaba seyayu danasani, dan taga alamun wannan tsagerar daya aura kamar suna cutarda Salma, dan ita sam wannan yarinyar batayi mata ba, banda rashin mutunci shekara guda da aure sannan sukazo yakawota gida sugaisheta shi kansa ya canza gaba daya, Haka yaita bata hakuri, yace insha Allah ze gyara amna yana kokarin yimusu adalci. da kyar khadija ta hakura ta kwana biyu a garin tace ita ya maida ita gida ta fuskanci danginsa basa kaunarta. Watan khadija biyar a gidan ta fuskanci tanada ciki, koda tagayawa Habib yayi murna matuka, tunda ya auri Salma shekara biyu kan na uku amma bata taba ko batan wata ba, sunje Asibiti ance lafiyarta kalau, dan haka yayi murna da wannan cikin "Habib kadena murna da wannan cikin zubar dashi zanyi wallahi!" Cike da mamaki ya dubeta "kamarya ya? Ina neman abu in samu kice zaki zubar khadija why?" "ban shirya haihuwa yanzu ba wallahi, da kuruciyata bazan tsufa ba wahalar yaya ta kasheni ba, tun kafin muyi Aure kasan burina inason yin karatu me zurfi a kasar waje, tayaya zanyi karatu da ciki, kwata2 yaushe nayi Auren zanyi ciki, wallahi sena zubar" "khadija kiyimin rai dan girman Allah kiyi hakuri, kibari ki haifamin cikin nan seki tafi karatun" "sekuma kayi, in kanason cikinka seka dauka ka maida shi jikinka ka haifa, amma indai a jikinane bazezo duniya ba gara ka hakura inkun matsu kaje kaimata cikin ta haifa maka" Saroro yayi yana kallonta, ba kunya take gasa masa wannna maganganun. . A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu 'oinku Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za' a fara posting din Littafin ABDUL JALAL  Facebook tundaga farko Insha Allah, za'afara posting a group din AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy's girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣1️⃣74 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ "haba khadija, yanzu dan sunnan zakice zaki zubarmin, ina son yara sosai, ki haifamin ko dayane seki tafi karatunki bazan hanakiba, mama tana matukar son yara, tanason jikoki, dan Allah kibari ki haifamin" Mikewa tayi ta shige toilet tabarshi a gurin a zaune. Tana shiga bandaki tayi tsaki tace "in maman nason yara, se itama ta haifa aiba abun kunya bane, aikin banza nibahakane yakawoni ba" "ikon Allah Salma nata nema ido rufe tana Addu'a, itakuma Allah yabata zata zubar" Haka Habib yaita fama da Khadija, a haka har yakoma Dubai, ta shirya ta tafi gidansu sunyi murna sosai da ganinta, khadija tanada kyauta tanayu musu aike sosai, kama daga Abinci sutura da kudi, amma idan Habib yayi niyyar yiwa yan uwansa kona Salma wani abu, indai tasani seta hanashi, amma itakuma ta nayiwa yan gidansu. Ranar dataje gida seda ta tsorata dataga Saudat tayi rama matuka, tayu duhu duk wannan kwalisar babu, har cikin ranta taji babu dadi yanayin dataga Saudat, dan haka ta dan damu, daki tabi Saudat tacewa sauran kanensu sufita subasu guri, b musu kowa ya watse, tazo kusada Saudat ta zauna ta kalleta tace "yar uwata, meyake damunki haka? Saudat kinga yadda kikakoma kuwa?" Tsaki Saudat tayi, ta juya mata baya "Saudat nasan ban kyauta mikiba, amma rayuwa bazata tafi a hakaba, kisani dama can Allah be rubuta Habib mijinki baneba, idan kika cigaba da wannan rayuwar tozaki kashe kanki a banza ne, tunda kinsan Bazaki samu Habib ba, Saudat inaso mucigaba da zumuncinmu, kimanta da abunda yafaru ki karbi kaddararki, Allah yafito miki da miji, indai kudine Saudat duk abunda kikeso zanmikishi Insha Allah" mikewa zaune Saudat tayi ta kalli Khadija "Zumunci nidake har abada wallahi, kin riga kin rusa alakar dake tsakanina dake, ke kinama yaudarar kanki ne da kike cewa wai mukoma kaman da, naji tawa kaddarar kenan da tasameni a sanadinki, kema ki saurari taki kaddarar, malama ki tashi kibaani guri, ficemin a daki" "Saudat nikike kora haka?" "na korekin ko uwata ce tamin abunda kikayi min sena rama, dalla malama fita munafuka" "shikenan tunda haka kika ce, inkika dawo hayyacinki zaki gane me nake nufi" khadija ta mike ta bar dakin. Bayan tafiyar Habib da yan kwanaki khadija Taje chemist tace subata maganin abortion, me chemist din yace shi gaskiya baya irin wannan harkar, take ta zube masa uwar kudi, take jiki na rawa yabata magani da yadda zata bi cikin ya zube, ta dauki maganinta ta tafi gida, yadda yace mata haka tayi amfani dashi, aikuwa ba adau wani lokaci ba mararta ta dinga ciwo wuni tayi tana murkususu a haka har seda cikin nan ya fita, tasha wahala matuka, gashi ba wanda tagayawa, ko Salma da suke zaune gida daya bata mata magana, haka tai wahalarta ita kadai ta gama. Saboda daukin cikin da Habib yakeyi, sati uku yayi ya dawo gida, gurin khadija yafara sauka, se wani sabon kalan soyayya yake nuna mata sabida duk zatonsa cikin yana nan. Da daddare yana cin Abinci shida khadija, ya kalleta yace "cwt Deejah, Wani suna kikeso musakawa babynmu inkin haihu, ina son in sanarwa su yaya hajjo, cewar munsamu rabo, ko baby" dan ya tsina baki tayi "mhmm kaga dakabar wannan batun gayawa mutane ansamu rabo, bayan tafiyarka na fadi a toilet cikin ya zube, ban gayamaka bane saboda kar hankalinka ya tashi" Abincin daya hadiya ne yaji ya makale masa a makogwaro yaki wucewa, "kin zubarmin da ciki ko khadija?" "niba zubarwa nayi ba zu..... " Shut up!!! " Yafada cikin tsawa da sedata razana " saboda kin rainamin hankali kike cewa zubewa yayi, wato baki hakura ba shine kika zubarmin da ciki, dan kinga ina lallaba ki ko? Nikikayiwa haka ko? Har innuna miki abunda nakeso amma ki shure kiyi son ranki, kin zubar Minda ciki nagode " "Ahhh Hayatee wallahi..... " yimin shiru" Ya katseta, ya tashi ya dau wayoyinsa yabar palourn, dafe kai tayi bata taba tunanin Habib ya iya fada haka ba, saboda gaba dayansa silent ne, bashida hayaniya sam. Amma fushinsa baze hanata cinma burinta na rayuwa ba. Wasa2 tunda yabar part dinta seda yai sati guda bata ganshi ba, ko ta waya, dan haka ta shirya ta nufi part din Salma, tana zuwa ta tarar Salma na kitchen tana girki batabi takan Salma ba ta nufi palour na biyu, "lafiya zaki shigomin ba sallama ki wucemin daki?" "ba ruwanki ba gurinki nazo ba" ta shige tabar Salma a gurin, tana shiga kuwa ta tarar da Habib a palourn yana karanta jarida, karasawa tayi ta zauna kusada shi "Hayatee kwana bakwai banganka ba, meyasa dana gayamaka abunda yafaru baka yadda daniba" shiru yayi yaki dagowa ya kalleta, hannunsa ta riko ya dago  a fusace Amma seyaga fuskarta sharkaf da hawaye, nan take jikinsa yayi sanyi "Hayatee, duk lokacin danakiraka Hayatee i mean it har cikin raina kai rayuwata ne, meyasa ka karyatani baka yadda bani na zubar maka da ciki ba, inason abunda kakeso tsautsayine ya gifta cikin ya zube dan Allah kayi hakuri" ta zube akan gwiwoyinta tana kuka, hannu yasa ya dagota ya rungumeta yana share mata hawaye "is ok am sorry my deejat, ya wuce kidena kuka" a hankali tace "I miss you Hayatee, dan Allah karka kara fushi dani haka" "I miss you too baby, bazan kuma ba" Khadija yar duniya ce yanzu kana zaune zata siyeka. ganin shirun yayi yawa yasa a fusace Salma tanufo palourn, Amma abunda idonta ya gane mata yasata ja da baya da sauri, jitayi kaman andoramata dutse a zuciyarta, kitchen takoma ta toshe bakinta tana kuka, tanaji tana gani anzo har cikin gidanta an kwace mata miji. Antyn Jalal ta kalli Jalila data tattara duk wata nutsuwarta kaman tana daukar karatu tace "kinga rana tayi, shabiyu takusa, kuma da azahar zamu koma maiduguri, zan kara takaita miki labarin nan dannima bakomai nasani ba, Amma kinsan meyasa khadija tayi nasara ta kwace mijin Salma?" Girgigiza kai Jalila tayi "Salma ta zurawa Habib ido tana ganin kaman yadena sontane, maimakon ta tashi tsaye tayi fighting ta gwada masa soyayya, ta kwaci mijinta, seta karaya da wuri tana ganin kaman bazata iya kishi da khadija ba tafi karfinta, ta zuba musu ido" Haka rayuwa tacigaba, seda Khadija ta zubar da ciki kusan hudu Habib be saniba, data fuskanci tasamu ciki setaje ta zubar, daga karshema taje tai planing hankalinta kwance ba wanda yasani, tacigaba da cin amarcinta, yau suna wannna kasar gobe suna waccan kasar, khadija tayi duk me yuwuwa takara farraka tsakanin Habib da Salma baya Jin maganar kowa se khadija, khadija yar kwalisa ce yar gayu, ta iya gayu ga girki da iya magana, yanzu zatayi laifi amma take zata mantar dashi duk wani laifi datayi, seda khadija ta shekara uku tana cin duniyarta da tsinke ta taka wanda takeso duk meson wani abu a hannun Habib seya biyo ta gurinta, Salma kam yau da lafiya gobe babu saboda bacin rai kullum cikin guma mata khadija take, duk wani abu datasan zatayi ta bata mata shi takeyi.  Sedai ta shiga daki tayi kuka. A yan shekarun nan Saudat haka takeyinsu ba walwala tayi iya tunaninta taga hanyar dazata rama abunda Khadija tayi mata amma takasa samu, kuma tayiwa kanta Alkawarin kozata mutu wajen daukar fansa setayi, zata nunawa khadija ba ita kadai ta iya makirci ba, zata rama inda babu wanda ze gani balle ya tausayawa khadija. Saudat haka tasamu FCE ta shiga take zuwa makaranta dan ta ragewa kanta zafi. Tsawon shekarun nan uku zazzafar gaba Saudat tajeyi da khadija duk abunda tasan ya shafi khadija nuna masa kiyayya take muraran, har mutane suka fara fuskantar hakan, yan gidansu sunyi mamakin dama akwai abunda ze hada khadija da Saudat dazesa sununawa juna kiyayya kasancewar ba'ajin kansu. Khadija ta hurawa Habib wuta kan lallai ita seyasamo mata Admission a Dubai ko Egypt tafara karatu, ya nunamata yan uwansa bazasu yadda da hakaba, tayi hakuri duk makarantar datakeso a Nigeria ze kaita amma banda kasar waje, amma fafur ta badawa idonta toka taki, haka yafara nema mata Admission a Dubai ba wanda yasani seshi da ita, Allah ya temaketa tasamu, yasamu Salma yace itama ze nema mata se sukoma can gaba daya, Salma tace bazata ba sedai su barta anan duk sanda yayi niyya in yasamu lokaci yazo yaganta, ya kada ya raya amma Salma tace itafa bazata ba suje se sun dawo. Haka Habib da khadija sukaje suka tare a Dubai, ita tana karatu shikuma yana kasuwancinsa, seyafi wata uku bezo Nigeria ba gurin Salma ba inma yazo bayafin kwana goma ze juya, hatta mahaifiyarsa ta zuramasa ido, tana masa Addu'ar Allah ya shiryeshi, yana daga cikin kaddararsa Auren hatsabibiyar mace. Wani zuwa da mahifiyar Habib tayi itada kannensa mata nida yayata, Gidan bakowa se Salma kawai mama ta tambayeta ina Habib ina khadija nan ta fashe da kuka tagaya mama duk abunda yake faruwa, Mama hankalinta ba karamin tashi yayi ba, ta dinga yiwa Salma fada, danme bata gayamata irin rayuwar da takeyi agidanba kenan, nan da nan ta kira Habib tace kome yakeyi ya yanke su dawo Nigeria tana nan tana jiransa. Yagaywa khadija tace wallahi bazat bar karatunta ta taho ba, shidai ya tafi shikadai, haka Habib ya taho yabarota a can. Ba karamin bacin rai mama ta nunawa Habib ba tace masa yazama wajibi yadawo da Khadija Nigeria bata yadda da batun karatu a kasar waje ba tunda bashida hankali, ya tare a gindin mace yana zaluntar yar uwassa, yaita bata hakuri, gefe yana fargabar yadda ze sanar da Khadija batun fasa karatunta. Yaita bawa mama hakuri amma fafur taki yadda tace se khadija ta dawo kasa Nigeria, hankalin Habib ya tashi yarasa ya zeyi da wannan batuna A Mama, haka ya shirya ya koma dubai yasanarwa khadija hukuncin mama, amma tace ita bazata dawo ba, yasan yadda zewa mama ta hakura amma ita karatunta yafara nisa dan haka yayi hakuri. Mama tanata matsa masa lamba akan ya dawo da khadija gida, ana cikin wannna halinne khadija ta fuskanci tana dauke da juna biyu abun ba karamin mamaki yabawa khadija ba, yaza'ayi ace tana planing amma tasamu ciki, nan da nan ta shiga damuwa. Tabass barin cikin nan shize hanata da ciigaba da karatunta, gashi bata san kowa ba a Dubai balle tanemi maganin zubar da ciki, dan haka ta samu Habib tace masa ta yadda sukoma Nigeria, ba karamin mamaki yayi ba yadda akayi ta yadda ta dawo Nigeria. Bayan sun dawo ne, taje inda tasaba samun maganin zubarda ciki tazo ta sha, seda ta kwana biyar tana zubarda jini ba wanda yasan me yafaru, da kyar tasamu jinin ya tsaya amma ba karamin galabaita tayi ba. Ammame bayan jinin ya dauke haka tacigaba da rashin lafiya, kullum ba lafiya tana kwance kusa  wata biyu taki zuwa asibiti seda taji tana neman ta mutu sannan ta shirya ta tafi Asibiti lokacin Habib baya nan, Asibitin dasuke zuwa taje sukayi mata gwaje2 suka tabattar mata tanada cikin wata uku da sati biyu, abun yabata mamaki dama cikin nan yana nan be fitaba, suka dubata suka bata magunguna, tana barin Asibitin bata zame ko inaba se chemist din da take karbar magani, tai masa bayani yabata wani maganin dayafi  wancan karfi, sannna ta tafi gida. Khadija na barin Asibitin, doctor Hisham yakira Habib ya sanar masa yanzu amaryarsa tabar Asibitinsu kuma tana dauke da juna biyu na wata uku da sati biyu. Habib yayi murna a take yaiwa Hisham transfer na kudi, tukuicin Albishir, yana katse wayar ya kira khadija "Madam sannu ya jikin naki" "Wayace maka banida lafiya?" *"Hisham ya sanarmin kina dauke da babyna, na wata uku Ashe shike wahalar min dake, Allah maji rokon bawa abunda nake ta nema tunda kikayi bari se yanzu Allah yasa aka kuma samu, Masha Allah, Allah yarabku lafiya my deeja" hade rai tayi kaman tana gabansa amma ta maze "Hmm Hayatee ka kyaleni, nasha magani duk jikina ya mutu" "Eyya sannu, i wish ina kusa danamiki tausa, amma a satin nan zan dawo Insha Allah" "shikenan se anjima" ta kashe wayarta, lallai doctor Hisham munafikine shine har ya kira yagayawa Habib, to gara ma yadena rawar kafa dan "kafin kadawo na zubar dashi ta rariya sedai kai yadda zakayi se burina yacika, senayi karatu me zurfi a abroad " Haka takuma shan maganin zubar da ciki ta dinga malalar da jini, ta kira Habib tagaya masa hankalin sa ya tashi sosai, amma bata gayamasa wani abu ta shaba, yakira doctor Hisham ya sanar dashi, har gida sukazo don duba khadija, dole suka dauketa zuwa Asibiti, da kyar aka ceto ta saboda tasha wahala sosai, a satin Habib ya dawo an rike Khadija a Asibiti ana bata kulawa ta musamman still akayi scanning still cikin yana nan be fitaba, doctor Hisham ya gano tayi Amfani da Abortion pills amma be gayawa Habib ba. Ya sameta ya dinga mata nasiha, sannan yace idan makamancin haka yakuma faruwa ze sanarda Habib gaskiya, ze gayamasa tana shan Abortion pills ne. Sannan doctor Hisham ya sanar da Habib cewa zata samu sauki ya kwantar da hankalinsa. Tunda Habib yasamu labarin cikin nan yakuna tattare a gurin khadija, yake matukar lallabata, itakuwa khadija batun cikin nan ya tsaye mata a rai, sam bata kaunar cikin nan, ga cikin ya hanata sakat saboda laulayi yauda lafiya gobe ba lafiya Habib yana bata kulawa iyayinsa amma ita kawai yadda zata zubar da cikin nan takeyi, takuma shiryawa ta tafi tasamu me chemist din nan tace masa ita so take inba ze iyaba ya hadata da wanda zasu ciremata cikin nan. Me chemist din nan ya nuna mata illar yin hakan zata iya rasa ranta kokuma tajawa kanta mummunan ciwon daba lallai ta warke ba. Haka khadija takoma gida, duk yadda zatayi cikin nan ya zube wannan karon kin fita yayi, dukda basa jituwa da dangin Habib amma sunyi murna da cikin nan nata, Abun duniya yakara hadewa Salma, tarasa meyake mata dadi, gaba daya Habib ya canza kaman ba Habib dinta dasuka sha soyayya a bayaba, ga sharri da khadija take mata taita hadasu rigima da Habib, ga rashin lafiya data ketayi, tana zuwa  Asibiti Akai mata gwaje2, aka sanarmata mata jininta ya hau sam hankalin Habib da nutsuwarsa ya tattarasu akan Khadija. Salma ta shirya taje maiduguri tasami mahaifiyar Habib tace mata dan Allah tasa baki Habib ya saketa bazata iya zama dashi ba ta gaji, mahaifiyar Habib tai kokarin bata hakuri amma ta fashe da kuka "mama wallahi in Habib be sakeni ba zan iya rasa raina, dan Allah ki amince ya a raba Aurenmu" mahaifiyar Salma ma ta yadda tace a sakar mata yarinyar ta baze yuwu a kashe mata ya da bakinciki ba. Mama takira Habib tace tanason ganinshi ya shirya ya tafi. Koda yaje maiduguri mama tagaya masa abunda Salma ta bukataHabib kuma yace besan zance ba, mama tace yadda Salma takeson Habib harta bude baki tace ya saketa lallai abun ya kai makura dan haka ta goyi bayan ya saketa ta huta haka, Salma taje ta samu Habib tace "Habib nasoka tun bansan meye soba, ka koyaddani sonka, Habib ina maka sona gaske shiyasa banason ka kasance cikin wanda Allah ze hukunta ranar Alkiyama, Habib banason Allah yakamaka da laifin rashin adalci a tsakanin matanka, shiyasa nakeso ka sakeni dan Allah Habib, sakina shize kara tabattarmin har yanzu akwai tausayina da kaunata a zuciyarka ka sakeni Habib " tana zuwa nan a maganarta ta sume a gigice Habib ya dakko ruwa ya zuba mata amma bata tashiba haka aka kaita Asibiti jininta ya hau sosai, kwanam ta guda da wuni a asibiti sannan ta farfado, koda ta farfado da kuka ta farfado akan dan Allah Habib ya saketa, Mama ta titsiye Habib tace seya saki Salma, "Mama wallahi bazan iya sakin Salma ba ina sonta" "Kana sonta ka hada kai da makirar matarka kuke neman kasheta, Ka Saketa kokuma in maka baki" Jiki a sanyaye ya furta ya saketa saki daya. Take Salma tayi ajiyar zuciya tareda murmushi tace "Nagode Habib ina maka fatan rayuwar Aure managarciya da matarka, Allah yabani mesona har abada" Habib yayi zarya maiduguri akan Salma ta dawo amma fafur aka rasa me goya masa baya, Salma kuma tace itada gidansa har gaban Abada!!! Khadija kam ko a jikinta, Murna ma tayi tace zata cigaba da rayuwarta yadda takeso, dama kishi da ita se wadda tayi gagarumin shiri, ganin yadda Habib yatada hankalinsa yasata tayi duk yadda tayi ya manta da babin Salma suka cigaba da Rayuwarsu. Ba karamin kaduwa Saudat tayi ba dataji labarin Salma ta bar gidan Habib, bata taba tunanin hatsabibancin khadija ya kai taraba Salma da Habib ba. Dan haka abun yakara yiwa Saudat ciwo, yanzu duk wannan uban gidan da uwar dukiyar ita kadai ce matar gidan. Nan take taji Ranata yakara baci, "zaki gane baki da wayo khadija wallahi sena miki Abunda ga dukiya amma seta gagareki ci cikin kwanciyar hankali" Haka khadija tacigaba da rainon cikin da tayi kokarin yafita amma yaki. Wata tara labour yazo amma bazata iya haihuwa da kanta ba se cs akai mata aka ciro mata da namiji kato kaman Habib yayi kaki ya tofar saboda kama. Seda akayi sati biyu ta warke saboda cs din da aka mata sannan akayi gagarumin shagalin suna, sam be gayawa khadija sunan dazesawa jaririn ba se ranar suna, ya sanar da sunan yaron ABDUL JALAL, sunan mahaifin Salma kenan!!!! Tabdijan da alama Habib ya debota da zafi sunan baban Salma fa yasakawa dan khadija. A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu 'oinku Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za' a fara posting din Littafin ABDUL JALAL  Facebook tundaga farko Insha Allah, za'afara posting a group din AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy's girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣3️⃣76 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ Saudat ta danyi shiru sannan tace "kumafa hakane amma tayaya kenan?" "bari muje gida zan gayamiki meyakamata kiyi" Watarana Khadija ta shirya da dauki Jalal taje gidansu, suka wuni acan se magariba suka koma gida a hanyarsu takomawa ta hadu da Kabir, amma ta dauke kanta kaman bata sanshiba ta zuge glass din motarta tai tafiyarta, Kabir yayi mamakin girman motar da khadija take ja, kana ganinta zaka san tana cikin daula da jin dadi, gefe ga danta kaman ba dan hausawa ba kyakyawa dashi. Taja motarta tabar gurin ya dubi shikuma irin rayuwar dayakeyi ta wahala, ya gyada kai yace "wallahi khadija senayi silar kin fito daga wannan daular dan bazaki yaudareni a banza ba" Haka Rayuwa tacigaba da gara Kabir wanda hakan yasa yafara shaye2 miyagun kwayoyi. Bayan Rabuwar Salma da Habib an takuramata a gida akan lallai setayi Aure, wani Ambassador yafito yana sonta, akayi bikinsu, abun Allah ko wata guda batayi a gidansa ba Allah yasa ta samu ciki, Masoya da yan uwa sun tayata murna sosai har Allah yasa ta sauke lafiya ta haifi namiji akasamasa Mahmud, bayan mahmud ta haifi Yusuf da Yasmin, Mahmud shine wanda mukazo dashi, zakiga yana kama da Jalal. Amma Allah yayiwa Ambassador Ahmad Rasuwa shekaru biyar dasuka wuce. Dan haka tai zamanta a England. Khadija ta karbi makudan kudi a hannun Habib tafara kasuwanci, tana zuwa kasashe daban2 tayi sarin kaya ta sayar, tana da manyan shaguna a fadin kasar nan, wanda dukkansu mallakinta ne. Saudat ta haifi diya mace, bayan danta munir, wadda itace Ilham, khadija taita zaryar Asibiti akan tanason takuma samun ciki, amma abu ya gagara har wasu kasashen sukaje da Habib amma aka sanar matada bazata kara samun ciki ba, Mahaifarta tasamu matsala sakamakon rauni datayi saboda yawan shan abortion pills datai tayi, khadija ta damu sosai har tagaji ta hakura. Saudat ta nunawa khadija komai ya wuce, Khadija ta dinga mata barin kudi baji ba gani, Khadija tagayawa Saudat halin da take ciki "Saudat naso ace nakuma samun haihuwa, ko mace in haifa, Jalal yasamu dan uwa" "tunda Allah yabaki Jalal dinma ai ki gode masa, dan wani har ya mutu bazega kwansa a duniya ba" Gefe guda Saudat tayi farinciki jin cewa khadija bazata kuma haihuwa ba, hakan yasa takara kudurcewa ranta seta Rama abunda Khadija tayi mata akan Jalal. Ummi ta dade bata haihu ba, sunyi girma lokacin da Allah yabata haihuwa, Tunda Allah yasa Ummi ta haifi yarinya mace, hakan yakara saka Jalal zaunewa a gidansu Jawwad, kullum suna tare suna Rainon Kanwarsu, Jalal yaitabin Uncle Aliyu kanin mahaifin Jawwad yana cemasa dan Allah asakawa jaririyar nan sunansa wato Jalal. Aliyu yabiye masa yace Jalal sunan mazane amma insha Allah zanmaka takwara, karka damu, Ranar Suna yasamata Jalila, yace yayiwa Jalal takwara, Habib yaji dadin karar da Aliyu yai masa, yadda suke nunawa dansa soda kauna, duk rikicin da Jalila takeyi intaji muryar Jalal yanzu zata fara murna, gaba daya Jalal jiyake Jawwad da danginsa sune komai nasa. Fafur khadija tahana adinga kai Jalal dangin mahaifinsa, acewarta tunda basa kaunarta danta ma basonshi suke ba, Amma a haka Habib yake zuwa yakaishi ko a ranar ne su juyo, duk dangin Habib sunsan Jawwad, Jawwad yanajin yaren kanuri kaman yadda Jalal ma yafara jin fulatanci saboda kauna da shakuwa. Jalila na karama sosai Mahaifinta yanemi Aiki a garin kaduna yatafi da Ummi da Jalila, saboda yawan tsangwama da iyalannasa ke fuskanta, dukda lokacin Jalal da girmansa yashiga secondary, amma haka ya dinga rikici yana kuka, Shi be yadda a tafi da Jalila ba ya saba da ita. Tare yake cin Abinci da ita, komai yagani na wasa se yace ita ze kaiwa, komai yaci seya ajiye nata. Jalal ya dade yana damuwa akan barin gari da uncle Aliyu sukayi, Abun har yafara bawa khadija haushi, yadda ya tashi hankalinsa akan wanda ba dangin iya ba na baba sun bar gari. Ummin Jalila seda tayi kuka lokacin dazata bar kano, saboda ta riga ta shaku da yaranta Jalal da Jawwad Bisa ga Shawarar zulaiha, Saudat seta dakko Ilham tace ga Ilham nan tabawa khadija ta dinga debewa Jalal kewa ze manta da waccan yarinyar, khadija tayi murna da wannan kyauta da Saudat tayi mata, lokacin Ilham nada shekara takwas khadija ta karbeta, amma sam Ilham basa shiri da Jalal dan sam bata da kunya shikuma ga son girma, dan haka har dukanta yake, Jawwad yaita masa fada yace Ilham kaman Jalila takefa itama kanwarmuce, Jalal yace "Jalila ba mara kunya bace, ni Jalila ce kawai kanwata ba wannan ba" Har yanzu khadija bata fasa yawace2 kasuwanci ba, Jalal ya tashine a tsakanin kwararo ba bu shakuwar uwa a tareda shi, Allah ne ya dubi Jalal ya hadashi da mutanene kirki irin dangin Jawwad. Jalal yanada matukar kwakwalwa, sarrafa abu da haddace shi baya masa wahala, dan suna Jss2 suka Sauke Al'qur'ani, suka juya hadda, wanda wannan nasara tasu da taimakon Allah da taimakon Ummine da mijinta, Saboda itake tsayawa taga sun iya dukkan wani karatu dasuka koyo a makaranta, sunyi nisa sosai a haddarsu dan sunkai izufi Arba'in Rayuwar Jalal tafara samun matsala, Jalal yana SS2 a secondary komai nasa yafara lalacewa, sakamakon haduwa da miyagun abokai dayafarayi, Jalal yanada kyauta ga faran faran da mutane, ba babba ba yaro kowa nasane, duk wanda yakeda bukata Jalal ze dauka yai masa, hakan yasa har manya suka fara girmama shi suna gaisheshi. Jalal lokaci daya ya canza watarana khadija bata kasa tana can harkar kasuwancinta daga Daddy se Jawwad da Jalal a gidan Ilham kuma tana gidansu, 'yan fashi suka shigo cikin dare, suka kama masu gadi suka kullesu, suka shiga cikin gidan, Habib yace su dauki duk abunda sukeso a gidan amma karsu taba masa yaransa, suka sakasu kneel down, sannan tattara abunda suka samu a gidan har zasu tafi dayan ya juyo ya saita Habib da bindiga, gaba daya yaran suka fara kuka, dan fashin ya musu tsawa amma suka ki yin shiru, dan fashin ya saita Jawwad yace "bari in kashe tilon dannaka dan yafiye maka komai a duniya kuma da alama yana sonka sosai" zatonsu shine Jalal, dan haka ya saita Jawwad da bindiga, Habib yace dan Allah karku kashemin shi, gaba daya yaranane, tunda kun samu abunda kuke so dan Allah ku kyalesu garani kukasheni, dan fashin nan yamasa banza ya dan kunamar bindigarsa, kawai Jalal ya mike tsaye, bullet din ya shigeshi a gefen kirjinsa, yan fashin na ganin haka, suka kwashi abunda suka kwasa suka gudu. A gigice Habib da Jawwad sukayi kan Jalal amma yana kwance kaman ba rai jini nata malala a kirjinsa, hakan ya firgita Jawwad kwarai shima ya suma a gurin, misalin karfe uku na dare haka ya daukesu ya tafi dasu Asibiti. Da kyar aka cire bullet din a kirjin Jalal, ya galabaita saboda a gefem zuciyarsa bullet din yasameshi, shima Jawwad da kyar aka samu ya farka. Wannan fashi ana kyautata zaton dasa Hannun Kabir a ciki, amma ba'a tabattar da hakan ba. Seda Habib ya kai su Jawwad Dubai aka dubasu acam sannan hankalinsa ya kwanta, seda akayi kwanaki sannan khadija tasan meyafaru. Akaita zuwa duba Jalal, Allah yatemakshi ba'a dadeba ya warke suka koma makaranta. Mahaifin Jalal ya hada mahaifin Jawwad da manyan mutane akan harkar kasuwancinsa, wanda silar hakan Allah yasawa mahaifin Jawwad nasibi a kasuwancinsa, yasai gida a Sharada NNDC, suka koma, Jalal yasamu daddynsa yace masa dan Allah yanaso yasaimusu gidan dayake makawabtaka danasu Jawwad sukoma, haka kuwa akayi suka tattara suka koma kusada juna, ga gida ga gida. Har yanzu babu jituwar Arziki tsakanin Jalal da Ilham, ba Ilham bama kawai hatta mamanta Saudat basa shiri saboda hakanan Allah be hada jininsuba, wataran Saudat tazo gidan, tabawa Jalal kyautar turare, da yanuna baze karba ba, Amma Jawwad yasashi ya karba, yace masa ba a haka mutum yamaka kyauta ka gwaleshi, Tunda Saudat uwace a gurinsa, Ranar suna kwance cikin Dare, Jawwad yaji kaman ana jijjiga gadon dasuke kwance dan haka ya tashi da sauri ya kunna fitila, yaga Jikin Jalal yanata Kakkarwa, abun yabashi tsoro sosai, ya tattaba Jalal yace "Dan uwa meyasameka kobaka da lafiya ne" Jalal ya masa shiru, koda Jawwad ya cigaba da magana se Jalal ya bude idonsa seda Jawwad ya firgita wani irin Green yaga kwallarsa tayi, ga jijiyoyin kansa sun tashi sunfito sosai har goshinsa, Jalal ya rike Jawwad yace "Jawwad wani hayaki ya shiga jikina, kamin Addu'a amma karka gayawa kowa, ka dauki turarenda Maman Ilham tabani ka jefar dashi, daga ciki hayakin yake fitowa" Jawwad yadinga karanto masa duk abunda yazo bakinsa a haka har bacci ya dauke Jalal, sannan Jawwad ya dauke turaren ya boyeshi, Jawwad beggayawa kowa ba kaman yadda Jalal ya bukata. Tundaga nan Jalal yafara zama wani iri, Suna SS2 Jalal yafara haduwa da miyagun abokai, ciki hada wani hatsabibi waishi Jabir Junaid, suna ce masa Jeje, gaban Jalila seda yafadi jin an ambaci Jeje, "tunda Jeje ya shiga Rayuwar Jalal komai nasa yafara lalacewa, ya koya masa shaye2, Jawwad yai kokarin ya raba Jalal da Jeje amma abu ya gagara, Jawwad be gayawa kowa Jalal yafara shaye2 ba, yayai2 amma Abun na Jalal kullum gaba yakeyi, a haka har mutane suka fara ganewa. Habib yashiga tashin hankali daya fuskanci Jalal yafara shaye2, ya shiga dakin Jalal ya tarar dashi a kwance ga kayan shaye2 Jawwad na gefensa yayi tagumi, hankalin daddy ya tashi, ya tambayi Jawwad me yake faruwa haka, nan Jawwad yaiwa daddy bayanin komai, amma be gayamasa tun asalin meya faruba, ya dai ce masa shima kawai gani yayi Jalal yana shaye2, yayi2 ya dena yaki Habib yashiga tashin hankali jin tilon dansa yafada mummunar Rayuwa, A lokacin khadija kusan watanta guda bata Nigeria, Bayan Jalal yadena maye ya zaunar dashi yaita masa nasiha yana masa fada, amma Jalal fadan nan ko a jikinsa. Bayan dawowar Mummy Habib ya dinga yi mata fada yana cewa "Khadija a sanadin rashin kulawarki, da sakacinki Rayuwar dana ta tasamma rugujewa, Jalal yakama hanyar lalacewa, wace irin uwace ke" A fusace tace "Nifa baangane inda maganganunka suka dosa ba, da can bakasan inada sakacin ba se yanzu?" "ABDUL JALAL yafara shaye2, shaye2 yakeyi" Zare ido tayi "Kamar ya shaye, ni dana baya shaye2, Jalal baze hakaba" "koki yadda kokarki yadda yarage naki, sekije ki bincika" a gigice ta fita tanufi dakin Jalal, aikuwa tana shiga ta tarar dashi yanata busa hayaki, cikin tashin hankali ta karasa cikin dakin "Jalal mekakeyi haka? Shaye2 fa kakeyi" Banza yamata yacigaba da abunda yakeyi, ta karaso ta nufo inda yake amma ya dakamata tsawa "Karki sake kizo inda nake tunda ba kyason bakya kaunata, bakida wata magana dazaki gayamin lokaci yariga ya kure, Mummy da hannunki kika rusa Rayuwata, kin fifita son zuciyarki akan Rayuwar danki, kifita ki barmin dakina, bana kaunar ganinki" "Amma Jalal........ Jifa yafarayi da duk abunda yaci karo dashi cikin tsawa yake cewa" Kifita Nace bana son ganinki, kije kudi su baki farincikin da duk kike bukata, kifita kibani guri, Jawwad ne yashigo dakin da Sauri yaga abunda Jalal yake da sauri yaje ya rikeshi, Mummy ta juya cike da damuwa tabar dakin. Tundaga wannan lokacin Rayuwar Jalal tashiga rudani, yadena jin magana ibada ma baya iyayi, yadena ganin girman kowa, yadena ganin mutuncin kowa, kowa ya janye dansa daga shiga huldar Jalal, Jawwad ne kawai be barshiba, da mahaifiyar Jawwad ta fuskanci Halin da Jalal yafada setayi kokarin ta rabasu, saboda kar itama nata dan ya lalace. Amma abu ya gagara mahaifin Jawwad yace indai tai kokarin raba Jawwad da Jalal batayi adalci ba Addu'a yakamata tayi musu gaba daya, wasa2 abu yafara shafar kwakwalwar Jalal ya manta abubuwa saboda shaye2, a haka suka gama secondary suka shiga jami'a, Jawwad na mechanical engineering, shikuma Jalal yana karanta civil engineering, shima a university din haka yakara lalacewa da shaye2, kullum Jawwad kokari yake yaga Jawwad yadena abunda yakeyi amma abu ya gagara. Suna level 1 kakar Jalal mahaifiyar khadija ta rasu, Jalal yazama rikakken dan shaye2, yazamana in har Jawwad bega Jalal ba to a Club ze tsintoshi. Dukdahaka lokaci zuwa lokaci Jawwad yana raka Jalal maiduguri su gaida dangin mahaifinsa Khadija tacewa Jalal bata yadda yakuma zuwa maiduguri ba, inyakuma bata yafe ba tunda dangin mahifin sa basa sonta shikuma Jalal yace sedai katta yafe, ita mutum nawane sukace basu yafe mataba, Jawwad yace masa be kamata yadinga zuwaba tunda tace bazata yafeba hakkinta ze iya kamashi, dama dangin Habib tuni suka dena zuwa saboda wulakancin Khadija. Jalal yana shekararsa ta karshe a Jami'a abun nasa yakara ta'azzara, da yana iya karatu dukda yana shaye2, yana da kwakwalwar sosai dan yana daga cikin wanda ake ji dasu ga barin kudi dayakeyi, amma a final year kwakwalwar Jalal takara birkicewa, yakasa karatun ga mantuwa, makarantarma gaba daya yadena zuwa, se yawon club, abokansa yan iska suka kara like masa saboda yadda yake sakar musu kudi, gaba daya iyaye suka hana yaransu shiga harkarsa, suka shiga tsangwamarsa da an ganshi se a tashi abar guri yazama abun kyama, kowa ya gujeshi se Jawwad, hakan yakara tunzurashi yafara rashin mutunci yadena ganin girman kowa, memakon amasa nasiha ko Addu'a se akaita Allah wadaran da halinsa, hatta dangin Khadija basason yaje inda suke bayan abaya harsosuke yaje saboda sunsan indai yaje seya musu barin kudi, ana cikin wannan halinne Ilham ta nuna tanason Jalal a haka, hakan ya tabattar da akwai abunda Ilham suke shiryawa dan daukar fansa akan Khadija da danta, Amma hankalin khadija be kaiba itama ta goyi bayan hakan tana ganin tahaka ne zata wanke zuciyar Saudat akan abunda taimata, har zuwa wannan lokaci ake wannan turka turkar. Kakar Jalal mahaifiyar Habib tayi kuka lokacin data samu labarin yanda jikanta yakoma, gashi kiri kiri an hanashi zuwa inda take da wannan bakincikin takoma ga Allah, tanawa jikanta fatan shiriya, amma ranar dasukazo gaisuwa suka juya, Mummy tahana Jalal kwana, wannan abun yakara bakantawa danginmu Rai, muka dauke kafarmu daga gidan Habib tsawon shekaru. Babban abun godiya ga Allah shine Jalal baya neman mata ba ruwansa da mata, ko a makaranta ko a club ba ruwanshi dasu, ze sha giya yayi askin banza, yayi rashin mutunci, baya ganin girman kowa musamman Mummynsa dayake ganin sam batayi masa adalci ba a matsayinsa na danta, tunda ta goyi bayan ya auri Ilham, da nufin ta wanke laifinta na baya yakara jin haushin mahaifiyarsa. Antin Jalal ta kamo Hannun Jalila da fuskarta ta jikebda hawaye tace "Jalila nagaymiki iya abunda nasani gameda rayuwar Jalal, wani abun nima har yanzu ban saniba, nasan zanbarki cikin dunbin tunani, amma Jalila bantaba zaton Akwai wanda ze iya karkata hankalin Jalal ba, duk lokacin daka dakko yimasa Nasiha ko ransa yabaci sekaga yafita hayyacinsa idonsa ya canza kala yafara jifa da abubuwa, kin dakko hanyar daidaita Rayuwar Jalal amma bata sigar dakika fara ba, duk lokacin dakika batawa Jalal rai seya gayamin, Jalila akwai abubuwa da bangayamiki ba saboda ba'a bakina yakamata kijiba, wannan tarihin danabaki nagaya mikine bisa Amincewar Jalal, yanzu mu tashi kinga azahar tayi wanka zanyi inyi Salla zamu juya. Jiki a sanyaye Jalila ta mike suka nufi cikin  gidan, Jalila kam waje tayi, ta tafi gida, tana zuwa gida ta tarar da Nana a harabar Gidan, Nana tana ganinta tace "Jalila ina kika shiga ne? Tun dazu nake nemanki nakira layinki amma wayar na daki" Jalila batace uffan ba ta wuce daki, tana zuwa ta zube akan Gado, ta fashe da kuka "ban kyautaba, Mummy meyasa? Meyasa kikayi haka, Ashe shiyasa Jalal yake cewa Kinfiye sonkanki, Saboda kudi da son zuciya kin bata farincikin mutane da dama, kinyi sanadin Rayuwar danki, Jalal ka yafemin bansaniba" takara fashewa da kuka A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu 'oinku Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za' a fara posting din Littafin ABDUL JALAL  Facebook tundaga farko Insha Allah, za'afara posting a group din AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy's girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️ Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣4️⃣77 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ Sosai Jalila take Hawaye, tareda surutai a hankali, Nana ce ta shigo dakin, da sauri Jalila ta goge hawayenta, zuwa tayi ta zauna ta kalli Jalila "Jalila lafiya kuwa, meyasameki? Meyasaki kuka kuma ina kika shiga tun dazu nake nemanki" Jalila bata san wace tambayar yakamata ta fara amsawa Nana ba, Jalila ta dan girgigiza kai tace "Bakomai karki damu" "Yazakicemin ba komai, kuka fa kikeyi" "Nana bakomai" "Shikenan tashi muje, Bakin su Jalal zasu tafi, taso Anty Amina tace inkiramata ke" se yanzu Jalila tasan sunan Antin Jalal dinma, ba musu ta mike suka fito tare, suna shiga gidan suka tarar dasu sunfito zasu tafi, Mahmud ya kalli Nana yace "Nana gashi zan tafi bangama ganinki ba" murmushi Nana tayi "Nima bangama ganinka ba, kaje kayi zamanka a England, memakon kadawo Nigeria muma mu amfana da iliminnaka, kaje se wani uban kumatu kakeyi" "Allah hajiya Nana, ke bakiga yadda kikakoma bane, kinzama wata madam, yanzuma Anti Amina mukayi waya, zasu zo nan kano, shiyasa nadawo nace nima suzo dani zan dade a Maiduguri kafin inkoma England" ya kalli Nana yayi kasa da muryarsa yace "Nana wannan ce Jalila ne?" "itace kasanta ne?" "A'a na tambayekine kawai, naga tana kama da wata ne, just forget, bani lambarki" "Seka biya tukuna" murmushi Mahmud yayi, "Yimata kudi ko nawane imbiya" Nana tai dariya ta karbi wayarsa tasamasa lambarta, Suna tsaye suna jira Jalal yafito suyi Sallama amma tunda Jalila taimasa abun nan da safe, ya shige daki yaki fitowa ko sallama suyi, Jawwad yanata masa magiya amma yaki bude kofar nan. Anti Amina takamo hannun Jalila tayi gefe da ita, ta kalleta tace "Jalila kuka kuma? Meyasa? Munasa ran samun nasarar daidaita rayuwar Jalal ta hanyarki amma muga karaya a taredake, karkimana haka Jalila, banbaki labarin Jalal dan isaki damuwa ba" kaman ta ziga Jalila takuma fashewa da kuka, Rungumeta Anti Amina tayi tana sharemata Hawaye cikin kuka Jalila tace "Anty dana san haka Rayuwar Jalal take daban zama daya daga cikin masu kara rusa farincikinsa ba nasan na dade ina bata masa Rai amma....... " Jalila kina yimasa hakane dan inyaji haushi ya dena abunda yake nasani karki damu kinji kidena kuka" Jalila ta jinjina kai, suka musu rakiya har mota suka daga suka tafi. Jalila jikinta a sanyaye takoma gida, daki takuma komawa ta kule akan gado tayi shiru nan ta shiga tunani daban2, "Kenan Kabir shine Oga Kb? , Jeje yataka Rawa gurin lalacewar Jalal, menen alakar Kabir da Jeje?" dafe kanta tayi tai tagumi hannu bibiyu tai shiru sekuma wani abu yakuma fadomata a rai "Saudat tabawa Jalal turare, aranar yadinga karkarwa cikin dare yana firgita, kenan Saudat ma wani abun tayi masa kokuma mene? To wa zangayawa? Mema yakamata inyi ne? " "Yasalam" Jalila ta furta da karfi tareda dafe kanta, da Hanzari Nana ta shigo dakin ta tarar Jalila ta dafe kai tana kuka "Jalila lafiyarki kuwa? Tun dazu nake tambayarki meyasameki amma kinki gayamin se kuka kike kinga yadda idonki yayi Ja kuwa?" Murmushin dole Jalila ta kakalo, "Karki damu kaina namin ciwo sosai, allow me to rest" ta ture Nana ta kwanta, Nana ta dade tana mamakin meyake damun Jalila haka? Yadda Jalila taga Rana haka taga dare, banda zunzurutun tunani da tambayoyi ba abunda ke kai komo a zuciyarta, ga wani irin tausayin Jalal dake ratsa zuciyarta, antarwatsa Rayuwarsa akan abunda lokacin da ake laifin baya duniyar, gaskiya Mummy bata cancanci zama uwa ba, ta fifita duniya akan Rayuwar danta. Har gari ya waye Jalila idonta biyu, Halima da Nana ne suka hada breakfast, nanma sukayi sukayi taci Abinci takici, Abun yafara bawa Nana tsoro, dan haka taje tagayawa Maama halin da'ake ciki "Nono kikeso inkamota in bata ko goyata zanyi inta jijjigata?" "Maama bahakaba, at least yakamata musan meyake damunta, kartayiwa kanta illa, tun jiyafa bataci Abinci ba tanata kuka, kinsan batada cikakkiyar lafiya fa?" A fusace Maama tace "fita kibarmin daki, kar Allah yasa taci, inta kashe kanta aita huta" "Amma Maama.... " Bazaki fita ba sena makeki" ba shiri Nana ta fito, ta nufi part din Jawwad amma bayanan, takira wayarsa harta katse be dauka ba, daki takoma tazubawa Jalila ido data kwanta ta rufe ido, amma hawaye nabin gefen idonta "Jalila dan Allah kitashi kici Abinci, wallahi gaba daya zuciya ta babu dadi, na damu matuka, dan Allah kici wallahi inbaki ciba nima bazanci ba" A hankali Jalila ta bude ido, ta mike zaune ta kalli Nana tace "zubo muci, banason kizauna da yunwa" Nana ta zuba Abinci amma Jalila ta dan cakala ta barshi. Wunin Ranar Haka Jalila tayi duk surutun nan amma yau tsit kakeji, Nana tayi tambayar harta gaji ta samata ido. Da daddare Jawwad ya shigo yasamu Maama a palour yake gaya mata Ankai Jalal Asibiti. Da sauri Jalila ta mike ta fito palour ta labe Maama tace "meysameshi haka?" "kinsam jiya yan maiduguri sunzo, kuma dai kinsam babu jituwa tsakaninsu da Mummy, andai bata masa rai yaje ya kulle kansa a daki, yafasa abubuwa sosai sannan cikinsa da yunwa ya sha wani abun bansan meyasha ba, da kyar na bude dakin dazu, naganshi a sume shine muka kaishi Asibiti, yanzu can zantafi zan kwana dashi" Maama ta kalleshi "ohhh Jawwad Allah yayemaka wannna Jaraba, wannan yaron Jalal kullum seyajanyo abun daze hanaka hutawa, sekayi tayi ai wahalalle" Murmushi Jawwad yayi yace "Maama kenan, ai duk dan halak baya manta alkhairi, bari in tafi seda safe" ko kallonsa bata kumayiba, har ya juya ze fita Nana tace "Yaya Jawwad amasa sannu dan Allah, kuma wallahi Baby ma inaga wani abu na damunta tunjiya kuka takeyi, taki cin Abinci da kyar nasata taci kadan" "Haba dai? Kuma kin tambayeta meyake damunta?" A fusace Maama tace "fita katafi inda zaka, bazasu hadu sukasheka ba kowa  ya kwaso iskancinka akanka ze sauke, kaidabaka san ciwon kanka ba" Jiki a sanyaye Jawwad ya juaya yafita, Jalila takoma daki ta kwanta tai shiru tamarasa tausayin wa yakamata taji. Jin batun Jalal na gadon Asibiti abun yadameta. Har gari yawaye Jalila nata kasa kunne taji wanda zeyi zancen halin da Jalal yake ciki, har wajen azahar shiru, Jalila tace "Nana naji kaman yaya Jawwad yace an kai Abokinsa Asibiti?" "Eh acanma ya kwana, har yanzu kowaya beyoba, dazu Maama takirashi a waya amma bata shiga" "to ya jikinnasa?" "Nima bansaniba wallahi, amma bari mujira zuwa anjima" Jalila ta gyada kai, ta dakko wayarta tana dubawa taga missed calls rututu Call logs dinta tashiga tatarar da missed calls na Zahrah, Jalila ta kirata a waya bugu biyu ta dauka "Salam alaikum, Jalila ina kika shiga tun jiya nake kiran wayarki amma ba kya dagawa" "Am sorry ina wani mahimmin abune, se yau na dakko wayar, ya akayine?" "Hmm Jalila sarkin Sabga, dama gayamiki zanyi anbada belin Baban Samir Fa shida duk wanda aka kamasu, shine nace kina ganin ba abunda ze faru kuwa insuka ganomu" "Zahrah karki damu babu abunda ze faru, koda anganomu muka shirya wannan abun, to ki zame kibanni ba ruwanki balle baza'a gane ba, Burina ya cika na tonawa duniya asirin ya da Uba, duk wani cin zarafi da wulakanci dasu Saleema sukeyi dole sudena, saboda wannan mummunan abu. Kunya dasuka aikata, Amma tabbas zankuma gauraya dasu, Alhaji Kabir da Jeje, Nagode kigaida Umma" Jalila ta kashe wayarta, tacigaba da duba kiran da akayi mata takuma cin karo dana Hanan, da sauri ta kira Hanan, seda takusa tsinkewa sannan Hanan ta dauka, tace "Se yanzu zaki kirnaiko? Tun jiya nake kiranki amma kinki dagawa yar wulakanci kawai" "Yi hakuri Hanan, lokacin bana tareda wayar se yanzu na duba nagani" "To na hakura Allah ya temakeki, dama zamuje Bauchi nan da 2 weeks, Daddy yace zamuzo mu tambayi Abba inya yadda mutafi dake Inna taganki" Jalila tace "Hanan zanyi murna da zuwanki, ina cikin matsala inason inganki" "Matsala kuma Jalila? Meyafaru?" "Hanan na dade ina tafka kuskure, yanzu ina nadamar abunda nayi, abun baze yuwu ta waya ba, nafison mu hadu" "Subhanallah Jalila nadamar mekuma? Zaki banni cikin damuwa da tunani, ki gayamin menene?" Jalila ta dan share Hawaye tace "Hanan for all this time i have hurting Jalal, calling him with different bad names, he is innocent, Hanan an gayamin tarihinsa, Jalal abun a tausaya masane, inajin kunyar hada ido dashi, Hanan ban kyauta ba" "Is ok kidena kuka, ai duk dan adam baya wuce aikata kuskure, Calm down, abunda na dinga nunamiki kenan a baya amma baki ganeba, baka yankewa mutum hukunci kai tsaye akan abunda kaga yana aikatawa, idan nazo zamuyi maganar, amma ya akayi kikasan ba laifinsa bane?" " Ai baze yuwu a waya ba, se mun hadu" "Amma yakamata ki wanke lefinki" "Hanan tayaya, tunda na riga nayi" "Hakuri zaki bashi mana" "Hakuri kuma?" "Eh mana, yakamata kinemi ya yafe miki" "mhmm Inasu Yaya Abdallah? Inason ganinsa ma ina neman yamin wata Alfarma inze iya" "Wace Alfarma kenan?" "Ina ruwanki semun hadu nida shi, ki gaida Baba" "Hmm shikenan zeji Insha Allah" sukayi Sallama Jalila kasa jurewa tayi ta dau waya takira Jawwad amma baya dauka, haka ta hakura. Washegari shiru2 Jawwad be dawo ba. Har bayan Azahar gashi baya daga waya, hakan yasa Jalila ta kara shiga damuwa, ta fito harabar gidan, dan tasamu ta kadaice tayi tunani, tana nan Zaune tayi nisa sosai a tunanin tarasa ta ina yakamata ta fara, gaba daya abubuwa sun hargitse mata. Motsi taji abayanta yasatayi saurin waigawa, Jawwad ta gani a tsaye tai sauri ta mike tsaye. "Baby meke damunki hakane? Tun dazu nake magana amma kinyi shiru, gayamin meke faruwa?" Murmushi Jalila ta kakalo, "Yaya Jawwad bakomai kawai dai banji bane, ina ka shiga bana ganinka nakiraka a waye baka dagawa" "Jalal ne ba lafiya, na kaishi Asibiti na manta wayata a gida" "Meyasameshi?" Ajiyar Zuciya Jawwad yayi sannnan yace "jininsa ya hau, yana damun kansa dayawa, Jalal baya iya controlling bacin Ransa, yanada saka abu a ransa, ga kinsan shan taba yana kara saka hawan jini, amma Alhamdilillah jikinsa da sauki an sallameshi tare muka dawo gida" jinjina kai Jalila tayi "Allah yabashi lafiya" "Ameen Baby, meyasamin ke kuka kika kasa cin Abinci Nana ta gayamin" "Nikuma ai kaina ke ciwo kawai itakuma tabi ta damu, amma na warke ai" "Anya kuwa, karya ba halinki bane, fuskarki ta nunamin kina cikin damuwa" "bana cikin wani damuwa ni, kako ci Abinci naga kaman a gajiye kake" "Hmm wato ba kyason incigaba da tambayarki ko?" "bahaka bane, banaso ka zauna da yunwa ne" Murmushi Jawwad yayi, "Ina jin yunwa kam, samomana wani abun, Jalal ma beci Abinci ba, yaki cin Abinci wallahi, nayi2 amma yaki, Yana cikin damuwa sosai, anyway samo mana abunda yasamu in lallabashi koze ci" gyada kai Jalila tayi ta juya da sauri ta tafi cikin gida. Tana shiga palour ta tarar da Maama tana mata wani irin mugun kallon banza, Jalila ta dauke kai kaman bata san meke faruwa ba tai kitchen abunta. Ta dafa masa jallof spaghetti, ta hada da juice bayan tagaama take tunani yanda Maama ta zauna a palou  tana mata kallon banza, yanzu in tace zata kaimasa Abinci wani bacin ran zata jawa kanta dan haka ta kirashi a waya tace yazo ya dauka, befi minyi bakwai ba sega Jawwad yaje kitchen ya dauki Abincin. Har yazo ze fita Maama takirashi, yadawo ya zauna a gabanta yace "Maama gani, Allah yasa ba laifi nayi miki ba" "laifi kuma tun yaushe kake sabawa umarnina, minyi magana akan muna son hada Aurenka Naja amma har yanzu baka kumabi takan zancen ba, sekara shigewa wannan algungumar yarinyar kakeyi, ban isa ingayamaka magana kajiba ko?" "Maama dan Allah kiyi hakuri, na yadda in Auri duk wadda kikeso, amma bazan iya Auren Naja ba" "Jawwad kake kallon tsabar idona kake cemin bazaka iya Auren Naja ba" "Maaama Naja yar uwata ce bazankita haka kurum ba amma... " Yimin shiru badai akan waccan hatsabibiyar kake rawar kaiba, idan ina raye ayi ingani, tashi kabani guri" Jiki a sanyaye cike da damuwa Jawwad ya mike yabar palourn. Tunda yan maiduguri suka tafi Jalila bata kara saka Jalal a idonta ba dan sam yadena zuwa gidansu, ga Jawwad yanata complain akan Jalal bayacin Abinci yana damun kansa sosai, ga matsalar da Jawwad yake ciki shima Maama nata tursasa shi tace se ya Auri Naja, amma ita Nana ta tirje tace bazata Auri faruk ba an kyaleta, Jalila tarasa yadda zatayi taga Jalal, duk abun yafara damunta. Ga yaya Jawwad dinma ta dena ganinsa ko waya basa yi, yadena shigowa cikin gida. Zaman cikin gida ya isheta dan haka ta fito danta sha iska, ta fito ba dadewa Jawwad ya shigo yayi parking, duk taga ya dan rame, yafito ya kulle motar, takarasa inda yake "Yaya Jawwad wai meyake damunka hakane, ka rame kuma tun shekaranjiya ban kuma ganinka ba" cike da damuwa yace mata "Baby Jalal, yana nema ya kashe kansa" "Kamar yaya?" "Ankuma kwantar dashi a Asibiti, tun shekaranjiya ina can, banason inkira Daddy kar adaga masa hankali, idan Mummy taje gurinsa, seyace seta tafi bayason ganinta yanzu haka jikinsa yakuma rikicewa, yanzu haka tun jiya yana ICU, maybe yau zasu fito dashi" nan da nan jikinta ya hau rawa, cikin rawar murya tace "Subhanallah Allah yabashi lafiya, if you don't mind zan rakaka in dubashi" "Shikenan naji amma kibari seda safe in Allah ya kaimu zanzo muje" ta jinjina masa kai takoma cikin gida Yau Hannah har gidan Jeje taje nemansa tayi sa'a kuwa yana nan, Jeje yayi mamakin ganinta sosai "yau kece da kanki a gidana" "Eh nice amma kasan duk lokacin daka ganni bukatace ta kawoni, almost one week ina nemanka, bana ganinka layinka baya shiga, amma naji ana rumors ankamaka kai da megidanka a gidan karuwai meye gaskiyar lamari" shiru Jeje ya danyi ya kalli Hanna "Ni ina zargin dasa Hannunki akan abunda yafaru dani, shekara da shekaru inawa Oga Kb aiki inasamun rufin Asiri a gurinsa, ina hutawa da 'yarsa ba tareda yasani ba lokaci daya aka masa cunen gidan danake zuwa yakamamu, yanzu ya sallameni tareda cin alwashin seyaga bayana, wallahi Hannah indai dasa hannunki a wanna cin zarafin da' akamin bazaki tsira daga sharri na ba" Murmushi Hanna tayi sannan tace "Aidama karshen alwa kasa, kuma ramin mugunta kurarrene, Jeje idan har zanmaka wannan manakisar yan sanda suka maka kaida uban gidanka to wallahi da duk yadda zanyi bazaka fita daga hannun yan sanda ba daga kai harshi, dara ce taci gida kawai, kakoma kayi tunani ka sake nazari waze iya aikata maka haka, kasan innice nayi maka wannan aikin bazanji tsoron gayamaka bako? tunda irin tarbar danasamu daga gurinka kenan shikenan nagode ni na tafi, amma kakiyaye shiga hanyata, kasanni ban da kyau" tanagama fadin haka ta juya tanufi motarta, yayi Yunkurin ya biyota amma ta tashi motar tabar gurin. Yauma Jalila ba bacci, saboda tashin hankali da damuwa, se addu'a da takeyi, Nana kam ta gaji da tambayar ta meyake damunta. Da Asuba Jalila tai wanka tai salla ta shiga kitchen ta dama kunun gyda da dankalin turawa, karfe bakwai tagama shiryawa tsaf tana jiran Jawwad, Nana tai juyi akan gado ta kalli Jalila "wai shirin mekikeyi hakane?" "Asibiti zan raka Yaya Jawwad muduba Yaya Jalal" dan zaro ido Nana tayi, sannan tai murmushi "Yaukuma da kanki kike cewa Yaya Jalal" takuma murmushi tace "Zanso inje nima induba shi, amma wallahi bacci nakeji, kuyi masa sannu in an sallamoshi naje in duba shi, kokuma in Maama zata semuje tare" Nana ta juya tashige bargo, Jalila na nan zaune, wajejen karfe takwas Jawwad yakirata a waya yace tafito su tafi, da sauri ta dakko kwandon kayan Abincin ta fito, Jawwad ya kalleta yace "Baby hada hidima haka, Abinci kika mana" "Eh Yaya, koba kwaso?" "haba mu mun isa, taho mutafi" ta shiga mota suka tafi, suna zuwa Jawwad yaimata jagora har dakin da Jalal yake, suka tura kofa suka shiga ta tsorata da ganin Jalal, yana kwance akan gado dagashi se dogon wando da singlet, yanata sauke numfashi a hankali, ya rame matuka gashi yayi duhu se dogon hancinsa yakara fitowa sosai, drip yana shiga jikinsa a hankali, hawaye yafara bin idon Jalila a ranta tace "idan har Jalal ya mutu ina da alhaki, ninakara assasa bata masa rai" Jawwad ya dora hannunsa akan gadon da Jalal yake ya sunkuyar da kai, Yana dago ido Jalila taga kwalla a kwance a idonsa "Yaya karka karaya mana, zeji sauki" Jawwad yai murmushi yace "Baby Jalal wani bangarene na rayuwata, inajinsa a raina kaman wani bangare na rayuwata, banason rasashi, banason wani abu yasameshi da inada yadda zanyi in kawar masa da damuwarsa, danayi amma ba yadda na iya kaddara tariga fata, haka Allah ya kaddara masa, ina fatan Allah ya musanya masa da kyakyawar kaddara " Jawwad yai ajiyar zuciya yace "Bari inje gurin doctor inji meze ce, kizauna anan anjima su Ilham zasuzo nima yanzu zan dawo, inkuma ya tashi kafin in dawo kikirani beci Abinci ba" ta jinjina kai, Jawwad yafita yabar dakin guri ta samu ta zauna akan kujerar gaban gadon Jalal, Hawaye tacigaba da sharewa lokaci zuwa lokaci tana dorawa kanta alhakin wannan rashin lafiyar da yake, A hankali Jalal yai juyi, da sauri ta goge idonta ta tsaya tana kallonsa bude idonsa yayi a hankali ya saukesu akan Jalila dake goge hawaye, kura mata ido yayi ko kyaftawa ba yayi. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣5️⃣78 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ Ya dau lokaci yana kallon ta, cikin rawar murya Jalila tace "Sannu ya jiki?" shiru yayi bece komai ba ya lumshe idonsa, "Ko inkira maka Jawwad" still shiru yayi bece mata komaiba tamarasa mezatayi, idonsa a lumshe taga hawaye nabin gefen idon Jalal, hankalinta yakara tashi "Inkira maka likitane" takarasa maganar tana hawaye, bude idonsa yayi ya juyo yana kallonta "Kukan mekikeyi? Nakumamiki wani laifinne? Nasan bazakiyi kuka dan halin danake ciki ba, zakifiso in mutu saboda yayanki ya huta ba?" Girgigiza masa kai Jalila ta shigayi amma takasa magana Ya hade rai yace "kidenamin kuka, nagaya miki kincikamin kunne" "Yi hakuri na dena" tasa hannu ta share hawayenta, Jawwad yashigo da likita suna zuwa kan Jalal ya bude ido, Jawwad ya zauna kusada shi yace "Sannu ya jikin naka?" "Alhamdilillah naji sauki azo a sallameni" murmushi likitan yayi sannan yace "kai Jalal da wuri haka, bazamu sallameka yau ba, se mun tabattar dakabi dokokin dazamu saka maka, bamaso se mun Sallameka akuma  dawo da kai Rai a hannun Allah" Jawwad yace "rabu dashi doctor yi masa abunda yakamata, baza'a sallameshi ba seya warke gaba daya" Jalal ya tashi zaune, Likita yakara duddubashi, sannan yayi rubuce2 a file din Jalal, ya rubuta wata takadda yace "Ga wannan Jawwad bamu dasu a pharmacy sekaje cikin sabon gari zaka samoshi" Sannan likitan ya kalli Jalal yace "Man yakamata ka cire abunda yake ranka, karka kashe kanka da kuruciyarka kana matashinka, kana da kudi kana cikin Ni"'imar ubangiji meze daga maka hankali haka? " kallonsa Jalal yai ya dauke kai likitan yacigaba da cewa " Jininka ya hau sosai, dole kadena damuwa sannan u must reduce the amount of cigarette and shisha you take every day (PEOPLE WHO SMOKE ARE ABLE TO DIE YOUNG!!!) so you should be careful, akwai sinadarin dayake saka hawan jini a cikin taba, shanta yana kawo lung cancer ko tuberculosis, and you should reduce Alcohol intake, ka rage shan giya shima, tana saka cututtuka da dama, kaman Ciwon Hanta, ciwon koda, tana kara asassa ciwon sugar akwai kuma nauo'in ciwon ido dake sakawa, dan haka a hankali yakamata ka rage, sannan kadinga cin Abinci kaga Ulcer yana nema yazeme maka chronic " shiru Jalal yayi ya sunkuyar da kai, Jawwad yace "Shikenan doctor za'a kiyaye Insha Allah" "Yawwa masha Allah, Allah yakara sauki" doctor ya juya ya fita, Jawwad ya zagayo ya zauna kusada Jalal yace "Kaji abunda doctor yace ko? Please and please kakiyaye dokokin da aka samaka kaji Dan uwa" Jalal dai bece komai ba, ya sunkuyar da kansa, Jawwad ya juya ya kalli Jalila yace "Baby miko kwandon Abincin nan a hada masa yaci se inje siyo masa maganin" Ta dakko kwandon, ta zuba kunun gyada cikin  wani katon kofi ta zuba dankali ta mikawa Jawwad, Jawwad ya zare ido yace "Kai Baby yazeyi da wannan kunun yayi yawa ai, bakiga bashida lafiya ba, aibaze iya shanye wannan ba" Jalila tace "Au haba, ka tuna lokacin dana kwanta a Asibiti cikin katon kofin nan yazare min ido sena shanye, shima ka zare masa ido ya shanye" takarasa maganar tana dan tura baki, Bakinta Jalal ya tsaya yana kallo shikuwa Dariya Jawwad yai yace "itaku kedashi, kema seki zare masa ido ya shanye, bari inje in siyo maganin" Jawwad ya mike ya fita, Jawwad na fita Jalal yai kokarin komawa ya kwanta beci Abincin ba da sauri Jalila tace "Ai bakaci Abincin ba" ya kalleta "Bazanci ba" yakuma kokarin kwanciya Abincin ta dauka ta dora a inda ze kwanta tace "wai meyasa kafiye taurin kaine? Cewa fa akayi kaci Abinci" "Ke har na kaiki taurin kaine? Waima ina ruwanki danine? Dan giya, mara tarbiyya, zan lalata miki dan uwa, me kike nema a gurina, dauke Abincin ki bazan ciba, kintaba gayamin idan na mutu bakida Asara to meye naki na damuwa da banci Abinci ba?" yasa hannu ya dauke Abincin ya dora akan drower na kusa da gadon sannan yace "Dama a duniya daga daddy se Jawwad ne suke sona se yan uwan daddy, nan duniya idan na mutu ba wanda yakeda Asara, sesu" kura masa ido tayi "Meye kuma kike kwalalamin idanuwa haka, kidena kallona" yai kwanciyar sa. Kawai Jalila ta mike ta fice daga dakin, Ajiyar zuciya Jalal yayi dayaga ta fita ya dakko Abincin data zuba ya ci ya aje sauran. Jalila na fita tasamu guri ta zauna a waje ta dakko wayarta tafara chatting tana daga kai ta hango Ilham da mahaifiyarta a harabar Asibitin kallo daya tayiwa Saudat tagane itace mahaifiyar Ilham, da sauri Jalila ta tashi ta koma dakin Jalal, tana zuwa taga yaci Abincin yana kashingide ya lumshe ido, yana jin motsinta ya bude ido, "Ke meya dawo dake, ko dama bakida zuciya?" cikin tsiwa tace "dama ina naga zuciya, tunda kaima bakada ita" Dan zare ido yayi, ashe halin nata yana nan Ta fara hada kan kwanuka, Ilham ce da Mamanta suka shigo da sallama yanajin muryarsu yai Sauri ya rufe idonsa. Kai kace bacci yake, Tunda Ilham taga Jalila a gurin Jalal ta hade rai kaman taga kashi Jalila ta maze tace "Sannunku da zuwa" yawwa maman Ilham ta amsamata, tabasu guri suka zauna Ilham se harar Jalila take, ita kam Jalila data kalli Ilham seta mata murmushi Maman Ilham tace "Yame jiki?" "da sauki Mama" "naga alamar kaman yana bacci ne ko?" Jalila ta waiga ta kalleshi yawani rufe ido kaman gaske amma idonsa biyu, se Jalila ta kudurce wani abu a ranta dan haka Jalila tace " eh likita yamasa Allurai yasamu bacci, likita yace baze farka ba se bayan Awa biyar, yanzu besan me ake ba" Maman Ilham ta kalli Jalila tace " Sedai bangane wannan ba, bakowa a gurinsa seke? ko itama a dangin babanasa take?" Ilham tai farat tace "Inafa," yar shishshigi yar wahala dai, me hana ruwa gudu, me cusa kanta inda Allah be kaita ba" Jalila tace "haba Ilham, wani ma se yazata banida kirki, menamiki haka ina laifin kice, Sauro me hana giwa bacci, Raina kama kaga Gayya" Jalila ta karasa maganar tana murmushi tace "Mama bari in saka wayata a caji, in karbo muku ruwa a waje" Jalila ta mike ta dau wayarta ta dan daddana sannan tasaka ta a caji ta fita. Ba'a wani dade ba, Jalila ta turo kofa ta shigo da ruwan roba ta ajiye musu ko sha basuyi ba suka tashi sukace tafiya zasuyi. Tai musu sallama suka mata banza Ilham nata gaya mata bakaken maganganu  bata damu ba suna fita taje ta dauki wayarta ta bude, maganganun dasukayi tsaf tayi recording dinsa tai Saving tajuya ta hada kan kwanukan da Jalal yaci Abinci,  bude idonsa yayi yana kallon ta tana dagowa suka hada ido "Akwai matsala ne?" Jalila ta tambayeshi "Wani Apple kika hanani ci kika musanya ranar da mukayi baki?" tambayar tazo mata a bazata, ta dan tabe baki sannan tace "Apple kuma ni ban san zancen ba" "Karya kikeyi" Hade rai tayi sosai "Eh kasan na saba" tacigaba da abunda take, ko ina yasan wannam maganar oho masa, ta mike tsaye taji ya janyo ta da karfi kan gadon, take jikinta ya hau rawa ta tsorata sosai ta ware ido tana kallon sa "Ina tambayar ki kina rainamin hankali wani Apple kika hanani ci, kuma meyasa?" "ni nace maka ban san zancen ba, ka tambayi wanda suka gayamaka mana, ni kacikani"  kara karfin rikon yayi taji kaman ze karya ta, sannan yace "ke bana son karya, for the last time ki gayamin" kawai ta fashe da kuka, mamakine yakama shi, in wani ya shigo se a zata wani abun yayi mata, dan haka a hankali ya sake ta ta mike da sauri ta koma waje, tana fita ta dakko wayarta kunna maganganun Ilham da mamanta. Kawai taji maganar Ilham tana cewa "Umma wannan itace munafukar da nake gayamiki duk lokacin danayi wani yunkuri zanyi wani aiki akansa itake lalatawa, na dade da gane take takenta sonshi take, amma taki yadda tana rainamin hankali, tasamun Ido ta hanani sakewa, duk lokacin danayi Yunkurin wani abu idonta na kaina, seta wargaza gashi ta hadani dawata tsinanniyar karuwa wai budurwar Jalal ce, hatsabibancin yarinyar nan ya wuce tunaninki, harda wani alwashin indai tana Raye  seta rusa shirina akan Jalal" mamanta tace "Ke sokuwar inace? Kika kasa gayamin tuntuni mu dau mataki akan shegiya" "Umm har gurin Malam na kaita amma yace baze iya komai akanta ba, dakike ganinta ita ta musanya Apple din dana sawa maganin ranar, makira tsinanniya" umma ta girgigiza kai tace "Tab aikuwa da sake, dole muyi wani abu karta bata mana aikinmu, amma Khadija kuwa tazo taga halin dayake ciki?" Ilham tace "Ai ingayamiki baya son ganin ta, kinga abunda ya dinga yi kuwa sekace ya haukace, dakinsa na nan kaman kantin mahaukaciya ya fasa komai a dakin, sangartacce ubansa na dawowa za'a canza masa komai" suka cigaba da maganganun su a zatonsu duk Jalal bacci yake besan mesuke ba, ita kuwa Jalila tana sane tayi haka. Shiru Jalila tayi tana tunani "Kenan Jalal yaji duk maganganun da sukayi shine yake tambayata? Kafin kuga bayana zanga naku" Jawwad ta hango ya taho da leda a hannunsa, yana zuwa inda take yace "Am sorry na tafi nabarki ko? Na dade bansamu maganin bane, bari inzo in maida kw gida nasan kin gaji" "To Yaya sannu da zuwa" "Yawwa babyn Yaya" yai mata murmushi ya wuce, yakai minti goma sha biyar sannan ya fito ya dauki Jalila suka tafi gida. Suna zuwa gida gaban Jawwad yafara faduwa, sakamakon tarar da Maama a harabar gidan da sukayi a tsaye da alamu a zuciye take, Jalila ta fito daga mota, Maama ta dinga jefamata wani irin mugun kallo, Jalila ta basar tace "Maama sannu da gida" tafada tana kokarin wucewa cikin gida "Dakata algunguma" ta dakatar da Jalila, Jalila ta tsaya ta sunkuyar da kai, Jawwad yafito ya rufe mota yakaraso gurin Maama yace "Maama, meyafaru ne?" "Ubanka ne yafaru, daga gidan ubanwa kuke? Da kuka fita tun farar safiya se yanzu kuke dawowa?" Jawwad ya dan girgigiza kai yace "Kiyi Hakuri, ta rakani gurin Jalal ne, muna Asibiti tun dazu" "Yimin shiru makaryaci banza da na wofi, kai ko kunya bakaji ka dingamin karya, Asibitinne se yanzu zaku dawo, tafara janka gantali ko, wallahi ka biye mata kafara aikata wani abu dayasaba da al'adunmu se ranka yabaci, tun yaushe Nake maka magana akan Naja, fafur kaki kaje ko inda take, tunda abun naka hakane Naja ta dawo gidan nan, kuma kobakabso seka Aure ta" ta juya ta kalli Jalila tace "Kekuma ko mayyace sekin kyalemin dana, akan me ke baki da zuciya ne? Wallahi kifita daga idona, shegiya mayya" ba Jalila ba hatta Jawwad seda ya dago Ido suka kalli Maama a tare, Jalila ta juya ta shige cikin gida ta barsu a gurin, tana shiga palour ta fara kicibisa da yaya mairo da Naja, a ranta tace "Ashe wannan ibilishiyar matar ce tazo shiyasa yau akemun saukalen Rashin mutunci, tun daga harabar gida ai shikenan" Aibata gama zancen zucin ba ta tsinto muryar Yaya mairo tana fadin "Ga shedaniyar nan makira, wallahi kozaki mutu gidan nan ma se ya gagareki zama, kuma seya Auri Naja, danbazamu Aura masa Arniya ba, wadda uwatta ta gudu tazabi barbadanci ta battaba, Nutsatsiya zamu aura masa yar musulmi" Jalila ta tsaya ta waiga taga daga ita se su a palourn Maama tana waje tana cigaba da saukewa Jawwad kwandon jaraba, Jalila tace "To ayi mugani mana, karewar nutsatsiya masallaci Zaku Aura masa, sannan kika kuma zagarmin uwa wallahi sena kira taki uwar na zaga dan uwa bata fi Uwa ba" Naja ta mike a fusace tace "Ke dan uwarki uwatawa zaki zaga" "badai uwata ba, wannan tsohuwar banzar kika zaga, kinbiyata ladar haihuwarki datayi, kuma Na zageta ita wacece? Ko fin tawa uwar tayi? Kuma wallahi takuma zagarmin uwa sena fasa mata kai da wannan flask din" Jalila ta nuna tea flask din da takaiwa Jalal Abinci a ciki, hangame baki Yaya mairo tayi Jalila tace "Yanzu nasan ciwon kaina, ina zubarda hawayena ne a inda yakamata, nadena asararsu akan maganganun ku, iyakaci duk tsufan mace ta zagarmin uwa sena rama wallahi, Sannan ke Naja naji ance kindawo gidan nan da zama, kinyi kwantai ana cusa masa ragowa yana baya so amma, saboda ansan baki da mamora, se cusaki akeyu, to kinkawo kanki, bacin ran da uwarki ta dinga kunsamin tsawon shekaru sena ramasu akanki wallahi, kuma kafin inbar gidan nan sena sena tabattar da kin barshi tukuna" Jalila ta juya tai wucewarta daki yayinda Naja da yaya mairo suka rasa abun cewa, Naja tai karfin halin cewa "Lallai yarinyar nan rashin mutuncin ta yakara yawa, amma karki damu, ni zan saita mata zama namiki alkawarin, setabar gidan nan da kafarta, kuma sena Auri Jawwad, kiyi hakuri zan ramamiki" Naja na rufe bakinta, sega Maama sun shigo ta sako Jawwad a gaba tanata masa masifa shikam ya sunkuyar da kansa kasa har suka shigo cikin palourn Nan Maama da yayarta, Yaya mairo suka saka Jawwad agaba da fada, shikam yayi shiru yakasa cewa komai babban abunda yake kona masa rai be wuce yadda suke cin mutuncin Ummi ba, matar da basuda tabaccin tana raye ko bata raye, seda sukayi suka gama sannan ya mike ya bar palourn, Yaya mairo tacigaba ds zuga Maama tana kara cusa mata tsanar Jalila a ranta. Yaya mairo ta tafi tabar Naja a gidan, koda Nana ta dawo gida ta tarar da Naja a gidan ba karamin haushi taji ba, dan sam Allah be hada jininta dasu ba. Jalila takira Hanan a waya, tagayamata abunda ke faruwa, Naja ta dawo gidan da zama ita ake so Jawwad ya aure. A fusace Hanan tace "Kan bala'i, wallahi ba'a isa ba" cikin mamaki Jalila tace "Kamar yaya kenan?" "kamar yadda nagaya miki, ai wannan fadan banaki bane Jalila nawane, ai muna nan zuwa Kanon very soon, ina baze yuwu ba, ai gara in barmiki Jawwad da ina gani ya Auri wannan yarinyar, gentle man like Jawwad, be dace da Auran ballagaza kaman wannan yarinyar ba dukda kasancewar ta yar uwassa" Hanan ta dinga masifa karshema ta kashe wayarta. Mamaki duk yakama Jalila dama dagaske Har yanzu Hanan bata hakura da Jawwad ba? Haka Jalila taita tunani. Washegari aka sallamo Jalal daga Asibiti ba laifi jikinsa yaji sauki sedai rashin kwarin jiki, Jawwad ne ya dawo dashi daga Asibiti, Dakin Jalal sam yayi kaca2 da kwalabe da abubuwa dan haka suka wuce dakin Jawwad. Jalal ya kula da yanayin Jawwad kaman ransa  a bace yake, dukda Jalal dinma nasa ran ba dadi amma yace "Jawwad meyake damunka ne? Saura kacemin bakomai dan fuskarka ta nuna" Jawwad yace "Jalal duk na rasa meyakamata inyi" nan ya kwashe komai yagayawa Jalal" "Bazaka Auri wata Naja ba" "Wallahi Jalal nima bana sonta amma Maama ta dage na rasa ya zanyi" "Karka damu zamu samu mafita amma wannan yarinyar ba matar Aure bace, dan sam baku dace ba" Jalal yaita kokarin kwantar wa Jawwad hankali yayin da shikuma gefe guda tasa damuwar nakuma sassakar zuciyarsa, musamman idan ya tuna maganganun dayaji Ilham tanayi da mamanta akansa. A ranar da yamma daddynsa ya dawo, bagan magariba Jawwad yaiwa Jalal rakiya zuwa gidansu, har palourn daddy sedai daddy beji dadin yadda ya tarar Jalal yai rashin lafiya be Sani ba, Jawwad yace "Ai yaji sauki daddy ya warke, bekamata kana can mu tayar maka da hankali ba gashi yaji sauki" daddy yace "Hakane ya jikin naka?" Jalal yai ajiyar zuciya sannan yace "Naji sauki" Mummy ce ta shigo palourn da cup din tea a hannunta, tazo ta samu guri kusada daddy ta zauna sannan tace "Ya jikin naka?" Banza yayi yaki kulata, sema dauke kai da yayi, Jawwad yace "Jalal Mummy namaka magana fa" wani uban tsaki yakuma yi ya dauke kai, daddy yace "Haba Son Mum cefa, at least kagaya mata how you feel zataji dadi" mikewa Jalal yayi ya nufi hanyar fita Jalal yabishi yana cewa "wai Jalal wani irin mutum ne kai? Baka kyauta ba meyasa kake hakane, mahaifiyarka cefa?" tsayawa yayi ya kalli Jawwad yace "Ta haifeni ne kawai, amma bata amsa sunan uwata ba, ka gayamin ya dace abunda taiwa dangin mahaifina, shikenan ni haka zan kasance bawanda ze dinga rabata, ba soyayyar uwa, ba dangi ba abokai, haka zan kare Rayuwata, kaikadaine ka iya jure halin mahaifiyata kae taredani har zuwa wannan lokaci, Jawwad yaushe zan samu sassauci akan kaddarorin Rayuwata why me? Mahaifiyata amma kullum itake kokarin rusani itafa ta haifeni, bata tausayamin kodan irin Rayuwar dana shiga saboda ita? Kowa ya gujeni nazama abun kyama, shikenan nasan matakin dazan dauka" yana zuwa nan a zancensa kawai ya juya ya fice da Sauri, Jawwad ya mike ze bishi daddy yace "Son kyaleshi, inka bishi maybe ya sauke maka yabata maka Rai karkaje inda yake a yanzu, zoka zauna nan ina so zamuyi magana da kai, Jawwad ya dawo ya zauna, Daddy ya kalli Mummy yace" Khadija dan kina mahaifiyar Jalal, dole kicire girman kai ki nemi Afuwarsa dan tabbas kin cutar dashi, Mummy tace "Nifa ina mamakin cewa dakuke nice sila, wace uwace zata sa hannu danta ya lalace, menayi dayazama nice silar lalacewar sa, Jalal ne yakamaga yanemi yafiyata batamin randa yakeyi" Ta mike a fusace tabar palourn, Jalal kam yana fita yacikaro da Ilham a harabar gidan yabita da wani mugun kallo na tsantsar tsana, seda tasha jinin jikinta, yasa kai ya fice a fusace, Jalila na kan step din palour taga Jalal ya shigo gidan ya nufi part din Jawwad, se hada hanya yake kaman baya ganin gabansa sosai daga inda take ta hango kaman da hawaye a idonsa, da Sauri yakarasa part din Jawwad ya tura kofa ya shiga aiko itama da sauri ta sakko tabi bayansa. Amma tana zuwa kofar dakin seta tsaya tafara tunani "to idan naje mezan ce masa? Inkuma ya makeni fa?" juyowa tayi zata koma, kawai taji kaman Jalal yana fidda numfashi da Sauri. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣6️⃣79 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ Da sauri ta bude kofar ta shiga, yana tsaye yana kaiwa yana komowa, idonsa yazama abun tsoro saboda ja, ga jijiyoyin kansa duk sunfito sun mimmike, gashi da kyar yake sauke numfashi, se faman runtse ido yake, da Sauri Jalila takarasa tace "Jalal meya sameka? Wani abun yafarune? Ko jikinne?" Banza yai mata ya juya mata baya, da sauri ta zagaya gabansa tana kokarin kallon fuskar sa, amma yasa hannu ya hankade ta, bige hannu tayi ajikin center ta rike gurin tana dan cije lebe tareda ya mutsa fuska alamun taji zafi, ta bugu sosai a hannun, mikewa tayi takuma komawa inda yake, a hankali ta ga ya sulale ya zauna yana motsa bakinsa alamun yanaso yai magana amma yakasa, kawai ya lumshe ido hawaye na fitaa a gefen idonsa, gaba daya yanzu Jalila tausayinsa takeji, tabbas Jalal na cikin kaddarar rayuwa amma hanyar daya dauka ba itace mafita ba. Taje gabansa ta zauna ta dan kura masa ido na wasu mintuna sannan tafara magana cikin nutsuwa da kwantar da harshe "dukkan dan adam ba abarinsa ba tareda jarabbawa ba, Kowa da kalar tasa kaddarar, inkaji ta wani sekaga taka ba komai bace, Annabi Ibrahim alaihi salam, Annabin Allah ne, ya kira mutanensa akan bautar Allah shikadai, amma Mahaifinsa be musulinta ba, hakan besa ya saba masa a matsayinsa na mahaifinsa ba, karshe ma har wuta aka hada domin a kasheshi amma Allah ya tsallakar dashi. Annabi Yusuf alaihi salam, Mahaifinsa na matukar Kaunarsa amma se aka Jarrabeshi akan Yan uwansa, suna masa hassada da kaunar da mahifinsu kemasa kaga matsayin sa na Annabin Allah amma har kurkuku yayi, amma daga karshe kaga daukakar daya samu. Annabi musa alaihi salam shima yayi gwagwar maya, bayan Allah ya tsalakka dashi daga sharrin fir'auna, kalli butulcin da mutanensa sukayi masa, kowane Annabi da kalar jarrabawar da Allah yai masa. Annabawa kenan ina gamu daba kowan kowa ba, wasu na Kabari, wasu na Asibiti se an kwantar an tayar, wasu na prison basu ba kara shakar iskar yanci, wasu na gidan masu rangwamen hankali, wasu na gidan marayu ana musu kallon shegu, wasu guragu ne, suna maula a gefen hanya, wasu yaki yasa sun rabu da iyalansu da yan uwansu, duk cikin wannan ba wanda Allah ya jarabceka dashi, karka zama me butulci da Ni'imomin ubangiji no matter how worst the situation is kazama me gode masa, kanada dama, kanada lokaci kayi kokari ka gyara barnar dakayi a baya, ka yafewa mahaifiyarka inka yafe mata se Allah ya shiga cikin lamarin ka. Anyway for now don't try to kill yourself without changing your life style. Yai shiru idonsa a lumshe amma nasihar Jalila yaji tana tasirir a zuciyarsa a zuciyarsa ya shiga Fadin Astagfirullah wa atubu ilaihi, amma deep into his heart in ya tuna yadda take masa rashin mutunci se haushinta yakama shi, a fili ya bude idonsa yace "Tashi kibani guri bana son ganinki a inda nake, kinadaga cikin mutanen dasuka kara saka zuciyata cikin garari, da tashin hankali, kinsan yadda nakeji inkika jefeni da kalmar mara tarbiyya, kin dade kina gayamin maganganu masu kona zuciya, a maimakon kalaman kwarin gwiwa, ki tashi kibani guri karki kara zuwa inda nake, nasan da Umminki tana nan nasan komai munin halina bazata taba kyamata ko tagayamin bakar magana ba, bazata taba zama cikin masu kyamata ba, ta nunamin so da kauna, kuma batun yafiya tsakanina da mahaifiyata wannan abunda ya shafeni ne, i never expect such type of behavior from you, why? Why do you hate me before, baki taba tunanin me ya jawomin nake irin wannan rayuwar ba, Never judge book by it's cover, please dismiss from here, in ina ganinki kina kara batamin rai" Idon Jalila kyar akansa bata ko kyaftawa har yayi gama yana huci, "Naji zan tashi, Nagode sosai, karka manta da kashedin likita, kaci Abinci kasha magani, sannan ka rage shaye2" "bazan ba uwatace ke dazaki dinga min kashedi haka? Wai ina ruwanki dani ne, meya shafeki da inyi lafiya ko kar inyi" "A'a ba daya, in kayi inma bakayi ba kanka kayiwa ba Jalila ba, Amma kaji tsoron Allah, kakiyaye dokokinsa sannan ka kulada ibada" ta mike jiki a sanyaye ta fito waje, maganganun da Jalal ya gayamata babkaramin bata mata rai sukayi ba, dukda taji zafin maganganun da Jalal yagaya mata, amma idan ta tuna itama abubuwan data dinga masa abaya setaga bata kyauta ba. Daddy ya kalli Jawwad yace "Jawwad Abbanka kuwa yana gari ina son ganinsa" Jawwad yace "A'a Daddy be dawo ba tukuna yana lagos amma a satin nan ze dawo Insha Allah" daddy yace "Allah yadawo da shi lafiya, Yaww Jawwad naji Jalal yacemin ka kamalla Masters dinka last Couple of months ko?" Jawwad yace "Eh Daddy Alhamdilillah na kamalla, ina jiran sakamakone, atayamu da Addu'a" daddy yai murmushi yace "Kullum cikin yi muku nake? Kuma nasan da sakamako me kyau zaka fita Insha Allah, nasan yarona  akwai himma ai, dama vacancy na samu, federal zata dauki ma'aikata a farkon sabon shekara anbani vacancy na mutum daya a babban branch din NNPC na Abuja, shine nace ka turomin CV dinka ta Email dina, inkuma zaka karo karatune kuma to, semuga yadda za'ayi kaje ko England ne can wajensu Mahmud ka karasa" shiru Jawwad yayi ya sunkuyar da kai yakasa cewa uffan daddy yace "Jawwad kona bata maka raine?" Jawwad ya girgigiza kai yace "Daddy banida bakin yi maka godiya, tun ina karami kake dawainiya dani, amma ina tunanin dan uwana, daddy Jalal shifa me za'ayi wands za'a tallafawa Rayuwarsa" daddy yai ajiyar Zuciya yace "Jawwad bana tunanin koda Jalal yanada dan uwa ciki daya ze nuna masa kaunar da kake masa, Amma Jawwad ba yadda zanyi ina za'adauki Jalal aiki a wannan halin da yake ciki, yana shaye2 baya son mutane, ga zafin zuciya kana gani ko mahaifiyarsa baya raga mata, anyi2 yakoma makaranta yaki " Inda na godewa Allah ko bayan raina Jalal yanada kadarorin da in ya tattala ze iya rike kansa, inkuma yabarnatar shikenan" Jawwad yace "Daddy bazanyi musu da hukuncin ka ba, amma inaso Jalal ya samu makoma shima, koya koma karatu koya samu aiki, amma idan na tafi Aiki na barshi a wannan halin senake ga kaman banyi masa halacci ba, kuma shaye2 munmasa addu'a muna fatan ze dena very soon, tunda ya rage ba kaman da ba" shiru daddy yayi yana kallon Jawwad dayake magana idonsa taf Hawaye dake nuna hakikanin gaskiyar abunda yake fada har zuciyarsa. "Jawwad kenan Allah ya dawwamar da haske a cikin Rayuwarka, gwagwarmaya da kaunar dakake wa dana banida abun biyanka, Allah yatemakeka ya baka abunda kake nema duniya da lahira" "Ameen daddy" daga haka ya tashi ya fita. Oga KB yana zaune yatasa Samira da wata katuwar bulala, da alamu jibgarta yagama yi, jikinta duk a kumbure dan fuskarta a kumbure gefen idonta yana zubar da jini, Oga KB yace "Tun tsawon wani lokaci kike tareda Jeje?" Cikin kuka tace "Ranar muka fara haduwa da shi" kafin ta rufe baki yakuma zuba mata bulala tareda fadin "Karya kikeyi, munafuka zaki gayamin ko sena takeki na kasheki, matsiyaciya yanzu shikenan Sunana yagama lalacewa a idon duniya, nida 'yata a gidan karuwai, dana san irinki za' a haifamin da tun a ciki sena zubar dake, Wallahi idan Nagano wanda ya shirya min wannan manakisar sena kasheshi kowaye, ki gayamin tun yaushe kuke tare?"kokuma yanzu inkasheki da poison na kashe banza shedaniya" "Shekararmu biyar Tare dashi" zaro ido yayi "Shekara biyar amma bansaniba, Cigaba ina jinki se akayi yaya?" "tun ina secondary muke tareda shi, bayan haduwa ta da Saleema, nasanshi ne ta hanyarta, daga baya yake nunamin yasanka, Yaronka ne akwai aikin dayake maka, duk lokacin danazo maka da bukata baka damuwa da bukatuna, kafi son faruk dani, kana cewa bazaka kara yadda da mace ba koda yar cikinka ce, nikuma bukatuna bakamin, umma ma bayimata kake ba, balle nima ina sa rai, shine Jeje yajani a jiki shine ya koyamin bin maza, yana baani kudi masu yawa sannan ya hadani da masu kudi Shida Saleema, Sau biyar ina zubar da ciki biyu duk nasane" Wata irin zuface ta shiga tsatstsafowa Alhaji Kabiru mikewa yayi ya shake Samira yana fadin "Samira anya kuwa nine Ubanki, kodayake a rina barewa bata gudu danta yai rarrrafe uwarkima karuwanci tayi ta tuba na Aureta, watakila bayan na Auretanma bata tuba ba" Mahaifiyar Samira ta fito a fusace tace "Sakarmin 'yata wallahi bazaka kasheta ba, tun dazu inamaka kawaici shiru kawai nake, tunda abun naka yazoda cin fuska bari in tunamaka, kana tunanin hakkin uwarka ze kyaleka ne,? kokuma shi yaron dakasa aka lalata ba dan wasu bane? Yaronne yai maka laifi? Kokuwa uban me ya kaika gidan karuwai? Duk nasan abunda ka keyi kyaleka kawai nakeyi dan haka sakarmin yarinya ni Addu'a nake Allah ya shirya yaran musulmi amma wannan bakar zuciyarta ka me cike da sharri dole kaima kaga sharri akan yaranka", A fusace yayo kan mahaifiyar Samira, amma Samira ta rike rigarsa cikin ihu da kuka take cewa "Wallahi karka sake ka tabamin uwa, nidin dai ko kasheni kayi nasam baka da asara, ai a ranar da aka kamamu  a gabaana zizo yace kaima ana kaimaka karuwai gidan hutawarka, tunda na taso katsaneni saboda kawai ni macece ka fifita soyayyar danka namiji akaina, gaka da kudi amma baka moramin komai danme yasa bazan nemawa kaina mafita ba" jin hayaniya yasa tuni mutane suka fara shigowa dan ganin meyake faruwa, Alhaji Kabiru yasa hannu yai wurgi da Samira, take ta fafi bata ko motsi, nan da nan mutane sukayi kanta amma ana dagata sega Jina nata zuba daga jikinta. Shikam Alhaji Kabiru motarsa ya dauka ya fice daga gidan be zame ko ina ba se gidan Jeje, Yana zuwa Jeje baya nan, dan haka ya tafi Club din dayasan lallai zs same shi a can Jeje yana nan, yanata shaye2 shida wasu mata, tareda wasu abokansu. A fusace ya daka musu tsawa yace su basu guri, daya ta kalleshi cike da maye tace "Wollah ba inda zamuje, ji mutum kazo kasamemu sannan kace mufita "Jeje yace "Am sorry Guys don't mind him" Jeje ya dawo da dubansa kan Alhaji Kabiru yace "I thinks you said it's over between me and you ba, bayan tsawon lokaci dana dauka inamaka aiki, inamaka bauta dan ka kamani da 'yarka,' yan sanda sunkamamu, shine kacimin mutunci kamanta halaccin danayi maka" "Shut up!!!"  yayi wa Jeje tsawa "Duk wahalar danayi maka A rayuwa, tun kana karamin dan isaka na daukeka naimaka gata, na dinga yimaka wahala tsawon shekaru, baka cikamin burina na ganin ankai Jalal kurku a kasksance uwarsa da ubansa na kuka ba, memakon ka maida hankali akan aikin dana saka, sema komawa da kai kana cin amanata, yar cikina kake lalata da ita, kakoya mata bin maza, ga shaye2 ta tabattarmin da sau biyar tana zubar da ciki biyu daga ciki kuma nakane, Ka saurari abunda ze biyo baya, hukuma ce zata rabani da kai" "Kafin ka kaini gaban hukuma yakamata ka amsawa kanka wannan tambayoyin? Kai yara mata nawa ka lalata? Ko agaban Allah wace hujja zaka bayar na bada kwangilar lalata Rayuwar ABDUL JALAL da sunan daukar fansa? Uwa uba karka manta da babbar haramtacciyar harkallar da mukeyi na saida makamai da miyagun kwayoyi" cak Oga KB ya tsaya yayinda Jeje ya kyakyake da dariya yace "Ramin mugunta kenan inzaka gina, gina shi gajere dan kila kai zaka fada" Wani mugun bakin ciki da bacin raine yakama Oga KB ya juya ya shako wuyan Jeje yafara bugashi akan tebur, dayake a buge yake sam jikinsa babu kwari, nan take matasan dake gurin su taso sukayi kan Oga KB, dan har jini yafara fita daga hancin Jeje, Oga KB na juyawa ya rarumo wata kwalbar giya ya bugawa Jeje a goshi nan take Jeje yafara zubar da jini hakan be isheshi ba seda yakuma soka masa kwalbar nan a kafada, Jini ya dinga fita a jikinsa nan take jiri ya kwashe Jeje ya fadi kasa, da kyar security din gurin suka rike Oga KB suka tafi dashi suka kuma mikawa 'yan sanda shi. Sannan aka dauki Jeje zuwa Asibiti rai a hannun Allah. Ita kuwa Samira da aka kaita Asibiti ta galabaita ashe wani cikinne a jikinta bata saniba, da kyar aka ceto ranta sedai an tabattar da mahifarta ta lalace bazata kara daukar ciki ba har abada. Jawwad yakoma gida ya tarar da Jalal a part dinsa, a zaune a akan kujera, Jawwad yaje kusada shi ya zauna, ya dinga masa nasiha tareda rarrashi akan abubuwan dayakewa mahaifiyarsa, Jalal yai shiru yaki kula Jawwad har yai surutansa yagama dan babu alamar Jalal ya dau Nasihar Jawwad, seda ya bari Jawwad yagama tsaf sannan yace "inka gama bani aron key din motarka" "ina zakaje?" "In tuhumata zakayi bar abunka" "A'a ni na isa, gashi amma kabi a hankali kasan bakada lafiya kayi driving a hankali" Jalal bece komai ba yasa hannu ya karbi key yafita. Jawwad ya nemi guri ya kwanta ya dan huta yana tunanin karamcin da daddy yake nuna masa. Jawwad yasamu yayi bacci, se bayan la'asar ya farka, yaje yai wanka yai salla yana kokarin neman Abunda zeci ya tuna  dakin Jalal yana nan kaca2 yasan inba'asa an gyara ba Jalal baze gyaraba ko dakin ze shekara ahaka, kuma ze iya zuwa yayi shaye shayensa yace ze shiga ya kwanta ga kwalabe da ya farfasa a zube a dakin, Jawwad ya mike ya fita, yana fitowa kafin ya kaiga bakin gate yaji muryar Naja ta kashe murya tana masa magana "Yayana dan Allah inbazaka damuba sonake ka rakani unguwa" Jawwad ya kakalo murmushin dole yace" "Eyya am very sorry, kinga aiki zanyi ne yanzu na gaggawa dan Allah kiyi hakuri" yana gamawa bejira mezatace ba ya fice daga gidan, tsayawa tayi turus tarasa me zatace. Haka ta juya takoma cikin gida tana cizon yatsa, tana komawa daki ta tararda Jalila tana gyara gashin ta agaban mudubi, ta dinga tsaki tana aikin banza, ita dai Jalila bata kulata ba, seda tagama tsaf ta dauki mayafi ta daure kanta ta dau wayarta ta fice, tana bukatar yin waya domin jin inda harkalarta ta kwana. Jawwad yana zuwa yafara tattarre Kwalaben dakin yana sakasu a dustbin yana bawa megadi yana fita dashi, Jawwad ya duba bega tsintsiya ba dan haka yakoma gida don ya dakko, yana zuwa ya hangota tana waya, kallo daya tayi masa tai murmushi ta sauke wayar tace "Ya dai naga kayi gumi haka? Meyafaru?" Murmushi yayi yace "Wallahi Jalal nake gyarawa daki, yayi fata2 da komai, kuma in ban gyara masa ba a haka ze barshi, kar inje ya bugu yace ze shiga dakin ya kwanta a haka" Jalila tai murmushi tace "Allah yasadaka da dukkanin wani alkhairi na duniya da lahira hakika ka cancanci yabo, Yaya Aliyu Jawwad sha gwagwarmaya, amma meyasa sekai zaka gyara masa?" "Kinsan halin dan uwan nawa, bakowa yake so yashigar masa daki ba, baya son sa ido" "Hakane muje in tayaka" "Anya kar in takura miki fa" "Bawani takura gyaran gida aina matane" ta rakashi suka dakko tsintsiya suka fito akan idon Naja suka fita tare aikuwa tasaki Ashar, Da sauri Nana ta kalleta "Lafiya kike mana Ashar haka sekace ba musulma ba" "Dalla rabu dani yanzu nacewa Jawwad ya rakani unguwa yace bazashi ba yanada abunyi, amma kalli sunfi ta tare da wannan jakar yarinyar, zasu gane kurensu bari Maaman ta dawo" Nana ta tabe baki tace "Wallahi Naja duk inda kikaje sekinja masifa, muna zamanmu lafiya amma kinzo zaki tayar mana da hankali Aikin banza kawai" Nana ta mike ta fice tabar mata dakin. Jalila ta dinga taya Jawwad suna kwashe kayan daya fasa suna fita dashi a hankali dakin yafara hankali kula tayi kaman Jawwad yagaji sosai tace "Yayan Baby what's wrong" yace "Baby yunwa nakeji sosai, ga Jalal yafice ban san inda ya tafiba koya ci Abinci oho" "Allah sarki jekaci kadawo ina jiranka, Abincin yana nan a kitchen" "God bless you my dear, yanzu zan dawo Insha Allah" Sosai Jalila tacigaba da aikin dakin, bedroom din zuwa palour ta gyara komai, taje tana goge kan fridge kawai ta bude, kwalabene manya da kanana, tanagani tasan giyace ga kwalayen sigari nan duk ya shiryasu a  ciki sekuma kwalayen madara da Apple a ciki amma kwalaban giya sunfi yawa, fito dasu ta dingayi daya bayan daya ta taresu agabanta ta girgigiza kai, ta tattaresu guri daya tadinga bude kwalbar tana tsiyaye giyar a cikin  dustbin, ta zazzage tabar nan a cikin shara, tacewa megadi yafita da ita. Ta koma dakin ta juya baya tanata mopping taji an rikota ta baya.. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣7️⃣80 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL_ Da sauri ta waiwayo don ganin waye ya cukumota haka, tozali tayi da Ilham ido cikin ido, a fusace Jalila tace "Malama lafiya? Meye haka sekace wata mara hankali" "Nikike cewa mara Hankali? Uban me kikeyi a dakin nan?"  wani irin kallon rainin hankali Jalila tayi mata "Uban da kikeyi shina keyi, Dan Cikani mana" kara rikon Ilham tayi "Bazan sakekiba, munafuka ranar kinje gurinsa kin zauna a Asibiti dan shishshigi, yau kuma uban me yakawoki dakinsa? Makira Annamimiya" "Ilham ba ina binki a sannu bane dan ina tsoronki, uban dayake kawoki dakinsa shiyake kawoni kicikani" "Bazan cikaki ba se kin gayamin uban meye hadinki dashi da har zakizo dakinsa wai kina gyarawa, akan me wayasaki, ke nifa ban yadda dake bama wallahi" hankade ta Jalila tayi ta nunata da yatsa, kikakuma gigin tabani wallahi sena baki mamaki, inkin isa in yazo shikije ki titsiye shimana kokuma kema ki dinga shige masa in zaki samu gindin zama, wallahi Ilham ki kiyayi shiga sabgata inbahakaba sekin gane bakida wayo, bar yimin kallon haka, sakarya kawai" A Fusace Ilham tayi kan Jalila ta riko hannun da Jalila ta fadi akai sanda Jalal ya tureta fadi, "Wallahi sekin gayamin meye hadinki da Jalal, sannan meyasa kike shishshigi a lamuransa, bazaki bar gurin nan ba sekin fadamin uban da kukeyi"  "Dalla cikani, ubankine Jalal din ko dan kekadai aka halliceshi, sha3 mutumin dabata taki yake ba, inma wani abun mukeyi kema kizo kuyi" Jalila ta fizge hannunta aikuwa Ilham ta dauka mopper tayo kan  Jalila, tana cewa "Wallahi sekin gayamin yau senaga uban da yatsaya miki koni koke, matsiyaci ya kawai, wallahi sena miki dukan dabazaki sake shigowa gidan nan ba. Jalila tai sauri ta dauki Ruwan mopping ta shekawa Ilham shi gaba daya a jikinta, sannan ta bita tana kwala mata bokitin. Seda yafara fashewa a jikin Ilham, inda Allah ya temaketa bokitin robane, Jawwad ne yakawo kai yaga  ana wrestling, Ilham ta durkusa tanata ihu Jalila tana bugamata bokiti tana huci, da sauri yaje ya riketa yana fadin "Subhanallah lafiya kuwa? Jalila meye haka?" A fusace Ilham tace "Dole ka tsaya kana tambaya mana kaima munafuki, wallahi tun wuri kajamata kunne inbata kiyayeni ba sena illata ta wallahi, nikika jika da ruwan datti kika dakeni ko? Wallahi sena sa kinyi danasanin zuwanki duniya" "Karki fasa, nikuma bazan gaji da lakada miki dukaba tunda bakya gane yaren mutane sena jakuna in an dakeki" Jawwad yace "Jalila yimin shiru, Ilham dan Allah kiyi hakuri komene nasan Jalila ce bata da Gaskiya, rigimanmiya ce tun asalinta dan Allah kiyi hakuri" "wallahi ni inada gaskiya, akanme zatazo tana zagi....... Jawwad yace" yimin shiru ko in zane miki jikinki yanzun nan, bata hakuri sannan ki wuce kitafi gida sarkin fada kawai" Jalila tai murmushi tace "Ilham dan Allah kiyi hakuri, sharrin shedanne, Insha Allah inkika dena shiga harkata bazan kuma tabaki ba, amma kika cigaba da rainamin hankali zaki gane bakida wayo" Jalila ta juya tai ficewarta, Ilham tacigaba da zazzaga bala'i Jawwad yana ta bata hakuri. Seda Ilham tagama zazzagewa Jawwad rashin mutunci sannan ta bar dakin, Jalila tagama gyara dakin fes, sedai ruwan mopping data zubawa Ilham duk ya kwantaa a gurin, Jawwad yasa abu yai mopping din gurin, har kusan goma na dare sannan Jalal ya dawo, koda ya dawo gidansu ya wuce, yaje ya siyo kayan shaye2, yana shiga dakinsa ya ganshi fes kaman ba dakin ba koba a fada ba yasan Jawwad ne ya gyara, ya danyi Murmushi ya karasa inda fridge dinsa yake amma me yaga an kwashe komai na ciki se madara, iya saninsa Jawwad baya taba masa kayan shaye2 tunda suka taba fada akan haka, a fusace ya mike ya fita harabar gidan yana kwalawa Me gadi kira, a sukwane me gadin yazo dan Jalal baya shiga harkarsa indai yaji yamasa wannan kiram to akwai matsala Jalal yace "Bayan Jawwad waya shigarmin daki? Seda gabansa ya fadi take ya rikice yace yace "Ammm Ilham ce yallabai" a fusace Jalal ya juya ya shiga cikin gida, dakin Ilham ya nufa yana zuwa ya tarar ta fito daga wanka tana sanye da rigar wanka, tana duba goshinta inda Jalila ta daketa da bucket cike da tsana yace "Ke ubanwa yabaki izinin zuwarmin daki?" "Nikuma?" "tambaya ta ma kike zan tattakaki, ina kayana da kika kwashe a fridge?, nakine koke kika ajiyemin, ina kayana"? Yafada cikin shouting "Ni ban taba maka kaya ba, kaje dai ka duba" fizgota yayi ya dauke ta da mari, "nizaki Rainawa hankali kinsan nawane kudin kayan nan kuwa, ki gayamin ina kayana ko in shakeki, inkuma kinfara shane kema se inji" dafe kunci tayi tana kuka "Ban saniba, niban daukarma komai ba, meyasa kai Azzalumi ne wallahi se Allah yasaka....... Tas! Yakuma wanka mata mari wallahi sekin fitomin da kayana, gobe in ance kikuma shigarmin daki bazaki ba yai kanta, da sauri ta haye gado tana ihu sosai  "Nashiga uku, atemakeni wallahi ya haukace ze kasheni, bashida hankali " kalmar hauka data kirashi yakara bata masa rai, kan gadon yabita ya shaketa dama kuma a buge yake, Da sauri Mummy ta nufo dakin a gigice, tana zuwa ta tarar ya shake Ilham idonsa yayi Jawur, Daddy ma da sauri ya fito ya nufo dakin, a gigice Mummy tace " Jalal meye haka inka kasheta fa?" " Na kashe banza, ubanwa ya kaiki dakina kika tabamin kaya" Da kyar daddy ya kwace Ilham a hannun Jalal, Daddy ya kalli Ilham yace "Ilham meya kaiki dakinsa mekika taba masa?" "ni wallahi bani bace ba, Jawwad ne ya shiga, kuma nida naje Jalila na tarar tana gyra dakin, ni ban taba masa komai ba" takarasa fada tana kuka "Jalila tabbas itace" ya fada a ransa juyawa yayi ya fice daga dakin da sauri. Daddy yaita bawa Ilham hakuri, suka fita suka bata guri, Ilham fashewa tayi da kuka "lallai Jalila bata da mutunci, bayan dukan datayi min shine taje ta kitsamin sharri, wannan wce irin Jarabace" haka Ilham taita kuka. Shikuwa Jalal yana komawa dakinsa yarasa mezeyi ya huce, Jalila ba karamin Asara tai masa ba, yasan itace ba wani ba, giyace me matukar tsada da wuyar samu, ga kwalayen sigari duk ta kwashe masa haka ya kwanta yana tunanin mezeyiwa Jalila ya huce ne. Nana tanata waya da Mahmud, abun nasu ya rikide yakoma Soyayya, Jalila ta kule a cikin bargo tana chatting, Zahra take sanarmata ankuma kama baban Samira, ya zaneta ashe tanada karamin ciki, sannan yaje Club yakama Saurayin Samira ya sossoka masa Kwalba, A sukwane Jalila ta tashi zaune, takira Zahra, Zahra na dagawa tace "Jalila kinga sakona ko?" "Eh nagani Zahra dan Allah dagaske kike koda wasa?" "Haba Jalila yazan miki wasa a wannan maganar wallahi gaskene, har wasu sunje dubata tana Asibiti" "Thank you for the Update dear, nagode sosai Zahra Allah ya biyaki" ta kashe wayarta, ta shiga tunanin mezatyi wanda zata sa A rike Alhaji Kabiru wannan karon kar asakeshi a gurfanar dashi a kotu. Take Suleiman ya fado mata a rai, wani dan guntun murmushi tayi, tamike ta shige toilet ta rufe kofa sannaan ta kira suleiman, sun dade suna waya, tagaya masa komai, tace dan Allah inda wani taimako daze mata yayi, a karbi case din abawa wanda zasu jajirce a gurfanar dashi a kotu, yamata Alkawarin zeyi iyayinsa, sannam intanada wani sheda ta tura masa, ta turawa suleiman dukkan waya da chat dasukayi da Alhaji Kabiru, ta tiramsa har recording din maganar su Samira da barazanar da suka dingayiwa Zahra, Suleiman yace insha Allah zeyi kokari yaga me ze iyayi, yace zesa amasa bincike, kafin yazo kano tai masa godiya sukayi sallama sannaam ta fito daga toilet din, tana fitowa Nana ta dan tsuramata ido sannan tace "Jalila kekam me kike a bayi haka, kinkusa awa daya fa, murmushi Jalila tayi tace " Ke Awa nawa kikayi kina waya, kai Nana Allah ya shiryeki da sa'ido wallahi" sukayi murmushi gaaba daya banda Naja, data ketawani hura hanci tana shan kanshi, Jalila ta kalli Inda Naja take sannan tace "Bari inzo inkira Yaya Jawwad inji in yayi bacci, in beba ya tayani hira, Tunda ke Nana naga hankalinki nakan wannan Mahmud din" Nana tai murmushi tace "Jalila bazaki gane ba Mahmud ya hadu, he is so romantic" "Aifa gashi nan gaba daya kin Afka soyayya ba kyaji ba kya gani" suka kuma dariya, Naja ta tsurwa Jalila ido, jira take taga Jalila ta kira Jawwad tai mata rashin mutunci amma taga Jalila tayi kwanciyar ta. Can cikin bacci Jalila ta farka, take jin surutu kasa2, tai shiri setaji Naja ce take waya da Saurayi kusan karfe ukun dare, ga wayar tasu batsace kawai sukeyi, Jikin Jalila yai sanyi, "Yanzu wannan ake kokarin a hada salihin bawa kaman Jawwad da ita, bazan taba bari hakan ta faruba, ai gara Hanan da wannan" Naja tacigaba da wayarta dan tunanin ta gaba daya bacci sukeyi, haka Jalila takasa komawa Bacci har Asuba. An samu Jeje ya farko da kyar, ya zubarda jini sosai, dan haka ana bukatar akara masa wani, duk abokan shaye shayensa suka zame sukece bazasu iya ba, suma jinin be wadace su ba, balle su bashi, Jeje yace dan Allah agayawa Jalal yasan ko kowa ya hanashi Jalal ze bashi Jini, sukace dan dai sako zasu gayawa Jalal. Kusan kwana hudu Jalal be kara ganin Jalila ba, Jalal yarasa yadda zeyi ya ga Jalila, ko gidansu yaje ya dena ganinta, sannan kuma ta dena zuwa gidansu, gaba daya ransa a bace yake, saboda wannan mummunar Asara datayi masa, shiba kudinne damuwarsa ba se wahalar samu da irin wannan giyar take dashi, kuma ita kadaice in yasha yake jin yaji yadda yakeso. Yana zaune yaji karar mota, ya leka ta window palourn sa yaga Daddy ne yafita shida Mummy, jinjina kai yayi, Wayarsa ya dauka ya kira Jawwad, tana fara ringing Jawwad ya dauka, Jalal yace "Kana inane?" "Maama ta dan aike nine, ya akayi?" "Kagayawa kanwarka Mummy na nemanta" Jawwad yace "to bari in kirata zatazo" ya kashe wayar, Jawwad ya kira Jalila a waya yagaya mata, bata kawo komai a ranta ba tace zataje. Jalila ta dauki gyalen doguwar rigarta ta saka, ta fito ta tafi gidansu Jalal, sam ta manta da tasaka an fita da kayan giyar Jalal. Koda taje gidan ba kowa, abun yabata mamaki, ta hangi Ilham a kitchen tana hada Abinci, dan haka ta dan Jira Ilham tafito, tana fitowa Jalila tace "Yawwa Ilham, ina Mummy kuwa? Ance tana nemana" A fusace Ilham ta kalleta "Ban saniba matsiyaciya jarababbiya, wallahi senasaki kuka kaman yadda kikemin, saboda kin iya makirci, kikayi min sharri gurin Jalal bayan dukan da kikamin, shima yazo ya shakeni ya kusa kasheni, wallahi in sharri ne gidan kika tarar, sekin gane bakida wayo, ina nan ina shirya miki trape kuma wallahi sekin fada" cikin mamaki Jalila tace "Ke ni ban gane wani makirci na miki ba, shi makircin ba kekika sanshi, dan Allah ina Mummy"? "Ninake nemanki ba itaba" waigowa tayi ta kalli Inda Jalal ke tun karo ta, tsayawa tayi kaman wata gunki tana kallonsa har ya karaso inda take, A fusace yakamo hannunta yai waje da ita yana janta, Ilham na ganin haka tace "Allah yasa yamata dukan mutuwa" cikin sanďa ta biyo bayansu. Be tsaya da ita ko ina ba se part dinsa a gaban fridge, ya bude fridge din ya kalleta a fusace yace "Ina abubuwan da kika kwashemun a fridge?" kallonsa tayi ido cikin ido, ta dauke kanta tai masa shiru "Magana nake miki ina kayaana?" "Meye kayan naka?" "Tambayata ma kike?" "Eh, ai bansan wani kayan bane gara ka gayamin, idan nina dauka, se ince maka nina dauka inbani bace ba zance bani bace" "Ke meyasa a rayuwarki, kikeson rainamin hankali ne? Kekika dauka ko kaffara bazanyi ba, ina kayana ko in kakkaryaki yanzun nan" ta kalleshi cike da tsiwa da gadara tace "Na dauka na zubar a shara, nabayar an fita dashi ansaka a bola" ta kare maganar tana kallonsa up and down, wani mugun takaici ne ya kama Jalal, shi takewa wannan gadarar haka, hannunta ya janyo, sukazo daf suna iya jin numfashin juna sannan yace "Ubanwa yasa ki daukarmin kaya, kekika ajiyemin?" "ba uban daya sani, nina sa kaina, kaga sakarmin hannu, last week ka hankade ni kakusa karyani yanzu kuma kana kokarin karasamin hannu, cikani" lallai Jalila ta kai makura wajen iya rainin hankali, ta masa laifi kuma tana masa gadara "Ka cikani nace kobaka jinane, kaikam Allah ya shiryeka, kota lafiyarka bakayi, se tsabar masifa da taurin kai ni cikani.... Wanka mata mari yayi, wanda yasa Jalila dena gani na wani dan lokaci, "bansan a dadin lokutan dana dauka ba ina miki kashedi akan kifita daga harkata, ke wace irin mara zuciya ce, wace irin uwar shishshigi ce ke? Darajar Ummi da Jawwad kikeci da tuni na kakkaryaki na karya banza, ina ruwanki da mara tarbiya wanda baya ganin darajar iyayensa, ina ruwanki dani? Ke kullum burinki kiyi abunda zaki bata min rai ko?" tuni Hawaye ya wanke mata ido, dan sau daya aka taba marinta shima Hanan ce, kuma seda ta koyawa Hanan din darasi, idonta na kwararar da hawaye, cikin nutsuwa tace " Hakane na fiye shishshigi, kuma inka karyani ka karya banza, amma da ina cin darajar Ummi da Jawwad koda wasa bazaka mareni ba, dan nasan Jawwad baze taba marin wanda yafito daga ahalinka ba, Nagode sosai da wannan marin da kaimin, bazan taba mantawa ba, Allah yabaka Hakuri, Allah ya huci zuciyarka nadena maka shishshigi Insha Allah, Kacigaba da shan giyarka Jalal da dukkan wani nau'i na shaye2 karka dena, bazan kuma takura rayuwata akanka ba, na tafiyar da lokuta masu tarin yawa akan tunani dan ganin kazama mutum kamar kowa, sannan mutane sudena kyamatarka, nashiga damuwa da gwargwamaya saboda kai, but this is what I deserve from you, dana san abunda naimaka ze bata maka rai ta kai gaka mareni da banyi ba, ina me baka hakuri, Insha Allah dana kammala abunda nake zan dena maka shishshigi, balle incigaba da bata maka rai" gaba daya jikin Jalal yayi sanyi, be gama gane inda magamganun Jalila suka dosaba "Cikani in tafi" yana kokarin yin magana, cikim Zafin Rai tace "Kacikani Jalal tun kafin in rama marin dakayimin, kaine mutum na biyu daya mareni a rayuwata, wadda taimin na farko seda na tabbatar da na koya mata darasi, kaima wasu dalilaine zasu hanani ramawa ka cikani nace maka" tai maganar tana Hawaye, gaba daya Jalal ya rikirkice, ta fizge hannuta ta fito waje ta tafi gida, seda ta tsaya a waje ta gyra fuskarta ta maze sannan ta shiga gida. Ilham da take labe kuwa gida ta koma tana murna tareda yiwa Jalila Allah yakara. Shikam Jalal guri yasamu ya zauna yai shiruu yana tunani, danasanine ya lullube shi, meyasa ya mareta ya akayi har ya mareta, "Jalila ce fa ya akayi na mareta ne? Mtseww yarinyar nan ta fiye shishshigi da taurin kai" magamganun Ilham da mamanta da sukayi a Asibiti ne suka dinga dawo masa. Mikewa yai da sauri yabi bayan Jalila amma kodayaje gidansu ma tariga ta shige cikin gida, dakin Jawwad ya tafi ya zauna yai shiru duk abun duniya ya dameshi musamman inya tuna Hawayen daya gani a fuskarta. Wayarsa ce tafara ringing, lambace ba suna ya daga yasa a kunensa, anan aka sanar da Jalal Jeje yana kwance a Asibiti rai a hannun Allah yana bukatar jini amma an rasa me bashi, bill din Asibitin dana magani ma ba'a biyaba, Jalal yace Insha Allah gobe zezo Asibitin aduba jininsa in yayi daidai asawa Jeje, sannan ze biya bill din Asibiti. Jalila bata taba zaton Jalal ze iya marinta ba, yau taki kula kowa har dare ba wanda ta kula, duk yadda Naja taso ta tsokane ta suyi rigima Jalila taki yadda. Washegari karfe sha daya na safe Jalal ya shirya ya tafi Asibitin da Jeje yake, ya tausaya masa ganin halin dayake ciki, bakowa a gurin Jeje se shikadai gashi ba'a wani kula dashi saboda ba'a biya kudin Asibiti ba, Jalal yana zuwa yabiya kudin Asibiti, sannan yasa aka canzawa Jeje daki, Jalal yana zaune agaban gadon Jeje, yana jira likitocin suzo aje lab a duba in jininsa zewa Jeje, 'Yan sanda biyu suka shigo dakin suda wani babban mutum sekuma Jalila mamakine yakama Jalal ya tsaya yana kallonsu, Kokusa Jalila bata nuna tasan Jalal ba sukaje gaban gadon Jeje, y'ansandan suka mikawa Jalal hannu suka gaisa, amma hankalin sa yana kan Jalila, ta kalli babban mutumin ta nuna Jeje tace "Yallabai wannan ne, shine wannan" mutumin ya gyada kai yace "aidaganinsa kaga criminal, ni kaman na taba ganinsa a wani guri, amma wannan fa, dan uwansa ne kokuwa? Shima wannan da gani drunker ne" kalmar drunker da Suleiman yafadawa Jalal, Jalila taji bataji dadi ba, amma ba yadda zatayi tunda Jalal yana shaye2 Jalila tace "Yallabai yanzu zakaji komai daga bakinsa" ta taka a hankali ta tafi gaban gadon Jeje ta tsaya ta kalleshi ya kalleta tace "Yau nacika maka alkawarin dana dade inayi maka, senaga bayanka, inaga kusan sau hudu ina gayamaka wannan kalmar, bari inbaka wani sako kagayawa ubangidan ka Oga KB, kokuma ince Alhaji Kabiru, kagaya masa Ni Jalila Aliyu Imam, ni nasaka aka kamaka da shi da 'yarsa a gidan karuwai" gaba daya suka juyo suna kallon ta. ❤️❤️❤️❤️ ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 inayinku irin sosai din nan comments dinku nasani nishadi da bani karfin gwiwa inayinku ina kaunarku nima Allah ya barmin ku 😍😍😍😍 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣8⃣81 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Gaba daya sukayi shiru suna sauraranta, tareda kallon mamaki, tacigaba da cewa "Sannan kuma zan tabattar maka da zarginka Nice kuma nasaka aka dauke Jalal ranar birthday dinsa" ta juya ta kalli Suleiman tace "Yallabai gashi nan, ku tambayeshi" Suleiman ya janyo kujera gaban gadon Jeje ya zauna, ya kalli Jeje yace "Ya jikin naka dan uwa" da kyar Jeje ya motsa baki yace "Da sauki" suleiman ya gyra zama yace "Inbazaka damu ba, zamuyi maka tambayoyine gaskiya muke bukatar ka gayamana in kayi karya, zamu daukeka a haka mutafi da kai office ka warke a can, mecece Alakarka da mutumin daya yi maka wannan raunukan?" Jeje yace "Ubangida nane, ni yaronsa ne" "Ubangidanka kamar yaya? Aikin me kake masa, A ina kuka hadu? Yaushe kafara masa Aiki?" Jeje ya juya ya kalli Jalal ya sunkuyar da kai kasa, a fusace Suleiman yace "magana fa nakeyi maka, kabani Amsa kuma in kayimin karya seka gane kuskuren ka" Jeje ya juya ya kalli Jalal yace "Jalal ina fatan zakamin Afuwa jin abunda ze fito daga bakina, Asalina nidan garin Azare ne, a cikin wani kauye, mahifina ya dakkoni yakawoni Almajiranci lokacin inada kananun shekaru dabasu fi takwas ba, tunda aka kawoni bawanda yakuma zuwa inda nake, balle susan halin danake ciki, sedana shekara goma shahudu sannan naje gida, kodanaje gida mahaifiyata ta rasu, nayi bakin ciki me tarin yawa nadawo kano, Rayuwar Almajiranci Rayuwace me matukar matsi da wahala, ba kula ba Abinci sabulun wanka wanki, balle magani komai kai zakayiwa kanka Rayuwa tayimin Zafi nafara shiga kasuwa domin neman na kaina, na gudu daga makaranta a haka na shiga makarantar boko, a kasuwar nan nasamu aiki a gidan karuwai nake musu aiki, a haka nakoyi shaye2, neman mata tunda kananun shekaruna, Jagaliya da bangar siyasa ba wadda ba'adamawa dani, mun hadu da Alhaji Kabiru a gurin campaign din wani ubangidansa, ninake jagorantar group din jagaliya da 'yan daba, Alhaji Kabiru ya gayyaceni gidansa da zummar yanaso inmasa wani Aiki zena biyana, na yadda na Amince, ya nunamin hoton Jalal yace akansa yakeso inmasa Aiki, nace kamar yaya, yace soyake Jalal yazama mugun dan shaye2 dan Jagaliya kamar ni, nace masa amma tayaya hakan ze faru yacemin inyi duk yadda zanyi zena biyana duk wata dubu Ashirin, idan har burinsa yacika Jalal ya lalace ze bani wasu kudi masu yawa, Na amince na karbi Adress din Jalal nafara zuwa unguwar su, na lura yanada saukin Kai dayawan kyauta, dukda na girmeshi haka na dinga kokari ina shiga jikinsa, ina turamasa Akidar shaye2, dabe amince ba har sabani muka samu, amma daga baya bansan ya akayi ba ya Amince da kansa, Abokinsa Jawwad yayi kokari yaga ya rabamu amma abu yaki, haka nakoya masa zuwa clubs daban2 kasancewar yanada kudi kayan maye se wanda mukeso zamu sha, Nayi kokarin in koyamasa bin mata amma yaki, sam hankalinsa baya kan wannan shidai kawai yayi shaye2 Alhaji Kabiru yacigaba da biyana makudan kudade kafin daga baya ya nunamin sana'ar dayakeyi ta saida miyagun kwayoyi da makamai ta barauniyar Hanya, idan Jarinsa yai kasa senazo nasan yadda nayi na karbo masa kudi masu yawa a gurin Jalal seyaraba yabani kasona, nazama babban Aminin Jalal, Alhaji Kabiru yasa nadinga Jan ra'ayin Jalal akan mutafi Dubai semunfi holewa acan bame samana ido, mussaman shi da mahaifiyarsa take takuramasa aikuwa ya yadda, shikuma Alhaji Kabiru yahada baki da wasu ma'aikata za'asaka kwayoyi a kayan Jalal, yadda semunje dubai za'a kamashi, idan mukaje dubai aka kamashi da wannan kayan hukuncin kisa ne, Amma abun mamaki se a Airport Jalal yace yafasa tafiyar nan, Saboda Jawwad. Ba karamin fushi Alhaji Kabiru yayi dani ba, yana ganin sakacina ne, da wannnan ya wuce se muka shigo da Hanna wata karuwa cikin tafiyar tamu, Saboda tasirin mace ga da namiji, Amma duk yadda taso ta janyo hankalinsa kanta yaki, Idan yayi shaye2nsa yayi bacci A gurin wataran Jawwad ne yake zuwa ya dauke shi, muka hada baki aka shirya masa birthday party, da nufin cewa za'ayi party ne imu imu abokan shaye2nsa, Amma abun mamaki muka ganshi shida yan uwansa dasu Jawwad, muka shirya idan aka bashi kayan maye a gurin zamu faki idon mutane mu daukeshi, za'a kaishi wani gida da aka kama Hayarsa na wasu yan awanni, Zamu kai Jalal can, a gidan Akwai manyan makamai, Akwai yara kanana da aka hayo aka saka a gidan, Alhaji Kabiru ya saye wasu manyan "yan sanda da kudi, cewar za'azo akama Jalal a wannan gidan, da wannan kayan za'ace an kamashi da miyagun kwayoyi, da Makamai sannam yana safarar yara mata, Amma shima se akasa aka Sace Jalal a gurin party muka nemeshi muka rasa, shima Alhaji Kabiru yai fushi dani da kyar ya hakura, Sekuma karon karshe da Alhaji Kabiru yakamani da 'yarsa a gidan Karuwai, da muka dau tsawon lokaci tareda ita, Yallabai wannan shine Abunda ke tsakanina Da Alhaji Kabiru " gaba daya dakin yayi shiru, Jalal cikin Rawar murya da sanyin jiki yace " Jeje waye Alhaji Kabiru, Menayi masa haka A rayuwa? Laifin menayi masa yazabi ganina a wannan Kazamar Rayuwar?" Jeje yace" Alhaji Kabiru shine mahaifin wannan Abokin naka Faruk, da mahaifinsa ke yawan yimasa kashedi akanka, sannan kuma shine tsohon Saurayin mahaifiyarka data Yaudara, Yasha alwashin daukar fansa" "Shine ya zabi Ramawa akaina? Ina ina lokacin dahaka tafaru tsakaninsu? Meye Nawa a ciki? Meyasa kowa akaina yakeson daukar fansa? Meyasa? Jeje nikayiwa haka ko? Kashiga Rayuwata ka lalatamin komai, harda kokarin Rabani da Aminina Jawwad na yadda da kai amma aka hada kai da kai ana hadamin wannan miyagun tarkunan, Yanzu badan Allah ya kiyayeni ba.... Kasa karasa maganar yayi, Hawaye yafara fita a idonsa ya mike yanufi hanyar fita da Sauri, bayansa Jalila itama tabi da Sauri, tana kiran Sunansa amma kafin ta cinmmasa tuni ya hau motarsa ya kunna, ya tasheta da gudu yabar Asibitin. Haka ta dawo dakin data bar Suleiman, suleiman ya kammala tambayoyinsa. Jeje ya kalli Jalila yace "Kin shammaceni fiye da tunanninki, ban taba zaton karamar yarinya kamarki zata iya aikata wannan abunba, kin kassaramin Rayuwa, kisani Babu wanda ze iya daukar mataki akan Oga KB, saboda za'a sakeshi ki Saurari abunda ze biyo baya idan aka sake shi" wani mugun kallo tayiwa Jeje "Duk wani zalunci da kassara Rayuwa yabiyo bayan wanda kukayiwa Jalal, Azzalumi daga kai har uban gidan naka, Kaike min kallon karamar yarinya, duk abunda nasa gaba sena ga bayansa, zamu gani nagama da babinku har gaban Abada, kuma ka saurara kagani ko ansakeku zalincin dakukayi baze barku ba" Ganin Jalila ta dau zafi sosai yasa suleiman yace "Kwantar da hankalinki, ki share hawayenki wanda zan dankawa case din shima wanine, za'adau matakin daya dace, kaikuma ina gurin kake wannan maganganun ko? Ka kara daure kanka zaka gane bakada wayo" sannan ya kalli Jalila yace "Shi waye wannan din? (JALAL) Jalila tace" Yaya nane" "Gaskiya an cutar dashi Sosai, and he needs counseling, kusa ido sosai akansa sannan ku kuladashi, ajashi a Jiki a dage da Addu'a har Allah yasa a raba shi da shaye shayen nan" "Hakane Insha Allah za'ayi kokarin hakan, " Yawwa yanzu dai muje in ajiyeki a gida ko? " " A'a ka ajiyeni a hanya dai" Yai murmushi yace to muje. Jalila ta koma gida cike da farinciki jin  kamshin Nasara tana saka ran tunda aka kama Jeje to ko Jalal be dena shaye2 ba ze rage sosai, tunowa tayi a halin da yabar Asibitin "ko yana ina yanzu?, Allah yasa yazo gida lafiya" ta shige cikin gida abunta, tana shiga Nana tace "Jalila ina kika tafine?" "Hmm kedai bari kawai, gidansu Zahra naje, amma ai gani na dawo" "Kinci sa'a Abba baya nan, shiyasa kika samu sake" Murmushi Jalila tayi tace "Aiko yana nan ma baze ce komai ba" "kyaji dashi dai, anjima ze dawo yayo waya ya tambayeni kina ina? Nace masa kindan fita" "Dagaske anjima ze dawo? Bari inzo inshiga kitchen dole in kintsa cikin Abbana, wannan karon ya dade a lagos" Nana tai murmushi "'Yar gidan Abba, dama yafi sonki akanmu" Jalila dariya tayi ta wuce cikin daki, ta shiga da Sallama amma Naja bata amsaba sema wani dogon tsaki data ja, Jalila ko a jikinta bata damu ba, dan ita nasarar data samu ta fiye mata duk wani neman magana da Naja takeyi, Jalila tanemi guri ta ajiye jakarta da hijjabinta, Wayar Jalila ce tafara ringing ta duba taga Hanan ce, Murmushi Jalila tayi ta daga wayar, tace "Hanan wai yaushe zaku zone?" "ke ba gaisuwa ba tambayar ya nake se yaushe zamuzo, idan munzo mezaki bani?" "Ba'abunda bazan baki ba, yau ina cikin farinciki, nasamu Nasarar daban taba zaton samunta ba" "Wannan wace irin Nasarace kekuwa kike ta murna haka?" "Bazaki gane ba, bakina akwai magana sosai, kedai kawai sekunzo" "Gaskiya kifara gayamin yanzu dan zaki barni da tunani" "Gaskiya bazan gayamiki yanzu ba, innafara bazan iya gamamiki ba, kuma zakiso kiji komai, kawai se kinzo dai" "Amma naso kifara gayamin yau, daddy ya kira Abba, amma yace yana Lagos kifara hada kayanki zebamu ke, tare zamu tafi Bauchi" "Eh dama yau ze dawo Abban, Wayaga Jalila a Bauchi, zanga gari inci waina inture" "Ji kwadayayyiya, ke burinki kici waina, to bazakici wainar ba" sukayi dariya gaba daya, Hanan tace "Baby, ina Abun kaunata" dan jimm Jalila tayi sannan tace "kinada lambarsa ai, meya hana ki kirashi" "Ban niyya ba, ke nakeso ki amsamin" "Yana lafiya" Jalila tafada a takaice "Kimikamin sakon soyayya, kigaya masa kullum yana kawwame a cikin wani bigire me girma a zuciyata, I Love Him, Kaunar Jawwad a jinina take, kigaya masa ina nan zuwa sati me zuwa, in ganshi" "Kan bala'i wane Jawwad din, ke banason karamin karauwanci, kobaki San anmasa mata bane?" NaJa ce take masifa daga gefe jin an ambaci Jawwad, dayake duk wayar da suke tana ji, Hanan tace "Jalila se anjima ki isarmin da sakona gurin abun kaunata, ba ruwana da kowace mace ko mata hudu aka masa Wallahi seya saki daya ya Aureni, sannan kigayawa me maganar nan Hanan tafi karfin tayi karamin Karuwanci se babban Karuwanci me lasisi, sati me zuwa Insha Allah zan shigo kano, zan gwada mata nawa salon karauwancin, ki gaida mutan gidan" Hanan ta kashe wayarta. Naja ta hau bala'i ta inda ta shiga bata nan take fita ba, yayinda Jalila ta samu guri ta zauna ta dinga kyalkyala dariya, tace "Allah ya kaimu my Hanan tazo, za'a sha drama, zanga yadda zata kaya, agama mu fece Bauchi in garin dadi in zamana se ankuma ganina" Hakan yakara bakantawa Naja rai, ta tashi fuuuu tabar dakin, Seda Jalila tagama dariyarta sannan ta mike lokaci2 Jalal yana fado mata a rai. Kitchen ta tashi ta tafi, ta tarar an Aiki Nana, ta shiga tafara Kokarin dora sanwa musamman dataji batun Abba ze dawo, tana tsaka da Aiki Jawwad ya shigo ya sameta "Sannu kukunmu, kullum cikin adanamana cikinmu kike, weldone baby" ta juyo ta kalleshi tana murmushi "Allah yatemaki babban Yaya, da girman kujerarka, Nace Yaushe za'a dakkomin Abban, na dade ban ganshi ba fa" takarasa cikin shagwaba, karasowa yayi gabanta yace "Autar Abba saekin rikici anjima kadan zanje dakko shi ai" "Yawwa naji dadi sosai, Ina dan uwanka ne?" "daga gurinsa nake, bayajin dadi ya kwanta bacci" "Meyasameshi haka?" "Jalal ba a rabashi da damuwa, be gayamin ba, yace yana bukatar hutu ne kawai" dan jinjina kai, har cikin ranta takejin tausayin Jalal, hawayen dataga yanayi dazu a Asibiti ya tsaye mata a rai, basarwa tayi tace "Yaya Su Hanan zasuzo a cikin next week Insha Allah, zamuje Bauchi in Abba ya yadda" "Bauchi kuma? Zasu daukemin ke?" "Ai bazan dade ba ai, nima zanga gari sosai" "Bawani nan nidai bansoba gaskiya, banason kiyi nisa dani" tai murmushi tace "Hanan tace inmiko mata gaisuwa, tace in gaisheka" "nifa nayiwa Hanan laifi Jalila, da tana kirana mu gaisa amma yanzu ta dena" "Karka damu Yaya Jawwad, nasan halin kayaya don't mind her" "Kinsan banason in batawa kowa rai ni" "Ni zanbada wannan shedar akanka, kai abun sone ga kowa Yaya Jawwad, Irinka basu dayawa ko a cikin mutane shiyasa........ " To maye bita zaizai" gaba daya suka juyo, Maama ce itada Naja a kofar kitchen din, suka karasa shigowa "Jawwad ban isa in gayamaka magana kaji ba saboda wannan shegiyar yarinyar ko? Sam kaki saurarar Naja kaki kulata, ka tare a gindin wannan 'yar macen, to wallahi baka isaba Jawwad, Akan yarinyar nan idan na juya maka Baya sedai kanemi wata uwar baniba" da Sauri Jalila ta kalli Maama, Naja se kara zigata takeyi, Maama tace "Eh kalleni da kyau, munafuka Mayya za' a mallakemin da kaman yadda uwarki ta mallake ubanki aka dinga wulakanta ni a lokacin, wallahi baki isaba kinyi kadan, kuma dan uwarka dan ubanka Naja zaka Aura, kekuma kije kinemi mara mutunci mara Asali irinki, ba dana ba dan dangi gaba da baya" Jawwad yace "Maama dan Allah kiyi hakuri, kidenai gaya mata haka" "Wato bakason bacin Ranta, gara batamin Rai akanta ko? Nikae gayawa abunda zanyi, ka kiyayi bakina Jawwad" A hankali Jalila ta tako ta rabe gefen Maama zata wuce, Naja ta kamayi mata Gwalo, bata kulata ba ta wuce daki. Tana zuwa daki tasamu gado ta Haye, ta sunkuyar da kanta se Hawaye wani nabin wani, Jalila ba karamin dagawa Maama kafa take ba amma sam ita bata gani, amma lokaci yana zuwa da zata gane kuskuren abunda take mata, amma tayiwa kanta Alkawarin seta koyawa Naja hankali. Koda Nama ta dawo tayi mamakin ganin Ran Jalila a bace, tabarta da fara'arta amma ta dawo ta tarar da ita rantaa a bace, Nana tace "Jalila nasan wasu lokutan zaman gidan nan baya miki dsdi, mussaman da Naja ta dawo gidan nan, amma kiyi hakuri komai me wuce ne, dukkan tsanani yana tareda sauki" Murmushi Jalila tayi tace "Ni nace miki ammin wani abunne? Bana jin dadine kawai" "Amma ai idonki ya nuna kuka kikayi" "Baki yadda dame ma fada ba kenan" Nana tace "shikenan Tashi muje, tunda kin kafe, amma idonki ya nuna akwai damuwa, muje mukarasa girkin" Jalila tai kokarin ta danne damuwarta sucigaba da aiki amma abun yaki yuwuwa, ko yaya Nana ta kauce se Jalila zubda Hawaye, ita kanta tasan tana Hakuri da kauda kai akan wasu abubuwan. Da la'asar sun kammala komai Jalila tayi wanka ta canza kaya, amma duk ranta ba dadi, tasan Jawwad ma yana nan ransa babu dadi, da sunci karoda Naja seta dinga yar mata da miyagun maganganu, ga Maama agurin babu damar ta rama, "Ai wallahi Maama mungode Allah, danginmu a tsarkake muke, ai karshen masifa a hada maka zuri'a da Arna" Maama tace "Godewa Allah kam yarinya, dukkanmu musulmi ne, babu shegu babu Arna" Naja tace "Maama 'ya' yan halak dinma im aka bincika wasunsu shegune, dan Arna da Auren suma bin maza suke" A fusace Nana tace "Naja waike dabbar dajin inace? Wani irin hauka... Maama ta katseta ta hanyar cewa "Rufemin baki ko make miki baki, aiba karya tayi ba kudinma babu tabbas kun hada jini da ita" ficewa Jalila tayi gaba daya daga cikin gidan tafito harabar gidan. Nanna ta yunkura zata bi bayan Jalila Maama tace "wallahi kika bita sena baki mamaki, wuce ki zauna daga nan inta tafi karta dawo, haka Nana ta koma ta zauna" Koda Jalila tafito harabar gidan, taga Manu driver da abokansa, a harabar gidan suna gyran flowers, ta duba taga bataga motar Jawwad ba, dan haka ta wuce part din Jawwad, ko ganin gabanta batayi, ta samu gefen kujera ta zauna ta toshe bakinta tafara kuka, bata son kowa yaganta balle a rarrasheta ta zauna tana kukanta, tanajin yadda ranta yake mata zafi. Tana tunanin meyakamata tayi ta huce yadda Maama ke wulakanta ta, bata son gayawa Abba halin da'ake ciki, tasan hakan ba karamin matsala ze jawowa Maaman ba, tana bukatar wanda zata gayawa damuwarta koba komai ta rage damuwa, tasan Hanan zigata zatayi tayi rashin mutunci, gashi ita bada kowa ta yadda ba, balle tagayawa wani abunda ke damunta,,  tana cikin tunani tareda kuka taji magana "Meyasaki kuka haka?" bata san da mutum a dakin ba, dan haka ta juya da sauri da doguwar sumarsa ta ganeshi, sam bataga kowa a dakin ba, shiru tayi tacigaba da kukanta, karasowa yayi gabanta ya zauna ya zuba mata ido, ji tayi duk ya takurata a hankali yace "Meyasaki kuka haka?" "dan Allah nika kyaleni, ina ruwanka da kuka na" "Inada ruwa da kukanki, kamar yadda kike da ruwa da Rayuwata, now talle me what happens?" ❤️❤️❤️❤️ ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 inayinku irin sosai din nan comments dinku nasani nishadi da bani karfin gwiwa inayinku ina kaunarku nima Allah ya barmin ku 😍😍😍😍 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  2️⃣9️⃣82 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Banza tai masa ta dauke kanta, yakuma kallonta yace "Gayamin mana" A fusace tace "bazan fada ba, meye hadinka da damuwa ta?" "Nasan kinajin haushina saboda kuskuren da'aka samu, amma... " kace kuskure? Ba wannan ne karo na farko daka mareni ba, kace na fiye maka shishshigi, nakuma yi Alkawarin na dena yimaka kaikuma meye naka nayi min shishshigi, dalla matsa kabani guri in wuce" "zan baki guri ki wuce, amma meyasa kika damu dani haka, kike bani wannan kariyar bansaniba, dukda irin halayena? Kinyi kokarin kareni a lokuta daban2 bansaniba meyasa? Gashi kinsan abubuwa dayawa dani ban saniba, at least kin haska wani bangare a Rayuwata da yakasance me tsananin duhu, nesanta Jeje dani hakika haskene me yawa a rayuwata, bansan ya akayi na yadda da Jeje nafara wannan muguwar rayuwar ba, kawai na tsinci kaina a wani yanayi dani ka dai nasan menakeji, amma meyasa kika temakeni, kike kokarin ganin kin canza akalar Rayuwata?" yai tambayar yana kara tsareta da ido,  itama kallonsa takeyi dan bata san mezatace masa ba, wani uban tsaki taja ta wuce ta gefensa ta fice daga dakin. A hankali ya koma ya zauna yana tunanin abubuwa da dama, abubuwa dayawa ya dinga tunawa, Jalila tayi Rawar gani a Rayuwarsa, yanzu ya gane abubuwa dayawa da a da sam besan dasu ba. Itakam guri tasamu tai zamanta taki komawa cikin gidan tanata zancen zuci, karar motar Jawwad ne ya dawo da ita hayyacinta, shida  Abba ne ya dakko shi a Airport, da fara'a Jalila ta tashi ta nufi inda suke, Abba yace "Jalila bakida lafiya ne? Naga kin rame haka" murmushi tayi "Haba Abba duk wannan kibar danayi kayana sunmin kadan fa" "Anya kuwa in yadda? Idonki kaman kinyi kuka fa" "Abba nikam meze sani kuka yau zanganka? Bacci nayi kawai, kawo jakan in rike maka" tasa hannu ta karbi jakarsa, Jawwad yana ganin dakiyar Jalila daka ganta kasan tana cikin damuwa, amma ta maze tanata kokarin boye damuwar. Ba karamin murna sukayi ba dawowar Abban nasu, Jalila tasan koba komai zata samu saukin wani Abun, bayan sallar magariba suka gabatar masa da Abinci yaci, nan suka sake aka shiga hira da Abba, Maama tanata dan dari2 kar Jalila tagaya masa wani abu, dan ta lura tun dazu Abba yake tambayar Jalila koda matsala amma tace ita ba komai. Sekusan goma na dare suka watse suka tafi dakunansu. Ilham tagaji da azabtarwar da Jalal yake mata, yakamata sunemi wata mafitar, tsawon shekarun datayi a gidansu Jalal bataga alamar zasu cinma burinsu ba, Jalal mugun baudadden mutum ne, ga tsabar jaraba da masifa, gashi da rashin yadda, kwanan nan ta lura kaman yakara tsanarta batasan metayi masa ba, ta lura yanzu har uwassa ma yakara fita harkarta, ko cikin gidan baya shigowa, mikewa tayi ta tafi palourn mummy, ta tura kofa bako sallama ta shiga ta samu guri ta zauna Mummy ta kalleta tace "Ke lafiya kika shigomin bako sallama meye haka?" "Mummy yaushe zaki cikamin alkawari na ne?" "Wanne kenan?" "Mummy har yanzu banga alamar Yaya Jalal ze yadda ya Aureni ba, lokaci fa kuremin yake ni macece yakamata zuwa yanzu kiyi wani abu akai, ina sonshi, banajin zan iya Auren wani bashiba, kitemaka Mummy dan Allah kiyi wani abu" Ajiyar zuciya Mummy tayi "Ilham yakikeso inyine? Yaron naan kullum wutar kiyayyata ruruwa take a ransa, kiduba rashin lafiya nayi amma da naje kansa ga yadda ya rikice gana sambatu infita baya son ganina, ya zanyi Ilham? Kaina ya kulle al'amarin Jalal sunfara bani tsoro" "Kina nufin in hakura dashi kenan?" "Bahaka nake nufi ba, amma kidan karamin lokaci, nina miki alkawari ai, bakuma zan saba ba" "Shikenan Mummy seda safe" Ilham ta tashi ta fita ranta a bace, ji take kaman ta shake Mummy, takoma dakinta ta kulle kofa, ta dau waya takira ummanta tagaya mata abunda ke faruwa, tace mata ta kwantar da hankalinta, in tasamu lokaci taje gida, zasu san yadda zasu bullowa lamarin Jalal da Mummy. Da sassafe Jalila suka shiga kitchen hada Abinci, bayan sun kammala kowa ya hallara a palour don karyawa, bayan an gama breakfast suka shiga hira, anan Maama ta sanarda Abba ai Naja tazomusu hutune, sannan akwai maganar datakaeso zasuyi da Abba amma ba yanzuba, ba karamin faduwar gaba Jalila taji ba dan tasan be wuce zancem Auren Jawwad da Naja ba. Abba nan yashiga rarraba musu tsaraba kamar yadda ya saba in yayi tafiya, Abba yabada zuma a gwangwani yace akai gidansu Jalal, A ajiyewa daddyn Jalal, ya daga waya ya kira Jawwad yace yana son ganinsa, bayan yagama waya da Jawwad ya kalli Jalila yace "Baby Babanki yayo waya daga Kaduna (baban Hanan) yace nan da kwana uku zasuzo, yanaso zasuje dake Bauchi yana neman Izinina, nace masa inkin amince ba damuwa amma bana so ki dade a can" Jalila tai murmushi tace "Na yadda Abba, zanje" Nana kam ta hade rai tace "Ni gaskiya ban yadda ba" Abba yace "Jalila nayi mamakin saurin Amincewarki da batun tafiyar nan, iya sanina dake ba kyason barin gida, amma ya'akayi haka, ko akwai wani abu bakyason gayamin ne?" "Haba dai Abba, ba wani abu ni kawai inason inzaga inje garuruwan dabantaba zuwa ba" "Eh hakan yana da kyau, amma bazan bari ki dade ba kinga ga komawa makaranta" Jawwad yai Sallama ya shigo palourn, ya durkusa ya gaida Abba sannan ya gaida Maama, aciki ta amsa masa dan tanajin haushinsa, yakoma gefen Abba ya zauna yace "Abbana gani, Allah yasa ba laifi nayi ba" "Aini baka laifi a gurina, da dai wannan ce tafi kowa iya laifi" Abba ya fada yana nuna Nana, dariya sukayi, yayinda Nana ta dan hade fuska da sigar shagwaba tace "Abba niko? Aikam bana wani laifi ni" Abba yace "Anya kuwa a tambayi Jalila?" haka Abba yasake ya dinga wasa da dariya dasu, banda Maama da take ta cika tana batsewa, Naja kam dama tuni tabar gurin, Abba ya kalli Jawwad yace "Babban mutum, daddynka yamin magana yace yasamo maka aiki a NNPC amma kace kai A'a, yace in rarrasheka ka karba, meyasa bakason Aikin" "Abba ba banaso bane ba, banason tafiyane saboda Jalal, bansan wani hali ze shiga ba, dukda Alhamdilillah ana samun cigaba a daidaituwar lamuransa, amma banason in tafi yacigaba da mummunar Rayuwa tunda......... Ai kafin yakarasa a fusace Maama tace" Jalal din ubanka ne? Kai meyasa bakada tunani ne? Ana nema amaka gata amma kana maganar wani, baka isaba seka karba ka tafi, tunda kagama karatun zaman jiranwa zakayi? Shiru Jawwad yai bece komai ba, a hankali Nana da Jalila suka zame suka bar palourn ya rage saura Maama, Jawwad da Abba, Abba yace "Jawwad tashi kaje zamu karasa maganar" Jawwad ya tashi ya tafi, Abba yace "Waime yasa mata wasunku bakuda halaccine? Haba Maman yara, Abunda Jawwad yayi, yai dai2 shine halacci irin kaunar da yaron nan yake masa bekamata kice hakaba, ki kyale shi zuwa wani lokaci tukuna mugani, kinsan kowane dan adam baya wuce rabonsa" "Naji, Amma Jawwad ya kai munzalin da a yanzu yadace ya fuskanci Rayuwarsa, ya nemi Aikinyi sannan ya mallaki iyali" "Eh gaskiyane, samun Aiki ba wani babban Abu baneba, kuma bacewa yayi bazeyi Aikin daza'a samomasa ba sedai yace abashi lokacine saboda Jalal, Amma kuma aini har yanzu becemin ga wata wadda yakeso ba tukuna, kinsan mutumin nawa da kunya Akwai fulatancin sosai a tareda shi, Allah yasa ko budurwa ma yanada ita" Abba ya karasa zancen cikin murmushi, Maama tace "inma bashida ita se asmomasa, bazan cigaba da zura masa ido se ya tsofe ba Aure ba, dama maganar danakeson yimaka kenan, ga Naja nan 'yar gidan Yaya mairo da ita nakeso in hadashi, tunda yarinyar itama ba laifi akwai hankali" Abba ya danyi shiru sannan yace "To banki ta takiba, Amma banason ayi abunda ze zamana an cutar da dayansu, yakamata muji ta bakinsu tukuna" "Kamarya semunji ta bakinsu, muba iyayensu bane ba dole subi abunda mukeso, hakan ze kara karfin zumuncin dake tsakaninmu" "To Allah ya tabattar mana da alkhairi, ni bari in wuce daki zan dan kwanta, kar amanta akaiwa Baban Jalal wannan zumar" "Za'akai" Abba ya wuce daki. Jalila tanata tunanin yazata bullowa wannan lamarin, dan in aka hada Jawwad Aure da Naja an zalunceshi, gashi tasan Maama bazata taba barin Jawwad ya Aureta ba, nan duniya tasan inta Auri Jawwad tayi sa'ar miji, salihin bawa da baruwansa da hayaniya"da taga tarasa mafita taje ta janyo trolley dinta ta fara shirya kayan dazatayi Amfani dasu dan tafiya bauchi, taji gara ta dan bar garin tayi nisa maybe ta huta da wannan abubuwan daga wannan se wannan. "Kayan me kike hadawa haka?" "Kayan da zan tafi dasu Bauchi mana" "Jalila bana son kitafi, badan hutunmu next week ze kareba da binki zanyi" "Allah sarki my Nana, nikaina zanyi missing dinki da kiriniyarki" "Mtseww Allah raka taki gona, inkin tafi karki dawo bakar kaya kawai, daga nan kema kitafi inda uwarki ta tafi" Nana ta juyo ta kalli Naja a fusace tace "Wai Naja ke wace irin mahaukaciya ce" da sauri Jalila ta dakatar da ita ta hanyar cewa "Ke Nana wayagaya miki in kare yana Haushi ana kulashi, kyaleta dan Allah, innaje Bauchi me kike so in kawo miki" Naja tace "Ke kin isa kice min Karya, uwarki ce Karya baniba" Jalila tai sauri tace "Nana naji kaman muryar Maama tana kiranki yi Sauri kije" Jalila ta tura Nana waje ta dawo ta zauna ta kalli Naja tace "Uwata batada katon baki da zako zakon fika kuma bata haushi kaman uwar wata, ki kiyayi ranar da bomb dina ze tashi dake, Naja har inda Yayarki Sa'adah ke zuwa a zubar mata da ciki nasani, tsohuwar karuwar Alhaji Kabiru ce dayanzu yake can ana shirin gurfanar da shi a kotu ko karya nayi? " zaro Ido Naja tayi "Karya kike ubanwa yagaya miki haka? Waye yayiwa Sa'adah sharri " "Kinga bana son wani borin kunya, ganina kawai kike amma bakisan waceni ba, bana zama da mutum ba tareda nasan wayeshi ba, karkiyi mamakin kema nasan komai akanki Jalila ta wuce tunaninki Naja, kibini a sannu im bahakaba zanmiki tonon sililin da sekin kasa hada ido da mutane, tun ranar dana ji kina waya cikin dare da Saurayi kema na fara bin diddigin ki dan haka ki kiyayeni" Gaba daya jikin Naja ya sanyi, yayinda gumi ya shiga tsatstsafo mata ta goshi, tunani tafarayi ya akayi Jalila ta san wani abu akansu haka, bakowa yasan wannan abubuwan da Jalila ta fada ba amma ita ya akayi tasani, Jalila ta tashi tabar inda Naja take tacigaba da hada kayanta. Tundaga Ranar Naja takejin tsoron yiwa Jalila rashin mutunci dan ta tsorata da kashedin datayi mata. Shikam Jalal yakara takure kansa, tun ranar bekuma haduwa da Jalila ba, yana son ya ganta amma baya samun damar hakan, dan ko a waje baya ganinta, Jalal baya son kowa yaje inda yake, baya iya cin Abinci idan ya tuna abunda Jeje da uban gidansa yayi masa saboda laifin da banashiba seyaji duniyar takara yimasa Zafi, ga abunda yaji Da kunnensa Ilham na fada akansa itada mahaifiyarta, Gakuma Jarumatar da Jalila ta gwada saboda shi abun ya dade yana bashi mamaki ya akayi Jalila ta gano Jeje da uban gidansa akansa suke Aiki harta hada wannan gwaramar, yana son jin wasu abubuwan daga gareta, idan yaji duniyar tayi masa zafi, seya sha giya ya bugu sannan yake jin dadi. Jalila tashirya kayanta tsaf tun dare, ji take kaman za'acireta daga prison zata tafi kwana biyu ta huta da tension din da suke kanta. Tun safe Jalila tayi wanka, tai waya da Hanan tace mata zasu karaso da wuri. Jawwad yaje ya takura Jalal yaci Abinci ya dinga yi masa Nasiha akan wannan takura Rayuwarsa da yayi, Jalal yace "Dan uwa, Nayiwa Kanwar ka laifi fa, nikuma tayimin Abunda har in bar duniya bazan manta ba" Jawwad yasan Jalila yake nufi yace "Allah yasa ba wani laifin tayi maka ba? Nasan Halin Baby sarai in wani abun tayi maka Allah yabaka hakuri" Jalal yai murmushi yace "Ba laifi tayimin ba, Amma tayimin abunda banida abun biyanta, inajin kunyarta abubuwan danayi mata abaya" Jalal ya karasa maganar idonsa fal kwalla "Subhanallah haba Jalal, haba 'yan mazan daddy, hawaye a idonka, kadena damuwa kaji, komai ze wuce banason ganin ka cikin damuwa muje kaci Abinci, Yau Jalilanma zata tafi bauchi" "Bauchi kuma?" "Eh Jalal, nima ban soba amma tasamu ta huta, zaman gidanmu sam baya mata dadi, Maama tana takuramata kuma Yaya mairo ce take zigata, banajin dadin abunda suke mata, inta tafi ta huta kwana biyu, tashi muje ka karya" Jalal be kuma cewa komai ba yabi bayan Jawwad suka fita. Da kyar Jawwad ya takura Jalal yaci Abinci shima kadan yaci yace ya koshi. Jawwad yaita tunanin me Jalila tayiwa Jalal haka har yake cewa baze manta ba?. She kusan karfe daya na Rana su Hanan suka karaso kano gidansu Jalila, a guje Jalila ta fito daga cikin gida ta rungume Hanan cikin farinciki, Hanan tace "Nayi missing dinki 'yat Baba" suka kuma rungume juna suna murna, Jalila ta kalli Abdallah tace "Babban Yaya sannunku da zuwa ya hanya?" "Hanya Alhamdilillah, da tuni munzo amma Hanan tasa muka makara" "Aina sani ita tahana kuyi sammako" Hanan tace "to mukoma kenan?" "A'a ni bance ba, ina Baban yake?" Hanan tace "Daddy shida Mummy zasuje su tarar da mu acan, dama zamuyi biki, yarinya har Anko daddy ya dinka mana nida ke" Jalila tai musu jagora har cikin gida a palour tabasu gurin zama, taje ta sanarda Abba su Hanam sunzo, dukda wulakancin da Maama takewa Jalila, amma ta sakarwa su Hanan fuska ba laifi, Jalila taje tagayawa Nana su Hanan sun karaso. Naja najin haka ta biyo su dan ganin wai wacece Hanan din nan ne tana zuwa palourn tayi turus, se yanzu ta tuna suntaba haduwa a gidan kamarta daya da Jalila, Amma Hanan takara kyau sosai seda Gaban Naja ya fadi, Hanan tanada kyau sosai gata ta iya gayu, Nana ta fito palour suka gaisa dasu Hanan nan aka shiga hira a palourn, Abdallah yace "Nifa banga Jawwad ba da mutumina Jalal" Nana tace bari inje in kiramaka shi, nasan besan kunzo ba tashi tayi ta fice a palourn Maama da kanta ta kawo musu Abinci, Abba ba ruwansa ya zauna suka dinga hira da Abdallah, Jalila ta janye hannuna Hanan zuwa dakinsu, Nana ta dawo itada Jawwad, Jawwad yashigo da fara'a ya zauna kusada Abdallah suka gaisa daga nan sukayita hira. Naja ta babbake a daki, dan haka Jalila bata samu damar yiwa Hanan hirar datake so ba sukayita hirarsu ta rayuwa, Hanan taji muryar Jawwad a palour tacewa Jalila zanje wanke Hannu" "baga toilet ba kishiga mana ki wanke" "Ba wanke Hannu zanba Jawwad nakeson gani" Naja tace "Ke mekikace meye hadinki da shi dazaki ganshi?" Ko tsayawa Hanan batayi ba tayi waje, amma kafin takarasa palourn ta tsaya ta daidaita nutsuwarta sannan ta fito palour, Da sauri Naja ta fito itama, unexpected Jawwad ya daga ido yasauke akan Hanan, takara kyau dressing dinta ma yayi ba karya, gaba daya besan lokacin dayake kallonta ba, tabass Hanan kamarta daya da Jalila a ransa yace "tsarki ya tabatta ga Allah, ba dangin iya bana Baba, amma ya halicci masu kama daya kuma ba twinsa ba, sedai sunada dan banbanci" Cikin kasaita ta wuce shi a palour ta nufi kitchen. ❤️❤️❤️ ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 inayinku irin sosai din nan comments dinku nasani nishadi da bani karfin gwiwa inayinku ina kaunarku nima Allah ya barmin ku 😍😍😍😍 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  3️⃣0️⃣83 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Hanan takuma dawowa zata wuce Abdallah yace "Auta bakiga Jawwad din naki bane" dan kallon Jawwad tayi, tayi murmushi tace "Naganshi mana" Naja kamewa tayi a gurin musamman dataga Jawwad yana kallon Hanan, da alama beji dadin yadda Hanan taki kulashi ba. Abdallah yace "Wallahi Hanan totally dinta se a hankali, duk ta takuramin wai muyi Sauri muzo taganka amma ta ganka ta wani basar" Jawwad yai murmushi yace "Kyaleta Abdallah zamu shirya ne, maybe gajiyar Hanya ne ya hanata yimin magana" "Bawani gajiya tsabar wulakanci ne kawai" Hanan ta murgudawa Abdallah baki, suna hada ido da Jawwad ta kashe masa ido daya, gaba daya ya rikice, gani yake kaman kowa yaga Abunda Hanan tayi gaba daya yakasa sukuni, ita kam Hanan ta wuce Naja takoma inda tabar Jalila a daki, ba kunya Naja takuma biyota dakin, Hanan tana shiga tace "Ohh God, Jalila Haidar yakara kyau yakuma zama babban mutum, wayyo dadi kasheni, naga farincikin zuciya ta" Jalila tace "Waye kuma Haidar?" "So kike indinga kiransa da sunan da kike kiranshi ne, kowa yace Yaya Jawwad nima ince Yaya Jawwad, Haidar dai kaman in sace shi in gudu haaka nakeji, yawwa Queen ranar muna waya dake naji wata namin kashedi akan abunda yake mallakina, wacece dan Allah?" "Nice nan, kuma wallahi duk maitarki iyayenmu sun tsaida magana, bashida wata mata in baniba, mayun banza dana wofi marasa zuciya" Naja ce taketa fiffika tana fadan maganganu Hanan taja wani dan tsaki tace "Jalila aina dauka wadda take cewa zata auri Jawwad din mace ce, ashe mata maza ce mata ta rako duniya, ke cewa akayi ya Aureki, nikuma Jawwad yana sona ne" , dan saurin kallonta Jalila tayi, lokaci da dama Jalila tana daukar abunda Hanan take a matsayin wasa, dukda tana ganin tsagwaron gaskiyar abunda Hanan din ke nufi a idonta Jalila na cikin wannan tunanin Hanan tace "zan tabattar da hakan anan kusa ba a nesa ba, ke Queen ina mutuminne tunda nazo ban ganshi ba" "Wakenan?" "kinfini sani, Jalal mana" tsaki Jalila tayi tace "Nifa bana son maganar wannan shirmammen" "Jalal dinne shirmamme?" "Eh shidin, ke Akwai Labari amma semun je bauchi Lafiya insha Allah" "To Allah ya kaimu lafiya" Abdallah yace "Jawwad nikam ina Jalal ne naganka kai kadai?" Jawwad yace "Yana part dina baya jin dadi" "Allah sarki, muje inganshi, muyi salla Azahar sannan mu wuce" Suka tashi suka tafi part din Jawwad, suka tarar da Jalal zaune akan kujera, yana kallon TV amma sam hankalin sa baya kan Tv, shigowarsu yasa ya daga kai, murmushi yayiwa Abdallah, ya mika masa hannu suka gaisa "Jalal ashe bakaji dadi ba? Sannu gaskiya ka rame, Allah ya sawwake" "Abdallah aini na warke tuntuni, Jawwad ne da zuzuta abu" Jawwad yace "Au ni nake zuzuta abu, dadinta kallo daya za'ayi maka asan baka da lafiya" sukayi Salla, suka zauna sukayi ta hira, Jalal ya sake sosai. Can aka jima Abdallah ya kira Hanan a waya yace su fito yanzu zezo su tafi, Hanan tace masa to, Jalila ta nunawa Hanan akwatinta tace "Hanan kaimin mota, bari in sa kaya" Nana tace "bari inje ingayawa Abba zaku tafi" Hanan ta ja trolley Jalila ta kai bakin mota, amma motar a rufe, tasan Abdallah suna part din Jawwad kanta tsaye ta tafi part din, tundaga waje take iya jiyo hayaniyarsu, shiga tayi da sallama duk suka amsa mata, ta fadada murmushin fuskarta ta Kalli Jalal tace "Yaya Jalal kwana dayawa, Yakake ya gida amma naga ka rame sosai" shima murmushi yayi mata yace "lafiya kalau Hanan, amma aini hakanake dama can ban rame ba, yagida ya hanya?" "Alhamdilillah, ina wannan kanwar taka, yama sunanta?" Abdallah yace "Kai Aku me magana, daga zuwanki kinfara zuba kaman kanya" Dan hade rai tayi "kace mufito kuma ka kulle mota, ga kayan queen can na fito dasu, kazo ka bude in samata a mota" "Sedai kizo ki karba kibude, bari mugama hira" "Gaskiya Abdallah ka dinga jin tsoron Allah muka katse namu hirar kace mu fito kaikuma ka zauna" Taki kallon inda Jawwad yake, balle yasaka ran zata kulashi, Jawwad ya karbi key din motar a hannun Abdallah yace "muje in bude miki motar, Abdallah bashida niyyar tashi yanzu" Dan murmushi tayi ta juya, Abdallah yace "tasamu abunda takeso, dama ba dan Allah tazo nan dinba, sarkin gulma wani inzo in bude mata mota, kawai kice Jawwad yataso gurinsa kikazo, sewani Iyayi kike" Hanan taji kaman kasa ta bude ta shige, Abdallah mugun dan rainin hankali ne Jalal yace "Ahha kai Abdallah ina ruwankane? Yada shishshigi haka?" "Auto nayi shiru, tunda ka goyi bayanta" Suna fitowa Hanan ta nufi hanyar komawa cikin gida, Jawwad ya kira sunan ta, ta tsaya amma bata juyo ba, ya karasa gabanta yana kallon ta amma ta sunkuyar da kai, "Hanan, menayi mikine? Tunda kikazo kin kula kowa amma ni kin shareni" "Bakomai" "Ban yadda ba komai ba, laifin menayi miki?" "Haidar dan Allah ka kyaleni, banason matsala, kace baka sona, gaa nazo na tarar da wata tana gayamin ita zaka Aura ya zanyi? Ina kokarin in cireka a raina amma nakasa, ganinka din nan ma yana karamin pressure ne, na damu da kai sosai kaikuma ka nuna baka sona, base in hakura ba, mezesa incigaba da shishshige maka?" Abun mamaki hawaye ke kokarin fita a idon Hanan, hakan na nuna maganganun da take fada har cikin ranta, Jawwad yace "Zannemi wata alfarma daya a gurinki, zakiyi min? " "Alfarma kuma? Wace iri" "Sekinyi min Alkawari zakimin Alfarmar" "Inkuma bazan iya bafa?" "Bazan tambayi abunda bazaki iyaba ai, abune me sauki" "To fadi in zan iya" yai murmushi yace "Sonake inkuma jin sunan dakika kirani dashi please, yanamin dadi" Dan zumbura baki tayi ta noke kafada, "Niba wani suna" "Kince fa zakiyi min Alfarma" cikin shagwaba tace "ni banyi Alkawari ba ai" "Please, ko inyi kuka ne sannan ki fada" "Eh to yi kukan in gani tukuna" sukayi dariya a tare, yanayin irin tsokanar Jalila haka Hanan takeyi, amma Hanan bata iya komai ba akan Jalila, Jawwad yace "Hanan da bakina ban taba cewa bana sonki ba, ban taba soyayya ba, amma nasan ina son Jalila so ba na wasa ba, kinga akwai alaka me girma tsakanin ki da ita, sannan batun Naja da kikeyi Wallahi Hanan yanzu haka ina dauriya ne kawai, Naja zabin Maama ce, tanason in Aure ta ni inason yiwa Maama biyayya amma bana tunanin zan iya Auren Naja, Hanan nasan kinshiga damuwa saboda ni but am very sorry, banason kowani rai ya shiga damuwa saboda ni, ta mussaman ke ce a gurina" Hanan tai murmushin da seda hakoranta suka fito, ta jingina da motar tace "Kasan meyake kara burgeni da kai Haidar?" "A'a sekin fada" "A dukkanin maganganun ka kana kokarin fadar gaskiyane, sannan kanada tausayi shiyasa nake kara sonka, Amma bari ingaya maka wani abu, alakar dake tsakanina da Jalila bazan so ta baci ba, saboda ina mata so na gaskiya, bazanyi wani abu in cutar da ita ba, Amma maganar gaskiya kanawa Jalila so ne irin na 'yan uwantaka ba soyayya ta Aure ba, haka ma zuciyar Jalila tana maka sone na' yan uwan taka, nasan zakayi mamaki, Jalila bata taba soyayya da wani ba, tanada Samari Amma har yanzu taki yadda zuciyarta akwai wanda takeso saboda taurin kanta, kaima zan baka lokaci zaka gazgata abunda nake nufi" Gaba daya zuciyar Naja ta gaama tsinkewa, Ganin Hanan taki dawowa yasa ta fito harabar gidan, amma tayi tozali da Hanan da Jawwad se murmushi yake, tunda take da Jawwad maganar minti goma bata hadasu balle yaita wannan murmushin, Nana ma befiye shiga harkarta ba, a da tayi tunanin ko Jalila yake so, wato wannan yarinyar me girman kan bala'i ita yakeso, koma dai duka yake sonsu ne tana tsaye tana kallonsu Jawwad yafara magana "Hmm Hanan ina kika samo wannan ideology din, yazakice Baby Akwai wanda takeso, kuma munayiwa juna son 'yan uwan taka?" "Ban fada domin in shiga tsakanin ku ba fa, nawa hasashen ne haka, Ita kanta Jalila bata son wa take so ba, bakowane lokaci take yadda da zuciyarta ba tana karbar abubuwane da lissafin kwakwalwarta" "Hanan ya akayi duk kika san Jalila haka ne?" "Haidar a zaman danayi da Jalila motsi tayi nasan abunda take nufi, nasanta fiye da yunwar cikina" kyar yake kallon Hanan ko kyaftawa bayayi yana juya maganganun ta a ransa, ganin yanata kallonta yasa tace "ya dai kona bata maka raine?" "Ina so kicigaba da magana ne, komai kikayi kyau yake miki" murmushi tayi tana rufe fusaka, yace "masha Allah yanzuma bakiga yadda kika kara kyau ba" Abdallah da Jalal suka fito daga part din Jawwad, ba karamin matching Jawwad da Hanan sukayi ba, suka nufosu Abdallah na shirin sukarasa ya tsokane su, shikuma Jalal Jawwad kawai yakson ya titsiye yau, amma kafin su karasa Naja ta rigasu dan Naja ba karamin kulewa tayi ba, dan haka ta taho kaman wata kura, ta nufo su Jawwad, tana zuwa ta rike kugu tace "ke wace irin matsiyaci ya ce haka? Nace miki Jawwad shine wanda zan Aura na meye zakizo kina wani shige masa, kina wani salon karuwanci meye haka?" Hanan kaman tayi magana, sekuma ta fasa tace bari inga matakin daze dauka Aikuwa Jawwad yace "Naja meye hakane wai? Yazaki kirata da karuwa me tayi miki? Wannan wace irin magana ce" "Eh dole kace wace irin magana ce mana, kasan ni zaka Aura amma kazo kunfi minti Ashirin a nan gurin alhalin niko hirar minti goma bakayi dani"  Jalal yace "wai dan Allah meyake damun wasu matanne, yanzu meye hakan kuma?" Abdallah yace mata se Addu'a ai, se yanzu Naja ta lura da shi, wancan zuwan ma tare sukazo, ita da Abdallah ze Aureta aida ta hakura da Jawwad Abdallah yace "kinga baiwar Allah kiyi hakuri dan Allah, Kekuma Auta, Jawwad fa Ustaz ne, kinzo kin wani kanainaye shi tun dazu, kina kashe masa murya kina fari, Ashe ma ankusa Aurar dashi, ai seki hakura" gaba daya sukayi dariya suka maida Naja kaman wata mahaukaciya, Hanan tayi murmushi cikin kasaita tace "Macen data kai mace, itace idan tace tanason take samu, ba ragowar muna mata ba" shikam Jawwad ba karamin kunya Abdallah yabashi ba Sannan Hanan tace "gaskiya Abdallah kai dan hana ruwa gudune, Yaya Jalal ka shiga tsakanina da Abdallah, My Haidar karka damu da Abdallah haka yake da wannan takurar" Jalal yace "Inyee ashe har suna aka canza maka abun masoya kai Jawwad, se anyi magana ya dinga sunkuyar da kai waishi kunya, bayan yagama zuba kalamai shima" Da sauri Naja ta shige cikin gida, tanata kumfar baki a palour ta tarar da Nana sun fito  Jalila daga part din Abba "Ni za'ayiwa hauka, ni wannan  yarinya zatayi wa karuwanci, wallahi yau duk bala'in da za'ayi se anyi, shegiyar yarinya a gabana kaman zata hadiye Jawwad kan bala'i, a fusace Nana tace "Ubanwa ya hana kiyimusu  can sekinzo mana nan, inkina yiwa Jalila tana kyaleki, ita wannan a yanzu intaga dama wallahi zata saka sojoji sumiki dukan mutuwa, dan ko a ina take a a fadin kasar  nan akwai yaran babanta" Jalila tace "Nana, bari inje waje inga meke faruwa, Nasan halin Hanan sarai, ba kanwar lasa bace, dukan sojoji yafiye maka dukan wannan bakin nata, koba komai yau na huta, Anamin maganin karya me remote" Aikuwa Jalila takara angizo Naja, "ke dan abu ta kazakazanki, nikike cewa karya?" Ai Jalila bata jira taji metake cewa ba ta fito. Jawwad duk yarasa ya zeyi dasu Jalal, se tsokanar sa sukeyi shida Abdallah yana sunkuyar da kai, itakuwa Hanan ko a jikinta data fuskanci sun takura masa, se tace "cwt Haidar don't mind them, kaga Abdallah aiba a magana shima haka yake zuwa ana kashe masa murya, idan ana masa wannan kashe muryar seka sace shi ka gudu be saniba" seda ta danyi murmushi sannan tace "Kaga yaya Jalal Allah kadai yasan shime ake masa, shima nasan yana zagayewa yaje akashe masa muryar dayake takura maka, kaima ka dinga ramawa amma zanso inga budurwar Yaya Jalal inga in an kashe masa muryar shi ya yakeyi, sweet Haidar sena koya maka magana, adena takuramana" Jalal yai dariya yace "Ni Hanan aibana soyayya, ban santa bama balle inje a yimin wasu kalamai,, in aka fara yimin kalaman zan kiraki kizo kigani, sedai fatan Allah ya hadamu da masoyanmu  na gaski..... Jalila ya hango tana sakkowa daga steps, tayi kyau sosai, amma abunda yabashi mamaki ta rame, "ko bata da lafiya ne? Tayi rama sosai, itama tana daga ido sukayi ido hudu, taji gabanta ya fadi "kaddai ace har yanzu Jalal bashida lafiya, wace irin rama yayi haka?" kallonta yake yadda take tafiya step by step, Hanan kam tuni taga abunda yake faruwa tai murmushi a ranta Jalila ta karaso tace "Yaya Jawwad ina fatan komai lafiya, naji Naja tanata masifa, Hanan me kikayi mata ne?" "meko zanmata? Dan kawai ta ganni da Haidar ne" Abdallah yace "karya takeyi tun dazu ta tsareshi anan tana zuba masa kalamai, tun yana jinkunya naga alamar kalaman sun fara shigarsa, murmushin yake Jalila tayi tace" nikam ki lallaba ku rabu lafiya" "karma a rabu lafiyan ba abunda ya dameni bane, haidar dina ne agabana" Abdallah yace "ke Hanan kinfiye zakewa, ance miki anbadashi amma kin nace" Hanan ta lura yadda Jalal ke kallon Jalila, itama Jalila tana satar kallonsa amma bata bari su hada ido, Hanan ta gyar murya tace "Queen kinga Yayyenki nan biyu sun takuramana, shi Abdallah nasan yadda Siyama ke kasheshi da kalaman soyayya, amma shi Yaya Jalal ban saniba, da nasani da na ramawa Haidar, amma gayamin ko kin san budurwarsa?" hararar Hanan tayi tace "Aiba tare muke yawo ba balle in san budurwarsa, seki tambayeshi ai" Hanan ta tintsire da dariya dama tana sane tayi hakan? Jawwad yace "Baby ina Abba ne?" "Yana cikin gida, yaya Abdallah ku shiga sekuyi sallama da Abban" "ok bari muje" Jawwad ya musu rakiya suka nufi cikim gida Jalila tayi mamaki yadda Jalal yake hira bazakece shine ba, Jalila tafara kokarin saka jakarta a mota Jalal ya dan kara kurawa Jalila ido, yazo kusada ita ya tsaya, ya danyi kasa da muryarsa yace "meyake damunki kika rame haka?" bata dago ba tace "ni ban wani rame ba, dama haka nake" "hmm, shikenan tunda kince haka, amma yaushe zaki dawo?" "Ka Aike nine, wai ina ruwanka danine?" "Aiba abun zafi bane, meye nayin fushin kuma?" "idan na tafi bazan dawo ba, idan na tafi zan hutawa raina indena ganin masu ba kanta min rai, kaima ka huta dame yi maka shishshigi, kaci karenka babu babbaka, inka gadama kaima ka gina club din shna giya" "meyasa ba kya mantuwane? Abu baya wucewa a gurinki kenan?" Su Hanan ya gani suna fitowa dan haka yace mata "zaki iya zuwa ki zauna a wani garin, kibar Jawwad din naki da Nana tsawon lokaci?, idan ina ganin ki inajin kwarin gwiwar dena wani abun, dama zan miki sallama ne dan inaga kafin ki dawo, zan koma Dubai da zama, bazan kara dawowa Nigeria ba, har abada, ina fatan kiyafemin kura kuran danayi miki, Sannan Nagode da kokarinki a kaina, keda Ummi bazan tabawa mantawa daku ba, sannan A shekarun baya, wani zuwa da kikayi, Su daddy sun baki kyaututtuka, ciki hada wani Jan Alqur'ani me red din box, nina baki kyautar wannan Alqur'ani sannan Akwai Ajiya ta a ciki. ❤️❤️❤️ ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 inayinku irin sosai din nan comments dinku nasani nishadi da bani karfin gwiwa inayinku ina kaunarku nima Allah ya barmin ku 😍😍😍😍 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. ..🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  3️⃣1️⃣84 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Kallonsa Jalila take kaman wata sokuwa, ya daga kai yaga su Jawwad da Abba suna tahowa, yakuma durkusowa yace mata "Allah ya kaiku lafiya" Hanan tana kallon abunda yake faruwa harsuka karaso inda motar take, Abba yayi musu nasiha tareda fatan suje lafiya, Abdallah ya shiga ya kunna mota, yafito da ita daga cikin gidan, Nana tace "Jalila dan Allah inkin tafi karki dade, zanyi missing dinki sosai" "Bazan dadeba Nana, nima zanyi missing dinki" suka rungume juna sannan Jalila ta karbi jakarta a hannun Nana. Hanan tazo bayan Jawwad ta wajen kunnensa tace "I love you Haidar, i wish to see you soon" ta juya ta shiga mota, murmushi kawai Jawwad yayi, Jalila ta bude mota ta shiga amma hankalin ta yana kan Maganganun Jalal. Jalal yazaga sukayi musabiha da Abdallah yace "Allah ya saukeku lafiya, ya kiyaye hanya" Suka amsa da Ameen banda Jalila da taketa zancen zuci. Abdallah ya kunna mota yafara ja a hankali Jalila tanata waigawa tana kallon Jalal harsuka bar layin, Hanan ta daki cinyarta tace "To ai seki dena kallon nasa haka" dan hade rai Jalila tai tace "kamarya indena kallonsa? Wakenan?" "Jalal mana, aishi kike kallo tukuna ma meya gaya miki ne naga jikinki yayi sanyi?" "Bansaniba, niba shinake kallo ba" Hanan tai dariya tace "Queen ba dai taurin kai ba, bakyason gazgata zuciyarki, ga abu a zahiri amma kinata wani basarwa" "Ke dan Allah ki kyaleni Hanan" Hanan tace "Na kyaleki" Abdallah yana jinsu yai murmushi yace "Hanan kokece sirikar tamu ne? Keda Jalal kuke boyewa" "Tab Allah ya kiyaye, bawani sirika, wadda ze Aura tana gidansu cousin dinsa ce Ilham" Hanan tace "karya kikeyi, kefa kikace bazaki bari ya Auri Ilham ba" "to dan ban bari ya auri Ilham ba kuma ni seya Aureni?. Abunnasu na nema yakoma fada dan haka Abdallah ya shiga yimusu hira aka manta da wannan zancen, Jalila ta rarraba hankalinta me Jalal ya ajiye mata a cikin Al'qur'ani tsawon wannan lokacin bata taba ganiba? Sannan mezesa yace ze bar kasar nan haka taita zancen zuci, Hanan ta fuskanci Jalila nacikin damuwa, Amma taurin kai ya hanata yadda. Nana taji babu dadi sosai da Jalila ta tafi jinta take kaman marainiya, Naja taje ta samu Maama ta gayamata abunda yafaru, Maama taimata alkawarin tasan matakin dazata dauka, zata kawo dukkan karshen wannan yaran, zatayi wa Abbansu Jawwad magana. Jalila se kusan takwas na dare suka isa garin bauchi, wani irin katon estate ne, dake dauke da gidaje dayawa a ciki, kuma kusan duk irinsu daya, tundaga farkon estate din suke cin karo da sojoji, da sunzo wucewa Abdallah yake daga musu Hannu, wani gida suka nufa, duk gidajen da Jalila ta gani a estate din wannan gidan yafi shi girma, shima akwai sojoji abakin gate din, bude musu akai Abdallah yashiga sunata daga masa hannu, Abdallah ya tsaya suna gaisawa, suna masa sannu da hanya, daya sojan cikin gurbatacciyar hausar sa yacewa Hanan "Madam ba magana? Ko gajiyar ce?" Hannaan tace "kai ba'a magana nagaji kam" dubawa yayi yaga Jalila a motar, kafin yayi magana Abdallah yaja motar zuwa makekiyar harabar dake cikin gidan, Abun yabawa Jalila mamaki bayan sojojin dake bakin gate akwai wasu a cikin gidan, Hanan tafara fita sannan Jalila dukda magariba tayi, amma ko ina hasken fitulu ne, Jalila ta bude motar ta sakko, ga mamakin ta gaba daya idan mutanen dake harabar gurin yadawo kansu, harta dan fara tsarguwa, Abdallah ya bude motar yana janyo kayansu. Abdallah ina kasamo wannan kuma? Ko dama Hanan tanada sister ne? Suka dinga jerowa Abdallah tambayoyi, Hanan ta kalli wani soja tace Phillips ga kaya nan shigo dasu upstairs taja hannun Jalila suka shige cikin gidan. Gidan shiru se kamshin turare da Abinci dake tashi, gidan shiruu wani tangamemen palour suka shiga, tundaga palourn Hanan take kiran "Anty fiddo, kina inane?" wata matashiyar mace ce wadda bazatafi shekaru Ashirin da biyar ba ta fito tana cewa "Hanan wane irin kirane haka, Salla nakeyi ai yau kinzo kowa se san kin iso wannan ba.... Bata karasa maganar ba tayi shiru, ganin Hanan tareda Jalila, matar tace "Hanan menake gani haka, ina kika samo wannan me matukar kama dake?" Jalila tai murmushi tace "ina wuni Anty" Hanan tace "daga zuwanmu kin isheni da tambaya, ina mutan gidanne?" "suntafi shirye shiryen biki, anjima maybe kiga sun shigo" ta kalli Jalila tace "Sannu da zuwa baiwar Allah, shigo" Hanan tace "aiba gurinki tazo ba, innancy tana dakinta ne?" "Hanan ko kara babu, tana daki tana salla" Hanan taja hannun Jalila zuwa wata kofa, dakine me dauke da katuwar katifa da tv da bandaki da komai a ciki, gefe wata dattijuwace sanye da hijjabinta tana salla, daga imda Jalila take tana iya ganin dattijuwar fara ce tas daganinta kasan tana hutawa amma Jalila gani take kaman ta taba ganinta amma ta manta a inane. Hanan tace "Shugabaa Inna salla ake tayi ne? Jalila ga toilet nasan zakiyi Alwala bari in dawo" Jalila tace to, koda Jalila ta shiga cikin toilet din shima ya hadu, kaman ba na tsohuwa ba, Jalila tai alwala ta fito harta tada salla tsohuwar bata idar ba. Koda Hanan ta fito se tambayoyi suke mata ina suka samo Jalila, Hanan tace "Anty fiddo kimfiye tambaya wallahi" Abdallah yace "kusan shekarunsu takwas kenan a tare, yarinyar da daddy yake gaya muku ce yayi ya mekama da Hanan, itace yace zekawow Inna taganta" Wadda suke cewa Anty fiddo tace "Masha Allah, sekace wadda taimana maganin Hanan ce, kai amma Abdallah bantaba ganin wanda ba yan uwa ba masu kama kaman Hanan da wannan yarinyar ba, bari in kaimata Abinci masha Allah ashe itace 'yar daddy" Jalila ta idar da salallolinta a lokacin tsohuwar ta kammala nata lazimin, kurii ta zurawa Jalila ido, Jalila ta idar tazo kusada tsohuwar ta zauna tace "inna barka da yamma" kasa amsawa tayi sedai kallon Jalila da takeyi, Anty fiddo ce tashigo tareda su Abdallah, Inna ta daga kai ta kalli Hanan ta kalli Jalila tace "Haba nifa imce, nasan Hanan bata da wannan nutsuwar, amma ko idona neke ganin ba daidai ba, kamar duk Hanan dince?" tsohuwar kana jin yadda take magana kasan bafulatana ce, hausarta bata fita sosai Anty fiddo tace "daidai idonki ke gani, kinga me kama da Hanan ko? Ita daddy yake cewa ze kawo miki ki ganta ai" Inna tariko Hannun Jalila tace "mairo ashe dama kina raye zankuma ganinki, baki ganeniba, hafsatunki cefa? Allah sarki mairo ina kika shiga tsawon lokaci bamganki ba" sosai tsohuwar ta rike Jalila tana kuka, saroro Jalila tayi tana kallon Inna, Hanan tace "kekam Inna wai har yanzu bazaki dena wannan abun ba dan Allah?" Abdallah yace "Inna idan mairon takice haka zakiganta bata tsufa kamarki ba, wannan fa yarinya ce sosai, bakuwarmuce kamar da takeyi da Hanan dinki yasa Daddy yace ze kawo miki ita ya nemi alfarmar mahaifinta alfarmar mahaifinta ankawomiki ita amma kina kuka" Goge hawayenta tayi tace "yi hakuri yarinyata, daga zuwanki zanmiki shirme, zauna kusada ni" Anty fiddo tacewa "Inna bari muje taci Abinci se adawo miki da ita" inna tace "ita ya sunanta ne? Ko itama Hanan din ce" Abdallah yace "sunanta Jalila" "Kai wannan sunan da wahalar fada, na dauka itama Hanan dince ko mairo" Anty fiddo tace "Jalila taho muje" Jalila ta mike suka fito, Anty fiddo tace "Kiyi hakuri haka takeyi wani lokacin haka takewa Hanan ma, wani lokacin setayi ta kuka wai Hanan tana abu kaman kanwatta, kumafa mu bamu san kanwartata ba, bawanda yasan inda take wata kilama ta mutu, amma har yanzu inta tuna setaita kuka" Jalila tace "Allah sarki, kinsan babu abunda yafi dan uwa dadi duk tsufansa duk yarintarsa" "Hakane kam" Sun karrama Jalila sosai sukayi dinner sannan Hanan takai Jalila masauki, Jalila tace "Hanan bari inwa Inna seda safe ko?" Hanan tace "inkikaje bazatayi bacci ba kuka zata cigaba, ki kyaleta seda safe" "to shikenan, amma Hanan meyasa duk gidan nan naku sojojine, koduk saboda babanane?" "Aiba daddy ne kadai soja a estate din nan ba, sannan duk wanda kika gani a estate din duk family dinmune, kaso uku bisa biyu na mazan dake estate din naan sojoji ne shiyasa kikaga sojoji ko ina, yanzu gobe in Allah ya kaimu zan kaiki kigansu akwai yan mata kamanmu, amma basu san munzoba, da yanzu an cika part din nan, Inna itace tushen family din nan, duk yarantane da jikoki da yaran jikokinta, sekuma kanin mijinta shima ya rasu amma akwai yaransa shima da jikoki a cikin estate din nan, mijin inna ya rasu shekaru bakwai baya, amma bata tunanin sa kaman kanwar nan tata tanabamu labarin kanwar ta, babban dantane kawai ya san kanwartata, shima bashida wayo sosai lokacin amma haka wataran take birkicewa ta wuni kuka" Jalila tai ajiyar zuciya tace "Allah sarki, tunda kika ga haka ba karamin shakuwa ne tsakanin ta da kanwar tata ba" sukayi ta hira sannan suka kwanta bacci, amma Jalila tana tunanin meyasa bata dakko Al'qur'anin nan ta taho dashi ba, tana son sanin me Jalal ya ajiye a ciki, ita tsawon lokacin da qur'ani yayi tareda ita bata tab ganin komai a ciki ba, to me Jalal yake nufi. Nana duk gidan yamata ba dadi, se yanzu takejin akwai shakuwa sosai tsakanin ta da Jalila, Naja kam haushin kowa takeji musamman Nana, Nana tarasa mema zatayi taji dadi, ta dakko waya ta kira Jalila suka sha hira, bayan sungama waya da Jalila, wajen karfe shadaya Nana ta fara kwalemar dakinsu kaman yadda Jalila takanyi wani lokacin, ta hargitsa komai tana gyarawa, Ilham ce ta shigo dakin babu ko sallama Nana ta daga kai ta kalli Ilham tace "Ilham anya ba batan hanya kikayi ba yaukece a gidanmu haka, yaushe rabonki da gidan nan" Ilham ta tabe baki tace "ba dole indena zuwa gidan nan ba na fuskaci anamin zagon kasa, dama mummy ce ta aikoni, tace ace tanason ganin Jawwad, naga bayanan, kuma bakowa a palour, kuma naji ance wannan yarinyar bata nan shiyasa nazo nan dakin, badan hakaba bazan shigoba" Nana tace "nifa bangane mekike nufiba Ilham, wani irin zagon kasa akemiki hakane a gidan nan"? "Haba Nana karki rainamin hankali mana, kema haushinki nakeji kun hada kai za'akwacemin Jalal" "wai dawa kike ne haka kimin bayani dalla2, dawana hada kai za'a kwace miki Jalal din?" "wannan tsinanniyar 'yar uwar taki mana, Kun hade kai zata kwace min miji" "Wai kina nufin Jalila ce takeson Jalal kokuma yaya" A fusace Ilham tace "Nana nifa wannan maganganun nan naki batamin rai suke karayi, ta yaya zakidinga rainamin hankali ne Nana, kina nufin bakisan kulla2 datakeyi na kokarin rabani da Jalal ba, son Jalal takeyi kuma nida ita tace seta rabamu akanme zan kaunaceta" Naja ce ta shigo dakin ta kalli Ilham tace "to yanzu tsakanin nidake watake rainawa hankali, waini narasa wannan shedaniyar yarinya ya take? Ba'agane gabanta ba'a gane bayanta, kekince tanason yayanki, ni daza'ayiwa baiko da Jawwad yace ita yakeso, katsam sega wata jarabbabbiyar tazo wai itama shi take so, nibana gane kan wannan yarinyar sekace dan wake Allah kadai yasan gabanta" Nana tace "Allah me iko, Allah gatan bawa, kowa ya kwaso tarkacen tsiyarsa seta jibge akan marainiyar Allah, yanzu ke Ilham keda Jalila tace miki tanason JALAL iya sanina ko shiri basayi dashi, tayay zakizo da wannan maganar kuma yanzu?" "Nana ke kanki yanzu haushin ki nakje kina rainamin hankali, ninaga abunda baki ganiba, sonshi takeyi kuma wallahi bata isaba" Naja tace "Ai daga ita har Nanan bakinsu daya, kedai kiyi iyayinki ki kwaci Saurayinki dan wallahi bata isa ta auri Jawwad ba daga ita har wannan kodaddiyar yarinyar, banda zalama ki hada maza kice kina so duk jarabarta ai daya zata Aura" Ilham tace "Aikuwa ba dai Jalal ba sedai ta Auri Jawwad dan bata isaba" Nana zuba musu ido tayi, dan tarasa mema zatayi kotace Naja tace "Ayi mu gani ai tafi dacewa da wanann dan shaye2, ba Jawwad ba kema banda jaraba mezakiyi da mashayi, ki kyalesu taje ta aureshi suta haukan tare" "ke gyara kalamanki ni dan shaye2 nakeso, kika fadi bakar magana akan Jalal zanmiki ba dadi wallahi" Abu yanemi yakoma fada tsakanin Naja da Ilham, Har Ilham ta juya zata fita, ta dawo ta nufi gaban drower da Nana ta fito da komai amma banda wani Dan karamin redbox, gaban drower taje tasa hannu ta dakko Al'quranin ta kalli Nana tace "Nana ya akayi wannan Al'quranin yazo gidan nan?" Nana tace "Na Jalila ne lafiya?" "Wallahi Nana ke makaryaciya ce, to wannan Al'quranin Jalal ne, kakrsa ce ta fanso masa a saudiyya, yanzu gashi a gurin ta, nace miki suna soyayya amma kin karyatani" Nana tace "kinga Ilham wannan Al'quranin fa tun wani zuwa datayi akabata shi daga gidanku, kekika kawo kayan amma kina wani zance daban" Ilham tace "to tunda kince nina kawoshi, to yanzu zan dauka, bekamata Abunda yake na Jalal yaje hannunta ba, kinsan son dayakewa Al'quranin nan kuwa?" "Ilham karmu yi haka dake, ki bani inta dawo sekuyi da ita" "Inta dawo kice meshi tazo ta dauka, inta matsu ta biyoni ta karba" Bayan Jalila tagama waya da Nana, sunyi waya da Jawwad yagaya mata yakira Abdallah yace masa sun sauka lafiya sukayi waya, ta kira Abba ma ta gasheshi, Hanan taja Jalila suka koma gurin Inna, Suna zuwa takuma rungume Jalila ta shiga yimata hira da labarai irin nasu na tsofaffi, Inna tanada abun dariya sun dade auna hira, zuwa jimawa 'yan mata da samarin gidan suka ding shigowa duk wanda yaga Jalila seyayi mamakin kamaninsu da Hanan kaman yan biyu, Hanan ta dinga zagawa da Jalila cikin estate din nan, suna da karamci kaman dama can sunsan Jalila tasamu kyakyawar karba, kwanan Jalila uku a garin daddyn su Hanan ya iso shida Mummynta, yaji dadin ganin irin karbar da'akayi wa Jalila, wannan karon sam Mummy bata nunawa Jalila tsana ba sema mamakin girman da Jalila tayi take. Inna tacewa daddy "dan Allah dan nan kacewa baban yarinyar nan yabarmin ita, wallahi kamar mairona haka take, musamman intana dariya ko tafiya" Daddy yace "haba inna, yazasu barmiki diyarsu, yanzunma sunyi kokari dasuka bari tazo nan" haka yaita lallaba Inna ta hakura. Dukda kulawar dasuke bawa Jalila hankalin ta yana kan Jalal tanason sanin hali dayake ciki, amma bata san wazata tambaya ba. Yau daddare Har sunyi shirin kwanciya Hanan tace "Jalila kina fama da damuwa a ranki, kuma nasan akan Jalal ne meyasa kika damu dashi haka, in ance kina sonsa kice karyane?" "niba damu dashi ba, ni bantaba jin son Jalal a raina ba, ina tausayinsane kawai" "karya kikeyi Jalila, kina son Jalal" "Hanan keba wadda zan boyewa wani abubace ba, bantaba jin son Jalal ba" "Naji bakyason Jalal, amma mekikeji akansa?" "Ina tausayinsa ne kawai, dakuma kasancewarsa da Abu mafi soyiwa a gurina wato Jawwad, ina tausayinsa ne da son ganin yazama mutumin kirki saboda Jawwad Hanan koke kikaji labarin rayuwar Jalal zaki tausaya masa" Nana Jalila tagayawa Hanan komai na labarin Jalal, har kokarin da tayi na ganin an kama oga KB da Jeje, dakuma abunda Jalal yagaya mata lokacin dazata taho Hanan jikinta yayi sanyi matuka sannan takara jinjinawa Jalila da wannan namijin kokari datayi da sa kanta a hatsari a boye ba tareda kowa yasani ba Hanan tace "gaskiya Jalal ya cancanci a tausaya masa, Amma kina ganin kowane ze iyayiwa Jalal abunda kikayi masa, Amma tsaya kinason sanin me Jalal ya ajiye miki a Alqur'ani" "tunda muka taho nakeson Sani" "yakamata musani, kira Nana a waya kiji in Alqur'anin yana nan ta duba mana" "Ai in banda ke seshi Jalal ba wanda yasan me nayi" "eh ai bazata gane ba" Jalila ta amince ta kira Nana, seda suka gama hira da Nana, kafin Jalila ta tambaya Nana tace "Baby  Ilham fa taga Alqur'anin ki wannan Jan, yau inayimana gyaran daki tazo, tace wai na Jalal ne, kakarsa ce tabashi ya akayi yazo gurinki tace inkin dawo kisameta ki karba" A fusace Jalila tace "What!!!? . 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  3️⃣3️⃣86 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Kara hade rai yayi ya shiga palourn ya zauna becewa kowa komai ba ya zauna, daddy ya kalleshi yace "son ka tashi lafiya" "Alhamdilillah" daddy yai murmushi yace "Masha Allah, kayi breakfast ne?" "A'a ina jiran Jawwad ne kuma bezoba" "bari a hada maka anan kaci" daddy ya kalli Ilham yace "Ilham hadawa yayanki Abinci mana" Jiki na rawa ta mike ta nufi dining din daddy ta hado masa kayan breakfast ta kawo ta ajiye, shidai be kulata ba ya zauna yafara cin Abincin sa, daddy suka cigaba da hirarsu shidasu Mummy, shidai Jalal bece musu uffan ba, yana kammala cin Abincin sa ya mike ze fita, daddy ya dakatar dashi ta hanyar cewa "Ina kuma zakaje? Zamuyi magana ne ai" Dawowa yayi ya zauna yana kallon daddy, daddy yace "Jalal kaga zamanka haka baze yuwu ba, tunda ansamu degree daya da kyar, kaga shekarunka sun fara Ja daga kai har Jawwad zuwa yanzu yakamata ace ansama maka abokiyar rayuwa a matsayinka na namiji, amma bantaba jin kacemin ga budurwarka ba, ko akwai wata bansaniba " Wani irin kallo Jalal yayiwa daddy sannan yace" dan Allah adena wannan zancen, in lokacin Auren yazo za'ayi, amma dan Allah for now a kyaleni" "A'a Jalal babu batun a kyaleka, banason cigaba da ganinka a haka ba Aure, bakasan Aure shine cikar mutum ba, inma baka da budurwa ne ga Ilham tace taji ta gani tana sonka a haka, meye laifin Ilham? Dan haka nakiraka tunda kaida Ilham duk dayane" "A zato na a baya munyi wannan Maganar ta wuce? Wannan tamkar maida hannun agogo bayane, nace bana sonta, bana sonta akan me za'a takuramin, kuma ai naga Aure ba wajibi bane, balle ace in banyiba nayi laifi, dan haka a kyaleni bana sonta bazan Aureta ba" A fusace Mummy tace "Baka isa ba wallahi, da abun kunyar da kake shirin jawomana gara aimaka Aure, kokana so kobakaso Aure se anyi shi" "Abun kunya na nawa kuma? Koke har yanzu abubuwan da nakeyi basu isheki kunya ba? Nagama magana ba wanda ya isa yamin Auren dole wallahi, duk duniya natasani wannan yarinyar natsani duk wani abu da yashafeta, Aurene bazan Aureta ba" Ilham ta rushe da kuka tace "Nashiga uku Mummy, menayiwa Yaya Jalal haka?" Mummy tace "rabu dashi, Aurene babu fashi, tunda yasan yafara biye biyen mata, har karuwai sufara biyoshi gida, rashin mutuncin sa ya wuce yaje ya samesu a can, se yafara kawosu gida, ai dole a dau mataki akansa" daddyn Jalal yaso ya hana Mummy karasa maganar amma seda ta karasa, Jalal dake shirin fita ya tsaya cak ya juyo "Niza kiyiwa sharri dan nace bana son wannan shashashar, Nine nakebin mata, kirasa dame zaki alakanta ni se wannan mummunan Aiki, to wallahi da in Auri Ilham gara a dauramin Aure da Akuya, Nagode da sharrin da kika yimin a matsayinki na uwata" "Ba sharri tayi maka ba Jalal, gaskiyane" juyowa yayi inda daddy ke magana, nan da nan idonsa ya canza ya harzuka matuka yace "daddy da bakinka? Kaima ka yadda zannemi matan banza? Ka yadda ni Jalal zan kawo karuwa cikin gidan nan? Ka yadda ni Jalal ina neman matan banza, lalacewata bata kai haka ba" daddy yace "Ya isa Jalal, ba sharri akayi maka ba, ni yarinyar tasamu a waje tace gurinka tazo, ita tacemin Akwai alakar dake tsakaninku wadda bata kamata inji ba, kuma lallai insaka Aureta shine kawai hanyar tsira da mutuncinta da naka, ka gayamin meye hakan inba neman mata kake ba?" Shiruu Jalal yayi ya marasa meze ce, mamaki gaba daya ya kamashi, a iya tunaninsa babu wadda zatayi masa haka, su Jeje ne kuma zuwa yanzu suna hannu kodai duk shirin Mummy ne haka? Amma a tunanin sa be cancanci daddy yayi masa wannan mummunan zargin ba, ba tareda yayi bincike ba ana alakanta shi da dabi'ar dayafi tsana a rayuwarsa wato zina. "Shikenan daddy naji na gode, Jalal danka mashayi kuma manemin mata, Daddy da ina neman matan banza da lalacewar da zanyi tafi haka, da ba tun yanzu ba matan banza sun dade suna zarya a gidan nan, dukda Jawwad yana rufamin asiri a abubuwa da dama bana tunanin ze yadda ya zauna da mazinaci, shikenan nagode amma kusani Wallahi bazan Auri wannaan shedaniyar yarinyar ba" Mummy tace "dalla rufemin baki, kai har kanada bakin dazakace bakason Ilham? Ba rufamaka asiri zatayi ba, kanada bakin kiranta shedaniya ka..... "Enough Mummy!!! Karki kara zagina waye silar komai, natsani Ilham natsani me sonta" yakarasa yana Zazzare ido, daddy yace "Jalal ya isheka haka, danme zaka dinga cewa ka tasani yarinya metayi maka haka? Lokaci yayi dayakamata kadinga dagawa mahaifiyarka kafa" "Daddy kayanke min hukunci bakayi bincike ba, kasan bana maka karya, nidai fatana kayi bincike kadena zargina, daddy kanamin uzuri a abubuwa da dama ban taba zaton haka daga gareka ba, sannan maganar Ilham wani abune daba lallai in gaya maka meyasa nace bana sonta ba, duk ku kwantar da hankalinku Insha Allah a satin nan zanbar muku gidanku, in bar muku kasarma gaba daya ku huta" Ya juya a mugun fusace yafito daga part din daddy, gaba daya jikin daddy yayi sanyi tausayin Jalal ya kamashi, ya juya ya kalli Ilham yace "Ilham mekika yiwa Jalal ne yake miki haka?" Ilham cikin kuka tace "daddy ni bansan menayi masa ba, yakemin wannan muguwar kiyayya" Mummy ta dinga rarrashin Ilham. Jalal kam tunda yafito yaji wani abu ya tokare masa kirji, dakin Jawwad ya tafi yana zuwa yatarar da Jawwad kwance akan gado ido a rufe, Jawwad yana kwancene zuciyarsa ba dadi yarasa yadda zeyi da matsalar ke damunsa, jin Jalal ya shigo ne yasa Jawwad ya bude ido, ya tashi zaune ya dake ya boye tasa damuwar ya kalli Jalal yace "Lafiya kuwa naganka haka meya farune?" Kasa magana Jalal yayi, sedai jijiyoyin kansa da suka mimmike idonsa jawur, se huci yakeyi kai dagani kasan akwai damuwa sosai. Jawwad yace "ka gayamin mana meke faruwa?" "Jawwad zan nemi visa, dole zan bar Nigeria a satin nan, kuma wallahi na tafi bazasu kara ganina ba" "meyasa Jalal, meyasa zakace haka?" "Jawwad nagama yanke hukunci, wannan karon karka cemin komai dan mutuwa ce kawai zata hanani tafiyar nan, zan bar Nigeria idan na tafi wallahi bazan kuma dawowa  ba". A kwanakin nan sam Jawwad be gayawa Jalal shikuma tasa damuwar ba, sedai kokarin lallaba Jalal dayake yayi hakuri ammma fafur yaki se shirinsa yakeyi, sannan sam yadena shiga gidansu ya kashe wayoyinsa dan karma anemeshi. Hanan da Jalila suna zaune suna hira da Inna a dakinta, Hanan tanata chatting ta dan dago ta kalli Jalila tace "queen Haidar baya daga waya lafiya kuwa?" tai maganar a shagwabe Jalila tace "kunfi kusa ai, nima bamuyi waya ba" "nifa duk na damu a satin nan sam banji muryarsa " Inna tace "waye kuma haidar, da kike kula dashi haka"? "Sirikinki ne, kwanan nan zezo kiganshi kyakyawa dashi in gayamiki yafi mijinki Alhaji kyau, kai kaf family dinku babu me kyansa" Inna tace "ke tafi can, anya akwai me kyan mijina, ai Imamu mijin Mairona ce kawai na yadda yafi mijina kyau" Jalila da sauri tace "Imamu kuma, shine mijin kanwartaki?" "Eh shine shima dan uwanane, dan Autan su Imamu shine baban Hanan" Jalila tace "Inna to wai ina suke yanzu ita kanwartaki" Inna ta danyi shiru tace "bari yarinya ta, Mu ukune a gurin babanmu nida mairo da yayanmu magaji, ni na Auri Alhaji dan yayar Innarmune, itakuma mairo ta Auri Imamu, dan kanin babanmu ne, yana son mairo sosai, 'yan fashine suka addabi garinmu, watarana suka shigo suka harbi wasu, sukayi Garkuwa da wasu, akayiwa wasu daga cikin matan fyade aka kora dabbobinmu sannan aka sakawa bukkokinmu wuta, kafin hakan tafaru yayanmu magaji ya saida  wasu daga dabbobin gadonmu nida mairo yarabamana kudin, to lokacin da 'yan fashi suka shigo garin mairo da mijinta basu dawo daga kiwo ba, A wannan harin aka kashe yaya magaji, nida Alhaji da matar Yaya magaji, da yaranta da nawa yaran muka gudu abun be ritsa damu ba, haka muka baro garinmu muka taho nan bauchi, lokacin duniya na kwance akabamu masauki, muka cigaba da rainon yaranmu, bayan wasu shekaru A hankali bayan wasu shekaru muka dinga haduwa da wasu daga cikin  'yan uwanmu, duk inda mukaa hadu sesu sedawo nan gurin mu su zauna, a haka har mukayi wannan yawan, Amma har yanzu danake miki wannan zancen bansan inda mairo da imamu suke ba, ni ko bangansu ba inga zuri'arsu, Hanan tana matukar kama da ita, amma dana ganki senaga kunfi kama da ita, komai naki irin natane, Allah yasa ke irin zuri'arta ce" Inna ta fashe da kuka, Jalila tace "Allah sarki inna, kiyi hakuri kinji Insha Allah zaki ganta ko 'ya' yanta, amma ni ban san kakannina ba inada kanan shekaru suka rasu, maybe da Yaya Jawwad ne ze iya sanin wani abun amma ni bansan komai akansu ba" Suna cikin maganar Yusuf yayi sallama ya shigo, su Jalila suka gaiaheshi ya amsa, ya nemi guri ya zauna ya kalli Jalila yace "'yar Baba kije palourn kasa, second floor kinada bako" gaban Jalila ne yai mummunar faduwa da sauri Hanan ta mike zaune tace "Bako kuma?" "Kece Jalila?" Yusuf ya tambayeta shiru Hanan tayi tana tunanin waye wannan kuma, ya biyo takan Yaya Yusuf, jiki a sanyaye Jalila ta mike, Hanan ma mikewa tayi zata biyo Jalila, Yusuf yace "ke dawo nan ki zauna, koke nace kije?" Hanan tadawo ta zauna ta zumbura baki, tana nazarin waye kuwa wannan" Jalila taje daki ta dakko hijjabinta har kasa tasaka, ta tafi a hankali ta tura kofar palourn ta shiga kanta a sunkuye tayi sallama. "wa'alaikum salam warahmatullah" dan daga kai tayi ta kalleshi ido hudu sukayi tai sauri sunkuyar da kanta Yace "karaso mana queen" Jalila a ranta too queen kuma iyayi, ta karaso ta zauna a kujerar da take facing dinsa, "barka da dare" "yawwa barkanki dai my queen fatan kina lafiya?" "Am not queen Jalila sunana" Murmushi yayi yace "to ai duk daya, koba haka Hanan take ce miki ba, kuma aini ya cancanta in fadi wannan sunan koba hakaba?" Shiru Jalila tayi, "to ya gajiyar biki?" "Gajiya tabi lafiya Alhamdilillah" "Masha Allah, ni sunana Ahmad nasan kinganni a bikin Yusuf, kobaki ganni ba nina ganki kuma kinyimin Jalila, nagayawa Yusuf ya nemamin izinin zuwa gurin ki a gurin daddy, daddy yabani damar inzo, sannan yace inmuka cika wasu sharuda sannan kin amince ze bani ke" ya danyi shiru sannan yace "Jalila harga Allah kinyimin inasonki Aurenki nakeson yi tsakanina da Allah, amma bazan miki doleba se abunda kikace" Shiru Jalila tayi tana wasa da yatsun hannunta "queen kice wani abu mana" still ahiru tayi "ko banyi miki bane? Ki gayamin ba komai, bazan miki dole ba" Girgiza kai tayi alamar A'a yace "to gayamin abunda ke ranki" Fafur Jalila taki magana yai murmushi yace "dago ki kalleni" Noke masa kafada tayi kaman yanda yara sukeyi sannan tace "to ni me zance?" "wow muryar ki da dadi Jalila, gaki shagwababbiya" murmushi ta danyi Wayartace tafara ringing, ya kalleta yace "daga wayar mana" Ta daga wayar tasaka a kunne Nanace tace "Baby ya kike dan Allah yaushe zaki dawo"? "kai Nana wai yaushe zan dawo ba rana sena gama hutawa" Nana tace "department dinku sukoma tun last week, nai shiru ban fadawa Abba kun koma ba, karyayi miki fada, sannan an kafe exams dinku yau" "dagaske menasamu?" "nidai nasamu upper credit, but Baby wallahi you are the most luckiest girl i ever seen in my life, kaf department dinku babu me points dinki, se zancenki ake, wasu sun sanki wasu basu sanki ba, lectures sunata a nuna musu ke" "Alhamdilillah yanzu ina Yaya Jawwad kwana biyu baya daga waya?" "Baby da banyi niyyar gayamiki ba, shiyasa naketa damunki ki dawo, Abba ya yadda Naja ta Auri yaya Jawwad, memakon yaya Jawwad yace masa bayasonta amma yayi shiru kinsan halinsa nan da kwana tara za'a kai kudin Auren sa gidansu Naja" Jalila ta manta da wani Ahmad a gurin a razane tace "What, Nana dagaske kike dan Allah" "Wallahi Baby dagaske nake, gashi yanata fama da Yaya Jalal shima wai ranar Asabar ze bar kasar nan, da se wani satin ze tafi, amma wani abun akayi masa a gidansu, yace wallahi inya tafi bazasu kuma ganinsa ba, ke yaya Jawwad yana cikin damuwa, gashi kusan kullum se Naja tasa anyi masa fada" Mikewa Jalila tayi ta dafe goshinta tace "Nana am coming back this week Insha Allah, Idan har Abba yabari akayi Auren nan an rusa Rayuwar Yaya Jawwad gaba daya, kuma ina tausayin Hanan, zan dawo a satin nan Insha Allah, dole afasa Auren nan" Sukayi sallama da Nana ta mike zata koma cikin gida Ahmad yace "Jalila lafiya kuwa? Naga kin shiga wani yanayi ko akwai damuwa ne?" "A'a bakomai" "Bari in kyaleki, nadawo na karbi lambarki zamuyi waya" gyada masa kai tayi ta fice da sauri. Jalila na zuwa Hanan tafara yimata tambayoyi "Jalila wai waye Yaya Yusuf yace kinyi bako?" "ke kyaleni dan Allah wani ne nina manta sunansa ma, Hanan satin nan, maybe nan da kwana uku zankoma Kano" "Jalila meyasa? Saboda Yaya Yusuf?" "A'a Hanan Akwai matsala ne, dole inkoma" "Matsalar mene haka? Jalila kar mutan gidan nan su zargi ko wani lefi sukayi miki" "bahaka baneba Hanan, Ankoma makaranta sannan ina bukatar zuwa gida" Hanan tace "hmm ko dai saboda Jalal ne? Gayamin wani abune yafaru dashi ne?" Cikin damuwa Jalila tace "Hanan dagaske Jalal yake in yabar kasar nan baze dawo ba, wai anyi masa wani abu a gidansu, fitarsa kasar waje hatsari ne" Jalila ta boyewa Hanan batun kai kudin Auren Jawwad kar Hanan ta damu. Hanan taso ta tsokani Jalila amma ganin ta in serious mood yasa ta fasa tace "gaskiya yakamata kikoma bari daddy ya dawo se muyi masa magana" Yusuf ne yayi knocking kofar dakin nasu sannan ya shigo da sallama ya kalli Jalila yace "Jalila yaya kun gaisa da Captain Ahmad?" "Eh yaya Mungaisa" "to bazamuyi miki dole ba, kigaya masa abunda ke ranki, inkinada wanda kikeso kigaya masa tun wuri" "tana da wanda takeso fa, tana jin nauyin kane bata fada ba" Yusuf yace "inkika kuma magana sekinyi tsallen kwado sau sittin a gurin nan, dake nake magana?" Shiru Hanan tayi yacigaba da cewa "Jalila banason mu cutar dake gidan nan ba'ayi wa kowa dole, nayiwa daddy maganar, in ba kyasonsa ki gaya masa kinji" Jalila ta gyada kai, yace to seda safenku. Yusuf na fita Hanan tace "ke Jalila captain Ahmad ne dama, to tun wuri kice masa bakya sansa, har sunkai magana gurin daddy Yaya Yusuf baya wasa, wallahi dagaske suke, in Baba ya tambayeki kice be mikiba ba kya sonsa, kinada wanda kike so" "Haka nace miki bana sonsa? Wanake dashi a yanzu danake so? To ni yayi min" "karya kikeyi wallahi, Jalal shine kike so, ba wani aranki seshi" Ina yinku ABDUL JALAL group irin sosai din nan fa 😍😍😍 inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing duk bayan kwana biyu, kuna bari ina lalaci posting duk sati 😜😜😜 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  3️⃣4️⃣87 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Tsaki Jalila tayi, taje ta dakko trolley tafara zuba kayanta, A daren Jalila taje tasamu dadyn Hanan tace masa zata koma gida jibi saboda sunkoma makaranta, daddy beji dadi ba yacewa Jalila da kansa ze maida ita gida. 'yan gidansu Hanan sunji babu dadi batun tafiyar Jalila, sun mata Alheri sosai, Inna ma taji babu dadi, tace itama wataran zatasa akaita kano gurin Jalila, ranar da Jalila zata koma tun safe tagama shirinta tsaf, karfe goma na safe daddyn Hanan da kansa yasa Jalila a mota ya tafi kai Jalila gida, suna tafe suna hira. Jawwad yayi duk yadda zeyi ya hana Jalal tafiya amma wannan karon Jalal ya dage, yayi rantsuwa yace seya tafi sannan yaki gayawa Jawwad hakikanin abunda akayi masa a gida, Jawwad ya tafi gidansu Jalal yasamu daddy bayan sun gaisa yace "daddy me akayiwa Jalal ne yace in yatafi baze sake dawowa ba, bansan me akayi masa ba" Nan daddy yagayawa Jawwad abunda yafaru. Jawwad yace "Amma daddy meyasa kake zargin Jalal akan wannan, daddy zan iya rantsuwa da Alqur'ani Jalal baya neman mata, koma wacece sharri take masa daddy" "Jawwad se daga baya naga  nima ban kyauta masa ba, ka bashi hakuri, yadena fushi da daddyn sa, amma kokana da masaniyar dalilin dayasa Jalal ya tsani Ilham, ko tayi masa wani abun ne?" Jawwad yayi Jim sannan yace "A'a daddy nima bansaniba, ban san metayi masa ba" "Anya kuwa Jawwad zan yadda bakasan komai ba?" "daddy dagaske nake bansan komai ba" "to shikenan, amma Jawwad dan Allah kahana Jalal tafiyar nan, nasan yana fushi dani, amma karya tafi ya bar daddyn sa" "Insha Allah daddy zanyi kokarin yin hakan" Jawwad ya tashi ya fita, tun lokacin da Abba yayiwa Jawwad zancen kai kudin Auren Naja yake rashin lafiya amma be gayawa kowa ba, ga kuma tension din Jalal, yakoma daki ya tarar Jalal yanata hada kaya, ya zura masa ido, yarasa mema zece masa, kansa ne yake sarawa sosai ya kwanta akan doguwar kujera ya lumshe ido, yanata sakawa yana kwancewa. Nana tasan da dawowar Jalila dan haka tanata murna, tana shirye2 itakuma Naja so take Jalila ta dawo ta kuntata mata rai. Karfe biyu na rana Su Jalila suka iso kano, Nana ta fito ta taresu ta rungume Jalila suka dinga murna, Abba baya gari, ya tafi da Maama lagos, kwanansu uku da tafiya, dan haka Jalila ta budewa daddy sitting room ya zauna. Nana ta dauki kayan Jalila ta shiga dasu cikin gida, ta kawowa daddy ruwa da lemo da Abinci. Duk abun nan, Jawwad besan su Jalila sun dawo ba, Jalila da kanta ta tafi part din Jawwad tana shiga palourn sa ta tarar da Jawwad a kwance akan kujera ya lumshe ido Jalal kuma yasa TV a gaba amma sam ba tv yake kallo ba tunani yakeyi. Sallama Jalila tayi, sallamar tata ce ta dawo dashi daga dogon tunanin da yakeyi, be taba zaton kafin ya tafi zega Jalila ba, seda suka danyi seconds suna kallon kallo, dauke kanta tayi ta nufi gurin da  Jawwad yake kwance, "Yaya Jawwad" ta kira sunansa amma be amsaba, hannu takai ta dafa goshinsa yayi zafi sosai da sauri tace "Subhanallah" dan girgiza shi tayi, A hankali ya bude ido yana kallonta murmushi yayi mata yace "Baby saukar yaushe haka ba Labari?" Cikin kulawa tace "Yaya Jawwad baka da lafiya ne haka"? Mikewa yayi zaune yace "kai amma nayi murna da dawowarki, munyi missing girkinki da kiriniyarki" "Yaya Jawwad keep jokes aside ka rame sosai baka da lafiya, nakira layinka baka dagawa, Hanan ma ta kiraka amma bata shiga, yanzu daddyn Hanan ne ya kawoni, yana son ganinka" Jawwad yace "Shikenan bari inje" Jalal ya kalli Jawwad yace "dagaske baka da lafiya? Meyasa baka gayamin ba?" Jawwad yace "meye Amfanin gaya maka banida lafiya? Kaika gayamin dalilin dayasa zaka bar kasar nan? se dazu daddy ya gayamin abunda yafaru, kuma matakin da kake shirin dauka shine ya dace? Gaba daya hankalina a tashe yake Jalal, ni bakasan a matsalar danake ba, gashi kaikuma da maganar dakazomin, gaba daya hope din iyayenka akaina yake, bakaga magiyar da daddy yakemin akan kar inbari ka tafi ba narasa yadda zanyi ba dole rashin lafiya ta kamani ba, gaba daya narasa meyake min dadi" gaba daya tausayin Jawwad yakama Jalila Jawwad Ya mike ya fice a dakin ba tareda Jalal yace masa uffan ba, Jalila ma bayan Jawwad tabi. Ba karamin tausayi Jawwad yabashi ba, shikansa yana tunanin yin rayuwa ba tareda Jawwad ba, amma yana daga cikin dalilansa na son barin kasar nan yanaso Jawwad yasamu kwanciyar hankali, ya karbi Aiki ya hutawa ransa dawainiyar daya dingayi masa tsawon shekaru a ganinsa wannan ce kawai hanyar dazewa Jawwad halaccin abunda yayi masa. Jawwad yaje gurin daddy, sun dan dade suna magana da Jawwad sannan yayi musu sallama yatafi. Tunda Jalila ta koma gidan Naja take habaici tana yada magana "ko anki ko anso, koda dariya koda kuka seta Auri Jawwad, Jawwad ba mijin kafura bane" Jalila tabawa banza ajiyarta, duk yadda Naja taso ta tsokani Jalila, Jalila taki kulata. Bayan daddy ya tafi, bayan la'asar Jalila ta tafi dakin Jawwad domin tana son yin magana dashi matuka, dakin ta shiga da sallama amma bakowa a palourn, bedroom dinsa taje tana knocking sannan ta bude dakin, ta hango Jawwad yayi rigingine ya lumshe ido kaman me bacci, sallamar Jalila ce tasashi ya bude ido, mikewa yayi zaune a hankali tareda kakalo murmushi yace "Babyn Ummi, ya gajiyar hanya? Na zata by now kina can kina hutawa" "ina batun hutawa Yayana ba lafiya, ya jikin naka?" "lafiyata fa kalau" "A'a ni ban yadda ba ina zuwa" Jalila takoma cikin gida ta hadawa Jawwad tea ta kawo masa, ya karba ya shanye yace "Nagode Jalila" "meye kuma na godiya? Yaya Jawwad magana nakeso muyi da kai" Gyara zama yayi yabata dukkan Attention dinsa Jalila tace "Yaya Jawwad meyasa ka amince da Auren Naja?" Ajiyar zuciya yayi ya danyi shiru sannan yace "Jalila Maama ta takura na rasa yadda zanyi ne" "Yaya Jawwad, tun tasowarmu bantaba son wani sama da kai ba, amma ganin Hanan tana sonka, kuma Maama bata son Alkarmu tare, banason tayi fushi da kai, bana son ta fadi wani mummunar kalma akanka dazeyi tasiri a rayuwarka, Yaya Jawwad ba dan nadena sonka nakoma gefe na zuba maka ido na barwa Hanan kai ba, ina ganin kona barka Hanan zata maye maka gurbina, Amma meyasa zaka yadda da Auren Naja, Na tabattar Abba besan komai game da Wacece Naja ba, ita kanta Maama akwai abubuwan da bata saniba game dasu Naja" Jalila takarasa maganar idonta taf Hawaye, "Yaya Jawwad, Hanan zata shiga damuwa sosai, tana maka so bana wasaba shiyasa na yadda da soyayyar da Hanan take maka ne dan samun nutsuwa da daidaituwa tsakaninka da mahaifiyarka, amma meyasa zaka Amince da Auren Naja?" "Jalila bijirewa Auren Naja ze kuma jawomin wata damuwar ne, Har Yanzu Maama takasa gane Yaya mairo ba kaunarta take ba, ta riga ta zigata idan nace banason Auren nan komai ze iya faruwa, Amma ni kaina bana son Auren nan Jalila, Jalila na hakura da kene kawai saboda nasan idan har na Aureki bazaki samu kwanciyar hankali da nutsuwa ta fannin dangin mahaifiyata ba, Jalila bayan tafiyarki Maama ta kirani akan maganar Auren tace Abba zemun zancen Auren muddin na bijire nace ke nakeso" sekuma yayi shiru yakasa cigaba "Ina jinka bakomai karasa" "Jalila Maama cewa tayi muddin na bijirewa maganar Auren Naja nannunawa Abba ke nakeso bata yafemin ba" Zare ido sosai Jalila tayi, ta danyi shiru sannan ta girgiza kai "Yaya Jawwad ka kwantar da hankalinka kayita Addu'a komai zezo da sauki Insha Allah, Allah ya ganar da Maama, Amma zaka iya Auren sister na ko Yaya?" Shiru yayi bece komai ba "Yaya Jawwad nida Hanan duk dayane, tana sonka sosai Zata kulamin da kai yadda yakamata, Insha Allah zanyi duk kokarin da zanyi amma bana son kacigaba da damuwa" "To Babyn Abba na dena Insha Allah" "Yawwa Yaya Jawwad dina, kamanta da wannan batun gaba daya, Mutum managarci kamarka be dace da mace irin Naja ba, kadena damuwa kar ciwo yakama ka" Gyada mata kai yayi yana murmushi. Jalila ta mike ta fito daga dakin tanajin wasu Hawaye, harga Allah tana kaunar Yayan ta a zuciyarta babu macen dazata so tarasa managarcin mutum kamar Jawwad, harzata fita ta hango abu akan center table, dan haka ta dawo da baya ta tsya tana dubawa. Jalal yana dakinsa yakuma tattar dukkan wani abu dayake bukata, ya hadesu guri daya sannan ya fito ya tafi cikin gidansu, dakin daddy ya tafi ya tarar dashi yana Aiki akan system dinsa. Daddy na ganin Jalal ya ture system din yana murmushi "Welcome my son" "Thank you dad" Jalal yasamu guri ya zauna sannan yace "Daddy naga bazan iya tafiya ba tareda nayi maka sallama ba, ina kaunarka fiye da tunani dukda kamin abunda bazan manta ba, amma bazan iya rabuwa da kai ta har Abada ba, daddy duk inda zan kasance a fadin duniya muna tare, Dubai zan tafi zamu dinga haduwa in kaje can, zan dinga zuwa Nigeria saboda wasu mutane, Amma Mummy taje ta riki Ilham a matsayin yar data haifa " "My son nibana farinciki da wannan tafiyar taka, nafison ka kusada mahaifiyarka, Jalal idan katafi ba idon kowa akanka babu mece maka bari, bam san wace irin Rayuwar zakayi a can ba, Dan Allah Jalal " Ya isa haka daddy karka rokeni dan Allah 🙏, Mummy bata sona bata kaunata, bata son farinciki na kanta kawai tasani, damuwarta ce kawai damuwa damuwar wani bata ta bace, daddy kasan yadda zuciyata takemin idan nasan cewa uwata na raye amma bana tareda soyayyar ta saboda wani dalili nata, kalli Rayuwar danakeyi saboda son zuciyarta, daddy Jawwad yayi yayi yaga nakoma mutumin kirki amma abu ya gagara, Amma wani dalili da ban taba tunani ba yana kokarin sani in rabu da shaye2, daddy idan har na cigaba da zama a kasar nan Mummy tanamin abunda takemin to bana tunanin bakin ciki ze bari in rabu da shaye2" Hawaye sosai Jalal yake kaman mace Jalal yakamo hannun daddy ya rike a cikin nasa, Sannan yadanyi murmushi yace "Daddy na kasan wani abu? Inada Ajiya a Nigeria bazan iya barinta gaba daya ba, in kaga nabar Nigeria gaba daya to Ajiyata na dauka, kamin fatan Alkhairi daddy na" Yana gama maganar ya sumbaci hannun daddy ya sakeshi ya juya ya fice, daddy yarasa abunda yake masa dadi, idan Jalal bayaji ta wani fannin baya ganin laifinsa saboda tabbas rayuwarsa cike take da kalubale daban2. Jalila takoma daki sukayi waya da Hanan amma batace mata komai akan Batun Auren da za'ayiwa Jawwad ba, sannan tacigaba da kokarinki kwantarwa da Jawwad Hankali tareda bashi karfin gwiwa, Jalila sam taki kula Naja, ta maida ita kamar wata mahaukaciya, tayi zage zagenta da habaici amma Daga Nana har Jalila sukaki kulata. Ilham ta shirya takuma zuwa gidansu gurin ummanta, domin din yadda sukayi da malaminsu, "Ilham malam ya tabattar min Jalal baya neman mata, Sannan aikin da'akayi masa har yanzu yana nan ajikinsa, amma akwai matsala" Da sauri Ilham tace "matsalar menene kuma?" "Malam yace aikin da'akayi masa ya rage tasiri akansa, saboda akwai wanda yake ta kokarin rusa komai" Girgiza kai Ilham tayi tace "Umma wallahi wannan yarinyar ce da na nunamiki a Asibiti, hatsabibiya ce ta gaske ni Jalal yaciwa mutunci agaban iyayensa yace ya tsaneni ya tsani me sona" Zare ido Umman tayi "Yatsaneki ya tsani me sonki dan Iskanci, kan bala'i ai wallahi daga shi har khadija basu isaba senaga abunda ya turewa buzu nadi" "to ai Umma ba wannan bama, akan case din nan na zargin yana neman mata, yace kasar nan ze bari wai inyaso Mummy ta rikeni ni ta haifa bashi ba" "Yabar kasar nan saboda me? Ke Ilham akwai aikifa baki kirin agabanmu, idan yaron nan ya tafi be Aureki bafa? Ita khadija me tace?" "me kuwa zata ce ranar kaman ze rufeta da duka" "tsinanniya ni dama ya daketa ta mutu in yaso yakare rayuwarsa a prison" "Ahha umma akan me? Ta mutu akaishi prison bamu mallaki dukiyar damuke Hari ba?" "to ai Ilham tsawon zamanki a gidan nan ba wani kokari da kikeyi, ace duk wannan shekarun ko kallon kirki baya miki sema tsana" "to Umma yazanyi? Ni tun farko sonayi inyi me gaba daya kowa ya huta, kuma kiris ya rage amma ina shegen taurin kaine da shi kamar dutse ne a kirjinsa ba zuciya ba" Umma ta numfasa tace "Munyi maganar da maman Yaseera, tacemin akwai wani malaminta a can Nijar, munyi da ita zanje ta rakani shima mu jarraba irin nasa Aikin mugani" "to Amma Umma tayaya? Kasar fa ze bari" "Dan ubanki kije kiyi duk yadda zakiyi, ki lallabashi in ta kama hada kuka akan bakya so ya tafi, ni nama rasa dalilin dayasa ya tsaneki haka wallahi, keba muniba to kodai yasan abunda mukeyine?" "Haba dai yaza'ayi yasani? Ni dai Umma dan Allah ki kai Sunan yarinyar nan kawai intakama a kasheta, dan wallahi yanzu ba zargi nake ba, na tabattar ita yakeso" "tayaya kika sani?" "Umma ninake ganin abunda nake gani, wallahi Umma idan kinga Jalal ya tabani to bisa kuskure ne, koda wasa baya bari ya tabani, bama ni kadaiba kinsan halinsa bayason mata su rabe shi, amma ganin idona naga ya rungumeta, itakuma makirar tsinanniya tayi luf a kirjinsa, Allah ka dai yasan abunda sukeyi wallahi na tsaneta kamar mutuwata, kuma bakiga yadda baban Jalal din yake mutunta ba, keba shi kadai ba har Mummy bakiga yadda take mata ba" Jinjina kai Umma ta shiga yi sannan tace "kyaleni da ita, zata gane kuskurenta, nasan yadda zan bullowa lamarin zata gane bata da wayo, kafin inje gurin malamin, zan gayamiki yadda zakiyi kowa se ya tsaneta" Haka sukayi ta hirarsu su saka wannan su kwance wancan. Jalila kullum dare setayi salla takaiwa Allah kukanta haka take raba dare, gata gwana gurin yawan tilawar Alqur'ani, shiyasa Jalila ta yadda da duk wani abu da take aikatawa a rayuwarta take Nasara tasan dogaro ga Allah, riko da ibada  da nacewa Alqur'ani shine matakin dukkan wata Nasara a rayuwarta, duk abunda ta tinkara setaga bayansa, ta taba duk wanda takeso komai matsayinsa amma babu abunda ze faru da ita, ta yadda da dukkan abunda ta roki Allah intaga bata samu ba to lokaci ne beyiba, ta yadda wannan shine matakin Nasararta a rayuwa wadda Umminta da akewa kallon tubabbiyace ta dorata a wannan tafarkin. Tunda Jalal yace zeyi tafiyar Nan Mummy hankalinta yakasa kwanciya, gashi tasan yadda Jalal yakejin haushin nan nata baze saurareta ba, Amma yazama dole Jalal ya Auri Ilham dan cikawa Saudat Alkawarin ta wannan ne kawai abunda zatayi ta wanke laifin ta a gurin Saudat. Mummy tayiwa daddyn Jalal magana akan yayi wani abu ya hana Tilon danta tafiya ya yabarta amma amsar daya bata ta mata ciwo "da lokacin danake miki maganar ki hakura da tafiya karatu kikula da tilon danki da kinji magana ta da koba duka ba ko yaya da Jalal yaji maganarki, ko kin manta watansa bakwai kika dena bashi Nono, a wata bakwanma se lokacin da kika gadama, niba abunda zan iya ki kyaleni" Ba karamin ciwo maganar daddy tayi mata ba amma ba yadda ta iya. Ilham ta shirya taje dakin Jalal don jarraba ganin ko ze saurareta amma kusan ya kwashe komai nasa dake dakin nan se abunda ba'a rasa ba, tasan yana gidansu Jawwad dan tunda abun nan ya faru yakoma can dan haka ta bishi can gidan. Jalila ta kaiwa Jawwad Abinci amma baya nan, se Jalal a palour, bata kulashi ba ta shiga tana gyrawa Jawwad bedroom. Tagama ta fito palour yana zaune inda Tabarshi yana daddana waya, ta fito tazo ta zauna a teburin dake gabansa, tana fuskantar sa, dagowa yayi ya kalleta, kallon dayake mata dukta tsargu, basarwa tayi tace "Abokin Yaya wai dagaske tafiya zakayi?" A ranshi yace lallai yarinyar nan sekace bata san sunansa ba, nikam nace ai kaima haka kake cemata kanwar Jawwad 🙄, Sauke idonsa yayi sannan yace "Kafin kiyi tafiya ai nagaya miki ko?" "Aini ban zaci dagaske kake ba" dagowa yayi yana kallon ta karo na biyu yace "na taba yimiki karyane? Ko Ba kya son in tafine?" "to inma ka zauna mekake karamin inka tafi hutunane ai, dan ba karamin wahala nake sha saboda kai ba, da inka tafi na huta banga abunda kayiba balle inji haushin ka, amma ni Su Mummy nake dubawa da Yaya Jawwad" Ilham ce ta shigo dakin da Sallama Amma abunda ta gani zata iya kiranshi da mummunan gani, Amma ta dake tunda sulhu take nema, gaba daya suka daga kai suna kallon Ilham, tattara nutsuwarta ta boye damuwar ta ta tako a hankali tazo gaban Jalal ta tsuguna tace "Yaya gurinka nazo" Bece mata uffan ba itama Jalila bata tashi daga gabansa ba, Ilham tace "Yaya Jalal san girman Allah dukda kace baka sona, dan Allah karkayi tafiyar nan, bana son ka tafi, Mummy ta shiga damuwa sosai bata iya cin Abinci se kuka takeyi dan Allah kayi hakuri nikaina zan shiga damuwa sosai, Jalal so fa ba karyane ba ni ganin gilmawarka a cikin gidanma ya isheni farinciki amma bansan dalilin dayasa kake kina hakaba " Wani kululun bakinciki ya tokarewa Jalal rai a fusace yace " dalla malama ki tashi kibani guri, ai bakinku daya Mummy karkinemi ki rainawa kanki hankali, bana sonki bana kaunarki kifita daga rayuwata tun kafin inyi miki Illa, babu wanda ya isa ya hanani tafiya ba kukan Jini ba ko Hawayen karfe zatayi ba ruwana, ta manta sanda nake mata magiya take tafiya tana barina, lokacin danake matukar bukatar ta, kinga dalla bacemin daga nan ko in ballaki" yakarasa yana zazzare ido gaba daya jikinsa bari yake "wai dan Allah wace irin zuciya ce da kai, baka yafiya baka mantuwa, koma metayi maka ai ita takawowaka duniya, tana sonka shiyasa bata so ka tafi, Yaya Jawwad ya dena zaman gidan nan saboda bayason ya dinga tuna zakayi tafiyarka ka barshi, kalli yadda Ilham take kan gwiwoyinta tana kuka amma kai ko a jikinka meye hakane?" Kafe Jalila yayi da idanuwansa da ita kanta wani lokacin suke bata tsoro, gashi yakara hade rai sosai. Wani bakinciki yakara tokare kirjin Ilham kamar zuciyarta ta fito waje. A hankali yafara motsa baki yace "Wallahi idan har banyi tafiyar nan ba to bana raye, ba ruwana da halin da wani ze shiga saboda babu wanda ya damu da halin da nake ciki" yafada yana kallon kwayar idon Jalila Kawai sukaga Jalila tana dariya, wadda ke matukar kara mata kyau tace "to shikenan Ai seka tafi in gani" ta mike tsaye takuma kallon sa ta kwashe da dariya seka dawo, karka fasa tafiya naga ta inda zaka tafi ai, kekuma Ilham na dawo koki dawo da abunda kika dauka kokuma inzo da kaina" Kawai ta juya ta fice ta barsu a zaune suna mamakin maganar ta. Ina yinku ABDUL JALAL group irin sosai din nan fa 😍😍😍 inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing duk bayan kwana biyu, kuna bari ina lalaci posting duk sati 😜😜😜 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  3️⃣5️⃣88 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Mikewa Jalal yayi ze fice yabar dakin Amma Ilham ta mike ta sha gabansa "Haba Jalal yanzu bazakaji magiyar danake maka ba, dan Allah Jalal kayi hakuri, karkayi tafiyar nan, zan shiga mugun yanayi dan Allah Jalal, wallahi ina sonka, tunda kuruciya ta har kawo I yanzun" "Ke waini sa'an wasankine? Wallahi koki matsa ko in tattaka ki" Ya tureta gefe ya fice Abunsa, Abun duniya duk ya dami Ilham, Jawwad ne kadai ke iya sarrafa zuciyar Jalal wani lokacin, yanada matukar kafiya da taurin kai, gaba daya tunanin ta ya kwace. Jalila takoma cikin gida ta tattara abubuwan dazata bukata dan gobe in Allah ya kaimu zata koma makaranta, Karamar wayartace ta cika dakin da ringing, Jalila taga bakuwar lamba ta share tacigaba da Aikinta, amma still aka cigaba da kira har kusan karo uku, seda ta danyi tsaki sannan taja wayar tasa a kunnenta Ajiyar zuciya akayi sannan akace "Masha Allah, kin karyamin record bana kiran mutum sama da sau biyu, komai tsananin bukata ta kuwa, Amma ta dalilin son danake miki har sau hudu ina kiranki" Sarai ta ganeshi amma ta maze tace "ko zan iya sanin da wa nake magana" "Ohh am sorry dear, bankoyi miki sallama ba, balle mugaisai nafara miki surutu, Ahmad ne" "Ok Allah sarki yakake ya gida ya iyali"? "Alhamdilillah queen, kin tafi bako sallama, ban san zaki koma kano ba ai" "Aikam abune na gaggawa ya tasomin, in ban manta ba ranar agabanka aka kirani" "Hakane fatan kowa da komai lafiya" "lafiya kalau, ya na baroku?" "komai lafiya amma kintafi kin barni da kewarki, duk lokacin danake wani abu kona rufe idona ke nake gani Jalila, kitemaki zuciyar maraya" ya karasa maganar cikin sigar magiya "Kai karka bada maza mana, yanzu idan abokan Aikinka sukaji wannan aise suyi Maka dariya, babban soja kaman kai kana haka akan mace, macenma wata 'yar yarinya" Murmushi yayi yace "Jalila ai babu wani batun namiji ko soja in ana maganar fage irin na soyayya, ba ruwansa da matsayinka, girmanka ko mukaminka, ba ruwansa da na birni kona kauye, dan haka kidena wani batun maza" "hmm Wannan bayani haka yakamata ka bude makaranta ka dinga bada darasi" Murmushi yakumayi yace "Tunda haka kikeso ai se ayi, kece director mukuma dalibanki" "Tab aini bansan komai a wannan harkar ba" "Ahh haba dai?" "dagaske nake fa" "Aikam zan koyardake yadda yakamata" "to shikenan seda safe, gobe in Allah ya kaimu zanje school" "hakane hakan yayi kyau, Allah yabamu alkhairi, zamu hade a dreams zanbiyoki har kano kan shinfidarki" Murmushi Jalila tayi "Allah yabamu Alkhairi" Ta katse wayar ta danyi murmushi, can ta hango Nana ta shige bargo ga uban zafi se wani kashe murya take ba'ajin abunda take cewa, Jalila ta mike ta yaye bargon, Nana ta hada gumi amma ko zafin bataji saboda tana soyewa da Mahmud, Jalila tace "Allah ya shiryaki". Ilham ta dade tana Nazarin me Jalila take nufi da Jalal baze tafi ba, danta fara karaya da lamarin Jalila yarinyar sekace Aljana idan tayi niyyar abu setayi shi. Jawwad sam yaki kula Jalal gashi gobe in Allah ya kaimu karfe biyu na Rana ze tafi, yanzuma da Jawwad yadawo daga sallar isha'i daki yayi tafiyarsa ya kwanta, Jalal yabishi dakin ya zauna kusa dashi yace "Haba nawan yanzu fushi kake dani haka?" Mikewa zaune Jawwad yayi yace "Jalal dan Allah ka kyaleni, kace zaka tafi gaka nan ga hanya seka dawo" "Jawwad nima inajin abunda kakeji a ranka, A tunanin ka rabuwa da kai abune me sauki a gurina, shekaru Ashirin da bakwai muna tare idan ban manta lissafin ba, Jawwad tafiyata shine samun saukinka, kaima ja maida kai karasa gina rayuwarka, bazan iya barin Nigeria gaba dayaba saboda ku biyu daddy zamu dinga haduwa a can dubai dashi" "Jalal wannan ba uzuri bane ba, ni na gaba gayamaka na gaza da kai menakeyimaka na wahala, Allah ne ya hada jinina da kai bani da dan uwa Namiji kaidin nan dai tare muke faduwa mu tashi tsawon wannan lokacin, sannan lokaci daya kace Zaka barni tayaya zanyi farinciki Jalal" "Am sorry Jawwad nasan babu dadi, kuma kana tunanin Wace irin Rayuwar zanyi a inda zanje, Jawwad Ina kokarin dena shaye2, A sanadinka a tsatsonka nasamu me haskamin bakar hanyar danakebi, dama lokaci dayawa kadaici da bacin rai dakuma miyagun abokai kesani kara kaimi gurin shaye2, Amma yanzu an janye miyagun abokai daga jikina, Jawwad idan na tafi inason in koma makaranta " Sa sauri Jawwad ya kalleshi yace" dagaske kake? Da kanka kake fadin zaka koma Makaranta? " " Kwarai kuwa zankoma Insha Allah " Rungumeshi Jawwad yayi yana cewa" naji dadi dan uwana amma naso ace kana nan kusa dani, Amma dukda haka ni zan dinga biyoka Dubai din" Kasan zuciyar Jalal ba wata makaranta kawai dan hankalin Jawwad ya kwanta ne "kobakazo bama nizan dinga zuwa akai2" Haka suka cigaba da hira. Da wuri Yau Jalila ta shirya manu driver ya kaisu makaranta, 'yan ajinsu Jalila sunyi murnar dawowarta nan aka dinga nunawa wanda basu santa bama, hatta malaman dasuke tsangwamarta suke ganin bata iya komai ba tabasu mamaki kwarai dagaske, saboda ba'a mata tambaya ta amsa a Aji, se lokacin data ga dama take zuwa lectures, wataran ma bata Attending, bata handout sedai in malami zeyi lectures ta dakko jotter, idan malami yayi ba dai2 ba bazatayi shiruba setayi magana, wannan bakin nata kesawa a koreta daga Aji, Akwai malamin da har test ya hanata yi, Amma a haka babu wanda yake da points dinta a kaf department din nan, hakika wasu mutanen 'yan baiwa ne, shiyasa har Abada karka wulakanta mutane dan kowa baka san irin baiwar da Allah yayi masa ba. Ba iya dalibai ba hatta malamai sunyu mamakin Jalila ce takeda wannan kwazon. Amma ita Jalila abunda yafi daukar hankalinta be wuce yadda har yanzu ake surutu akan abunda yafaru da Saleema da mahaifinta, Saleema ta warke amma bata iya shiga cikin mutane dan gaba daya ta dena zuwa makarantar, Sameera kam da farko ta tausayawa kawarta abunda yasameta Amma daga baya tunda aka sakesu daga police station tacigaba da abunda takeyi. Jalila a ranta ta dinga jin anya kuwa ta kyauta abunda tayi, yanzu tayiwa Saleema dalilin dena zuwa makaranta, ta kunyata ta a idon duniya itada mahaifinta, Amma data tuna abunda Alhaji Kabir ya aikatawa Jalal, dakuma yadda ya dinga takuramata se yayi lalata da ita, da yadda ita kanta saleema suka addabi makarantar se taji hakan shi ya dace dasu. Tun safe Jawwad ya bar gida sukayi sallama da Jalal yabar gidan. Wajen sha biyu na rana Jalal yagama shirinsa tsaf, ya tsaya ya duba passport dinsa don yasa a karamar Jakarsa, Amma passport yace daukeni inda ka ajiye, ya duba ya duba amma be ganshi ba, hankalin sa ya tashi sosai ya duba kayansa be ganshi ba, gidansu yatafi ya duba dakinsa amma be barshi acan ba, yana kokarin fita daga dakin ne Mummy ta shigo dakin. Ya tsaya yana kallon ta, "Yanzu Jalal tafiya zakayi ka barni, laifina har ya kai ka kauracemin gaba daya, Haba Jalal koba komai nifa mahaifiyarka ce, kai kadai nake da baka tunanin halin dazan shiga inka tafi ka barni?" Maganganun Mummy sam basuyi tasiri a zuciyarsa ba, seda yabari tagama gaba daya, kawai yaraba ta gefenta ya fice, danshi mugun haushin ta yakeji. Mummy tarasa abunda yake mata dadi, ta zauna ta rushe da kuka a gurin, Abunda yakara bawa Jalal haushi be wuce yadda yana fitowa yakuma cin karo da Ilham ba, itama magaiyar take masa amma yai biris yai ficewarsa. Jalal yayi duk tunanin daze yi amma ya rasa inda Passport dinaa yake, wayarsace tayi kara alamar sako ya shigo, Abuda ke cikin sakon ne ya razanashi sosai yasashi mutuwar tsaye wai an soke visa dinsa. "Why!!!? Ya fada da karfi ji yayi yana neman ya fadi jikinsa na rawa, yanemi guri ya zauna ya dafe kai yai shiruu to laifin meyayi aka soke masa visa haka? Shidai yasan a Dubai be taba zuwa yayi laifi ba, Meyasa haka kodai Jawwad ne ya dauke masa passport, kai yasan Jalal beze masa hakaba Anya ba daddy ne yasa aka soke visa ba. "Seka tafi in gani Ai, naga ta inda zaka tafi" Maganar Jalila ya tuna, "to Amma tayaya Jalila zata iya sawa a soke masa visa, wata sani babba haka dazata saka ayi masa haka? Koma ita ta dauki passport dinsa, kai baya tunanin Jalila zatayi haka" Amma dayayi shiru ya tuna irin gwaramar data hadawa Jeje da Alhaji Kabir abun ya zarce hankalin sa. Aikuwa a gigice ya tashi ya fito ya nufi gidansu. Zahra batazo makaranta ba sunyi waya da Jalila tace mata batajin dadi ne shiyasa batazo school ba, bayan sungama lectures din farko Jalila tafita neman abunda zataci, gashi tana son zuwa banki ATM dinta yayi expire, dan haka ta siyi Ruwan jarka da biscuit tasaka a Jakarta ta nufi banki dan taje ta dawo da wuri, wayartace tafara ringing kaman karta daga, ta daga setaji muryar Ahmad, gaisawa sukayi suka shiga hira, Ahmad ya iya hira ga ban dariya shiyasa Jalila take sauraronsa, gashi ya iya soyayya da tattali, tabar department tayi nisa tana tafiya da waya a kunnenta taji Anyi wani jakin parking a bayanta, tsayawa tayi ta waiga a birkice dan ganin wani me kokarin ne haka, Amma wanda taganine yasa gabanta dukan biyar biyar, Jalal ne babu alamun Rahama a fuskar sa, ya tamke fuska sosai kamar be taba dariya ba. Addu'a ta shiga yi a zuciyarta Allah yasa kar yayi mata tijara a bainar nasi. Ahamd yanata magana a waya amma shiru, Takowa yashiga yi yana nufota, yayinda ita kuma tarasa abunyi, ta kame a guri daya tana zare ido, yana zuwa yasa hannu ya janyo ta, ba musu tabishi ya bude gaban motar ya turata ya rufe, ya zagaya ya kunna motar yafizgeta a guje, tunda suka shiga motar bece mata uffan ba itama haka, Sedai tasaka hannunta ta rike kanta ta sunkuyar da kai dan tana matukar tsoron tukin Jalal, tukine na ganganci yakeyi kamar mara hankali. Can Jalila taji yawan karar motoci ya ragu, A hankali ta bude ido taga sun doshi wani katafaren gida, yana zuwa masu gadi suka bude masa gate, ya shiga da motar yayi parking, se daga masa hannu sukeyi amma ko kula su beyiba, bude motar yayi ya fito ya bude mata a tsawace yace mata "fito" ba musu ta fito yakuma fizgarta  zuwa cikin gidan dabata san ko inane ba, A can kasar zuciyarta tana ta Addu'a kuma tanada yakinin Jalal baze cuceta ba. Suna zuwa wani tankasheshen palour, ya saketa ya kalli cikin idonta da yau ya raina fata take tsuma, a tsawace yace mata "Ina passport dina?" "Ni ban dauka ba" "Karya kikeyi" "Niba karya nakeyi ba, ban dauka ba" "Jaleela you are lying" jin yadda ya fadi sunan tayi ya tsarga tundaga kanta har kafarta. "Nifa ba karya nakeba, dan Allah ka maidani, inada lectures fa" "Ba abunda ya dameni bane, ni kika hana nawa uzurin kike gayamin kinada lectures, kibani passport dina" "wai waya cemaka nina dauka? A ina zan ganshi?" "keki gayamin jiya, kuma kika cigaba da rainamin hankali sena kakkaryaki, kibani passport dina ko in babbalaki" "to Amfanin me zemaka bayan an soke visa?" "Kekika dauka kenan? Ban abina tunda banaki  bane, meyasa kikayimin haka? Akan me? Me nake tsinta a kasar nan banda bakinciki, Wace Rayuwa ce me Amfani nakeyi anan din, kowa yana kyamata da halayena babu soyayyar uwa a taredani ta fifita bukatarta akan farinciki na, se kokarin cusamin yarinyar dake neman halakani take, mahaifina danake da kwarin gwiwa akansa amma shike zargin ina neman mata, zaman menake a Nigeria banda takura da bakin ciki? Kowa kyamata yake akanme? Ba gara inje inda ba'asanniba inyi Rayuwata ba wanda yasanni ba, kibani passport dina" idonsa gaba daya ya koma Ja, jikinsa tsuma yakeyi. Jalila ta fuskanci idan tayiwa Jalal rashin kunya yadda yake a fusacen nan ze iyayi mata ba dadi, dan haka ta kwantar da murya tace "Shikenan is Ok, samu guri ka zauna zamuyi magana" Cikin tsawa yace "bazan zaunaba, kibani passport dina" "Idan baka zauna ba bazan gayamaka inda yake ba, Zauna tukuna" Seda ya danyi jimm sannan ya zauna, ta zuge jakarta ta dakko ruwan da ta siya zata sha, ta bude ta mika masa, ba musu ya karba ze fara sha tace "Kayi Bismillah" seda ya dan harareta sannan yayi ya shanye ruwan se sauke numfashi yakeyi saboda bacin rai "Kasan wani abu? Nina ga passport dinka akan center table na dauka, sannan nina saka aka soke maka visa" Tsareta yayi da ido amma bece komai ba "banyi haka dan inbata maka ba, nayi hakane dan sama maka mafita, kasan hukuncin me sabawa iyaye, muddin kayi tafiyar nan bada san ransu ba zaka iya samun matsala, Abokin Yaya laifin da mahaifiyar ka tayi maka wannan tsakanin tane da mahaliccinta, Amma abunda kake mata ba dai dai bane ba, kamata yayi ku zauna lafiya cikin hikima ka nunamata kuskuren da take aikawa, na baka misalai wancan karon daka kusa karyamin hannu, inkaji kaddarar wani zakaga taka ba komai bace ba, nima misali ce a gareka, na tashi ba mahaifi Allah ya karbi abunsa inada karancin shekaru, ga tsangwama saboda mahaifiyata daga baya ta musulunta, yanzu itama babu ita bansan a ina take ba, Natashi da kaunar Yayana, amma mahaifiyarsa batasona inaji inagani saboda kar mahaifiyarsa tayi masa baki na sadaukar da soyayyata na hakura " Ta danyi shiru hawaye nabin fuskarta "ABDUL nasan dacin a tsangwami mutum amma kai da gatanka kana tareda iyayenka, kana da gata, suna kaunar ka wata kaddarace ta gifta dazaka iya gyarata, yau inka dena shaye2 ka gyara tsakaninka da Allah da iyayenka ze wuce kamar bakayi ba, nikuwa fa? Nasani ko Aure nayi se an gorantamin rashin dangin uwa, na ubanma waye Abba ne kawai, tare kuke da Yaya Jawwad kasan komai wani abunma ni bansaniba, Why Jalal, wanda yarasa iyaye yayi kuka, kai kana taredasu amma idonka ya rufe" Sosai Jalila take kuka, yayinda jikin gogan yayi sanyi gaba saya, Jikin Jalal yayi sanyi matuka, kura mata ido yayi, yana tuno lokacin dasuke mata wasa shida Jawwad yana tuno abubuwa dasuka shude gaba daya tausayinta ya kamashi, handkerchief ya dakko a Aljihunsa, yana goge mata Hawayane yayinda taketa sheshaekar kuka kaman wanda akayiwa dole yace "kidena kuka please" "Ni kylaeni bazan dena ba din" tasa hannu a jakarta ta dakko passport din ta aje masa "ga passport dinka nan, seka dawo" tana kokarin tashi seji tayi yace "Aina fasa" tsayawa tayi tana kallonsa "Eh dagaske nafasa" "Meyasa kafasa?" "da farko kin dakukemin passport, kuma kin lallaba kinsa an sokemin visa daya zan tafi?" "Kayi hakuri nasan kaji ba dadi abunda nayi, amma zaka iya nema na wani kasar katafi" "Nafasa amma ya akayi kikasa aka soke visa na" Ta goge hawayenta sannnan tace "daddy Hanan nagayawa ranar dazamu dawo, shine yace kar indamu zssa a soke" Jinjina kai yayi ya danyi shiru tace "nika tashi ka maidani" "Saboda me?" "Saboda haka nace, meyasa zaka kawoni inda ban saniba, ga gidan bakowa ni gaskiya ka maidani" "hmm hakane nan inda baki sani bane, zan maida ke amma sekin gama kukan, nan gidanmu ne na gadon kaya inda aka haifeni, inda nayi rayuwa me dadi, dukda ba me dadi ce yadda nakeso ba, amma nayi Rayuwa dani da Jawwad daddy Rayuwa me cike da jin dadi" ya mike tsaye yace 'ina zuwa" Ya hau kan benen ya dan jima sannan yafito da wata Jaka a hannunsa duk ta danyi kura, yadawo yasamu guri ya zauna, har yaje ya dawo Jalila bata dena kukan datake ba, yasa hannu ya dan karkade Jakar sannan ya bude zip din, wasu uban hotuna ne aciki masu tarin yawa, yasa hannu ya debo wasu, ya mikawa Jalila, tasa Hannu ta karba tafara dubawa a tsanake, fuskarta sharkaf da hawaye amma hoton farko data gani yasata yin murmushi, Jalal ne da Jawwad suna kanan basufi shekaru biyar ba sun zazzaro ido suna sanye da kaya iri daya, haka ta dinga kallon hotunan tana dariya, galibin hotunan hada Umminta a ciki kan wani hoto taje, Jalal ya nutsu ya dauki wata Jaririya yana kallon ta, Tace "Wannan wacece? Kanwarka ce" "gata nan dai kalleta baki gane wace ba?" Jinjina kai tayi alamar Eh, karba yayi yakuma duba wani yabata yace "wannan fa" itace batafi shekara biyu ba Idonta duk hawaye Sunsata a tsakiya Ba karamin dariya hoton yabata ba "Wannan ai nice" "wancan ma kece ai" "to a ina kasamu wannan hotunan haka" "Abee yanada camera da, shiyake mana hotuna in aka wanko daya abawa Ummi daya abani nake tara nawa, wasu kuma a gurin ummi na karbesu, wasu hotunan bani dasu suna gurin Ummi" "lallai ka iya Ajiya" Nan tadinga kallon hotunan, har hoton Iyayen Ummi akwai seda ya nuna mata, gaba daya ya manta da fushin dayakeyi, ita kuma ta manta tanada lectures kan wani hoto ta kai, Ummice a jiki da Abeenta, sunsakata a tsakiya duk sun kalleta suna murmushi, ta tsaya ta zubawa hoton ido, sekuma Hawaye ya shiga zubowa daga idonta kuka sosai Jalal yai kuri da ido yana kallon ta, hannu yasa ya zare hoton "Bani tunda kuka zakiyi, ban hotuna na" Cikin kukan tace "yi hakuri na dena" "baza'a hakuran ba, bani nan" Yasa hannu ya tattare su, rikewa tayi "dan Allah kabari in karasa" Yana kokarin fizgewa ne hotunan suka zube a gurin, idonta ne yakai kan wani hoto dayasa taji hantar cikinta ta kada. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹               _ABDUL JALAL (2020)_        _Story and written by_       AISHA HUMAIRA (daddy's girl)             PART 2                                   _PAGE  3️⃣6️⃣89 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com                                          _MY FIRST NOVEL _ Da sauri ta dauki hoton tace "Wannan wacece?" Karba yayi ya duba sannan yace "bakisan wannan ba? Kakarkuce wadda ta haifi su Abba" "Wannan ai kakar su Hanan ce" "kamar yaya?" ya tambayeta cikin rashin fahimta, nan ta kwashe komai tagaya masa na zuwanta bauchi jinjina kai yayi yace "masha Allah, nina san wannan kamar da kuke ba'a banza ba, tabbas abunda kakar Hanan tagaya miki haka yake, Sun baro garinsune saboda hari da ake kaimusu, amma yanzu karkiyi saurin fada, Abba yakamata kifara samu da wannan maganar, ya dade yana bincike ko Allah zesa yasamu wani daga dangin iyayensa, tunda basu san kowa ba daga family dinsu, Inna kawai suka sani da baba" "Allah yasa gaskene Su Hanan 'yan uwan su Abba ne, inda suke sunada yawa sosai estate ne guda gaba daya family dayane" "' yan uwankune Insha Allah, bari in mayarda hotunan nan se in maida ke" Ta gyada masa kai ta jirashi ya mayar ya dawo, ya kalleta yace "muje ko" Ta wuce gaba ya biyo ta abaya ta tsaya ta wigo ta kalleshi "dan Allah karkayi wannan tukin, dan Allah" bece komai ba ya bude motar ya shiga, itama budewa tayi ta shiga ya kunna motar, aka bude masa gate ya fita, masu gadi nata daga masa hannu amma yayi musu banza, "Suna maka magana amma kayi musu banza ba dadi fa" "to mezan musu? Ko sokike in sauka in tsaya ina surutu?" "A'a bahakaba at least ko daga musu hannu kayi" Be kuma kulataba ya cigaba da tukinsa, Sarkar wuyansa ta kalla, sekace ba ďan musulmi ba, "Kafasa tafiyar dai ko?" "baki yadda dame na fada bane?" "A'a ni banceba, Amma dan Allah kadena yi wa Mummy abunda kake mata, dan Allah" "Waike ba Adda tagaya miki komai game da rayuwata ba mekikeso inyiwa Mummy?" "Bahaka bane ba, inka mutu tana fushi da kai Allah ma zeyi fushi da kai, kila sanadiyar yafemata kaga Allah ya daidaita maka Al'amuranka, mutane zasu dena kyamarka" "Anya Al'amurana zasu gyaru? Mutane bazasu taba sakin jiki daniba kowa ya riga ya gujeni se kalilan din mutane" "Al'amuranka zasu gyaru inkaso mana" "Ta yaya?" "I will help you do that, sekowa ya dawo yana sonka" "how?" ya tamabayeta a takaice "Just believe me, you Can change, I will help you change your life, trust me" Kallonta yayi sannan yai murmushi "I have trust you already, ko iya haka you bring a lot of changes in my world, Thank you" "kasan wani abu daga lokacin da ka kasance tareda abunda kakeso lokacin kake kara samun nutsuwa da kusanci zuwa gareshi, Iyaye abun sone, dakana kokarin ka manta abunda Mummy tayi maka ka kyautata mata wataran zaka manta da komai" "bazan manta ba kuma ni yadda take kara cusamin Ilham ke batamin rai" "wai me Ilham tayi maka haka?" Kallon Jalila yayi irin kin rainamin hankali "kinsan komai amma kina rainamin hankali, lokacin dana kwanta a Asibiti kikace musu ina bacci, sunsaki baki itada mahaifiyarta naji duk abunda suke cewa kuma kina tambayta me tayimin bansaniba" Dauke kai tayi ta danyi murmushi. Suna shigowa bakin layin suka ga wani dattijo yanata tattare ledojin da suka dan bata layin, da Sauri tacewa Jalal ya tsaya "me zakiyi?" "Kaga dattijon can zamu tsaya mu gaisar kaimasa Alheri" "saboda me?" "Maganar me mukayi dazu, you want change" Hade rai Jalal yayi "Wannan mutumin ba irin zagin dabemun ba farkon fara shaye2 na" "kayi hakuri ka nuna masa ka manta please" Jalal yaja motar suka karasa inda dattijon yake suka gaisa sukayi masa sannu da aiki, sannan Jalal ya dakko dubu daya ya bashi yasa hannu ya karba ya dinga godiya sannan suka wuce, "Kiduba Ajiyata dana gaya miki"? Ya jefo mata tambayar, Jalila bata son rigimadsa tasan intace Ilham ta dauka fada zasuyi dan haka tace "Wace Ajiyar fa?" ta tambayeshi irin ta manta din nan Ya gano so take ta raina msa hankali dan haka ya kyaleta yayi parking Akan idon Ilham Jalila ta fito daga motar Jalal. Ilham aranta tace "dama tazo dazan bakantawa Jalila insa a tsanate" dan haka Ilham da gudu ta shiga cikin gida tana kwalawa Mummy kira ta samu Mummy a daki idonta yayi Ja saboda kuka tana lazimi "Mummy wallahi Jalal bashida mutunci bashida Imani, duk yadda kikayi kina kuka bakyason ya tafi seda ya tafi, gashinan a banza mace tasashi ya dawo yafasa tafiyar, wallahi gaskiyar daddy Jalal neman mata yakeyi" Cikin rashin fahimta Mummy tace "Ke bangane me kike nufi ba" "Mummy Jalal yadawo be tafi ba saboda Jalila" "Kamarya saboda Jalila?" "Oho musu dai, wallahi gashi can shida Jalila sun dawo, saboda ita yafasa tafiyar" "ke ya akayi kikasan saboda ita yaki tafiya?" Ilham ta gyara zama tace "Mummy nifa shiru kawai nakeyi, Allah kadai yasan abunda nake gani a tsakaninsu, bana son yawan bata miki raine" A fusace Mummy tace "Ilham bana son shirme da shashashanci, kimin bayani yadda zan gane, ban fahimci ke kadai kika san abunda kike ganiba kimin bayani" "Wallahi Mummy ba tun yauba akan yarinyar nan bakiga rashin mutuncin da takemin ba, kuma wallahi ita take ziga shi yakemiki wani rashin mutuncin, har dakinsa take zuwa gurinsa, Allah kadai yasan me sukeyi" Mummy tayi shiru tace "lallai yarinyar nan makira ce, agaban idona take bude baki tacewa Jalal mara tarbiyya, Ashe itama mara tarbiyya ce, tunda take biye masa suna lalacewa, wallahi bata isaba dole in nesan tata da dana, dan bazan zuba ido yana ta'amalli da itaba, akan me na yadda da ita  ina mata kallon mutuniyar kirki amma zatayi min haka? Gaskiyar dsddynsa yana neman mata kenan inbahakaba uban me take zuwayi dakinsa, kema banda rashin mutunci ubanme ya hana ki gayamin abun tun farko" " Mummy dan Allah kiyi hakuri, kawai nidai bana son ki tayara da hankalinki ne a zatona zan iya shawo kan abun, tunda naga abunda yafaru yau kalli banbamin dayake miki dankice kar ya tafi, Amma dayake akwai abunda sukeyi ai baze iya hakura ya tafi ba, yanzu ki kwantar da hankalinki kawai dai kiyi kokari ayi mana Aure da shi a wuce gurin " " Ke kina batun inyi kokari ke wani kokarin kikayi?, tsawon shekaru kina gidan nan amma kinkasa janyo hankalin sa, Amma kanwar kanwarki wannan 'yar yarinyar hartasan taja hankalinsa duk taurin kansa, da uwar me tafiki? Niba ina nufin ki zubar da mutuncinki ba amma abun ya dauremin kai, ace har taci mutuncinsa agabana amma dayake bashida zuciya har tasamu kusanci dashi fiye dani da kema gaba daya Kinga tashi kibani guri ni raina ya gama baci" Ilham ta mike ta fita tana zunbura baki, Amma dai tayi Nasara tunda har Mummy tafara daukar zigarta ta harzukata haka yanzu saura next plan dinta. Jalila ta tsaya ta kalleshi tace "to ni zan shiga gida, Amma kabawa daddy hakuri" "Hakurin me zan bashi? Jiya da daddare ya tafi U.K ai" "to Mummy fa?" "mezan mata, akanta nake kokuma wani abun nayi mata? " "Ohh God kanada taurin kai, Just recently kace you want change, kuma yanzu kana wata magana, she's your Mother, komene halinta kuwa, Aljannarka tana karkashin kafarata, ko kanaso kashiga wutane?" Tayi masa tambayar kaman tana tambayar karamin yaro Kallonta yayi amma bece komai ba "Kadinga zuwa inda take, kayi hakuri da duk yadda take, kadena bata mata rai, kaji dan gidan daddyn sa, your Mum is so kinda, she loves you, you have to show her love too, batun Ilham kuma babu dadi kace baka son mutum agabansa kaji" Tai maganar tana murmushi sannan ta shige gida. Sumar kansa ya shafa yayi murmushi shima. Gida ya shige yayi wanka ya ci Abinci ya tafi gurin Jawwad, Jawwad na ganinsa yafara dariya "mutanen Dubai ya akayine?" Jalal ya dan hade rai "naga alama da hadin bakinka kanwarka tasa aka hanani tafiya" "niba hadin bakina, amma nasani daddyn Hanan tagayawa, tun a lokacin nasan za'a soke visa dinka, amma nayi shiru ban gaaya maka ba, Amma ya akayi kasan itace tasaka, ina fatan zakayi hakuri karka hukunta ta" "Hmm Jawwad kenan, yarinyar nan nasan halinta sarai, tun ana gobe zan tafi take dariya tace taga ta inda zan tafi, kaga inba itaba babu memun haka, akwai abunda tayi da har yanzu yake bani mamaki shiyasa akwai abubuwan da idan tayi bazan mamaki ba. Sannan yazan mata ta riga tayi, ban mata komaiba tare muka dawo ma" Murmushi Jawwad yayi yace "zoka bani Labari, yaushe kuka dena fada ne? Ya akayi ka sakko da wuri haka? Nazata inka gano itace semunzo ban hakuri kar a hukuntata hukunci me tsanani" "ta fini gaskiya ne, a da dinma abubuwan da take fada akaina gaskiya take fada, nina nake fadan rashin gaskiya, sedai tafiya tsiwa a gadarance take gayamin magana abunda yake harzikani kenan" "to yanzu fa?" "Bansaniba babana kasani agaba se antayamin tambayoyi kake, sekace EFCC, kaje ka tambayeta mana" Dariya Jawwad yayi tareda dan jan kunenen Jalal dake cin Abinci ta sigar wasa yace "Allah ya huci zuciyarka ranka ya dade nidai tunda baka hukunta taba kagama min komai" Murmushi Jalal yayi sannan yacigaba da cin Abincin sa. Sunata hirarsu shida Jawwad gwanin sha'awa, Naja tana gaban mudubi, tasha kwalliya kaman zata gasar rawa, duk tabi ta tsuke jikinta, ta feshe jikinta da turare se taunar chewing Gum takeyi Nana tace "Ehemm su hajiya Naja ko anyi sabon kamune wannan wanka haka?" "bawani Sabon kamu, gurin Masoyina zanje tunda shi bezoba ai gara inje inda yake" Jalila kallin Naja take kawai dan ba karamin tausayi take bata ba yanzu, rashin sani yafi dare duhu, da Jalila zata fadi wani abu data rusa duk wannan rawar kan da farincikin Naja har karshen rayuwarta, abunda ita kanta Najar bata san dashi ba "Allah ka kiyayemin Yaya Jawwad dina ka tsaremasa Imaninsa tareda dukkan Musulmi, dan a wannaan shigar da Naja tayi tana wannan masifaffen Kamshin indai Lafiyayyane namijine da wuya ya iya shallake wannan mugun tarkon na shedan. Nana ko cewa tayi" kekam dan rashin aji dan yaki zuwa ke sekije inda yake, Sannan kalli shigar ki bata daceba kayan sun matseki" "A'a ke kyaleni, A haka zanje irin wannan shigar da ita ake kama zuciyar masoyi kuma tana kara kusanci da kauna" Itadai Jalila batace komai ba har Naja ta fice, sedai girgiza kai datayi tana cigaba dayiwa Jawwad addu'a. Jalal yagama cin Abincin sa ya dakko system dinshi yana dubawa yace "Jawwad next month fa zaka tafi Abuja gurin Aikinka" Da sauri yace "Saboda me?" "Saboda nima haka na shirya maka kafin intafi, dan haka seka tafi" "haba Jalal meyasa, Abba na kokarin bude mana store ne muyi ruining dinsa da kanmu kaga base nayi aikin gwamnati ba mun huta" Dan tsurawa Jawwad ido yayi a ransa yace "mezanmaka a rayuwa Jawwad in biyaka kauna da alherinka, Sarai Jawwad yasan Jalal yanada tarin dukiya a kasa, Amma bayason ya kashe masa zuciya kar ya nemi na kansa" "Kaga idan ka tafi nika barni da harkar kasuwancin zanyi mana, Amma seka tafi fa" "Amma Jalal hakan...... " Salam Alaikum " Muryar Naja ta katsesu gaba daya suka juyo suna kallonta Wato har wani pink take saboda tsabar bleaching, saboda daganin wannan farin banata baneba, ga gaba daya dakin ya gauraye da kamshin turarenta tareda karnin mayukan da take Amfani dasu, tasaka riga da skirt na material dasuka kama jikinta matuka duk saman kirjinta a waje. Dauke Kai Jalal yayi, yacigaba da danna system dinsa "Masoyina gurinka nazo fa" Tai maganar tana kokarin zama a kusada Jawwad, Jalal kam mikewa yayi ya shige bedroom din Jawwad, yana tunanin meyasa wasu matan basuda kunya basu san ciwon kansu ba, ace mace budurwa kaman wannan amma tana nanikar namiji haka ba kunya ba tsoro, hakama Ilham take masa wani lokacin, To Amma meyasa ita Jalila bata haka? Shidai yasan ba ruwansa da mata hasali yana gudun taba macen daba maharramarsa ba, Amma ita Jalila bayajin komai dan ya tabata, yana jin kaman hakan shi a gurinsa ba laifi bane, sannan duk lokacin da hakan tafaru a tsakanin su yana ganin matukar tsoro da rikicewa a idonta. Haka yacigaba da zancen zuci yanata tunani daban2. "Haba masoyin, Meyasa baka zuwa inda nake Yaya Jawwad, wallahi banajin dadin abunda kakemin sam baka nunamin soyayya" Matsawa yayi daga kusada ita yace "Naja soyayya daban Aure daban a yanzu keba halalina bace ba meyasa zakimin irin haka? Ke ko kunya ta bakyaji ne haba Naja kidinga kama kanki mana" Matsowa takumayi jikinsa tana kashe murya tace "meye wani kama kai, Aurena fa zakayi dan Allah kasaki jiki ka nunamin soyayya haba Jawwad" takai hannu tana shafo fuskarsa Gaba daya jikin Jawwad rawa yakeyi Tsaki yayi yana kokarin mikewa, tunda ya fuskanci bazata ganeba Riko hannunsa tayi tana kokarin Rungumeshi, A fusace ya hankadeta kasa yana kokawa da numfashi, Tashi takuma yi tace "bazanyi zuciya ba" sekace mayya take kuma shanye ido kamar tana maye, ta rungume shi. "Ke!!!" ya daka mata tsawa a fusace wadda seda yasa Jalal fitowa a sukwane yayi jifa da ita "ki tashi kibarmin dakina, Allah ya shiga tsakanina dake ban taba aikata mummunan sabo ba bazan fara akanki ba, get out from my room ko in illataki" idon Jawwad yayi jawur jikinsa yana rawa, gaba daya ta kasa gane dama Jawwad yana fushi haka? Jalal ya karaso ya rike Jawwad yace  "Jawwad kyaleta yi hakuri, calm down" "bazanyi hakurin ba ka kyaleni, wallahi takuma zuwarmin daki sena bata mamaki, bata san a bisa umarnin Maama zan Aureta ba, in bahakaba me zanyi da ita? Me take dashi daza'a kalla a ce wannan mace tagari ce ya dace a Aureta? Itada mahaifiyarta sun shiga sun fita sun rabani da kanwata shekara da shekaru suna uzzuramata suna bata mata rai suna cimata mutunci, na hakura, ance sena Aureta na hakura nayi biyayya, be isheta ba seta nemi tasana aikata laifi me muni" Kallon Naja Jalal yayi, kaddai ace wannan yarinyar ya yadda ze aura, Amma Jawwad hakurin nasa yayi yawa. Naja ba karamin mamakin abunda Jawwad yayi mata tayi ba, ita babban mamakinta bata taba ganin yana fada ba, saboda tasan mutum ne me kunya da kawaici. Jalal yace "Naji kadaiyi hakuri" "bazanyi hakurin ba Jalal" Jalal yace "da nine da yanzu kacemin masifaffe, haba dan uwa Aliyu Haidar zakin Allah, katangar sikari na Hanan kowa ya jingina da kai seya lasa, fari me farar aniya kai a cikin masu sunan ma na dabanne kayi hakuri" Jalal yana lallaba Jawwad ne saboda yasanshi be iya fushi ba, seya shafe shekaru be fushi ba amma idan yayi abun baya kyau. Naja tace "kagama duk masifunka, wallahi nidin dai ni zaka Aura kuma zaka gane baka da wayo, bari Maaman ta dawo zaka gane ka taka tarkon mace. Jalal ya hanashi magana, suka kyaleta a gurin yaje ya dinga rarrashin Jawwad, ana haka Hanan ta kira wayar Jawwad, Jalal yai murmushi yace "kaga ka daga wayar nan ayi maka kalamai, zaka huce" "A'a ka kyaleni, am not in mood" Aikuwa Jalal ya daga wayar suka gaisa yace "Hanan ga mutumin naki, Amma ransa a bace yake fa" "Subhanallah dan Allah wayakai min zuciyarsa bango har akasamin shi fushi, dan Allah ka bashi wayar" girgiza masa kai Jawwad yayi alamar baze karba ba "kiyi hakuri, baze karba ba fa, ransa a baci yake" Hanan a shagwabe  tace "Shikenan tunda baze karba ba amma zuciya ta bazataji dadi ba, Allah kuka zan tayi duk daren nan, wallahi har naji tawar zuciyar tafara nauyi" Ai tuni Jawwad ya zare wayar a hannun Jalal yasa a kunnensa yace "Hello Hanan kina jina?" "haidar dina me akayi maka?" "wani little issue ne, kuma yanzu komai yayi settling" "little issue baze bata maka raiba" "ki manta kawai, kar inga abunda yasamin ke kuka" Jalal yaji Jawwad ba kunya anataya masa kalamai agabansa. ya minstili kafar Jawwad yace "dan rainin hankali kawai" Jawwad yai murmushi Jalal ya daga masa hannu ya wuce gida. Yanayin maganar Hanan kaman Jalila, tuno moments dinsu yayi dazu dayake ta dage bilhakki tana masa fada, da yadda take da ido idan batada gaskiya murmushi ya dingayi shi kadai, har ze kwanta ya tuno maganganun Jalila game da Mummy. Mikewa yayi ya nufi cikin gidan, babban palourn Mummy yasa hannu ya bude kofar. Salla takeyi yanemi guri ya zauna, rabonsa da dakin  nan harya manta yana jiranta yana sake2 a zuciyarsa mema ze ce matane?. Ta idar tagama lazimi, ba karamin mamakine yakamata ba ganinsa a part dinta Ta kalleshi tace "Lafiya kuwa? Ashe baka tafi ba, uwarka wadda tafini, wadda take baka abunda bana baka ka fasa tafiya saboda ita. " Wakenan? " 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹 _ABDUL JALAL (2020)_ _Story and written by_ AISHA HUMAIRA (daddy's girl) PART 2 _PAGE 3️⃣7️⃣90 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com _MY FIRST NOVEL _ "wakenan?" ya tambayi Mummy yana kallonta "eh da ita yarinyar daka dawo dan ita mana, tunda tana maka abunda bana maka, wallahi kaji tsoron Allah, ba irin Magiyar da banyi maka ba, Amma kayi biris amma yanzu dayake tafini ai gashi kadawo" Tsyawa yayi ya zubawa Mummy ido tagama, Yayi tsaki ya tashi ya fice yana masifa. Haka yakoma dakinsa yana mita yana tunanin meyasa ma yaje inda take. Jalila tanata lissafi gobe su Abba zasu dawo, dan haka ta tsananta Addu'a Allah yabata sa'a yasa Abba ya janye batun Aurawa Jawwad Naja. Yauma Jalila taje school, sun kammala lectures, sunfi to itada Zahra, Zahra tace "Yawwa nikam Jalila naji Wata suna hira tace wai jiya wani hadadden gaye yazo yasaki a mota ya tafi dake, amma wai dagani dan shaye2 ne dan wuyansa hada sarka, ga wani irin Aski akansa, ina fatan lafiya ba wata matsalar bace?" Dan karamin tsaki Jalila tayi aranta tace" dan jaraba da masifar mutane komai kayi idonsu akanka "Eh haka akayi, seme kuma?" "A'a ba komai dama nayi tunanin ko mutanen baban Saleema ne" "basu bane, Yayana ne" Jalila tabata amsa a takaice, Dan zare Ido Zahra tayi "dama kinada yaya dayake shaye2, na zata Yaya Jawwad ne kawai Yayanki" "Akwai wani to, kuma akansa nayiwa Alhaji Kabiru baban Saleema, abunda yanzu yana daf da zuwa prison shida 'yan tawagarsa" "Amma Jali.... " Ke zahra kin isheni wallahi, nagaji ga yunwa ina ji se faman tambayoyi kikemin, sekace wata likita, haba se Allah ya kaimu gobe" Inda sabo Zahra tasaba da halin Jalila, tanada saukin kai Amma tanada tsari a komai nata, in bakasan halinta ba zakace batada kirki ne kawai, bata da san yawan tambaya. Mummy ta bawa Ilham kudi tace ta kaiwa Nana ta ajiyewa Maama in ta dawo a bata, Ilham ta karba harta shiga gidansu Nana wani tunani ya fado mata a rai, dan haka tayi murmushin mugunta tashi. Tana fitowa hakan yayi dai2 da dawowar Jalila daga makaranta sukayi karo a kofar gida. Ilham ta tsare Jalila da ido tana mata kallon zaki gamu dani ne. Jalila tace "Ilham wai kin manta maganar danayi mikine? Ki dawomin da Al'qur'anina tun muna sheda juna dake" Ilham ta rike kugu ta kalli Jalila "idan naki fa? Me zakiyi?" "Aimeyi baya fada se dai kigani a aikace, zakiga matakin dazan dauka, ki kawomin abina na gayamiki" "ina jiran ganin matakin dazaki dauka din, amma kafin ki dauka ni ki saurari nawa" "banida lokacin saurarar duk wani shirmenki, ba abunda kika isa kiyi min, nagama magana Ilham" Jalila tasa kaii ta shige gida. Kwana hudu kenan basu kara haduwa da Jalal ba, haka nan yaji yana kewarta sosai. Koba komai yayi missing neman maganar ta. Sannan tunda abun nan yafaru tsakanin sa da Mummy be kuma shiga cikin gidan ba. Mikewa yayi yafito zetafi gidansu Jawwad. Yana kokarin fitowa daga part dinsa Ya hango Ilham a jikin mota tanata boye kudi a jikinta, yana ganin haka yasan bata da gaskiya amma bebi takanta ba ya fice. Jalila tana zuwa ta dire Jakarta ta shiga tayi wanka, ta fito tayi sallar Azahar ta kwanta bacci, se la'asar ta tashi, tayi sallar la'asar sannan taji tana jin yunwa. Jalila tana zaune akan dadduma kafin tabar kan daddumar ta, Ahmad ya kirata suka dinga hira har kusan 40 minutes, Nana kallon ta kawai takeyi seda tabari tagama sannan tace "Jalila wai dan Allah ina kika samo wannan Ahmad din, iya sanina ba kya son duguwar waya amma kalli yadda kika zage kina waya" Jalila tayi murmushi sanna tace "Nana a Bauchi na samo shi, yanada kirki sosai" "kinga niba wannan ba magana nakeso muyi masu mahimmanci" "inajinki amma ki hanzarta inajin yunwa" "bawani in hanazarta, ki zauna kigama wayar se yanzu zakiji yunwa? Jalila dan Allah ki gayamin hakikanin meke tsakanin ki da Yaya Jalal?" Jin maganar tayi wani banbarakwai, batayi zaton jin wannan tambayar ba "kamar yaya? Kinga wani abune da baki yadda dashi ba? Meyasa kikamin wannan tambayar" "Jalila ruwa baya tsami banza yadda Ilham ke takura tsanarki tabbas wani abun tagani, tana claiming kuna soyayya ne, nima da nayi wani nazari zancenta yana kusada gaskiya" "Mtseww niban san yakuke so inyi ba, da muna fada da shi, ance banida kunya inamasa rashin kunya, yanzu na dena ance ina sonsa to ya zanyi, Nana niba son Jalal nakeba, ina tausayinsa ne musamman danaji labarin waye shi, Nana a baya nikaina nasan na bata masa rai dayawa, yadda nake masa rashin mutunci da bakaken maganganu, naga ban kyauta ba sannam ba'a gyara da barna, muddin kanaso ka temaki mutum ya dena aikata laifi indai zakayi masa hayaniya baze dena ba, zaka kara tinzira shine, na fuskance shi yanada mataukar saukin kai, na gane hakanne a zuwan dasu Hanan suka danyi, Hanan gashi sa'ata ce, tafini tsiwa amma yana sakarmata fuska har yayi mata wasa, ita bata masa rashin mutunci kamar ni, shiyasa nima na sassauta yi masa wulakanci, Amma babu soyayya tsakanin mu, ina fatan kin gane" Mikewa tsaye Nana tayi tana shirin fita ta waigo tace "Naji amma ban yadda ba" Nana ta fice daga dakin, tunani Jalila ta dingayi kozata gano wani dalili ne yasa ake kallon soyayya ce tsakanin ta da Jalal amma bata ganiba share wannan tunanin tayi ta mike ta fito itama domin neman abunda zataci dan ba karamin yunwa takeji ba. Koda ta duba kitchen ba'ayi girki ba bakomai tayi tsaki ta fito daga kitchen din. Daki takoma ta hado goldenmorn dinta ta fito farfajiyar gidan domin shan iska, tasamu kujera ta zauna tana cin Abincinta, Abba takira a waya yakara tabattar mata da gobe Insha Allah ze dawo, ji take kaman ta Jawo gobe Abba yadawo dan ta kagu ta dau mataki akan Naja. Tanata wannan tunanin aka kira wayarta, A zatonta Ahmad ne amma se taga bakuwar lamba dagawa tayi tasaka a kunnenta tareda yin Sallama Caraf taji matar ta Ambaci sunan ta "Jalila yakike ya gida?" "lafiya kalau Alhamdilillah" "Antyn Jalal ce, nasan baki gane me maganar ba" Murmushi Jalila tayi tace "yi hakuri Anty ban dau muryarki bane, ya gida ya kukaje gida ranar" "lafiya kalau nasan baki dauki muryata bane, Jawwad nakira nace ya turomin lambarki mudinga gaisawa, ya mutan gidan naku?" "lafiya kalau Anty, yasu Mahmud?" "Ahha Mahmud Nana zaki tambaya shi, muntafi da kwana uku yakoma U.K" "Allah sarki, aikam kullum suna tareda Nana a waya" "Aikam naga shi can nasa hankalin ya karkata, se fatan Allah ya tabattar da alkhairi" "Hakane Ameen ya Allah" "Jalila ya Amanata dana bar miki?" Dan murmushi Jalila tayi tace "Yana nan Anty" "Kundena fadan dai ko?" Murmushi Jalila takumayi tace "Anty kenan" "Au kunya na baki? Jalila bamuda kalaman dazamuyi Amfani dasu gurin gode miki akan namijin kokarin da kikeyi keda Jawwad akan Dan uwanmu mungode Allah yasaka maki da Alkhairi" "Haba Anty meye wani abun godiya kuma? Ni banga wani abu da nakeyi ba" "inke baki ganiba mu mungani ai, ko iya yanzu kin taka rawa gurin canza abubuwa dayawa a tareda shi, munyi waya dashi yacemin daze bar kasar nan kika hanashi" "hmm sa'a kawai nayi, nazata ma ze min duka, Allah yakara shirya shi, nima nagani ya rage Abubuwa sosai" "Ameen Jalila, haba baze iya dukanki ba ai, he respect you fiye da yadda kike tunani, ki kulamin da amanata Jalila, inaji a jikina abubuwan da Jalal yake zezama tarihi sanadinki" "Allah yasa, Munagodiya Jalila, Allah ya jikan magabatanki" Jalila ita bataga me tayi ake mata wannan godiyar ba, Jalal din da banda fada ba abunda ke hadasu, dan haka Tace "Anty yaushe zanzo abani turaren maiduguri ne? " "Kibari in Aurenki yazo har kano zanzo in hadaki, kamshi sekin gaji, Allah ya nunamin Aurenki" Dariya Jalila tayi ta kashe wayar, Antynsa tanada saukin kai, gata da abun dariya, Amma ita bataga me tayiba daza'ayita yimata wannan godiyar ba. Washegari da safe Jalila bata tafi makaranta da wuri ba, seda tagama gyara gidan dan kusan kwana biyu Naja bata gidan, Halima dama Maama ta dade da sallamarta, Manu direba be dawo daga kai Nana ba, tunda ita Nana da wuri ta tafi school yau, Taita gyaran gida, da kokarin dora girki saboda dawowar su Abba, be kamata abar gidan bakowa ba gashi ba'ayi girki ba. ta fito ta leka part din Jawwad, taga inya tashi ta kaimasa Abinci, Amma ta hango Jalal yana shan sigari, Jawwad kuma baya palourn, da niyyarta ta fadawa Jalal bakar magana amma tafasa ta shiga palourn. Batayi sallama ba unexpected ya daga kai ya ga Jalila, hade rai tayi sosai taki kulashi shima be kulata ba, ta duba ta kalleshi tace "Ina Yaya Jawwad?" "ki duba mana" yabata amsa a takaice "Ina zan duba?" ta tambayeshi a ransa yace "lallai yarinyar nan kyaleta yayi bekuma kulata ba yanata shan sigarinsa, tambayarsa takuma yi " wai yana ina? " "Zoki duba rigata kona sashi a ciki" Bude baki tayi tana kallon sa, Jalal dan rainin hankali ne, amma ta shareshi ta dakko wayarta takira Jawwad be dauka ba, tsaki ta danyi taje tayi knocking kofar bedroom din Jawwad amma ta tarar yana bacci. Mayarwa tayi ta rufe ta juyo zata fita, Amma Jalal bashida niyyar dena shan taba, gashi yana kallon boom TV ne music ne kawai yake tashi, yana shan sigarinsa yana lumshe ido, ya jingina a jikin kujera. Dan girgiza kai tayi tazo gabansa ta tsaya ta dauki remote ta mayar saudi qur'an, bude ido yayi ya kalleta sannan yace "Meye haka?" "Abunda ka gani" ta bashi amsa "mayarmin inda take da farko" "Bazan mayar ba" dago Jan idonsa yayi yana kallon ta, wani tunani tayi a ranta, ta fuskanci fitsarar da rake masa baya sashi dena abunda yakeyi, dan haka tace "Ka karyane? Da safiyar nan kake shan sigari, kamanta me likita yace maka ne? Kobaka son lafiyar kane?" Shiru yayi ya dauke kai, ba karamin haushi takeji tana masa magana ya mata banza ba amma ta dake tace "Am talking to you, kamanta you said you want change, and i promise to help you out, please badanni ba a kashe sigarin nan please, na zata dena mu'amalarka da wannan jakin Jejen zesa ka canza kadena shaye2, amma meyasa har yanzu baka dena ba?" Juyowa yayi yana kallonta, tayi kalar magiya, a hankali yace "ba lokaci daya nafara shaye2 ba, don't expect me to stop it at once, Jeje ya dade yana cutar dani, na dade ina shaye2 bazan iya dena wa lokaci daya ba" Tausayinsa ne yakamata, dan haka tace "I understand, kadena sha dayawa, a hankali zakaga ka dena" gyada mata kai kawai yayi, ta dan kalleshi maganar zahra ta tuna, "wani handsome guy" Ba karya Jalal yanada kyau, inama ba ya wannan shaye2, da seyafi haka kyau, Amma tana fatan Allah yasa abunda ta shirya akansa yayi tasiri ya dena shaye2. "inaso kamin wata Alfarma" "fade ta Allah yasa zan iya" "zama ka iya, ba me wuya bace ba" "inajinki" "Dan Allah kadena saka sarkan nan, you are Muslim, bekamata ace kana yawo da itaba, da dinma nasan saboda Jeje ne kaima ka kwaikwaya please ka cireta" Kallonta yakeyi amma bece komai ba, can kuma ba tareda ya cire sarkar ba yace "meyasa idan aka kirani da dan shaye2 kike jin haushi bayan kema kina gayamin? Dan shaye2 mara tarbiyya wanda ya raina iyayensa, idan wani ya gayamin kinajin haushi, Amma kekina gayamin" Gaba daya taji jikinta yayi sanyi, har bataso ta tuna irin bakaken maganganun datake masa abaya, musamman idan ta tuna labarin Rayuwarsa tabbas tayi wauta, amma tace "Waye ya kiraka da dan shaye2 naji haushi?" "mutane dayawa, bari in tuna miki daya, Oga KB mahaifin Faruk, ban taba tunanin yadda kika tsaneni a wannan lokacin ranki ze baci dan anci zarafina baa" "har yanzu kanajin haushin abunda nayi maka abaya ko? " ko kadan gaskiya kika fada ai, banida tarbiyya, ban cancanci zama Abokin yayanki ba kaddararsa ce tareda tawa shi....... "Enough dan Allah, wannan abune daya riga ya wuce please" Kallonta ya kumayi sannan yasa hannu ya cire sarkar wuyansa yace "Insha Allah nayi alkawarin bazan kuma saka sarka a wuyana ba" Murmushi tayi "Are you serious" "dagaske nake miki" "kai gaskiya na yadda you want change, Allah ya shirye ka da gaggawa" murmushi yayi yace "Ameen ya Allah" daga nan ta mike tayi waje a ranta tace "da haka Insha Allah kafin inyi Aure seka dena shaye2 in Allah ya yarda" Yau fasa zuwa school tayi ta zauna ta shirya Abinci saboda dawowar su Mummy, bayan tagama ta kaiwa Jawwad nasu, ta gyra ko ina a gidan se kamshi yakeyi. Bayan tagama komai ta zauna tana tilawar Alqur'ani, wajen karfe daya Abba suka dawo gida, ta dinga murna tana musu barka da hanya, duk hassadar mutum yasan gidan nan ya sha gyara amma Abba ne kawai ya yaba, Maama nunawa tayi bataga ma me akayi ba. Bayan sunyi salla ta kawo musu Abinci. Takoma dakin su. se la'asar Nana ta dawo daga school nan ta dinga murna su Maama sun dawo, Jawwad seda magariba ya shigo cikin gidan yayiwa Su Abba barka da dawowa, wannan karon kamar kullum Abba yarabawa kowa tsaraba sunata murna, sun hadu a palour ana hira. Abba yace "Jawwad ranar Asabar Insha Allah za'akai kudin Aurenka kamar yadda Maamanka ta bukata, inda wani shiri da kake ganin zakayi to kaje kayi, Jalal yagama komai next month Insha Allah zakafara zuwa gurin Aikinka" Wani irin gumi ya dinga tsatstafowa Jawwad, yariga yagama karaya, sannan yana jin matukar kunya da nauyin ya bude baki yagayawa mahaifinsa baya son zabin da mahaifiyarsa tayi masa, Jalila ta kurawa Abba ido alamar bata gamsu da abunda yafada ba, Abba ya kalleta yace "ya dai 'yar Baba? Kokinada magana ne?" Juyawa tayi ta kalli Maama data tsareta da ido, magana kam akwaita a bakinta amma ba' a gaban Maama ba, girgiza kai tayi alamar A'a, ta mike ta tafi dakinsu tanata safa da marwa, tana tunanin ta ina zata fara yiwa Abba bayani, tasan kotayi Maama karyata ta zatayi. Gajiya tayi da sintirin datake taje ta bude wardrobe zata dau towel tayi wanka, ta bige wata jakar Naja ta fado kayan ciki suka zubo dayake bata zugeta ba, a sama inner wears dinta ta dora a kai, amma kwayoyi ne da kwalaban syrup a cikin jakara, binsu da ido Jalila ta dingayi yayinda tayi mutiwar tsaye. Da sauri ta durkusa ta tattare mata su ta mayar mata da jakarta yadda ta ganta, nan tunani yakara yiwa Jalila yawa bazata taba bari a Aurawa namiji kamar Jawwad wannan tanbadadiyar ba,ko Nana bata gayawa abunda ta gani ba, tayi shiru da bakinta. Wasa2 duk yadda Jalila taso ganin Abba personally Maama ta kankane, ta tattare a part dinsa bata matsawa ko nan da can, seda aka kai kudin Auren nan, naira dubu dari Abba yaje ya kaimusu, su Yaya mairo hada kira wayar Maama tana mita wai duk Arzikin da Allah yayi musu amma ace kudin Aure akawo dubu dari, mecec dubu dari a kudin da suke dashi, Maama taita lallabata tace tayi hakuri zasu hade a kayan lefe. Yayinda gefe abun duniya ya damu Jawwad, begayawa Hanan halin dayake ciki ba, ko Abinci baya iyaci, duk ya rame. Jalila da kanta taje ta dinga bashi kwarin gwiwar yacigaba da Addu'a komai zeyi dai2. shikansa Jalal abun ya dameshi, meyasa za'ayiwa namiji Auren dole, ko mace be kamata ayiwa ba balle Namiji, shima Jawwad saboda nusaranci da kunya baze iya cewa baya sonta ba, wani lokacin kawaicin Jawwad yana batawa Jalal rai. Jalal yanata tunanin wani taimako ze iyayiwa Jawwad, dan shima baze bari ayi wannan Auren ba, tunda Jawwad baze iyaba zeje yasamu Abba da kansa yagaya masa Jawwad baya son yarinyar nan, yana wannan tunanin yaji message ya shigo wayarsa, Koda ya karanta, tsayawa yayi yanata juya message din shidai yasan tabass wannan message bana sa bane saba lamba akayi, dan haka ya barshi a matsayin anyi missing number ne aka turo masa, dan hukumar dasuka turo message din da sun san wayeshi sun san laifin dayake aikatawa da basu turomasa abunda suka turoba. Jalila ta yanke hukuncin yau zata samu Abba ko agaban waye, zata nuna masa illar abunda yake shirin yi Kai tsaye part din Abba taje, ta shiga da sallama a bakinta, ya amsa sallama sannan yace "dama ina son ganinki, Baby ankaiwa yayanki kudi ze Auri 'yar uwassa, kune' yan mata kunfi sanin menene kuke so, kuma kuna tareda ita, maybe a kayan lefe akwai abunda takeso maybe ku tayi hirar daku, ba lallai tagayawa iyayen ta ba, dan haka inda wani abu da take bukata kokune tagayawa kota rubuto, saboda asan me za'a samata a kayan lefe" "Abba wannan Auren fa bame yuwuwa bane?" mamakine ya kamashi yace "meyasa Jalila?" "Baya sonta fa" "Amma na kirashi na tambayeshi yace min ya yadda" "Haba Abba zuwa yanzu yakamata kagane halin Yaya Jawwad, tunda kake ka taba nuna kana son Abu yace bayaso? Wallahi Abba Auren nan tamkar kasa hannune da kanka ka rusa doguwar tsaftataciyar katangar rayuwar Yaya Jawwad ne, Abba please kayi bincike" "karya kikeyi bakar munafuka, ba wani bincike daza'ayi, yarinya 'yar dangice, me tarbiyya da sanin yakamata suna son junansu, Amma dan munafunci shine kike bata mata suna a gurin sirikinta, kedai Azzaluma ce, ni ina kudina ma da Mummy ta bayar akawomin? Ilham tace tabaki amma dan son zuciya baki baniba seda na buga waya aka gayamin ke aka bawa" Daga Abba har Jalila tsayawa sukayi suna kallon Maama, Jalila takasa gane inda Maama ta dosa 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                                  *ABDUL JALAL*        _Story and writing_               By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girls_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                       *P.W.A*✍️                   PART 2                                   _PAGE  3️⃣8️⃣91 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                                          _MY FIRST NOVEL _ Abba ransa ya baci dajin kalaman da Maama ke fadi dan haka yace "zainab meye haka kuma? Kibar ta ta fadi abunda yake bakinta mana, be kamata ki katse mata hanzari kidinga jifanta da wannan muna nan kalaman ba akanme? Na dade ina tunanin Jalila bata jin dadin zaman gidan nan, Allah ka dai yasan mekike mata inba na nan, nayi shiru ne dan bata taba gayamin wani abu akan irin zaman da take ba, kallonki kawai nakeyi zainab " Se yanzu Maama ta shiga hayyacinta take tuna maganganun data fada idonta ya rufe ta manta shaf agaban Abba tayi su, cikin kokarin kare kai tace " kayi hakuri Abban Jawwad, raina ne ya baci, iya sanina Naja batada wani aibu amma Jalila se kokarin kushe Auren take, kuma da ina cuzguna mata aida zata gaya maka tunda kasan bakinta baya shiru" Jalila kallon Maama kawai take, Abba yayi tsaki yace "Inajinki Jalila cigaba da maganar ki" Jalila tace "A'a Abba base muncigaba ba, Amma Maama ni Ilham bata bani kudinki ba, tsawon zamana a gidan nan ban taba daukan cokali da sunan ha'inci ba, kina aikena gurare da dama da kudi, har banki kike turani da ATM card dinki ban taba batar miki da ko kwabo ba abaya, wallahi ni Ilham bata bani kudi ba" Yadda Jalila take maganar kasan zuciyarta a cunkushe take da bacin rai, dan har idonta yatara Hawaye, Maama kuwa fakar idon Abba tayi ta watsawa Jalila wani kafirin Kallo. Abba yace "ke Zainab kikoma can kuyi maganar kudinku, ni 'yata bata sata, bata ha' inci na yadda da ita, Jalila tashi kije Allah yayi miki Albarka, karki sake ki zubar da hawayenki a banza" Jalila jinjina masa kai kawai tayi ta mike, tana fitowa taji hawaye nabin fuskarta wani bayan wani, koda Jalila ta koma daki Nana tana bacci dan haka ta samu guri ta takure ta fashe da kuka, hada sheshsheka tana kuka tana surutai "Ummi kingani ko? Da tun farko kin tafi dani da kome zefaru tare ze samemu amma kinmin Nisa, kin barni inata fama da wahalar Rayuwa, banida matemaki se Allah" cikin bacci Nana taji kukan Jalila, koda ta bude idonta Jalila ce ke faman sharbar kuka, da sauri ta sakko daga kan gadon tazo gabanta tareda fadin "Jalila lafiyarki kuwa? Gayamin me yasamiki?" Shiru Jalila tayi se kuka data cigaba, duk yadda Nana tayi Jalila taki gayamata me yafaru, Nana ta rumgumeta tana fadin "tunda bazaki gayamin ba bazan takuramiki ba, Amma dan Allah kidena kukan nan, Jalila banajin dadin ganin kina kuka haka dan Allah kidena in bahakaba nima zaki sani kukan" Jinjina mata kai kawai Jalila tayi, ta zame ta kwanta akan cinyar Nana, ta juyarda kanta hawaye na cigaba da zuba. Da Naja ta dawo gidan seda Maama tagaya mata abunda ta tarar da Jalila tana gayawa Abba, Naja ta dinga masifa taana zataga bayan Jalila, setasa ta bar gidan da kafarta, tunda ita mayyace, Maama ta gaya mata wai Jalila ta cinye mata kudi dubu tamanin Abba yace karta kuma daga maganar shi yasan Jalila bazatayi haka ba, suka kuma haduwa sukasa Jalila a gaba da gori, Maama ta hade kai da Naja suka cigaba daYiwa Jalila barin miyagun maganganu, Amma sam Nana bata san meyake wakana ba, zuwa makaranta ne kawai kesa Jalila samun raguwar pressure dake kanta, shima yanzu makarantar idan taje kuka takeyi bata jin lectures din. Jalila batayi mamakin abunda Ilham tayi mata ba dukda abun yamata ciwo, Amma a yanzu ita ba wannan ne ya dameta ba, maganar Auren nan ce yake damunta. Wasa2 Jawwad yayi rama ta ban mamaki, yana cikin tashin hankali an saka biki a kusa watanni shida, ko Abinci baya iya ci, nutsuwarsa daya idan yana waya da Hanan, kokuma Idan Jalila tana masa nasiha da bashi kwarin gwiwa, ko Abinci baya iyaci, duk haskensa seda yayi duhu, Jalila tarasa ta ina zata fara shawo kan matsalolin nan. Yanzuma gurin Jawwad ta tafi don ba karamin tausayi yake bata ba, taje ta kaimasa Abincin rana, ta tarar ya idar da salla ta jira Jawwad yayi Addu'oin sa ya shafa, sannan tace "Yaya Jawwad nasan kana cikin damuwa, amma kadinga kokarin kwantar da hankalin ka, ina nan inata kokari sannan ina Addu'a Allah ze kawo mafita" Murmushin yake  yayi wanda yafi kuka ciwo yace "ina Addu'a baby, ina fatan Allah yabani ikon cin Jarrabawa" "Insha Allah komai ze wuce sannan nace ya batun zuwan ku kaduna kuwa? Bana son plan dina ya tafi a banza" "Ina sane Jalila, zamuje Insha Allah, kafin lokaci ya kure" "to shikenan, amma ka dena wannan damuwar kaji Yayana?" "Na dena babyn Ummi" Murmushi tayi masa "yawwa haka nakeson ji, bari in dawo in gyara maka dakin nan, naga yayi kura" "to shikenan Autar Ummi nagode sosai, Allah ya sanyawa Rayuwar ki Albarka, Yadda kike kokarin faranta min Allah yabaki mijin daze kula dake ya soki ya rikemin ke Amana, a lokuta da dama kina sadaukar da farincikinki dan ganin wasu sun samu nasu farincikin, Allah yabaki wanda ze kulada ke, yabaki mijin marainiya, wanda ze kula dake da maraicinki" Taji dadin Addu'ar yayan nata, Amma takasa cewa Ameen sema Hawaye daya taho mata. Tagama abunda take a cikin gida, taje domin gyara bangaren Jawwad, Jalal na kalmashe akan kujera yana game a system, sukaci Abinci shida Jawwad, yacigaba da game dinsa, tunda ta shigo ba wanda ya kula wani tsakanin ta da Jalal, Maama takira Jawwad a waya tace yaje cikin gida tana son ganinsa, jiki ba kwari ya tashi ya tafi, dan yasan be wuce akan maganar Naja ba. Jalila tasan babu alamun Jalal yayi sallar Azahar, ta duba taga system din a jikin caji take yake amfani da ita, tasa hannu ta kashe main socket na dakin, system ta dauke dama babu caji, kallonta yayi  a fusace ze masifa amma yakasa, ganin irin kallom da take masa, "Kayi sallar Azahar kuwa?" "ban Sani ba, ko innayi ke zanyiwa?" "Subhanallah karkayi sabo, ai ba fada bane, Salla fa, haske me girma ga tarin lada ga ma'abota yinta akan lokaci, kaga da kana bata mahimmanci sosai da yanzu Rayuwarka ta canza, da abubuwa dayawa kadaina aikata su, karfe uku ta wuce amma bakayi salla ba, wanda ya mutu baya salla kasan makomarsa wuta ce ta saqara, wadda ake sa wanda basa salla, Ai baka son shiga wuta ko dan gidan daddy? Ta tambayeshi kaman tana magana da yaro karami" Be Amsa ba se kallon ta dayake, tasa hannu ta janye system din "Yawwa abokin Yaya, kayi yaki da shedan, ka yaki zuciyarka ka daure, kaga in kayi sallah sekayi Addu'a, Allah na karbar addu'a bayan sallar farilla, kaje kayi salla" Mikewa yayi ya nufi bedroom din Jawwad ba tareda yace mata kala ba yaje yayo Alwala, yana shiga tayi Ajiyar zuciya mutum kaman wani dan karamin yaro, komai se an lallabashi Allah ya shirye ka, yanzu tagama gane halinsa, ba yasan fada ne sam, indai zaka gaya masa magana da fada, to zakuiyi fada dashi. Jalila tanata goge2 ta kunna TV takai sunna tv ana karatun Al'qur'ani, tana aikinta tanayi, sosai takejin dadin karatun suratul Yusuf,  dauke wuta akayi dan haka tv ma ta dauke, ta danyi shiru, kawai taji an dora daga inda ta tsaya, waigawa tayi ta ga Jalal yana karasa mata ayar, ya iya karatun qur'ani, bata manta randa ya kaita makaranta ba ranar data fara jin yana karatu, Murmushi tayi tace "cigaba mana" "A'a kedai kicigaba, na manta Aya tagaba, bana tilawa, bana tuna haddata duk na manta, kwakwalwar ta toshe" "Ahh waika manta, ba wani kamanta" "Am serious na manta, cigaba maybe inkin cigaba in tuna" Ba musu kuwa ta dora, tana cikinyi setaji yakama yanayi, "Amma kace ka manta? Dama ka iya karanta Al'qur'ani haka, inama kana yawanyi da ko a hanya kaga giya zaka dauke kanka ne, waye ya koya maka karatu haka?" "A islamiyya sannan kuma Ummi, bazan manta ba" Maama ta cazawa Jawwad kai akan Naja, yana zuwa dakin ta shiga yi masa fada "Wallahi Jawwad ka kiyayeni tun ban bata maka rai ba, shine ka hada kai da wannan makirar yarinyar take kokarin ziga mahaifinka akan Auren nan ko? To wallahi ka kiyayeni akan Auren nan zan iya cimaka mutunci, kuma in har muna raye baka isa ka kuskurewa Auren nan ba, indai zanyiwa yayata biyayya kai waye da bazaka yimin ba? " Sunkuyar da kai Jawwad yayi yace" kiyi hakuri Maama, niba ina kokarin kuskurewa Auren nan bane, kiyi hakuri dan Allah " "ni rufemin baki, se anyi magana kadinga wani ayi hakuri, Naja tagayamin wulakancin dakake mata, ka fifita waccan yarinyar akanta shima ka kiyayeni Aure zakuyi da Naja, dole ka dinga janta a jiki ku fuskanci juna" "to Maama yadda kikeso haka za'ayi insha Allah" duk abun nan Naja na gefe a zaune tana tauna chewing gum, tana hararsa, da Nana tana dakin Maama itama, amma bacin rai yasa tabar dakin. Har Jawwad ya yunkura ze fita yabar dakin, Naja tayi karaf tace "Yaya Jawwad dan Allah zan shirya zaka kaini anguwa" shiru yayi bece komai ba, Maama tace "kobazaka kaita bane?" "zan kaita bari inyi sallar la'asar" Haka ya taho ransa babu dadi, yarasa me yake masa dadi, gaba daya Maama ta canza yaya mairo kullum cikin zigata take kansa har wani sarawa yake yi, ya nufi dakinsa amma yana zuwa dakinsa abunda ya tarar ya bashi mamaki, kunnuwansa suna jiye masa kira'ar Jalal, yana karanta qur'ani , wanda rabonda Jalal ya karanta Al'qur'ani baze iya tunawa ba, to mutumin dabe damu da salla ba, ina zeyi karanta alqur'ani. Jalal yana cikin biyawa ya kakare, Jawwad yakarasa masa, tuni Jawwad ya manta da bacin ran dayake yi yace "Jalal yau kaike karatu haka? Amma naji dadi, yaushe rabo" "kanwarka ke kokarin ta kureni, nace mata na manta tace senayi shine nake tunowa naji ashe da saura, haddar bata gama zubewa ba" Jalila tace "niba kureka nake ba, aiba takura maka nayiba" Jawwad yace "Baby kinga Jalal, wallahi ba karamin kwarone ba da muna yara, kwakwalwar sa tana kawo wuta, duk lesson din daza'ayi a kansa yake daukewa, gaskiya yau kinciri tuta baby, yanzu dai mu cigaba da tilawar nima ayi dani" Murmushi Jalila tayi, Jalal yabata mamaki yau sosai, da Jalal yacigaba da karatu da al'umma zasu amfana yanada kwakwalwa sosai, Jalila tace "to kucigaba ni zanyi Alkalanci" dariya Jalal yayi wadda take masa kyau dan be fiyeyiba yace "Jawwad kai zaka fara, nifa babu haddar ta zube, shekaru Ashirin baya da yin haddar kuma kaga bayi nake ba" Jawwad yace "hakan ma ka yi kokari fa, amma dan cigaba zan na tuna maka, nayi missing din karatun ka" murmushi Jalal yayi, yafara kokarin dorawa, yana cikinyi ne kawai yafara tari, jikinsa yana rawa, Jawwad yace "lafiya meyafaru Jalal?" Tari sosai Jalila ta dakko ruwa Jawwad ya karba yana kokarin bashi amma yasa hannu ya make ruwan, ya fadi kasa, nan take idonsa yafara juyewa jijiyoyin kansa dana fuskarsa suka mimmike, nan take fuskarsa tayi murtuk yakoma Jalal dinsa na ainihi dan shaye2 wannan murmushin da Annurin na fuskarsa ya dauke gaba daya, tashi yayi daga kan kujerar dayake yakoma kan doguwar kujera ya kwanta ya rufe idonsa. Jalila tace "Yaya Jawwad meyasameshi kuma?" Ajiyar zuciya yayi yace "Jalila haka yakeyi wani lokacin, ko yana cikin nishadi inka fara masa nasiha gaba daya jikinsa ze hau rawa, ya canza Amma ze ware Insha Allah" Jinjina kai tayi takarasa aikinta tana mamaki sannan ta fice. Jawwad yayi mamakin yaushe suka shirya haka har take sashi abu yayi, Amma da ya tuna kokarin da Jalila ke tayi akan Jalal, da kuma Alkawarin data taba yi masa akan zata taya shi addu'a da kokarin ganin Jalal ya shiryu, murmushi yayi yace "lallai baby kinada sa'a mace ta farko daya ji maganar ta tun bayan lalacewarsa" Jawwad sam ya manta da batun wata Naja, seda Maama ta kirashi a waya, haka ya tashi ransa ba dadi ya dakko key din motarsa ya fito. Shigar data saba yice yauma tayi, jikin nan duk a matse se wani dan ficicin gyale, ya bude motar ya shiga, itama budewa tayi ta shiga gaba daya motar ta bule da kamshin turarenta dayake hawa ka, ya kunna motar yace "Ina zaki?" "Shopping zaka kaini zan sayi kayan kwalliya" Bekuma ce mata komaiba ya kunna motar yaja, ya kaita kofar wani store ya ajiyeta, ta kalleshi "to muje mana" "Ba inda zani, in bazakiba inada abun yi" yafada a hasale Tsaki tayi ta bude motar ta fita, tana fita ya kashingida ya kira Hanan, seda ta kusa katsewa ta daga cikin muryarta na shagwababbu tace "My Haidar am sorry bana kusada wayarne" murmushi yayi yace "gaskiya ban hakura ba, seda ta kusa katsewa za'a daga wayar" "ni gaskiya kayi hakuri ko inyi kuka" "No don't cry, Ya kike?" "Lafiya kalau sedai ina missing dinka" "Insha Allah zan shigo Kaduna next week zanzo in ganki, na kusa tafiya lagos Daddy ya samo min Aiki a can" "masha Allah can't wait to see you my dear, wallahi naji dadi Haidar, Allah ya kawomin kai lafiya, ina yayana kuma sirikina?" "Wake nan?" ya tambayeta "Yaya Jalal mana" "Eh ina sa ran tare zamuzo dashi, Amma yaushe yazama sirikinki?" "Yacemin yabani kai yazama sirikina, nikuma zan masa tukuici da Jalila dan ita zan bashi shine tukuicin dazan bashi" dariya Jawwad yayi yace "ba ruwana kunfi kusa keda su" Sosai ya manta da batun Naja, yaketa murmushi, Kuruciyar Hanan tana birge shi, yanzu duk wata kunya ya ajiyeta, She's so kind Har Naja ta dawo motar wayarsa yakeyi da Hanan. Naja ta fusata matuka a hargitse tace "wannan wane irin rashin mutunci ne? An samana rana Amma kana waya da wata wannan ai wulakanci ne kuma a gabana" Karaf a kunnen Hanan, Jawwad kashe wayar yayi dan yasan yanzu kome zece Hanan bazata saurareshi ba yanzu, dan taanada matukar kishi, ya kalli Naja yace "Ke zabin Maama ce" wannan kuma zabina ce, dan haka ki kylaeni" "ni kake gayawa haka ko? Wallahi zakaga rashin mutunci, kuma ko bakaso seka Aureni, kacigaba da yimin wulakanci, nikuma zancigaba da hadaka da mahaifiyarka" Bece mata komaiba ya kunna motar yatafi, shi gaba daya hankalinsa da tunanin sa yana kan yaze shawo kan Hanan. Suna zuwa gida yafita ya barwa Naja motar, daya koma daki ya tarar Jalal ya tashi, yazo ya zauna kusada shi yace "Sannu ka tashi kenan?" Jalal ya jinjina masa kai Jawwad yace "Jalal dan Allah sati me zuwa, inaso inje kaduna" murmushi Jalal yayi yace "Zakaje gurin Hanan kenan?" "Eh amma tare zamuje da kai, zaka rakani" "meyasa sena raka ka?" "kaima naka zuwan yanada mahimmanci, dan Allah ka rakani" "to naji, amma senayi shawara" Jawwad yace "ba wata shawara da zakayi, Akwai damuwa ne?" Jalal yace "damuwar menen?" Nan yagayawa Jalal yadda sukayi da Naja, har Hanan taji, Jalal yace "tun farko bekamata ka boye mata halinda ake ciki ba, Amma yanzu ka kira kanwarka ka gayamata, tafara yimata bayani kafin kaje kaduna" Jawwad yace "Hakama za'ayi ka kawo shawara, kai Amma Inajin kunyar Jalila sosai" "meye kuma Abun jin kunyar? Kirata ni zan gaya mata" ba musu ya kira Jalila a waya yace tazo farfajiya yana kiranta. Befi 3 minutes ba sega Jalila tazo, Hannunta dauke da wani karamin teddy da kuma wayarta, bakinta kuma dauke da alawa me tsinke, Jalal kura mata ido yayi aransa yake zancen zuci in be manta ba, saura watanni shida Jalila tacika shekaru gome sha tara Amma har yanzu bata dena halin yarinta, kana kallon ffuskarta zaka san yarinyace, sedai Kwakwalwarta ba kowane babbane ze iya lissafin da kwakwalwarta takeba tasamesu akan fararen kujeru a harabar gidan, tayi mamakin ganin Jalal kaman bashine dazu ya canza gaba dayaba. Taja kujera ta zauna tace "gani Allah yasa ba lefi nayi ba?" Jalal yace "ke tunda kin saba lefi, duk lokacin da aka kiraki bakya kawo komai a ranki se laefi kikayi, kodayake ke ai aikata laifi a jininki yake" Bakinta yayi jawur saboda Alawar datake sha, kallonsa tayi ta harareshi ta dan murguda baki tace "Eh tunda kullum 'yan sanda sesunzo sun tafi daniba, aidole kace laifi a jinina yake" Yadda bakinta yayi jawur din nan tana juyashi ba karamin birge Jalal yayi ba, Jawwad yayi murmushi yace "Allah yabaku hakuri, dazu gwanin sha' awa naji dadin yadda naganku, Amma yanzu kuma zakuyi fada" Jalila cikin shagwaba tace "toba shine yace ina laifi ba" "to kice ba kyayi mana? Shekarun baya ina seda kikasa Abba zuwa kaduna kin tabo 'yar gidan masu bullet" gaba daya sukayi dariya, saboda Jalal da sigar tsokana yayi maganar" gaba daya Jalila mamakin Jalal takeyi, ya iya barkwanci da tsokana, Amma inbaka zauna dashiba bazaka gane hakan ba, kuma abun mamaki lokaci daya seya birkice yakoma Jalal dinsa mashayin giya. Jawwad yace "Baby wani taimako nakeson kiyimin" Ta gyara zama takara rungume teddy tace "with due respect, ina jinka babban yaya" Ya yunkura zeyi magana suka jiyo hayagagar Maama ta nufosu itada Naja, "saboda ka cimin mutunci kake gayawa Naja wai baka sonta kanada wadda kakeso, Jawwad yaushe kakoma haka? Yaushe kafara bijirewa umarnina? Ya koyamaka ko? Zama da Jalal yasa kafara bijiremin, har kake waya da wannan shedaniyar yarinyar a gabanta, na samaka ido tsakanin ku kar mahaifinka yakawo wani abu aransa amma duk baka ganiba ko? " Jawwad yace" Maama nifa bahaka mukayi da itaba, kuma ba ruwan Jalila bada ita nake waya ba, na gayamata ita zabinkice, nima inada zabina" Tas Maama ta dauke shi da mari, gaba daya sukayi tsit dan ba karamin mamaki abun yabasu ba, Shiru Jawwad yayi ya sunkuyar da kai ko tari beyiba, cigaba tayi da zazzga masa masifa Jalila tace "haba Maama, biyayyar da Yaya Jawwad yake miki in baki gode masa ba bekamata ki zageshi ba, kuma da ze canza hali da ya dade da canzawa dan Allah karki kuma dukansa" "rufemin baki kasurgumar munafuka kawai, bake kike zigashi ya bijirewa umarnina ba, jarababbiya wallahi zanyi maganinki, kuma baki isa ki hana Auren nan ba, jarababbiyar banza" "Kuma makira barauniya ba, mara usuli gata barauniya abun kunya itace ke kokarin kusheni wai kar a Aureni, ai garani da dangina uwa da uba, kekuwa fa, dangin uba babu, na uwarma ba wanda yasansu, kodayake ina wani dangi daza'a nuna tunda Arnane" Naja ce take wannan maganar tana jujjuya ido da kebe baki kamar uwatta. Jalila tace "Naja, nina godewa Allah da yadda ajiyeni, da naso rushe Aurenki lokaci daya zan bata komai wallahi, Maama Niba barauniya bace ba, Ilham bata bani kudinki ba, akira Ilham din gani gata tafada miki lokacin data bani, sannan ni bazan ziga Yaya Jawwad ya bijirewa Umarninki ba, Amma kijawa Naja kunne wallahi takuma zagina, sena ambaci uwatta na zageta, nagaji da abunda kukemin Maama menayi miki, kullum ba damar inyi motsi se anciwa uwata mutunci? " A fusace Maama ta daga hannu zata mari Jalila, Jalal da tun dazu beyi magana ba yai sauri ya shiga tsakani ya rike Hannun Maama, ya girgiza kai yace "A'a Maama, Jawwad ma dana san zaki mareshi bazan bari ba, gaskiya Jalila tafadi, uwa batafi uwaba, sannan in baki godewa Jawwad kiyiwa Allah godiya da samun da nagari ba, be kamata ki butulce ba, ya miki biyayya akan abunda bayaso amma baki ganiba, mahaifiyata misali ce a gareki, nikadai ta haifa amma nakasa yimata biyayya, karkiyi kuskuren da Mummy tayi a rayuwarta, kizo kina da nasani, dan Allah" Ina yinku ABDUL JALAL group da sauran masoya wannan Novel irin sosai din nan fa 😍😍😍 inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing, gashi nan na muku dogon page, in banga ruwan comments inna shura takalma na posting se rana ita yau 😂😂😂 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                                  *ABDUL JALAL*        _Story and writing_               By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girls_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                       *P.W.A*✍️                   PART 2                                   _PAGE  3️⃣9️⃣92 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                                          _MY FIRST NOVEL _ Jalal nagama magana yasakarwa Maama hannunta, Jawwad kam mamaki da bacin rai ya hanashi magana, Maama bata taba marinsa ba, lokacin yaji yakara tsanar Naja, juyawa Jawwad yayi ya nufi part dinsa zuciyarsa tana suya, da sauri Jalila tabi bayansa ta bar su Agurin a tsaye, Jalal ma bin bayansu yayi, ita kanta Maama jikinta yayi sanyi da marin da tayiwa Jawwad, yadda taga ya sunkuyar da kai ya tafi bece mata komaiba da kuma maganganun da Jalal yayi, Amma ta maze ta cigaba da banbami. Jawwad na zuwa ya zauna ya dafe kansa yayi shiru yana saka abubuwa daban2 a ransa, da sauri Jalila ta karaso ta zube agabansa tana kuka amma takasa magana se sheshsheka, dagowa Jawwad yayi ya zuba mata ido amma yakasa magana, Jalal ne yakaraso ya tarar dasu a haka, yasamu guri ya zauna a kusada Jawwad, ya kalli Jalila yace "kidena wannan kukan haka, kikoma gida komai ze wuce Insha Allah" Shiru tayi tacigaba da kukan a hankali cikin kuka tafara kokarin furta "Am sorry Yaya Jawwad,...." Maganar ta sarke takasa karasawa, Jawwad yace "Jalila ke yakamata abawa hakuri, tashi kije kidena kuka, nasan abunda kikeji akan yadda akemiki a gidan nan but am really sorry komai ze wuce kinji" gyada masa kai kawai tayi, tace "Yaya Jawwad karka canza lokacin tafiyar nan, kayita tanada mahimmanci" "zanyi Insha Allah" yabata amsa jiki a sanyaye, ta mike zata fita ta juyo ta kalli Jalal tace "Ilham! Ilham.... Sekuma tacigaba da kuka ta fice da sauri ta tafi cikin gidan da yanzu takejinsa kamar prison. Nana batasan me akeba, tana can tana manne da Mahmud a waya, dan haka koda ta fito palour Maama ta tarar tana sababi, ita zuwa yanzu lamarin Maama har tsoro yake bata, kullum cikin fada take, takoma halin 'yar uwatta na masifa ko gajiya batayi, Nana batabi kan maganar da Maama takeba ta wuce kitchen tadora girki. Jalila ta shigo palour, Maama na kokarin shiga dakinta se hararta takeyi tana tsaki, sannan ta shige Naja ma wani tsaki tayi tace "hmm nidake naga wanda ze Nasara, duk wani iyayinki da iya munafurci da kinibibi na kafirai da kuka iya sedai kiyi kigama dan nafi karfinki wallahi kar nake kallonki nafiki iya tashanci, banza 'yar Arna kawai, wadda uwarta ta yasar ta tafi gararinta" idon Jalila yayi jawur dan kuka, cikin matukar bacin rai da masifa Jalila tace "Naji nakuma yadda kinfini iya tashanci, tunda kin tsotsa a Nono mana, nagode Allah har mahaifina ya koma ga mahallicinsa ba'akamashi da 'yar waniba, naki uban fa? Shekararsa biyar a prison da kyar aka karboshi, tashanci gashi nan ke kinayi yayarki da ďan uwanki nayi, sannan kinfini tashanci nikuma nafiki kai da iya wasa da hankali, ki kiyayi ranar dazan miki tonon silili, kuma Aure ne da yardar Allah baza' ayi shiba, saboda nagama shirina akanki, lokaci kadan ya rage kifada tarkona" Nana data fito daga kitchen bata taba jin wannan labarin na mahaifin Su Naja ba, itakuma Naja daskarewa tayi a gurin dan mugun mamakine yakamata, dan ta girmi Jalila kuma tun kafin a haifeta abun yafaru bakowa yasani ba, Amma ita ya akayi tasani. Jalila tuni ta shige daki, ta nufi bandaki ta dauro Alwala tazo ta hau sallaya tafara gabatar da sallar magariba. Jalal yanata rarrashin Jawwad "Jawwad tun asalinka me biyayyane da hakuri ba kamar niba, dan Allah kayi hakuri ka kwantar da hankalinka, kasan iyayenmu mata daukar ziga baya musu wahala, ka kwantar da hankalinka kayi hakuri" Wata irin Ajiyar zuciya Jawwad yayi yace "Jalal Abunda yafaru naji babu dadi, amma abunda yafi batamin rai halinda wannan marainiyar Allah keciki, Jalal hakurin Jalila yakai a yaba mata, duk fitinarta tanada kawaici da hakuri, kuma tanada biyayya, duk abunda Maama take mata bata taba nuna mata bacin ranta ba, akan Jalila nasan Abba ze iya rabuwa da Maama, amma bata taba gayamasa abunda ke faruwa ba, Jalal inajin tausayin yadda rayuwar Jalila ke kasancewa daga wannan se wannan, nasan yau kwana zatayi kuka, kuma Jalal abunda Ilham tayi bata kyauta ba, be kamata tayiwa Jalila hakaba, son zuciya ba halinta bane" "Nasani Jawwad, komai zezo da sauki zan dau mataki akan hakan, kaji ka kwantar da hankalinka" "Shikenan Jalal, ka shirya jibi Insha Allah zamuyi tafiyar nan" "Allah ya kaimu" Jawwad ya amsa masa da Ameen, Jalal ya tashi ya fito, a harabar gidan yaci karo da teddyn Jalila da sweet dinta a kasa, yasa hannu ya dauka teddyn ya tafi dashi. Bayan Jalila ta idar da salla, Nana tace "Jalila dan Allah meya faru kikewa Naja wannan maganar? Abun yabani mamaki ni bantaba jiba fa, kodai fushi ne yasaki"? Jalila idonta Jawur ta kalli Nana tace "Nana duk bacin raina banawa mutum kazafi, kuma bana gori yauma raina ne ya kai makura a baci, sannan ba karya nayiwa mahaifin Naja ba, kuma na fada ne kozan samu sassauci akan bakanta min da ake, kullum aka tashi gori sedai ace uwata Arniya, kawai saboda...... Kasa karasawa tayi, maganar ta sarke saboda kuka "Am really sorry sister, i feel your pain nasan ba dadi abunda yake faruwa dake amma kiyi hakuri dan Allah" Wayar Jalila ce tafara ringing Ahmad ne Amma bazata iya dagawa ba ta kashe wayar. Jalal na zuwa gida ya ajiye teddyn Jalila akan gadonsa ya tafi cikin gida, a palour ya tarar da Mummy amma ya shareta ya nufi dakin Ilham, tana kwance akan gado tana chatting ya fado dakin, zumbur ta mike zaune dan tasan indai taganshi a dakinta toba Arziki, ya kureta da jajayen idonsa yace "Tambayarki zanyi, idan kikamin karya sena shakeki, yaushe kika kaiwa Jalila kudi tabawa Maama?" hade rai tayi "Na kaimata kudi, nace ta ajiyewa Maama inji Mummy" "karya kikeyi" "niba karyanake ba" "zan tattakaki wallahi, karya kike" "wayyo Allah mummy, kizo ki temakeni" ganin tana ihu ya harzuka Jalal jikinsa yafara rawa ya janyota daga kan gadon ya zuba mata mari "Nizaki rainawa hankali? Nizakiyiwa ihu uban me nayi miki?" Mummy kam a sukwane takaraso dakin "lafiya meye haka metamaka?" Banza yayiwa Mummy yace "waike wace irin dabbace ne? Ranar akan idona kike soke kudi a jikinki, naganki da idona amma saboda baki da mutunci kin dorawa yarinya kinsa se kuka take, wace irin zuciya ce dake haka?" Se yanzu Mummy tagane inda ya dosa dan haka tace  "to mara mutunci, dama saboda waccan yarinyar kazo kake wannan zare idon kake kokarin shaketa, kaji kunya wallahi ka fifita wata banza can bare akan 'yar uwarka" "Karki kara dangantani da wannan shedaniyar niba' yar uwata bace ba, tanemi 'yan uwanta can baniba, kuma kicigaba karki fasa, indai wannan yarinyar ce you know what she's capable of doing, ba' a tabata ta hakura, kuma wallahi kika kuma yi mata wani abu makamancin haka sekin bar gidan nan tunda ba gidan ubanki baneba" Mamakine yakama Mummy suka bude baki suna kallonsa gaba daya, A fusace Mummy tace "kai ka kiyayeni, akan waccan banzar yarinyar zaka ci zarafin Ilham, kuma har kake nema ka gayamin bakar magana haka? Jalal kanayiwa kanka hisabi kuwa?" "Karki kara ce mata banza, ga banza nan agabanki" ya nuna Ilham "tayimin abunda ko raina nabata bazan biyata ba, bashida amfani yimiki wani bayani tunda son zuciyarki kawai kikasani, amma lokaci ze bayyana komai" har ya juya ze fita daga dakin idonsa ya sauka akan Alqur'ani nan a saman rio, zuwa yayi yasa hannu ya dauka ya duba tabbas Alqur'anin ne, Amma me yakawo shi hannun Ilham? Be tsaya tambayarta ba yai waje abunsa. Yana fita Ilham ta dora hannu aka tace "Nashiga uku mummy, wannan wace irin masiface? Wace irin kiyayya yaya Jalal yakemin haka?" Mummy tace "kinga dan Allah darene, kidena min ihu, hankalina ya karkata wani gurin, tabbas yaron nan yana sonta, kenan seta juyamin ďa, yadda yake wannan masifa kanta, har yana wannan kumfar bakin akanta ina baze yuwu ba wallahi, ba'a haifi yarinyar dazata juyamin ďa ba, koya fifitata akaina ba" (su Mummy amanta lokacin da ake juya ďan wata🙄) Ilham cikin kuka tace "Wallahi bawani sonta dayake, tana bashi kanta ne kawai, nikuma bazan iyaba shiyasa baya sona se ita dan Allah Mummy kiyi wani abu". "ke rufemin bakini, yanzu ba wannan issue dinne agabana ba" ta juya tabar Ilham da sakakken baki. Koda Abba ya dawo beji motsin yaran nasa ba, dan yasaba yazo yatarar da Nana da Jalila suna kallon ko wani abun a palour, dan haka yake tambayar Maama "wai ina yaran nan ne? Banga kowa a cikinsu ba, Jawwad har ya rufe kofarsa, sukuma 'yan matan banga kowacce ba lafiya dai ko?" Maama tace "lafiya kalau, sun kwanta da wurine kawai" dahaka suka bar zancen. Washegari da safe yakasance Asabar, Jalila tana baccin dole, dan kwanakin naan bata iya bacci, ga matsanancin ciwon kai saboda kuka, wayartace tafara ringing Hanan ce dan haka ta daga, amma da mamakinta taji Hanan tana kuka, nan da nan hantar cikin Jalila ta kada tace "Hanan lafiya kuwa?" Cikin kuka Hanan tace "Jalila dama Haidar Aure zeyi kuka boyemin?kuka kyaleni naketa masa wannan makauniyar soyayyar?" "Haba Hanan, waya gaya miki haka?" "ya zakice waya gayamin? Jiya muna waya da kunnena naji, muna waya dashi wata tana cewa wai ankusa bikinsu yake waya da wata, Jalila am so disappointed, meyasa kukayumin haka?" "Hanan bazaki ganeba, yanzu haka cikin rikici muke dagani har Yaya Jawwad" "Jalila duk rikicin da kuke ciki bekamata kumin haka ba, amma nagode" Jalila na kokarin yimata bayani amma Hanan ta kashe wayar ta, dafe kai Jalila tayi ta marasa dame zataji, Hanan, Jalal, Jawwad kokuma wannan tashin hankalin. Jawwad ya gayawa Abba zeje kaduna, Abba be hanashi ba, ya fuskanci Jawwad baya walwala, amma Abba yabarshi a stress ne na shirye shiryen biki da kuma tunanin rabuwa da gida ze tafi wani gurin aiki. Jalal yakira yagayawa Abdallah cewar zasuzo, Hanan kam tasha kuka, Abdallah yazo mata da labarin Jawwad zezo, amma sam batayi murna ba, Mummy se rarrashinta take, amma kuka kawai takeyi. Daddyn Hanan yasan da zuwansu Jawwad dan haka befita  ba yana gida. Shabiyun rana su Jalal suka iso kaduna garin gwamna, sunsami kyakyawar tarba a gurin iyayen Hanan. Har cikin gida Abdallah ya kaisu Jawwad suka gaida Mummy, Abunda ya daurewa Mummy kai be wuce yanayin abubuwan Jawwad sak Yusuf dake bauchi, boye mamakin ta tayi suka gaisa sosai, har cikin ranta ta yaba da hankalin Jawwad, har ranata takw Addu'ar Allah yasa Jawwad ya auri Hanan. Abdallah yaje dakin Hanan yasameta a daki idon nan jawur ta sha kuka, yace mata "to uwar kishi gashi can yazo, yakamata kije ya ganki tunda danke yazo, amma fa naga shima kaman bashida lafiya ne, naga ya rame sosai" Da sauri ta mike zaune tace "dan Allah bashida lafiya?" "hmm magulamaciya, da kikace haushinsa kikeji, keda a rayuwarki ba kya uzuri, inkin ga dama kicigaba da kukan karkije" ya fice yabar mata dakin, bayansa tabi da harara, tayi zamanta taki tashi, seda Mummy ta biyo sahunta taita mata mita sannan ta mike, jallabiya tasaka baka se mayafinta ta tafi palourn da aka sauki su Jawwad. Kallo daya zakayi mata kasan tasha kuka, tana zuwa tasamu guri ta zauna ta takalli Jalal tace "Yaya Jalal sannu da zuwa ya hanya?" Murmushi Jalal yayi yace "lafiya kalau Hanan, ga Jawwad din na kawomiki" Kallon Jawwad tayi kawai tafara kuka, Jalal yace "Ikon Allah, su mata komai nasu na kukane, hakama Jalila takeyi, mikewa yayi yafita yabasu guri. Jawwad ya tashi daga inda yake yazo gabanta ya zauna ya dan zuba mata ido sannan yace " dama zaki iya fushi dani haka? Haba My i don't expect this from you, Hanan bakiga na rame ba, ina cikin damuwa komai yayi min zafi narasa ya zanyi" nan ya kwashe komai ya gaya mata, gaba daya tausayinsa yakamata tace "Am sorry Haidar kishinka yasani nayi maka haka, dan Allah kayi hakuri, Amma yaya Jawwad bazan iya jure ganin ka Auri wata baniba, Jawwad zan iya hakura ka auri wata ka hadamu amma banda wannan yarinyar" "Meyasa?" "sister dinkace, nibazan fadi komai ba, Amma zancigaba dayi mana Addu'a" Jawwad yaayi ta rarrashinta harta saki jikinta suka fara hira Koda Jalal yafito Abdallah ya janye shi dakinsa suka dinga hira, bayan sunyi Sallar Azahar, suka tafi part din daddyn su Abdallah. Daddy ya karbesu da fara'a ya kalli Jawwad yace "barka da zuwa sirikina ashe kuna tafe" Sunkuyar da kai Jawwad yayi saboda kunya kodan karamcin nan da sukayi masa zenemi alfarmar Abbansa ya barshi ya auri Hanan. Matsana suka zauna a kujerun dake palourn suka gaisa, ya tsaida idonsa akan Jalal ya lura da yadda bayason magana sosai, sedai in anyi abu ya danyi murmushi Daddy yadubi Jalal yace "My son, Kaine Jalal kenan?" Jalal yayi mamaki dan yasan daddyn Hanan besanshiba, amma ya akayi yakama sunansa haka? Jalal ya gyada kai yace "eh nine" Daddy yace "Ai ina ganinka naganeka, ammm nace bakaga tex message da'aka turamaka ba?" Jalal ya dan dirirce yace "Wane message?" Daddy yace "Eh akwai hukuma dasuka turomaka message na daukar aiki mana, zakaje screening" Shiruu Jalal yayi sannan yace "Ammafa daddy nima ina shaye2, tayaya NDLEA zasu daukeni aiki?" Tausayinsa ne yakama Jawwad yace "haba Jalal aiba a haka, ka amince mana, sun san kanayi suka daukeka ai" Daddy yace "ABDUL JALAL don't mind kaji, ai munsan kana shaye2, karka damu you are my son dukda bansanka abaya ba amma yanzu nasamu ďa, dama yaran sunmin kadan, nayi magana da daddynka ma, An riga an baka aikin, ba wani abu ai zaka iya, Jajircewarka akeso sannan kaikuma kayi kokarin denawa, zaka temakawa hukuma, ni yadda naganka din nan with good body structure aida a soja nasaka kaima" Gaba daya sukayi murmushi tunda daddy cikin sigar zolaya ya karasa maganar banda Jalal daya shiga tunani yayi shiru, Daddy yakuma cewa "Am sorry munmaka laifi nida diyata ko? Tasani nasa an soke maka visa, tuba muke bamuyi hakan dan bata maka ba" Murmushi Jalal yayi ya sunkuyar da kai suka cigaba da hira, bayan Azahar suka daura haramar komawa gida, sukayi sallama dasu sannan suka nufo kano, daddyn Hanan duk ya lurada yadda Hanan take nan nan da Jawwad ya yadda ba karamin so takewa Jawwad dinba. Bayan tafiyar su Mummyn Hanan tace "Daddy ka lurada yaron nan Jawwad kamarsa daya da Yusuf, wallahi hatta murmushinsa irin na Yusuf din Baba sagir ne" "Na gani nima, Amma kamnin twins girl dina yafi fitowa, tun lokacin dana ganta nakeji ajikina kaman akwai alaka tsakaninmu, Amma ni yanzu abunda yake raina inason tuntubar mahaifinsu, indai Jawwad yana sonta yafito kawai, tunda naga hankalinta yafi karkata gareshi" Kaman Mummy tayi masa bayanin yakusa Aure, amma tafasa tace "To Allah ya tabattar da alkhairi amma gaskiya ni na yaba da hankalin sa, gashi nutsatse" Tunda suka taho hanya Jalal yayi shiru yakasa magana, Jawwad ya dubeshi yace Jalila sosai take rashin lafiya, bata ko cin Abinci zuciyarta a cunkushe bata sha'awar komai, ga wani matsanancin ciwon kai dayake hanata bacci, ko makaranta bata iya zuwa, Nana tayi2 taje Asibiti tace mata ba wani matsala bane damuwa ce kawai take damunta, Ta yunkura ta mike zata shiga toilet, kawai taji jira gaba daya garin yayi mata baki kirin, aikuwa ta fadi a gurin tana fidda numfashi da kyar, Naja na kan gado tana kallon Jalila tace " ahaka bakinciki da mugun abunki zasu hadu su kasheki, ki barmu a duniyar nida Jawwad muyi Aure, Allah yasa ki mutu shegiya" Jalila tanajin Naja amma bazata iya motsa ko dan yatsanta ba Nana data dawo dauke da kofin tea ganin Jalila a kwance yasa ta jefar cup din tazo kanta da sauri tana girgizata, Jalila tasa hannu ta dafe kanta tace "Nana kaina ze fashe" "Sannu Insha Allah ze dena ina zuwa" Taje ta dakko youghurt a fridge tazo tana bawa Jalila danta fuskanci hada yunwa ke damun Jalila, Naja ta kallesu tayi tsaki "Aikin banza wahalallu" Tunda su Jawwad suka nufo kano, Jawwad yakejin faduwar gaba dan besan meze tarar ba dan shi yanzu ko zuwa gidan baya so, shikam Jalal se sakawa yake yana warwarewa, shi meye amfanin yin wani aiki, Jawwad yaji shirun yayi yawa dan haka yace "ya dai naji kayi shiru haka? Ko har yanzu baka yadda da aikinbe?" Jalal ya danyi tsaki sannan yace "Jawwad nifa kaina yagama daurewa a ina Baban Hanan yasanni da harze bani aiki, kuma yana cewa sungama magana da daddy, yaushe akayi wannan zancen bansaniba? Tayaya zan fara hana wasu sha da fataucin miyagun kwayoyi bayan ni inayi? Ka gayamin tayaya?" "wannan ba abun damuwa bane bafa, kaiba ruwanka da wani tone2 na meyasa aka baka aiki, kuma ai ansan kana shaye2 akabaka ko?" Shiru Jalal yayi baya tunanin ze iya wannan aikin, tayaya za'ace me hana laifi yana aikatawa. Haka suka cigaba da shiru kowannensu yana sakawa yana kwancewa har suka iso kano. Jalila tunda ta danci Abinci tasha magana tasamu nannauyan bacci yayi awon gaba da ita. Koda su Jalal suka dawo, kowa gidansu ya nufa, Jalal ya tafi gida, shima Jawwad ya tafi gidansu. Kwana uku da zuwan su Jawwad kano, tunda suka dawo Jawwad baya shiga gidan saboda gudun fitina sam baya wuni a gidan. Jalal yayiwa teddyn Jalila guri akan gadonsa, yana son yaganta yabata abunta sannan ya tambayeta ya akayi Alqur'ani daya bata yaje hannun Ilham? Har yayi wanka ze kwanta yaji kamar ana hura masa wuta a zuciyarsa da kansa gaba daya jikinsa ya dau zafi a sukwane ya nufi fridge dinsa ya ciki cikinsa da giya sannan yaji daidai. Da safe Jalal yasamu daddynsa a daki yana bacci dayake saukar dare yayi, ba tunanin komai Jalal ya tasheshi, koda daddy ya tashi Jalal yafara jeramasa tambayoyi "daddy da saninka aka samomin aiki a hukumar sha da hana fataucin miyagun kwayoyi?" daddy yace "Dafarko dai ban saniba sedaga baya, General Abdurrashed ya kirani a waya, yacemin 'yarsa tanemi ya sama maka aiki a wannan hukumar inbazan damuba in turamasa CV dinka, shikenan na amince" Jalal yayi saroro yana kallon Daddynsa "Wace' yar tasa?" "kai zan tambaya ai" Shiru Jalal yayi, kawai ya mike ya sakko daga kan gadon daddy yafice daga dakin. Jawwad yana dakinsa, Nana tazo tace masa Abba yana kiransa, haka ya tashi gabansa na faduwa, yana fatan Allah yasa ba wani laifin yayi ba, yana zuwa, ya tarar da 'yan gidan a palour banda Naja, Abba yayi shirin fita, Abba yace masa "Jeka ka canza kaya, Bauchi zamuje yanzun nan" Cikin mamaki Jawwad yace "Bauchi kuma Abba?" "Eh bauchi mana, kayi sauri a yau nakeson mudawo" Cikin Mamaki Maama tace "Abban Jawwad ni nakasa gane meke faruwa haka, tun jiya kake bacin rai, kaki saurarata yaukuma ba zato ba tsammani kace bauchi zaka tafi, mezakiyi a bauchi ne?" Kallon ta ya danyi yace "ba dole inki saurararki ba, ki shirya munyi magana da baban Jalal, ranar Lahadi shida 'yan uwansa zasu kawo kudin Auren mahmud da Nana, sannan zanje bauchi inne mawa ďana Auren' yar mutunci, sannan karki kuskura in dawo in tarar da yarinyar nan Naja a gidan nan, tabarmin gidana a yau" "Amma meyasa?" "in mun dawo kyaji meyasa" Jalila dake gefe tace "Abba Allah ya kaiku lafiya, ka gaishemin dasu, kuma akwai wani albishir dana boye banyimaka ba sekaje bauchi zaka gani" Abba yayi murmushi yace "to shikenan Baby, kema inason kafin lokacin bikin Nana ki fidda miji ku karasa karatun a dakinku" Jalila ta sunkuyar da kai tana murmushi,  Abba kuma yasa kai yabar palourn. Mummy tana zaune suna hira daddy a babban palour Jalal yashiga da sallama, suka amsa masa gaba daya, yaje kan Mummy ya tsaya fuskarnan babu alamar walwala ya jefa mata wata jarida a hannunsa yace "ga shi nan yanada kyau ki duba Labari na uku a cikin wannan jaridar, yanada mahimmanci agareki" Ina yinku ABDUL JALAL group da sauran masoya wannan Novel irin sosai din nan fa 😍😍😍 inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing, gashi nan na muku dogon page, in banga ruwan comments inna shura takalma na posting se rana ita yau 😂😂😂 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680.     🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                                  *ABDUL JALAL*        _Story and writing_               By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girls_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                       *P.W.A*✍️                   PART 2                                   _PAGE  4️⃣0️⃣93 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                                          _MY FIRST NOVEL _ Tsayawa Mummy tayi tana kallonsa, yace "ki dauka kiduba mana, kika tsaya kina kallona, ganin da yayi Mummy bata da niyyar taba jaridar yasashi yasa hannu ya bude ya ajiye mata a gabanta, Hoton Kabir ne da Jeje da wasu mutane da bindigogi agabansu, tittle din ta karanta, da hanzari jikinta na rawa ta dau jaridar tafara dubawa, an yankewa Kabir zaman gidan yari na shekaru goma sha biyar sakamakon saida makamai da fataucin miyagun kwayoyi, sannan an yanke masa shekaru Ashirin a prison saboda Yunkurin kisan kai, da kuma shekaru goma sha hudu sakamakon lalata da kanan yara mata. Sekuma su Jeje da'aka yankewa hukuncin shekaru ashirin2 a gidan prison. Daddy ne yasa hannu ya karbi Jaridar shima ya duba, Jalal yace "Mummy Allah yakawo karshen mutumin da dasa hannunsa a lalacewata, shiyabada kwangilar koyamin shaye2 saboda ya huce takaicin abunda kikayi masa akaina, kalli keda laifi nida karbar hukunci" Daddy yace "Jalal kai waya gayamaka shiya bada kwangilar hakan?" "ba gayamin akai ba, Jeje abokina yaronsa ne, idan nagaya muku wanda yayi sanadiyar kama Jeje da uban gidansa har nasan wannan lamarin kila karyatani zakuyi, sanin hakan bashida Amfani, Mummy yakamata ki zubar da makamanki kikoma ga Allah tun kafin kema ya dankeki, Kabir makiyinane na boye bansan dashiba sedaga baya, nasan makiyana na fili, suma ina nan nasasu a Addu'a very soon Allah ze yimin maganinsu" Yasa hannu ya dauke Jaridar ya fice. Daddy yaja ajiyar zuciya yace "Khadija lokuta da dama bana ganin laifin yaron nan, ba wai ina goya nasa bayane ba, amma kinmasa laifuka masu tarin yawa, ba kya duba haka se wanda yakemiki, anyway Ansamosa aikinyi na gwamnati wanda muke saka ran ze dauke masa hankali daga kan shaye2" Kallon Daddy tayi tace "bangane ansamosa aiki ba, wani irin Aiki? Me Jalal yanema yarasa da zeyi wani aiki, ina kamfaninsa na sarrafa robobi meyasa bazaka bashi abunsa ya rike ba?" "ba an samomasa aiki ne dan wani abuba, ansamo masa ne dan hakan zesa yayi kokarin dena shaye2, kuma bazan iya cewa wanda yasamo masa din A'a ba, kuma nima naga dacewar hakan" "wai waye ya samo masa?" ta tambaya cikin kosawa "General Abdurasheed ne" Dan zare ido tayi tace "Ina yasanshi daze bashi aiki, sannan wani irin aikine haka? Dan dana baze aikin soja ba" "Eh ya gayamin Jalila ce tace tanason yasama masa aiki a NDLEA, hakan ze temaka masa wajen dena shaye2" Hade rai tayi sosai tace "Baze yuwu ba, baza'a mayar minda ďa bawa ba, Akan mene? Meye hadinta dashi dazata sa a samo masa aiki, banda cin mutunci tasan yana shaye2 shine zatace yayi aiki a hukumar yaki da shaye2 salon tasaka akama shi, kokuma taji dadin juya shi yadda takeso ko? Dama yanzu na fuskanci maganarta yakeji akanta ba irin wulakancin daba yawa Ilham, to bata isaba da raina babu yarinyar dazata juyamin ďa, baze yuwu in haifi ďa wata ta juyamin shiba" Mikewa daddy yayi tareda yin murmushi yace "Eyya kin makara khadija, duk abunda kayi se an maka, ki gode Allah da yarinyar ba cutar dashi take ba, dan ta damu da halin dayake cikine hartasa a sama masa aiki, nayi farinciki da hakan, kuma batun kice baza'a juya miki ďa ba daga baya kenan aikin gama ya gama" be jira yaji martanin da zatayi ba ya shige bedroom ya kulle kofarsa. Jawwad ko sallama basuyi da Jalal ba suka tafi bauchi shida Abba. Maama kam a sukwane take tambayar Jalila "me Abba ke nufi, me kika gaya masa haka? Sannan wa zeje nemawa Aure? "niba abunda nagaya masa, yaushe rabon da in zauna dashi balle ince masa wani abu, nibansan waze nemawa aure ba be gayamin ba" A fusace Maama takoma dakinta tana tunanin yazata bullowa lamuran. Jalila takoma daki suka dinga murna itada Nana, Jalila tace "Nana ban taba zaton Abba ze yadda da abunda nagaya masa ba" Dan bata rai Nana tayi tace "Jalila nayi mamakin abunda ya fusata Abba haka, har yayi fushi yake ikrarin abar masa gida, nayi mamaki sosai be taba hakaba fa" "to yanayi na rayuwane Nana, tunda kikaga haka akwai abunda ya bata masa raine, sannan akwai dalilin dayasa yayi haka" Nana ta dan numfasa tace "Jalila nifa damuwata naji Abba yana batun akawo kudin Aurena, Allah yasa ba dana Yaya Jawwad za'a hadamin ba, nan da wata hudu da 'yan kaifa kenan" Nana takarasa maganar kaman zatayi kuka Jalila tace "to meye aciki? Keda rabin rankine fa Mahmud zaku kasance inuwa daya" "To Jalila karatun fa? Kinsan Mahmud a kasar waje yake nasa karatun tayaya abun ze yuwu?" "ze yuwu mana, kicigaba da naki karatun a can riba biyu, Allah sarki Rayuwa hajiya Nana za'a zama matan Aure, bari in lissafa yaushe zaki haihu" Hade rai Nana tayi "Ke Jalila komai sekin sako wasa a cikine? Inamiki maganar serious kinamin wasa, ke yanzu akace za'ayi aurenki nan da watanni hudu kin shiryane? Ni yanzu ma meyasa Abba bece a hada dake ba" Dariya Jalila tayi tace "gidan Ahmad yana bauchi, shi yana aiki a maiduguri, ni ina karatu a kano tayaya kike zaton inyi Aure yanzu, se nagama tukuna" Wayar Jalila tafara ringing, ta kalli Nana tace "Excuse me, let me pick the call" Nana ta daga mata kai, Jalila ta amsa wayar tareda yin sallama Amsamata yayi sannan ya dora da "Babyna kwana biyu kin gujeni you are not picking my calls, ina fatan ba laifi nayi miki ba?" Cikin siriyar muryarta na shagwaba tace "Ohh no ni bakamin laifi ba, bana dan jin dadine kawai, amma yanzu Alhamdilillah naji sauki" "Ya salam amma baki gayamin ba, yau zan shigo kano dama shiyasa na kiraki, in kin amince zanzo in ganki" "Babu damuwa my one, ina fatan in ganka nima am missing you" "Like serious, karkisa inyi Ihu attention din mutane ya dawo kaina" Murmushi tayi tace "ba sekayi ihuba, aini yakamata inyi, kwana nawa zakayi a kano?" "zanyi sati daya Insha Allah, zanyi wani assignment ne" "Shikenan Allah yakawo ka lafiya" "Ameen my queen, bazaki tambayi Antynki ba?" Dan yamutsa fuska Jalila tayi tace "Ainasan tana lafiya tunda najika haka" Murmushi yayi yace "Queen da alama kinada kishi sosai, anyway sena shigo, idan nazo da wuri zaki ganni yau, in ban shigo da wuri ba se Allah ya kaimu gobe" "to shikenan Allah ya kaimu, take a good care of your self" "Ok Baby i will Insha Allah" ta katse wayar, Nana ta zuba mata ido tana kallonta, Jalila tace "Madam lafiya kuwa?" "Lafiya mana, nina kasa gane inda kika dosane, gane lamarinki se Allah mutum baya taba ganeki, gaba daya rayuwarki zigza ce" Sosai Nana tabawa Jalila dariya tace "rayuwartawa ce zigza, lallai ma Nana bakida dama, Rayuwata normal ce kaman ta kowa" "A'a ban yadda ba, Allah yasa ayi miki aure kafin ayiwa Yaya Jawwad" "Ba Ameen ba, back to sender muguwa kawai" "eh amma ni kikayimin fata saboda son kai" Wayar Jalila ce takuma daukar ruri, ta kai hannu ta dauka tana dubawa taga Hanan ce dan haka ta kashe wayarta. Tunda suka fara tafiya Abba beyiwa Jawwad wani gamshashen bayani akan wannan tafiyar ta bazata ba, yanason yayiwa Abba magana amma yakasa duk sunyi shiri Jawwad na driving, "Dama Aliyu akwai wadda kakeso kaki ka gayamin kabari ake kokarin auramaka wannan yarinyar?" Tambayar tazowa Jawwad a bazata, kuma idan yaji Abba ya ambaci sunansa na gaskiya kai tsaye haka, alama ce ta  he is so much serious. Jawwad ya dan sosa keya yayi shiru "yaka sosa kai kayi shiru? Kamin bayani mana" Cikin kame2 Jawwad yace"Amm.. Dama Abba, ai..." Abba yacce " Jawwad da farko sister dinka Jalila tagayamin inyi bincike akan yarinyar nan Naja, tacigaba da gayamin hakan, sannan taki gayamin komai game da Naja, sedai cewa inyi bincike, tacigaba da nunamin cewa kunyarka da kawaicinka baze bari ka nuna abunda ke ranka ba, na dauki maganarta serious nafara kokarin bincike, ina kan binciken ne, Mahaifin Hanan ya kirani yamin magana akan in dai dagaske kana son 'yarsa yabaka dama ka fito, wanda ni bansan da zancen ba, nayi kokarin in zauna da kai muyi maganar kafin ta kai ga haka Jalal yazo ya sameni har gurin aiki yamin bayani akan alakarka da' yar gidan general Abdurrasheed, sannan ya daukeni ya kaini inda aka gayamin komai akan Naja, bantaba tunanin Mamanka zata zaba maka mace irin wannan mara kamun kai a matsayin mata ba, Jawwad meyasa baka gayamin abunda ke ranka ba, kabari nakusa gangancin saka rayuwar ka a hatsari? " "Abba nasam bazaka zabamin abunda ze cutar dani bane, banason bijirewa umarninka dana Maama, shiyasa na amince" "Nasan da wannan Jawwad, amma dukda haka a matsayin mu na iyaye yanada kyau mudinga baku zabi, ba wai bin son zuciyarmu da tirsasamuku akan abunda bakwa ra'ayiba, yana da kyau kadinga faďan ra'ayinka ba laifi bane naji dadin kokarin yimana biyayya dakayi, Allah yayi maka Albarka yakara haďamin kanku, Allah ya shirya mana ABDUL JALAL dukda kasancewar halinsa amma yadamu da lamuranka sosai, yadda yazo ya sameni kaman zeyi kuka, Alhamdilillah nayi mamaki naga abubuwan sa sun fara raguwa, yafara dawowa hanya, ya rage rashin ji" "hakane ya rage sosai makuwa, abokiyar fadansa keta kokarin sashi a hanya ai" "Wa kenan?" Abba ya tambaya "Jalila mana, tanata kokari akansa, kuma naga inga masa nasiha koba duka ba yana ďan dauka" Abba yace "masha Allah, at least kaga an samu improvement, itama General Abdurrashed yamin magana, yace akwai abokin ďansa dayake sonta, wai Ahmad sunansa kowaye?, yabiyo ta hannunsa a nema masa Aurenta, amma nace na bashi wuka da nama shima babanta ne, duk abunda yaga dace yayi" Jawwad yai murmushi yace "hakane Abba, lokacin da mukaje kaduna yamin zancen nima, yace shima mutumin sojane yana da kirki sosai" "Hakane, Allah ya tabbatar mana da alkhairi yamuku zabi da abokan zama nagari" Jawwad a zuciyarsa yace Ameen. Hanan taita kiran wayar Jalila amma Jalila taki dagawa, saboda bataji dadin abunda Hanan tayi mata ba, sako Hanan ta turimata kamar haka     "Assalamu Alaikum, Am very sorry my twiny, nasan na miki laifi kiyi hakuri dan Allah, Yaya Jawwad yazo kano shida Jalal, yamin bayanin komai abunda ke faruwa, kiyi hakuri so dakuma kishinsane yasa namiki haka, sannan naji Yaya Abdallah yana maganar Ansamawa Jalal aiki za'a gama interview ranar laraba amma har yanzu bejeba, you have to take action" Jalila nagama karantawa ta kira Hanan, seda Jalila ta kira sau biyu sannan Hanan ta dauka tace "'yar rainin hankali inata kiranki kinki ďagawa, amma da kikaji batun ABDUL JALAL harkin kirani" Jalila ta hade rai kaman Hanan na ganinta tace "ke banason wulakanci, ai banji dadin abunda kikayimim ba sam wallahi" "Nasani amma ai nace kiyi hakuri, you won't understand how far my loves go on your brother, inasonshi ina kishinsa shiyasa na shiga damuwa, inata addu'a dai amma ina cikin damuwa Queen" Tausayin Hanan yakama Jalila tace "ki kwantar da hankalinki kinji my twiny, komai ze wuce kece zaki zama matar Yaya, ina nan ina tayaku da Addu'a" "Masha Allah, Allah yabiya ki da mafificin Alkhairi Jalila, bazan iya biyan kaunar da kike nunamin ba" "bakomai Sister na, nace are you serious Jalal beje interview din nan ba?" "Wallahi dagaske nake miki, hala aikinma kekisa aka samo masa?" "to meye naki aciki nason kisani, nice nagayawa Daddy ya samo masa, kuma be isa ya watsamin kasa a ido ba zan sameshi, seyaje interview din nan" Dariya Hanan tayi tace "wai zaki sameshi irin Mum din nan tasa, kai lamarinku din nan yana birgeni wallahi, kowa da guntun taurin kansa dan Allah duk yadda kukayi ki gayamin dan wallahi.... Katse wayarta Jalila tayi jin Hanan zata fara mata bare2. Ilham shiryawa tayi takanas ta tafi gidansu, domin taji abunda yakamata suyi, dan ita ta riga ta karaya da lamarin nan bata tunanin akwai nasara dan kullum Jalal kara bauďewa yake, babu alamar ze sakko. Tayi sa'a ummannata tana gida, suka kule a daki kaman yadda suka saba in Ilham ďin tazo. "Umma nifa najiki shiru ya'ake cikine? Na ďora mata sata amma Jalal bakiga rashin mutuncin dayayi min ba, wallahi son yarinyar nan yake, kincemin zakije Nijar gurin wani malamin amma shiru kullum abubuwan kara tabarbarewa sukeyi" Umma tace "ke nayi maganar zuwa nijar, munyi waya da mutumin na masa bayanin komai, amma budar bakinsa wai yayi bincike akan yarinyar indai inason a yimin aiki akanta zan bashi dubu ďari biyar, nikuma ina naganta? Banida ita bani da wata kadara da zan sayar in bashi wannan uban kuďin, dan haka nakoma gurin wanda muke zuwa tun farko, shikuma yacemin baze iya aiki akanta ba sedai a kara watsa rayuwar Jalal" "to Umma batun Auren namu fa?" "shima za'ayi ne amma yace muďan kara hakuri" "umma kenan, mu kara hakuri fa kikace? By mistake idan Asirin ya karye gaba ďaya kuma yaya zamuyi?" "bazeyiba, malamin yabani wannan tabbacin ki kwantar da hankalinki burinmu seya cika, sena wulakanta shi shida uwarsa hada uban nasa, bana yafiya ga wanda yamin laifi" "to shikenan Umma, Allah yasa, ni bari in tafi, zan ďan tsaya inyi siyayya". Dogon wandone a jikin Jalila da riga, dan haka ta ďakko katon hijjabinta me hannu tasaka ta fito part ďin Jawwad taje tana tsammanin ganin Jalal a can amma baya nan, rabonta da shiga gidansu Jalal kuwa harta manta, direct ta nufi gidansu Jalal, amma tarasa ina zatayi tasan dai be dace ta tafi part dinsa nemansa ba, fasawa tayi ta juyo tanufo gate zata fita itakuma Ilham ta shigo. Tsayawa sukayi suna kallon kallo itada Ilham, haďe rai sosai Ilham tayi tareda yin tsaki tazo zata gifta gefen Jalila ta wuce, caraf Jalila tasa hannu ta riketa ta janyota gabanta suna fuskantar juna, a fusace Ilham tace "ke dalla malama meye haka? Meyasa bakida tunani ne?" Jalila taja wasu seconds tana karewa kwayar idon Ilham kallo sannan tace "banida tunani kam, dole ki fadi haka, kinsan ba'a tabani a zauna lafiya, dan haka sekinyi hakuri da duk abunda zaki gani har se kin biya abunda kikayimin" Hararta Ilham tayi takuma kokarin rabawa ta wuce ta barta, amma Jalila takuma shan gabanta tace "Ilham nasani tsawon shekaru ina bata miki rai, kinyi alwashi daban2 akan ganin bayana, baki taba nasara ba se wannan karon da kika ďora min sata, to bari kiji in gayamiki wani abu dabaki saniba, babu abunda zakiyi a rayuwa ki rama abunda nayi miki, na riga nagama dake Ilham, kuma Wallahi Jalal baze taba aurenki ba, nagaya miki dama muddin kudirina yayi karo da naki sena watsa naki, kudirinki akansa yaci karo da nawa na watsa shirinki watsawa ta har gaban abada zanso ingaya miki wani abu daya kamata ki sani amma ban saniba ko kinason ji" Kallonta kawai Ilham take batareda tayi magana ba, Jalila ta ďora tace "Ranar da Jalal ya kwanta a Asibiti, kukazo duba shi keda Mahaifiyarki kisani idonsa biyu yaji duk abunda kuke faďa, dan haka ki cirewa ranki cewar burinki ze cika, Na riga naganoki Ilham tuntuni shiyasa nayi miki illa inda ba wanda ze gani, na illata shirinki bakida wata dama data miki saura, damarki ďaya shine ki jajirce kicigaba da jarraba sa'arki kozaku daidaita" Jalila takarasa maganar tana mata wani mugun kallo sannan ta juya tayi ficewarta, gaban Ilham ne ya shiga dukan hamsin2, kaddai Jalila dagaske take, amma to in hakane da yaji aida yaďauki mataki, "kai karyane bejiba, koma yaji wallahi seya Aureni, se burin mahaifiyata yacika" Ta shige cikin gida da sauri hada tuntube. Maama takasa zaune takasa tsaye, Naja batasan budurin da'akeba dan lokacin da Abba yayi wannan maganar bata nan tafita yawonta, harta dawo Maama tarasa ta inda zata fara mata bayani. Jalila na fitowa taga Jalal ya dawo a mota, yana kokarin shiga gida, ganin da yayi ta tsaya ta ki tafiya ta kura masa ido yasan akwai magana a bakinta, tsayawa yayi agaban ta yayi parking, yana tsayawa ta zagaya inda yake, ďan ďage mata gira yayi alamar meke faruwa? Ďan kallonsa tayi tace "daga ina?" "kin aikenine?" ya tambayeta "Ohh No Allah yabaka hakuri" Yace "Ina Jawwad ne? Na duba baya nan ban san inda ya tafiba?" hade rai tayi itama tace "ka duba shi mana, kokabani ajiyarsa ne?" Kallonta yayi, wato ta rama kenan Yace "A'a ban baki ajiyarsa ba" "dama.." sekuma tayi shiru "Dama me?" "inada magana ne" "fadi ina jinki" "toka fito daga motar mana" "In fito kuma? Gaskiya ni yunwa nakeji, zuwa zanyi in kwanta, naje neman Abinci narasa me zanci, dama in kin bawa Jawwad nake ci nima amma yanzu baya nan nasan bazan samuba" "Hmm to kace Ilham tabaka mana" Hade rai yayi sosai yana Kallonta, sunkuyar da kai tayi tana dariya kasa2 "Yi hakuri, ai yanzu mundena faďa ka jirani a part din Yaya Jawwad zan kankaro maka kanzo in za kaci" tayi maganar tana dariya, tana matukar kyau idan tayi dariya, gyaďa kai yayi ta juya ta tafi, yabi bayanta da kallo harta shige gida, sannan yaja motar ya shiga da ita gida. Gida takoma taje ta ďakko masa breakfast ďin Jawwad da yatafi beci ba, dayake da zafinsa a cikin flask, tana zuwa ta tarar dashi a zaune a palourn Jawwad yana jiranta, ta shiga tayi sallama amma be amsaba, seda tazo kansa ta tsaya takuma yimasa sallama ya ďago ya kalleta ya amsa a hankali, ta ajiye tray din tace "Yana daga hakkin musulmi akan musulmi in yayi sallama ka amsa masa, kadinga amsa sallama please" Shiru yayi yaki kulata, Jalila tarasa wane irin miskilin mutum ne Jalal, koma tace ďan rainin hankali kana masa magana yana jinka amma yayi maka banza dan tsabar wulakanci, ta aje masa Abincin ta zauna a kujerar dake kallonsa. Ta danne fushinta Ya hada Abincinsa yafara ci, can yace "Me ya kai Alqur'ani dana baki hannun Ilham?" yai tambayar kamar bashi yayi ba "ďauka tayi" tabashi amsa a takaice "Ya'akayi ta ďauka baki hanata ba?" "Ina bauchi aka aikota taganshi shine ta ďauka" Bekuma cewa komai ba yacigaba ds auna loma, can Jalila tace "Ya akai kasan yana gurin ta?" Kallonta yayi ya danyi murmushi "in kinaso in dawo miki dashi, yana gurina, amma bakiga abunda na ajiye a cikiba ko?" ďan yatsina fuska tayi sannan tace "Nifa tsawon lokacin da yayi a gurina banga komai a ciki ba" "zan dawo miki dashi kikuma dubawa" "to naji zan duba" Ya cigaba da cin Abincin sa, can ta ďan nisa tace "An baka aiki ance kaje interview kaki why?" Ďagowa yayi ya kalleta, "dama nayi tunanin kece kikasa aka nemamin wannan aikin, tayaya ina shaye2 zakice asamomin aiki a hukumar dake yaki da shaye2, amfanin me zanyi ko nima so kike a kamani?" "calm down let me explain, mezesa in so akamaka? da hakane naso akamaka da nasa an ka maka kaida abokinnaka jeje ai" ďagowa yayi ya haďe rai kaman be taba dariya ba "Am sorry banyi hakan da wata manufa ba, sedai inkana aikin na farko ze rage maka yawan damuwa, sannan ze sa ka kara kokarin kadena shaye2 kaima, at least in kana da gurin zuwa ze kara dauke hankalin ka daga kan Shaye2" Zuba mata ido yayi yana tunani daban2 akanta, ta damu dashi dayawa, she's so simple and calm, matsalarta kawai taurin kai da rashin kunya, Amma tanada zuciya me kyau. Tsarguwa tafara yi da kallon dayake mata tace "Ya dai?" "meyasa kika damu dani haka?" Shiru tayi dan bata san mezatace masa ba, basarwa tayi tace "dan Allah kaje interview din nan karka watsamin kasa a ido" "Senayi shawara" yabata amsa "shawara kuma, dan Allah mene kuma na wani shawara dan Allah Yaya Jalal kaje please karkasa inji kunya" da shagwaba takarasa maganar Bude baki yayi tareda yin murmushi kaman karta dena magana "Nine Yaya kuma yau, yarinyar bakida kunya fa" "Aida ďinma dan muna fada ne amma yanzu mundena faďa, dan Allah kaje ba dan halina ba, kaji Yayana ďan gidan daddy abokin Yaya Jawwad, badan halina ba" murmushi yayi ya ďan girgiza kai yace "Aikuwa kinsan indan halinkine bazaniba, innayi tunani zan gaya miki" "to Allah yasa inji alkhairi" Be amsaba ya kai hannu ya dauki cup ya kai bakinsa amma jikinsa yafara rawa yakasa kaiwa "lafiya menene kuma?" Ajiye cup din yayi, yai shiru yana rintse ido" Da sauri ta mike ta nufi inda yake tana faďin "Subhanallah meyafaru?" Dagowa yayi idonsa yayi jawur yace "Gi.. Giy..... Giya,.... Giya zansha, ita nakeson sha" "giya kuma? Meyasa zaka sha giya?" Numfashi yake ja ya mike tsaye ya nufi hanyar fita, idonsa yayi jawur jikinsa se rawa yakeyi da sauri ta sha gabansa "dan Allah Jalal karka sha giya, meyasa idan kuma kasha ka bugu daga nan ka mutu mezaka cewa Allah? Dan Allah karka sha kayi hakuri zaka ji bakason sha" Tureta yayi ze fita, takuma tare kofa tana masa magiya, yasa hannu ya hankadata jikin kofa ta bige kafaďa ta faďi a gurin shikuma ya fice kaman wani horrorn dayake bukatar jini. Godiya mara iyaka ga members na kungiyar mu me tarin Albarka Perfect writers association, Allah yakara haďa kanmu. Abdul Jalal Novel Fans❤️🌹 kaunarku a ruhina take, inajin dadin comments dinku hada wakokin da'ake reramin😂😂😂 Masu bina private suna min comment kokuma bani karfin gwiwa, da masu biyoni suna neman littafina da masu karantawa wanda bansansu ba ina godiya Allah yasaka da alkhairi Allah yabar kauna. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680.         🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                                  *ABDUL JALAL*        _Story and writing_               By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girls_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/                       *P.W.A*✍️                   PART 2                                   _PAGE  4️⃣0️⃣93 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                                          _MY FIRST NOVEL _ Tsayawa Mummy tayi tana kallonsa, yace "ki dauka kiduba mana, kika tsaya kina kallona, ganin da yayi Mummy bata da niyyar taba jaridar yasashi yasa hannu ya bude ya ajiye mata a gabanta, Hoton Kabir ne da Jeje da wasu mutane da bindigogi agabansu, tittle din ta karanta, da hanzari jikinta na rawa ta dau jaridar tafara dubawa, an yankewa Kabir zaman gidan yari na shekaru goma sha biyar sakamakon saida makamai da fataucin miyagun kwayoyi, sannan an yanke masa shekaru Ashirin a prison saboda Yunkurin kisan kai, da kuma shekaru goma sha hudu sakamakon lalata da kanan yara mata. Sekuma su Jeje da'aka yankewa hukuncin shekaru ashirin2 a gidan prison. Daddy ne yasa hannu ya karbi Jaridar shima ya duba, Jalal yace "Mummy Allah yakawo karshen mutumin da dasa hannunsa a lalacewata, shiyabada kwangilar koyamin shaye2 saboda ya huce takaicin abunda kikayi masa akaina, kalli keda laifi nida karbar hukunci" Daddy yace "Jalal kai waya gayamaka shiya bada kwangilar hakan?" "ba gayamin akai ba, Jeje abokina yaronsa ne, idan nagaya muku wanda yayi sanadiyar kama Jeje da uban gidansa har nasan wannan lamarin kila karyatani zakuyi, sanin hakan bashida Amfani, Mummy yakamata ki zubar da makamanki kikoma ga Allah tun kafin kema ya dankeki, Kabir makiyinane na boye bansan dashiba sedaga baya, nasan makiyana na fili, suma ina nan nasasu a Addu'a very soon Allah ze yimin maganinsu" Yasa hannu ya dauke Jaridar ya fice. Daddy yaja ajiyar zuciya yace "Khadija lokuta da dama bana ganin laifin yaron nan, ba wai ina goya nasa bayane ba, amma kinmasa laifuka masu tarin yawa, ba kya duba haka se wanda yakemiki, anyway Ansamosa aikinyi na gwamnati wanda muke saka ran ze dauke masa hankali daga kan shaye2" Kallon Daddy tayi tace "bangane ansamosa aiki ba, wani irin Aiki? Me Jalal yanema yarasa da zeyi wani aiki, ina kamfaninsa na sarrafa robobi meyasa bazaka bashi abunsa ya rike ba?" "ba an samomasa aiki ne dan wani abuba, ansamo masa ne dan hakan zesa yayi kokarin dena shaye2, kuma bazan iya cewa wanda yasamo masa din A'a ba, kuma nima naga dacewar hakan" "wai waye ya samo masa?" ta tambaya cikin kosawa "General Abdurasheed ne" Dan zare ido tayi tace "Ina yasanshi daze bashi aiki, sannan wani irin aikine haka? Dan dana baze aikin soja ba" "Eh ya gayamin Jalila ce tace tanason yasama masa aiki a NDLEA, hakan ze temaka masa wajen dena shaye2" Hade rai tayi sosai tace "Baze yuwu ba, baza'a mayar minda ďa bawa ba, Akan mene? Meye hadinta dashi dazata sa a samo masa aiki, banda cin mutunci tasan yana shaye2 shine zatace yayi aiki a hukumar yaki da shaye2 salon tasaka akama shi, kokuma taji dadin juya shi yadda takeso ko? Dama yanzu na fuskanci maganarta yakeji akanta ba irin wulakancin daba yawa Ilham, to bata isaba da raina babu yarinyar dazata juyamin ďa, baze yuwu in haifi ďa wata ta juyamin shiba" Mikewa daddy yayi tareda yin murmushi yace "Eyya kin makara khadija, duk abunda kayi se an maka, ki gode Allah da yarinyar ba cutar dashi take ba, dan ta damu da halin dayake cikine hartasa a sama masa aiki, nayi farinciki da hakan, kuma batun kice baza'a juya miki ďa ba daga baya kenan aikin gama ya gama" be jira yaji martanin da zatayi ba ya shige bedroom ya kulle kofarsa. Jawwad ko sallama basuyi da Jalal ba suka tafi bauchi shida Abba. Maama kam a sukwane take tambayar Jalila "me Abba ke nufi, me kika gaya masa haka? Sannan wa zeje nemawa Aure? "niba abunda nagaya masa, yaushe rabon da in zauna dashi balle ince masa wani abu, nibansan waze nemawa aure ba be gayamin ba" A fusace Maama takoma dakinta tana tunanin yazata bullowa lamuran. Jalila takoma daki suka dinga murna itada Nana, Jalila tace "Nana ban taba zaton Abba ze yadda da abunda nagaya masa ba" Dan bata rai Nana tayi tace "Jalila nayi mamakin abunda ya fusata Abba haka, har yayi fushi yake ikrarin abar masa gida, nayi mamaki sosai be taba hakaba fa" "to yanayi na rayuwane Nana, tunda kikaga haka akwai abunda ya bata masa raine, sannan akwai dalilin dayasa yayi haka" Nana ta dan numfasa tace "Jalila nifa damuwata naji Abba yana batun akawo kudin Aurena, Allah yasa ba dana Yaya Jawwad za'a hadamin ba, nan da wata hudu da 'yan kaifa kenan" Nana takarasa maganar kaman zatayi kuka Jalila tace "to meye aciki? Keda rabin rankine fa Mahmud zaku kasance inuwa daya" "To Jalila karatun fa? Kinsan Mahmud a kasar waje yake nasa karatun tayaya abun ze yuwu?" "ze yuwu mana, kicigaba da naki karatun a can riba biyu, Allah sarki Rayuwa hajiya Nana za'a zama matan Aure, bari in lissafa yaushe zaki haihu" Hade rai Nana tayi "Ke Jalila komai sekin sako wasa a cikine? Inamiki maganar serious kinamin wasa, ke yanzu akace za'ayi aurenki nan da watanni hudu kin shiryane? Ni yanzu ma meyasa Abba bece a hada dake ba" Dariya Jalila tayi tace "gidan Ahmad yana bauchi, shi yana aiki a maiduguri, ni ina karatu a kano tayaya kike zaton inyi Aure yanzu, se nagama tukuna" Wayar Jalila tafara ringing, ta kalli Nana tace "Excuse me, let me pick the call" Nana ta daga mata kai, Jalila ta amsa wayar tareda yin sallama Amsamata yayi sannan ya dora da "Babyna kwana biyu kin gujeni you are not picking my calls, ina fatan ba laifi nayi miki ba?" Cikin siriyar muryarta na shagwaba tace "Ohh no ni bakamin laifi ba, bana dan jin dadine kawai, amma yanzu Alhamdilillah naji sauki" "Ya salam amma baki gayamin ba, yau zan shigo kano dama shiyasa na kiraki, in kin amince zanzo in ganki" "Babu damuwa my one, ina fatan in ganka nima am missing you" "Like serious, karkisa inyi Ihu attention din mutane ya dawo kaina" Murmushi tayi tace "ba sekayi ihuba, aini yakamata inyi, kwana nawa zakayi a kano?" "zanyi sati daya Insha Allah, zanyi wani assignment ne" "Shikenan Allah yakawo ka lafiya" "Ameen my queen, bazaki tambayi Antynki ba?" Dan yamutsa fuska Jalila tayi tace "Ainasan tana lafiya tunda najika haka" Murmushi yayi yace "Queen da alama kinada kishi sosai, anyway sena shigo, idan nazo da wuri zaki ganni yau, in ban shigo da wuri ba se Allah ya kaimu gobe" "to shikenan Allah ya kaimu, take a good care of your self" "Ok Baby i will Insha Allah" ta katse wayar, Nana ta zuba mata ido tana kallonta, Jalila tace "Madam lafiya kuwa?" "Lafiya mana, nina kasa gane inda kika dosane, gane lamarinki se Allah mutum baya taba ganeki, gaba daya rayuwarki zigza ce" Sosai Nana tabawa Jalila dariya tace "rayuwartawa ce zigza, lallai ma Nana bakida dama, Rayuwata normal ce kaman ta kowa" "A'a ban yadda ba, Allah yasa ayi miki aure kafin ayiwa Yaya Jawwad" "Ba Ameen ba, back to sender muguwa kawai" "eh amma ni kikayimin fata saboda son kai" Wayar Jalila ce takuma daukar ruri, ta kai hannu ta dauka tana dubawa taga Hanan ce dan haka ta kashe wayarta. Tunda suka fara tafiya Abba beyiwa Jawwad wani gamshashen bayani akan wannan tafiyar ta bazata ba, yanason yayiwa Abba magana amma yakasa duk sunyi shiri Jawwad na driving, "Dama Aliyu akwai wadda kakeso kaki ka gayamin kabari ake kokarin auramaka wannan yarinyar?" Tambayar tazowa Jawwad a bazata, kuma idan yaji Abba ya ambaci sunansa na gaskiya kai tsaye haka, alama ce ta  he is so much serious. Jawwad ya dan sosa keya yayi shiru "yaka sosa kai kayi shiru? Kamin bayani mana" Cikin kame2 Jawwad yace"Amm.. Dama Abba, ai..." Abba yacce " Jawwad da farko sister dinka Jalila tagayamin inyi bincike akan yarinyar nan Naja, tacigaba da gayamin hakan, sannan taki gayamin komai game da Naja, sedai cewa inyi bincike, tacigaba da nunamin cewa kunyarka da kawaicinka baze bari ka nuna abunda ke ranka ba, na dauki maganarta serious nafara kokarin bincike, ina kan binciken ne, Mahaifin Hanan ya kirani yamin magana akan in dai dagaske kana son 'yarsa yabaka dama ka fito, wanda ni bansan da zancen ba, nayi kokarin in zauna da kai muyi maganar kafin ta kai ga haka Jalal yazo ya sameni har gurin aiki yamin bayani akan alakarka da' yar gidan general Abdurrasheed, sannan ya daukeni ya kaini inda aka gayamin komai akan Naja, bantaba tunanin Mamanka zata zaba maka mace irin wannan mara kamun kai a matsayin mata ba, Jawwad meyasa baka gayamin abunda ke ranka ba, kabari nakusa gangancin saka rayuwar ka a hatsari? " "Abba nasam bazaka zabamin abunda ze cutar dani bane, banason bijirewa umarninka dana Maama, shiyasa na amince" "Nasan da wannan Jawwad, amma dukda haka a matsayin mu na iyaye yanada kyau mudinga baku zabi, ba wai bin son zuciyarmu da tirsasamuku akan abunda bakwa ra'ayiba, yana da kyau kadinga faďan ra'ayinka ba laifi bane naji dadin kokarin yimana biyayya dakayi, Allah yayi maka Albarka yakara haďamin kanku, Allah ya shirya mana ABDUL JALAL dukda kasancewar halinsa amma yadamu da lamuranka sosai, yadda yazo ya sameni kaman zeyi kuka, Alhamdilillah nayi mamaki naga abubuwan sa sun fara raguwa, yafara dawowa hanya, ya rage rashin ji" "hakane ya rage sosai makuwa, abokiyar fadansa keta kokarin sashi a hanya ai" "Wa kenan?" Abba ya tambaya "Jalila mana, tanata kokari akansa, kuma naga inga masa nasiha koba duka ba yana ďan dauka" Abba yace "masha Allah, at least kaga an samu improvement, itama General Abdurrashed yamin magana, yace akwai abokin ďansa dayake sonta, wai Ahmad sunansa kowaye?, yabiyo ta hannunsa a nema masa Aurenta, amma nace na bashi wuka da nama shima babanta ne, duk abunda yaga dace yayi" Jawwad yai murmushi yace "hakane Abba, lokacin da mukaje kaduna yamin zancen nima, yace shima mutumin sojane yana da kirki sosai" "Hakane, Allah ya tabbatar mana da alkhairi yamuku zabi da abokan zama nagari" Jawwad a zuciyarsa yace Ameen. Hanan taita kiran wayar Jalila amma Jalila taki dagawa, saboda bataji dadin abunda Hanan tayi mata ba, sako Hanan ta turimata kamar haka     "Assalamu Alaikum, Am very sorry my twiny, nasan na miki laifi kiyi hakuri dan Allah, Yaya Jawwad yazo kano shida Jalal, yamin bayanin komai abunda ke faruwa, kiyi hakuri so dakuma kishinsane yasa namiki haka, sannan naji Yaya Abdallah yana maganar Ansamawa Jalal aiki za'a gama interview ranar laraba amma har yanzu bejeba, you have to take action" Jalila nagama karantawa ta kira Hanan, seda Jalila ta kira sau biyu sannan Hanan ta dauka tace "'yar rainin hankali inata kiranki kinki ďagawa, amma da kikaji batun ABDUL JALAL harkin kirani" Jalila ta hade rai kaman Hanan na ganinta tace "ke banason wulakanci, ai banji dadin abunda kikayimim ba sam wallahi" "Nasani amma ai nace kiyi hakuri, you won't understand how far my loves go on your brother, inasonshi ina kishinsa shiyasa na shiga damuwa, inata addu'a dai amma ina cikin damuwa Queen" Tausayin Hanan yakama Jalila tace "ki kwantar da hankalinki kinji my twiny, komai ze wuce kece zaki zama matar Yaya, ina nan ina tayaku da Addu'a" "Masha Allah, Allah yabiya ki da mafificin Alkhairi Jalila, bazan iya biyan kaunar da kike nunamin ba" "bakomai Sister na, nace are you serious Jalal beje interview din nan ba?" "Wallahi dagaske nake miki, hala aikinma kekisa aka samo masa?" "to meye naki aciki nason kisani, nice nagayawa Daddy ya samo masa, kuma be isa ya watsamin kasa a ido ba zan sameshi, seyaje interview din nan" Dariya Hanan tayi tace "wai zaki sameshi irin Mum din nan tasa, kai lamarinku din nan yana birgeni wallahi, kowa da guntun taurin kansa dan Allah duk yadda kukayi ki gayamin dan wallahi.... Katse wayarta Jalila tayi jin Hanan zata fara mata bare2. Ilham shiryawa tayi takanas ta tafi gidansu, domin taji abunda yakamata suyi, dan ita ta riga ta karaya da lamarin nan bata tunanin akwai nasara dan kullum Jalal kara bauďewa yake, babu alamar ze sakko. Tayi sa'a ummannata tana gida, suka kule a daki kaman yadda suka saba in Ilham ďin tazo. "Umma nifa najiki shiru ya'ake cikine? Na ďora mata sata amma Jalal bakiga rashin mutuncin dayayi min ba, wallahi son yarinyar nan yake, kincemin zakije Nijar gurin wani malamin amma shiru kullum abubuwan kara tabarbarewa sukeyi" Umma tace "ke nayi maganar zuwa nijar, munyi waya da mutumin na masa bayanin komai, amma budar bakinsa wai yayi bincike akan yarinyar indai inason a yimin aiki akanta zan bashi dubu ďari biyar, nikuma ina naganta? Banida ita bani da wata kadara da zan sayar in bashi wannan uban kuďin, dan haka nakoma gurin wanda muke zuwa tun farko, shikuma yacemin baze iya aiki akanta ba sedai a kara watsa rayuwar Jalal" "to Umma batun Auren namu fa?" "shima za'ayi ne amma yace muďan kara hakuri" "umma kenan, mu kara hakuri fa kikace? By mistake idan Asirin ya karye gaba ďaya kuma yaya zamuyi?" "bazeyiba, malamin yabani wannan tabbacin ki kwantar da hankalinki burinmu seya cika, sena wulakanta shi shida uwarsa hada uban nasa, bana yafiya ga wanda yamin laifi" "to shikenan Umma, Allah yasa, ni bari in tafi, zan ďan tsaya inyi siyayya". Dogon wandone a jikin Jalila da riga, dan haka ta ďakko katon hijjabinta me hannu tasaka ta fito part ďin Jawwad taje tana tsammanin ganin Jalal a can amma baya nan, rabonta da shiga gidansu Jalal kuwa harta manta, direct ta nufi gidansu Jalal, amma tarasa ina zatayi tasan dai be dace ta tafi part dinsa nemansa ba, fasawa tayi ta juyo tanufo gate zata fita itakuma Ilham ta shigo. Tsayawa sukayi suna kallon kallo itada Ilham, haďe rai sosai Ilham tayi tareda yin tsaki tazo zata gifta gefen Jalila ta wuce, caraf Jalila tasa hannu ta riketa ta janyota gabanta suna fuskantar juna, a fusace Ilham tace "ke dalla malama meye haka? Meyasa bakida tunani ne?" Jalila taja wasu seconds tana karewa kwayar idon Ilham kallo sannan tace "banida tunani kam, dole ki fadi haka, kinsan ba'a tabani a zauna lafiya, dan haka sekinyi hakuri da duk abunda zaki gani har se kin biya abunda kikayimin" Hararta Ilham tayi takuma kokarin rabawa ta wuce ta barta, amma Jalila takuma shan gabanta tace "Ilham nasani tsawon shekaru ina bata miki rai, kinyi alwashi daban2 akan ganin bayana, baki taba nasara ba se wannan karon da kika ďora min sata, to bari kiji in gayamiki wani abu dabaki saniba, babu abunda zakiyi a rayuwa ki rama abunda nayi miki, na riga nagama dake Ilham, kuma Wallahi Jalal baze taba aurenki ba, nagaya miki dama muddin kudirina yayi karo da naki sena watsa naki, kudirinki akansa yaci karo da nawa na watsa shirinki watsawa ta har gaban abada zanso ingaya miki wani abu daya kamata ki sani amma ban saniba ko kinason ji" Kallonta kawai Ilham take batareda tayi magana ba, Jalila ta ďora tace "Ranar da Jalal ya kwanta a Asibiti, kukazo duba shi keda Mahaifiyarki kisani idonsa biyu yaji duk abunda kuke faďa, dan haka ki cirewa ranki cewar burinki ze cika, Na riga naganoki Ilham tuntuni shiyasa nayi miki illa inda ba wanda ze gani, na illata shirinki bakida wata dama data miki saura, damarki ďaya shine ki jajirce kicigaba da jarraba sa'arki kozaku daidaita" Jalila takarasa maganar tana mata wani mugun kallo sannan ta juya tayi ficewarta, gaban Ilham ne ya shiga dukan hamsin2, kaddai Jalila dagaske take, amma to in hakane da yaji aida yaďauki mataki, "kai karyane bejiba, koma yaji wallahi seya Aureni, se burin mahaifiyata yacika" Ta shige cikin gida da sauri hada tuntube. Maama takasa zaune takasa tsaye, Naja batasan budurin da'akeba dan lokacin da Abba yayi wannan maganar bata nan tafita yawonta, harta dawo Maama tarasa ta inda zata fara mata bayani. Jalila na fitowa taga Jalal ya dawo a mota, yana kokarin shiga gida, ganin da yayi ta tsaya ta ki tafiya ta kura masa ido yasan akwai magana a bakinta, tsayawa yayi agaban ta yayi parking, yana tsayawa ta zagaya inda yake, ďan ďage mata gira yayi alamar meke faruwa? Ďan kallonsa tayi tace "daga ina?" "kin aikenine?" ya tambayeta "Ohh No Allah yabaka hakuri" Yace "Ina Jawwad ne? Na duba baya nan ban san inda ya tafiba?" hade rai tayi itama tace "ka duba shi mana, kokabani ajiyarsa ne?" Kallonta yayi, wato ta rama kenan Yace "A'a ban baki ajiyarsa ba" "dama.." sekuma tayi shiru "Dama me?" "inada magana ne" "fadi ina jinki" "toka fito daga motar mana" "In fito kuma? Gaskiya ni yunwa nakeji, zuwa zanyi in kwanta, naje neman Abinci narasa me zanci, dama in kin bawa Jawwad nake ci nima amma yanzu baya nan nasan bazan samuba" "Hmm to kace Ilham tabaka mana" Hade rai yayi sosai yana Kallonta, sunkuyar da kai tayi tana dariya kasa2 "Yi hakuri, ai yanzu mundena faďa ka jirani a part din Yaya Jawwad zan kankaro maka kanzo in za kaci" tayi maganar tana dariya, tana matukar kyau idan tayi dariya, gyaďa kai yayi ta juya ta tafi, yabi bayanta da kallo harta shige gida, sannan yaja motar ya shiga da ita gida. Gida takoma taje ta ďakko masa breakfast ďin Jawwad da yatafi beci ba, dayake da zafinsa a cikin flask, tana zuwa ta tarar dashi a zaune a palourn Jawwad yana jiranta, ta shiga tayi sallama amma be amsaba, seda tazo kansa ta tsaya takuma yimasa sallama ya ďago ya kalleta ya amsa a hankali, ta ajiye tray din tace "Yana daga hakkin musulmi akan musulmi in yayi sallama ka amsa masa, kadinga amsa sallama please" Shiru yayi yaki kulata, Jalila tarasa wane irin miskilin mutum ne Jalal, koma tace ďan rainin hankali kana masa magana yana jinka amma yayi maka banza dan tsabar wulakanci, ta aje masa Abincin ta zauna a kujerar dake kallonsa. Ta danne fushinta Ya hada Abincinsa yafara ci, can yace "Me ya kai Alqur'ani dana baki hannun Ilham?" yai tambayar kamar bashi yayi ba "ďauka tayi" tabashi amsa a takaice "Ya'akayi ta ďauka baki hanata ba?" "Ina bauchi aka aikota taganshi shine ta ďauka" Bekuma cewa komai ba yacigaba ds auna loma, can Jalila tace "Ya akai kasan yana gurin ta?" Kallonta yayi ya danyi murmushi "in kinaso in dawo miki dashi, yana gurina, amma bakiga abunda na ajiye a cikiba ko?" ďan yatsina fuska tayi sannan tace "Nifa tsawon lokacin da yayi a gurina banga komai a ciki ba" "zan dawo miki dashi kikuma dubawa" "to naji zan duba" Ya cigaba da cin Abincin sa, can ta ďan nisa tace "An baka aiki ance kaje interview kaki why?" Ďagowa yayi ya kalleta, "dama nayi tunanin kece kikasa aka nemamin wannan aikin, tayaya ina shaye2 zakice asamomin aiki a hukumar dake yaki da shaye2, amfanin me zanyi ko nima so kike a kamani?" "calm down let me explain, mezesa in so akamaka? da hakane naso akamaka da nasa an ka maka kaida abokinnaka jeje ai" ďagowa yayi ya haďe rai kaman be taba dariya ba "Am sorry banyi hakan da wata manufa ba, sedai inkana aikin na farko ze rage maka yawan damuwa, sannan ze sa ka kara kokarin kadena shaye2 kaima, at least in kana da gurin zuwa ze kara dauke hankalin ka daga kan Shaye2" Zuba mata ido yayi yana tunani daban2 akanta, ta damu dashi dayawa, she's so simple and calm, matsalarta kawai taurin kai da rashin kunya, Amma tanada zuciya me kyau. Tsarguwa tafara yi da kallon dayake mata tace "Ya dai?" "meyasa kika damu dani haka?" Shiru tayi dan bata san mezatace masa ba, basarwa tayi tace "dan Allah kaje interview din nan karka watsamin kasa a ido" "Senayi shawara" yabata amsa "shawara kuma, dan Allah mene kuma na wani shawara dan Allah Yaya Jalal kaje please karkasa inji kunya" da shagwaba takarasa maganar Bude baki yayi tareda yin murmushi kaman karta dena magana "Nine Yaya kuma yau, yarinyar bakida kunya fa" "Aida ďinma dan muna fada ne amma yanzu mundena faďa, dan Allah kaje ba dan halina ba, kaji Yayana ďan gidan daddy abokin Yaya Jawwad, badan halina ba" murmushi yayi ya ďan girgiza kai yace "Aikuwa kinsan indan halinkine bazaniba, innayi tunani zan gaya miki" "to Allah yasa inji alkhairi" Be amsaba ya kai hannu ya dauki cup ya kai bakinsa amma jikinsa yafara rawa yakasa kaiwa "lafiya menene kuma?" Ajiye cup din yayi, yai shiru yana rintse ido" Da sauri ta mike ta nufi inda yake tana faďin "Subhanallah meyafaru?" Dagowa yayi idonsa yayi jawur yace "Gi.. Giy..... Giya,.... Giya zansha, ita nakeson sha" "giya kuma? Meyasa zaka sha giya?" Numfashi yake ja ya mike tsaye ya nufi hanyar fita, idonsa yayi jawur jikinsa se rawa yakeyi da sauri ta sha gabansa "dan Allah Jalal karka sha giya, meyasa idan kuma kasha ka bugu daga nan ka mutu mezaka cewa Allah? Dan Allah karka sha kayi hakuri zaka ji bakason sha" Tureta yayi ze fita, takuma tare kofa tana masa magiya, yasa hannu ya hankadata jikin kofa ta bige kafaďa ta faďi a gurin shikuma ya fice kaman wani horrorn dayake bukatar jini. Godiya mara iyaka ga members na kungiyar mu me tarin Albarka Perfect writers association, Allah yakara haďa kanmu. Abdul Jalal Novel Fans❤️🌹 kaunarku a ruhina take, inajin dadin comments dinku hada wakokin da'ake reramin😂😂😂 Masu bina private suna min comment kokuma bani karfin gwiwa, da masu biyoni suna neman littafina da masu karantawa wanda bansansu ba ina godiya Allah yasaka da alkhairi Allah yabar kauna. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *ABDUL JALAL* 🌹🌹🌹🌹🌹🌹 *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/              _*Story, &writing*_ _and edited_                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *P.W.A*✍️       PART 2️⃣                                  _PAGE  4️⃣1️⃣94       Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724            _MY FIRST NOVEL _ Jalila ta bugu sosai, ta rike hannunta tana rintse ido saboda azabar zafi, shikam yasa kai ya fice yabar dakin. Ta dade a gurin a zaune, sannan ta mike ta koma cikin gida tana yamutsa fuska. Su Jawwad kam har la'asar sannan suka isa Bauchi, Abba yakira daddyn Hanan a waya yagaya masa sun karaso, aka turo wasu sojoji sukazo suka tafi dasu har estate din, Ba Jawwad ba har Abba seda yayi mamaki irin tsaruwar da estate din yayi sekace barrack duk inda ka juya sojoji ke shawagi a ciki, akai musu Jagora zuwa gidan daya kasance nan ne center. A dankareren dakin Daddy akayi musu iso, da murna daddyn Hanan ya tarbi su Abba, suka gaisa yai musu barka da zuwa, seda suka fara gabatar da salla sannan daddy yai umarnin akawo musu Abinci. Wasu matasan 'yan matane dabasu wuce sa' anin su Hanan ba su uku suka kawo Abincin suka ajiye, tareda gaida Abba da Jawwad, ďaya daga cikinsu wadda da gani kasan hutu da jin dadi ya ratsata tace "daddy wannan yana matukar kama da Yaya Yusuf, ko shine sirikin naka?" Jawwad ya sunkuyar da kai saboda kunya Daddy yace "kaniyarki yusra, sarkin surutu, tunda kunkawo Abincin kukoma, ki gayawa Inna bakin sun iso zasu shigo anjima su gaisheta" Murmushi Yusra tayi tace "Yadda kace haka za'ayi daddy" Abba yace "General wannan ma 'yar wajenka ce?, tana kama da Hanan" "' yar wana ce, gaba dayansu yaran 'yan uwanane, Aini Hanan da Abdallah kadai Allah yabani, sekuma diyata Autar mata Jalila, Zuma kenan ga zaki ga harbi" Gaba daya sukayi dariya, daddy yace su ci Abinci, Amma gaba daya Jawwad yakasa sakewa yaci Abincin nan saboda kunya "Sekace wani mace🙄, (ya kuke gani in goga Jalal ne? 😂 yaseen cin abunsa zeyi) " Daddy yace "Jawwad baka cin Abincin nan fa, nifa banason fulatanci, ka saki jiki kaci Abinci" Jawwad murmushi kawai yayi yakuma sunkuyar da kai. Bayan sun kammala, Abba ya gyara zama sannan yace "to Captain ni dai da farko Jawwad be gayamin yana soyayya da Hanan ba, har nayi masa zabin matar Aure nida mahaifiyarsa, Amma yanzu nagane akwai matsala a dangane da zabin da mukayi masa, kuma Kanwarsa Jalila da Dan uwansa suka sanar dani halin da'ake ciki har kaima ka kirani a waya kazomin da wannan zance na Jawwad ya fito in dagaske yake" Daddy yace "Hakane, nima mahaifiyar Hanan dince ta sanar dani halin da'ake ciki, kuma gaskiya yarinyar tanada manema dayawa kuma ta nuna shi Jawwad din takeso, shiyasa nima nayi maka magana" Abba yace "Hakane, Amma zangaya maka wani abu, inkaga zaka bawa Jawwad 'yarka a haka to shikenan, inkuma kaga baze yuwu ba semu hakura" Daddy yace "ina jinka fadi muji" Abba yace "kaga maganar gaskiya a yanzu a bangaren mahaifi Jawwad bashida kowa se Allah sekumani, sedai bangaren mahaifiyarsa, banida wa bani da kani, kani na ďaya shine mahaifin Jalila kuma Allah yayi masa rasuwa tun Jalila nada shekaru biyar, kuma daga ni har mahaifinta babu wanda yasan suwaye dangin iyayenmu sakamakon suma gudun hijira sukayi daga garinsu, in kana ganin zaka iya bashi 'yarka a haka shikenan " " Haba Alhaji Usman, Ai Jawwad ko ďan tsintuwa ne babu abunda ze hana in bashi' yata indai yana sonta, yanada hankali ga nutsuwa da tarbiyya wannan ba abun damuwa bane ba, bari muje ku gaisa da Mahaifiyata semu karasa gidan Yayana, shi ze karbi kudin Auren" Abba yace "Nagode kwarai da wannan karamcin naka general, Allah yasaka da alkhairi" Daddy yace "tsakanina da kai babu batun godiya, bari muje". Jalila takoma gida ta fara baccin dole saboda azabar zugin da hannunta yakeyi, se kusan la'asar ta tashi, shima hayaniyar Naja ce ta tasheta dayake ita Naja wani lokacin kaman banza haka take bata magana a hankali, ga hauma hauma kamar rainon gabuwa, wannan hargowar ce ta tashi Jalila. Sannan da alamu har yanzu Maama bata gaya mata sakon Abba na tabar masa gida ba, dan har yanzu tana giginta da rawar kai, Jalila ta tashi tayi sallar la'asar tanemi abun zubawa a cikinta. Shikuwa Jalal tunda yaje ya sha giyarsa yayi tatul wani nannauyan bacci ne ya kwashe shi be farkaba se magariba, ya shiga yai wanka yai sallolinsa, bayan ya idar ne ya dau wayarsa yakuma kiran Jawwad, wannan karon Jawwad ya dauka Jalal yace "wai dan Allah ina ka shiga ne haka? Tun safe ban ganka ba, na tambayi kanwarka tace bata san inda kake ba" "Aiba bata nayi ba, kuma ba saceni akayi ba kaganni tareda Abba muna Bauchi" "Bauchi kuma? Me ka keyi a Bauchi?" "bazaka gane ba, sena dawo kawai akwai Labari" Murmushi Jalal yayi, yadda yaji muryar Jawwad yasan yana cikin farinciki, Jalal yace "To seka dawo din, amma tafiya ba sallama haka?" "Nima ban san da tafiyar ba, babu shiri Abba yace inzo mutafi" "to shikenan Allah yadawo daku lafiya" "Ameen ya Allah" sukayi sallama Bayan sunyi sallamane Yusuf ya shigo palourn daddy, Sallama yayi suka amsa gaba daya, Yusuf ya kalli Abba ya durkusa ya gaisheshi ya amsa masa cikin sakin fuska, ya juya ya kalli Jawwad ya mika masa hannu suka gaisa. Daddy yace "Yusuf ga Abban Jalila fa" Murmushi Yusuf yayi yace "Ai ina shigowa jikina yabani, ina kallonsa naga akwai alakar Jini, wannanne yayanta kenan sirikinmu" Daddy yace "ya akayi kasani?" Yusuf yace "Kai daddy yadda yarinyar nan ke fadarsa, ko kunya ba taji ranar inajinta itada Nawwara (matarsa) tanata yabonsa hada yi masa waka, kaf estate din nan ba wanda besan haidar ba ko ince Jawwad" Gaba daya sukayi dariya, Yusuf yace "ďan uwa Allah yabaka wuyan ďauka, dan wallahi Autar daddy fitinanniya ce, ga yarinta a cikinta" haka sukaita taba hira Yusuf yajanye Jawwad suka fice zuwa bangaren Inna. Suka shiga da sallama, kamar kullum tana kan darduma tana lazimi, suka zauna a gefe suna taba hira harta idar, sannan ta juyo ta kallesu dan kura musu ido tayi, Jawwad yace "Sannu Inna" "Yawwa ďan nan, Yusuf wannan kuma ina ka samoshi, kar in fadi wani abu ace nayi rikici" Yusuf yace "Inna Yayan Jalila ne" Murmushin fuskarta ya faďaďa sannan tace "Masha Allah, Nayi farincikin ganinka yarona, Kanwarka me kama da mairota da na dauka itace, ashe ba ita bace ba ina kabaromin me sunan larabawan?" "Tana lafiya Inna, tace a gaisheki" "Allah sarki yarinyar kirki me hankali, idan ina basu labarin kanwata se suyita lallabani wai kar in rikice musu da kuka, itakuwa kanwarka zama take muyita hira naita bata labarin wannan kanwartawa" Yusuf yace "zaki farako inna, dan Allah kiyi hakuri, kekowa sekin bashi labarin kanwarki, ko labarin tsofaffinki ba kyayi kamar ita, kimsan bakida cikakkiyar lafiya" Jawwad yace "A'a kabarta ta fada maybe hakan ze rage mata damuwa, tunda kaji haka akwai kyakyawar alaka a tsakanin su" Yusuf yace "Ai intana wannan labarin nata daga nana zata fara kuka, kuma in tafada bata iya cin Abinci jininta ya hau sosai" Sallamar Su daddy ce ta katse musu hirar suka amsa musu Sallamar amma banda inna da ko juyowa takasa yi. Daddy yakaraso gabanta ya durkusa yace "Inna ga baban Jalila, kuma sirikinki yazo ya gaisheki ne" jinjina kai tayi ba tace komai ba, Abba ya zagayo gabanta ya durkusa gaba daya ta zuba masa ido ko kyaftawa batayi, tace "Imamu ne? Imamu ina Mairona" cikin sanyin jiki Abba yasa hannu yakamo Hannunta ya rike a nashi a hankali ya furta "Innarmu.... Inna Hafsatu, Allah yasa kece, kece wadda Inna take bamu Labari Yayarta" Fashewa da kuka tayi ta rungume Abba tana fadin "Alhamdilillah nagaya musu, Amma sunki yarda suna ganin kaman rikici nane kawai, tunda naga yarinyar gurinka nasan tsatson Mairamunace, nasan zuwa yanzu ba lallai tana raye ba, amma ina son inga ahalinta" Hawaye sharkaf a idon Abba yace "Na dade ina bulayin neman ki Inna, Allah ya karbesu gaba daya, dasu da tilon ďan uwana, ya mutu yabarmin 'yarsa Jalila se yarana biyu, ban taba tunanin Allah ze karbi Addu'a ta ba, yau naga dangin iyayenmu" Gaba daya jikinsu yayi sanyi, kowa seda yayi hawayen tausayi, Abba yasha wuyar bulayi da yawo garuruwa ko Allah zesa yasamu wani nasa ashe suna kusa da juna, alakar yara ta haďa amma basu saniba, Ashe shiyasa kamannin Jalila da Hanan sukayi yawa, hatta yanayin halayensu iri daya. Abba yasa hannu yana gogewa Inna hawaye cikin zolaya yace "Kamanki daya da Innarmu, sedai duk babanmu yafi ku kyau" Murmushi tayi tace "Ai shima ďan uwana ne, kuma mairo tafishi kyau, Allah yayi musu rahama gaba ďaya. Nan hirar asali da tushe ya barke, nan da nan Labari ya karaďe estate din nan cewar ansamo dangin mairo kanwar Inna, nan da nan gidan yafara cika da dangi da 'yan uwa don ganewa idanunsu hakikatul Amri. Daddy yace tunda hakane kadasu Abba sukoma yau, su ďanyi musu ko kwana ďayane Inna taji ďaďi kuma sannan suga' yan uwa. Haka kuwa akayi, Abba yakira Maama yace bazasu dawo a yauba saboda wasu dalilai, ba wanda suka gayawa abunda yafaru, hatta Daddy be gayawa su Hanan ba. Jalila takira Ahmad ya sanar da ita cewar baze shigo yauba, saboda yayi dare a hanya sedai zuwa gobe Insha Allah, seda suka sha soyayya sannan sukayi sallama gefe daya kuma hannunta se ciwo yakeyi, da wanine yai mata abunda Jalal ya mata yau da seya gane bashida wayo, shima ďin dan yanzu bata son yawan fitina da shine saboda gaba ďaya yanzu tausayi yake bata, da dane da seta rama. Amma to meyake damunsa haka? Lokaci ďaya mutum ya rikice kaman wani me tabin hankali, yana zaune lafiyar Allah amma ya birkice lokaci daya wai seyasha giya. Jawwad kasa boye farincikinsa yayi, seda ya kira Jalal a waya, yana ďagawa Jawwad yace "My man kana inane?" "Ina gida mana, ina zanje tunda baka nan? Wai yaushe zaku dawo? Tun dazu nake zuba ido amma baku dawo ba" "Ai mu ba yau zamu dawo ba" "Se yaushe?" "Ai bazaka gane ba Jalal bansan yadda zan fasalta maka farincikin danake cikiba" "Abba yaje nema maka Auren Hanan a Bauchi" Jalal yafada kai tsaye Da mamaki Jawwad yace "ya akayi kasani?" "Zuciya tace tagayamin" "ban yadda ba dama can kasani kai shiru kaki gayamin, amma akwai saura ai" "to gayamin inaji" "Abba ya gano danginsu daya daďe yana nema" Murmushi Jalal yayi yace "Alhamdilillah, na dade ina fatan hakan ya tabatta, kakarsu Abdallah ce Inna Hafsatu da Inna mairo take fada take bamu Labari ko?" Cikin mamaki Jawwad yace "wai dan Allah ya akayi kasani?" "Allah ne yasanar dani, dan Allah kadawo da wuri, ni bana jin dadi in baka nan" "wai kana in dawo da wuri, kamanta in Allah ya kaimu next week zan tafi inda aka turani aiki"? "kumafa hakane se yanzu nakejin babu daďi, amma Insha Allah hakanne mafi Alkhairi agaremu baki daya" "Amma ni ina mamaki yadda akayi duk kasan wannan zancen ni ban saniba" dariya Jalal yayi yace "Ba abun mamaki bane, kai dai seka dawo kawai Seda suka gama hira da Jalal ya katse wayar, Jawwad yaji kaman ya kira Jalila amma ya fasa, dan yasan idan ya kirata farinciki seyasa yagaya mata abunda ke faruwa kuma Abba ya gargade shi akan kar kowa yasan wannan zancen a yanzu harse sun koma gida. Maama tarasa ta inada zatayiwa Naja bayanin Abba yana bukatar ta bar masa gida, saboda tana matukar Jin tsoron Masifar Yaya Mairo, tarasa abunda yake mata dadi, yanzuma da Abba yayo waya seda ya jadadda mata baya son ya dawo ya tarar da Naja cikin Iyalinsa, tarasa ta inda zata fara harga Allah bazata iyaba sedai inya dawo shiya koreta da kansa, can wani bangaren na zuciyarta yake cemata banda ma ya raina miki hankali, ita Jalila dake zaune a gidan meyasa bece ta bar gidan ba, shekarar Jalila nawa a  gidan, se yanzu zece Naja tabar gida, indai Naja zata bar gidan nan to dole Jalila ma ta kama gabanta, Maama tayi kwafa tace "Zaka dawo ka sameni, dai2 nake da kai" Naja se iyayi take tana wasu irin abubuwa na ban haushi wai ita zatayi Aure, A gaban su Nana take waya da kawarta sunata shirye shiryen abunda zasuyi da biki, ba kunya Naja take cewa a mata booking na kayan mata na tashin hankali, masu tsada, se wasu irin lissafi takeyi, kala2 party da zatayi, da irin expensive clothes da zasu saka itada kawayenta. Tagama wayarta su Jalila suna jinta, tana gamawa Nana ta tinstire da dariya, cikeda tsarguwa Naja tace "ke Nana meye abun dariya haka?" "A'a ni ba dake nake ba, mahmud ne yabani dariya a waya" Itakam Jalila bata samu zarafin dariya ba tana fama da ciwon hannu, ko uffan ba tace ba. Nana tagayawa Jalila Abba yace bazasu dawo yauba, Akwai abu me mahimmanci daya rikesu, Jalila a ranta taketa addu'ar Allah yasa abunda take tsamanni ne ya tabatta. Washegari da safe Monday ce Jalila tace bazata makaranta ba, Dan haka Nana ita kadai ta tafi, tai kwanciyar ta tana bacci, Zahra takirata a waya tagaya mata zasuyi test karfe goma shadaya da rabi na safe, Jalila sam bata da niyyar zuwa makaranta haka ta tashi tana tsaki tayi wanka tasaka kaya, doguwar riga pitch da mayafinta se wata 'yar karamar Jakarta ta dauka, iyakacin Jakar nan ta dauki waya da kudi da ďan abunda baza' a rasa ba sekace jakar roko, Jalila Ta fito fuskar nan babu walwala,  ta tarar Maama na palour tana karyawa itada Naja, yanzun ma hirar bikin suke, Jalila ta durkusa tace "Maama zan tafi school, yanzu aka kirani zamuyi test anjima" Banza Maaman tayi mata taki kulata, dama batayi tsamannin Maama ta amsa ba, tayine dan hakan shime tarbiyar da Ummi ta dorata, ta mike jiki a sanyaye Zata fita Naja tace "Aikin banza wai za'a school za'a tafi yawon gantali dai irin wanda uwale ta saba yi" Maama tace "dan Allah kidena shiga harkar yarinyar nan shiyasa take kara rainaki" ai kafin Maama ta gama magana Jalila ta waigo tace "ta Uwale tayi kyau, kekuma ki saurar kiga naki sakamakon, anzo an bararaje ana cin duniya babu a house, gara ki zage ki ciki kafin ki kara gaba, Akuya kawai" Ashar Naja ta mulmulo zatayi Maama ta dakatar da ita, Jalila kuwa tayi ficewarta ranta bakikkirin babu dadi. Maama tace "kyaleni da ita, ki zuba ido zakiga matakin da zan dauka akanta" Jalila na fita ta hango Mummyn Jalal  tareda Ilham da alamu wani gurin zasuje, da kaman ta basar tayi tafiyarta sekuma taga hakan be dace ba, dan rabonta da taga Mummy harta manta dan ko gidan bazuwa takeba yanzu, dan haka ta nufi inda motarsu take, Mummy tana kokarin shiga, Jalila da fara'arta ta karasa ta durkusa ta gaida Mummy, amma ga mamakin ta taga Mummyn tayi mata wani irin mugun kallo kamar bazata amsa ba sekuma ta amsa da kyar, Jalila taji ba dadin abunda Mummy tayi mata, amma ta dake ta mike tace "Mummy Adawo lafiya sekun dawo" Mummy ta yamutsa fuska tace "Yawwa dama ina son ganinki kuwa, akwai magana me mahimmanci da nakeson mu tattauna dake, dan bazan saka ido abunda ke faruwa yacigaba ba" Seda gaban Jalila yai mummunar faduwa, wannaan wane irin abune ita kowa ma laifi take masa, kowa ya tsanenta a fili tace "to Mummy Allah yasa ba laifi nayi miki ba? Zanzo Insha Allah, Adawo lafiya" "Munafukar banza barauniya, me bin ďan mutane, Akuya kawai" Taji sautin maganar Ilham ta sauka a kirjinta saitin zuciyarta, dukda yadda maganar tayi tsauri tareda dukan zuciyar Jalila, amma ta danne taki juyowa ta kuma kallon inda suke, ta mike tacigaba da tafiya. Jefa kafarta take ba tare da tasan ina take saka kafar tata ba, Hawayene yake bin idonta, Allah ya temaketa unguwar tasu se kayi minti goma babu wanda yazo ya wuce, kuma wajen karfe tara ne duk wasu sun riga sun fita, hakan yakara bata damar zirarar da hawayen ta son ranta, tana cikin tafiya ne taji ana mata horn kaman za'a kashe mata kunne, ita dai iya saninta ba a tsakiyar titi take tafiya ba gefen hanya ne, Amma an cika mata kunne da horn, banza tayi tacigaba da tafiyar ta. motar aka sa aka sha gabanta, sannan yafito daga motar yace "Bakya jin ina miki horn ne ? Sekace wata kurma, Kuma Se yanzu zaki tafi school karfe tara? Allah ya shirye ki, zo muje in ajeki ta nan zan wuce" ya dinga jero maganar daya bayan daya Juyowa tayi ta kalleshi, ya saka farin yadine dukda kansa babu hula yayi kyau sosai, dan zata iya kirga sau nawa taga Jalal da dogayen kaya, kallonta yayi sosai yaganta kaman a birkice, hawayene a fuskar ta, idonta har yafara Ja, cikin tsiwa tana hararsa tace "bazan hauba ai da can ba kai kake kaini ba, salon in hau motar ka, ka karasa karyani bazan hauba" "hmm bazaki hauba ko? Bazaki hau motar mahaukaci ba, Dama interview din nan zani, Amma tunda bazaki hauba se inkoma kuma bazan kuma zuwa ba" Cikin sauri tace "A'a yi hakuri zan hau, Amma dan Allah karkayi gudu dani" tafada hawaye na zubowa daga idonta Gaba daya tausayinta ya kamashi, kome yasata kuka haka a titi, itada take da dakakkiyar zuciya? Abunda ze satana tafiya tana kuka ba karami bane ba "bazan ba, a hankali zan tafi" ya faďa a takaice Ta bude motar ta shiga, shima yazaga ya bude ya shiga, ya kunna motar yai mata key, suka fara tafiya, ya kalleta yace "Kukan me kike?" "bakomai" "bana son karya fa" Shiru tayi masa, ta maida kanta titi kyaleta yayi tunda yaga batasan faďa masa, maybe is her personal issue. Suna cikin tafiya Jalal yayi parking ya kalleta yace "Zoki rakani zanci Abinci, banyi breakfast ba" "Ni bazaniba, kaje ka dawo, nibana son ana ganinmu tare" ta fada tareda dauke kanta daga kallonsa Ba tareda ya kalleta ba yace "ohh yeah, be kamata adinga ganinki tareda ďan iska mara tarbiyya ba, kar azata irinmu daya, bari yanzu zan  dawo" Ta fuskanci haushi yaji, amma ta basar dan itama ranta a bace yake Befi 5 mintues ba ya dawo da leda a hannunsa, ya kunna motar suka cigaba da tafiya, yana tuki tana goge hawaye, sekace kurame, baya son ya kalleta yaga tana kukan nan, kukanta yanasa shi tuna lokacin da Umminta ka gudn abunda ze sashi kuka shida Jawwad, gani Jalila tayi ya canza hanya dan haka da sauri tace "A'a yanaga ka canza hanya?" Be kalleta ba yace "Wani guri zaki rakani" Zare ido tayi "saboda me makaranta fa zani, zanyi test" "Nasan makaranta zaki, amma tunda kika shigo motata sekinje, don't mind club zamuje kawai, zan danyi caji" (🙄🙄 tab ba ruwana, yan ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP, kunji Jalal dinku da rigima,) Abba sunga "yan uwa sunga dangi, Abba be taba tunanin suna da wannan dangin ba, a hakanma sunada 'yan uwa a wasu garuruwan, A yau Abba yace lallai zasu koma kano saboda yanada ayyuka dayawa, se sun dawo ziyara ta musamman dan kara sanin juna, ba karamin farinciki akayi ba ganin Inna ta samu zuri'ar Kanwar ta, Ashe ba a banza ba Jalila da Hanan suke wannan kamannin. A ranar su Abba suka dawo gida, tun Asuba suka taho, basu baro bauchi ba seda aka yanke watanni hudu, a matsayin lokacin Auren Jawwad da Hanan, sedasu Abba sukayi maganar Ahmad, Abba yace duk abunda daddy ya yanke dai2 ne, daddy yace "se Jalila ta kammala Makaranta ze bawa Ahmad, saboda yanayin karatunta dakuma aikin Ahmad Su Abba se  karfe shadaya suka sauka a kano, Suka sauka da matukar farinciki. Abba na shiga cikin gida yaci karo da Naja, a palour tana waya, bece mata komaiba ya wuce part dinsa, Maama haushinsa takeji akan yace Naja tabar masa gida dan haka tana jin sun dawo taki zuwa inda yake, ya shiga part dinsa yai wanka ya canza kaya,  da kansa yaje ya sami Maama a daki Yace "kina jin mun dawo amma kikasa fitowa kiga yamuka dawo? Shikenan ina miki Albishir Anbawa Jawwad Auren 'yar wajen Captain Abdurrasheed wato Hanan nan da wata hudu Insha Allah" Wani mugun kallo tayiwa Abba tace "kamar yaya? Yaza' ayi akaiwa Naja kudin Aure dan munafunci kuma aje akaiwa wata, mata biyu ze Aura kenan, Jawwad din kwaya nawa yake daze auri mata biyu?" "mace ďaya ze Aura wato Hanan, maganar Naja na soketa an barmusu kudin Auren, zanje da kaina in samu iyayenta, Sannan kije ki sallami yarinyar nan tabarmin gida, tun kafin raina ya baci, bana kaunarta a cikin iyalina, kema yakamata kuje ku kara binkice akanta" "Impossible" Maama ta fada da karfi Masoya kaunar da nake kumu tasa nai muku dogon page gashi nan, senaji Comments dinku love you all 😍😍😍🌹❤️❤️❤️🌹🌹🌹🌹 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣2️⃣95 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Cikide fusata Maama ke fadin "ni zakayiwa haka? Ka watsamin kasa a ido, a kai kudin Auren yarinyar mugama gayawa duniya za'ayi biki sannan kazo min da wata maganar banza, wallahi baze yuwu ba Jawwad bashida matar data wuce Naja Abba yace "Shikenan tunda ke zaki daura masa auren ai seki aura masa Najar in gani" Ya juya ze fice tace "Kuma wallahi bazata bar gidan nan ba, in dai Naja zata bar gidan nan to Jalila ma seta bar gidan nan" Cak Abba ya tsaya ya juyo yace "gida nawane, duk wanda yake ciki a karkashin ikona yake, idan yarinyar nan ta kai magariba a gidan nan to Wallahi zaku tafi tarene, ta tattara tabarmin gida nagaya miki, Jalila nan gidansune, nine mahaifin Jalila, Jalila bata da uwa ba uba seni, ita kuma wannan tanada iyaye dan haka ta koma gidansu, kowa ya zauna a gidansu" yana gama fadin haka ya juya ya fice. Jawwad yana zuwa ya canza kaya, ya nufi gidansu Jalal amma yatarar baya nan, dan haka ya koma gida ya samu guri ya kwanta dan ya huta A fusace Jalila tace "Wallahi bazani club ba, ka tsaya in sauka in yaso kaje inda yafi club be dameni ba" Shiru yamata ya cigaba da tukinsa, yana satar kallon yadda ta rintse ido tana masifa, ganin yaki kulata yasa a fusace tace "Magana fa nake maka, wai meye haka?" Fitooo yafara yi mata yana murmushi, Jalila ta kai karshe a kuluwa, ya dan kalleta yace "meye kuma na tashin hankali bafa cewa nayi zamuje Kisha giya  ba rakiya kawai zakiyi insha mutafi" Ta fuskanci so yake ya raina mata hankali, dan haka tayi shiru taga gudun ruwansa, ta dauke kanta zuwa ga kallon window tana share kwalla lokaci zuwa lokaci gani tayi tafiyar taki karewa dan haka takara fashewa da kuka me sauti Da sauri Jalal yace "Ke meye haka kuma? Nifa ba Jawwad bane da zakimin shagwaba" Ido duk hawaye tace "Eh aida Yaya Jawwad ne yasan inada test bazemin haka ba, kuma Allah ya kiyaye in maka shagwaba in maka shagwaba ince nayiwa wa?" tai maganar tana harararsa da kumburarrun idanunta Dan hade rai yayi yacigaba da tukin ba tareda yace komai ba itakuma tana hawaye. Wata unguwa suka shiga, wadda kome za'ayiwa Jalila bata san inane ba, wani katon dogon gini ya nufa, kana ganin yanayin ginin da girmansa kasan kamfani ne, yana zuwa aka bude masa wani katon nannauyan gate ya shiga da motar, tundaga bakin gate din ma'aikatan ke durkusawa suna gaisheshi, dagani gurin kamfanine, yaje yasamu guri yayi parking, da sauri akazo aka bude masa motar ya fito,  ya zagaya yace mata "fito" "ni bazan fito ba, kawai ka maidani inda ka dakkoni" "Wallahi in baki fito ba zakiyi biyu babu, kirasa test dinki kuma inki zuwa interview" Kara hade rai tayi sosai ta bude motar ta fito tana zumbura baki, fuskarta tayi jawur, yayi gaba ta bishi abaya. Babban abunda ya daurewa Jalila kai be wuce yadda taga duk inda Jalal ya ratsa ma'aikata manya da kanana suna girmama shiba, dan wasu har kasa suke zubewa suna gaida shi, Akayi sa'a in suka gaisheshi yana daga musu Hannu, Haka Jalal ya dinga ratsawa da ita tsakanin ginin katafaren gurin daya kayatu yadda yakamata, ko ina tsaf dashi, suna zuwa wata kofa sukaga wani mutum, ya girmi Jalal sosai ya mika masa hannu sukayi musabiha, mutumin yace "Yallabai yau akwai ruwa da kankara kaine a kamfani yau, rabonka da nan shekara nawa?" Murmushi Jalal yayi yace "Ya aikin?" "Lafiya kalau anata fama" Jalal yace "Masha Allah hakan yayi kyau" Daga nan yai gaba Jalila tacigaba da binsa, wata katafariyar kofa sukazo Jalal yasa hannu a aljihunsa ya dakko key yabude kofar ya kalli Jalila yace "Bismillah" tareda yi mata nuni da cikin gurin, jiki a sanyaye kuma a matukar tsorace ta shiga ta tsaya a bakin kofar tana rarraba ido, Office ne dankarere, sekace na hamshakin sarki ko gwamna, babu abunda babu a ciki, idonta ne ya sauka akan hotunan dake cikin Office din, akwai hoton shugaban kasa, gwamna da na sarki, sekuma hoton Daddyn Jalal, ta juya daya bangaren tangamemen hoton Jalal ne da Jawwad sanye da kaya iri daya sunyi murmushi an rubuta J&J global concept, sekuma hoton Jalal shikadai, ba karamin kyau yayi a hoton ba Ganin da Jalal yayi a tsorace take ta takure a tsaye, ya maida kofar ya rufe yasa mata key, kallonsa Jalila ta tsaya ta nayi a matukar tsorace hankali yace "muje ko?" "ni ba inda zani, ka maidani makaranta zan tafi fa" Baya kaunar wannan gaddamar ta Jalila dan haka be tsaya bata lokaci ba ya danko hannunta da karfi, hakan yasa ta saki wani uban ihu saboda zafi, hannun dayake mata ciwo ya rike, a tsorace ya cikata yana kallon yada tuni ta rike hannu tana Hawaye "Meye haka? Sekace wadda nayiwa wani abu" ya fada adan gigice "eh dole kace haka mana, jiya ba kai ka hankadeni na fadi akan hannun ba, yana min ciwo shine ka famamin" Jalila gaba dayanta shagwababbiya ce Dan shiru yayi yana kokarin tuna abunda ya faru shi gaba daya ya dauka a mafarki abun ya faru ba gaske ba yace "Ok naji amma yanzu zauna" Guri ta samu akan kujera daya ta zauna, yace "zan iya ganin hannun?" "Bazaka gani ba" ta fada tareda janye hannunta "Shikenan tunda kimce bazan ganiba, am sorry, ban san nayi miki ba, a tunanina mafarki ne, idan kinga na shiga wannnan yanayin kidena zuwa inda nake, kome zanyi karkiyi kokarin hanani, in bahakaba wataran zan iyayi miki illa" Dan kallonsa tayi tace "to meyasa kake hakan?" "Nima ban saniba, haka kurum nake tsintar kaina a wannan yanayin, Jawwad ne kawai ya damu da halin da nake shiga, Mummy da ba damuwa tayi daniba, tana ganin kawai shaye2 danake ne ya janyo min hakan, dayawa idan nayi kokarin dena shaye2, kokuma raina ya baci, se in shiga wannan yanayin " yayi maganar cike da damuwa, cikin tausayawa tace " Ka dinga yawaita Azkar, kuma ka kulada ibada zaka dena jin abun insha Allah" "bazan iya ba" ya fada kai tsaye "Meyasa bazaka iyaba?" "Har yanzu baki gama sanin waye ABDUL JALAL ba dukda yanzu kinsan abubuwa da yawa akaina fiye da iyayena, just keep praying for ABDUL JALAL, and I really appreciate your efforts on me, Thank you, Allah ya jikan Abee" Jinjina kai tayi amma takasa magana, Can tace "dan Allah me nayiwa Mummy? Na gaisheta dazu da kyar ta amsamim tace inje tana son ganina, Allah yasa ba laifi nayi mata ba?" "meyasa kike tunanin laifi kikayi mata?" Hawayene ya zubo daga idonta, shi Jalal har mamaki take bashi, kaman shan ruwa haka take kwararar da Hawaye, basa mata wuya sam tace "Yanzu duk lokacin dana motsa ko nayi wani abu se ansamu wanda zasuce na musu laifi, kowa ya tsaneni komai nayi laifine, mutane kalilan ne suke sona A duniyar nan, daga masu kirana munafuka, se makira, barauniya, karuwa, Arniya se masu cewa uwata ta gudu ta banni, ba ataba barina inyi awa24 cikin farinciki se an samu me batamin rai" Takarasa maganar cikin kuka muryarta na sarkewa, tasa hannunta biyu ta rufe fuskarta tana kuka me tsuma zuciya, Jalal jin kukan nata yake a kahon zuciyarsa, yaji gaba daya komai ya kwance masa, yace " Kidena kuka mana, kin manta ke kikemin nasiha amma yanzu kike kuka, Allah baya mantawa da bawansa, Allah yasan halinda kike ciki, ni da nake gabanki a yanzu na isheki misali na isheki darasi, ba'a nasara ba tareda an sha wahala ba, kisawa ranki matakin nasarar kine kike takawa, duk wanda yayi miki gori a rayuwa ko ya cutar dake kisa a ranki kinfi shine, Allah yana son bayinsa masu hakuri, semene dan duniya batayi dake in har ubangijin da yayiki yanayi dake shikenan, kiran da Mummy tayi miki karki sake kije, bashida wani amfani na gaya miki" Ya mike ya nufi wata katuwar drower ya bude, ya duba ya debo wasu takaddu yazo gabanta ya zube su yace "dauki wannan takaddun, ki dubamin abunda za'a iya nema a gurin, zanyi breakfast yanzu" Yakoma kan kujera daya yazauna ya fara cin Abincin sa daya siya dazu, Jalila tasa Hannu tana duba takaddun, duk na makarantun da Jalal yayine, abun mamaki results dinsa sunnuna shi din kwarone, kuma duk an masa kyakykyawan yabo a jikin results din, daga ido tayi tana kallonsa yana cin Abincin sa hankali kwance, ba ita yake kalloba amma taji yace "Ya dai kike kallona? Ko zakici ne?" girgiza masa kai tayi alamar A'a, tareda maida hankalinta kan Takaddun gabanta Yace "Au Ashefa bazaki iya cin Abincin hannun dan iska ba, karkije na zuba kwaya a ciki ko?" Shiru tayi masa yagama ciye ciyensa, ya mike yana kuma duba wasu takaddun, yaji muryar Jalila tace "wai Inane nan?" "Kamfanina ne?" ya bata amsa Zare ido tayi, ya kalleta yace "kina mamakine? Nawane mallakina, akan wannan dukiyar ne aka halakar da rayuwata, dukiya mugun abu me halakar da mutane, me haddasa gaba da kiyayya, me tafiya da Imanin ma'abota kwadayinta, Akan dukiya Mummy tayi cin amana tayi yaudara ta auri daddy, Akan dukiya Mummy ta ajiyeni tayi tafiyarta lokacin da nake bukatar taimakon ta, Akan dukiyar akabada kwangilar ruguza rayuwata,  Akan dukiya Mummy ta rabu da mutane dayawa, Akan dukiya da daukar fansa aka halakar da rayuwata, Ilham da mahifiyarta suna son su dauki fansa akaina ne su gaje dukiyar dana mallaka, itakuma Mummy takasa fahimta, tunda suka kyalla ido sukaga Daddy yasayi kamfanin nan yabani, suka kasa nutsuwa, ke sheda ce, Kinsha kama Ilham na kokarin samin magani a Abinci, kuma ta dade tanayi min hakan saboda dukiya, Akan dukiya....... Sekuma yayi shiru ya dafe teburin gabansa yayi shiru, gaba daya Jalila ta zuba masa ido, jin yadda yake sarrafa magana daki daki ta sigar rarrashi da wa'azi, ko a mafarki in wani ya gaya mata Jalal ze haka karyatawa zatayi. Yacigaba da cewa "Ban taba kukan babu a rayuwata ba, babu innemi abu in rasa ban taba ba, bansan talauci ba, Amma nidai wannan dukiyar da taza memin bala'i, gara ace talaka futik Mummy ta aura in tsira da mutuncina, A rayuwa bazan manta da mutanen dasuka soni dan Allah ba, family dinku mutane ne masu mahimmanci a rayuwata, kinga Jawwad na yadda in rasa duk abunda na mallaka saboda shi, Yana sona badan dukiya ta ba, duk abunda zamuyi baya sako lissafin dukiya ta, bayan Umminki da Jawwad ban taba zaton zan samu wanda ze tsaya akan lamarina ya damu dani kamar ki ba, bana manta Alkhairi, kinmin abunda banida abun biyanki, dukda bakida kunya, ga taurin kai da tsaurin ido, ga rashin kunya da iyayi, bazan manta yadda kike putting rayuwarki a risk saboda dan iska mara tarbiyya me kama da 'yan daba, dan daba yana godiya" ya karashe maganar yana kashe mata ido, Murguda masa baki tayi ta dauke kai, ya danyi murmushi yace "Ai bazaki taba canza hali ba" Ya kwashi takaddunsa ya mayar da sauran yace mata "Tashi mu tafi" ta mike tayi gaba yazo ya bude kofar suka tafi, sosai Jalal ya dingayiwa ma'aikatan nan barin kudi kaman besan ciwonsu ba. Suna cikin tafiya Jalila tace "Amma meyasa baka zama a kamfanin, at least you will keep yourself busy zaka manta da wasu abubuwan" dan shiru yayi sannan yace "Ta yaya ina cikin wannan halin zanzo inyi aiki, Akwai manager kamfanin nan dan abokin daddy ne shike kulada komai, duk lokacin danazo na zauna da sunan zanyi Aiki se wannan abun yasa meni, idan na birkice senayi barna sosai kafin in bar gurin, wani lokacin har illa nake wa wasu, shiyasa wasu ke kallon ko inada tabun hankali, kokuma illar shaye2 ne, rabona da gurin nan nafi shekaru goma, yanzun ma saboda takaddun nan nazo, kuma abun mamaki naga nashiga na fita lafiya yau saboda muna tare da ke" "To Allah ya baka lafiya, Amma yakamata kanemi magani sannan ka dinga Addu'a" Tasa hannu ta cire farin carbin counter dake hannunta ta ajiye masa tace "ka dinga Amfani dashi, ze temaka maka" Be iya cewa komai ba se kallon ta da yakeyi, har Jalila manta data bashi sekuma taji yace "Thank you" itama banza tayi dashi taki kulashi. Haka suka cigaba da dan taba hira har sukazo makarantar, zata bude tafita yace "tsaya, wai ke wannan ce jakar makarantar?" "Eh mana" ta bashi amsa "wannan ba jaka bace sekace Jakar tara kudin bara, ina litattafan karatun?" "Jakar tara kudin maulace bata bara ba" Ji yayi kaman ya tuntsire da dariya amma ya fasa, yasa hannu ya dau Jakar ya bude jotter ce se biro da kudinta dari biyar se waya, yasa hannu a Aljihunsa ya dakko kudi yasamata ya mika mata, ta kalleshi "Ni inada kudi cire abunka" "Fitarmin daga Mota ko insa lock inyi gaba dake wallahi" Hannu tasa tana kokarin cire kudin ta ajiye masa yace "Bana kyauta amayarmin, karki bari raina ya baci fita ki barmin mota, mara kunya" Ikon Allah yanzu suka taho girma girma cikin mutunci amma se wani korarta yake kaman rokarsa tayi, ta hade rai ta bude motar sannan tace masa "Allah yabada sa'a" "Ameen" ta rufe masa motarsa tayi gaba. Maama fa hankalin ta ya kai makurar tashi, idan tace zata tsananta maganar nan zata iya rasa Aurenta, dan haka ta nufi part din Abba dan ganin ta inda Zata bullowa Al'amarin, Amma ta tarar yayi ficewarsa, takoma daki tanata nazari, daga baya ta yanke shawarar gayawa Naja halin da'ake ciki, takira Naja dakinta ta sanarda ita abunda ake ciki, Amma bata gaya mata batun Abba yace tabar masa gidansa ba Aikuwa take Naja tafara ruwan bala'i "Harni za'a ciwa mutunci dan tsabar wulakanci da cin fuska, Akaimin kudin Aure in fara shiri sannan ace anfasa saboda tsabar rashin ilimi, wannan ai halin banzane da Jahilci" Maama na kokarin yiwa Naja bayani amma taki saurararta tayi ficewarta, taje ta kira Yaya mairo a waya tana kuka gaya mata, ai tun daga wayar Yaya mairo tafara surfa zagi ta inda ta shiga bata nan take fita ba ta cewa Naja gata nan zuwa gidan. Jalila test kawai tayi ta dawo gida, dan har yanzu bata jin karfin jikinta sosai tanata nazari akan Jalal, mutumin daya mallaki wannan dukiyar mezeyi da wannan Aikin? Amma akwai ayar tambaya game da Al'amuran nasa, wani lokacin har mamaki yake bata in yana abun Arziki kaman bashi ba, kuma babban abun mamakin dukda yadda Jalal yake wasa da ibasa, yake shaye2 hakan besa dukiyarsa rashin habaka ba, haka taketa tunani harta koma gida, Amma abun takaicin tana zuwa gida ta tarar da wannan rigimar da akeyi, Hakan ya tabattar mata dasu Jawwad sun dawo, muryar Yaya mairo data jiyone yasa gabanta faduwa, dan sam bata kaunar matar nan, Jalila tana ta Addu'a ta shiga palourn, ta tarar Naja tanata kuka, yayarta sa'ada tana rarrashin ta, Maama tayi zugum Yaya mairo tana sirfa mata bala'i, Jalila tayi sallama ta maze zata wuce, Gaba daya suka dawo kanta da zagi da cin mutunci da tsinuwa, ai kawai tayi kamar kujeru ne kawai a palourn ba mutane ba, ta shige daki ta canza kaya abunta, tayi tunani a ranta muddin tacigaba da zama a yanzu, zasu cigaba da zaginta ne itakuma bazata hakura ba, dan ba shiru zatayi musu ba mussaman in aka hada da cin mutuncin iyayenta, dan data san abunda zatazo ta tarar kenan da bata dawo gidan yanzu ba, ta mike tasa hijjabinta, takuma zuwa ta ratsasu a palour tayi ficewarta tana jinsu suna ita ta haddasa komai ita tayi munafunci batabi takansu ba takara gaba. Tana fita motar Abba ta shigo layin dan haka tayi murmushi aranta tace "yau gidanmu akwai drama" ta tsaya tana jiran karasowar Abba, ya karaso kofar gidan yayi parking cikin fara'a tace "Abba saukar yaushe?" Shima cikin fara'a yace "Ai tun karfe goma muka dawo, na dan fitane nayi wani uzuri" "Masha Allah, sannunku da Hanya, amma tunda na dawo ko Yaya Jawwad ban ganiba" "Ina zaki ganshi dama? Yana can farinciki ne ya hanashi fitowa Jeki aiken da'akayi miki ki dawo Akwai albishir masu yawa, babyn Ummi" Cikin murmushi tace "to shikenan bari inyi sauri in dawo" tafada cike da zakuwa, Abba ya shiga gida, se yanzu tafara tunanin ina zata? Kawai ta yanke shawarar zuwa gurin Mummy taji laifin da tayi mata, dukda Jalal ya gargadeta akan yin hakan. Tana shiga gidansu Jalal ta tarar da motarsa, abun ba karamin mamaki yabata ba, Anya kuwa yaje interview din? Ta tambayi kanta, taga moyar Mummy dasuka fita dazu alamar sun dawo, haka tayita wasi2 harta shiga cikin gidan, palourn ba kowa tayi sallama amma shiru tasamu guri ta zauna akan kujera, wata yarinya da take musu aiki tacewa dan Allah tayiwa Mummy magana, seda Jalila tayi kusan mintuna goma shabiyar sannan taga Mummy ta fito, da fara'a Jalila tace "Mummy ina wuni?" Mummy tace "rike ina wuninki, na baya da kikayi ma sun isa, Allah ya amfana" nan take Jalila ta sha jinin jikinta, Mummy tasamu guri ta zauna ta dubi Jalila a wulakance tace "Dama na kiraki naki dan inyi miki kashedi akan ďana, sannan in soke haramtacciyar alakar da take tsakanin ku" cikin rashin fahimta Jalila tace "Mummy haramtacciyar Alaka kuma?" "Eh haramtacciya mana, ko ta halatta ne? Tunda yake jin maganar ki fiye da tawa ai dole akwai abunda ke tsakanin ku, da kike masa Ilham ma sheda ce" Nan Mummy ta ware ta kwalawa Ilham kira, Ilham ta fito tana ganin Jalila ta ya mutsa fuska kaman me shirin yin amai dan taga kashi, Ilham tazo ta zauna tace "Mummy gani" Mummy ta nuna Jalila tace "gata nan nace Akwai haramtacciyar alaka tsakanin ta da Jalal amma ta karyatani" "Mummy ai kinsan ba mutunci ne da ita ba tunda bata san darajar manya ba, tarbiyya ta mata karanci" Mummy ta gyara zama tace "Ina bukatar duk wata alaka dake tsakanin ki Da Jalal tazo karshe a yau, kiyi nisa da dana, ba ruwanki dashi kome ze aikata, ai ba fina sonshi kikayi ba, a palourn nan agabana kinsha kiransa mara tarbiyya, lattace, kuma dan rashin kunya seki lallaba kina kokarin kara lalata min shi bayan abaya duk fitinarsa ba Ruwansa da mata, Amma kina kokarin kizama se abunda kikeso shi zeyi ni uwarsa ban isa dashi ba seke?" Jalila shiru tayi ta sunkuyar da kai ko tari kasa yi tayi Ilham tace " Wallahi Mummy na sha ganinsu suna rungume juna, kuma har part dinsa take zuwa dakin sa, in karya nayi ki karyatani mana munafuka, Kuma...... Setayi shiru takasa karasawa, sakamakon saka idonta da tayi a na Jalal dayake tsaye ya harde hannunsa a kirjinsa, ba Ilham ba hatta Mummy seda ta tsorata,  cikin is da Izza yace "Kuma me? Karasa mana" Zazzaro ido Ilham tafara yi, jin muryar sa yasa Jalila daga idonta sukayi ido hudu takuma sunkuyar da kai. Yakara so cikin palourn ya kalli Mummy sannan ya maida idonsa kan Ilham yace "ki karasa maganar ki ina jinki, ke dan baki da kunya har kin manta ke abunda kika dinga yimin abaya ko danni bana zuwa ina fada, wato kin manta lokacin da kike kawomin kanki har part dina in dare yayi ko?" zare ido Ilham tayi tafara kokawa da numfashi, bata taba tsammanin ze iya fadar hakan ya tona mata asiri ba Ya kakkafe Ilham da, ido yace "koba ayi bane?" kasa magana tayi se wani gumi data dinga jinsa yana ratsa cinyoyinta, ya maida idonsa ga Mummy yace "Kinji kunya, 'yar cikinki cefa, yarinyar data dingayi miki biyayyar dani da kika haifa ban miki ba, ita kikewa wannan bakaken maganganun, meye da ďannaki da za' a dinga, binsa, niba hankali ba niba tarbiyya ba, sedai abini ko asoni dan dukiya ta amma bani da abunda mace kamar Jalila zata bini sedai irinsu Ilham dabasu san ciwon kansu ba" gaba daya suka zubo masa ido, da sauri Jalila ta mike tayi hanyar fita, jin yana kokarin janyo mata bakin jini tana fita ya rufa mata baya, Ilham tace "Wallahi Mummy Jalal karya yakemin, ni ban taba kai masa kaina ba, Mummy dan Allah kisa baki ya Aureni, wallahi Asiri tayi masa" "ke dalla rabu dani niba wannan ne ya dameni ba, kina gani yake gaya min magana akanta, ashe har an samu uwar data haifi wadda zata mallakemin da, ya gayamin magana akanta? Baze yuwu ba wallahi, se na dau mataki akansa da ita kanta" Ilham ma mikewa tayi tabi bayan Su Jalal dan ganewa idonta meze faru, ayita ta kare a yau. Har suka fito harabar gidan yana kiranta taki tsayawa, seda yasa hannu ya fizgota sannan ta tsaya "Jalila meye haka? Ina miki magana kina jina kinki tsayawa, uban me yakawo ki bance karki zoba dama?" Cikin kuka tace "Dan Allah malam kadena min shouting, meye Amfanin abunda kayi? Zaka sa mahaifiyarka da kanwarka su kara tsanata, Mahaifiyarka tace batason ganina tareda kai, ko a hanya karka kara nuna ka sanni, bani ba kai, kayiwa mahaifiyarka biyayya kanemi Aljannarka, dama ba wani abune tsakaninmu ba mutunci ne da girmamawa tunda bata so shikenan " Gaba daya idon Jalal yayi Ja, a hankali yace "kince kowa yaje yayi rayuwarsa ko? Kinfison in kara komawa cikin harkar shaye2 kenan kaman yadda nake abaya? Ke Garkuwa ce a taredani me kike tunani idan kika barni, sanadiyar kasancewar ki tare dani yasa ina kara kokarin yaki da shaye2 da nake abaya, kina tunanin inkika min haka kin min adalci? " " Kayi Rayuwarka inyi tawa, yafi adinga min kallon mazinaciya, zancigaba dayi maka Addu'a a duk inda kake, Amma bani ba kai ko a hanya balle a cigaba da zargina" Tofa! Masoya kaunar da nake kumu tasa nai muku dogon page gashi nan, senaji Comments dinku love you all 😍😍😍🌹❤️❤️❤️🌹🌹🌹🌹 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣3️⃣96 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Juyawa tayi ta fice da sauri tana goge hawaye, Ilham dataga duk abunda yafaru tayi wani tsallen farinciki, amma da tuna irin tonon sililin da Jalal yayi mata dazu se taji jikinta yayi sanyi ta juya da sauri ta koma gida. Jalal bashida zabi da ya wuce ya bar gurin shima kamar wanda kwai ya fashewa a ciki yakoma part dinsa, zuciyarsa kaman an kunna masa wuta saboda bacin rai, side bed dinsa ya kalla yaga Alqur'anin nan da kuma teddyn Jalila a gurin, a hankali yace "do she really mean what she said, zata barni gaba daya, bani ba ita? Jalila why? karkimin haka mana, nasan ba'a kyauta miki ba, Amma kar laifin Mummy ya shafeni" ya zauna a gefen gadon sa ya rintse ido, ya dinga tuno moments dinsu tare, da fitar da sukayi dazu, ji yayi kansa yana juyawa zuciyarsa ta masa nauyi, ya kunna sigari yafara sha, ya sha takai kara biyar amma beji yadda yakeso ba seda ya dakko merlot red wine ya sha ya fita daga hayyacinsa sannan ya yada kwalbar a gurin shima ya zube. Ita kuwa Jalila seda ta samu guri a cikin flowers tayi kukanta ta gode Allah sannan ta nufi palourn gidan, tunda ta shiga ita dai taji Abba yana bayani yayinda Yaya mairo keta haya gaga, sam Jalila bata gane me suke fada danji take kaman zata fadi ta wucesu ta shige daki ba tareda ta kula kowa ba, tana zuwa ta haye gado ta ja blanket ta cigaba da kuka da kuma tunani, shikenan yanzu kuma kallon mazinaciya mahaifiyar Jalal take mata? Gaskiya tsakanin ta da Ilham se Allah yasaka mata, amma ba komai zata rama ne, zatayi wa Ilham daurin da bata isa ta kwance ba" Jawwad ya farka daga baccin dayake cike da farinciki ya tashi yayi salla, sannan ya nufi cikin gida dan ganin Maama dakuma 'yan kannensa dan yasan zuwa yanzu sun dawo daga school. Yana fitowa manu direba ya shigo harabar gidan da mota, ya jira manu yayi parking Nana ta fito daga motar kallo daya zakayi mata kasan a gajiye take, se jefa kafa take kawai tana ganin Yaya Jawwad ta yalwata murmushinta tareda fadin "Oyoyo mutan Bauchi, Ashe kun dawo?" "Mun dawo Nana, ya school din? Naganki ke kadai ina Jalila?" "Yaya Jawwad kasan Jalila manyan kwarine, yau bataje school ba, amma ancemin angan ta dazu ta shiga zasuyi test" "Shikenan mukarasa ciki, yau Akwai Albishir masu dadin gaske, muje in gaida Maama tukuna" suka jero tare zuwa cikin gida. Abba yace "Hajiya mairo ban yanke wannan hukuncin dan cin mutuncin ki kona zuriyarki ba, sedai dan hakan shine masalaha  ga yarona, idan baki saniba yaka mata kikara sa ido da bincike akan yaranki, Amma dana san haka abun yake, da tunda fari ban yadda da batun hada Auren nan ba, nasamawa Jawwad wata yarinyar itama Naja, taje Allah ya hadata da rabonta dan binciken danayi akanta gaskiya bazan iya bari Jawwad ya aureta ba" Yaya mairo tace "dama dai can ka shirya cin mutuncina nida yarinya ta, amma inda arziki da mutuci ita daudar gora ai a ciki ake shanyeta, koma me take aikatawa silar Auren ai sekaga ta shiryu" "Hajiya Mairo, da abunda ze yuwu ne da na hakura anyi auren nan amma baze yuwu ba, kuyi hakuri, sannan Naja ta koma gidan mahaifinta ta zauna" Maama da tun dazu batayi magana ba tace "Dan girman Allah kayi hakuri mun yadda ya auresu su biyu ma bakomai, amma idan akayi haka kaman amci mutuncin gidanmune" Abba yace "Ni ban Janye batun Auren nan dan cin mutuncin wani ba, amma da abunda ze yuwu ne dana hakura anyi, zanje in samu mahaifinta muyi maganar, dan ba dake ma yakamata muyi wannan zancen ba" Naja kam se rusa uban kuka takeyi "Dan Allah ku kyale masa dansu, sekace shi kadaine namiji, kokuma mijin gold ne? Banda kaddara me zatayi da wani Jawwad mutum sam be waye ba waishi Ustaz, dalla kidena kuka kiyi rayuwar ki kamar kowa, ki manta dashi" Sa'adah ce ke wannan maganar cikin fitsara da rashin kunya, Abba ya mike yana kokarin bar musu palourn su Jawwad suka shigo jin hayaniya yasa Jawwad yace "Abba lafiya kuwa?" "Rufe mana baki kasurgumin munafiki daga kai har ubannaka da waccan makirar jarababbiyar, kun shiga kunfita kafasa Auren yarinyata dan ku kunya tamu a duniya to ta Allah ba taku ba, Matsiyatan banza dana wofi hadda wai tabar gidan nan dadinta tanada gidan uba ba'a titi take kwana ba" Yaya mairoce ta wangale makogaro taketa zazzaga rashin mutunci san ranta, ta kalli Naja tace "Jeki kwasomin kayanki mu tafi, Nina gayamiki sekin samu wanda ya fishi, Azzalumai kawai" Maama ke kokarin kwantarwa da Yaya mairo hankali ta hanyar cewa "Yaya dan girman Allah kiyi hakuri, zan shawo kan matsalar nan, dan Allah" Naja tace "ba wani shawo kan matsala, ni bana son karya irin wadda kika saba yi, an kaimin kudi kin lallaba kun hada kai ze auri wata, kuma ana kokarin yimin sharri wallahi Allah ya isa ban yafe ba aikin banza kawai" A harzuke Jawwad yace "Wallahi kika kuma zagarmin uwa sena wanka miki mari, baza'a Aureki dinba, waze Auri mace irinki ace itace uwar yaransa, Kika kuma zagarmin iyaye sena bata miki rai" Aikuwa Yaya mairo tayi kansa ta hanyar cewa "Rufemin baki mara mutunci, har kanada bakin magana, iyayennaka ba kananan mutane bane, masu baki biyu, matsiyacin ubannaka dan Allah ya bashi Arziki ze wulakanta munida yarana" A fusace Nana tace "A'a kinga Yaya mairo dakata, ubanmu fa ba sa'anki baneba, Maama ce 'yar uwakki dan haka kuje kiyi keda ita, da kike kiran ubanmu matsiyaci ya gama muku komai, dawainiyar ku ba wadda baya dauka yayi muku rana, da tsiyar tasa da kike fada ya muku rana ya maganta muku abubuwa dayawa, meye ba' ayi muku a gidan nan, wani abunma ku sata sann......... "Ke Nana rufemin baki, Yaya mairon Sa'ar kice? Maama ta katse ta, Jawwad juyawa yayi ya fice, dan a rayuwarsa baya son tashin hankali sam, Nana tace "Allah sarki Jalila baiwar Allah, dukda abubuwan dakike mata Maama nasan Jalila bazata taba kallon tsabar idonki takira ki da makaryaciya ba, yau sega wanda kikeso din suna zagin ki, dama Allah ai ba Azzalumin sarki bane, musamman Naja tazo gidan nan danta kori Jalila, ga reshe ya juye da mujiya ai, bata kori Jalila ba, bata auri Jawwad ba kuma ita an koreta" Nana tai wucewarta zuwa daki ta barsu a tsaye cirko2 suna cigaba da masifa. Nana na shiga dakin ta tarar da Jalila ta kima bargo akanta tanata bacci duk hayaniyar nan baccinta take, Nana ta tatttaro kayan Naja ta fito mata dasu palour ta ajiye, Tace "ga kayanki nan, daga nan bama bukatar ki a dakinmu" Ta juya takoma daki tasa key, ta barsu da Maama a gurin. Jawwad sam ransa ba dadi, bangare daya yana cikin farinciki, bangare daya kuma ransa a bace yake ya tafi dakin Jalal domin suyi hira, yagaya masa halinda ake ciki, Amma abun haushin yana zuwa ya tarar da gogan yayi mankas baccin sa kawai yakeyi, dan dafe kai Jawwad yai ya zauna ya tattare kayan shaye2n gefe daya, ya zauna a gefen gadon Jalal, yana kallonsa garin da dan sanyi sanyi ga fanka ga A. C Amma Jalal gaban goshinsa se zufa yake, Jawwad ya dan girgiza kai, tareda fadin "Allah ya shirye ka dan uwa" sannan yasa hannu ya daddaki pillow da Jalal yake kai, a hankali Jalal ya bude ido ya saukesu akan Jawwad ya mayar ya lumshe idonsa, Jawwad yace "Jalal ka tashi kai salla" dan karamin tsaki Jalal yayi yace "nika kyaleni please" "haba Jalal bakayi salla ba, ka daure ka tashi mana" Juyawa Jawwad baya yayi ya rungume pillow se ya tuna maganar Jalila "Inkaana Ibada, kana Addu'a Rage wasu Abubuwan" Sekuma ya danyi juyi ya mike da kyar yaje yai wanka da Alwala yazo ya gabatar da sallar Azahar da la'asar, fuskar nan tasa murtuk kaman be taba dariya ba. Jawwad ya dinga masa hira yana bashi labarin abubuwan da suka faru a Bauchi, da dramar da aka gama yi a gidansu yanzu, Amma se ya lura sam hankalin Jalal baya kansa yayi zurfafa a tunani ne, lokaci zuwa lokaci ya kanyi tsaki. Jawwad yace "Jalal wai me yake damunka ne? Ina ta magana hankalin ka baya kaina, se faman tsaki kake, menene?" Ajiyar zuciya Jalal yayi sannnan yace "Bakomai don't mind me" "ban yadda bakomai ba, ka gayamin please" "Am serious bakomai, kawai yanayin ne bayamun dadi" "to Allah ya sawwake, Amma Jalal kwana biyu ina ta murna ka dena zuwa club, shaye shayen ma kaman ka dena amma nazo na tarar kasha giya, haba Jalal why" Dan shiru Jalal yayi dan yanajin muddin baze rabu da wannan damuwar ba akwai yuwuwar yakoma ruwa tsundum, dan maganganun Jalila sunyi matukar tasiri a zuciyarsa, a fili yace "Am sorry Jawwad, ina bakin kokarina, kasan wani lokacin halinda nake shiga idan ban shaba, Amma Insha Allah very soon zan dena gaba daya" "to Allah ya amince" Daga nan Jawwad ya lallaba Jalal ya jashi suka fita zaga gari da nufin ya debe masa kewa. Seda aka gama wannan tarzomar aka gama su Yaya mairo suka tafi sannan Allah ya nufi Jalila da tashi daga baccin da take, ta kalli Nana tace "Nana meyasa baki tasheni ba? Gaskiya na sha bacci tunda na dawo na kwanta se yanzu na tashi" Nana tace "Mhmm ke kinta bacci bakisan drama da'akayi ba yau" "Tame fa?" Jalila ta tambayi Nana irin bata san meyafaru ba, Nana ta labarta mata komai, Jalila ta jinjina kai ita babban abunda ya bata mata rai be wuce yadda Nana ta gaya mata irin cin mutuncin da suka dingayi wa Abba ba, hatta zagin da sukayi wa Maama yabata mamaki, bata taba zaton zasu yiwa Maama hakaba saboda yadda take kyautata musu. Nana ta gayawa Jalila cewar tunda Abba ya shige daki da wannan abun yafaru ko Abinci be ciba, ba karamin tausayin Abba ne yakamata ba takara tabattar da Yaya mairo daga ita har Yaranta basuda tarbiyya dan haka Jalila salla kawai tayi ta shiga kitchen ta dora Abincin dare saboda Abba ya samu yaci. Sunkuma waya da Ahmad ya gaya mata yauma tayi hakuri abubuwa ne sukayi masa yawa shiyasa baze samu zuwa ba, Jalila ta karbi uzurinsa saboda yanayin aikin nasa. Jalila ta shirya Abinci me rai da lafiya, bayan sallar magariba ta kaiwa Abba nasa har daki, Amma da mamakin ta ta same shi cikin fara'a, yace "'yar gidan Abba Girki akayi min haka ne?" "Eh Abba, gashi nan kaci ka koshi sannan inzo inji Albishir din da zakayi min" Yai murmushi yace "Ai Albishir din bana kine ke kadai ba, ki kira womin sauran' yan uwanki muci Abincin tare" "to shikenan Abba yadda kace haka za'ayi" Haka kuwa akayi taje ta kira Nana, ta wuce dakin Jawwad dan kiransa, Amma Jawwad yanata rubuce2 shikuma Jalal yanata babbakawa cikinsa hayaki. Dauke kanta tayi kaman bata ganshi ba tace "Mutanen Bauchi, Yaya Jawwad ko kanemeni ko?" Haka nan jin muryar ta yasa gaban Jalal faduwa har yake kokarin boye sigarin hannunsa Jawwad yace "nina isa, dazu na shiga cikin gidan amma na tarar ana fitina shiyasa na tafi" "to shikenan, Abba yace in kiraka duk tare zamuci Abinci saboda Akwai Albishir daze mana" Jawwad yace "Allah Auta, wane Albishir zeyi mana?" "Ahh kajika ai kai yakamata in tambaya, tunda tare kuka dawo" "to shikenan gani nan zuwa" Jalila ta mike ta fice, Sam Jalal beji dadin wannan dauke kan da tayi masa ba, Jawwad yace "Jalal zo muje" "A'a jeka seka dawo" Jalal ya bashi amsa, Jawwad yace "Wallahi baka isaba, tashi muje, Abban bakonka ne? Yakamata muje tare" Jawwad ya takurawa Jalal, badan yaso ba ya bishi, suna shiga palourn Abba Idon Jalal akan Jalila yafara sauka, tana sanye da riga da skirt na Atamfa, kaman ajikinta aka dinkasu cif dasu, tayi parking din gashin ta, ta kashe dauri ba kwalliya a fuskar ta amma tayi kyau matuka, bata kalli inda Jalal yake ba suka cigaba dayiwa Abba surutu ita da Nana, Su Jalal suka Zauna, Jalal suka gaisa da Abba, Abba yace Jalila zubawa su Jalal Abincin mana" Ba tace komai ba ta fara zuzzuba musu Abinci, dakin yayi shiru suna Cin Abinci se surutun Nana dake tashi, gaba daya Jalila takasa sakewa taci Abinci saboda tsabar kallon da Jalal yake mata, bakowa ze gane ita yake kallo ba amma ita tasan ita yake kallo, shi kansa ba iya cin Abincin yake ba jujjuya cokali kawai yakeyi, Jalila tace "Abba ka gayamana Albishir din naka, nifa duk na kagu inji" Abba yayi murmushi ya kalli Jawwad yace "Jawwad gaya musu mana" sunkuyar da kai Jawwad yayi yana murmushi, Abba na yayi murmushi sannan yace "Na canza maganar Auren Naja da Jawwad, zuwa Jawwad da Hanan, nan da wata hudu Insha Allah" Wata irin Ajiyar zuciya Jalila tayi, Nana tace "dama ni zuciya ta tabani, Masha Allah, Allah yasanya Alkhairi ya nuna mana lokacin" Jalila tace "Abba ni na rasa abunda zance gaba daya, mungode Allah daya sa ka gano abunda nake ta maka nuni, Abba Allah yasaka da alkhairi wannan aini akayiwa ga Yayana Kuma 'yar uwa ta, Amma shine Yaya Jawwad baka gaya mana ba, itama Hanan bata gayamin ba" Abba yace "Itama Hanan din bata sani ba ai, daddynta be gaya mata ba, sannan babban Albishir na biyu shine; Kakar Hanan itace yayar mahaifiyar mu, Inna Asma" au" Da Sauri Jalila ta waiwaya gurin Jalal dan in bata manta ba sunyi zancen da shi, amma kawai ta basar tace "Abba tunda naje tabani Labari nayu tunanin hakan, Amma nayi shiru ban fada ba saboda bani da tabbas, godiya ta tabatta ga Allah" Jalal yai karfin halin cewa "Abba kaga yadda Allah ke juya lamarin sa, a baya kayi ta bulayin neman danginka, ashe suna tare da kai baka sani ba, ina tayaku farinciki Abba, Allah yakara hada kan iyalanka" "Ameen Ya Allah ABDUL JALAL, Amma naji dadin wannan Addu'ar taka, kuma zance ka gaskiya ne, na dade ina bulayin nemansu amma ba zato ba tsammani na samesu ta silar 'yar Auta ta" Sukayi murmushi gaaba daya. Abba ya dora da cewa " munyi magana da daddynka, Jalal ranar Asabar Insha Allah zasu kawowa Mahmud kudin Aure, suma tareda na Jawwad za' a hada, gaskiya zanso a hada da naka, yadda kuka taso tare ga aiki ya samu kamata yayi a hada da kai gaskiya" Dan guntun murmushi Jalal yayi wanda iyakarsa lebensa yace  "Abba Jawwad dai yayi, nikam se yadda Allah yayi, babu uba nagari da ze bawa ďan shaye2 auren 'yarsa, koda za' a bani saboda dukiya ta ne" Gaba daya tausayinsa seda yakama su Abba yace "karka damu kaji Jalal, babu wanda ze hanaka 'ya, kai mutumin kirki ne, wanda ya zauna da kai ne ze gane hakan, Insha Allah komai ze wuce, ka cigaba da Addu'a sannan ka dinga kokarin ka dena shaye2, babu abunda ze hana abaka' ya Aure" jinjina kai Jalal yayi yace "to shikenan nagode Abba" Nana ta dan zumbura baki tace "Abba wai meyasa baza'a hada dana Jalila bane?" Abba yace "Saboda ban gaji da ganinta ba" "Auni ka gaji da ganina kenan?" Nana tai maganar kaman zatayi kuka. Abba yace "A'a Munyi maganar da Babanta, yace; Abari ta kammala karatu tukuna saboda yanayin Aikin Ahmad din, nan da shekara daya ne zata kammala in Allah yasa zamu gani itama zan Aurar da ita ga Ahmad" Gaba daya kunya ta kama Jalila ta mike tace "nikam seda safenku Abba" ta mike da sauri ta bar palourn, gaba daya Jalal ji yayi kaman Abba ya masa yayyafin wuta a kirjinsa, shima ya mike yai musu seda safe. Haka suka watse daga palourn Abba, babu wanda yabi takan Maama balle susan halin da take ciki, ta kule a daki ta rasa abunda yake mata dadi, bata taba zaton yaran yaya mairo zasu iya zaginta ba, gashi mijinta da yaranta ma sundena shiga harkar ta suna fushi da ita. Koda Jalal ya shiga gida, part din Daddy ya tafi, yana zuwa kaman wani karamin yaro ya tarar da daddy yana aiki akan system, Mummy na gefe suna hira, yana zuwa ba tareda ya cewa kowa komai ba ya zauna kusa da daddy ya kwanta akan cinyar sa yayi shiru kaman mara lafiya. Daddy yace "Jalal lafiya kuwa?" Jalal yace "daddy Anmin screening da interview, an turani Lagos zanyi wata uku acan, Jawwad ze tafi nasa gurin Aikin next week Monday " Daddy yace "Eyya shiyasa ka damu haka? Kayi hakuri kaji yaron kirki, yasa haka shine mafi Alkhairi a gareku" Mummy tace "nifa gaskiya bana son wannan aikin da zeyi, meya nema ya rasa da ze tafi wani yawo daban" Mikewa Jalal yayi tareda yin tsaki yabar dakin, ya koma Part dinsa, koda ya koma ya sauya kaya ya kwanta domin yayi bacci amma abu ya ga gara, juyi kawai yakeyi idonsa ya bushe, ta shi yayi zaune ya kurawa teddy dinta da carbin da ta bashi ido, abubuwa da dama na masa yawo a kwakwalwa, Espicially lokutan da sukeyi tare, yana kallon teddy ya tuna lokacin da take rike da teddy ga sweet abakinta tana dariya, yana tuna tsiwarta, kwarin gwiwa, tausayinta, nasiha da murmushinta, ya tuno maganganun Abba dazu wai za'a Aurar da ita ga wani AHMAD!!! gaba daya yaji kansa yana juyawa, yazama dole ya nisanta kansa da duk wani abu da zazesa ya dinga tunata, Baze manta Alkhairan ta ba, tunani yakasa barinsa dan haka ya mike ya fice daga gidan gaba daya. Jalila ma juyi ta dingayi tana tunani da tausayin Jalal, tabbas Jalal abun tausayi ne, yana bukatar me jansa a jiki musamman yanzu da Jawwad zeyi nesa dashi, tana fargabar yakoma shaye2 kamar da, Amma a yanzu bazata iyayi masa komai ba, dan gudun kuma fadawa mummunan zargin da mahaifiyarsa ke mata. A takaice se gefin Asuba bacci ya dauke ta Jalal be dawo gida ba se Asuba, yaje club ya kwana yana shan giya, seda yayi mankas, da Asubar ma bata sake shi gaba daya ba ya dawo gida cike da maye. Yau tun bayan da Jalila ta dawo daga school, tayi waya da Ahmad ya gaya mata yau zezo, dan haka se shiri take domin tarbarsa. Jalal tunda giyar ta sake shi, yai wanka ya shirya kayansa daze bukata a Akwati, yaje cikin gida yai sallama da Daddy, yaita saka masa Albarka tareda fatan Nasara, tunda Ilham taji batun yasamu Aiki ta hanyar Jalila, kuma zeyi wannan tafiyar akan Aikin, hankalin ta ya tashi, wai se yayi wata uku acan, to in baya nan tayaya zata cigaba da gudanar da aikinta akansa?. Karfe biyar yagama shirinsa, saboda Jawwad ne ze kai shi Airport, ya sa hannu ya dauki teddyn Jalila da Alqur'anin nan da kuma carbin data bashi, ya nufi gidan su Jawwad, saboda so yake ya nesanta kanshi da dukkan wani abu daya shafe ta. Amma abunda yayi tozali dashi bayan ya shiga gidanne yasa yaji tamkar jijiyoyinsa sun dena harba jini yadda yakamata. Autar Ummi wato Jalila ya gani tayi kwalliya cikin wani dankareren leshi, tayi kyau matuka suna hira da Ahmad, kai da gani suna cikin shaukin soyayya, Jalal yaji wani Abu ya tsarga masa tun daga kansa zuwa tafin kafarsa, kirjinsa yai masa nauyi matuka A hankali yafara jan kafarsa dayake ji tamkar ba nasa ba ya nufi inda suke. Idonsa Akan Jalila har ya karasa inda suke, Jalila ce tafara daga kai tana kallon sa, gani tayi kamar ya danyi rama, yana zuwa Ahmad ya miko masa hannu da nufin su gaisa, kawai Jalal ya daga masa hannu, ya zubawa Jalila idanunsa da sukayi jawurr wanda yasa hantar cikinta kadawa, Ya ajiye mata Alqur'anin, a gabanta da teddyn, ya juya ya nufi hanyar fita Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what's App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry. Ina godiya da kulawa. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Watpad @Ayshercool7724                                                🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣4️⃣97 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Shiru Jalila tayi ta kalli kayan daya ajiye mata sannan tabi bayansa da kallo har ya fice daga gate, din shiru tayi ta tafi tunani, Ahmad yace "my queen, meya farune?" Da sauri ta dawo hayyacinta tace "bakomai fa" "Amma waye wanan?" ya tambayeta yana me kureta da ido, ta dan sauke numfashi tace "Yaya na ne" "Yayanki queen, ba Jawwad ne kawai Yayanki ba?" "Abokin Yaya Jawwad ne, dan haka Yayana ne kawai" "Amma babu wani abu a tsakanin ku kuwa?" "Meyasa kake min wannan tambayar? Ko baka yadda dani bane?" "Ahh haba waneni ince ban yadda da gimbiyata ba, ina so ne in tabattar da abunda ke tsakaninku, dan da idonsa yana shaye2" Ba karamin haushi maganar Ahmad ta bata ba, kenan shima yanayi, in ba yanayi ba, ba abunda idon Jalal yayi dayake nuna yana shaye2, dan haka tace "baya shan komai, kawai bashi da son magana ne, baya kula mutane" Kyaleta Ahmad yayi yaga alamar bata son zancen suka cigaba da hira, Jawwad ne ya fito ze wuce su Jalila ya tsaya suka kuma gaisawa da Ahmad dayake dazu sun gaisa, Jawwad yace "to sirikina zan iya ce maka se anjima, ni zan tafi kai Jalal airport ne" Da sauri Jalila tace "Ina zashi?" Jawwad yayi murmushi yace "Aiki mana, an tura shi Lagos, se lokacin biki inaga ze dawo, bari inje karyai ta jirana, kin san baya son jira, se anjimanku" Sukayi sallama da Ahmad ya fita. Ahmad ya maida idonsa kan Jalila yace "Gimbiya naso a haďa bikin nan hada namu, na kagu in mallakeki" Murmushi kawai tayi amma hankalinta baya kansa, tanata zancen zuci ne, dayaga haka yace "queen naga kaman Akwai abunda yake damunki, bari in tafi semunyi waya" Ta mike ta rakashi har bakin gate sannan ta dawo ta zauna akan kujerun tana nazari "At least yakamata ace sunyi sallama da Jalal, tayi masa nasiha, Amma bata tunanin zata iya kuma rabarsa ba saboda mahaifiyarsa. Jawwad ya ga sam fuskar Jalal a daure take, babu alamar walwala ko fara'a, Jawwad yai masa magana yafi a kirga, amma ko daya be bashi amsa ba, dan haka ya kyleshi suka cigaba da tafiya a haka kaman kurame. Gajiya Jalila tayi da zaman tunanin ta mike ta tafi cikin gida, Nana tana zaune a palour suna waya da Mahmud, "Nana waike dan Allah ba kya gajiya da wannan wayar ne? Kuyita surutu tun ana fadar gaskiya se an koma fadan karya" Nana taki kula ta seda ta gama wayarta sannnan tace "waike Baby an gaya miki kowa irin kine me tsarin tsiya, ke yadda ba kya son yawan waya kowa ma hakane, ai a rana inji muryar Mahmud sau hamsin bazan gajiba, musamman mu da muke distance relationship, ai Ahmad din nan ma ban wani yadda kina sonsa ba" "Inasonshi sosai, amma hakan bashi ke nufin a dinga uzzuramin da surutu ba" "Hajiya Jalila, kyaji da shi dai" Hanan ca ta kira Jalila a waya, ta daga tasa a kunnenta "hello Baby, 'yar uwata rabin jikina ashe Family dinmu daya Baby? Narasa inda zan sa kaina dan farinciki, dazu Abba yake gayamin kuma wai an kawo kudin Aurena da Haidar, Baby na rasa me zanyi dan farinciki" Murmushi Jalila tayi tace "na riga ki ji ai, kiyi Azumi ki godewa Allah" "queen na rasa inda zan saka raina dan farinciki, daddy yace zasuzo karbar kudin Nana, narasa yadda zanyi dan murna" "haka Al'amarin ubangiji yake Hanan, yana juya komai yadda ya so" "Hakane Queen, amma naji haushi da baza'a hada da nakiba, ni ina Jalal ne ma?" "yaje interview din nan ai, an turashi lagos zeyi wata uku" "Allah sarki bawan Allah, wallahi Jalila bana kaunar Aurenki da Abokin Yaya Yusuf din nan, in duniya da gaskiya Jalal ya kamata ki Aura" Wani dogon tsaki Jalila tayi ta kashe wayarta, dan bata son Hanan ta bata mata rai. Jalila ta mike har zata bar palourn taga Maama tazo ta wuce kitchen, gaba daya Jalila bata jin dadin yadda kowa ya fita harkar Maama, dukda abubuwan da Maaman tayi mata, Akwai lokutan da ta kyautata mata, dan haka taga be dace ta mata hukunci da laifin da take mata ba, dan haka tabita kitchen din, Maama na kokarin kunna gas Jalila tayi maza taje ta karbi lighter tace "Maama kawo in kunna miki, me zaki dafa?" "barmin Abina zanyi" "A'a Maama, tunda ba abunda nake ki barshi in dora miki" Jalila ta karbi lighter ta kunna gas, dan jimm Maama tayi tana Kallon Jalila, yadda Jalilan ke Acting kaman Maama bata taba yi mata wani abu na bacin rai ba. Jawwad suka isa airport yayiwa Jalal Sallama amma ya amsa masa a ciki, sam baya walwala, yasan halin Jalal baya son takura, tunda be niyyar gaya masa meke damunsa ba, ya ja Akwatinsa yayi gaba yabar Jawwad. Haka Jawwad ya taho yanata tunanin me akayiwa Jalal yake wannan bacin ran haka? Bayan Jalila ta gana yiwa Maama girki, ta koma daki, ta dauki Alqur'anin nan tana ta jujjuyawa, Kamshin turaren Jalal yakeyi, hakama dan teddyn ta, tasa hannu ta ta dinga duba Alqur'anin nan page by page, amma sam bata ga komai a ciki ba, kodai Jalal dama yana son raina mata hankali ne kawai? Shiru tayi ta tuna yadda taga yana yinsa bayan ya gansu tareda Ahmad, Fuskar nan tasa a daure babu alamun sassauci, tayi shiru ta cigaba da zancen zuci, ;yanzu ze tafi lagos bashi da kowa a can, babu me kula dashi, Allah kadai yasan meze aikata, "kinfi so in cigaba da shaye2 na ko? Ke Garkuwa ce a gareni" ire iren wannan maganganun nasa da Maganganun Antynsa da take gaya mata tabata amanar Jalal ne yasa take tunanin Anya hukuncin data yanke yayi dai2 kuwa? To Amma nikuma mutuncina fa? " gaba daya ta rasa me yakamata tayi? Yanzu tana gaya Hanan, tasan Hanan zata canza mata magana tafara kawo wani abu daban, dan haka tabar Abun a ranta ta cigaba da Yiwa Jalal Addu'a. 'yan kwanakin nan sam Abba ya dena shiga harkar Maama, har gara Jawwad ma yana zuwa gaisheta, Nana kuwa seda Jalila tasata a gaba ta nuna mata be dace ba abunda take yiwa Maama, wannan abunda yafaru tsakanin ta da Abba ne da kuma' yan uwan ta, sannan ta samu Nana ma take shiga sabgar Maaman, Abba ya gayawa Maama ranar Lahadi zasuyi baki, za'a kawo kudin Auren Nana, abakin su Nana taji batun haduwa da 'yan uwan Abba a Bauchi, ba tayi mamaki sosai ba jin ance su Hanan' yan uwansu Abba ne ba, sakamakon matukar kamannin dake tsakanin Jalila da Hanan, sedai taji haushin rashin sanar da ita da Abba beba. Tun ranar Juma'a suke shirye2 domin bakin daza'ayi, Jalila ce jagorar girke2 da shirin yadda za'a karbi baki. Gefe guda Jawwad yana ta shirye2 Ranar litinin shima ze tafi gurin nasa Aikin, ba karamin kulawa Hanan take bashi ba, da soyayya da kuma shagwabarta, yanayin yadda take nuna yarinta  a wasu bangaren ba karamin birge shi yake ba. Kamar yadda aka saka ranar lahadi daddyn Hanan yazo Kano aka karbi kudin Auren Nana, itama lokaci dayane dana Jawwad dakuma Abdallah Yayan Hanan, ranar har mutan bauchi seda sukazo garin kano karbar kudin, da kuma kara taya juna murnar haduwar su a matsayin 'yan uwa. Jalila taji dadi da akazo hadda Hanan da Mummynta, Maama seda ta sha jinin jikinta ta raina kanta ganin manyan mutanen da sukazo gidan, Abun Arziki ya hadu dana Arziki, dangin Su Jawwad dana Su Jalal, Ranar anci ansha, kai ka dauka bikin Aure akeyi rana ce me matukar tarihi da wannan Ahali bazasu manta ba. Jalila sam bata samu kebewa da Hanan ba, saboda Hanan na manne da Jawwad, sam bata jin kunyar kowa take nuna masa soyayya. Mummyn Hanan se mita take tace "Ni gaskiya naso a hada abun nan hada na Jalila, in aurar da 'ya' ya uku, amma in shirya da kyau, amma bakomai anata se nafi shiri ko Jalila?" Ita dai Jalila sedai tayi murmushi ta sunkuyar da kai. Duk yadda Maama take jin kanta take kuma jin haushin Auren Hanan da Jawwad boyewa tayi, Saboda sam bata da makusa, 'yar dangi ce, kuma' yar uwar dan tace, tana da kyau dai2 gwargwado kuma tana da Ilimi, yanayin kyau da gayun mahaifiyar Hanan ya isa ya nuna maka 'yar ta ma hakan take. Koda ta hasko Naja seta ga abun se A hankali, kuma tun abun nan da sukayi mata ta tabattar da Ko Auren akayi Naja zata iya wulakanta ta. Da ire iren wannan tunanin yasa ta ajiye duk wani bacin rai aka shiga hada2. Tareda tsara yadda suke ganin bikin ze kasance, Ba laifi Mummyn Hanan ta saki jiki Maama, Sunyi hira sosai kaman sun saba, sannan suka tattauna akan yadda harkar bikin yaran nasu ze kasance. Se la'asar Suka tafi, mutanen Bauchi suka tafi, Su Hanan ma a ranar suka juya kaduna saboda Su Hanan suna jarrabawa, su kuwa danginsu Mahmud, suna kawowa Mahmud kudin Aure sukaci Abinci suka juya Borno. Wasa2 sosai tunanin Jalila ya hana Jalal sukuni, da yafara aiki in ya tuna da ita gaba daya se yaji duniyar tayi masa zafi, yarasa inda zesa kansa, meyasa Mummy tayi masa haka? Idan yaji abun ya dameshi se ya tafi club yaje ya cika cikinsabda giya, dukda wasu lokutan yana bawa aikin da yaje yi mahimmanci, Sam Jalal bashi da sakewa da mutane, dan haka be saba da kowa ba, sedai yana girmama shugabanninsa na gurin aiki, girmamasun da yake besa sunga alamar ze bari su taka shi ba, inda yake burgesu yana maida hankali akan aikinsa sosai. Duk lokacin da yaje Club mata da suke damun sa ne ga kuma shigar tsirara da suke yasa shi dakatar da kansa ga zuwa Club, idan yaji ba yadda zeyi se yayi shaye2 se yayi abunsa a dakinsa na hotel da yake ciki. Amma duk da haka yarasa dalilin da yasa mata ke binsa, sedai in baze fito ba. Hannah ce zaune akan kujera tana kwalliya, Sa'ada na kwance akan gado tana danna waya, dan dakatawa da kwalliyar Hannah tayi ta dan kurawa madubi ido, sekuma can ta daki kan mirror tace "Impossible baze yuwu ba wallahi" Sa'adah ta waigo ta Kalle ta tace "lafiya kuwa?" "Akwai matsala Sa'ada" Hannah ta bata amsa "matsalar me fa?" "Sa'ada ki kalleni ki kara, kimin kallon tsaf tun daga sama har kasa, ki kalli yadda nake gara kan maza, in taka wanda naso in wanke wanda naso, amma a hakan har rububina wasu suke, in sauke Ajina in cewa Jalal idan ya Aureni zan dena bariki, Amma ya watsa min kasa a ido" Wani dogon tsaki Sa'ada tayi tareda fadin "Nina dauka ma wani mutumin kirkin ne, A she akan wannan mashayin ne, ni ba wannaan ya dameni ba a yanzu" Hannah tace "Mutumin kirki ne mana, ki kalleshi kallon tsaf Sa'ada Namiji ne irin wanda duk wata mace zatayi burin Aure, shaye2 ne kawai matsalar sa, da farko da nakewa su Jeje aiki, nna zata zan samo kansa ta sauki ya yadda dani, Amma duk wata dabara da kisisina ta matan bariki nayi amma yaki amincewa dani" "to kibi wani mana, ko shine kawai namiji?" "bazaki gane ba Sa'ada, bakiga irin kirar da Allah yayi masa bane, kuma da kike ganinsa a haka, dukiya ce dashi kaman abun banza" "Ya akayi kika sani, nasan dai babansa yana da kudi, amma shikam ko aikinyi ba shida shi" Sa'ada tayi maganar tana yatsina fuska "Hmm to wallahi har ki mutu in ba wani ikon Allah ba, kaf danginku daku da abunda kuka mallaka, bazaku kaishi dukiya ba, yana da kudi da mahaifinsa yasa ake juya masa, Jeje yaso ganin bayan dukiyar nan shida mai gidansa amma abun be yuwu ba suka kare a prison" Sa'ada ta tashi zaune tace "to ke yanzu meye abunyi, ni ban taba sani ba, kin san ya taba kusa tonamin Asiri ina zuwa club agaban babarmu" Dariya Hannah tayi tace "Abune mawuyaci ya tona miki Asiri, bar ganinsa a haka, yasan abunda yakeyi, naje har gidansu na dana masa tarko, amma ga dukkan alamu ya tsallake shi, wannan karon zan masa tarkon da zan rike shi a wuya, be isa ya kuma subuce min ba" "Yakamata kam, Amma ni nan tunanin yadda zan huce abunda abokinsa Jawwad yayiwa Naja nake, kiri2 yafasa Auren ta, yarinyar nan duk ta shiga damuwa" "Allah sarki, to wai ya'akayi aka fasa Auren? Waye yaje yai mata gulma a gurin baban nasa?" "ya za'ayi in sani, Amma da nafi kyautata zaton wannan munafukar kanwar tasa ce" "Wace kanwar tasa ya'akayi tasan abunda Naja take? Ko dai itama tana ta bawa?" "Ke bari, wata yarinyace yadda kika san boka haka take, ni dai ban san tana wani biye biye ba, Amma kina zaune in taso seta nemo waye ubanki koda ke baki sani ba, wai ita Jalila makirace ta bala'i, idan tace bata san abu seta ga bayansa, tasa Jawwad ya fasa auren Naja se kawarta" Jin an ambaci Jalila yasa Hannah zare ido tace "Kan bala'i ai nasan wannan yarinyar, tabdijan ni zan gaya miki makira ce, ke wallahi keda kike bariki tafi ki iya rashin mutunci, ke zata iya yuwu wa ita tasa aka hana, bari in gayamiki yarinyar nan tafiki bala'i, dan koni tasa min ido akan Jalal, ita take rusa min komai " Cikin mamaki Sa'ada ta kalli Hannah tace" wai kin santa ne? " " Nikuwa na santa, kuma nasan illar ta, munyi Arranging da Jeje mun gama komai, zamu sace Jalal ranar birthday din sa, idonta na kanmu, muka bugar da shi da giya ta shammace mu tasa aka dauke shi daga gurin, ke ina jin kishin cewa ita tasa aka kama Oga KB" Zaro ido Sa'ada tayi cike da mamaki tace "Ke haba dai? Shikuwa oga KB yana me,duk iya kuri da gadarar rashin mutuncin nasa, yarinya ce fa karama" Hannah tace "hmm ke dai bari, mace kenan, kaidin wata yafi wata, irinsu kuma sa'a ce dasu a rayuwa, kibi a sannu kawai" "Tabdijan amma babu kama, dan bakiga cin mutuncin da muke mata ba mu da babarmu, kin san uwarta tsohuwar arniya ce, bakiga cin mutuncin da muke mata ba" Hannah tace "Yawwa kuma ga cin mutuncin da tayi muku nan, kuma ta gama daku ba" "Sosai makuwa ta gama damu" "shiyasa wannan karon shirina ita da Jalal ne, dan bana ta wannan Ilham din dan wannan ba mace bace, wannan tafi hatsari, baze tsallake wannan tarkon ba a yanzu, na duba mashayar da yake zuwa ba adadi amma ance ya dena zuwa, duk da haka zan nemoshi" Yauma duk da tarin farinciki da Jalila ta tsinci kanta a ciki yau, amma bacci ya kauracewa idanuwanta, jikinta na bata Jalal yakoma shan giya, da kyar ta samu bacci ya dauke ta, amma mafarkin Jalal a cikin wani yanayi na shaye2, yasata farkawa, gabanta na wata irin mummunar faduwa, wayarta ta dakko ta duba karfe biyu da rabi na dare, ga shi ita ba lambar Jalal ce da ita ba, tarasa mema zatayi gallery dinta ta shiga tana dubawa, tsofaffin ajiyayyun hotunan ta take dubawa, hotunan da sukayi da Jalal tun wani zuwa da Hanan sukayi, haka taita kallon hotunan, a haka har ta kawo kan hotunan birthday dinsa, cin karo tayi da wani hoto da'akayi harda Hannah a ciki, take gaban Jalila ya fadi, dan sam ta manta da Hannah, kuma barin Hanna ba tareda daukar wani mataji ba tamkar kashe maciji ne ba'a sare kansa ba a rayuwar Jalal. A hankali ta ajiye wayar, ta sakko daga kan gadon ta shiga toilet tayi alwala tazo ta tada salla. Ranar litinin Jawwad shima yayi nasa shirin tsaf domin tafiya Gurin nasa aikin dake birnin tarayya, Abba yayi masa Nasiha sosai tareda sa masa Albarka, haka ma bangaren Maama, tayi masa Addu'a da sa Albarka, dukda marin da Maama tayi masa akan Naja, hakan besa ya nuna mata har yanzu yana fushi ba, Bangaren Jalila kuwa har kuka tayi, saboda zatayi kewar Yayan nata sosai Abba yace "Jalila kina kuka dan zeyi tafiya, kuda kwanan nan zeyi Aure gaba daya zasu bar gidan, su barki seke kadai" Kara fashewa da Kuka Jalila tayi, Nana tace "Abba ka gani ko? Wannan yar taka ta fiye shagwaba wallahi" Jawwad yace "haba babyn Abba, sekace ba jaruma ba, zan dawo ai kidena kuka" Sukayi ta tsokanarta ita kuwa dagaske take kukanta. Haka sukayi sallama da Jawwad shima yakama hanyar tafiyar sa. Jalal yana waya da daddyn sa sosai, sannan suna waya ds Jawwad, suna shirye2 yadda biki ze kasance a tsakanin su. Abban su Jawwad yana kasuwanci ne a tsakanin Kano da lagos, dan haka in yaje suka haduwa da Jalal. Jalila Nason sanin halin da Jalal yake ciki, amma babu wata hanya da zata san hakan, dan haka taketa kokarin boye damuwarta. Maama Allah ya temaketa Abba ya sakko daga fushin dayake da ita, sannan tunda abun nan ya faru Su Yaya mairo ko a waya basu kara neman Maama ba, abun ya dameta sosai dan haka ta shirya da kanta taje gidan su. Tunda tayi sallama suka amsa suka shareta suka ki kulata, ita tayiwa kanta gurin zama, ta gaida Yaya mairo amma taki kulata, seda ta bata 'yan kayan data saba kaimusu, shine Yaya mairo ta dan saki rai suka gaisa, Naja ta gani a lullube tana bacci, Maama tace "Yaya, Naja ba lafiya ne?" Kafin Yaya mairo ta amsa Naja ta fara magana cikin maye "Ni... Ni.. Ba... Wallahi baaaaani da.... Da lafiya, Shiyasa naiwa kaina caaajiii, baaaa danki yaki Aure na baaaaaa, wallahi.... Cikin tsawa Yaya mairo tace" yimin shiru dan ubanki, ciwon mara take, shine ta sha magani fiye da ka'ida" Gaba daya jikin Maama yayi sanyi saboda babu tantama Naja maye takeyi. Shiru tayi takasa cewa komai, Naja ta cigaba da surutai, can kuma ta kwalla uwar kar, sega jini na gudu a tsakar dakin daga karkashin Naja. Se bayan la'asar su Jalila suka gama lectures ta gaji matuka, haka kurum tun suna lectures takejin gabanta yana faduwa, da kyar ta tsaya aka gama lectures ta fito, danma manu direba ne yaje dakko ta daga school, abunda yabata mamaki be wuce ganin motar Hannah a gabansu ba, tana tsala gudun wuce sa'a, kuma da alama layinsu zata shiga, Jalila tasa Manu direba yayi parking a farkon layinsu, ta sauka ta shiga layin da kafarta, aikuwa tana zuwa taga Hannah tayi parking din motarta ta shiga gidansu Jalal, Jalila batayi shawarar komai ba ko tunani tabi bayan Hannah zuwa cikin gidan. Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what's App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry. Ina godiya da kulawa. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Watpad @Ayshercool7724     🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣4️⃣97 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Shiru Jalila tayi ta kalli kayan daya ajiye mata sannan tabi bayansa da kallo har ya fice daga gate, din shiru tayi ta tafi tunani, Ahmad yace "my queen, meya farune?" Da sauri ta dawo hayyacinta tace "bakomai fa" "Amma waye wanan?" ya tambayeta yana me kureta da ido, ta dan sauke numfashi tace "Yaya na ne" "Yayanki queen, ba Jawwad ne kawai Yayanki ba?" "Abokin Yaya Jawwad ne, dan haka Yayana ne kawai" "Amma babu wani abu a tsakanin ku kuwa?" "Meyasa kake min wannan tambayar? Ko baka yadda dani bane?" "Ahh haba waneni ince ban yadda da gimbiyata ba, ina so ne in tabattar da abunda ke tsakaninku, dan da idonsa yana shaye2" Ba karamin haushi maganar Ahmad ta bata ba, kenan shima yanayi, in ba yanayi ba, ba abunda idon Jalal yayi dayake nuna yana shaye2, dan haka tace "baya shan komai, kawai bashi da son magana ne, baya kula mutane" Kyaleta Ahmad yayi yaga alamar bata son zancen suka cigaba da hira, Jawwad ne ya fito ze wuce su Jalila ya tsaya suka kuma gaisawa da Ahmad dayake dazu sun gaisa, Jawwad yace "to sirikina zan iya ce maka se anjima, ni zan tafi kai Jalal airport ne" Da sauri Jalila tace "Ina zashi?" Jawwad yayi murmushi yace "Aiki mana, an tura shi Lagos, se lokacin biki inaga ze dawo, bari inje karyai ta jirana, kin san baya son jira, se anjimanku" Sukayi sallama da Ahmad ya fita. Ahmad ya maida idonsa kan Jalila yace "Gimbiya naso a haďa bikin nan hada namu, na kagu in mallakeki" Murmushi kawai tayi amma hankalinta baya kansa, tanata zancen zuci ne, dayaga haka yace "queen naga kaman Akwai abunda yake damunki, bari in tafi semunyi waya" Ta mike ta rakashi har bakin gate sannan ta dawo ta zauna akan kujerun tana nazari "At least yakamata ace sunyi sallama da Jalal, tayi masa nasiha, Amma bata tunanin zata iya kuma rabarsa ba saboda mahaifiyarsa. Jawwad ya ga sam fuskar Jalal a daure take, babu alamar walwala ko fara'a, Jawwad yai masa magana yafi a kirga, amma ko daya be bashi amsa ba, dan haka ya kyleshi suka cigaba da tafiya a haka kaman kurame. Gajiya Jalila tayi da zaman tunanin ta mike ta tafi cikin gida, Nana tana zaune a palour suna waya da Mahmud, "Nana waike dan Allah ba kya gajiya da wannan wayar ne? Kuyita surutu tun ana fadar gaskiya se an koma fadan karya" Nana taki kula ta seda ta gama wayarta sannnan tace "waike Baby an gaya miki kowa irin kine me tsarin tsiya, ke yadda ba kya son yawan waya kowa ma hakane, ai a rana inji muryar Mahmud sau hamsin bazan gajiba, musamman mu da muke distance relationship, ai Ahmad din nan ma ban wani yadda kina sonsa ba" "Inasonshi sosai, amma hakan bashi ke nufin a dinga uzzuramin da surutu ba" "Hajiya Jalila, kyaji da shi dai" Hanan ca ta kira Jalila a waya, ta daga tasa a kunnenta "hello Baby, 'yar uwata rabin jikina ashe Family dinmu daya Baby? Narasa inda zan sa kaina dan farinciki, dazu Abba yake gayamin kuma wai an kawo kudin Aurena da Haidar, Baby na rasa me zanyi dan farinciki" Murmushi Jalila tayi tace "na riga ki ji ai, kiyi Azumi ki godewa Allah" "queen na rasa inda zan saka raina dan farinciki, daddy yace zasuzo karbar kudin Nana, narasa yadda zanyi dan murna" "haka Al'amarin ubangiji yake Hanan, yana juya komai yadda ya so" "Hakane Queen, amma naji haushi da baza'a hada da nakiba, ni ina Jalal ne ma?" "yaje interview din nan ai, an turashi lagos zeyi wata uku" "Allah sarki bawan Allah, wallahi Jalila bana kaunar Aurenki da Abokin Yaya Yusuf din nan, in duniya da gaskiya Jalal ya kamata ki Aura" Wani dogon tsaki Jalila tayi ta kashe wayarta, dan bata son Hanan ta bata mata rai. Jalila ta mike har zata bar palourn taga Maama tazo ta wuce kitchen, gaba daya Jalila bata jin dadin yadda kowa ya fita harkar Maama, dukda abubuwan da Maaman tayi mata, Akwai lokutan da ta kyautata mata, dan haka taga be dace ta mata hukunci da laifin da take mata ba, dan haka tabita kitchen din, Maama na kokarin kunna gas Jalila tayi maza taje ta karbi lighter tace "Maama kawo in kunna miki, me zaki dafa?" "barmin Abina zanyi" "A'a Maama, tunda ba abunda nake ki barshi in dora miki" Jalila ta karbi lighter ta kunna gas, dan jimm Maama tayi tana Kallon Jalila, yadda Jalilan ke Acting kaman Maama bata taba yi mata wani abu na bacin rai ba. Jawwad suka isa airport yayiwa Jalal Sallama amma ya amsa masa a ciki, sam baya walwala, yasan halin Jalal baya son takura, tunda be niyyar gaya masa meke damunsa ba, ya ja Akwatinsa yayi gaba yabar Jawwad. Haka Jawwad ya taho yanata tunanin me akayiwa Jalal yake wannan bacin ran haka? Bayan Jalila ta gana yiwa Maama girki, ta koma daki, ta dauki Alqur'anin nan tana ta jujjuyawa, Kamshin turaren Jalal yakeyi, hakama dan teddyn ta, tasa hannu ta ta dinga duba Alqur'anin nan page by page, amma sam bata ga komai a ciki ba, kodai Jalal dama yana son raina mata hankali ne kawai? Shiru tayi ta tuna yadda taga yana yinsa bayan ya gansu tareda Ahmad, Fuskar nan tasa a daure babu alamun sassauci, tayi shiru ta cigaba da zancen zuci, ;yanzu ze tafi lagos bashi da kowa a can, babu me kula dashi, Allah kadai yasan meze aikata, "kinfi so in cigaba da shaye2 na ko? Ke Garkuwa ce a gareni" ire iren wannan maganganun nasa da Maganganun Antynsa da take gaya mata tabata amanar Jalal ne yasa take tunanin Anya hukuncin data yanke yayi dai2 kuwa? To Amma nikuma mutuncina fa? " gaba daya ta rasa me yakamata tayi? Yanzu tana gaya Hanan, tasan Hanan zata canza mata magana tafara kawo wani abu daban, dan haka tabar Abun a ranta ta cigaba da Yiwa Jalal Addu'a. 'yan kwanakin nan sam Abba ya dena shiga harkar Maama, har gara Jawwad ma yana zuwa gaisheta, Nana kuwa seda Jalila tasata a gaba ta nuna mata be dace ba abunda take yiwa Maama, wannan abunda yafaru tsakanin ta da Abba ne da kuma' yan uwan ta, sannan ta samu Nana ma take shiga sabgar Maaman, Abba ya gayawa Maama ranar Lahadi zasuyi baki, za'a kawo kudin Auren Nana, abakin su Nana taji batun haduwa da 'yan uwan Abba a Bauchi, ba tayi mamaki sosai ba jin ance su Hanan' yan uwansu Abba ne ba, sakamakon matukar kamannin dake tsakanin Jalila da Hanan, sedai taji haushin rashin sanar da ita da Abba beba. Tun ranar Juma'a suke shirye2 domin bakin daza'ayi, Jalila ce jagorar girke2 da shirin yadda za'a karbi baki. Gefe guda Jawwad yana ta shirye2 Ranar litinin shima ze tafi gurin nasa Aikin, ba karamin kulawa Hanan take bashi ba, da soyayya da kuma shagwabarta, yanayin yadda take nuna yarinta  a wasu bangaren ba karamin birge shi yake ba. Kamar yadda aka saka ranar lahadi daddyn Hanan yazo Kano aka karbi kudin Auren Nana, itama lokaci dayane dana Jawwad dakuma Abdallah Yayan Hanan, ranar har mutan bauchi seda sukazo garin kano karbar kudin, da kuma kara taya juna murnar haduwar su a matsayin 'yan uwa. Jalila taji dadi da akazo hadda Hanan da Mummynta, Maama seda ta sha jinin jikinta ta raina kanta ganin manyan mutanen da sukazo gidan, Abun Arziki ya hadu dana Arziki, dangin Su Jawwad dana Su Jalal, Ranar anci ansha, kai ka dauka bikin Aure akeyi rana ce me matukar tarihi da wannan Ahali bazasu manta ba. Jalila sam bata samu kebewa da Hanan ba, saboda Hanan na manne da Jawwad, sam bata jin kunyar kowa take nuna masa soyayya. Mummyn Hanan se mita take tace "Ni gaskiya naso a hada abun nan hada na Jalila, in aurar da 'ya' ya uku, amma in shirya da kyau, amma bakomai anata se nafi shiri ko Jalila?" Ita dai Jalila sedai tayi murmushi ta sunkuyar da kai. Duk yadda Maama take jin kanta take kuma jin haushin Auren Hanan da Jawwad boyewa tayi, Saboda sam bata da makusa, 'yar dangi ce, kuma' yar uwar dan tace, tana da kyau dai2 gwargwado kuma tana da Ilimi, yanayin kyau da gayun mahaifiyar Hanan ya isa ya nuna maka 'yar ta ma hakan take. Koda ta hasko Naja seta ga abun se A hankali, kuma tun abun nan da sukayi mata ta tabattar da Ko Auren akayi Naja zata iya wulakanta ta. Da ire iren wannan tunanin yasa ta ajiye duk wani bacin rai aka shiga hada2. Tareda tsara yadda suke ganin bikin ze kasance, Ba laifi Mummyn Hanan ta saki jiki Maama, Sunyi hira sosai kaman sun saba, sannan suka tattauna akan yadda harkar bikin yaran nasu ze kasance. Se la'asar Suka tafi, mutanen Bauchi suka tafi, Su Hanan ma a ranar suka juya kaduna saboda Su Hanan suna jarrabawa, su kuwa danginsu Mahmud, suna kawowa Mahmud kudin Aure sukaci Abinci suka juya Borno. Wasa2 sosai tunanin Jalila ya hana Jalal sukuni, da yafara aiki in ya tuna da ita gaba daya se yaji duniyar tayi masa zafi, yarasa inda zesa kansa, meyasa Mummy tayi masa haka? Idan yaji abun ya dameshi se ya tafi club yaje ya cika cikinsabda giya, dukda wasu lokutan yana bawa aikin da yaje yi mahimmanci, Sam Jalal bashi da sakewa da mutane, dan haka be saba da kowa ba, sedai yana girmama shugabanninsa na gurin aiki, girmamasun da yake besa sunga alamar ze bari su taka shi ba, inda yake burgesu yana maida hankali akan aikinsa sosai. Duk lokacin da yaje Club mata da suke damun sa ne ga kuma shigar tsirara da suke yasa shi dakatar da kansa ga zuwa Club, idan yaji ba yadda zeyi se yayi shaye2 se yayi abunsa a dakinsa na hotel da yake ciki. Amma duk da haka yarasa dalilin da yasa mata ke binsa, sedai in baze fito ba. Hannah ce zaune akan kujera tana kwalliya, Sa'ada na kwance akan gado tana danna waya, dan dakatawa da kwalliyar Hannah tayi ta dan kurawa madubi ido, sekuma can ta daki kan mirror tace "Impossible baze yuwu ba wallahi" Sa'adah ta waigo ta Kalle ta tace "lafiya kuwa?" "Akwai matsala Sa'ada" Hannah ta bata amsa "matsalar me fa?" "Sa'ada ki kalleni ki kara, kimin kallon tsaf tun daga sama har kasa, ki kalli yadda nake gara kan maza, in taka wanda naso in wanke wanda naso, amma a hakan har rububina wasu suke, in sauke Ajina in cewa Jalal idan ya Aureni zan dena bariki, Amma ya watsa min kasa a ido" Wani dogon tsaki Sa'ada tayi tareda fadin "Nina dauka ma wani mutumin kirkin ne, A she akan wannan mashayin ne, ni ba wannaan ya dameni ba a yanzu" Hannah tace "Mutumin kirki ne mana, ki kalleshi kallon tsaf Sa'ada Namiji ne irin wanda duk wata mace zatayi burin Aure, shaye2 ne kawai matsalar sa, da farko da nakewa su Jeje aiki, nna zata zan samo kansa ta sauki ya yadda dani, Amma duk wata dabara da kisisina ta matan bariki nayi amma yaki amincewa dani" "to kibi wani mana, ko shine kawai namiji?" "bazaki gane ba Sa'ada, bakiga irin kirar da Allah yayi masa bane, kuma da kike ganinsa a haka, dukiya ce dashi kaman abun banza" "Ya akayi kika sani, nasan dai babansa yana da kudi, amma shikam ko aikinyi ba shida shi" Sa'ada tayi maganar tana yatsina fuska "Hmm to wallahi har ki mutu in ba wani ikon Allah ba, kaf danginku daku da abunda kuka mallaka, bazaku kaishi dukiya ba, yana da kudi da mahaifinsa yasa ake juya masa, Jeje yaso ganin bayan dukiyar nan shida mai gidansa amma abun be yuwu ba suka kare a prison" Sa'ada ta tashi zaune tace "to ke yanzu meye abunyi, ni ban taba sani ba, kin san ya taba kusa tonamin Asiri ina zuwa club agaban babarmu" Dariya Hannah tayi tace "Abune mawuyaci ya tona miki Asiri, bar ganinsa a haka, yasan abunda yakeyi, naje har gidansu na dana masa tarko, amma ga dukkan alamu ya tsallake shi, wannan karon zan masa tarkon da zan rike shi a wuya, be isa ya kuma subuce min ba" "Yakamata kam, Amma ni nan tunanin yadda zan huce abunda abokinsa Jawwad yayiwa Naja nake, kiri2 yafasa Auren ta, yarinyar nan duk ta shiga damuwa" "Allah sarki, to wai ya'akayi aka fasa Auren? Waye yaje yai mata gulma a gurin baban nasa?" "ya za'ayi in sani, Amma da nafi kyautata zaton wannan munafukar kanwar tasa ce" "Wace kanwar tasa ya'akayi tasan abunda Naja take? Ko dai itama tana ta bawa?" "Ke bari, wata yarinyace yadda kika san boka haka take, ni dai ban san tana wani biye biye ba, Amma kina zaune in taso seta nemo waye ubanki koda ke baki sani ba, wai ita Jalila makirace ta bala'i, idan tace bata san abu seta ga bayansa, tasa Jawwad ya fasa auren Naja se kawarta" Jin an ambaci Jalila yasa Hannah zare ido tace "Kan bala'i ai nasan wannan yarinyar, tabdijan ni zan gaya miki makira ce, ke wallahi keda kike bariki tafi ki iya rashin mutunci, ke zata iya yuwu wa ita tasa aka hana, bari in gayamiki yarinyar nan tafiki bala'i, dan koni tasa min ido akan Jalal, ita take rusa min komai " Cikin mamaki Sa'ada ta kalli Hannah tace" wai kin santa ne? " " Nikuwa na santa, kuma nasan illar ta, munyi Arranging da Jeje mun gama komai, zamu sace Jalal ranar birthday din sa, idonta na kanmu, muka bugar da shi da giya ta shammace mu tasa aka dauke shi daga gurin, ke ina jin kishin cewa ita tasa aka kama Oga KB" Zaro ido Sa'ada tayi cike da mamaki tace "Ke haba dai? Shikuwa oga KB yana me,duk iya kuri da gadarar rashin mutuncin nasa, yarinya ce fa karama" Hannah tace "hmm ke dai bari, mace kenan, kaidin wata yafi wata, irinsu kuma sa'a ce dasu a rayuwa, kibi a sannu kawai" "Tabdijan amma babu kama, dan bakiga cin mutuncin da muke mata ba mu da babarmu, kin san uwarta tsohuwar arniya ce, bakiga cin mutuncin da muke mata ba" Hannah tace "Yawwa kuma ga cin mutuncin da tayi muku nan, kuma ta gama daku ba" "Sosai makuwa ta gama damu" "shiyasa wannan karon shirina ita da Jalal ne, dan bana ta wannan Ilham din dan wannan ba mace bace, wannan tafi hatsari, baze tsallake wannan tarkon ba a yanzu, na duba mashayar da yake zuwa ba adadi amma ance ya dena zuwa, duk da haka zan nemoshi" Yauma duk da tarin farinciki da Jalila ta tsinci kanta a ciki yau, amma bacci ya kauracewa idanuwanta, jikinta na bata Jalal yakoma shan giya, da kyar ta samu bacci ya dauke ta, amma mafarkin Jalal a cikin wani yanayi na shaye2, yasata farkawa, gabanta na wata irin mummunar faduwa, wayarta ta dakko ta duba karfe biyu da rabi na dare, ga shi ita ba lambar Jalal ce da ita ba, tarasa mema zatayi gallery dinta ta shiga tana dubawa, tsofaffin ajiyayyun hotunan ta take dubawa, hotunan da sukayi da Jalal tun wani zuwa da Hanan sukayi, haka taita kallon hotunan, a haka har ta kawo kan hotunan birthday dinsa, cin karo tayi da wani hoto da'akayi harda Hannah a ciki, take gaban Jalila ya fadi, dan sam ta manta da Hannah, kuma barin Hanna ba tareda daukar wani mataji ba tamkar kashe maciji ne ba'a sare kansa ba a rayuwar Jalal. A hankali ta ajiye wayar, ta sakko daga kan gadon ta shiga toilet tayi alwala tazo ta tada salla. Ranar litinin Jawwad shima yayi nasa shirin tsaf domin tafiya Gurin nasa aikin dake birnin tarayya, Abba yayi masa Nasiha sosai tareda sa masa Albarka, haka ma bangaren Maama, tayi masa Addu'a da sa Albarka, dukda marin da Maama tayi masa akan Naja, hakan besa ya nuna mata har yanzu yana fushi ba, Bangaren Jalila kuwa har kuka tayi, saboda zatayi kewar Yayan nata sosai Abba yace "Jalila kina kuka dan zeyi tafiya, kuda kwanan nan zeyi Aure gaba daya zasu bar gidan, su barki seke kadai" Kara fashewa da Kuka Jalila tayi, Nana tace "Abba ka gani ko? Wannan yar taka ta fiye shagwaba wallahi" Jawwad yace "haba babyn Abba, sekace ba jaruma ba, zan dawo ai kidena kuka" Sukayi ta tsokanarta ita kuwa dagaske take kukanta. Haka sukayi sallama da Jawwad shima yakama hanyar tafiyar sa. Jalal yana waya da daddyn sa sosai, sannan suna waya ds Jawwad, suna shirye2 yadda biki ze kasance a tsakanin su. Abban su Jawwad yana kasuwanci ne a tsakanin Kano da lagos, dan haka in yaje suka haduwa da Jalal. Jalila Nason sanin halin da Jalal yake ciki, amma babu wata hanya da zata san hakan, dan haka taketa kokarin boye damuwarta. Maama Allah ya temaketa Abba ya sakko daga fushin dayake da ita, sannan tunda abun nan ya faru Su Yaya mairo ko a waya basu kara neman Maama ba, abun ya dameta sosai dan haka ta shirya da kanta taje gidan su. Tunda tayi sallama suka amsa suka shareta suka ki kulata, ita tayiwa kanta gurin zama, ta gaida Yaya mairo amma taki kulata, seda ta bata 'yan kayan data saba kaimusu, shine Yaya mairo ta dan saki rai suka gaisa, Naja ta gani a lullube tana bacci, Maama tace "Yaya, Naja ba lafiya ne?" Kafin Yaya mairo ta amsa Naja ta fara magana cikin maye "Ni... Ni.. Ba... Wallahi baaaaani da.... Da lafiya, Shiyasa naiwa kaina caaajiii, baaaa danki yaki Aure na baaaaaa, wallahi.... Cikin tsawa Yaya mairo tace" yimin shiru dan ubanki, ciwon mara take, shine ta sha magani fiye da ka'ida" Gaba daya jikin Maama yayi sanyi saboda babu tantama Naja maye takeyi. Shiru tayi takasa cewa komai, Naja ta cigaba da surutai, can kuma ta kwalla uwar kar, sega jini na gudu a tsakar dakin daga karkashin Naja. Se bayan la'asar su Jalila suka gama lectures ta gaji matuka, haka kurum tun suna lectures takejin gabanta yana faduwa, da kyar ta tsaya aka gama lectures ta fito, danma manu direba ne yaje dakko ta daga school, abunda yabata mamaki be wuce ganin motar Hannah a gabansu ba, tana tsala gudun wuce sa'a, kuma da alama layinsu zata shiga, Jalila tasa Manu direba yayi parking a farkon layinsu, ta sauka ta shiga layin da kafarta, aikuwa tana zuwa taga Hannah tayi parking din motarta ta shiga gidansu Jalal, Jalila batayi shawarar komai ba ko tunani tabi bayan Hannah zuwa cikin gidan. Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what's App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry. Ina godiya da kulawa. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Watpad @Ayshercool7724          🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣6️⃣99 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Hannah gaba daya kanta ya kwance bata taba tsammanin abubuwa zasu kwabe mata haka ba, wai me yakawo Jalila a gabar da takeso kulla wannan gadar Zaren, da komai ya tafi dai2, Jalal baze taba tsallake shirinta ba, wayarta ce ta fara ringing amma Hannah tayi biris da ita, an kirata ya kai sau shida sannan ta dauka a fusace tace "dalla waye haka?" "ke dalla zizo ne, za'a miki abun Arziki amma kina wa mutane hauka, ki tattara kayanki tun wuri kisan inda dare yayi miki wallahi" "kamar yaya? Saboda me?" "Allah ne yake sonki da rahama, Wallahi Jiya na raka wani me gidana Unguwa, ya tsaya gurin wani me gidansa dan sanda ne babba, naji me gidannan sa yana waya, bayan ya gama yake gayawa maigidana, wai wani yabada izinin a kamo masa wata yarinya a ajiye masa ita har seta haihu, ta yaye yaron ya shekara biyar sannan a saketa, idan kuma ba tada ciki aita ajiye ta kar a saketa, kuma yadda mutumin nan yake kwatantawa na gano kaman kece, ban gasgata hakan ba se jiya da naje palace, wallahi cikin dare 'yan sada sukazo nemanki, dan haka in kin san da wata cakwakiyar da kika kulla tun wuri ki kama gabanki wallahi " Hannah ta hadiyi wani mugun miyau ta ce "Shikenan nagode sosai zizo" Ta katse wayarta ta mike tsaye tareda fadin "kan bala'i banga ta zama ba, ni Jalal zewa haka? Wallahi yadda ya fada din nan aka kamani kashina ya bushe, Amma wallahi in yasan besan wata besan wata ba, ni zesa akama, nizewa hauka? Banga ta zama ba" Ta mike da sauri ta  janyo Akwati tafara zuba kayanta tanayi tanayin surutai. Jalila tattar komai ta ajiye a gefe ta maida hankali akan karatunta, dan yadda takeji in bata dena yawan damuwar nan ba zuciyarta zata iya bugawa, sosai Maama ta rage wannan gabar da takeyi da Jalila, tana dan sakewa da Jalila har suyi hira, suna shirye shiryen yadda biki ze kasance, Jalila bata taba nuna mata tana fushi da ita akan abubuwan da tayi mata a baya ba, Maama har mamaki takeyi, wani lokacin yanayin halinta daya da Jawwad, ka musu laifi amma su nuna basu san kanayi ba, ita kanta Nana tayi mamakin yadda Maama tayi saurin karaya da Al'amarin da yafaru. Jalila tana kitchen tana aiki Nana ta sameta "sannu da aiki Jalila, har tausayi kike bani, ke ba kya gajiya da aiki, da ke zaki rigani Aure ai ban san ya zanyi da aikin gidan nan ba, dan ma su Yaya Jawwad basa nan, aikinsu sam baya karewa" Jalila tai murmushi tace "Nana uwar son jiki, keda zakiyi Aure ai son jiki banaki bane, madam get ready to face the challenge, Ba sauki a Aure" "Nasani amma gaskiya bazan iya yadda kikeyi din nan ba, tabdijan shikenan kai bawa baka da hutu" "Aikuwa mukayi miki aure kikaje kikayi shirme, in yace ze kar Aure Addu'a zamu taya shi, mu fidda anko mu sha biki" "Kan bala'i ji muguwa, to ta Allah bataki ba" "Kai Nana sarkin kishi" "ke ba dole inyi kishin sa ba, ke har mamaki kike bani, ainaga kokarin ki da zaki auri Ahmad din nan, inajinki Hanan tana gaya miki matarsa bata da kirki" Jalila ta murmusa tace "Nana kenan, macen da ta amsa Sunanta mace, wadda ta yadda da kanta bata batawa kanta lokaci akan wani kishi, duk rashin kirkin matarsa ai ba akanta zan zauna ba, zan maida hankalina ne akan mijina, zanyi kishine da matar da nasan ta fini Ilimi, kyau, dukiya da asali, se matar data hada wannan abubuwan lokaci daya itace watakila zan kalleta a matsayin kishiya" jinjina kai Nana tayi tace "Sannu Jalila, Aini ko Kaza za'a aajiye ace kishiya ta ce to hankalina baze kwanta ba, yaushe zan kashe kaina, ke masu irin wannan zuciyar taki bau da yawa" A tare sukayi dariya, Sannan Nana tace "Yawwa Jalila nikam nace ya akayi kika amso qur'anin nan daga hannun Ilham? Na ganshi a karamin drwower" Dan murmushi Jalila tayi tace "Nawane ai ba nata ba, dan haka tunda ya tafi dole ya dawo" "Amma dagaske yaya Jalal ne ya baki shi? Kamar yadda Ilham ta fada?" "watakila shi yabani dan bani da tabbas" Jalila ta fada ba tareda ta kalli Nana ba "Kamar Yaya baki da tabbas?" Nana ta tambayeta cike da mamaki Jalila ta juya ta cigaba da aikinta sannan tace "Kamar yadda nagaya miki mana, bani da tabbas na shi yabani koba shi bane ba" Nana tace "Kai Jalila kin fiye rainin hankali, mutum yayi miki magana ki raina masa hankali, in tai wari dai maji, Ke Jalila ban gaya miki ba" "Ina jinki hajiya Nana jarida" Nana ta dan hade rai tace "kefa 'yar wulakanci ce, wace irin Jarida kuma?" Jalila tayi murmushi tace "Allah yabaki hakuri" Nana Ta dan saki fuskarta tace "Wai bakiga kwana biyun nan Maama duk tayi sanyi bane" Cikin ko in kula Jalila tace "Ban lura da hakan ba, tana komai nata kaman yadda take a baya" "Shikenan tunda haka kika ce amma Anjima zaki rakani wani guri" "Ina kenan?" "In munje zaki gani, saura daga baya kice min bazaki ba" Jalila tace "zan raka ki Insha Allah, Amrya ba kya laifi" "kai Jalila har kinsa naji dadi" Nana takarasa fadar hakan tareda fita daga kitchen din. Koda Jalila ta kammala aikinta ta koma daki, ta tarar da missed calls a wayarta, ta dauka ta bude don duba waye ya kirata haka? Kiran na Jawwad ne da kuma Ahmad, tana kokarin kiran Jawwad ne kiran Ahmad ya shigo wayarta, dan haka ta fasa kiran Jawwad ta amsa kiran Ahmad, Jalila ta shafe lokaci me tsawo suna waya da Ahmad, Sosai Ahmad yake bawa Jalila kulawa, dan tana iya shafe lokaci me tsawo suna waya ba tareda ta kosa ba, sukanyi kwanaki basuyi waya ba, saboda yanayin Aikinsa, dan haka duk lokacin da suka samu dama suna daukar dogon lokaci suna tare a waya, tana cikin wayar ne kiran wayar Jawwad ya dinga shigowa, dan haka sukayi sallama da Ahmad, ta kira Jawwad, tana bugawa ya daga Jawwad yace "Baby dawa kike ta waya hakane? Da farko na kira baki daga ba, Nakuma kiranki busy busy, for more than hour" "Am sorry Yaya Jawwad , Ahmad ne ya kirani, shine.. sekuma tayi shiru Jawwad yace "Hmmm to shikenan nagane, dama munyi magana da Hanan tace; zasuyi magana da Nana irin kayan da zasu saka na dinner, za'a turawa Abba, A dakko musu, kayan sun iso, ta kira layin Nana baya shiga" Dan zumbura baki Jalila tayi kaman yana ganinta tace "suka dai za'a siyawa nikuma fa? Ko tun yanzu anfara ware ni" "Waya isa ya wareki babyn Abba, A sekin zaba sannan za'a basu su zaba suma" "to shikenan zan musu magana Insha Allah, ya Aikin kuma?" "Aiki Alhamdilillah gashi muna ta fama" "To Allah yabada sa'a" "Ameen Babyn Abba" "Ina Jalal? Ya nasa Aikin?" Jalila taji tayi maganar ba tareda ta shirya yinta ba. Jawwad yace "Kinfara missing dinsa ne?" Sekuma taji gaba daya ta dirirce tarasa me zatace "Amm a'a kawai na tambaya ne, don't mind me, yaushe zakazo" Jawwad yace "A'a tsaya, naji dadi da kike tambayarsa, dama be kamata ya samu aiki ta hanyarki, yakama hanya ya tafi nesa da gida kuma ace bakya bincikar ya yakeba, Jalal dai yana nan lafiya, kuma yadda yake nunamin yana jin dadin Aikin nasa, Alhamdilillah ana samun cigaba a rayuwarsa, muna godiya kanwar mu, Allah yabiya ki ladan wannan dawainiya damu da kike" "Ameen Yaya, to shikenan,  naji kaman Maama tana kirana" Jawwad yace "to shikenan munyi waya da Maaman dazu da safe, Amma in cewa Jalal kina gaisheshi?" ya tambayet cikin zolaya Da sauri tace "A'a karka fada, ni bana gaisheshi" Jawwad yai murmushi yace "Shikenan se anjima" sukayi sallama, ta danyi Ajiyar zuciya, sannan ta mike, ta tafi bandaki dan daura Alwala anata kiran sallar Azahar. Da la'asar Nana ta uzzurawa Jalila suka dau mota fita, seda suka tsaya a kasuwa sukayi siyayya, Sannan Nana tace ta rakata Asibiti dubiya, Sam Jalila bata kawo komai a ranta ba ta raka Nana Asibiti, suka shiga female ward, Nana ta tambayi wani daki, aka nuna musu, Seda suka shiga  dakin sannan Jalila ta lura da suwaye a dakin, Su Yaya mairo ne a dakin, se Naja dake kwance kaman gawa, ana samata ruwa, da Jalila tasan gurinsu Nana zata janyo ta, da bata biyota ba, Amma me sukeyi a Asibiti? Ta tambayi kanta, Sallamar dasu Jalila sukayi ne yasa su juyowa suga su waye, Ganin Nana da Jalila yasa su hade rai, Jalila ta samu guri ta tsaya, Nana ta karasa ta zauna, tace "Yaya Mairo ina wuni" Rai a hade yaya mairo tace "lafiya" "Yame jiki kuma?" Nana ta kuma tambaya A fusace Yaya mairo tace "ban sani ba gulayya, uwarki ta gaya miki shine kikazo ganin kwaf, hadda dakko wannan annamimiyar shedaniyar, to da dan uwanki ya fasa Auren Naja bata mutu ba tana da rai, sannan ki gaggauta dauke wannan tsinanniyar yarinyar ku bar gurin nan, dan na tsani yarinyar nan bana kaunar ta, Yarinya sekace mayya, wayasani ko bayan Kafirci ta gaji maita, kila ta sha a Nono, kiri2 tana kokarin rabani da 'yar uwata, za' ayi Auren nan amma ta shiga ta fita ta hana, makira sedai kici kanki wallahi, kurwarmu tafi karfinki" Jalila dake gefe tace "kinga nifa ban san nan zamuzo ba, dana san nan zamuzo da bazan biyota ba, ni ban san Naja bata da lafiya ba, dan haka kidena zagina, wallahi kika kuma zagarmin uwa sena rama, ko ina maita zanci naman kune? Me zan ci ajikinku jikin matsiyata, Azzalumai" Sa'adah ta taso a fusace tazo gaban Jalila ta nuna ta  tace "ke karki kuskura ki zagarmin uwa" "in aka zagetan me zakiyi?" Jalila ta tambayeta tareda sauke hannun sa'adah tace "uwata da aka haifa a cikin Arna, da ita nake Alfahari, dan haka duk wanda ya kuma Yunkurin zaginta se inda karfina ya kare" Nana ta mike da sauri taje tsakaninsu ta tsaya tace "haba dan Allah, nifa ban kawo Jalila gurin nan dan kuyi rigima ba, nazo in duba Naja ne nace ta rakoni, me yakawo zancen maita,  yaya Jalila tayi hakuri a lokuta da dama da kuke cin mutuncin ta, Yaya mairo a rayuwa mussaman idan kanada 'ya' ya bakayi wa dan wani gori, kokuma mummunan baki, ...... "rufemin baki ko in gaureki da mari, kema ta shanye ki, shine zakizo kimin rashin kunya, na rufe kofa in muku dukan tsiya a gurin nan" Jalila tace "Wallahi babu matar da ta isa in tsaya ta dakeni, wallahi Nana dana san nan zaki kawoni bazan biyoki ba, kuma ki kyalesu karsu fasa zagina, bacin ranki akan an fasa aurar 'yarkine, badan anyi yunkurin likawa Yaya Jawwad ita ba ba abunda zesa in fadi wani abu a kanta, tunda tun ba yauba nasan halin yaranki kaf, nasan Naja tana shaye2, an gayamin Sa'adah na bin maza kuma kowanne inada tabattaciyar hujja akan hakan, kuma bari kiji ni ce nan nagayawa Abba yayi bincike akan Naja, kuma bincike ya tabattar masa da ba mutuniyar kirki bace, nan gaba in zakiwa dan wani gori ki duba gaba da bayanki ki tabattar bakida abun gorin tukuna, Allah ne ya sa kamin cin mutuncin da kikemin nida uwata, kuma kadan kika gani wallahi, kekuma Nana ingo key din motar kya taho, ni zan hau ta haya in koma gida" Jalila tayi ficewarta, da sauri Nana ta biyo bayan ta, da kyar ta lallaba Jalila ta hau motar suka nufi gida, harsuka je gida Jalila bata kula Nana ba ta cika tayi fam, suka shiga da kayan siyayyar da sukayi daki, Jalila ta hade rai sosai Nana ta nisa ta zauna a kusada ita  tace "Jalila nasan zakiji ba dadi abunda nayi miki, na kawoki anci mutuncinki, Jalila nasa ki rakoni ne dan kiga sakayyar hakurin da kikeyi, Jalila me hakuri ba a taba ganin bayansa, duk takurar da sukayi miki abaya zagi da cin mutuci, Amma abun Allah agaban Maama cikin jikin Naja ya zube, Jalila sadaukarwarki da jajircewarki akan samarwa wasu farinciki, Allah baze taba barinki ki wulakanta ba, Jalila duk lokacin da naga hawayenki ina shiga matukar damuwa, amma dayawa kikanyi kukane idan kika kasa samarwa wani farinciki, kokuma wani yayi hurting dinki, amma hakan baya hanaki kokarin ganin kinsa nakusa dake farinciki, shiyasa na kaiki kiga sakayyar da Allah yayi miki akan makiyanki, masu saki zubda hawaye, Jalila ina sarawa kokarin ki, masu irin zuciyarki kadan ne a cikin al'umma, Allah ya dawwamar da haske a cikin rayuwarki" Jalila ta rungume Nana, tana zubda hawayen da bata da tabbacin na farinciki ne kona bacin rai, tace "Nana nagode da addu'ar da kikayi min, dukda kasancewar su yan uwan mahaifiyarki baki juyamin baya ba, Amma Nana har cikin zuciya ta bana murna da abunda yasamu Naja, duk abunda yafaru da mace daya a society makamancin wannan, gurba cewa ce ta al'umma, da Yaya mairo tayi musu tarbiyya me kyau, Allah ka dai yasan mutanen dazasu amfana dasu, kuma da bazan taba adawa da Aurenta da Yaya ba, Amma ina fatan Allah ya shiryesu, yabasu mafita " "Ameen Jalila " Tunda Jalal yayi wannan tafiyar be kara dawowa ba, sedai suyi waya da daddyn sa ko Jawwad, Amma Jawwad yaje sau biyu lagos gurin Jalal, dukkan wani shirye2 suna yinsa ne ta waya shida Jawwad, tunda sukayi wannan rabuwar da Jalila basu kara haduwa ba. Jalal yayi kalau dashi, bashi da tension sosai, sena tunanin irin missing din Jalila da yayi, 'yan kwanakin da yayi tareda ita, suna shiri ya tsaye masa, amma da zarar ya tuna maganar ta na babu shi babu ita gaba daya se yaji abun duniya ya dame shi, shi kansa yasan Jalila halitta ce me matukar mahimmanci a rayuwarsa, a yanzu yana kokarin yin salloli biyar a rana, dukda ba kowane lokaci yake yinsu akan lokaci ba, yana kokarin yaki da zuciyarsa yaga yayi salla. Amma duk lokacin da yaji abubuwa sun da meshi, yana zama yayiwa kansa caji da giya yadda yakamata. Sannan Jalal yasaka a nemo masa Hannah duk inda take, se yaga waye gatanta, dan yayiwa kansa alkawarin se yasa an ladabtar da ita, seta gane shiba sa'anta bane da zatayi masa hauka. Bangaren Jalila ma tana son sanin halin da Jalal din yake ciki, tana son sanin ko har yanzu yana shaye2? Wace irin rayuwa yakeyi zamansa a lagos? Tana tausayin Jalal sosai, musamman idan ta tuna da labarin rayuwarsa da kuma amanar da Antynsa ta bata, ko ba komai dukda fadan da sukeyu takan tuna Alkhairan sa, Amma da ta tuna abunda Mummy da Ilham sukayi mata, gaba daya se ranta ya baci, se taji bata sha'awar kuma shiga shirgin rayuwar Jalal, dama saboda Jawwad suke haduwa, in Jawwad yayi Aure ko ganinta baze kara yiba balle mahaifiyarsa ta zargi wani abu. Rana bata karya, sedai uwar diya taji kunya inji hausawa, Duk abunda aka sama sa rana inda rai da lafiya zezo, Shirye2 sunyi nisa game da wannan bukukuwa da wadannan iyalai ke tun kara, Jawwad yayiwa Hanan saiti uku na kayan lefe, be cika mata tarkace ba, sedai yazuba mata kaya masu matukar tsada da kyau, haka Nana ita set hudu mahmud yayi mata, itama an zuba mata dukiya (kunsan family su Jalal akwai masu gidan rana) gaba daya kayan lefen bauchi aka kaisu, a can aka karba kayan, na Abdallah ma aka kai kaduna gidansu siyama, gaba daya Basa zama, koda yaushe Hanan tana yawan zuwa kano saboda siyayyar biki. Duk wani shirye2 Jalila ce kan gaba gurin tsara yadda abubuwa zasu gudana, An shirya gaba daya bikin zasuyi shi a garin bauchi ne. Saura sati daya a fara biki, su Nana suka tafi garin bauchi inda acan za'ayi dukkan wata hada2 ta biki, Jawwad da Jalal tare suka je har maiduguri suka kai musu katin bikin Jawwad, dama ga abun dai2 da bikin Nana, rabon da Jalal ya taka kafarsa garin maiduguri har ya manta, Amma bisa ga mamakinsu sega Jalal, dangin Daddy sunyi matukar farincikin ganin Jalal, ya nutsu ba kamar da ba, yasa manyan kaya hada hula, gashi suka samu labarin har aiki yake, sunyi farincikin ganin sa, sun samu kyakyawar karba daga dangin Jalal, dama Jawwad ma dan gida ne, seda suka kwana biyu a garin maiduguri suka wuce bauchi shida Jawwad, sam Mummy bata san batun Jalal yaje maiduguri ba. Ayi hakuri yau typing babu yawa, nayi busy sosai ne Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Watpad @Ayshercool7724          🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣7️⃣100 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Shirye2 sunyi nisa sosai ana ta hada2, za'a shiga satin biki, Jawwad da Jalal sun kwana biyu a bauchi suka koma kano domin rabon invitation ga abokan Jawwad, Amma har suka tafi Jalila basu hadu da Jalal ba, duk inda amare suka shiga Jalila na biye dasu, tare sukaje gyaran kai, da kunshi na amare, hatta gyaran jiki da Jalila ake, se sheki take kamar itace Amaryar, in kaga yadda take zakewa kai kace itace amaryar, Ana gobe za'a fara bikin 'yan uwansu Jalal daga maiduguri suka zo (dangin su Mahmud) lokacin da suka zo su Jalila sun tafi gurin kunshi, tunda suka zo Antyn Jalal ke cigiyar Jalila, Amma aka sanar da ita sun tafi gurin kunshi, guri na mussaman aka tanadarwa dangin mijin Nana. Ana gobe a fara bikin su Jawwad suma suka dawo shida Jalal, duk inda zashi kafarsa kafar Jalal. 'yan uwa wanda sukazo daga wasu garuruwan, Inna ta dinga nuna musu Su Jalila Da Nana, tana gaya musu ga' ya'yan da jikokin kanwarta. Yaya mairo kam da zuri'ar ta kaf babu  wanda yazo taron nan, sedai sauran 'yan uwa da abokan Arziki. Se dare su Jalila suka dawo daga gurin kunshi, kallo daya zakayiwa fuskar amaren zaka gane yadda suke cikin farinciki, gashi sun dau kyau Masha Allah, suka tafi part din Anty fido a can suke kwana saboda estate din ya fara daukar harami da baki, kasancewar daddyn Hanan babban mutum ne asanshi sosai. Hakama Abba yanada mutane sosai, ga dangin su Jalal, dan haka estate din cike yake da mutane. Koda su Jalila sukayi sallar magariba, Hanan tace "gaskiya sena kira Haidar yazo ya ga kunshin nan" Jalila tace "ke zumudin me kikeyi? Kwana nawa ya rage?" "dan kwana nawa ya rage, se indena kula dashi? Se yaga kunshin nan, in yamasa ayi biki da shi, in yace be kyau ba a dirje shi a daren nan" Gaba daya sukayi dariya, Nana tace "ni dama muna gurin kunshi Mahmud yacemin; sunzo dazu suna tareda su Yaya Abdallah, ina son mu hadu da shi, inji ko yaci Abinci?" Jalila kallonsu kawai take tana murmushi, tana mamakin ya sukeji a ransu game da soyayya haka? Ita dai tasan tana son Ahmad, Amma bata tunanin zata iya wannan rawar kafar akansa kamar yadda su Hanan sukeyi, ko lokacin da take son Yaya Jawwad bata tunanin zata iya abunda su Nana sukeyi, tana kallonsu suka canza kaya, sukayi waya da su Yaya Jawwad suka fice babban palourn part din. Itama sallolinta tayi, tai wanka ta canza kaya, ta samu ta nutsu tana cin Abinci, ta nayi tana chatting da Ahmad, yana ta mata magiya akan ta fito yana son su hadu amma taki, se wasa take masa da hankali. Maama ta kira Jalila a waya tace taje main part ana neman ta, haka ta tashi ta tafi, da ita so take ta samu ta kwanta ta dan huta, ta fita ta kofar kitchen yadda su Hanan bazasu ganta ba. Koda taje, da kyar ta gano Maama saboda cikar da akayi a gidan, Maama tace "dangin mijin Nana ke nemanki, Antyn Jalal tunda sukazo take cigiyar ki fa" Jalila tace "Ai ban san sunzo ba, suna ina?" Maama tayi mata Jagora har masaukin da aka basu, Jalila na shiga Antyn Jalal ta fadada murmushinta tace " 'yar halak taki ambato, tun dazu nake cigiyarki" Cikin fara' a Jalila tace "Anty sannunku da zuwa, munje gurin kunshi ne shiyasa, ya kukazo? Ya hanya?" "Alhamdilillah Jalila, Allah yasanya Alkhairi, ya kaimu lokacin naki Auren, kalli yadda kike sheki kamar Amarya" Sunkuyar da kai Jalila tayi, alamun kunya, ta gefen Antyn ce tace "Masha Allah itace Jalila kenan, kai Jalila Allah yasaka miki da Alkhairi, muna godiya da nuna kulawarki ga danmu, last week sega Jalal a maiduguri, babban farinciki danayi, wai aikin dayake ta silarki aka same shi, mungode Jalila" Gaba daya Attention din sauran da suke dakin ya dawo kanta, wasu suna magana da hausa wasu nayi da yare, suka dinga yi mata Addu'a, tarasa Addu'a mema suke mata haka? Kamar wadda ta basu wata gagarumar kyauta. Dangin Jalal suna da matukar kirki da karamci, nan Antyn Jalal ta dinga nuna mata dangin Jalal, tana gaya mata kowacce mecece a gurin Jalal, 'yan gayune, kuma kallo daya zakayi musu kasan suna hutawa, gasu kyawawa abunda ta lura da shi shine, gaba dayansu babbar shedar da zaka gane family dinsu da shi, shine wannan dogon hancin irin na Jalal, mazansu da matansu haka suke kayan dogon hanci, Kamar sun saba da Jalila suka dinga yi mata hira, gaba daya Jalila jinta take a takure, Anty ta lura da hakan dan haka tayiwa Jalila sallama, tace seda safe. Jalila na fitowa tana sauri takoma part dinsu ta hadu da Yusuf a hanyar shiga babban parlour, yace "Yawwa Alhamdilillah, naji dadin ganinki a yanzu, zomuje kimin wani dan aiki" Jalila tace "to Yaya" yana tafe tana binsa a baya, ya shiga inda ake ta hada2 dafa Abinci, ya dakko wani kwando da manyan warmers akai da plates, da spoons da serving spoons, yabawa Jalila ta karba ta rike, shikuma ya dakko cartons na ruwa da lemuka, yace "muje Bakinmu nasa akayiwa girki, dare yayi Abinci ya kare " Jalila ba tace komai ba ya shiga gaba ta biyo bayansa, wani part din suka nufa, ita  bata taba sanin da gurin bama, saboda parts din da suke bangare daya na estate din ma dayawa, tundaga waje harabar part din ake iya juyo hayaniya na tashi da dariya na 'yan maza, Yusuf ya shige gaba yasa hannu ya bude kofar ya shiga, ya juyo ya ce mata "Shigo Jalila" ba musu ta bishi da kayna a hannunta, kallo daya tayi musu ta sauke kanta, mazane sun kai su bakwai a cikin palourn, inma basu fiba, dan haka duk taji ta takura, kanta a sunkuye ta dan risina ta gaishesu, suka amsa mata gaba daya, dayan yace "A'a wannan kaman Hanan" Taji muryar Abdallah yace "Ba Hanan bace, sister dinta ce, Amaryar Ahmad to be" Ahmad yace "Tun dazu nake magiya ki fito in ganki kika ki, cikin sa'a sega Yusuf ya kawomin ke, amma dan mugunta ya hadaki da wannan kayan nauyin, memakon shi ya dakko" Sunkuyar da kai Jalila tayi tana sauke kwandon hannunta, Yusuf yace "Au ban maka abun Arziki bako? Nida yakamata ka godemin" Ahmad yace "nina isa in fadi haka, ince bakayi min abun Arziki ba, Kamin abun Arziki sirikina, wallahi Yusuf ji nake kaman a daura namu auren nida Jalila" ya dan kalli Jalila yace My Queen yakamata muyiwa Daddy magana, yadda kikayi shar dake haka kamata yayi kawai muma ayi namu" Jalila ta sunkuyar da kai cike da jin matsananciyar kunya. Daya daga cikin Matasan yace "dan banza uban zumudi, dole kayi zaman jiran shekara guda, kacigaba da lallabawa da Ameera, kokuma kayi biyu babu" Gaba daya kunya suke bawa Jalila, tayi kokarin mikewa domin tabar dakin, ta mike kenan kawai idonta ya sauka ana Jalal da tunda ta shigo bata kula da shi ba, farar Jallabiya ce a jikinsa fara kal, sumar kansa ta sha gyara se sheki take, watanni hudu kenan bata ganshi ba, amma ya kara kiba, gaba daya ya tattara hankalinsa akan danna waya da yakeyi amma gaba daya idonsa akan Jalila yake, yana mata wani irin kallo da takasa gane na menene? Tuhumace, kokuwa meyake nufi? Muryar Abdallah taji yace "Queen kin san kuwa ranar dinner, Siyama zasuzo ayi dinner anan, ranar daurin aure in angama da nan, zamuje kaduna a can gidansu za'a daura namu" Cikin sakin fuska ta juyo tace "Dagaske Yaya Abdallah, zanga Siyama? Rabon da in ganta tun ranar dana bar kaduna" Ahmad yace "tasan Amaryar taka ne?" Abdallah yace "tabdijan Aminiyarta ce ta kuruciya, wadda take Jawa duka, kai Jalila ai an girma an dena neman magana, Siyama tana bani labarin wahalar da ta sha saboda ke, gaskiya badan badan ba sena rama mata" Jalila ta dan zumbura baki sannan tace "Seku rama din ai" Ahmad yace "Ka rama me? Munci bulus ko queen?" ta dan jinjina kai tana murmushi. Koda aka bude warmers din nan, jallof couscous ne, ya sha nama da kayan vegetables, ta dan kalli Jalal ta kalli Abincin tasan Jalal baya cin Couscous kome zeci oho? Kai bazakace Jalal yayi existing a dakin nan ba, duk hayaniyar nan da'ake yi, kala bece ba, shida kujerun gurin kusan daya, dan ko uffan baya cewa, ko abun dariya sukayi fuskar nan tasa murtuk take babu alamar wasa. Kallon da yake wa Jalila gaba daya yasa ta tsargu har taso ta diricice, dan haka tace "seda safenku" Ahmad yayi farat yace "tsaya in rakaki  zamuyi magana" Yusuf yace "Sena gayawa Amira, wannan rawar kan da kake yi" "Karka fasa gaya matan" Jalila ta nufi hanyar fita, dan gani take kaman Jalal ze iya tashi ya dizgata agaban mutane, tana kokarin wucewa tayi tuntube da kafar Jalal kasancewar ya mike kafafunsa kuma takusa da kafafunsa zata wuce, ga shi a rude take dan haka ta kusa faduwa, Allah ya temaketa bata fadi ba tace "Subhanallah" shikam Jalal ko a jikinsa dan ko kallon inda take beyiba, Ahmad yace "Haba ya haka? Kana kokarin nakasa min mata, ka baje kafafunka akan hanya, at least yakamata ka bata hakuri" Wani irin kallon baka isaba Jalal yayi masa ya maida kansa kan wayarsa ya cigaba da abunda yakeyi, ba tare da ya furta koda harafi daya ba Jalila tace "No karka damu, base yabani hakuri ba, wannan ai besan yayi laifi yabada hakuri ba, da na fadi kafar zan take inga ta tsiya" Kallon da Jalal yayiwa Ahmad ba karamin batawa Yusuf rai yayi ba, dan da'a waje ne wani civilian din yayi musu haka, seya gane shayi ruwane, shibe ma san daga Ina wannan mugun dan jiji da kan yake ba. Abdallah yace "Yusuf kabi a hankali, wannan da kake yabata hakuri, in yaso se ya hana abaka Auren nan, sirikin kane ka bishi a sannu, yayan Mahmud ne daze Auri kanwarku Nana, kuma babban Aminin Jawwad" Yusuf yace "wannan din"? "Kwarai Shidin" Jalila dai ta fice waje, Ahmad ya biyo bayan ta, "Jalila wai me wannan mutumin yake takama da shine da yakewa mutane kallon basu isa ba??" Jalila tace "ba kallon mutane basu isa bane, haka yake, haka halayarsa take, ka lura ko Mahmud da yake kaninsa baya kulashi sosai, Yaya Jawwad da Abdallah kawai yake shiga shirginsu" "Amma meye hadinki dashi da ze dinga kallonki haka?" "Ba wani kallona da yake, kaika ga hakan, bani da Abunda Jalal ze tsaya kallo, A lissafin Rayuwarsa baya shiga shirgin mata, koda 'yan uwansa ne, muna gaisawane kawai saboda Aminin Yaya Jawwad ne" "Kai queen, duk taurin kai da dagiyar namiji, baze iya dauke kai akanki ba, Amma me ya kai Jawwad abota da wannan bahagon mutumin". "Amintarsu hadin Allah ce" "to shikenan, abar maganar ya gajiya,? naga kunshi ki yayi kyau, kamar in saceki in gudu" Murmushi tayi tace "Tabdijan kaida Daddy kuwa, inka gudar masa da 'ya" Haka suka cigaba da hira, ya rakata har kofar part din Anty fido, sannan ya koma. Tana shiga part din tabi ta babban parlour, bakowa a ciki ta nufi makwancinsu, tana shiga Hanan ta kalleta tace "daga ina haka?" "Naje cikin gida ne, Yaya Yusuf yasakani aiki" Hanan bata kuma cewa komai ba, Maimakon su kwanta suka zauna sukayi ta hira, seda suka raba dare sannan kowacce ta nemi guri ta kwanta. Washegari yakama ranar daza'a fara biki, ranar ne za'ayi kamu, iya mata da yamma, ko Angwaye bazasu gurin ba, iya mata ne a gurin kamun, , a wani katafaren dakin taro, karfe biyar na Yamma, Amare suka iso dakin taron sanye da shiga irin ta fulani, Suka fito a ainihin usulinsu na fulani, 'yan matan ma, duk kayan fulani suka sa, se manyan iyaye da suka saka Atamfar anko na kamu, karshen haduwa kam sunyita ba' a magana, Sunyi kyau, Amara kirjin biki ma wato Jalila tayi kyau, ammata simple make up, gashi anmata ado da gashin kanta, sosai kayan suka karbeta, Anyi raye raye, anci an sha, an lika kudi, anyi hotuna da 'yan uwa da abokan Arziki, anyiwa Amare kamu, ba' a tashi daga gurin ba se karfe goma na dare, motoci sukazo suka kwashesu zuwa gida. A motar Ahmad Jalila ta koma gida, Jalila banda motar Jalal bata taba hawa motar wani ba se Ahmad, suna tafe yana yaba irin kyawun da tayi. Da suka koma gida ma a idon Jalal suka dawo, Jalila tayi kyau se hirarsu suke ita da Ahmad. Tunda suka koma, Jalila bata tsaya tabi takan kowa ba, ta tafi part dinsu, Mummyn Hanan ce tazo ta samesu a dakin da suke zama, tace "Kuyi maza kuzo, Uwar mijin Nana tazo, kuzo muje ku gaisa" (wato Salma uwargidan daddyn Hanan) Jalila najin haka tace "nima bari in biku" Ko kayan basu canza ba, suka bi bayan Mummy. Koda suka shiga masaukin da'aka bawa Maman Mahmud kamshin turare ne ya gauraye dakin, tana zaune akan kujera, Jalal na zaune a kusa da ita, se wasu 'yan mata, da kuma Antyn Jalal tana salla, da alama hira sukeyi da Jalal, kamarta daya da dan nata Mahmud, haka kuma tana dan yanayi da Jalal din, suka shiga da Sallama, ta dago cikin fara' a ta amsa, Mummy Hanan tace "to Hajiya Salma ga yaran naki nan, sune Amaren" Ta kallesu daya bayan daya, ta kalli Nana tace "ga sirikar tawa nan, ita nasan ta ai" Sukayi murmushi suka durkusa suna gaisheta. Jalal ya kalli Jalila tayi kyau sosai, Se murmushi takeyi, Hajiya Salma tace "Jalila baki sanni ba ko?" Jalila ta Kalle ta ta jinjina mata kai, Hajiya Salma tace "ni na sanki ai, kamar ki daya da mamanki, Amma kuma kusan duk kamaninku daya keda Amaren" Jalal ya juya harshe sukayi magana da Hajiya Salma. Nan ta shiga yi musu Nasiha akan Aure, da mahinmancin biyayyar Aure. Tana cikin yi musu ne Maama ta shigo, ta kawowa Hajiya Salma Abinci, nan suka hadu aka cigaba da yiwa Amare nasiha, Jalila kam ta kame tana sunkuyar da kai sekace itace Amarya. Jalal ma yana kusada Hajiya Salma ake musu wannan fadan, ko a jikinsa, be kula Jalila ba haka itama bata kulashi ba, tsakanin ta da shi se kallo. Jin da Jalila tayi Hajiya Salma tana bayani da manyan bakake, Mummy Hanan ba ruwanta suka dinga yiwa amare fada, da koyar dasu zaman takewar Aure, ba shiri Jalila ta mike zata fice, Maama tace "Ina zaki kuma?" "Amm... Zanje inci Abinci yunwa nakeji" Sosai Jalila ta bawa Hajiya Salma dariya, Tace "dawo ki zauna, ina da magana dake dama" shiko gogan har akayi aka gama ba inda yaje yana zaune, daga karshe ma Abincin da aka kawowa Hajiya Salma ya zuba yafara cin Abunsa. Yadda Jalal yake wa Hajiya Salma kamar irin dan Autan nan nata, kuma ga dukkan alamu tanaji dashi. Seda aka gama yiwa su Nana fada, Aka sallamesu amma tace Jalila ta tsaya, suka tafi Maama ma komawa tayi, dan Akwai Ayyuka sosai a gidan, Maama na fita Jalal yabi bayanta, yace dan Allah yanaso a bashi tea. Ya rage daga Jalal se Mummyn Hanan, Jalal da Hajiya Salma. Hajiya Salma tace "Jalila me dana yayi miki ne?" Jalila ta kalleta da alamar bata gane ba. Hajiya Salma tace "ABDUL JALAL mana babban dana kuma ďan Auta, kince bake ba shi, me yayi miki ne? Ba laifinsa bane, nasani laifin Mummyn sa ne, Amma kiyi Hakuri, Daughter Jalal yana jin maganar ki fiye da yadda kike tunani, Jalila Taimakon Rayuwar Jalal kike, Jihadi kikeyi, Allah ne kadai ze biyaki, karki duba abunda mutane zasu fada, kedai kiyi dan Allah, duk yadda muke da Jalal bana masa fada, idan nayi masa fada se yafara gaba dani ko wayarsa na kira baze daga ba, Amma da yake Allah ba yadda baya lamarin sa, kinga dake da Jawwad, musamman ke yanajin maganar ki, ban san me kikayi masa haka yake jin maganar ki ba" tai maganar cikin zolaya, sannaan tace "Naji dadin ganin cigaban da aka samu a rayuwarsa ta bangarenki, ko danginsa babu wata wadda yake sakewa da ita kamar ke, yana jin maganar ki dukda shirin naku na Tom and Jerry ne" Jalila ta sunkuyar da kai, Mummyn Hanan tace "gaskiya nima yadda na lura da shi, baya son. Mutane sam, mussaman ranar da suka je mana can Kaduna, Amma dukda haka a nutse yake". Hajiya Salma tace  "Wallahi sister badan kaddarar Rayuwa da ta faru da shi ba, yarona mutumin kirki ne, ki tambayi Jawwad kiji, Wallahi banga abunda bazan iya mallakawa Jawwad ba saboda dawainiyar da yayi dashi ba" Mummy tace "ke kika haife shine?" Hajiya Salma tai murmushi tace "Dan ex-husband dina ne?" Zare ido Mummy tayi "Haba dai, duk abun nan bake kika haifeshi ba?" sukayiwa Jalila nasiha sannan, Hajiya Salma ta sallami Jalila, sannan suka cigaba da hira ita da Mummyn Hanan. Tunda Hajiya Salma tazo, duk abunda take bukata sedai ta kira Jalila, duk inda zatayi kuma seta kira Jalila, kamar dama can sun san juna, Mafi yawan tattaunawarsu akan yanayi na Rayuwar Jalal ne, Sosai Hajiya Salma taji kaunar Jalila a ranta, Jalila tanada biyayya, da girmama mutane, ga kuma namijin kokarin da take akan yaransu Jalal. Washegari yakama ranar daza'ayi dinner, tun safe ake shiga ana fita a gidan nan, gida yacika da mutane, Shabiyun Rana Siyama ta iso itads 'yan uwanta, Labari na ishe Jalila Siyama ta karaso aids gudu ta nufi cikin gidan tana zuwa suka Rungume juna, Maama tace "Jalila kiyi a hankali, karki ji mata ciwo mana" Jalila tace "Siyama ta, dama zan kuma ganinki?" Siyama tace "gani kuwa kin ganni" Jalila ta janye Siyama, Zuwa bangaren Anty fiddo, Hanan Ma na ganin Siyama ta rungumeta itama tace "Na dauka tun ranar kamu zakizo, Amma shine baku zoba se yau" Siyama tace "Ai muma munyi kamu da party a can ne, saboda wanda bazasu samu damar zuwa nan ba" Suka gabatar da Siyama ga Nana, dan  basu san Juna a zahiri ba, Amma sukanyi waya saboda Jalila, "Nana tace, Sannu da zuwa Siyama, ya hanya?" "lafiya kalau Nana, ya taro?" "Alhamdilillah" Suka zauna suka dinga hira, suka shantake a gurin, suka dinga hira suna tuna kuruciya da shiritar da sukayi, Nan Jalila ta dinga basu labarin Artabun fadanta da Jalal, har lokacin daya taba yi mata duren hayakin taba. Sunsha dariya, Nana sam bata san rashin jituwarsu ta kai haka ba, Amma bata gaya musu fadi tashin da ta dinga da kokarin ganin ya shiryu ba, har labarin su Hannah da Jeje bata gaya musu ba. Suka shantake suna ta dariya. Anty Fiddo ta shigo ta samesu a zaune suna hirarsu suna ciye2, kaman karsu rabu, Anty fiddo tace "waikuna nan a zaune, kamata yayi ku hanzarta ku fara shiri, ku tafi gurin kwalliyar nan, kar a bata lokaci" seda ta kai aya ta lura da Nana, taana ganin Siyama "Tace Amryarmu, gaskiya Abdallah ya iya zabe, Jalila ke Alkhairi sanadiyar kawancenki da Hanan, mun gano 'yan uwanmu, kuma sanadiyar ki Abdallah yayi mata shima, Allah ya kaimu Aurenki da Ahmad" Hanan tayi farat tace "ba Ameen ba" Anty fiddo tace "Saboda me?" "nifa bana son Auren ta da wannan Yaya Ahmad din wallahi, matarsa bata da mutunci, wannan Ameeran tab, ni wallahi bana son Auren su" "ina ruwana da rashin mutuncin matarsa, dai dai da ita nake, ai dani ze zauna ba dake ba" Siyama tace "Nikam Jalila ina Jalal, ina son in ganshi" Tsaki Jalila tayi tace "ina nasan inda wani Jalal yake" Hanan tace "Karya takeyi, yana nan Haidar ya gayamin, suna tare" Nana tace "Too Siyama kema kin san Jalal, ai dole ki ganshi, nasan watakila anjima yaje gurin dinner zaki ganshi" Anty fiddo tace "kunga abar surutun nan haka, ku tashi ku fara shiri" Haka su fara shirye2, karfe hudu suka tafi gurin kwalliya. Karfe tara na dare Jalila tana tareda Amare an musu kwalliya me daukar hankali, kayansu iri daya, sea green din material, da takalmi da purse, Jalila kuma tasaka blue-black na material kaman yadda shine yazama ankon dinner, Tasaka bakin takalmi da jaka, jikinta babu mayafi, Su Jalila ne 'yan shigo da Amare, masu shigo da amare kowacce gefenta da namiji da, Amare da Angwaye, Jalila Ahmad ne a gefenta, suka shigo da Angwaye, ana musu hotuna tareda likin kudi, suka kai su har kan high table, nan aka tsaya aka fara hotuna, Ba zato ba tsammani Jalila taga Jalal, sanye da shaddarsa coffee colour, me tsadar gaske, ta sha aiki da bakar hula da takalmi sau ciki, tsinstiyar hannunsa dauke da wani dankareren Agogo, fuskarsa ba yabo ba fallasa, ya durkusa gefen Jawwad yana masa magana a Kunne, nan aka shiga hotuna 'yan uwa da abokan Arziki, Jalila anyi hotuna da ita ba Adadi, nan Hanan ta nunawa Siyama Jalal, Siyama tace "Yadda Jalila ke masa rashin mutunci bazakace haka yake ba, hadadde dashi" sukayi dariya ba karamin kyau Jalila tayi a idon Jalal ba, Amma ganinta ba mayafi yasa duk yaji ransa ya baci. Nan aka fara gudanar da taro kaman yadda aka tsara, dukkan bangarorin sunyi bajinta gurin lika dukiya kaman ba'a san dadinta ba, Hajiya Salma ba'a barta a baya ba gurin yin wannaan hidimar, tunda ta hau kan stage Jalal ya fito ya dinga lika mata kudi, kamar be san ciwonsu ba. Aka dinga mata kirari, ko Mahmud da ta haifa bata masa likin da tayiwa Jalal ba, ta koma gefe, takira Jalila tasa me hoto ya dinga daukarsu hoto itada Jalila da Jalal. Hakama Sunsha hotuna Jalila da Maama, Jalila tayiwa Maama likin kudi sosai ta dinga rungumeta suna hoto a wayar Jalila, kamar ba Maaman da take gallaza mata ba. Lallai halayar Jalila daban take, sam bata riko. Aka jima M. C ya kira Amare da Angwaye kan stage, suna dan takawa, yasaka wakar da Jalila ke matukar so, dan haka stage din nan ba kowa se Amare da Angwaye, Jalila ta fito, tafara Rawa itada  Su Hanan Jalila Rawa take me cikeda daukar Hankali, ba wani girgiza jikinta take ba, Amma ta dau hankalin mutane, Ahmad ya fito ya dinga mata barin kudi, ana musu hotuna. Jalal ya kai karshe a bacin rai, Ga jikinta ba mayafi, ga dinkin yayi fitting dinta, gata tubarakallahu tana da diri me daukar hankali bawata rawa take ba, juyi kawai take Amma Jalal ya kule musamman yadda Ahmad ke mata barin kudi, yana mata wani irin kallo, wayar Jalila ce tafara ringing dan haka ta sakko daga kan stage din ta fita daga hall din domin amsa wayar, tana fita Jalal yabi bayan ta. Tofa Fans Oga Jalal ya dau Zafi, A tunanin ku mezeyiwa Jalila? Nayi muku dogon typing dan haka ina bukatar Comments ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 My Love for you is endless, daku da masu bina pvt da masu karanta littafin duk ina godiya Allah yabar kauna, ina sonku kaman yadda kuke nunamin kauna Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣8️⃣101 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Daddyn Jalal ne a tsaye da yana rataye da 'yar karamar Jaka, da alamu zeyi tafiya ne, Mummy na kan three seater ta kalmashe kafa tana danna remote. Daddy yace "wai dagaske deeja bazaki bikin nan ba?" Ya tsina fuska tayi tace "Nifa bana son yin doguwar tafiya inba a jirgi ba kasani, kuma me zanje inyi musu, banda jaraba ayi biki a inda suke sun kwasa sun tafi wata uwa bauchi biki, ko meye amfanin hakan oho?" Daddy ya samu guri ya zauna yace "deeja, in duniya da gaskiya be kamata kiyi haka ba, duk gudunmuwar da Jawwad ya bawa Rayuwar danki, ga tsawon lokacin da kika dauka kuna makotaka, ga harkar kasuwanci da kikeyi da mahifiyar yaron nan, sannan koba komai kema Mahmud danki ne, shima kodan shi bazaki ba? " "daddy a dawo lafiya, ka musu Allah ya sanya Alkhairi in sun dawo na musu Allah ya sanya Alkhairi, bani da lafiya bazan iya zuwa ba, ka tabattar sakona ya isa gurin Jawwad" Ta juya ta cigaba da danna remote, haka ya mike ya fice daga palourn tabi bayansa da harara. Ya fita ba dadewa sega Ilham ta fito daga dakinta, tazo ta samu guri kusa da Mummy ta zauna. Ji tayi Mummy tana tsaki ta dan kalleta tace "Mummy lafiya kuwa?" "barni da abun haushi, daddy ze batamin rai, wai se in bishi bauchi gurin bikin nan, ta yaya zanje gurin da Salma zata, ana Auren danta inje, ai na gama zubewa, ba dan ita ba da kodan Jawwad senaje bikin nan, Amma saboda Salma da wannan banzar yarinyar bazani gurin nan ba, Amma bayan biki har can Abujan zanje gidan Jawwad in masa Allah ya sanya Alkhairi, yanzuma na bawa Daddy sako ya bashi, Amma ai naga ke kawar Nana ce, meyasa baki bisu ba? " Ya mutsa fuska Ilham tayi tace "Tabdijan akan me zanje, Ai daga baya na gane da hadin bakin ta Wannan banzar take son janye hankalin Yaya Jalal daga kaina, dan haka ba abunda zanje in musu, suje can su karata" Haka suka cigaba da hirarsu, Ilham na kara kushe Jalila a gurin Mummy. Jalila Tana fitowa daga hall din ta samu jikin wata mota ta tsaya tana waya, Ahmad ya kirata, tasa wayar a kunnenta tace "Hello my, ina jinka" ba"a iya jin me ake cewa amma tace "Shikenan in an nagama zan maka magana se mutafi tare" ta dan kumayin shiru tace "A'a idan na koma gida zanci Abinci, bazan iya cin Abinci yanzu ba, in aka tashi zan maka magana" Ta kashe wayar, tana juyowa taji gabanta ya fadi, Jalal ne a tsaya a bayan ta, ya kura mata ido ko kyaftawa ba yayi Dan tsayawa tayi itama tana kallonsa, tunda yazo ko sannu bata hadasu ba, ba karamin kyau manyan kaya sukeyi masa ba, gashi gaba daya ya cika gurin da kamshin turarensa, tayi kokarin bin ta gefensa ta wuce, ya kara tare mata hanya, dagowa tayi tana kallonsa ya hade rai kamar be san meye dariya ba yace " Zoki wuce mu tafi" Tai masa kallon ban gane nufinka ba tace "Kamar ya, mu tafi ina?" "ban sani ba, ki wuce mu tafi nace" yayi maganar cikin fushi" Zumbura baki tayi, tace "Wallahi ba inda zani ba'a gama ba" yasan halinta da taurin kai, dan haka yasa hannu ya janyo ta har tana kokarin faduwa saboda takalmin ta me tsinine, ba shiri tabi shi be tsaya da ita ko'ina ba se gaban motarsa, ya bude motar yace "Shiga" ta kalleshi, cikin muryarta me sigar shagwaba tace "meyasa zan shiga? Ina zaka kaini kowa yana can ana abun Arziki" "Wallahi in baki shiga ba zan sakaki da kaina" Zare ido tayi ta kalli idonsa, babu alamun wasa a abunda ya fada tabbas ze aikata, ba shiri ta shiga motar, ya za gaya ya shiga ya kunna motar, yafara tuki cikin nutsuwa ya bar harabar gurin, yafara tukin kenan aka kirashi a waya, ya daga wayar yasa a hands free, da'alama abunda ya shafi aikin suke tattaunawa shida wanda ya kira shin, dukda zuciyarta a kule take da haushi, Amma bayan ya gama wayar tace "Ya Aikin kuwa?" Kamar jira yake tayi magana yace "ban sani ba, bakida kunya, saboda ke na tafi aikin nan for almost four months baki nemeni ba, Rayuwa ta kaman wanda yake cikin rijiya ne yake neman taimako, kin mikomin abu ina kokarin fitowa kin saki nakoma ruwa, dan kinga ina lallabaki kikemin wulakanci ko? " " ni wani wulakancin nayi maka? Mekake so in maka kuma? In cigaba da bibiyar ka mahaifiyarka tana min kallon mazinaciya? Da kazo garin nan kana kallona shekaran jiya, har kusa faduwa nayi saboda dalilinka, ko kallona bakayi ba, so kake inta binka, kokuma goyaka zanyi? Ni kawai ana can ana Ta shagali nikuma ka dakko ni, duk gurin nan nika dai na tsole maka ido, ga Ahmad ma yama jirana, yanzu se yayi ta jirana, idan ya tarar bana nan bazeji dadi ba" ya lura gaba daya a fusace take, yai mata shiru taita mita, yadda Jalila ke kuma fadar Ahmad yafi komai bata masa rai, dan haka yaja wani uban birki a kan titi da seda ta firgita, ya juyo yana kallon ta, ya matso da fuskarsa daf da tata, har suna jin numfashin juna, Jalila najin saukar numfashinsa a fuskarta, gaba daya Jikin Jalila ya hau rawa, taji numfashinta na kokarin tsayawa, gaba daya kamshin turarensa ya cika mata hanci, ga kuma wani mugun kwarjini da yayi mata, cigaba da matso da fuskarsa yake daidai tata, har dogon hancinsa na shirin taba nata, rintse ido tayi sosai jikinta na cigaba da rawa. A hankali ya dauke fuskarsa, yace mata "stop shivering, kina tunanin wani abun zan miki? Ba abunda zan miki, sedai ina kokarin nuna miki illar shigar da kikayi ne, look at yourself," Jin abunda ya fada, Yasa A hankali ta bude idonta tana cigaba da sauke numfashi. Ya kuma kallon ta yace "kalli jikinki babu mayafi, kin hau stage kina Rawa, kowa ya zubo miki ido kina rawa, kalli jikinki, kalli yadda kayan nan suka matse ki, hakan ya dace? " Kallon kanta tayi, taga yadda rigar ta zauna a jikinta, taga irin yadda Jalal yasata a gaba da kallo, gaba daya seta ji kunya ta kamata, Amma ta maze ta dake, takuma hade rai tareda dauke kanta tace "Ai dai bahaka na keyi ba, dan dai yau daya, ana biki zaka wani takuramin, naga kai da gajeren wando kake yawo a layi, waye ya dameka?" Jalala seyayi kamar besan dashi take ba, ya fuskanci rigima takeji, idan ya biye mata fada za suyi a titi, banzan da yayi da ita, hakan ba karamin batawa Jalila rai yayi ba, wayarta ta fara ringing, tasa hannu ta ciro wayar daga jakarta, ta daga wayar tasa a kunnenta, beji me aka ce ba, sedai Jalila cikin shagwaba tace "please my, na dan fitane yanzun zan dawo Insha Allah, ka jirani semu tafi tare" Cigaba da wayarta tayi hankali kwance, ta gama tana kokarin ajiye wayar, Jalal yasa hannu ya fizge wayar daga hannunta yace "Wallahi bazaki koma gurin nan ba" "Saboda me? Ni gaskiya ka maida ni, wai meye haka?" "Wallahi kika kuma yi min gaddama, Kano zamu nufa a daren nan, daga nan zuwa a Asuba ma isa kanon, babu abunda yayi min zafi da wani zargi ko wani abu daza'a ce akan hakan, kinsan ni bana gudun magana" A firgice ta kalleshi, babu alamun wasa a idonsa, he mean what he said, yadda fuskarsa take murtuk din nan, ta tabattar ze aikata abunda yace dan haka taja bakinta tayi tsit, tana kallon wayarta tanata ringing, Amma Jalal ya share, ga shi tana tsoron abunda ya fada, dan ze aikata. Tanaji tana gani ya maida ita gida, yayinda ana can ana rakashewa, gaskiya Jalal ya kwafsa mata, suna zuwa harabar gidan taga motar daddy, da sauri tace "laa motar daddy yazo" Nan ma shiru Jalal yayi mata, yana parking ta bude motar ta fice, cikin Sauri ta nufi wata kofa, da ya kasance bangarene da Daddyn Hanan yake saukar manyan baki idan suzo, kamar yadda aka nuna mata. Tana zuwa ta bude kofar ta shiga da sallama, Daddyn Jalal ne, da Daddyn Hanan sekuma Abba, da wani babban mutum wanda Hanan tace mata baban Yaya Yusuf ne, suka amsa mata cikin sakin fuska. Tana zuwa ta zauna a gefen Abba, ta kalli daddyn Jalal tace "Daddy sannu da zuwa ya hanya?" "lafiya kalau Jalila ya taro?" "lafiya kalau Daddy" "to Masha Allah, Allah yasanya Alkhairi, Allah ya kaimu naki da rai da lafiya" Suka amsa da Ameen amma banda Jalila da ta sunkuyar da kai. Daddyn Hanan yace " 'yar baba, keko ganinki bana yi tunda aka fara bikin nan, ina kika shiga haka?" "Baba ayyuka ne dayawa, kuma naga baka dawowa se dare" "Hakane kam, sannun da aiki, Allah ya kaimu naki auren ' yar Baba" Abba yace "Baby ya akayi kika dawo ke? Naji ance kuna gurin walima, ina Kika baro Amaren?" "Suna can ba' a tashi ba, ba Yaya Jalal ne... Bata karasa ba Jalal ya turo kofar dakin ya shigo da sallama" Shikan sa daddyn sa rabon da ya ganshi wata hudun kenan, ya sha manyan kaya yayi kyau, babban abunda ya daurewa daddyn sa kai be wuce yadda yayi sallama ba kuma ya risina yana gaishesu, suka amsa Daddyn Hanan yace "ABDUL JALAL ashe kazo, Amma ban ganka ba, bamu hadu ba sam" Jalal yayi murmushi yace "banfiye fitowa ba shiyasa baka ganni ba" "Masha Allah, Yaya gurin Aikin na ka? " Lafiya kalau, ina jin dadin Aikin, Amma nafison zama na a kano, gashi sunce sena kara watanni, bana son zaman lagos din nan" Daddyn Hanan yace "Nayi farinciki ganinka ABDUL, kayi kalau da kai, me yasa baka son zaman lagos din?" Daddyn sa yayi murmushi yace "baya son sabga da Mata, kasan kuma lagos babu ruwansu da Addini ko Al'ada, in munyi waya yana gayamin ;shi baya son Abunda matan kabilun nan sukeyi" suka kwashe da dariya, Abba yace "Karka damu Kaji Jalal, kana da gaskiya" Daddyn Hanan ya kalli baban Yusuf yace "Kaga yaron dana ce ka samarwa Aiki, Ansamu improvement kwarai a tattare da shi, gaskiya 'yar Baba tana da kai sosai, ita tayi wannan tunanin a samo masa aiki, tace min in aka samo masa aikinyi hakan ze dauke masa hankali da ga barna da yake kuma ya rage masa damuwa da kadaici, a haka gata kaman bata iya komai ba se shagwaba da tsokana amma tafi Hanan kai" Baban Yusuf yace "ABDUL JALAL karka damu kaji, haka sha' anin Aiki yake, ba inda baya kai mutum, kai dai kayi gaskiya ka rike Addininka kuma kaji tsoron Allah" Sukace hakane, daddyn Hanan yace "Karka damu Jalal, za'a san abunyi, babban farincikin danayi, daga can lagos din sun kirani suna yaba maka, naji dadi sosai wallahi, Abunda yake kara shashi shaye2 da wannan phobia din na rashin son mutane,  hadda psychological issues, yana bukatar me jansa a jiki, be kamata saboda halin da yake ciki na shaye2 ayi watsi da shi da lamarin sa ba, kokuma a dinga yi masa mummunan furuci ba, ko mutane su kyamace shi gaba daya ba, kuma wannan yana daya daga cikin matsalar society dinmu, wallahi wanima ko masallaci yaje baza'a hada sahun salla da shi ba, daga haka suke fara janye jikinsu daga mutanen kirki, se na banza su janye su, maimakon a jasu a jiki da nasiha da rarrashi" Daddyn Jalal ya dan girgiza kai yace "Wallahi you said it all sir, Jalal gaba daya gudun mutane yake se tsirari, musamman mata, saboda yarasa wani babban jigo a rayuwarsa da duk wanda yarasa dole yayi kuka, shiyasa da Wannan 'yar tawa Jalila da Jawwad banida abunda zan biya su da shi, ko iya haka aka tsaya sun kawo gagarumin sauyi ga rayuwar ďana, bani da bakin godiya, ban taba tsammanin za' a samu sauyi kwatankwacin haka akansa ba" ya karasa maganar yana kokarin hadiye kwalla da ta taru a idonsa, gaba daya sukayi tsit cike da tausayin Jalal da mahifinsa, Jalal ya sunkuyar da kai, yana tuna Abubuwan da suka shude na rayuwarsa, Ya fuskanci kaddara daban2, gaba daya tausayin kansa dana daddy ya lullube shi. Jalila kam cikin sanyi jiki, tace "Haba Daddy, ni me nayiwa rayuwarsa dana cancanci wannan godiyar da kuke tayimin, wallahi banga abunda nayi masa dana cancanci hakaba, ni yakamata in baku hakurin cin zarafin sa dana dingayi a gabanku, nake kiransa da kalamai marasa dadi Amma.... Sekuma maganar ta kasa fitowa saboda kuka, dan Haka ta mike, da sauri tabar dakin. Shikam baban Yusuf mamaki ne ya cika shi, ace kamar wannan yarinyar ta sauya akalar Rayuwar matashi da ya riga ya dilmiya a gurbatacciyar rayuwa, itakuwa wace irin baiwa ce da ita, ko dayake ance mata 'yan baiwa ne, sedai kowacce akwai sigar da take Amfani da tata. Jalal yace "daddy seda safenku, zanje in kwanta" Abba yayi karfin halin cewa "to shikenan Allah ya tashemu lafiya" Ya amsa da "Ameen" ya mike ya fito kaman wanda kwai ya fashewa a ciki. Jalila takoma part dinsu ta canza kaya, tayi wanka, har tayi ta fito tausayin Jalal da daddy ne fal a ranta, se goge Hawaye take lokaci zuwa lokaci. su Hanan suka dawo, suna zuwa suka tarar har tayi bacci. Nana tasa hannu tasheta, Jalila ta mike zaune tana kallonsu tace "meye kuma na tashi na?" Nana tace "ya akayi kika taho ne? Tun a can Maama take nemanki, Ahmad se kiranki yake a waya baki daga ba" Se yanzu ta tuna wayar tana gurin Jalal. "Su Abba ne sukazo shiyasa na dawo gida" ta basu amsa Hanan tace "keda wa kuka dawo, dan nasan baki san hanya ba" "ban sani ba, uwar kwakwakwafi a isak na dawo" Hanan tace "daga tambaya? Allah yabaki hakuri" Siyama tace "Jalila wallahi Jalal ya hadu, kinata masa wulakanci, wani kallo da yake miki kamar ze cinye ki" Sukasa Jalila a gaba da tsokana tayi musu banza ta kyalesu. Jalal yana zaune yana ta tunanin abubuwan da suka faru dashi a baya, shi kansa yana sarawa namijin kokarin Jalila, ta iya lissafi gata da himma da kokari, duk rashin kunyarta da taurin kai, akwai kawaici da tausayi, duk zamansa da Jeje besan Cutar shi yake ba, Amma ita a ranar da suka fara haduwa ta gane hakan, ta saka rayuwarta a hatsari da dama saboda shi, besan mezeyi ya saka mata ba" kallon wayarta data ke faman ringing yayi, sunan My yana yawo akan screen din wayar, har wayar ta gaji ta katse, hotonta ne akan screen lock dinta tana murmushi, ya kurawa hoton idon na dan lokaci, ya sa hannu ya shara screen din, wayar ta babu key a kai, wallpaper dinma hotonta ne da Nana, kanta babu dan kwali, ta dan turo baki Nana kuma tana dariya, ya dade yana kallon wallpaper, yayinda kiran Ahmad ya shigo ba'a dadi, ya gaji sa wayar a silent ya ajiyeta ya cigaba da tunani, Yana cikin tunanin ne, Angwaye suka dawo. Jawwad beyi mamakin ganin Jalal a gida ba, dan ba karamin aikinsa ne gurin dinner din ma yaki zuwa gaba daya ba. Gaba daya Ahmad ransa a bace yake yana ta tunanin ina Jalila ta shiga haka? Ya kira har ya gaji amma bata dagawa, kuma ya duba hall din nan be ganta ba, sukayo wa Angwaye rakiya yana shirin fita daga dakin yace "Jawwad zan tafi seda safe, Dan Allah ko Jalila ta dawo ne ? Nakirata har nagaji bata dagawa" Jawwad yace "Aini tunda ta sauka akan stage din nan ban kuma ganinta ba, Amma ka kira wayarta mana" "Aina kira wayarta ta bata dagawa" Jawwad yace "Idan ma ta dawo yanzu nasan tayi bacci, Amma bari in kira wayar ta ta" Jalal yana jinsu amma be tanka musu ba, Jawwad na kiran wayar Jalila yaji ringing dinta a dakin, da yake yasan tone din wayarta, Jawwad ya kalli inda ringing din wayar ke tashi, tana kan teburin dake gaban Jalal tareda wayoyinsa, Jawwad ya tafi gaban tebur din, yaga tabbas wayar Jalila ce, Jawwad ya kai hannu ze dau wayar, yace "ya akayi kuma wayarta tazo nan?" Jalal ya sa hannu ya dauke wayar ya kashe wayar gaba daya yace "wayar tana gurina, tare muka taho" A fusace Ahmad yace "Amma dan wulakanci kanaji ana maganar kayi banza? Meyasa zaka dakko ta? Na lura tunda kazo kake wani jin kai da nunawa mutane gadara, ubanwa kafi? Zaka dinga nunawa mutane jin kai, meye naka na shiga sabgarta? Waye dinta kai? Dama ana fadin kana shaye2 wallahi kamin hauka kurata zansa sumaka duka" Jawwad da sauri yace "yi hakuri Ahmad, baka fahimci Jalal bane, shima yayanta ne yana da iko akanta, Bekamata ka dinga wannan maganganun ba, an riga an zama daya" Zuciyar Jalal wata irin tafasa take, ba dan Dalilin Jawwad ba wannan banzan ya isa ya tsaya gabansa yana zaginsa, dan takamarsa yanada kaki, idan takamar Ahmad kakin soja, shikuma yana da abunda ze siye shi da kakin nasa yasa Aljihunsa Kawai Jalal ya jingina da kujera ya zaro karan sigarinsa ya kunna yana kada kafa. Karshen kuluwa Ahmad yayi, wai uban me Jalal ya taka yake wannan gadarar. Abdallah ne ya shigo dakin da sauri yana fadin "Jawwad ana nemanku a part din daddy, kaida Ahmad" Jawwad yace "Allah yasa ba wani abun mukayi ba?" "ba abunda kukayi ance dai in kiraku" Jawwad yace "Amma a daren nan haka? " kuzo dai muje, ko menene kwaji a can" Seda Ahmad yayiwa Jalal wani banzan kallo, yayinda shikuma Jalal yakara yawan hayakin da yake fesarwa a iska, yana lumshe ido Ahmad ji yake da da bindiga se ya harbe Jalal, haka suka fita suka tafi. Su Jalila kam, babu alamar zasu kwanta yanzu, hira kawai suke suna shewa, Maama ta shigo dakin tace "har yanzu baku kwanta ba?" Hanan tace "Wallahi Maama, mun kasa baccin ne, shiyasa muke ta hira" Maama tace "lallai kam, ke Nana magana fa ta canza, da mun zata nan da sati biyu zaki tafi, Hajiya Salma tace; dake zasu tafi maiduguri, visar ki ta samu, in aka daura Aure gobe in Allah ya kaimu ranar Asabar zaku tafi maiduguri, litinin zaku tafi can England keda Mahmud, dan haka za'a kawo miki kayanki da zaki tafi dasu, bayan kun tafi" Take jikin Nana ya hau rawa, cikin rawar murya tace "Maama litinin fa, yayi kusa da yawa" Jalila tace "dan Allah Maama a barmin ita se nan da sati daya" Gaba daya suka fashe da kuka daga Nana har Jalila, Maama taga bazata iya zaman rarrashi ba ta tafi ta kyalesu, Ai Jalila har tafi Nana shiga damuwa, Hanan da Anty fiddo ba yadda basuyi ba amma suka ki yin shiru musamman Jalila, kwana tayi tana kuka, bata taba tunanin zataji haka ba in Nana ta tashi Aure, Kamar wasa har wayewar gari ranar daurin Aure kuka take, hakan ya saukar mata da ciwon kai da zazzabi me zafi. Hajiya Salma ta samu labarin halin da Jalila ke ciki, tazo ta dinga rarrashin Jalila, aka nemo likita yabata magunguna, aka samu tayi wanka. Daddyn Hanan yace akai Jalila bangaren sa ta samu ta huta saboda hayaniya. Haka kuwa akayi, wunin ranar bata fito ba daga bacci se salla, ta sha kuka shikenan Yaya Jawwad ya tafi da Hanan lagos, Nana ta tafi England, shikenan se ita kadai. Har aka gama wunin ranar tana kwance saboda zazzabi ga ciwon kai, ita kanta Nana wunin ranar da kuka ta yi shi, se bayan magariba, Mummyn Hanan ta shigo dakin da Jalila take dauke da Akwatin Jalila tace "Jalila maza tashi ki wanke fuskarki, ki sa hijjabinki ki biyoni ana san ganinki" Jalila tace "Nikuma? Amma me za'ayi da trolley dina anan" "in munje zakiji, tashi maza" jiki a sanyaye ta mike ta saka hijjabi, har yanzu kanta ciwo yake, dukda zazzabin ya sauka. Tabi bayan Maama har wani katafaren parlour da yake wani bangare na gidan, suna shiga taga Angwayen nan gaba daya da Amare, sekuma iyayensu maza. Jalal na gefen Jawwad a zaune. Ta samu guri kusa da Mummyn Hanan ta kwanta a jikin Maama saboda dikinta ba kwari. Sukai tai mata sannu. Da alamu an dade ana tattaunawa ita kadai ake jira, Maama ta rage murya ta radawa Jalila Daddyn Jalal ya gabatar da kyautar da Mummy ta bayar abawa Jawwad, kyautar gida a Kano, sannan ita ta bayar da sadakin da'aka biyawa Jawwad naira dubu dari. Jalila tayi mamakin hakan kwarai Kowacce aka mika mata sadakinta a hannunta, akayi musu nasiha da fada sosai tareda Addu'oi, aka sallami su Hanan, da Nana, Siyama bayan daurin Aure suka koma Kaduna, daddy yace Jalila ta tsaya, Jalal ma yana zaune a gurin. Abba ya mikowa Jalila bandir din kudi, Mummyn Hanan ta mika mata, ta sa hannu ta karba cike da mamaki "Abba wannan na menene?" ta tambayeshi tana juya kudin "Sadakin ki ne" a tsorace ta zare ido ta kalli kudin "Sadakina kuma? Waye mijin?" ta fada a firgice Daddyn Hanan yace "kwantar da hankalinki gashi nan a gefenki ABDUL JALAL ne ba wani ba!!!! Ai a zabure ta zubar da kudin ta ja da baya tana kallon Jalal da ya sunkuyar da kai tana zazzare ido. In ba'ayi Comments yadda nake so ba, in na tafi se bayan sati zanyi posting Ina son jin comments dinku, predictions, and your opinions thank you 😍 😍 😍 😍 😍 😍 😍 😍 😍 😍 Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724    🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE  4️⃣9️⃣102 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Jalal ya dago yana kallon Jalila, cikin kuka Jalila tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji un, Abba me yasa? Laifin me nayi a kayimin haka?" Abba yace "kwantar da hankalinki, nasan bazaki watsa min kasa a ido ba, ba laifin da kikayi, ganin da cewar hakan mukayi shiyasa muka yanke wannan hukuncin" Girgiza kai ta shiga yi tana kuka, daddyn Hanan yace "Calm down my daughter, kinga bakida lafiya, meye abun damuwa? Jalal ne kin sanshi ba wani aka Aura miki wanda baki sani ba, bakomai kiyi hakuri, Allah yabaku zaman lafiya, Kuma nasan kina sonshi ai ko?" Girgiza kai tayi da sauri tace "Ni wallahi bana sonshi, Allah bana sonshi haba daddy, duk 'yan uwana ba wanda akayiwa haka seni, daddy Why? Wallahi ni ba son Jalal nake ba tausayin sa kawai nakeji" Abba yace "ba cinya ba kafar baya" Daddy yace "to wa kike so"? "Ni Ahmad nakeso" ta fada kanta tsaye tana kuka. Jalal yasan za' a rina, yasan setayi daru, Amma be taba zaton Jalila zata iya furta bata sonsa ba agabansa haka" Mummy tace "Ke rufewa mutane baki, kaunar da'ake miki yasa aka zaba miki Jalal din, in kun zauna zakiji son, kar in kara jin wannan maganar a bakinki, Ahmad yana da mata, ko yanzu yaga dama ze iya neman wadda yakeso a bashi, kamar yadda kikace tausayin Jalal kike, to kiyi hakuri kicigaba da tausayin sa" Maama kanta jikinta yayi sanyi, seda ta bada shawarar a ji ta bakin Jalila kafin a yanke wannan hukuncin amma basu bi shawarar ta ba. Jalila ta mike da sauri ta fice daga palourn tana kuka. Baban Hanan yace "Jalal sekayi hakuri, kasan yarinya ce karama, kuma an shammace ta, ba zato ba tsammani aka daura mata Aure, kuma tana ganin duk 'yan uwanta su suka kawo wanda suke so, kayi hakuri da abubuwan dazata yi maka ze wuce kamar ba'ayi ba, gata nan Amana ka rike ta da amana" Sallamar Hajiya Salma, da kannen Mahifin Jalal, da shi kansa daddyn Jalal, ya katse wa Daddyn Hanan maganar da yakeyi, suka amsa musu sallamar. Suka karaso suka zauna, daddy yafara magana "Dukkan yabo da godiya da jinjina da kirari sun tabatta ga ubangiji ma daukakin sarki, me kowa komai, Alhamdilillah anyi taro lafiya an gama lafiya, muna fatan Allah yasa anyi kenan, Allah yabasu zaman lafiya, sannan Alhaji Usman, bazan gaza gurin kuma nuna godiya ga dawainiyar da iyalanka suka dingayi da ďana ba har kawo wannan lokacin da kukayi masa ko ince kuka yimana wannan karamcin, iyalanka sun Rungumeshi lokacin da mutane kowa ke gudun sa, Mungode mungode Allah yasaka da alkhairi, Allah yabiya ku da gidan Aljannah ya jikan magabata, Kuma Insha Allah bazamu baku kunya ba" Abba yace "Masha Allah, Alhaji Habib duk abunda nayiwa Jalal tamkar Jawwad nayi wa ne, ABDUL JALAL tun tasowarsu da Jawwad yake kaunar sa, kusan kaso mafi yawa na Rayuwarsa a gidana yayi ta, dan haka yiwa kaine Allah yabasu zaman lafiya" Itama Hajiya Salma godiya takuma yi da nuna farincikinta akan wannan lamarin. Jalila kam tana zuwa ta zube a jikin Hanan tana wani irin kuka me sauti, Hanan ta kalli Nana suka hada ido ta dan jinjina kai, sannan tace "Wai Jalila lafiya kuwa? Meyafaru ne haka?" Jalila ta dago idonta da tuni yayi Ja tace "Hanan wai an daura min Aure nima" Nana tace "Aure, dawa aka daura?" "Nana wai Jalal aka auramin, meyasa a kayimin haka? Takuma fashewa da kuka Hanan tace " kece baki sani ba, mu mun riga munsan za'a daura muku Aure" Zumbur Jalila ta tashi zaune ta kalli Hanan "Amma meyasa baku gayamin ba?" "Saboda ana gudun wannan shirmen dazaki yi, aka gargade mu karmu sake mu gaya miki, kuma ni banga aibun abunda akayi ba, hakan shine dai2" "Haba Hanan meyasa zakimin haka? Ko dan na tsaya tsayin daka kin samu wanda kikeso, shine ni zakimin haka?" "Jalila abunda ya dace akayi, nasan abunda akayi miki babu dadi, Amma iyaye basa zabawa yaransu abunda ze cutar dasu, wallahi Jalila sekin fi kowa Alfahari da shi nan gaba, Yana sonki, kuma kema kina sonshi, sann...... " Dan Allah dakata Hanan " Jalila ta katseta " dan bake akayiwa ba ko? Ina da wanda nakeso amma an Auramin wani daban, shine ya gaya miki yana sona, babu wani abu makamancin soyayya a tsakanin mu, ta yaya zan fara rayuwar Aure da Jalal, bahagon mutum me wani irin murdaden hali, Mahaifiyarsa bata kauna ta, ko kinsam tana zargina da ďanta, Mahaifiyarsa tana da wanda takeso ya Aura, ta yaya zanyi zaman Aure da wanda mahaifiyarsa bata sona, Hanan nasha wahalar Rayuwa, yakamata ace lokaci yayi da zan huta, wannnan Auren tamkar kara jefa Rayuwa ta cikin wata wahalar ne, nasha wuya Ina bukatar zuciyata ta huta Nashiga uku ni Jalila " " Subhanallah ke Jalila meye hakane kikeyi? " Muryar Mummyn Hanan ce take magana, da suka shigo ita da Maama, tace "duk Nasihar da'akayi miki baki jiba kenan? Meyasa bazaki dauki kaddara ba, ko ba'ayi haka ba dama Allah ya rubuta shine mijinki" Kuka Jalila takuna fashewa da shi maama tace "Jalila kidena kukan nan haka, batun mahaifiyarsa bata sonki ze wuce, musamman idan ta gane mahinmancin ki ga danta, Jalila tunda kika iya jure rayuwar gidana duk taren kalubalen da kika fuskanta daga gareni da 'yan uwana, bana tunanin akwai wani kalubale daze tsoratar dake, Anmiki ba dai2 ba tabbas, Amma kiyi hakuri ki rungumi kaddara ki riki mijinki, ki masa biyayya, idan kikayi hakuri kikayi biyayya se Allah yayi miki Rahama saboda hakan" Mummy tace "wannan gaskiyane, kuma shi Ahmad da kike magana, ai Daddy ne yace ya bashi da farko, yanzu kuma ya bashi hakuri, Jalila na tabattar nan gaba sekin fi kowa jin dadin zama da shi" Jalila sam bataji nasiharsu na shigarta ba, ita kawai an gama da ita basu san waye Jalal bane shiyasa suke fadar hakan. Maama tace "Nana ki shirya kayanku, gobe in Allah ya kaimu hadda ita zaku tafi maiduguri" Jalila na jin haka ta kuma rusheewa da kuka. Yusuf ne ya shigo dakin shima a fusace yana fada "haba Mummy, meyasa daddy zeyi haka dan Allah? Yaza'ayi a Aurawa yarinya wanda bata so, kuma bayan yasan ďan shaye2 ne, a family din nan ba wanda aka taba yiwa Auren dole meyasa za'a fara akanta?ga shi sam wannan yaron bashi da mutuci, ga gadara da girman kai" Mummy tace "Sannu jagoran marasa kunya, meyasa bakayiwa daddyn ba seni? Kafi su sanin abunda yakamata ne?" Hanan Kallon yaya Yusuf kawai take yadda yake zakewa yana masifa Jawwad nai yai sallama a dakin shima fuskarsa dauke da damuwa, ya hango Jalila ta takure a gefe idon nan kaman gaita saboda ja, ga fuskarta duk ta kumbura. Bebi takansu Maama ba gaje gabanta ya tsuguna yace "Baby why? Meyasa kike kuka haka? Gashi baki da lafiya? " "ba dole yarinya tayi kuka ba, an mata Auren dole, an Aura mata ďan shaye2 wanda bata so" Jawwad yace "Yusuf meye haka? Ana kokarin hankalin ta ya kwanta kana son ka kunna wata wutar, koma dai meye an riga an daura Auren nan, ayi musu Addu'a da fatan Alkhairi mana" Jawwad ya kalli Jalila yace "We are sorry Baby, kaddara ta riga fata, dana san ba kya son Jalal bazan bari ayi Auren nan ba, saboda nasan Jalal baze ban kunya ba shiyasa na amince" "Yaya Jawwad ni bana sonshi" "Jalila kulawar da kike bashi da babu so bazaki yi ba, na miki Alkawarin Jalal baze bada kunya ba, kuma shi Alkhairi ne  a rayuwarki, dan Allah Jalila ki kula da rayuwar Jalal kamar yadda kike yi abaya, Nabaki amanar ďan uwana please Jalila" ya karasa maganar kamar zeyi kuka. Girgiza kai Jalila ta shiga yi "Yaya Jawwad.... "Shhhh kiyi shiru, ki karbi Amana ta kidena wannan kukan" Hanan tace "Jalila son da Haidar yake miki baze bari a baki abunda ze cutar dake ba kiyi hakuri da kaddara Queen" Jalila shiru ta musu ba tace komai ba, ita ka dai tasan me takeji a ranta. Jawwad ya mike yace "Mummy seda safenku" sukayi sallama. Yusuf dai ya cigaba da banbami da mita. Su Maama suka cigaba da rarrashin ta tareda Nasiha. Hanan kuma ta shiga hadawa Jalila kayanta dukda tarin gajiyar biki dake tare da ita. Jawwad yakoma masaukin Jalal, ya tarar Jalal yana shirin kwanciya, Jawwad yace "Ango ka sha kamshi" Jawwad ya lura kaman Jalal baya walwala "Jalal Lafiya kuwa? Naga kaman baka walwala, ko baka son Auren"? "Jawwad ba wai bana son Auren bane, idan inason Auren itafa?" Jawwad ya dafa kafadarsa yace "brother karka damu, nasan zataji babu dadi da farko, saboda an mata bazata ba tareda masaniyarta ba an daura mata Aure, Amma nasan tana sonka, kuma a hankali zaku daidaita cikin kankanin lokaci" Jalal yace "Hmm haka dai kake gani" "Hakane ze kasance, ni dai gata nan Amana Jalal, kayi hakuri da ita" Jalal bece komai ba ya danyi murmushi, daga nan suka shiga wata hirar. Hatta Inna ba'a barta a baya ba gurin rarrashin Jalila da yi mata nasiha, dan ita Inna har cikin ranta Jalal yayi mata, dan seda ta zage Yusuf tsaf saboda masifar da yakeyi akan anyiwa Jalila auren dole. Jalila dai yau tayi kwanan bakinciki, dan sam bacci ko na minti goma batayi ba, Ga Jalal ya kwace mata waya balle ta kira Ahmad, gaba daya tausayin Ahmad takeji, yasaka rai akan Aurenta, yana da matukar kirki ya nuna mata soyayya, shiko wannan Jalal din da magana se ya ga dama ta ina ze nuna mata wata soyayya. Har akayi kiran sallar Asubah batayi bacci ba se sakawa da kwancewa, bayan tayi salla ta koma ta kwanta tana jin yadda kanta ke sarawa, ga kirjinta da yayi mata nauyi, se karanto Addu'oi take daban2 ko zuciyarta tayi sanyi. Wajejen karfe bakwai da rabi, Mummy tazo ta kira Jalila suka tafi cikin gida, dakin da'aka sauki hajiya Salma ta kaita, mutane sun ragu sosai duk an watse, se tsirarin mutane da zasu raka Hanan Abuja, sekuma ma'aikata da suke ta kokarin gyara gidan. Bayan sun shiga Jalila kanta a sunkuye ta gaida Hajiya Salma da Antin Jalal, Suka Amsa mata Antyn Jalal tace "Sannu Amaryar mu, Kin tashi lafiya?" Take Jalila ta kuma jin wasu hawayen suna zubowa daga idon ta, Mummy tace "Ikon Allah, har yanzu baki gaji da kukan nan ba?" hajiya Salma tace "haba Jalila, banyi zaton haka daga gareki ba, mun san an miki laifi amma kiyi hakuri, Jalila zakiyi Alfahari da mijinki, yana sonki fiye da yadda kike tunani, gaba daya hope dinmu yana gurin Allah kuma yana gurinki, dan Allah ki kwantar da hankalinki ku zauna lafiya, ki gode Allah, Jalal baya kule kulen mata, ke kadai ce macen dana san yana saurara, kiyi hakuri Jalila " Cikin kuka Jalila tace "Mummynsa fa bata sona, tace in rabu da shi, kuma ba irin maganganun da ban gayawa Ilham akan sa ba, na kirashi da sunaye marasa dadi, kuma kawai ace shi na aura" Hajiya Salma tace "to shine me? Mahaifiyarsa bata sonki ni ba'a gaya miki abunda tayi min ba, ita da Saudat, gidan mijina abun kaunata seda ta rabani da gidan hankalin ta ya kwanta, ko  kin fison a ya auri Ilham din ne? Jalila kece zakisa zaman gidan Aurenki yayi dadi in kin so, ki manta da abunda ya riga ya wuce kinji yarinya ta, Allah ya Albarkaci rayuwar Aurenku, kije ki shirya anjima kadan zamu tafi" "wai a maidugurin zanta zama? Makaranta fa?" Antyn Jalal tace "A'a ba'acan zaki zauna ba, Se a inda yakeso zaku zauna, amma akwai dalilin zuwanki can ďin" Jalila dai ba tace komai ba suka cigaba da rarrashin ta. Haka Maama tazo ta ja hannunta domin fara shirin tafiya. Daddy ya samu Hajiya Salma a masaukinta, shar da ita bakace ita haifi Mahmud ba, sekace kaninta, har yanzu tana tare da Gayunta, Daddy yace "To Salma kinga abun Allah ko ba zato ba tsammani danki ya samu matar Aure, kodayake na dade ina burin Jalal ya Auri yarinyar nan" Hajiya Salma tace "Hakane, yarinyar tana da nutsuwa da kirki, dangin yarinyar nan sun gama yimana komai, Amma daddy wai ya'akayi abun nan ya kasance" "hmm ai shekaranjiya dana zo, yazo ya ganni muna tare da iyayen Jalila, shine suke tambayarsa ya aikinsa? yace bayason zaman lagos, nake ce musu yanayin sabanin Addini da al'adun mutanen garin ne yasa baya son zaman garin, bayan ya tafi ne, kawai Captain Abdurrasheed yace ; inyana da wadda yake so ai masa Aure ya tafi da matar can lagos, se nake ce musu bana tunanin yana da budurwa, saboda yace yasan babu me bashi 'yarsa yana wannan halin, se captain Rasheed yace; indai yana son Jalila ya bashi ita, shine aka kira Jawwad da yaron daza' a bawa ita da, aka tambayi Jawwad yana ganin in aka Aurawa Jalal ita ze zauna da ita? Jawwad yace "ai Jalal yana sonta, dan haka suka kira shi wancan yaron suka bashi hakuri, shikansa Jalal be saniba se jiya a gurin daurin Auren" Hajiya Salma tayi ajiyar zuciya tace "Allah me yadda yaso, kaga Al'amarin ubangiji, ba zato babu tsammani my Son yasamu mace ta gari" "Hakane amma yaushe zaku bashi ita? Naji kince da ita zaku tafi maiduguri" Tai murmushi tace "Daddy kenan, yadda aka daura aure a bagas ba tareda ya sha wata wahala ba, bazan bashi yarinyar nan a bagas ba, bazamu bashi ita ba se mun tabattar da irin Son da yake mata, dagaske yana sonta kokuwa? Zata zauna damu tasanmu, sannan muyi mata shiri irin namu na 'yan barno" Daddy yai murmushi yace "haba Salma, a takaice dai ta wani bangaren kuna son ku wahalar min da yarone kawai" Tayi murmushi tace "Zamu temake shi dai, yawwa sannan Jalila tana kukan matarka Khadija bata sonta har tana zarginta da Jalal, wannan karon bazan lamunci duk wani nau'i na rashin mutunci daga gareta ba, idan baka dau mataki akan wannan lamarin ba, Zeyi wuya mu bawa Jalal matarsa anan kusa, saboda nafi kowa sanin khadija nasan abunda zata iyayi, a wannan karon bazan bari ta cutar da 'yar mutane ba kamar yadda ni tayimin ba" Ta mike tsaye tace "daddy bari inje in karasa shiryawa, da wuri zamu tafi" Ta wuce cikin dakin, Daddy yabi bayanta da kallo, har yanzu Salma tana nan da gayunta da iya kwalliya, nan ya dinga tuna abubuwa da dama da suka wuce a baya. Wanda zasu yiwa Hanan rakiya tuni sun shirya dan yiwa Hanan rakiya can gidan Jawwad dake babban birnin tarayya, Hanan tasha kuka, da kyar aka banbare Hanan daga jikin Mummyn ta, daddy yayi mata nasiha Sosai, suka hau motoci sukayi gaba. Da kyar Maama ta takura Jalila ta ci Abinci aka bata magani, Karfe dayan rana Aka gama kintsa Jalila da Nana, suka fito domin tafiya, Jalila ko ganin gabanta batayi saboda kuka. Tunda su Jalila suka fito Jalal ya sauke idonsa akanta ta rame sosai ga idanuwanta sunyi Jawur, gaba daya tausayinta ya kama shi, ko ya takeji a ranta oho? Sosai yake jin tausayinta a ransa. Yadda Jalila da Nana suke kukane yasa jikin Maama yayi sanyi, shikenan Nana zata bar kasar se lokaci2 zata dinga ganinta, duk kiyayyar da tayiwa Jalila a baya, bata taba zaton zataji babu dadi haka ba, Zatayi missing din yarinya me kara da kawaici, ga Jawwad shima ze tafi, zasu bar mata gidan se ita kadai, yadda Jalila ta rirrike Maama tana kuka kamar mahaifiyarta yasa Maama ta kamu da matsananciyar kunyar muzgunawaa Jalila data dinga yi, ba tayi aune ba taji itama Hawaye na bin idonta ta kuma rungume Jalila a hankali tace "ki yafemin Jalila" . Jalila ta kankame Mama tana cigaba da kuka Abba yace "haba in kina kuka zaki karya musu gwiwa ne, kiyi hakuri, ki gode Allah da ya nuna miki Aurensu kuka rabu lafiya" Antyn Jalal tace "Ai dole tayi kuka, kowace uwa haka takeji a lokacin da take bankwana da 'ya' yanta, yaranta uku zasu tafi su batta lokaci daya, maman Hanan ma tana can ta nayi" Daddy yace "ya za'ayi se hakuri" Haka aka sa su Jalila a mota, ana musu fatan Alkhairi. Mota daya Jalila, Nana da hajiya Salma suka hau, kanin Mahmud ne ze jasu, sekuma tawagar Angwaye da sauran 'yan uwansu dazasu biyo bayansu, Hajiya Salma tace Jalal ya biyosu a tasa motar, Jalila naji na gani suka ďaga suka nufi borno. Tunda aka kira Ahmad aka bashi hakuri akam Aurensa yarasa ina zesa ransa yana matukar kaunar Jalila, sannan duk yadda zeyi yaga Jalila be samu damar yin hakan ba har suka tafi. Yusuf kam ko sallama beyi musu ba saboda bacin ran abunda akayiwa Aminin nasa, haka kurum an hana mutumin kirki an bawa wannaan sakaran. Daddy ma ya shirya kayansa tsaf, yayi musu Sallama ya koma kano, yayinda Abdallah ma da tawagar abokansa suka tafi yi masa rakiya kaduna kasancewar a can ze zauna. Tuni Labari yafara karade unguwar su Nana cewar an ďaura Auren Jalal da Jalila, da yake Akwai wanda sukayiwa Maama kara sukaje mata biki 'yan anguwarsu, Labari ya zaga unguwa inda wasu suke ganin an kwari Jalila da aka Aura mata wannan mara tarbiyar dan shaye2, bayan ita kamila ce, me kirki da faran faran ga kowa, Amma duk abun nan ba wanda yaje ya Tari Mummy ya gaya mata. Bayan la' asar Daddy ya je gida, da ya koma gida be gaya mata ba, seda yaci Abinci yayi wanka yai salla. Suna zaune da Mummy tana ce masa "ya hanya? Ya kabaro su? " lafiya kalau Alhamdilillah, Jawwad da iyayensa suna godiya " Ya mike ya debo goro da alawowi dayawa ya zube a gabanta. Ta kalleshi tace "wannan kuma na menene? " " Na Auren ďanki ne" "ďana kuma? Wanne ďan nawa, daza'a abani wannan kayan haka?" "Aike yaran naki ukune, ga Jawwad, ga Mahmud, ABDUL JALAL" "Jawwad din dai, Mahmud ba ďana bane, sannan ba wanda ya isa yayiwa Jalal Aure ba da izinina ba, idan ma anyi ko 'yar uban waye se an fasa shi, kodayake wace mace ce zata yadda ta Auri wannan ďan naka?" Daddy yace "to shikenan tunda baki yarda ba" Ya dau remote ya kunna tv abunsa. Ta shi tayi tabar masa palourn ta koma dakinta, tunani ta fara yi, tasan daddy da zolaya wani lokacin, Amma kamar in serious tone yayi maganar, tana cikin tunanin ne wayarta ta fara ringing, seda ta kusa tsinkewa hankalin Mummy ya kai kan wayar taje ta ďaga "Salamu Alaikum" Mummy tace "wa'alaikum salam, hajiya Rahama barka da yamma" "yawwa Mummy ya gida ya taro?" "taro kuma?" "Au tambayata ma kikeyi? Baban su yacemin ;yaje ďaurin Auren ďan gidan Alhaji Usman a bauchi, ashe bayan na Mahmud har dana Jalal amma baki gaya mana ba, na miki magana ta what's App bakiyi responding ba" Ai Mummy bata jira me zata karasa cewa ba ta kashe wayar ta kunna data aikuwa messages suka dinga shigowa ana mata Allah ya sanya Alkhairi, wasu na mata mitar bata gayyacesu ba, jifa tayi da wayar kan gado ta nufi part din daddy "dama dagaske kayiwa Jalal Aure ba da izinina ba? Akan me? Saboda me?" "haba Deejah, kefa kikace Jalal ya isa Aure, to menen laifi a ciki dan namasa Auren? Kuma ma yana son matar da'aka Aura masan" "Sekuma nace kayi masa Aure ban saniba, wane irin wulakanci ne wannan? Wallahi baku isa ba daga kai har munafukan da kuka hada kai aka masa Auren" Sintiri tafara yi a dakin, wani irin gumi yana tsatstsafo mata ita Daddy ze yiwa haka? A fusace Tace "Tukuna ma 'yar gidan ubanwa aka Aurawa masa ba tareda masaniyata ba? Kowace' ya ce wannan ta tarowa kanta abunda bazata iya ba, dan sena ga bayan Auren nan Wallahi, sena murkusheshi, bazan taba bari Jalal ya zauna da matar da bani na zaba masa ba, dan babu yarinyar da zan yadda ta juya min ďa, nasan baya son Ilham shiyasa na dage ya Aureta, Amma yanzu Ace an min bazata an rusamin shirina baze yuwu ba wallahi " " Shikenan deeja abunda kike gudu akan ďanki fa se ya faru, Sannan koma wacece zatazo har nan ta gaisheki seki ganta. Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724              ..🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE 5️⃣0️⃣ 103 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Da Sauri Mummy ta sha gaban Daddy tace "Wallahi Habib seka gayamin dan me zaka yiwa Jalal Aure ba tareda nasani ba? Sannan kuma 'yar ubanwa aka Aura masa? Wato kaje kun haďa kai da wannan munafukan' yan uwan naka aka Aurawa ďana yarinya ban sani ba, to wallahi baze yuwu ba, ďa dai nawane nina haifi abuna, dan haka ba'a isa a yanke masa hukunci game da rayuwarsa ba tareda sani na ba" "sekuma kiyi, naga yadda zaki raba Auren ai, indai Jalal ne gaki nan gashi, dai dai yake dake, Akan kira bashi da yarinyar nan zaki kuma lalata alakarki da shine kawai, dan nagaya miki yana sonta" "karyane Wallahi, Jalal bashi da wata yarinya da yake so, Yarinyar dana zaba masa ita ze Aura" Dama daddy yasan ze fuskanci wannan kalubalen daga matar tasa, dan haka ya ture ta daga gabansa yabar mata palourn. Se magariba Su Jalila suka isa garin maiduguri, koda sukaje sun gaji sosai, musamman su Jalila, su da suka sha hidimar biki, basu huta ba akayo wannaan uwar tafiyar. Gaba daya Jalila ji take jikinta kaman ba nata ba saboda gajiya, har suka je maiduguri kanta a kasa yake, se dai ta jimgina da jikin Nana, ko mota tayi bacci, in aka jima ta shige cikin mayafinta tayi kuka, har sukaje Jalila bata kula kowa ba seda taji an tsaya ance sufito. Gidan da akayi parking din motar ne yayi awon gaba da tunanin ta, sekace ba a duniya ba, kallo daya zakayiwa gidan kasan mamallaka gidan sunyi hannun riga da talauci, ko da suka fito daga motar Se guďa akeyi, Jalal idonsa gaba daya yana kan Jalila da take a takure, Suka nufi cikin gidan, tun daga harabar gidan wani irin sassanyan kamshi ke tashi, har zuwa cikin gidan, cikin gidan da'a akwai mutane a gidan da sukazo domin karbar Amaren. Cikin gidan ma kamshin da yake na musamman ne, fiye da na harabar gidan. Aka basu ďaki, suka gabatar da sallolin da suke kansu, Sannan aka kawo musu Abinci, Jalila da Nana ne kawai a dakin dan haka Nana tace "Jalila ki daure kici Abincin mana" Girgiza kai Jalila tayi tace "Na koshi, ke dai kici kawai, ni kaina kemin ciwo" "to ko inyi musu magana a nemo miki magani?" "A'a base kinyi hakan ba, A yanzu dai babu wani magani daze warkar min da wannan ciwon kan" Suna cikin wannan mujadalar ne Anty ta shigo da tray din fruit a hannunta tace "Jalila kuci Abincin mana, ga dangin baban Jalal can suna son ganinku kafin su tafi" Nana tace "Anty Jalila taki cin Abincin, wai kanta ke ciwo" "Subhanallah har yanzu kan ke miki ciwo? To daure kici Abincin se a kira likita ya dubaki" Da kyar Jalila ta cakali Abincin nan ta barshi. Suka fito parlour inda dangin Daddy keson ganin Amare, se hausa suke suna hadawa da yarensu, sunga fuskar Nana yayinda Jalila ta dukunkune  a mayafi taki bari su ganta, dare ya farayi sukayi musu nasiha da Addu'oi, tareda jadadda godiyarsu ga Jalila sannan suka watse a hankali. Dakin da'aka bawa Su Jalila yana da kyau da matukar girma, suka koma suka canza kaya, Hajiya Salma da kanta ta kawowa Jalila magani ta sha, tana shan maganin ta nemi guri ta kwanta tayi lamoo akan gado, tana missing din wayarta, tun randa Jalal ya kwace be kuma bata ba, tana son tayi amfani da wayarta amma ya rike  a gurinsa sekace shi ya saimata. Nana na kwanciya Mahmud ya kirata a waya, Suka dinga hira suna soyewa, kaman ba gobe zasu tafi ba, suna ta soyayya gwanin sha'awa, Jalila ta tuna kowacce ta samu zabinta, ta auri wanda take so suna cikin farinciki amma banda ita, an haďa ta da wanda be damu da kansa ba ma balle wani, take taji wasu hawayen na zubo mata, ta tabatta Auren Jalal wani sabon shafi ne na kaddarar Rayuwarta. Hanan kam gidanta yana da girma amma ba can ba, Amma ya tsaru anyi masa gini na zamani, dauke da wadataccen gini, an kashewa gidan kudi sosai, Sannan daddy ya zuba mata kaya yadda yakamata. Wanda sukayi wa Hanan rakiya suna zuwa a ranar suka juyo gida, suka barota tanata rikici, Seda kowa ya watse bayan sallar magariba sannan Jawwad ya shigo gidan, ya sameta tayi zaman dirshan a kasa ta jingina da gado, ta takure kanta sosai, tayi kuka harta gaji, dan girgiza kai yayi ya karaso gabanta ya tsuguna se kamshin turare yake, A hankali yace "Haba Hanan, kukan ya isa haka, i know you miss home, Amma ba gani ba, sekace wadda akayiwa auren dole, ko kin dena sona ne?" Girgiza masa kai tayi alamar A'a "Yawwa my love 😍, kukan ya isa haka, yau ranar daza muyi farinciki ne, kar kanki yayi ciwo, ko nima kina so ki sani kukan ne?" ya fada yana goge mata hawayen fuskarta. A hankali tace "A'a ni karkayi kuma  nadena kukan" tai maganar cikin shagwaba Murmushi yayi mata yace "Yawwa ai nasan baza kiso ki ganni ina kuka ba, shiyasa nima bana son ganin kukanki" Haka ya cigaba da rarrashin ta har ta dan saki jiki tana hira, Jawwad da kansa yaje kitchen ya dakko plate da cups, ya bude musu kazar da ya shigo da ita, ya cika mata kofi da youghut me sanyi, yace "Bismillah" Ta kalli kazar ta kalleshi tace "Ni na koshi" "me kika ci da kika koshi?" "bakomai" ta bashi amsa, ya lura gaba daya a firgice take, har hakan yaso ya bashi dariya amma ya maze ya ďan bata fuska yace "in baki ci ba, zan kwana da yunwa ne, kuma ni inajin yunwa sosai, tunda aka fara biki bana samun cin Abinci fa, se Ulcer ta kamani ko?" Yai maganar a ďan shagwabe, dariya ya bata tace "in Ulcer ta kamaka ba rabin zamce ai, Dama haka ka iya shagwaba, wallahi tayi maka kyau" tai maganar tana dariya, cikin hikima yanayi ya namata hira ya dinga bata kazar tana ci, seda suka kammala, Jawwad ya jagorance su sukayi Sallar nafila, domin nuna godiyarsu ga Allah da kuma fatan zaman lafiya me dorewa a cikin Rayuwar Aurensu. Se Hamma take tana lumshe ido, da alamun gajiya da kuma bacci a tareda ita, Jawwad ya kalleta yace "Wannan hammar da kike karki hadiyeni mana" Tayi dariya ta Mike, tana cewa "gara in hadiyaka in huta ai" fita Jawwad yayi domin rufe kofofin gidan, da kuma tabattar da komai lafiya. Hanan ta canza kaya, ta nemi guri ta kwanta, wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita. Cikin baccin nata ne tana kokarin yin juyi ta jita a jikin mutum, a hankali ta bude ido tace "Haidar" "My love" ya amsa mata "bakayi bacci ba?" "Banyi ba" "meyasa?" "ina tunani ne" "Nasan me kake tunani, be wuce su Jalila ba, ni na gaya maka komai ze wuce, zasu koma normal, Jalila tana son Jalal, kawai dai kasan ta da taurin kai" A jiyar zuciya yayi, ya kuma kwantar da kansa a jikin ta yace "Naikaina na san Jalal yana sonta sosai, daga baya na yadda da maganar ki soyayyar 'yan uwatanka ne tsakanina da ita, hankalinta akan rayuwar Jalal take, a tunanin ta tausayinsa take ji, amma da haka sonshi yayi mata illa bata sani ba, kaman yadda ban fargaba naki son yakusa karasani" Ya kai bakinsa kunnenta ya rada mata "I Love you my Hanan" Makalkale shi tayi tace "I love you too Haidar" Daga nan hirar kuma ta canza salo zuwa wani abu na daban, tun Hanan tana daurewa tana biye masa, taji abun ya wuce tunanin ta, ta fara neman taimako, 'yan gidan su ba wanda be sha kira ba dama an hadu da uwar shagwaba, A wanna daren Jawwad ya saukewa Hanan wannan rawan kan nata. (nima me rahoto naga abun yafi karfina dan haka na dawo da baya, na fito 😜😜😂😂😂) Gaba daya Nana ta takurawa Jalila da waya, har sha biyun dare tana manne a waya seka ce wata mara aikinyi, haushi duk ya ishi Jalila tana ganin ta fiye zakewa, ji ta ke kaman suna karama ta takaicin da take ciki, ta ja bargo ta rufe har kanta dan ta dena jin abunda Nana take fada. Washegari tunda safe Su Nana suka fara haramar tafiya. Wayar Nana Jalila ta karba sukayi waya da Maama, har daki aka kawowa su Jalila breakfast, Nana kanta ba ta sake taci ba, saboda gaba daya ji take ba dadi, zata daga tabar kasarta ta haihuwa Aure kenan. Karfe sha dayan safe su Nana suka gama shirinsu, suka shirya domin tafiya airport, nan ma seda aka sha daru Da Jalila saboda kuka, haka sukayi Sallama Nana da Mahmud suka tafi. Hajiya Salma bata bisu ba ita seda ga baya zata koma. Bayan tafiyar Nana Jalila dakin ta koma ta kwanta gaba daya ji take duniyar tayi mata fadi, ba abokin hira an kawota inda ba wanda ta sani. Ta lura nan gidan Antyn Jalal ne, tana da yara 'yan mata guda biyu, daya zata girmi Jalila, Husnah da Amal, Amma sam basa san mutane basa shiga harkar mutane, dan haka ko sannu bata hadasu da Jalila, sedai sukan gaishe ta. Hajiya Salma ta shigo ta samu Jalila a kwance tace "Jalila har yanzu jikin ne?" Jalila tace "A' a naji sauki kaina ne kawai be dena ciwon ba" "ko dai likita za'a kira" "A'a Anty naji sauki" "to shikenan, Amma Jalila ki kwantar da hankalinki, ki cire duk wata damuwa a ranki, Kicigaba da raguwarki kaman yadda kike yi a da kinji" Jinjina mata kai kawai Jalila tayi. Koda Hajiya Salma ta fita dakin da Jalal yake taje, yana zaune yana kallon labarai a tashar CNN. "Sannu Jalal kana nan kana kallo, kai ko tambaya matarka bakayi, ka sameta a sauki, dan haka baka damu da ita ba ko?" "to me zance? Kokuma me zanyi? Nima ai bata nemana" "Au hakama zakace ai shikenan, yaushe zaka koma?" "gobe insha Allah" "zakaje kano ne kokuwa?" Jalal ya dan yamutsa fuska yace "daga nan gurin aiki zan koma, bazanje Mummy ta hargitsa min kai ba, lagos zan wuce" "Shikenan Allah ya kaimu goben" Jalal yace "Ameen Amma, se yaushe Zaku bani ita mu koma kano"? Hajiya Salma tace "ita wa kenan?" "Matata mana" ya bata amsa Hajiya Salma tace "au ashe matarka ce, baka da kunya Jalal, se lokacin dana shirya yayi tukuna, ashe dai ka damu da ita" Dan dage kafada yayi irin i don't care din nan. Jalal idan ya tuna yadda Jalila ta ce bata sonsa a gaban kowa da kowa, yana tunanin wani irin zaman Aure zasuyi? Tsawon lokacin nan dama bata taba sonsa ba kenan? To meze sa ya cigaba da bibiyar ta tunda tace bata sonsa. Bayan Hanan tayi sallar Asuba komawa tayi kan gado, wani wahalallen bacci ya kuma dauketa. Koda Jawwad ya dawo ya tarar ta koma bacci, ya hau kan gadon ya ďan tsira mata ido, baccin ta take hankali kwance, tuno darun da tayi jiya yayi, ya danyi murmushi ya janyo ta jikinsa ya kwanta shima baccin ya dauke shi. Wajen karfe tara Jawwad ya tashi, Amma Hanan bata farka ba, ya je ya dafa musu tea ya fita, ya fita ba dadewa Hanan ta tashi daga baccin, taje tai brush tai wanka ta saka wata doguwar riga mara nauyi, ta fito parlour amma bata ga Jawwad ba, ta nemi guri ta zauna a kan kujera, befi mintuna goma da fitowarta ba se gashi ya dawo hannunsa dauke da kaya, yayi sallama ta juyo ta amsa suna hada ido ya kashe mata ido, hakan yasata sunkuyar da kai tana murmushi, ya karaso ya ajiye kayan yace "good morning dear, kin tashi lafiya?" "lafiya kalau, kaima ka tashi lafiya?" tai maganar tana kokarin kaucewa hada ido da shi "lafiya kalau na tashi lafiya, How was your night?" ya kuma jefo mata tambayar. Pillow ta dauka ta rufe fuska tana murmushi haka Jawwad ya cigaba tsokanarta yana bata kunya. Ya dakko cups yana kokarin hada musu tea tace "Haidar waye ya dafa tea din nan?" "ni na dafa" ya bata amsa "Allah yasa dai baka bari yayi kanzo ba, dan na san baka iya girki ba" Dariya ta bashi sosai "Ai nafi ki iya girki in gaya miki, zaki kuma gani" "to ai shikenan hada min yunwa nakeji" "Ai wannan tea din nawane ni kadai, bazaki sha ba ke kazarki zaki warming a oven ki cinye" Zare ido tayi tace "gaskiya bazan ciba na koshi" Jawwad yayi dariya yace "se kin cinye ta kuwa" "aikuwa bazan ci ba, tsaya in baka a baki" ta dinga bawa Jawwad Abinci a baka, yana bata haka sukayi breakfast cike da kulawa da kaunar juna. Wunin ranar yau Jalila ji tayi duniyar ta kara mata fadi, ga har yanzu Bata kuma sa Jalal a idonta ba balle ta sa ran karbar wayarta. Bangaren Jalila ma tunanin ta yaza'ayi tayi zaman Aure da Jalal be damu da kansa ba balle ita, tana ganin shima an cusa masa ita ne kawai baya sonta, banda haka kwanan su nawa da zuwa be nemeta ba ga rashin lafiya tanayi amma ko keyarsa bata gani ba balle tasa ran ze mata sannu. Ko parlour bata fita tana ďaki, Hajiya Salma da Antyn Jalal suna monitoring din Jalal da Jalila domin ganin actions dinsu, Amma abun mamaki kowannensu yana nuna be damu da ďan uwansa ba, tunda sukazo kwana uku ba wanda ya nemi wani a cikinsu. Antyn Jalal tana zaune suna hira a parlour su Husnah suna cin Abinci Jalal ya shigo, su Amal suka gaisheshi a ciki ya amsa, dan sun fidda ran ze amsa musu, suka cigaba da cin Abincin su. Anty tace "Jalal ina zuwa haka?" "Zan koma lagos ne" Anty sukayi ido hudu da Hajiya Salma. Hajiya Salma tace "to wannaan tafiya haka kaman wanda ake kora? Ka gayawa matarka yau zaka koma?" Cikin ko in kula yace "in kun ganta ku gaya mata" Anty tace "dan kaniyarka mu zamu gaya mata ka tafi, Anya Jalal ka shirya rike yarinyar nan?" A ransa yace "ita zaku tambaya in ta shirya zaman Aure dani?" Hajiya Salma tace "nima dai haka nagani, tunda muka taho bata da lafiya, Amma yaron na ko ta kanta bebi ba, balle in sa ran ya duba ta, ya mata sannu" da sauri yace "bata da lafiya kuma? Me yasa me ta?" Hajiya Salma tace "ban sani ba" mikewa yayi ya kalli Husna yace "ina ne dakinta"? "tana upstairs kusa da ďakina" ta bashi amsa, be kuma bi takansu Anty ba ya haura saman. Kai tsaye ya bude dakin ya shiga, ya sameta ta dukunkune a cikin bargo, a hankali ya karasa gaban gadon nata ya kai hannu ya janye bargon. Wata sleeping dress a jikinta blue me matukar kyau, kanta babu dan kwali, dukda tayi parking din gashin nata amma gashin ya hargitse, bacci takeyi sosai, Amma tayi rama a baccin ma se ajiyar zuciya take. Ya kura mata ido fatarta se sheki take, a hankali ta motsa ta mike hannyen ta wajen kirjinsa, hannayenta sun sha ado da jan lalle, hannunsa yasa a nataa ya rike yana kuma kallon fuskarta, bacci take amma tayi kyau sosai. Ya bata lokaci sosai yana kallon ta. A hankali ya saki hannunta Ya dakko wata 'yar takarda a Aljihinsa da biro yayi rubutu ya ajiye mata akar kashin pillow dinta, ya mayar mata da hannun ta kan gado ya lullube ta ya fice. Koda ya sakko bekuma ce musu uffan ba yayi waje abunsa. Anty tace "kinga danki ko?" Hajiya Salma tace "ai bari kawai, Jalal Akwai taurin kai, suna son juna amma taurin kai neke damun su, se nunawa suke kaman basu damu da juna ba, Allah shi yabarwa kansa sanin dalilin dayasa ya hadasu, Amma wannan zaman Auren nasu da kallo" "hakane amma zamu cigaba da yi musu Addu'a, zasu dai daita, bari kiga sukoma gidansu da zama, bazaki sake jin kansu ba" "hakane Allah ya tabattar da alkhairi, Amma bazata koma kano yanzu ba, sonake hankalin ta ya kwanta ta sake nustuwa, daga nan ma waccan jarababbiyar watakila ta sakko" Anty tace "tab haba sister Salma, kin manta wacece khadija kenan, ai babu batun ta sakko yanzu, kawai dai mu tayasu da Addu'a" haka suka cigaba da hirarakin su. Koda Jalila ta tashi ji tayi gaba daya dakin ya gauraye da kamshin Jalal, dan tabe baki tayi ta shiga toilet tayi wanka ta sa kaya, tazo tana kokarin gyara gadon tana cire bedsheet din taga takadda ta fado, ta dauka ta bude, wani tsararren handwriting tagani a jiki. Am going back to lagos, get well soon ABDUL JALAL se signing dinsa da date Juya takaddar tayi ta jefar da ita a gurin tayi tsaki, "kwana nawa bani da lafiya, tunda aka daura auren ko ta kaina bebi ba, se yanzu ze wani rubuta min wata banzar takadda, ya tafi abunda yafi lagos ma ni be shafe ni ba, kuma maimakon ya ajiyemin wayata amma yakuma tafiya da ita sekace tasa. Haka Jalila ta cigaba da mita, har ta gama gyaran gadon. Parlour ta fito dan ta gaji da zaman dakin ga shi ba waya a hannunta balle ta debe mata kewa. Anty na ganin Jalila tayi murmushi tace "Jalila kin fito? Ya jikin naki kuwa?" "naji sauki Anty" "to Allah yakara sauki, dazu Mijinki ya shiga dubaki ai" Dan tabe baki Jalila tayi tai shiru. Tundaga Ranar kullum cikin turara Jalila suke da samfurin turaruka daban2, a rana se ayiwa kayan sawa turare kusan sau hudu, banda wanda ake tuarar mata jikinta, hatta ruwan wankan Jalila akwai turaren da'ake zubawa, sabulun wankan ta ma na musamman ne aka hada mata, ga mayukan shafawa dana kai, nan da nan Jalila jikin Jalila yara canzawa, duk inda ta gifta kamshi take, duk rashin son kitson Jalila wani na tsufa me kitso take zuwa tayi mata wani, hakama lalle, gaba ďaya wannan gidan sun maida Amfani da turaruka kamar ibada, babu wani aiki da takeyi sedai taci ta kwanta, ko ta yunkura zatayi aiki se a hanata, ga kyan gyra da'ake bata dan haka har wani kiba tayi abunta tai kalau da ita. Jalila idan tana son yin waya sedai ta ari ta Anty tayi, ta mata magana akan wayarta tace tabari Jalal yazo. Tunda Jalal yazo ko a waya be kuma neman inda Jalila take ba itama ba ta nemi jin inda yake ba. Mummy ta cigaba da tayarwa da Daddy hankali akan maganar Auren Jalal, amma sam yaki saurararta, ya tattara ya koma Dubai, duk abun nan da ake Ilham bata sani ba. Daddare Ilham na kwance tana chatting, ta shiga Twitter kamar wadda aka saka ta shiga profile din Jalal Alhamdilillah got married to Jalila Aliyu Imam shine abunda Ilham ta gani zumbur ta tashi Zaune tana kuma mutsukke ido, Amma still taga ba mafarki take ba. Da sauri ta kira layin Nana, Amma bata shiga, se lokacin ta tuna ai Nana Mahmud ta aura, a England zasu zauna. Fitowa tayi da sauri ta tafi ďakin Mummy tana kwala mata kira "ke lafiya kuwa kike min wannan kiram, meya faru ne?" Nunawa Mummy wayar tayi, mummy tace "me zan gani?" "Mummy wai dagaske ne Jalal yayi Aure" Ajiyar zuciya Mummy tayi tace "tun satin da Daddy yaje daurin auren Jawwad, ya hada baki da 'yan uwansa suka masa Aure, nayi2 ya gayamin wacece yaki" Innalillahi wa inna ilaihi raji un, Mummy kin san wacece kuwa? Jalila ce fa, kalli Abunda ya rubuta ita ya aura Mummy, na shiga uku, Mummy ki kashe Auren nan kafin sun tare, Wallahi idan suka tare na kade, zan rasa komai, komai nawa ya rushe" Gaba ďaya Mummy tsayawa tayi tana kallon Ilham "dolene in kashe Auren nan, baze yuwu ba, wallahi ko yana so koba ya so sena kashe auren nan, ni Hajiya zainab zata munafunta, a hada kai da ita a Aurawa ďana wannan makirar yarinyar, in abun gaskiyane ta aurawa nata ďan mana, indai nina haifi Jalal seya saketa, a ďaura masa Aure ko ya nemi inda nake, rabona da shi wata biyar kenan, baze yuwu ba wallahi" Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE 5️⃣1️⃣ 104 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Tunda aka gama biki Maama bata dawo ba, seda takuma kwana goma a Bauchi, taji dadin zaman garin sosai, gashi mutane ne masu karamci da son 'yan uwa, Abba ne yazo ya dauketa suka koma gida kanon dabo. Bangaren Angwaye da Amare da sukayi Auren soyayya Se shan soyayya da kauna suke, tsakanin su banda Jalila da Jalal da babu wanda yake neman wani  a tsakanin su, Jalila ita wannan zaman hutun ya isheta, ita dama kano suka batta tayi zamanta a gurin Maama ya fiye mata wanna zaman. Tana ta zancen zuci ne Husna 'yar gidan Anty ta shigo da waya ta mikowa Jalila, Jalila tasa hannu ta karba, video Call ne ta ďaga wayar tana ďagawa taga fuskar Jawwad cikin sauri ta mike zaune "Yaya Jawwad kaine?" "Nine Baby, yaya borno yasu Anty?" "lafiya kalau Yaya Jawwad, kayi kiba sosai kaman ba kaiba, ina Hanan?" "tana kitchen tana girki, kema gaki nan kinyi kibar ai, ya mijin naki?" Tabe baki Jalila tayi tace "yana can lagos" Hanan ce ta taho da gudu ta haye kan cinyar Jawwad tace "Hi queen, ya kike?" "Wow Hanan, wannan kwalliya haka, masha Allah, naji dadin ganinku wallahi nayi farinciki, Allah ya albarkaci rayuwar aurenku, yara muku kaunar juna" Tausayinta yakama su Jawwad, Hanan tace "Jalila kunyi waya da Nana kuwa?" "Eh munyi waya da su, ya Abuja ya zaman kadaici?" Jawwad yace "muba ma zaman kadaici ko My sugar, masu zaman kadaici suna Azabtar da zukatansu sun san kansu" yai maganar yana kallon Hanan, Hanan tace "Sosai makuwa, ba wani kadaici, kullum muna tare, kema kice akaiki gidan mijinki kigani in zakiji wani kadaici" "Allah ya kiyaye" Jalila ta fada tana harar Hanan. Wayar Jawwad ta fara ringing, Jalal ne yake kiransa, Jawwad yace "Baby mijinki ke kirana, bari inje in amsa" Hanan ta zauna akan kujera tace "Jalila wai yaushe zaku sauke wannan taurin kan ke dashi ku fuskanci juna?" "Hanan ya kikeso inyi ne? Nagaya muku Jalal ba sona yake ba, kawai an lika masa ni ne, tun lokacin biki nake rashin lafiya be nemeni ba, ko ta kaina bayabi, se ranar da ze tafiya ya ajiyemin takadda, sam be damu dani ba, Hanan ku kukayi dacen Auren soyayya amma bani ba, nasan da Ahmad na Aura baze watsi da lamarina ba" kan Jalila ta gama maganar har hawaye ya wanke mata fuska. Cikin taushin murya Hanan tace "Jalila, kina da Aure yanzu be kamata kidinga ambaton wani namijin ba, Sannan Jalila kinsan halin mijinki tun kafin kuyi Aure, bashida shiga sabagar mutane, dukda ke matarsa ce yanzu, Amma kiyi hakuri, komai ze wuce Jalila, kalli yadda kikayi kyau kamar a saceki a gudu, i wish yana nan yaga wannan kwalliyar taki se ya rude, waima me suke bakine kikayi wannan kyan" Murmushin takaici Jalila tayi tace "Hanan kenan, kina tunanin zanyi wani abu daze gani ya yabane? Ko ya burgeshi, shi ba sona yake ba kawai an aura masa ni, be damu da yasan a halin da nake ba balle ya yaba kwalliya ta, se an jima ki gaida Yaya Jawwad. Jalila ta ajiye wayar ta dora sabon kuka me sauti. ji tayi an dafata, ta dago ta kalli wanda ya dafata Husna ce fuskarta dauke da damuwa tace "Sorry dear, please stop crying, kidena kuka ko tunanin broz Jalal baya sonki, is not like that, ina kula da yadda kuke share juna kedashi, which is total bad, an riga an daura Aurenku, kamata yayi ku manta da abunda ya wuce, Jalal has a social disabilities at times, tun lokacin da yakoma drunker, mutane suke kyamarsa he decided to isolate himself from the people, he dint interact with people as before, believe me he loves you bazaki gane hakan ba sekin zauna da shi, yanada kirki sosai, ki dena yawan kukan nan please " Jinjina mata kai Jalila tayi Husna tace " Yawwa mrs Jalal, Jalal bashi da matsala bayan ta shaye2, zaki maida shi yadda kikeso, yana sonki ne shiyasa yakeyin abunda kike so, ba dan haka ba a duniya akwai abunda ba wanda ya isa Jalal yayi wani abun yayi. Husnah ta cigaba da rarrashin Jalila, a lokacin take gayawa Jalila Tanada Aure, mijinta baya gari ne, shiyasa itama tazo tayi zamanta a gida. Ilham takasa zaune takasa tsaye, kwanata kusan shida a gidansu suna sakawa da warwara akan yadda zasu bullowa lamarin ita da umanta, yanzunma zancen da suke kenan "Umma kin san kashinmu ya bushe idan yarinyar nan ta tare da Jalal, aikin ze lalace ne fa, zamu rasa komai, jiran da mukayi tsawon shekaru mu dauki fansa ze tashi a banza ne, indai yana tareda yarinyar nanmun rasa komai, daular da muke hange bazamu sameta ba" Umman Ilham taja numfashi ta hura hanci tace "Bazan taba yadda tsawon wannan lokacin daukar fansa ta ya tsaya akan lalacewar Jalal ba, dole in wulakanta khadija in mallake dukiyar da take takama da ita, sena ga ta wulakanta daga ita har Habib din" Ilham tace "Umma to tayaya?" "ki kylaeni kawai, nasan abunda zanyi, tunda ke kinkasa abunda ya kaiki gidan tsawon lokaci" "Umma kenan, ba kasawa nayi ba, nayi iya yina, ba daban wannan Jalilan ba da tuni an wuce gurin, Amma ni hankalina a tashe yake umma, kin san abunda Aure ga Jalal yake nufi fa a shirin mu, so soyayya da wata mace bayanni ga Jalal kim san barazana ce a garemu, wallahi ko bacci bana iyayi" "ni nace ki bar komai a hannuna, nasan me zanyi" "Shikenan Umma" Mummy har gidansu Jawwad taje da kanta, ta tarar da Maama tana ta fama da aikin gida. Cikin fara'a Maama ta tareta tana mata sannu da zuwa Aikuwa a fusace mummy tace "kinga niba yashe bakinki nazo gani ba, ba hakoranki nazo ki nunamin ba, baban su Jawwad na nan ne? " A'a baya nan lafiya kuwa? " " ina fa lafiya, saboda tsabar munafunci a haďa kai da ke a cuceni, a Aurawa Jalal wannan yarinyar dake kanki kinsam bata da cikakken Asali, meyasa baki yadda an An aurawa ďanki ba se nawa ďan, wannan yarinyar mara mutunci akan me?  Sumi2 da ita kamar ta Allah amma tana bin ďana" Maama tace "Subhanallah  ni kaina ban san da batun ďaurin aurensu ba se ana i gobe ďaurin Aure, kuma iyayensu mazane suka yanke wannan hukuncin baniba, da amincewar mahaifinsa aka aura masa ita" "ke kikasani koma suwaye suka amince, saboda tayi kwantai tarasa miji se abawa ďana, Allah kadai yasan abunda aka dukunkune aka bashi" "Mummy Jalila ba kwantai tayi ba, tanada masoya, Allah ne yayi matarsa, Sannan be kamata kidinga wannan maganganun ba karkizo kiji kunya wataran kamar yadda naji kunya nima, Ni data zauna taredani tayi zaman hakuri dani na tabattar Alkhairi ce ga rayuwar Jalal, a irin zamanbda tayi a hannuna nasan halinta" "kinga dan Allah ki sauraramin bana bukatar jin wa'azinki, tunda baya nan, ki gaya masa ya shirya karbar karamar bazawara, dan sena kashe Auren nan, ban ga dacewar Jalal da wannan yarinyar ba" Maama tace "Shikenan duk yadda kika gani, komai ya samu bawa mukaddarine, dadinta ma ďan naki ba wani kintsatse bane balle aji haushi dan an rabu da shi, naga ke kanki baki isa da shi ba, temaka masa akayi aka bashi yarinyar nan, kuma duniya da gaskiya baki isa ki biya Jalila da mahifiyarta abunda tayiwa ďanki ba" Maama takarasa maganar tareda shigewa ta bar Mummy a gurin. Mummy ta dawo gida tana cizon ya tsa, tana tunani iri2 a ranta. Jalila hankalin ta ya ďan kwanta, Husna na debe mata kewa suna hira lokaci zuwa lokaci, sannan duk lokacin da ta keso zata ari waya takira wanda takeso, Mijin Antyn Jalal professor Aliyu Ishaq  yana koyar da darasin turanci a saudiyya, be fiye zama ba, yana da tarin Ilimi, gashi mutumin kirki ne, yana da barkwanci da raha, Girmama shin da Jalila da take da yadda yaga tana gudanar da Al'amuranta yasa take burgeshi, yayiwa Jalal murnanr samun yarinya me kwazo da tarbiyya kamar Jalila. Be kara sarewa da lamarin Jalila ba seda Antyn ta bashi labarin irin Abubuwan da Jalila ta dingayi da kokarinta akan rayuwar Jalal, ya zamana Jalila tana sakewa da shi fiye da kowa a gidan, kamar yadda Ake kiransa Abee haka take kiransa, Jalila tana son mu'amala da mutane masu ilimi dazata Amfana dasu, indai Abee ze fito parlour Jalila zata zauna Suyita hira tana masa tambayoyi akan abubuwa da dama, shikansa duk lokacin da be ganta ba ya dinga tambaya tana ina kenan, yana mamakin kaifin hankalin ta da basirarta, gata da ilimin Addini " Yauma na gama dinner, Amma Jalila tanata hira da Abee tana bashi labarin irin fituntunun data dingayi lokacin kuruciya suna ta mata dariya, Hajiya Salma tace "Nikam Alhaji Aliyu me kayiwa Jalila haka take sakewa da kai hada hira, mu kaman tsoronmu ma takeji" Jalila tayi murmushi tace "Bahaka bane ba, Jalila Aliyu Imam, shine cikakken sunana, kuma Kafin Babana ya rasu Abee nake ce masa" Anty tace "Haba shiyasa wannan shakuwa haka, Ashe ya da uba ne" Abee yace "Eh ya ranku, yata kuma sirikata kuma malamata" Zare ido Jalila tayi tace "Wace ni, se dai in durkusa a koyamin, Seda safenku" Jalila ta fada tana mikewa tsaye, sukayi Sallama ta tafi dakinta. Bayan tafiyarta Abee yace "Kuna ganin raba yaran nan yanada wata fa'ida ne? Yana can matar tana nan" Anty tace "Eh mana, muna so mugane dagaske yana sonta ne kokuwa?" Abee yayi murmushi yace "Lallai kun manta waye ďan naku ne, shikenan Allah ya tabattar da alkhairi, Amma nayiwa Jalal murna samun yarinyar kirki kamar ta, tanada hankali sosai" Haka dai suka cigaba da tattaunawa. Jalalila kamar kullum ta gama wannan wankan turaren, ta shirya a cikin wata doguwar riga, dayake Anty sunyiwa Jalila sayayyar kayan sawa dana kwalliya tana kan wani karamin kujera tana gyara gashin ta. Husnah ce ta shigo dakin tana murmushi tace "Maigidanki yana hanya, broz Jalal zezo ba sanarwa ba komai, kuma nasan badan ke ba bazamu ganshi ba, tashi muje ayi masa girki, Anyiwa me kitso waya tana hanya, ki taso muje" Hade rai Jalila tayi tace "ba wani girki da zanyi, kuma ni ku kyalemin kaina a haka" Husnah tace "Haba Sister meyasa haka ne?" (nikam nace baki san halin Jalila da taurin kai ba) Jalila tace "wai meye Amfanin inta bawa kaina wahala akan wanda be damu dani ba? Watana daya da kwana Goma a gidan nan ko ta waya baya kira balle yaji ya nake, seni zan ta faman wahala akansa" Ajiyar Zuciya Husnah tayi tace "Kina da gaskiya Jalila Amma hakurin dazakiyi yanzu baze kai na baya ba, ki bari ki kama shi a hannu, daga nan seki rama, taso muje su Mummy suna parlour" Jalila bata da zabi sena ta mike tabi bayan Husnah, suna zuwa parlour Hajiya Salma tace "Yawwa Jalila, Jalal yayi waya yakusa isowa maiduguri, me kitso tana hanya, dama lallanki jiya akayi shi, in an gama kitson kafin ya karaso ayi masa girkin. Jalila ta samu guri ta zauna ba tareda tace komai ba, Husnah ta zauna a kusa da ita tana mata magana kasa2 "please sister idan yazo karki hade masa rai haka, karki biye masa dan Allah, ki bawa mara ďa kunya" Ita dai Jalila jinsu kawai take. Tunda Daddy ya tafi be kara dawowa Nigeria ba, Mummy tarasa me yake mata daďi, in dai Jalal ya zauna da yarinyar nan to zata kwace mata shine gaba daya, dan tun kafin ya aureta ma yana sonta tunda yanajin maganar ta, tarasa ta inda zata bullowa lamarin, gashi a yanzu tasan bata isa taje maiduguri tayi musu tijara ba. Kafin Jalal ya karaso har angama yiwa Jalila kitso, kitso akayi mata kanana sosai, gashi hannunta ya sha lalle, duk inda ta gifta kamshi take, ga fatarta ta kara kyau se sheki take. Anty tace " Jalila me yakamata ki girkawa Jalal ne? Mara nauyi sosai tunda naga alamar shigowar dare zeyi" Dan zumbura baki Jalila tayi tace "befiye cin Abinci da daddare ba yafi shan tea ko fruit, wani lokacin koya ci Abinci seya sha tea da daddare" ta fada tana dan tura baki cikin ko in kula Boye dairiyar su sukayi, banda Husna da seda ta dara, tace "Ya akayi kika san haka?" "Nike musu girki shida Yaya Jawwad a gida" tabata amsa Anty tace "Ke Husnah ina ruwanki ne? Jalila ki dafa masa abunda kika ga ya dace kawai" Jinjina kai tayi ta tafi ďakinta. . Seda ta tafi sukayi dariya, Hajiya Salma tace "Kai lamarin yaran nan sesu, ni ban san wanda yafi wani taurin kai a cikin su ba, ana so ana kaiwa kasuwa" Anty tace "Jalal yafita taurin kai, bafa yanzu yafara sonta ba shi, Jalal ya dade yana sonta, nasan komai, Dan yaga ya samu yanzu shine yake basarwa kaman be damu da ita ba" Hajiya Salma tace "Aike ta hannun damansa ce kinsan komai akansa, Allah ya daidaita tsakani" Suka Amsa da Ameen Lokacin sallar magariba Jalal ya iso gidan, ya sha tafiya dan a mota yazo ya gaji sosai, Jalila bata san ya karaso ba, har bayan sallar isha'i tana palourn Abee yana mata bayani akan wani littafi da yake son wallafawa, Husnah tana gefe tana dan tsoma musu baki lokaci zuwa lokaci, zaman da Jalila  tayi da su tafara gane yarensu kadan2, kaman gaisuwa da yaren. Suna hira kai kace 'ya da ubane, Anty ta shigo palourn tace "Jalila kina nan, tun dazu Jalal ya iso fa, nazata kina can kina shiryawa ne, kije ki shirya ki kaimasa Abincin" Jalila ta dan langabe kai tana kallon Anty. A ranta tace "Sekace wani mijin kirki ko wadda zata biki anata in shirya, bayan nasan ko kallo ban isheshi ba" Abee ya kalli Anty yace "Madam jeki zamuyi magana da' yar auta ta" "to shikenan nidai ayi Sauri, in ba sokuke yayi zuciya ba ya tafi" ta fada tana shirin barin palourn tareda yin murmushi, Ameera tana zaune bata fita ba. Abee yace "Jalila tambayar ki zanyi, ki gayamin tsakani da Allah, in dai kin baban dani ki gayamin kina kuwa son Jalal?" Taji ya mata tambayar ba tareda ta shirya jin hakan ba. Hade fuska ta danyi tace "Ni dai ban sani ba ko ina sonshi, shima fa baya sona" ta karasa maganar kaman tana shagwaba Fuskarta ya kalla, Akwai alamar kuruciya sosai a tareda ita, yarinya ce me tunani irin na manya, Amm lokuta da dama kuruciya tana dawainiya da ita. Yace "Shikenan daughter Allah ya daidaita ku, ki cigaba da hakuri zaki fara sonsa, Mijin kine yanzu, ki manta da halinsa kinemi Aljannar ki, kuma insha Allah komai ze wuce" Jalila tace "to Abee nagode" harzata fita Husnah tace "Jirani muje in miki kwalliya, nasan idan na kyaleki ba zakiyi ba" Ta tasa Jalila a gaba zuwa ďaki, ta ďakko mata wani material baki da adon jan flowers, riga da skirt ta mikawa Jalila ta karba tana zumbura baki ta saka, tayi kyau sosai, Husnah ta bata turaruka ta shafa, kamshi dai kam ya riga yagama kama jikin Jalila a gidan nan, Husnah tace "bari in miki kwalliya" "ni ba wata kwalliya daza'a yimin" "Jalila ya hakane? To sa kwalli da jan baki mana" Jalila ta saka kwalli se jan baki Ja, tasaka kwalli, tayi kyau sosai, Husnah ta bata karamin gyale Ja akanta, Jalila ta kalli kanta a mudubi, kayan nan sun kamata sosai ta kalli Husnah tace "Nikam gyalen nan yayi min karami gaskiya, ki bari in saka babba" "Haba Jalila, gurin mijinki zaki fa, Mijinki ne ba wani ba, in kuma kinki in barki da su Mummy" Husnah tasata gaba zuwa Kitchen ta shirya mata kayan Abincin a tray ta rakata har kofar palourn da Jalal yake tace "please Jalila don't mess up, karki bani kunya dan Allah" Jalila ba tace komai ba ta shiga gabanta se faduwa yake yi, Sallama tayi sannan ta shiga, bata tabaccin ya amsa sallamar nan tata. da farko dakin kamshin turarensa yakeyi, Jalila na shigowa kuwa temperature dakin ta canza zuwa kamshin turaren jikinta, kallo daya tayi masa ta dauke kanta, kanan kayane a jikinsa amma yayi kyau sosai sumarsa se kyalli take, duk ya dena saka wannan kalar dayake wa gashinsa, ya dora kafarsa akan center table, ko a ina zata ajiye tray din oho, ta gefen ido ya dan saci kallonta, tana zuwa bata kula shi ba ta ajiye tray din a kasa, ta juya zataje ta zauna hakan ya bashi damar kare mata kallo, tubarkallah she has a very beautiful heart and body structure, Jalila tana da kyau ga kyakywan surar jiki, ga zuciyarta me matukar tausayi, matsalarta taurin kai da Izza wani lokacin. Taje ta nemi guri ta zauna a kujerar da take kallonsa ta dora kafa daya kan daya tana kada kafa tareda dauke kanta gefe tana wasa da yatsun hannunta. Jalal a ransa yace 'Tsabar wulakanci ko ta gaisheni kota ce min ya hanya ba ruwan ta dani, hakan na nufin dagaske bata sona ne? Ko kuma tsabar rigima da taurin kaine? " Jalal ya gaza gano amsoshin tambayoyin sa, to bata kulashi da sannu da zuwa ba ma balle yasa ran zata zuba masa Abincin. Kallon ta ya kumayi, kayanta cif jikinta ga mayafin iyakarsa wuyanta, hanun nan yayi kyau da lalle, kanta ba dan kwali dan haka yana iya ganin tsagar kanan kitso dake kanta. Itama Jalila a ranta mita take "tsabar wulakanci koma ya tambayeni ya nake, bayan tafiyar sa ya na karke, ya tafi ya barni ba lafiya koya bugo waya yaji ya jikina, ya sani a gaba da kallo yaki cin Abincin in baze ci ba ni in tafi, mtseww ta danyi tsaki, tsakin ya fito fili ba tareda sanin ta ba. Saurin dagowa yayi suka haďa ido ta basar. Mikewa yayi ba tareda ya kalli inda Abincin yake ba ya mike ze fice, itama ta mike da sauri tasha gabansa suka tsaya suna kallon Juna, lokaci na farko da suka kasance tare tun bayan daura Auren su "lafiya meye haka?" ya tambayeta "ya zan kawo Abinci ka tashi baka ciba? Salon in koma ayita tuhuma ta" "in sun tuhumeki kice su koya miki yadda ake kula da miji, dan baki iya ba" Ta dan yatsina fuska ta kalleshi "Waye mijin? Aini banga miji anan ba, kaima yakamata a koya maka yadda ake kula da mace dan..... Se kuma tayi shiru ganin yadda ya kura mata ido, Ashe fa yanzu mijinta ne, ba kowace magana yakamata ta gaya masa ba "Ni kike cewa bakiga Miji anan ba ko?, Nagode sosai, matsa kibani guri in wuce" Hanya ta bashi ya fice daga dakin, bata bi ta kan kayan ba itama tayi waje abunta. Washegari ma da Safe Aka sa Jalila ta kai masa Abinci, haushin taki kulashi jiya yasa beci Abincin ba yakuma barinsa. Yana fita ya tafi gurin Abee, bayan sun gaisa Abee yanata tsokanarsa, Jalal yace "Abee so nake kasa baki su kaimin matata, ko in dauketa mu tafi basu sani ba" Abee yace "A'a baza'ayi haka ba ai, kwantar da hankalinka, ko gobe kake so za'a kaimaka ita zan saka baki suba ka ita, na goyi bayanka tunda Daddynka yana jin nauyinsu, ina dalili kanada Aure amma sun barka kana ta fama sun rike maka mata" haka Abee ya lallaba Jalal ya tafi. Yaje yasamu Anty yace mata "kinga tun wuri kubawa yaron nan matarsa yana son abarsa, yamuku kawaici amma kunki ganewa" Anty tace "Abee Akwai dalilin da yasa muka riketa anan ne" "A'a Ku bashi matarsa kawai, in baso kike kiga tafara miki laulayi a gidan nan ba, sannan ku kwasheta ku kaita" Zare ido Anty tayi "Haba dai" "Eh mana, yanzu da muka rabu da shi yake gayamin insa baki ku bashi matarsa" Aimin hakuri fa rashin posting akan lokaci, abubuwa sunyimin yawa, adinga min uzuri nagode da kulawarku Vote and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724                              🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹                   *ABDUL JALAL*              _Story, writing and edited _                                                          By                   AISHA HUMAIRA                   ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️             PART 2                                   _PAGE 5️⃣2️⃣ 105 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                    _MY FIRST NOVEL _ Zare ido Anty tayi tace "gaskiyane Abee, tunda ya iya budar baki yace a bashi matarsa he mean it, zanyiwa Anty Salma magana gaskiya, a bashi iga suje can su karata, tunda be san abun Arziki ba" Abee yace "gara dai kuyi tunani, wannan ba mafita bace ku bashi matarsa kawai" Tunda Abee ya bashi goyon baya A ranar Jalal ya shirya ya tafi kano ko sallama basuyi da Jalila ba, dan in dai suka hadu fada zasuyi. Yayi waya da Daddy ya gaya masa yana son zeyi magana dashi, Daddy yayi masa Alkawarin zezo Nigeria su hadu a kano. Ba zato ba tsammani Ilham ta dawo taga motar Jalal a harabar gidan, ai a guje takarasa cikin gidan ta nufi dakin  Mummy tana kwala mata kira, "Mummy Kinsan Jalal ya dawo kuwa?" Mikewa Mummy tayi "dagaske ko wasa"? "Wallahi dagaske nake, ga motarsa can" Jinjina kai Mummy tayi tace "Shikenan rabu dashi, nasan tunda yazo Akwai abunda ya kawo shi, kyleni da shi kawai" Ilham ta koma dakinta tana cigaba da tunanin wani mataki Ummanta ke shirin dauka akan wannan lamarin, Itakuma me yakamata tayi? Wasa2 kwanan Jalal uku da dawowa amma sam Mummy bata sa Jalal a idonta ba, da kanta taje dakin Jalal amma baya nan. Ilham ma duk yadda taso taga Jalal bata ganshi ba, ko ina yake tafiya oho?. Bangaren Jalila kuwa sekuma shan gyara takeyi, basu gaya mata Jalal yace zasu koma kano ba. Kwanan Jalal hudu a kano sannan Daddy ya dawo, koda ya dawo babu wata tarbar Arziki daya samu daga Mummy se mita da masifa, Bebi takanta ba ya cigaba da sha'anin sa, babban abunda yake kular da ita kenan, tasa shi agaba taita masifa Amma ya kyaleta yaki kulata. Ranar da Daddy ya dawo da daddare Jalal ya shigo, ba kowa a palourn dan haka ya wuce part din Daddy, shikansa Daddy yaji dadin ganin Jalal, Daddy yace "Ango, Ango se wani kyau ka keyi, alamu hankalin ka a kwance" Jalal ya dan bata fuska yace "Ina wani hankalina a kwance yake, Kawai su Anty sunje sun rike ta a can gurinsu ko mene amfanin hakan oho?" Daddy yai murmushi yace "Tunda sukayi haka Akwai dalili" Jalal ya dan hade fuska yace "koma meye dalilin nasu ni munyi magana da Abee zan dakkota tazo ta tare" "Jalal meyasa kai haka? Zasu ga kaman bakayi musu kara ba" "Daddy sati guda da komawa makaranta yakamata ace ta koma itama, sannan kasan in dai da Auren nan idan nazo kano bani da masauki, bani kwanciyar hankali saboda masifar Mummy indai nazo gidan nan, nasan bata son Auren nan, nikuma inason abuna, kaga ko nazo Kano a gidana zan sauka baseta ganni ba bazan zo mata gida ba" Murmushi Daddy yayi yace "koma dai meye she's your Mum, yakamata ka dinga mata uzuri sannan ka dinga hakuri da ita" Jalal yace "Daddy maganar gidan da zan zauna ne yasa nazo Kano fa" "to wane gidan zaka zauna, gadon kayan zaka koma kokuma yaya?" "No bazan koma gadon kaya ba, zamana a gidan nan zena tunamin abubuwan da suka wuce masu batamin rai" "to ya kake so ayi?" daddy ya tambayar yana bawa Jalal attention dinsa "gida zan siya a tarauni, a can zan zauna in danyi nesa daku, bana son yawan fitina ko hayaniya, Gobe in Allah ya kaimu se muje ka tayani zaban gidan" "hmm Jalal kenan, to ai tunda bani zan zauna ba, kai da ita matar taka yakamata ku zabi gidan da kuke so" "Kyaleta kawai duk gidan dana zaba baza tace beyi ba" "to shikenan ina fatan kun daidai ta kanku babu matsala" "karka damu Daddy, in Allah ya kaimu gobe muje a siyi gidan, ka gayawa Abba, next week Insha Allah in basu kawo ta ba, zanje in dakko ta" Daddy kallon Jalal kawai yake, jalal din maganar sa yake kansa tsaye kuma hankali kwance ba wata kunya ko makamancin haka a tare da shi. Suna ta hirarsu ba zato ba tsammani sega Mummy ta shigo ďakin, seda ta danyi turus ta tsaya, ganin Jalal da tayi kanan kayane a jikin Jalal kaman yadda yasaba sakawa, Amma abun mamaki dogon wandone har kasa a jikinsa, da riga me dogon hannu, wuyansa babu sarka, sannan babu wannan askin banzan da yakeyi kuma ya sawa kan color duk babu, yayi kiba abunsa kuma fuskarsa ba laifi a sake yana murmushi, sabanin da da kullum fusakarsa a murtuke. Idan lissafinta dai2 ne kimanin watanni shida bata ganshi ba ko a waya baya kiranta, dama ina ta kai matsayin da Jalal ze aje lambarta balle ya kirata. Jalal yace "Daddy in aka siyi gidan se a sai furnitures ma in saka, kayan kitchen ban san kansu ba maybe su Anty sa saimata, kokuma muje da ita ta siya" Wannan statement din data ji yafi kowanne bata mata rai, su Jalal basu san ta shigo ba, dan sun bawa kofar baya, nan Take ta shakunu ta karasa shigowa dakin fuskarta babu walwala ta zo ta tsaya. Jalal na ganinta ya maze ya jingina da jikin kujera ya dora kafa daya kan daya Ta kalli Jalal tace "Sannu mara mutunci wanda be san ciwon kansa ba, Jalal saboda ba ka maidani komai ba tsawon watanni shida ban saka a idona ba, kuma saboda kai ba dan mutunci bane har a hada kai ai maka Aire ba tareda izinina ba, saboda munafunci baka tuntubeni ba tunda akayi Auren nan ka hada kai da dangin ubanka kayi tafiyarka inda ta zaba maka, se yau ka dawo kana zaka saimata gida da furnitures, kudin na ubanta ne? Ko shi ya tara maka? Wallahi Jalal se an kashe Auren nan, ban yadda ka zauna da yarinyar nan ba, seka saketa kuma seka baro wannan tsinan nan aikin data samo maka a lagosa, tunda ba ita ta haifamin kai ba" cikin masifa Mummy take wannan hakilon Masifar, har Daddy ya fusata zeyi magana Jalal yace "No Daddy yi hakuri, ban sanka da fada ba, kayi shiru kawai, bari zanje in dawo" Jalal ya mike ze fita, Mummy ta kuma fusata tace "Nizaka mayar 'yar Iska ina maka magana, Wallahi Jalal in baka saki yarinyar nan ba sena maka baki" cak Jalal ya tsaya ya waigo yana kallonta. Daddy dafe kai yayi, dan shi a rayuwarsa sam baya son tashin hankali. Jalal yazo gaban Mummy ya kalleta yace "Mummy idan kikamin baki akan na wasu zaki ďora, inkin min baki baze dameni ba, tunda wanda yake dawainiya dani be ishekiba, baki da wata cikakkiyar hujja na kin Aure na, bazan saki Jalila ba saboda ina sonta, kema soyayya ce tasaki zama da mahaifina, nima na Auri wadda na rayu da sonta, baze yuwu amin Auren dole ba, tunda kema bashi aka miki ba" "Jalal ni kake gayawa haka?" Kai tsaye yace "Yau na fara gaya miki gaskiya? Bazan Auri macen da bana so ba saboda san zuciyarki, da in saki mata ta gara kimin bakin, dama can a lalace nake, in kika min baki kinga dorawa zanyi" Yana gama maganar ya fice. "Innalillahi wa inna ilaihi raji un, nashiga uku, dan dana haifa ya tsaya a gabana yana gaya min wannan maganganun, Habib Jalal ua zabi mace akaina da na haifeshi, ban taba zaton haka ba, tunanina Jalal shaye2 kawai yake, yaushe Jalal ya fara son Jalila da har yake gayamin wannan maganar akanta, tun yanzu, wallahi na tsani yarinyar nan" Daddy yace "Khadija be kamata kiyi wannan maganar ba, bari in tuna miki wani abu, Soyayyar da nake miki tasa na zauna dake tsawon shekaru, na fifita ki fiye da Ahalina, kika rabani da kowa nawa, Ashe ba dadi, na fuskanci Soyayya bazata yiwa Jalal da wasa ba, dan haka ki shirya sa hannu ki karbi irin abunda kika aikata kema" Mummy cigaba da rusa kuka tayi tama fadin "Wallahi baze yuwu ba, ni na haifi dana ba'a isa amin iko da shiba, babu wadda ta isa ta juyamin yaro, nasan wannan makircin Salma ne, zata ďau fansa a kan ďana, tana tunanin zata mallake min ďa saboda wannan banzan shirin nata? Wallahi bata isa ba" tuni Idon Mummy yayi jawur tana kuka tana masifa, Daddy ba shi da zabin da ya wuce yabar mata ďakin, dukda yadda yakejin kukan nata a zuciyarsa, Amma wannan faďan rashin gaskiyane kawai take yi. Ilham kuwa tana kitchen tana hada abunda zata ci, sama bata san Jalal ya shigo part din ba, tana daga kai ta window taga shigar Jalal part dinsa, gabanta ne ya fadi, ya wani kara kiba, wani tunani ne yazo mata, hakan yasa ta fito da sauri ta tafi part din nasa, tana zuwa ta tarar baya palourn dan haka kai tsaye itama ta bishi bedroom din nasa, Amma tana zuwa ta tarar har ya shiga toilet, gefen gadonsa ta samu ta zauna ba tare da fargabar komai ba, tayi a kalla mintuna Ashirin sannan ya fito sanye da gajeren wando jikinsa babu riga se karamin towel yana goge ruwan jikinsa, Sam Jalal be kula da Ilham ba, yayinda Ilham ta daskare a zaune tana karewa surar Jikin Jalal kallo, Gaskiya Jalal ya kai a so shi koba dan dukiyar sa ba, ko ina na jikinsa kwance yake da gashi tun daga kansa har kafafunsa, dogone jikin sa a murde yake, dama ga jikinsa yana cin karfe, kallo daya zaka masa kasan namiji ne me matukar kwarjini, yana ďaga kai yayi ido hudu da Ilham zaune akan gadonsa, a fusace yace "Ke meye haka? Uban me yakawo ki dakina a daren nan? Ta shi kifita ki barmin daki" Mikewa Ilham tayi ta tako gaban sa ta tsaya tana kuma kare masa kallo, "Jalal dagaske kayi Aure ko?" "Tambayata ma kike? Ban sani ba, fita ki barmin daki" Towel din hannunsa ta karba, ta ajiye ta zuba masa ido, Hawaye ne ya fara bin idonta "Jalal namaka son da ban taba yiwa wani namiji makamancin sa ba, Jalal why? Ina sonka Jalal, meyasa zaka Auri wata bani ba, Wallahi ina sonka, Jalal ka shmmace ni, ka Auri yarinyar da nafi tsana a rayuwata, Haba Jalal meyasa kamin hakan?" "kina son Jalal ko kina son cutar da shi? Kina sona nikuma na rayu da son yarinyar da kika fi tsana, saboda a duniya a yanzu babu wanda ya gwada min so kamar yadda tayi, I love Jalila with all my heart, ba abunda bazan sadaukar akanta ba, i am sorry, kema Allah yabaki me sonki" Wani kululun takaici ne ya tokare kirjin Ilham, Amma ta maze, hannu ta mika kirjin Jalal zata shafa kirjinsa amma ya rike hannunta, ya girgiza mata kai, Ya dan lumshe ido ya bude yace "Abunda yasa nake kara Son Jalila kenan, ba ruwanta da abunda ba nata ba, karki tsallake iyakar ki, karki taba mata miji kin san halin ta dai base na gaya miki ba, Abunda kike hari tsawon lokaci ya zama nata, a gaskiya ta miki ba dadi, ta rusa shirinki gaba ďay" ya karasa maganar yana ďanyin murmushin mugunta, sekuma ya haďe rai yace "malama get out from my room" Ilham tace "Amma Jalal" "ki fitar min daga ďaki malama, ko ba kya banbance abunda ya dace da wanda be dace ba? Kifita bana son ganinki" Jalal ya katseta "Yaya Jalal..." "kifita nace ko in miki Illa, natsaneki bama son ganinki, ki fita ki bar min daki ko in kakkarya ki" Yadda yakoma yana maganar a fusace ya sa Ilham ta fita da sauri ta bar dakin. Wani dogon tsaki Jalal ya ja ya saka doguwar Jallabiya ya kwanta. Ilham kwana tayi tana juyi ta kasa bacci, Jalal da ba ruwansa da mata yaushe ya fara Soyayya? Har yake gaya mata yana son Jalila fiye da komai, yadda taga rana haka taga dare zuciyarta kamar zata fito,tana karajin tsanar Jalila a ranta. Kamar yadda suka tsara, Jalal da Daddy sukaje suka sai gida a tarauni, gidan yayi matukar kyau da tsaruwa, yanada girma sosai gidan, palour biyu, bedroom uku kowanne da toilet se kitchen biyi da store da katuwar harabar gida. Daddy ya samu Abba akan, an sai gidan dasu Jalal zasu zauna, Jalal ze sai furnitures, Abba yace be yadda ba shi zewa Jalila kayan daki, Jalal ba dan yaso ba ya hakura, Abba da Maama sukaje suka ga gidan sun yaba gidan sosai, Abba seda ya cikawa Jalila ko ina da kaya, gidan ta yayi kyau ya tsaru matuka. Sam Jalila bata san abunda ake ba, ita dai taga su Hajiya Salma sunata kara shiryata, Hajiya Salma taje ta samu Jalila a daki tace "Jalila ki ware gashinki, me kitso zatazo ayi miki kunshi da kitso, ranar Asabar zaki tare" Zare ido Jalila tayi tace "Wai Asabar me zuwa?" "Eh mana, mijinki yace; se kin tare ya gaji da wannan sintirin" Shiru Jalila tayi ta sunkuyar da kai, Hajiya Salma tace "Haba Jalila meye kuma na damuwa? Allah ya baku zaman lafiya, karki damu kinji" jinjina mata kai kawai Jalila tayi ba tareda tace komai ba. Yau weekends ne, Hanan sun gama cin Abincin Rana da Jawwad, tana ta zuba shagwabarta yana biye mata, dan ba karamin birge shi wannan shagwabar take ba, yace " Habibty Inaga ranar Saturday fa sister dinki zata tare" "Wai Jalila?" Jawwad yace "eh ita, munyi waya da shi dazu da safe kina bacci, ya gayamin ya sai gida, an gama zuba komai ranar Saturday zata tare, inkuma sunki zeje ya dauketa ne kawai" Dariya Hanan ta kama yi, Jawwad yace "ya dai, ya naga kina dariya?" "Akwai kura ne" "Kura kuma? Meyasa kikace haka?" "Hmm bakomai, gaskiya yakamata muje kano, zanso inyi kallon yadda wannan rayuwar masoyan zata kasance" Jawwad yai murmushi yace "lafiya kalau zasu zauna" "Hakane wuyatta su zauna guri daya, bari a jima in kirata, naga har yanzu bata da waya, se dai kabani taka in kirata" Jawwad yace "Shikenan naga be bata wayarba har yanzu" "nasan ze bata insha Allah" Hanan ta mike ta tafi bedroom dinta. Jalila tarasa meya kema ta dadi, wai ita ce zata tare a gidan Jalal, a matsayin matarsa, tanata tunane2, Amal tayi sallama, Jalila ta amsa, Amal tace "Anty Jalila, Mummy tace in kawomiki phone, your sister wants to talk to you" Jalila a ranta tace ;kai yaran gidan nan sunfiye iyayi, ji yadda take magana kamar me koyon hausa Jalila tasa hannu ta karbi wayar tareda cewa "Nagode" Wayar aka sake kira Jalila ta daga wayar tareda fadin "Salamu Alaikum" Yanayin muryarta ze gaya maka tana cikin damuwa, Hanan tace "Amaryar Yaya Jalal, ke ko kirana ba kyayi se idan nina kiraki ko?" Cikin sanyin jiki Jalila tace " kinsan bani da waya tun ranar dinner da ya karba be baniba, bana son yawan takura musu da karbar waya" Hanan tace "hakane ya kike ya shirye2" "shirye2 me?" Jalila ta tambaya Hanan tace "Ahhh Haidar yacemin ranar Saturday In Allah ya kaimu zaki tare" Dan karamin tsaki Jalila tayi "shine wani ya shirye2, ba wani shirye2 ni abun duniya ya dameni, ina tunanin irin zaman da zanyi a gidan nan" "meye wani abun damuwa kuma? Karki dorawa kanki ciwo mana, Allah yabaku zaman lafiya yasa kina zuwa kiyi karo da shi" Jalila tace "inyi karo dame?" "ďan baba mana, nan da wata tara muzo suna" hanan ta bata amsa Wani uban tsaki Jalila tayi "Ke kinfiye shirme wallahi" "bawani shirme, Addu'a nai miki tagari" "rike addu'ar ki bana so, ni ba haka naje yi ba" Dariya Hanan ta dinga yi "Wallahi karya kike, abunda kikaje yi kenan, sekin cika masa gida da 'ya' ya duk shekara zaki dinga haihuwa" Kashe wayar Jalila tayi, tareda yin dogon tsaki, inta biyewa Hanan bata mata rai zata cigaba da yi. Shirye2 sunyi nisa, Hajiya Salma da Anty sun tsaya an gyara Jalila yadda yakamata, sun hada mata kayan turaruka daban2, Suka shirya mata kayanta a trolley. Ta wani bangaren Jalila tanata murna zata koma garinsu, ta cigaba da zuwa makaranta, Anty tace "Jalila na cika alkawarin dana taba yi miki, ga turaruka nan, in sun kare ma kiyi magana se in hado miki wasu" "to Anty na gode" Abee yayiwa Jalila nasiha sosai, tareda yi mata fatan Alkhairi, yabata kyautuka na litattafan Addini dana zamani, sekuma kyautar system yace taje taita karatu. Jalila tai tayi masa godiya. Hajiya Salma sunyi waya da Jalal, cewar zasu taho da Jalila gobe zasu tsaya a gidan su Jalila, sannan su kaita gurin Mummy daga nan akaita gidanta. Jalal yace "gaskiya bana son ku kaita gidan Mummy, dan seta bata muku rai, kawai ku kyale ta" "A'a Jalal baza'ayi haka ba, Mahaifiyarka ce akwai bukatar a sauke hakkinta na uwa, yakamata ta sawa Aurenka Albarka" Jalal yace "Shikenan yadda kuka gani, Amma ni a gurina babu bukatar hakan. Ilham bata taba sanin tana kaunar Jalal ba kamar yanzu, gaba daya kishi ya hanata sukuni ko Abinci bata iya ci, ita a tunanin ta tana so tayi soyayya da Jalal ne dan cika burin mahaifiyarta, Amma yanzu ta gane kaunar Jalal tayi mata illa, bata bacci sam, yadda taga rana haka taga dare, wai Jalal ke gaya mata shidin mallakin Wata mace ne, macen da ta dade tana cusa masa miyagun maganganu da cin mutunci amma saboda bashi da zuciya yake fadin shi mallakin ta ne, hawaye ne ya gangaro daga idon Ilham tace "Wallahi Jalal muddin baka Aureni ba sena fitini rayuwar Auren ka, sena uzzurawa rayuwarku, se Gidan Auren ka yazama kurku ta fishi 'yanci, idan har kuka ji dadin Aure ba Saudatu ce ta haifeni" ta cigaba da kuka da surutai a daki. Jalila se murna take zata koma Kano, koba komai zata dinga zuwa makaranta ta rage kadaici, karfe goma sha daya na safe suka shirya, Anty, Hajiya Salma, Husna, da wasu daga danginsu Jalal suka taho yiwa Jalila rakiya Kano, Se kusan karfe hudu na yamma suka iso, Maama ta san da zuwansu dan haka ta riga ta shirya komai, har 'yan uwanta da makwabta ta sanar, bayan sallar magariba za'a raka Jalila gidanta. Jalila tayi murna ganinta a gida, Abba yayi murna yadda yaga Jalila tayi kalau da ita tayi fes kaman wata matar hamshaki. Dakinsu taje komai yana nan yadda ta barshi, kewar Nana ta dinga ji a ranta, tana tuno abubuwa da dama da ya faru a wannan dakin, wasu ma farinciki wasu na bakinciki. Maama tazo ta sameta tace "Jalila ki debi duka abunda kike so akayanki, wanda zakiyi Amfani da shi nan kusa se a tafi miki dashi" "to Maama zan diba Insha Allah" Sukaci Abinci sukayi Sallolin da ake binsu. Anty tace "Jalila yakamata ki shirya muje a kaiki gurin uwar mijinki, kar dare yayi sosai" Ras gaban Jalila ya fadi! Jikinta yafara Rawa, ta shiga duniyar tunanin wace irin karba Mummy zatayi mata. Kamar wadda kwai ya fashewa a ciki ta Amsa, seda takuma wanka ta canza kaya, suka nadeta a cikin lafaya, se kamshi takeyi Maama ta kama hannunta ta kaita gurin Abba, ya dinga mata nasiha da Addu'a, Jalila se kuka take, yadda Abba yaji rabuwa da Jalila beji haka akan Nana da Jawwad ba, yana matukar tausayinta. Bayan ya gama ne Maama tayi mata 'yan nasihohi da Addu'a, dan sosai take jin kunyar abubuwan da ta aikatawa Jalila. Wasu daga cikin' yan rakiyar amarya sunyi gaba dan suje suga ďaki, Yayinda Hajiya Salma da Antyn Jalal suka nufi gidan su Jalal Da Amarya Jalila. Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724          🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 5️⃣4️⃣107 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                         _MY FIRST NOVEL _ Gaba daya jikinta yayi sanyi ta tsaya tana kallonsa, juyawa tayi ta koma daki ta barshi a parlourn, se bayan ta tafai yaji gaba daya jikinsa yayi sanyi, yake tambayar kansa meyasa yayi mata shouting? Laifin me tayi masa? Gaba daya se yaji ransa ya baci. Ya tashi ya bi bayanta, amma ya tarar ta rufe kofarta sannan ta kashe futile, haka ya hakura ya koma dakinsa. Washegari bayan tayi salla, ta shiga kitchen ta hada breakfast, kafin ya tashi har ta kammala abunda zatayi tai ficewar ta. Naja ce ta shigo gidan ko sallama babu sekace korarriya, Yaya mairo ta kalleta tace "ke meye haka ko sallama babu"? Dan guntun tsaki Naja tayi tace "wallahi matsiya ciyar yarinyar nan ta cuceni, da yanzu ina Abuja ina hutawa, Amma gashi ba Auren, kuma duk samarin nawa sun gudu ga talauci ya isheni" Yaya mairo tace "kema ke kika cuci kanki, shaye2 Naja, na miki fada har bansan adadi ba, ga wannan abun kunya da kikayi, ba dan Allah ya rufa asiri ya zube ba da shikenan, kinjamin masifa" "Amma da ya aureni aida zan dena, wannan bakar shegiyar ta zalunceni ita da Allah makira, kuma itama tayi Aure sun barni a titi" Yaya mairo tace "Aure kuma, wata aura?" Naja tace "Agurin daurin Auren aka bawa wannan dan shaye2 sadakarta, Jalal suke ce masa ko Jamilu oho dai" Sa'ada da tun dazu ke kwance na danna waya ba tace uffan ba se yanzu, ta kalli Naja tace "Ke bana son shirme, da gaske Jalal ta aura" Cikin tsiwa Naja tace "Bansani ba tunda baki yadda ba meye na son se kin tabattar aikin banza kawai, na tsani inyi magana a karyatani" "Sorry ba karyataki nayi ba, amma waya gaya miki?" Cikin kosawa Naja tace "Zancen duniya yana buya ne? A anguwarsu naji, har gidan seda aka kwatanta min, shi aka Aura mata, Ai Allah ya kara, Allah yasa yayi mata dukan da seya kashe ta" Yaya mairo tace "Ameen dai Naja, Ai Allah ne yasaka miki ya hadata da dai dai ita, yayi ta cin kaniyarta" Kallonsu kawai Sa'ada take da sun san me Jalila ke nufi a rayuwar Jalal da basuyi wannan maganar ba. Tashi tayi tsam tabar parlourn ta koma dakinsu ta dakko waya ta kira Hannah. Seda ta kusa katsewa sannan Hannah ta daga Sa'adah tace "ke Hannah, wai kina inane?" "kamar ya ina ina? Kefa na Gaya miki Jalal yasa 'yan sanda su nemoni, ina Abuja se ya huce zan dawo, daga nan na kara shirin tinkarar sa, dan koda tsiya sena cika burina" "ke dalla banza kina can kina garanci to yayi Aure" "ke saurara, kamarya yayi Aure? Ya Auri wa? Mutumin da ko budurwa bashida? Sa'adah tace " sadakar mata aka bashi a bati, wannan Jalilan dai ita aka bashi sadaka" Cikin tsawa Hannah tace "Impossible how? Ta yaya? Ke waya gaya miki? A ina kikaji?" "Yanzu Naja tazo tana zancen, tace haf gidan da yake ta sani" Hannah tace "please help me, kije ki tabattar min dagaskene, karki sa jinina ya hau bayan karyane" Sa'adah tace "ke nikike so inje gidansa in yana nan fa, kinsan ba cukakken hankali ne da shi ba, tijara zemin a bainar nasi" Hannah ta marairaice tace "please Sa'adah ki temakamin, i dan zancen nan ya tabatta sena kusa hauka wallahi, ke dole ma in zo kano ayita ta kare, dan girman Allah Sa'adah ki samomin sahihancin maganar nan" "karki damu zan duba miki Insha Allah" Hannah tace "Yawwa kawata ki temaka, dole in tattaro kayana in dawo, dama tazo min da zan nunawa yarinyar nan ta tari aradu da kai" Sa'adah tace "a da baki nuna mata ta tari aradu da kai ba se yanzu, da ta baku mamaki keda Kanwarsa, kuna nan kuna wahala ta aureshi ta barku" "haba Sa'adah kefa kikace sadakarta a ka Bashi, ta yaya kike tunanin ze so matar sadaka, kyaleni da shi kawai" "Hannah wani tabbaci kike da na cewa shi baya sonta, ke kina tunanin za'ayiwa Jalal auren dole a yadda yake ne" Hannah tace "ke mu bar maganar naan ji nake zuciya ta kaman ta faso kirjina saboda takaici, duk abunda kika gano kimin bayani" Sa'adah tace "shikenan zanyi kokarin bincika miki" Sa'adah takoma parlour tace "Naja nikam inane gidan yarinyar nan, inason inje inga kwakwaf, daga nan inci mata mutunci" Naja tace "kyaje ta bakanta miki rai, kin san ba mutunci ta cika ba" Sa'adah ta lallabata ta gaya mata kwatancen gidan Jalal. Koda Jalal ya tashi ya tarar harta tafi school, se yaji babu dadi dabe ganta ba, sedai tayi girkin breakfast ta ajiye masa, yayi breakfast yayi wanka ya fice. Jalila na daf da kammala lectures message ya shigo wayarta "in kin gama ina jiranki a harabar department dinku" ABDUL JALAL Ajiye wayar tayi, suka gama lectures sannan ta fito, tana fitowa daga lectures ta hango motarsa, tana zuwa ta bude gaban motar ta shiga ba tareda ta kula shi ba, kallo daya yayi mata yasan ta gaji sosai, Yace "Sannu" bata amsa ba sema kwanciya da tayi a jikin kujerar ta juyar da kanta daga kallonsa tana sauke numfashi. Dukda daddadan kamshin turaren Jalal da kuma turaren dake ta shi a cikin motar sa, hakan be hanata jin tashin wari sigari kadan2 ba. Ya kunna motar yafara tafiya can ba tare da kalleshi ba Jalila tace "Jalal ka sha sigari ko?" Jalal yace mata "Eh na sha" Tace "Good" "Amma kadan na sha guda biyu ne kawai fa" Shiru tayi masa har suka je gida, suna zuwa ma bata bi ta kansa ba tai tafiyarta dakinta tai salla ta huta sannan ta fito ta nemi abunda zata ci, jallof din macaroni tayi, ta zauna tana ci a parlour Jalal ya fito, yana zama ta tashi ta koma daki. Kasa daurewa Jalal yayi ya tashi ya bita dakin nata, ta harde akan gado tana cin Abincin ta, dan stool dinta na kwalliya ya janyo ya zauna a gabanta ya tsura mata ido. "kaga ni dan Allah kar kasa in kware, kasani a gaba da kallo, shiyasa na baro maka parlour ni bana son kallo" "Ai ba wani abun nake kallo ba nima, mezan kalla a jikin kwailar da na dauka a hannuna, na goya a bayana, na dinga jefawa sama ina cafewa, ga Yamin me zan kalla?" Jalila a ranta tace "Lallai Jalal dan rainin hankali ne ya cini wasa" Amma ta kara hade rai tace "to tunda ni kwailace bani da abun kallo meye na zuwa kasani a gaba ka tsiramin ido?" Ta yunkura zata mike, ya riketa ya zaunar da ita akan gadon yace "dan kinga ina shiga damuwa in kika dena kulani shiyasa kike ta hademin rai kina wani shareni ko?" Dagowa tayi ta kalleshi tace "Jiya kayimin shouting dan kawai nace kayi Azkar, kuma kasan bana son shouting, yau kuma ka sha sigari abunda yafi bata min rai, dan me ba zanyi fushi ba? Ko sokake in cigaba da shiga harkar ka kanamin shouting" Ta karasa maganar tana kara hade rai da dan tura baki. Hannayenta ya riko yace "Jalila na sha gaya miki ba lokaci daya na fara shaye2 ba, bazan iya denawa lokaci daya ba, kuma ina kokari sosai in dena, sedai lokuta dayawa inaji kamar zanyi hauka idan ban sha ba, duk da haka ina cigaba ds kokari, ki cigaba da yimin Addu'a, sannan Indai Adhkar ne zamu dinga yi shikenan? " Zumbura baki tayi tace " ba shikenan ba da saura" "me yayi saura kuma?" ya tambaya Tace "ba kabani hakuri ba fa" Dan tsura mata ido yayi yana kallon ta, yarinyartarta ta kara fitowa sosai musamman idan tana jin rigima "Nine zan baki hakurin?" "Eh kawai ka bani hakuri, ai laifi kayi min" "idan na ki baki hakurin fa? Ke bakiji kunya ba da kikace in baki hakuri?" "Kunyar me zanji kuma? Laifi fa kayi min, ko kai agurinka ba komai bane?" "to shikenan I am sorry, bazan kara ba" Murmushi tayi tace "Yawwa ko kaifa, Jalal duk lokacin da ka batawa mutum rai ko bani ba Dan Allah ka bawa mutum hakuri, Nagode, yi hakuri, dan Allah, kalmomi ne masu sauki se dai suna da wahala a harshen wasu mutanen, duk mutumin da baya gane kuskuren sa ya nemi afuwa hakan alamace ta girman kai, kumma Allah baya son masu girman kai, dan haka ka ko yarone karami ya in dai ka bata masa babu laifi ka bashi hakuri, bazaka ragu da komai ba" Yadda ta kwantar da kai take sarrafa harshenta gurin yi masa nasihar ne ya burgeshi. Amma yace "Waike bazaki dena kirana da Jalal kai tsaye haka ba, kefa baki da kunya" "to Yaya Jalal" Hararta yayi yace "niba yayanki bane ba, ni mijinki ne dan haka bana son wani Yaya da can ma inaji haka kike cewa Yaya Jawwad, amma ni saboda kin rainani wai ABDUL JALAL kai Allah ya yafe miki kwailar Ummi" Dariya tayi tace "waye mijin, wai kaine mijina, tabdijan, kuma wallahi niba kwaila bace, kuma Allah ya yafe maka dai, yadda ka dinga cin zalina, dan ma ina rufa maka asiri, amma ka ci zalina da yawa wallahi" Dariya yake sosai, befi ta kirga sau nawa taga yana dariya haka ba dariyar tayi masa kyau sosai yace "kin kyauta zakiyi bayani da manyan baki ne, bani Abincin nima inci tun dazu kamshi ya cikamin hamci" "wannan dan Abincin, me naci me na baka? Jeka dafa naka wannan nawane, meze sa ma kaci Abinci da kwaila?" ta fada tareda dauke plate din Abincin. Sakkowa yayi ya zauna kusa da ita yace  "dan sanmin mana, ko kadan ne" Jalila tace "to tsaya yi spoon daya" Tana miko masa plate din ya mike yace "Se anjima kin gama cin naki, sannan a kawomin wayata da'aka kwace, dan nasan 'yan mata na sun kirani ba adadi" "har zawrawanka ma sun kiraka ai, ni kayiwa wayo zan rama ne" Murmushi yayi ya nufi haanyar fita yace "kawomin wayar daki, zanyi wankane" A dan shirin da suke kwanan nan ta kara fuskantar he's so simple, yana da wasa da dariya ga shi ya iya tsokana sosai, abunda bata taba zata ba, saboda kusan koda yaushe ransa a hade, babu abokin hira, babu me sauraron matsalolinsa. Bayan fitarsa taje kitchen ta ajiye kwanon da taci Abinci ta dawo daki ta dakko wayar Jalal domin kai masa wayar a silent take dan haka akwai missed calls dayawa a wayar, ta karo volume din wayar ta shiga dakin nasa da sallama, ya riga ya shiga wanka, tana ajiye wayar, wayar ta fara ringing, Tace Jalal "ana kiranka a waya" "ki daga mana" "niba zan daga ba, gata nan dai anmaka miss calls da yawa" Jalal yace "nina ce ki daga ai, yanzun zan fito, kinsa ina surutu a toilet sekace ke" Daga wayar tayi tasa a kunnenta tare da fadin "Salamu Alaikum" Muryar mummy ce ke fadin "ke ina dana yake? Mara mutunci tun jiya nake kiran sa amma kika hanashi dauka, ki bani zanyi magana da shi mara mutunci" Jiki  a sanyaye Jalila tace "Mummy ina wuni, wayar tasa ce a silent shiya..... Ke dalla ki rufemin baki, mara mutunci wadda bata san darajar kanta ba, kingama zagun sa da cin mutuncinsa agabana kuma kinkoma kin lallaba kin aureshi kina kokarin rabani da shi, saboda wulakanci tunda ya bar gidan nan koda wasa bezo inda nake ba, to baki isa ba wallahi, kuma ki fara kirga kwanakin barinki gidan nan daf nake da datse auren nan bazan taba kaunarki ba, ki bashi waya zanyi magana da shi" Tuni hawaye ya jika fuskar Jalila tace "yi hakuri Mummy, wallahi ba laifina bane, nima... Dayake Mummy a hands free tasa wayar Ilham tana jin maganar dasukeyi, Ilham ta karbe wayar tace" dalla malama tace miki da danta take son tayi magana, ke wace irin dabba ce ne haka? Mara zuciya wadda bata ganewa, uwar mutum tace bata sonki dayake ke jinin maita ce kin like masa, dukiyarsa kike yiwa shiyasa kika hada baki da marikin ki kika aure shi, nasan dai ba wani sonki yake ba dan ba abunda zeyi dake, giyar da yake sha tafiye masa komai mahinmmanci ciki kuwa hadda ke, dan haka ba saurararki zeyi ba" Jalila ta kawo iya wuya, a ranta tace, idan bataka wa wannan Ilham din briki ba bazata sauraramin ba, so take taji halin da nake ciki a zaman gidan nan dan haka tace "kinga dan Allah saurara Ilham, ke meye naki a ciki da Mummy muke magana ba dake ba, tunda kin matsu bari in gaya miki yana bandaki yana wanka" Da sauri Ilham ta kalli Mummy ta Zare ido tace "wanka kuma?" Jalila tace "Eh mana wanka yake yi" Karaf a kunnen Mummy, hakan yayi dai2 da fitowar Jalal daga toilet yana goge kansa, karasowa inda Jalila take yayi yasa hannu ya karbi wayar daga hannunta, juyawa tayi zata bar dakin ya riketa, yasa wayar a kunnensa yaji muryar Mummy tana masifa "kinfadi sako, kuma naji, nasan dani kike, ni kike gayawa yana wanka, aiba se kin gayamin ba, mara mutunci" "ai ba dake take ba, Ilham ce ta tambaya aka bata amsa" Mummy najin muryar Jalal tace "Yanzu Jalal kayiwa kanka adalci, dama kana nan kana ji amma kaki amsa min waya, tun jiya nake kiranka a waya amma kaki dagawa" "Duk lokacin da zaki kirani abunda zaki batamin rai kikeyi, zuwana gida  bashi da amfani, Daddy baya Gari, daddy ne kawai yakeson abunda nake so, idan nazo ma Zaki yi maganar da ze batamin raine dan haka ba wani amfani kona zo inda kike tunda.. Rufe bakinsa Jalila tayi tana girgiza masa kai idonta duk hawaye A hankali tace "Mummy ce fa, karka fadi abunda ze bata mata rai, Allah zeyi fushi da kai" Tausayin Jalila ne ma yakama shi, yasan tunda yaga tana kuka yasan Mummy taci mata mutunci ne, ajiye wayar yayi yasa hannu yana share mata hawayen fuskarta. Jalila Tana tunanin zama da mutumin da mahaifiyarsa ke mata wannan mumunnar tsanar haka, ta tuna yadda mutunci da girmamawane tsakaninta da Mummy Jalal amma gaba daya ta canza mata, ta maida ita makiyyarta. "kidena kuka mana, ke har yanzu sekace wata jaririya, dukkan tsanani yana tareda sauki, so stop crying" ya karasa maganar yana yatsina fuska kaman zeyi kuka. Jinjina masa kai kawai tayi, ya cikata ta juya ta bar Dakin. Jalila a kwana uku tayi saukar qur'ani a cikin zuma da zam2, da safe kafin Jalal yaci komai take fara bashi zumar nan, sam Jalal baya son zumar nan, dan daya sha yakejin kamar zeyi amai, wani lokacin se sunyi fada sosai yake sha. Ga zam2 da take bashi me dauke da saukar qur'ani. Ta dage sosai akan ganin yana Addu'oi. Zaman nasu ba laifi sedai Jalal bashi da niyyar yi mata komai na bangaren Aure shiyasa ta kara sakin jiki da shi sosai. Jalila ta kai masa zumar da ta saba bashi, ta tarar yana waya da Jalal Jawwad yace "Jalal dan Allah ka siyo mana taura da magarya ka kai tasha a kawo mana, Hanan ce ke so, ni kuma ban san inda zan samu ba anan, kuma bazan iya gayawa Maama a siyo mata ba inajin nauyin hakan" Jalal yace "Tab to ai nima ban san inda ake saida wannan abun ba tunda ba sha nake ba amma zanyi maganar da Jalila se a siyo a aiko muku" sukayi sallama akan haka. Jalila tace "ga zumar ka ka sha, zanje in kwanta" Ya yamutse fuska yace " Nifa bana son abun nan ciwon ciki take sani" "yi hakuri ka sha mana, spoon daya kawai" sekace karamin yaro seda taita lallabashi sannan ya karba yana ya mutsa fuska Jalal ya kalleta yace "A ina ake saida magarya da taura?" Jalila tace "a kasuwa mana" Jalal yace "wai Hanan ce take so, za'a siya a aika musu" Jalila tace "gaskiya Hanan tana bawa yayana wahala, yau tace wannan gobe tace wancan, zan gamu da itane" Jalal ya harareta yace "dan me bazeyi wahala ba, da haka takeyi? Tunda shi yayi dole ya kula dashi" Ya kuma maze kamar bashi ya fada ba, itakuwa Jalila ji tayi kamar kasa ta bude ta shige dan kunyar abunda ya fada, ta mike tsama tace "Amma seda safe" Murmushi yayi yace "tun yanzu, yau baza'ayi Azkar din bane?" Tace "A'a ni nayi a dakina, kayi kai ka dai" Tana fita ya kwashe da dariya, yace "Jalila kenan, kema ina jiran lokaci ne, Allah ka cikamin burina akan Jalila yasa ta soni kaman yadda nake sonta" Yauma weekends ne dyk suna gida ta kammala aikace2, tana kallon bollywood, knocking din kofar parlor akayi dan haka ta tashi taje ta bude, ga mamakinta Naja ce da sa'adah amma ta boye mamakinta ta saki fuska "Ahh manyan baki sannunku da zuwa" ta basu hanya suka wuce suna mata wani irin kallon banza. Sukaje suka zauna a parlor, Sa'adah ta kalli Jalila tace "Ashe Aure kikayi?" Jalila tace "Aiba ashe bane, tunda gaki a gidana" Naja tayi tsaki tace "aka dai bada sadakarki tunda bashi yace yana so ba" "to ke abada sadakar taki mana, ai ba kowace mace ake bada sadakarta a karba ba se ishashshiyar mace" Sa'adah tace "Ke karki cimina mutunci dan munzo inda kike, matsiyaciya kawai" Jalila tace "aibani na gayyato ku ba" A fusace Naja tace  "ke  karki ci zarafinmu dan munzo gidanki" "aibana cin mutuncin kowa, musamman wanda yazo inda nake sedai da abunda kazomin dashi nake karbarka" Jalal tun farkon zuwansu yana jin duk abunda sukeyi, yasan Sa'adah ba zuwan Allah ne ya kawo su ba, shikam yana kokari ya toshe duk wata kafa da zata kawo masa tashin hankali a gidan sa. Dan haka ne ya fito daga daki ba tareda yace musu uffan ba ya wuce ya bude kofar parlor, 'yan sanda ne suka shigo, gaba daya suka razana dan basu san Jalal yana gidan ba. Jalal yanunawa' yan sanda Sa'adah yace "Arrest her" mikewa sukayi gaba daya Jalila tace "Jalal meyasa? Me sukayi maka?" Jalal be kulata ba yace "Arrest her har seta fito da inda Kawarta take" Sa'adah tace "Amma ni meye nawa a ciki, wallahi officer banyi komai ba" A tsawace Jalal yace "Arrest her, seta fito da Hannah" aikuwa haka ayi suka kama su Naja suka fita dasu. Jalila tace "Jalal meyasa? Me sukayi maka haka zaka sa akamasu?" "calm down, count yourself out of this, babu ruwanki" "Amma Jalal ace daga sunzo inda nake kasa an kamasu why?" Janyota jikinsa yayi ya kwantar da murya "Jalila duk abunda nakeyi, duk shaye2 na bana yadda in cuci wani, don't mind me" Jalila ta mariraice Tace "Amma" "Shhh bana son musu" Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724          🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 5️⃣5️⃣108 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                         _MY FIRST NOVEL _ Jalila kaman zatayi kuka tace "please Jalal, kome sukayi maka kayi hakuri kasa a kyalesu, karka karamin bakin jini a gurin mutane. Jalal yayi kasa da muryarsa sosai ya kai bakinsa kunenta yace "ko kowa ya ki ki, ni ina tareda ke kuma ina sonki, duk me kinki Bashi da gaskiya, duk wanda yake adawa dake wanda baya son cigaba nane, kinyi yaki da mutane da dama saboda ni, ina sonki Jalila," Gaba daya jikinta yayi sanyi taji tsigar jikinta na tashi, a hankali tace" Amma Jalal..... "karki kuma yimin magana akan su, akwai dalilin da yasani yin hakan, karki damu kinji my wife" Yaya mairo ta kira wayar su Naja babu adadi amma sunki dagawa, sun saba da gantalinsu bata damuwa amma haka nan taji yau takasa nutsuwa, har maghariba bata gansu, se wajen Isha'i Naja ta dawo a wahalce, ko Abinci bata ci ba ga yunwa da kishirwa. Yaya mairo tace "ke lafiya kuwa? Ina sa'adah take?" Naja tace "ina fa lafiya, sa'adah ta jamu gidan wannan Yarinyar mijinta yasa aka kamamu, wai ko seta fadi inda wata take, nima da kyar yayi waya aka sakeni" Yaya mairo tace "ke kimin bayani wai ina kukaje akayi muku hakan? Bangane me kike nufi ba" A fusace Naja tace "Wai meyasa ba kya ganewa ne, nace miki gidan Jalal ta ja mu, yasa 'yan sanda suka kamamu, ni sun sakeni ita tana can" "A' ahh to me kukayi masa? Wani station dinne?" "dan Allah ki barni in huta, Allah kadai yasan azabar dana sha ta yunwa amma kin uzzuramun da tambayoyi, niki kyaleni da banyi niyyar zuwa gidan nan ba amma ta jani ta janyomin masifa" Hankalin yaya mairo ya tashi sosai, gashi Naja taki ta tsaya tayi mata bayani yadds yakamata . Jalila ta kira Hanan suna ta waya tace "gaskiya Hanan kina wahalar da bawan Allah, yau kice wannan gobe wancan haka akeyi" Hanan tace "Jalila duk yadda zan Gaya miki bazaki gane ba seyazo kanki tukuna" Jalila tace "ba wani hadda shagwabarki da neman magana" "wallahi Jalila ina jin tausayin Haidar sosai, bana laulayi se dai bakomai nake iya ci ba shine kullum ke nema min me zanci, Amma ba yadda zanyi ne" . "Allah sarki, Allah yarabaku lafiya, wai watan cikin naki nawane? " wata na biyar " Zare ido Jalila tayi " wai har munyi wata biyar da Aure? Amma kina shiga kikayi karo da shi? " Hanan tace "ban saniba, da shi naje, 'yar rainin hankali wallahi satina biyu, naita ciwon kai muna zuwa Asibiti aka ce cikine" Dariya Jalila ta dingayi tace "angama iyayin, ana zuwa akayi karo, Allah yaraba lafiya" "Ameen dai, ina mijin naki, fatan dai komai lafiya?" "yana nan lafiya" Jalila ta bata amsa Hanan tace "Ina fatan komai Lafiya Jalila, Allah yasa kun daidaita" Jalila tace "gamu nan dai" "gaku nan dai kamar yaya? Har yanzu ba kwa shirin ne" "munayi sama sama" "Jalila waike wane irin taurin kaine dake haka?" Jalila tace "ke karki min fada mana, kin dameni fa, se anjima tafi gurin mijinki kiyi masa". Seda sukayi dan fadan da suka saba sannan sukayi sallama. Jalila ta tashi ta dauki zuma ta nufi dakin Jalal, yana ganinta da container zuman nan ya hade rai, murmushi ta farayi tana cewa "meye kuma na wani hade rai, sekace kaga wani abun gudu" Jalal yace "nifa nagaji da shan wannnan abar, kullum kizo kiyita bani, ciwon ciki take sani fa" Jalila tace "Ai ciwon cikin ba me damu bane, saboda magani nake baka, so nake inyi substituting din giyar da kake sha da zuma, kuma karatun qur:ani ne a ciki, Insha Allah very soon zaka dena shan giya" Jalal yace "ko yanzu ma aina dade ban sha giya ba, dan Allah ki dinga kyaleni da zumar nan, kodai wani abun kike zubamun, dan ki mallakewa Mummy danta?" Yai maganar yana kashe mata ido, tareda yin murmushi Dariya Jalila tayi tace "Kai mallake ka wani wahala zemin ne, ai base na baka magani ba idan ina son hakan?" "Allah ko?" Jalila tace "Eh mana, yanzu dai karbi ka sha spoon biyu kawai" Seda ya bata rai sannan ya karba ya sha yana ya tsuna fuska, dan jan dogon hancinsa tayi tace "barakallahu fik" Jinjina kai kawai yayi bece komai ba A shagwabe Jalila tace "baka fada ba fa" Yace "Ameen, thank you" Murmushi tayi ta shafa sumarsa "weldone dear, bari muyi Adhkar seka kwanta ko?" Jalal yace "yadda duk kikayi" Jalila tace "yawwa kafin muyi Adhkar bari muyi magana, wai yaushe zaka koma aiki? Kullum kana gida se dai kaje ka zaga gari ka dawo" "bazan koma aikin nan ba" "meyasa?" " bashi da Amfani ina can zuciya ta tana nan, sam bana samun nutsuwa, ga banbancin Al'adu da dabi'u da muke dasu, gashi nika dai nake tafiya babu ke, akwai damuwane gara inyi zamana inta ganinki kullum ina jin dadi" Jalila tace "Haba Jalal, dan Allah ka dena wasa, Aikin nan yana da mahimmanci sosai, at least you have something to do, dan Daddy yana baka duk abunda kake bukata, bashi ke nufin kaima bazaka nemi naka ba" Jalal ya danyi murmushi yace "waya ce miki Daddy ne kemin komai? Nasan Daddy yana min wasu abubuwan amma da kudina nake komai musamman abunda ya shafi gidana, da kefa mukaje kika ga kamfani na, Daddy ne kadai da wasu daga ma'aikata na suka san nawa nake samu a duk wata a kamfanina, Allah ya alabarkaci dukiya ta fiye da yadda kike tunani, dukda na kasance me sabon Allah, Amma Allah ya hadani da mutanen Arziki masu Amana da suke juyamin dukiya ta" Jalila tace "Amma in hakane, yakamata ace ko kamfanin ne kaje ka dinga aiki" "ke bazani ba ki kyaleni kawai" Jalila tace "to shikenan na kyaleka, amma gaskiya yakamata a ce munje gida ka gaida Mummy, tunda kaga harta fara magana, baka kyauta ba sam" Maimakon yayi magana ma harararta yayi yaja pillow ze kwanta, tasa hannu ta rike pillow "Haba Jalal idan kayi hakan baka kyauta ba, iyaye hakuri ake dasu komai girman laifin da sukayi maka sun gama komai tunda suka kawoka duniya" Sakar mata pillow yayi ya juya ya kwanta, gadon ta hau ta cigaba da magana "Please Jalal, dan Allah yakamata kaje wallahi" Janyota yayi jikinsa ya rungumeta kam a jikinsa, sosai ta firgice da abunda Jalal yakeyi mata. "Jalal dan Allah ka bari bana so, ana knocking kofar parlor fa" Cikata yayi ya lumshe ido, dirowa tayi daga gadon takoma gefe tana kallonsa tareda sauke numfashi, ci gaba da knocking akayi, Jalila tace "Ana knocking fa" Jalal yace "kije ki bude mana" "ni gaskiya tsoro nakeji bazan iya budewa ba" "ni inje in mutu kenan" "A'a niba haka ba, kaje ja duba dan Allah" Jalal ya kalli agogo goma saura, mikewa yayi ya tafi budewa tabiyo bayansa tana labewa a baya, yasa key ya bude kofar parlourn, yana budewa yafara sosa kai yana murmushi, matsawa gefe yayi, Abba da Maama ne suka shigo Jalila na ganinsu tayi tsalle taje ta rungume Maama. "Maama har na fidda ran zakizo wallahi" Maama tace "to ki bamu gurin zama mana, har kinfara complain" Gurin zama ta basu tanata murna, Jalila tace "Abba ina wuni" Abba yace "lafiya kalau Alhamdilillah" Jalal yace "Abba ina wuninku?" Maama tace "lafiya kalau Jalal ya gidan?" "lafiya kalau Abba" Jalila tace "Abba shine bakuzo da rana ba, seda dare yayi" Maama tace "yanzunma Allah ne yayi zamuzo, mun fita gaisuwa gidan abokinsa nace masa ya tsaya mu biyo mu ganki" Nan suka dinga hira, Jalila tace bari ina kawomu ku Abinci. Abba yace "ki barshi Baby, yanzu zamu tafi" Jalila tace "haba Abba, ai ba Abinci me nauyi bane, inada cake a fridge" Maama tace "Ahh in baya ci ni dakko min nayi missing girke girkenki" Jalila ta tafi kitchen, ta shiryo cake da lemo a tray zata dakko taga Jalal a bakin kofa yana mata dariya. Kallonsa tayi tace "dariyar me ka keyi ne?" Ya karaso inda take yace "juya" Ba musu ta juya, yasa hannu ya ja zip din rigarta ya karasa rufewa, zare ido tayi tace "kai wai a bude yake" Jalal yace "eh ba a rufe yake gaba daya ba" "na shiga uku, kuma sun gani?" Dariya ya fara yimata Kamar ze fadi, gaba daya tarasa me yake mata dadi, ta harari Jalal. Jalal yace "ki kai musu Mana dare yanayi fa" Ta kwabe fuska kamar zatayi kuka tace "ni gaskiya bazan fita ba kunyya nake ji" "kunyar wa kike ji?" Jalila tace "nikam inajin kunya wallahi" Jalal yace "karki damu basu gani ba fa, nika dai nagani, dauki muje" Ta dakko tray din ya biyo bayanta. Maama taja Jalila bedroom "Jalila ina datan babu wata matsala, kuna zaune lafiya?" Jalila tace "babu matsalan komai Maaama, lafiya kalau muke zaune" "dama an gaya miki, zaku zauna lafiya komai ze wuce, Ya shaye2 kuwa yanayi har yanzu kokuwa?" Jalila tace "A'a Maama, baya shaye2 yanzu ya dena" "ki ga yamin gaskiya Jalila, karki kare shi" "Maama da gaske nake, baya shan komai yanzu" Maama tace "Alhamdilillah, ki cigaba da hakuri dai, kinsan ita rayuwar Aure gaba dayanta hakuri ce, sannan ki toshe kunnenki akan abunda mahaifiyarsa zatayi miki koma take miki, ni kaina akan Auren  nan bakiga bacin ran da mukayi da ita ba, hatta harkar business da muke yanzu ta yanke ta a tskanin mu" Jalila tace "Ke Maama meye naki a ciki, da zata yimiki haka? Ranar daza'a akawoni ma bakiga yadda ta dinga muzanta Auren ba, shiyasa a tsorace nake da Auren nan" "karki damu, ki kwantar da hankalinki, komai ze wuce, zataji kunya ne a gaba kaman yadda nima naji" "Haba Maama wannan wace irin magana ce, meye wani jin kunya, dan Allah kidena wannan zancen, Yawwa Maama nifa shekaranjiya Su Naja sunzo gidan nan, Jalal yasa 'yan sanda sun kama su, na tambayeshi dalili yace babu ruwana narasa ya zanyi" "rabu dasu Jalila, yaya mairo ta kirani a waya ta zageni tsaf, aina dawo daga rakiyar su, tana' yar uwata amma tana min zagon kasa da hassada a rayuwa ta, dana zauna nayi tunani dukkan shawarwarin data dinga bani a baya, tasa nake aikata wasu abubuwan turin jeka ka mutu takemin, Jalila nayi dana sanin abunda nayi miki keda mahaifiyarki tsawon shekaru, dan Allah ki yafemin" Jalila tace "Maama dan Allah ki dena wannan maganar, komai ya riga ya wuce fa" Suka cigaba da hira, Jalal yazo ya samesu yace "Maama, Abba yace ki fito ku tafi dare yayi" Har bakin mota suka rakasu, sukayi musu sallama sannan suka dawo cikin gida. Koda suka koma Jalila ta duba kayan da su Maama suka kawo mata, fruits ne da kayan chocolate, ta zuzzuba a fridge. Jalal yace "My wife zomuje muyi Adhkar mana, zan kwanta" Hararsa tayi tace "tab bazanzo ba, sedai karka yi" ta gudu dakinta, murmushi kawai yayi ya girgiza kai. Ilham fa tayi rama sosai tayi duhh saboda bacin rai, Ummanta tace zatayi wani abu akan lamarin Auren  an amma taji shiru, babu alamar samun wata baraka a Auren, ba wanda yaji kansu, dama bata ta Mummy, Mummy se aukin masifar, Amma babu wani yunkurin daukar Action da tayi, gashi wasa2 soyayya da kishin Jalal na neman ya kwantar da ita rashin lafiya, ba shiri ta shirya ta tafi gida gurin ummanta, koda taje gidan bata nan, dan haka tanemi guri ta zauna tana jiran dawowarta. Tayi kusan awa guda sannan Umman tata ta dawo, tana dawowa ta tarar da Ilham din a kwance kaman gawa, a dan tsorace tace "ke Ilham lafiya kuwa na ganki a kwance?" Ilham ta dan yatsina fuska ta tashi zaune tace "To umma ba dole ki ganni a kwance ba, Wata nawa da yun Auren Jalal amma har yanzu banga matakin da kika dauka ba, kamar ma baki damu daki dau fansar ba, kuma ni wallahi Umma nagane son gaske nake wa Jalal wallahi, ko bacci bana iyawa" Umman tace "tabdijan ashe baki da hankali, sena makeki keda son gaskiyar, kin san irin fadi tashin da nake kuwa? Har kike fadan kinfara masa son gaskiya? Kinsan me fadawa soyayya da Jalal da kikayi yake nufi? Rushewar burinmu na daukar fansa, da farko munyi sake yafada soyayya har yayi Aure, kekuma kina kokarin rusa komai da kanki, ai idan har son Gaskiya kikewa Jalal hakan yana nufin bazakiyi abunda ya dace in rama abunda uwarsa taimin ba" Ilham tace "Amma Umma ban san ya'akayi nafara son Jalal haka ba, wallahi ina sonshi, soyayyarsa bazata hana in cika miki naki burin ba amma....... Cikin tsawa ta katseta "rufemin baki wawiya kawai, tun yaushe nake jiran ganin kokarin da zakiyi hakan ya tabatta, amma ba wani katabus da kikayu, sakacinki yasa har yayi Aure, na tattara abunda nake dashi na bawa malamai amun aiki akansa daga shi har matar tasa, ba ruwana ni daukar fansa ne a gabana" "Amma umma duk abunda kikayi masa be isaba? Naga ma bashi yayi miki ba fa, fadanku keda Mummy ne meye nasa a ciki? Wallahi bazan iya dena son Jalal ba, bansan ya'akayi nafara yi masa wannan son ba, nikam zan dau matakin karshe da zanbi in mallaki Jalal" "Aikuwa abunda baze taba faruwa ba kenan, indai bazaki auri Jalal dan burina ya cika bane to wallahi babu ke ba aurensa, dan na bada damar in haukatarwa ce ta kama, a haukata shi, shaye2 ya ninka na da har se ya haukace inga yadda khadija zatayi" Ilham tayi murmushi tace "Ayya umma kin riga kin makara wallahi, yadda kikace bazan samu Jalal ba indai ba burinki ne ze cika ba, kema ina miki Albishir da cewa indai yana tareda wannan mayyar yarinyar, babu me iya cutar dashi, tunda akayi Auren nake kasa kunne amma babu wanda yaji kansu, na ziga Mummy har na gaji amma babu wani kwakwkwaran mataki data dauka, Umma wallahi na gaji sannan na karaya, mu zubar da makamanmu tun........ "Ke rufemin baki, ko in tattakaki, bana yafiya, ko zan yafe komai banda cin Amanar da khadija tayi min, in kin gaji ki kyaleni ni zan karasa aikina da kaina" Ilham tace "kiyi hakuri Umma, zan cigaba da tayaki Allah ya cika mana burinmu, Sannan zanyi kokarin na cire shi a raina, inyi tunanin yadda burinki ze cika" Saudat ta rungume Ilham tace "Yawwa yar halak, haka nake son ji" Ilham kam goge hawaye tayi dan tasan babu ta inda zata dena son Jalal. Yaya mairo sam hankalinta yaki kwanciya, tayi zarya station harta gaji amma anki bata Sa'adah, ita kuma Sa'adah taki fadar inda Hannah take, wanke kafa tayi ta tafi gidan su Jalal. Bayan taje sun gaisa da Mummy, yaya mairo tace "Dan Allah zuwa nayi in nemi Alfarma, kisa baki danki yasa a sakar min yarinya ya, daga zuwa gidansa yasa an kamata, wai seta fito da wata, kuma tace bata san inda take ba, amma yayi mirsisi yaki sawa a saketa, naso inje gidan nasa da kaina amma ina tsoron karnima a kamani " Mummy tace "to ni mekike so inyi? Ina yarinyar ku yake Aure kije kisa ta saka shi a saketa mana, tunda yana jin maganar ta fiye dani" Kuka Yaya mairo ta saka "wallahi ni bani da wata alaka da wannan yarinyar, dan Allah kisa a sakarmin ita ko bacci bana iyawa wallahi" Tausayi Yaya mairo tabata dan haka A dan wulakance Mummy ta dauki wayarta ta kira Jalal Seda ta kira sau kusan uku sannan ya daga, daya daga ma shiru yayi bece komai ba Mummy tace "Jalal kana jina?" "ina jinki mana, meye faru?" Girgiza masa kai Jalila tayi muryarta kasa2 tace "greet her, Ka gaisheta mana" Kamar wanda akayiwa dole yace "barka da yamma" Kasa magana Mummy tayi, anya kuwa Jalal ne? Mummy tace "Jalal ne?" "wai baki san wa kika kira bane?" "A'a ina son tabattarwa ne, nace yarinyar daka sa aka kama, 'yar uwar Jawwad ga mamanta anan tana Kuka, ina neman Alfarma dan Allah a saki yarinyar nan" "bani da wani abu dazan miki alfarmarsa, ita kuma ki gaya mata hawaye yanzu ta fara, seta zubar da hawaye kwatankwacin wanda tasa Matata ta zubar saboda abunda suka dinga yi mata itada yaranta, koma yafi hakan,' yarta kuma baza' a sake ta ba setayi abunda nace, Hope i make myself clear" Daskarewa Mummy tayi a zaune, Jalal kuma ya kashe wayarsa, Jalila kaman zatayi kuka tace "Jalal abun nan dakake yi, jamin bakin jini kake da tsana a gurin 'yan uwanka da sauran mutane, kuma be kamata ka kasa yiwa Mummy Alfarma ba dan Allah komai ya wuce mana" "inkowa ya tsaneki ni ina sonki ai, sannan  komai baze wuce ba Jalila, Mummy ce silar duk wata mummunar rayuwa danayi, muka rayu cikin damuwa da bakin ciki saboda son zuciyarta, Jalila ban taba tunanin haske ze kuma shigowa ratuwata ba se bayan da kika jajirce a kaina, ko iya kulawar nan da kike bani nasan nasamu sassaucin rayuwa dana fidda ran samu, ki zauna kiyi hira dani, ki bani Abinci, ki saurari damuwa ta, idan raina ya baci ki rarrasheni, wani lokacin kina bani kulawa kaman da da uwa, tun bayan lalacewa ta na rasa wannan kulawar a gurin mahaifiyata da al'umma, wace Alfarma zata nema a gurina inyi mata? " Kwalla ta taru a idonsa, da alama baya son tuna abubuwan da suka faru, ta kai hannu ta shafa sajensa tace "Jalal, kowane dan adam kaddararsa a rubuce take kafin a haifeshi, dama can Allah ya kaddara you must go through that situation, koda Mummy ko babu sekayi wannan rayuwar, idan kayi hakuri ka bata matsayinta na uwa, se Allah ya yafe maka kaima, please Jalal forgive your Mum " " ki kyaleni da maganar Mummyn nan senayi tunani" Kara marairaicewa tayi tace "please Jalal" Dan hararta yayi yace "Jalal ko?" Murmushi tayi tace "Yaya Jalal" "niba na son wani Yaya Jalal gaskiya, i calls you with different love names, please dukda bani kike so ba, ki dan dinga kirana da suna me dadi nima inji dadi" Shiruu tayi ba tace komai ba, kasancewar a kwance yake akan cinyarta yasa ya juyo fuskarta tana kallonsa, dan motsa baki tayi amma ta yi shiru Jalal Yace "Nasan bani kikeso ba, akwai wanda kike so banina ba, kina tausayina ne kawai, Amma please ki gayamin abunda zanji dadi" Hannu tasa ta Dan shafa sumar kansa tace "idan nace ZAUJEE yayi?" Lumshe ido yayi tareda yin murmushi ya maimaita "ZAUJEE, you mean your husband?" Jinjina masa kai tayi alamar Eh Jinjina kai yayi yai murmushi yace "I like the Name kwailata" Ture kansa tayi tace "dagani tunda kacemin kwaila" Dariya yayi yace "ba zan tashi ba din ai keda cinyar duk nawane, ki shirya nan da next week Insha Allah Daddy ze dawo zamu je gida" Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724    🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 5️⃣6️⃣109 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724       Happy marriage lyf to you sister Amina, may yours be among the best.                 _MY FIRST NOVEL _ Mmurmushi Jalila tayi tace "Masha Allah naji dadi gaskiya, dama bana zuwa ko'ina daga makaranta se gida, gashi an gayyaceni biki 'yar class dinmu bansaniba ko zaka barni inje?" Dan hade rai yayi yai mata shiru, Tace "Kace wani abu mana" "gaskiya bazaki ba" yaba ta amsa A shagwabe tace "meyasa?" Jalal yace "har yanzu baki kama da me Aure ba, kawai kifita wani ya biyoki no gaskiya ki hakura" Kara marairacewa tayi tace "please, Allah tunda nazo gidan nan school kawai nake zuwa, dan Allah ka barni inje" Makale kafada yayi "yace ni dai A'a" Ya kalli cikin idonta yace "Allah me yadda yaso, Baby da dane nace karki fita ko kallona bazakiyi ba, ko baki niyya ba sekin fita dan ki ban haushi ko?" Shiru tayi ba tace komai ba Jalal yace "naji zakije, amma ni zan rakaki kiyi minti goma mu dawo, dan bazaki dade ba, kar inje wani ya kalleki koma wani ya biyoki yace yana so, tunda har yanzu baki gama amsa sunan matar Aure ba" Dan kallonsa tayi tace "saboda me? A gaban mutane fa aka daura min Aure" "eh nasani mana an daura miki Aure, har kikace ba kya son mijin da'aka baki, Amma ai bakiyi daya karatun ba daze maida ke matar Aure, ina da dauriya ko Jalila? Akwai dalilina dayasa na kyaleki kike cin karenki ba babbaka, ina jiran time ne" Yai maganar yana kashe mata ido daya, sarai Jalila ta gane meyake nufi Amma ta maze tace "karatu kuma? Wane irin karatu ne kuma haka?" Jalal yace "Au baki gane karatun da nake nufi ba?" Mikewa yayi zaune yace "bari in fara karanta miki kozaki gane" Ai zumbur ta mike tsaye ta fice daga dakin, Ba karamin dariya Jalal yayi ba yana son ya zolayeta a irin haka yaga yadda fuskarta ke bayyanar da tsoro" A zaman su Jalila ta gama fuskantar waye Jalal, mutum ne me matukar son a damu da shi, kulawa take bashi ba ta musamman dan kamar karamin yaro haka yake wani lokacin, ko Abinci ta kawo masa indai bata zauna ta bashi ba, ko ta zauna yana ci suna hira ba baze ci Abincin ba, sannan cikin hikima take canza masa wasu munanan dabi'un nasa zuwa kyawawa, ta tsaya tsayin daka akan kula da ibadar sa da kuma Adduo'i, kulawar da yarasa ce a baya ta taimaka gurin kara dulmiyashi harkar shaye2, Mummy harkar kasuwancinta da son zuciya tasaka a gaba, yayinda Daddy ba mazauni bane, Jawwad kuma ga makaranta ga sauran hidimominsa dukda ya taka mahimmiyar rawa a gurin Jalal, ga kyama da al'umma suke nuna masa saboda yanayi na shaye2 da sauran dabi'unsa, shiyasa abun yayi masa yawa, babu me jansa a jiki yaji matsalolinsa kome yake damun shi, wata shakuwa ce ta musamman ke kara shiga tsakaninsu. Bangaren Jalal ma babu Abunda ze cewa Allah se godiya, dan ya fidda ran yin kyakywar rayuwa kaman kowa, Amma ba zato ba tsammani dawowar Jalila karo na biyu a cikin Rayuwarsa tazo masa da Haske da tausayawa, a cikin rayuwar Auren nan nasu, dukda kasancewar a baya basa jituwa, Amma ta ajiye wannan a gefe tana ta iya kokarinta a kansa, tana masa biyayya dai2 iyawarta, duk wanda yasan irin rayuwar takun sakar da sukayi a baya, babu me cewa zata iyayiwa Jalal biyayya haka, musamman wanda yasan halinta a bangaren tsiwa da rashin daukar raini, tana zama tayi hira da shi, tai masa nasiha, idan abu ya dameshi ta rarrasheshi hakan ya mantar da Jalal duk wata mummunar rayuwar da yayi a baya. Tun Yaya mairo tana sintirin zuwa gidansu Jalal akan maganar sa'adah harta gaji ta hakura saboda korar wulakancin da Mummy tayi mata a cewarta "ta gaji da zaryar da take mata a gida suje can su daidaita" Ba yadda ta iya haka ta tafi gidan Maama kozata sa baki a sakar mata sa'adah, dan yanzu ko zuwa tayi police station ba'a bari ta ganta, ta kwashe duk yadda akayi ta fadawa Maama, Maama tace "to ni Yaya mairo ya kike so inyi?" Yaya mairo tace "Dan Allah zainab kisa baki, yarinyar nan Jalila ta gaya masa yasa a sakarmin 'ya ta dan Allah" Maama tace "Yaya mairo idan mukayi haka ai bamu da kunya kenan, ko kin manta irin cin zarafin da kikasa muka hadu muka dingayi mata? Se yanzu zamu nemi Alfarma a gurinta?" Yaya mairo tace "Dan Allah zainab ni dai ki roketa a sakarmin sa'adah, wallahi yaron  nan da yake ba dan mutunci bane, mahaifiyarsa tana rokonsa a sakarmin sa'adah se cewa yayi, se nayi hawaye fiye da wanda matarsa tayi" Maama tace "gaskiya Yaya bazan iya tunkarar Jalila da wannan maganar ba" Abba ne ya shigo gidan ya tarar da yaya mairo a parlour suna hira, Yaya mairo na gaisheshi be amsa ba yace "zainab ban gaya miki bana bukatar sake ganin yayarki a gidana ba? Ban hanaku zumunci ba, amma ku hadu a wani gurin, dan bazata dinga zuwa tana rarrabamin kan iyalai ba" Abba ya dubi Yaya mairo yace "dan Allah karki kara zuwarmin gida, in bahaka ba zan dau mummunana mataki akanki, ki tashi ki tafi" Yaya mairo tace "zainab kina kallo mijinki na cimin mutunci?" Maama tace "ba cimiki mutunci yake ba, maganar gaskiya ne ai, tunda yace ki bar masa gida kawai ki tafi" Haka Yaya mairo ta fito tana rusa kuka, ta koma gida ta rasa abunda yake mata dadi, ga Naja ma kwanan ta uku bata gida, ta kirata a waya tace mata "karta kara kiranta tana cikin koshin lafiya" Sa'adah kam da taji uwar bari tuni ta fadi inda za'a samu Hannah, akayi nasara kuwa 'yan sanda sukaje itama suka kamota amma ba' a saki sa'adah ba ma. Jalila ta gama shirinta tsaf na zuwa gurin biki, ta dakko Jakarta ta fito, tana fitowa Jalal ma ya fito, ya sanya shadda coffee color, kansa ba hula, ya taje sumarsa ta sha mai, se kyalli take, ga kamshin turarensa ya cika gurin yana kokarin daura wrist watch, Jalila ta kare masa kallo tace "wow looking so masha Allah" dagowa yayi ya kalleta yana murmushi, karasowa tayi ta karbi agogon ta saka masa, ta shiga daki ta dakko masa hula, tasaka masa sannan tace "kafi kyau da hula, bari inyi maka hoto" Jalal yace "gaskiya sekin biya zakimin hoton" Jalila tace "danma zan saka a wayata shine sena biya? To an fasa" Dariya yayi yace "hmm ni hotonki a wayata sunkusa dubu, nikuma ko daya nasan baki da shi, bakomai nidai ina sonki my wife" Jalila ta dan harareshi tace "ina ka samu hotona har kusan dubun?" "kina mamaki ne? In mun dawo zan nuna miki" "to shikenan Allah ya kaimu mu da wo din" Ta dinga daukarsa hoto, seda sukaci lokaci suna wannan hotunan, sannan sukayi nufin fita, Jalila ta kuma kare masa kallo daga sama har kasa, ta tuna lokacin da yake kan ganiyar shaye2, irin shigar daya keyi, yadda yake magana ga rashin fara'a, ta kalleshi yanzu a hankali ta furata "Alhamdilillah ' Jalal yace "lafiya kuwa kike min kallon kurilla, kinsan fa bana son kallo?" Dan murguda masa baki tayi tace "Sena kalla din in yaso a dau mataki" "haka kikace ko? Zan dau mataki kuwa" Ta dan laankwasar da kai tace "kayi kyau sosai, kaman karmu fita a ganka" Da sauri ya kalleta yace "do you really mean what you said? kina kishina kenan?" Dan tabe baki tayi tace "hmm to maybe, Amma kaman ba yau nafara kishinka ba, To ban saniba ko kishin ne koba shi bane" Wata ajiyar zuciya ya sauke yai murmushi yace "shikenan muje karki makara, dan 10 minutes kawai zamuyi kuma zamu dan tsaya a wani guri" Haka suka jera gwanin sha'awa, ya bude mata gaban mota ta shiga sannan ya kunna motar suka fice. Befi mintuna shabiyar da tafiyarsu ba Ilham tazo gidan, amma me gadi ya sheda mata cewar "masu gidan yanzun nan suka fita" Ilham Tace "megidan shi dawa suka fita"? Megadi yace "shida matarsa mana, da alama wani gurin zasu je" Ilham tace "basu gaya maka ina suka tafi ba?" A fusace yace "ke ko dai 'yar leken asiri ce ke? Nace miki sunfita ubansu ne ni da se sun gayamin ina zasu" Haka Ilham ta koma gida gwiwa ba kwari. Koda sukaje gurin biki kallo yakoma kansu, sunyi kyau sosai, a table daya suka zauna itads Jalal,' yan makarantarsu sukazo suka gaisa, dayake a cikin kawayen Jalila Jalal yafi sanin Zahra ya dan fi sakin jiki da ita, tunda yanzuma kokari yake yana gaisawa da kawayen nata dan kar yayiwa Jalila laifi, bayason taro kuma befiye sakewa da mutane ba, Zahra tace "Jalila gaskiya ya kamata ayi muku hotuna kaman a saceku a gudu" zahra taita zolayarsu, nan ma hotunan suka sha, maman amaryar tazo wucewa ta tsaya suka gaisa, Jalal yai mata alheri, Jalal kenan zuma ga zaki ga harbi. Seda sukayi kusan awa biyu a gurin, ya bar Jalila ta sake a cikin kawayenta, dan kanta tace ya tashi su tafi gida. Seda Jalal yafara biyawa ta police station tukuna, suna zuwa suka tarar da Yaya mairo a gurin tana magiyar a barta taga Sa'adah, Jalal kota kanta bebi ba, yayinda Jalila ta gaisheta Yaya mairo cikin kuka tace "na gamaki da girman rabbil izzati ki cewa mijinki ko ganin Sa'adah a barni inyi, ina cikin damuwa wallahi" Jalila ta dafa Yaya mairo tace "kiyi hakuri Yaya mairo, insha Allah za'a saketa yau din nan ki dena kuka, zesa a saketa" Jalal daya ga yadda Jalila ke rarrashin Yaya mairo ji yayi kaman ya maketa, wani lokacin halinta daya da Jawwad, komai girman laifin da kayi musu basa riko, ya tuna cin mutuncin da Yaya mairo tai mata a baya, Amma yanzu se lallabata take yi. Jalal ya gaisa da 'yan sanda cikin girmamawa sannnan D. P. O yai umarnin a kawo masa su Sa'adah, Sa' adah tayi baki kirin ga waga muguwar rama da tayi se uban hakora, Ga Hannah itama har dan gwara Hannah akan sa'adah, seda Jalila ta tsorata da ganin ta. Hannah seda ta sandare dan mamaki, Jalal ne a cikin wannan shigar manyan kaya na alfarma, yazama wannan kamilin haka? Gefensa ga matarsa Jalila, yarinyar da tafi tsana, lallai Jalila kwararriya ce gurin makirci, tai musu makirci itada Ilham ta aure Jalal Jalal yace "Yallabai wannan itace Hannah, ina son a auna ta a tabattar da tanada ciki? Idan tana da shi seta haifeshi ta shayar da shi ta raineshi inya shekara biyar ta bani shi, idan kuma ba ta dashi zanyi kararta a kotu ta nemomin cikina da ta zubar" Kallonsa Jalila tayi tasan rainin hankali na Jalal zatayi magana ya daga mata hannu, kuka Hannah ta farayi tace "wallahi Jalal karya nakeyi, bani da komai nayi hakane danka aureni, dan Allah karka yi min haka, zaka tozartani inkamin haka" Jalal yace "kina gudun tozarci ni kika tozartani a gurin iyayena, idan har karya kike alfarma daya zanmiki, kije dubai gurin mahaifina ki bashi hakuri ki karyata kanki" Cikin kuka tace "na shiga uku Jalal, ina naga kudin zuwa Dubai, kayi min rai dan girman Allah" Jalila ta kalli wani dan sanda tace "yallabai Sa'adah bata da lafiya ne naga ta rame sosai? Dan Allah Jalal a saki sa'adah tunda ta nuna inda Hannah take kaman bata da lafiya" Wani dan sanda yace "to kusan hakan, tana nan a tsare bata samun shan magungunan ta, ankira likita ya dubata maganinta na kanajamau da bata shane yasa yafara nunawa, amma an bata wani, sannan bazamu saketa ba saboda ta hada kai da wannan kawar tata Hannah sun damfari wani Alhaji makudan kudade, dan haka zamu gurfanar da su a kotu" Ba Jalila ba hatta Jalal da Yaya mairo seda suka sandare a gurin, Yaya mairo ta dora hannu aka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, sa'adah maganin da kike sha tsawon shekaru kikecemin na gyaran jikine dama na wannan cutar ne, Allah ya wadaranki Sa'adah ni Allah yasa baki gogamin ba bansaniba, abun naki hada damfara kai Allah ya wadaranku wallahi banyu dace ba nikam, daga ke har kanwarki da dan uwanku bana zabe, dan uwanku na prison saboda sata, ke karuwanci da damfara, kanwarki shaye2 da karuwanci nashiga uku ni mairo, Allah ya tsinemuku gaba dayanku 'ya' yan jaraba" Jalila tuni fuskarata ta jike da hawaye tace "kidena wannan maganar Yaya mairo, sannan kai kuma officer, this is confidential you don't need to expose her like this baka kyauta ba" Jalal ba kunya ya rungumo matarsa a gaban mutane yana goge mata hawaye yace "Haba Jalila kidena kuka mana, Allah ne ya saka miki, ke da'akewa gori Ana cewa tubabbiya ce mahaifiyarki ke gashi Allah yayi ki shiryayiya, SU da suke ikrarin an haifesu a musulinci, kalli yadda suka kare, musulincin nasu a bakine, mu tafi gida kidena kuka " Jalal yace" Yallabai zan dawo Insha Allah " Sa'adah ta sunkuyar da kanta tana zubda hawaye, aka tasa keyarsu aka mayar dasu ceil Sukayi sallama yasa Jalila a mota se gida. Da sukaje gidan ma taki walwalwala, duk abun duniya ya dameta, wayarta ta dauka ta hau online aikuwa tai sa'a Nana ma tana online suka dinga chatting Jalila ta Gaya mata abunda ya faru Nana tace "Alhamdilillah ai dama sharri dan aikene, tayi ya kuma koma kanta" Jalila tace "A'a Nana, a duk lokacin da musiba ta fada kan wani be kamata muyi murna ba musamman mata, duk abunda yasamu mace raguwar muce" Nana tace  "rayuwar su dai dan bandani, Allah ne yakamasu wallahi naji dadi kuma, dan sun dade suna zige Maama, yanzu naga ta bakin zagin 'ya' yan wasu" Jalal na zuwa ya karbe wayarta yaga da Nana take chatting voice message ya turawa Nana yace "Nana ki kyaleta ta zauna ta damu kanta akan wannan mutanen, ki mata fada kema, ki gaida su Mahmud da Anty Salma" Ita dai Jalila kallonsa kawai takeyi Ya ajiye wayar ya zauna kusa da ita ya bude system dinshi, ya shiga wata folder ya mika mata system din, dan zare ido tayi, dan kuwa hotunan tane kawai a folder sun kusa dubu kaman yadda ya fada tun daga na jariran taka har iyanzu, mamakine ya kamata, dan wasu hotunan nata bata taba tunanin sunfita daga wayarta ba tace "Jalal ya'akayi ka tara wannan hotunan nawa haka?" Dan hade rai yayi yace "Jalal ko?" "ohh sorry Zaujeee" ta fada tana murmushi Ya dan gyara zama yace "wasu hotunan naki tun kina gurin Ummi, wanda na nunamiki ne a gadon kaya, wasu hotunan kuma Hanan ce take turomin, Hanan ta dade tana supporting dina akanki, wasu a wayar Jawwad nake turawa be sani ba, ta saki ta turamata hotuna nikuma tana turomin" Bude baki Jalila tayi tace "Amma gaskiya Hanan bata da kunya, ashe an dade ana yaudara ta, inta antaya mata hotuna na tana tura maka, wayace ka kalleni ba mayafi a lokacin?" Tai maganar tana yamutse masa fuska kaman yarinya karama. Jalal yace "Abunda yasa nake kallonki yanzu ba mayafi shine yasani ake turomin hotunanki ba mayafi nake kalla" "mekenan?" ta tambayeshi "So mana" ya bata amsa, ya dora da cewa "Jalila kaman kina tantama akan son da nake mikine, tun a wancan lokacin da nayi kokarin in cire sonki daga raina ganin hankalinki yana kan Jawwad, Amma duk sanda nayi yunkurin yin hakan se inji ina kara azabtar da zuciya tane, Jalila so mugun ciwone, haduwar da mukayi sanda kikazo kano, nasaka miki wasika a cikin cover Al'qur"ani, amma bana tunanin kin gani, Jalila lokacin dana ganki da Ahmad seda naji kaman in kashe kaina saboda kishi, ko yan kwanaki nayi ban ganki ba sena shiga damuwa, dukda in muka hadu bawani abun arziki da ke hadamu" Ya kalleta ya dan murmusa yace "kinsan wataran Jawwad ya sha kamani ina kallon hotunan ki? Na maze na hade rai sedai ya kalleni ya kyaleni kawai, kwana biyu na hanashi taba wayata, abunda banayi a baya, ya dau wayar yaga na saka password yana saka sunaki ta bude, wallpaper na hotonki ne da mukayi a gurin birthday dina, aikuwa ya ritsani da tambayoyi, seda na tabattar masa dani har yanzu wannan soyayya da nake miki a baya tana nan, Amma kar ya gayawa kowa, shine yace ze shigemin gaba Indai Aurenki ze sani farinciki, Jalila na dade ina azabtuwa da soyayyarki " Ya kwanta a jikinta yace " please Jalila karki rabu dani, ko da ba kyasona ki cigaba da jin tausayi na dan Allah, ko iya tausayinne, nasan watakila watarn tausayin yakoma soyayya, nikam Soyayyar da Umminki tayimin da sadaukarwa da kikayimin, bazata taba bari in cutar dake ba Jalila, Ina sonki my wife ko baki soni ba dan Allah kiyi hakuri zama dani, kinfi kowa sanin halina da fuskantar abunda nake so ciki harda mahaifiyata, ina sonki" Hannu tasa tana shafa gashin kansa, tausayinsa duk ya mamaye jinkinta, ta kasa magana, shi kuma yayi lamo a jikinta kaman maraya Jalal Yace "Gobe in Allah ya kaimu zaki tafi da kayanki, Munyi magana da Abba yace zakuje bauchi da Maama tunda kunyi hutun makaranta, nima zan koma lagos zan cigaba da aikina Insha Allah, amma sati biyu zanyi kawai in dawo, sannan in kun tafi bauchi karki kirani a waya, sedai in nina kiraki" "But why?" "haka nan kawai, zakiji dalilin hakan amma, zanyi missing dinki sosai Baby gaskiya transfer zan nema, in ba hakaba damuwa zata min yawa" Jalila tace "kanemi zabin Allah kafin ka nemi transfer din nan Allah ya zaba abunda yafi Alkhairi" "zamana a kusa dake shine mafi Alkhairin ai" Tacigaba da shafa kansa a hankali tana tunani daban daban a ranta. Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 5️⃣7️⃣110 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                     _MY FIRST NOVEL _ Washegari tun safe Jalila take shiri tana murnar zata je gida, gefe guda tana tunanin in taje dole ne taje ta gaida iyayen Jalal, ko wane tarba Mummy zatayi mata oho? Ga abunda ya faru da su Sa'adah har yanzu abun yana damun ta sosai, karfe goma na safe ta kammala shiryawa tsaf, ta hada kayanta, tun dare ta hadawa Jalal nasa kayan shima wanda zeyi tafiya dasu Lagos. Jalal ma ya fito tsaf da shi, Jalila ta kulle ko ina, Jalal kuma yafita da akwatunan su, a mota taje ta tarar da shi ita kawai yake jira, ta bude ta shiga ta zauna, ya kalleta yace "Baby ya dai naga duk jikinki a sanyaye?" "bakomai fa" ta bashi amsa "shikenan tunda bazaki gayamin ba" Ya kunna motar suka tafi, koda yaje unguwar su yayi parking kin fitowa tayi daga motar, ya kalleta yace "Fito mana, ni nakasa gane meyake damunki ne?" Jiki ba kwari ta fito daga motar, Jalal yace "muje in gaida su Abba, daga baya sekije ki gaida Daddy" jinjina masa kai kawai tayi tabi shi, suna shiga cikin gidan kofar parloun a rufe take, Jalila ta dakko wayarta ta kira Maama, bugu daya Maama ta dauka Jalila tace "Maama ina kika tafine, ina gida amma kofan parlor a rufe" Maama tace "ya salam, ai ban dauka da wuri zakuzo ba, kinga mun dan fita da Abba ne, yanzun nan zamu dawo insha Allah" "shikenan se kun dawo" ta kashe wayar ta kalli Jalal tace "basa nan wai yanzu zasu dawo" Jalal yace "shikenan zomuje gida seki jira su" Dan shiru Jalila tayi tana kallon Jalal. "kina tsoron Mummy ne? Karki damu ba abunda ze faru muna tare, muje" Jiki a sanyaye tabi bayansa danji take kaman tace bazata ba, tasan bazeji dadi ba idan tayi hakan, gabanta nata faduwa tana karanta addu'oi daban2, tun daga harabar gidan har cikin parlor ba kowa part din daddy ya nufa tana biye da shi, suna shiga suka tarar da Daddy na zaune na kallon labarai su Jalal sukayi sallama, ya amsa tare da waigowa, yana ganin su ya fadada murmushinsa tare da dan bude baki, ganin Yadda Jalal yazama wani babban mutum. Jalal yana zuwa ya zauna kusa da Daddy, yayin da Jalila ta zube a gurin tana gaida Daddy, Daddy yace "Haba Jalila zauna mana semu gaisa, yazaki zauna a kasa" Cike da kunya da girmamawa Jalila ta dan zauna tana kuma gaida Daddy, ya amsa mata yana tambayarta ya gida. bayan sun gama gaisawa da Daddy ne Jalal ya dan risina  yace "barka da warhaka father, ya hanya?" Daddy yace "lafiya kalau, ya gidan naka kuma? Ya 'yartawa take? " "lafiya kalau, ba gata nan kana gani tana lafiya ba" Daddy yai murmushi dan tabbas inka kallesu zaka gane suna cikin farinciki Suka zauna sukayi ta hira da Daddy, Jalila se kunya takeji tana sunkuyar da kai, yayinda Jalal kam se zuba yake yana hira, daddy yaji dadin ganin Jalal, yadda yake magana yanzu ya sha banban da yadda yake yi da babu respect a maganganunsa a baya cikin gadara yake yinsu, amma yanzu gashi yasaki jiki yana hira babu hade rai da masifa. Daddy yace "gaskiya Son naji dadin ganinka, kaga yadda kayi kiba kuwa, ka wani zama babban mutum" Jalal ya kalli kansa yace "Allah Daddy thank God, and thank my wife efforts, she's behind the changes you saw on me, behind any successful man their must be a woman, da baku aura min ita ba ban san ya zanyi ba" Jalila ji tayi kaman kasa ta tsage ta shige dan kunya, daddy yace "tabbas Jalal matarka ta cancanci yabo da godiya, ubangiji Allah ya kara hada kanku, ya wanzar da zaman lafiya da kaunar juna a tsakaninku, Allah yasaka miki da alkhairi Jalila" Jalila ba tace komai ba, Jalal yace "Ameen ya Allah Daddy" Jalila tace "Daddy ina Mummy ne?" "bata jin dadi ne, ta sha magani ta kwanta bacci" Jalila tace "Daddy meyasa meta?" "kawai dai jikin nata ne bata jin dadi, gashi bata son zuwa Asibiti, likita yazo ya duba ta yabata magani" "Allah ya bata lafiya" Daddy yace "Ameen" yayin da Jalal ya basar kaman besan zancen da suke ba. Daddy yace "to nima zan dan fita ne, inada meeting dazan shiga karfe daya" Jalal yace "shikenan Daddy seka dawo, nima daga nan karfe hudu Insha Allah zanbi jirgi zan koma Lagos" Daddy yace "to Allah ya kaika lafiya, kafin in koma zan biyo ta Lagos din in ganka" Sukayi Sallama da Daddy ya shirya ya fita. Babban parlor suka dawo suka zauna suka cigaba da hirarsu kaman a gidansu dayake babu kowa a parlor. Jalal ya kalli Jalila yace "nifa yunwa nakeji" Dan zare ido tayi tana kallonsa "yunwa kuma? A yanzun"? "Eh ni yunwa nakeji" Jalila tace "to yanzu meye abunyi ga mutan gidan basa nan? Gashi ban fito da komai naci ba tunda ka zama jariri" Murmushi yayi yace "tashi muje kitchen mu duba seki dafa mana wani abun" Jalila tace "kana ganin babu matsala idan mukayi hakan?" Jalal yace "matsala kuma? Tashi muje ba wata matsala" Ta mike suka tafi kitchen. Ilham juyi take kawai akan gado, tarasa me zatayi taji dadi a ranta, tunda Jalal yayu aure ko bisa kuskure basu hadu da Jalal ba, gashi kaman masifa haka wutar son Jalal ke ruruwa a zuciyar ta ba dare ba rana, gaba daya ta rame tayi baki, idan ta tuna artabun da suka dingayi da Jalila a baya akan Jalal ta tuna yanzu ita ya aura, kuma har yake gaya mata wai yana son matarsa, setaji duniyar ta kara mata zafi taji kaman ta samu wuka taje gidan ta kashe Jalila, gashi yanzu fafutukar Ummanta akan ta dauki fansa ne kawai, gashi ta gaji da zigar da takeyiwa Mummy, ga ciwon so na neman halaka ta, ko Abincin kirki bata iya ci, bata taba zaton radadin ciwon so ya kai haka ba, ko da wasa batayi tunanin son Jalal ze juye ya koma mata gaske ba, ta yanke shawarar zuwa gidansu yaseera taji wace shawara zata bata, yunwa ta isheta dan haka ta sakko daga kan gadon dan neman abunda zata zubawa cikin ta. Kunun gyada Jalal yasa ta dama masa, ta soya masa irish potatoes, ta zuba sugar da madara ta na juya masa, yasa hannu ya karba, Jalila tace "kai zaujee se'a zata bana baka Abinci ai kabari ya huce in ka sha zaka kona baki ne" A dan shagwabe Jalal yace "ai ba kya bani in koshi duk na rame" "A hakan ne ka rame, kalli ka fara tumbi fa kalli kumatunka ma" Dariya yayi ya shafa cikinsa yace "bafa wata yunwa nake ji ba, kawai zanyi missing delicious food dinki, shiyasa nake so inci kafin in tafi" Murmushi tayi ta juya tana gyara gurin da ta bata tana tattarw kwanukan. Ilham da kusan mintunan ta biyar a tsaye a kofar kitchen din ba tareda sun san tana gurin ba, taka sa daga Koda karamin yatsanta, sedai ji da tayi kaman an kunna gobara a kirjinta. Abun mamaki Jalal se dariya yake shida matarsa, cike da kulawa, yasha kayansa na mutunci sabanin a baya,wanda ganin dariyar Jalal seka shafe wata baka ga yayi dariya ko sau daya ba. Jalal ya dau cup din kunun ya kai bakinsa, aiko yana sha ya  kona harshe saboda akwai zafi sosai, aje kofin yayi yana rintse ido, tareda zukar iska cikin bakinsa. da sauri Jalila ta juyo Tace "subhanallah sannu wai sha kayi?, dama na Gaya maka da zafi fa amma ka sha a haka" Janyota yayi da sauri ya hade bakinsu ya fara kissing dinta, Jalila ta tsorata sosai gaba daya jikinta yake rawa, sunyi kusan three minutes a haka sannan ya cikata ta ja da baya tana zare ido kaman mara gaskiya, ya dan kashe mata ido ya juya ya nufi fridge ze bude  ya hangi Ilham ta gefen idonsa, a kofar kitchen tana hawaye basarwa yayi ya dau ruwa a fridge ya sha, ya janyo kujera dake dining din kitchen din ya zauna. Kallon Jalila yayi ya ga yadda take rarraba ido kaman wadda aka kama tana aikata wani zunibi, ya dan kashe mata ido yace "inkin gama zare idon kizo ki bani Abinci, lokaci yana kurewa, zanje inyi salla inyi haramar tafiya" Kan table din dake gabansa ta aje Abincin, tana debo kuna tana hurawa tana bashi a baki. Ilham da tayi kaman ta juya ta fasa shiga kitchen din, amma ta dake ta shiga, ko kallon inda suke batayi ba, suma basu kulata ba, Jalila ce tace "Ilham ya kike ya gida, ranar me gadi yace kinje bama nan" Wata uwar harara Ilham ta jefawa Jalila tare da jan uban tsaki, ita kuma Jalila tayi kaman bata gani ba, ta cigaba da bawa Jalal Abinci. Jalal yace "Baby badan nayi sauri nai kissing dinki ba, da tuni harshena ya kone gaba daya" Dan murguda baki Jalila tayi tace "seda na gaya maka da zafi ai amma ka sha da zafin" "na matsu in sha ne shiyasa" "ai gashi nan ka kone, kayi shiru kuma karka kware dai" Shiru yayi yaci gaba da karbar Abinci kaman wani karamin yaro, yayinda Ilham keta kokawa da tukunya tana kokarin dora tukunya amma tarasa ta ina zata fara dora tukunyar saboda bakin ciki, kafarta se rawa take, saboda wani azababben kishi da taji yana taso mata. Jalal kaman ba kowa a gurin haka ya cigaba dayiwa Jalila shagwaba tana bashi Abinci har ya gama ci. Jalila ta kalleshi tace "dan Allah meyasa kace in ka tafi kar in kira ka for two weeks"? Dan murmushi yayi yace "inda zanje aiki babu network ko kin kira baze shiga ba" A shagwabe tace "Amma meyasa?" Kafin yayi magana Ilham ta jefowa Jalila tukunyar dake hannun ta, da sauri Jalila ta rike Jalal tana fadin "subhanallah" huci Ilham takeyi tana kuka tare da fadin "Allah ya isa ban yafe miki ba, wallahi sekinga abunda zanyi miki, sena hanaki sukuni da jin dadin rayuwa makira Azzaluma, kika dinga nuna ba wanda kika tsana sama da Jalal dan mugunta kin aure shi, wallahi ciwon son Jalal baze kasheni ba sekin dandani abunda nakeji" Ta kuma rarumo food flask ta jefowa Jalila, da sauri Jalila ta shige bayan Jalal ta rirrike shi. A fusace Jalal yace "ke wace irin mahaukaciya ce haka? Wallahi kika illatamin mata se na daureki" Daga bayan Jalal, Jalila tayiwa Ilham wani irn gwalo passionately tareda kashe ido cike da neman tsokana tace "ni nace miki na tsaneshi? in ma na fada a da yanzu na janye" Wani farinciki ne ya ratsa zuciyar Jalal tundaga sama har kasa da jin abunda Jalila ta fada akansa. Hannun ta ya rike suka fice suka bar mata kitchen din. Jalal yace "kidena biye mata dan Allah, lokaci nake jira itama seta girbi abunda ta shuka, samunki a rayuwata yafi komai dadi a rayuwa ta" Murmushi Jalila tayi tace "nikam muje in duba in Maama ta dawo, dan bazan zauna ta nakasta ni a banza ba" Jin hayaniya ne yasa Mummy ta Farka daga baccin da take ta fito dan ganin meke faruwa, tana fitowa parlor taga Jalal da Jalila yana gyara mata mayafinta, Ilham ta fito daga kitchen ido duk hawaye da katon muciya a hannun ta tana ihu tana "wallahi sena ga bayanki muguwa makira, yadda kika kunsa min bakin ciki sekin kunshi wanda yafi nawa, saboda makircin ki burin mahaifiyata be cika ba, nikuma ciwon so ya kamani ina ta azabtuwa, wallahi sena tozarta ki" "wallahi ba'a haifi 'yar da zata tozarta ni ba, ko ta wulakantani ba, kuma ni makirci ai uwarsa ce ni, nina haifeshi na yanke masa cibi, na goya shi a bayana, ke bari in gaya miki har yanzu ina nan a Jalila na da kika sanni ba abunda ya canza, kuma sedai ciwon son ya kasheki, zan bar Jalal ya auri duk macen da yake so a fadin duniya amma banda irinki, tunda na shiga baki isa ki shigoba wallahi, a baya ma bakiyi nasara ba balle yanzu" Yadda Jalila ta hakikance yafi komai yiwa Jalal dadi, In dai hakane Jalila ba yanzu ta fara sonshi ba, tunda ba yau ta fara fada saboda shi ba, Jalal yace "Baby keep quiet, kar ranki ya baci a banza" ya hade rai ya kalli Ilham, gaba daya ya koma Jalal dinsa yace "idan baki taba ta ba bakya kaunar Allah, mahaukaciya wadda bata san darajar kanta ba" "Ai babu babban mahaukaci sama da kai, bakaji kunyar yadda kake zakewa saboda mace ba, akan wannan shedaniyar yarinyar, Jalal kayi asara kaji kunya, ka fifita mace akaina, shine kake ciwa Ilham mutunci saboda kake kiranta mahaukaciya, shekara da shekaru tana sonka amma babu tausayin ta a zuciyar ka, kaje ka auri wannan me soyayyen idon" Mummy ce take kumfar baki tana masifa Wani irin murmushi na rainin hankali yayi, yayin da Jalila ta tsakure guri daya takasa cewa uffan, Jalal ya kalli Mummy yace "Inason Jalila sosai, kuma kamar yadda ta fada, tunda ta riga ta shiga babu wadda zata biyo bayan ta, wallahi ko Ilham zata haukace bazan aureta ba na tsane ta, tarihi na shirin maimaita kansa Mummy, dama nazo ne dan kiga namijin kokarin da sirikarki keyi akan danki, kuma nason kin gani sedai son zuciyar ki" "Jalal you have to watch what you are saying, Mummy ce fa, be kamata ka daga mata murya ba, balle ka fadi abunda ze bata mata rai" "Ohh Sorry dear zan gyara insha Allah" be bar Jalila ta kuma magana ba ya janyeta sukayi waje, yayinda Mummy ta daskare a gurin, Ilham kuwa dora hannu tayi a kanta tana rusa uban ihu. Suna fita Jalila tace "Jalal meyasa kakemin haka a gaban Mummy, hakan ze kara sawa ta tsaneni ne" "Jalila wallahi bazanji kunyar nuna miki soyayya ko agaban waye ba, ai ba haramun nayi ba, kuma ina so Mummy taji abunda Hajiyar Daddy taji lokacin da baya sauraren kowa se ita. "Amma ai ba kai yakamata ka yi ba, komai ya wuce ai, dan Allah Jalal ka dena yiwa Mummy haka mahaifiyarka ce fa, ita ta haifeka, ko yaya she deserves to be respected as a mother" Jalila kenan dukda abunda yake wa mahaifiyarsa yana jin dadin yadda take nuna damuwarta akan iyayensa "shikenan naji, amma bazan iya boye soyayyar da nake miki ba ko a gaban waye, muje ki dau trolley dinki, zan tafi airport yanzu" Koda ta dau trolley seda ya rakata har cikin gidan, yace shi baze shiga ba yasan yanzu suka dawo karya takura musu. Memakon ta tafi tsayawa tayi tana kallonsa Yace "ya dai, ki shiga mana" Dawowa tayi Ta dan langabe kai ta rike hannunsa tace "bakomai, Allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya, Allah ya  tsare gabanka da bayanka, Allah yabaka abunda kaje nema ya daukaka a harkar aikinka, Allah ya azirtaka da halal ya tsareka da haram, Allah ya wadata ka ya karfafi imaninka, ka kula da kanka kaji, ka dinga cin Abincinka, ka dinga adhkar da sallolinka akan lokaci kaji zaujee na" Takarasa maganar tareda dan jan dogon hancinsa, Jalal kallonta kawai yake yi, komai nata a nutse ga Addu'oi, yasan da Ilham ya aura baze taba samun haka ba. Hugging dinta yayi ya kai bakinsa daidai kunnenta yace "Ameen ya Allah, thank you very much my love, na miki Alkawarin zan kula da kaina, zanyi azkar da sallolina akan lokaci, Kema Allah ya kaiku lafiya ya dawo da ku, Alhamdilillah for having you as my wife, jin wannan Addu'oi seda ga bakin mace tagari, Allah yayi miki tukuici da gidan Aljanna" Murmushi tayi ta shafa kansa tace "Ameen Zaujee, kaje kayiwa Mummy sallama, sannan kayi hakuri kome zatayi maka, karka fadi abunda ze bata mata rai" jinjina kai yayi ya cikata, taja trolley dinta ta shige. Tana shiga ta tarar da Nana a parlor, ai da gudu suka rungume juna, Jalila tace "My Nana kece? Saukar yaushe"? "Saukar yau mana, dazu Maama sukaje suka dakkoni a airport" Kara rungume juna sukayi, Jalila tace "Maama shine baki gayamin zatazo ba" Maama tace "ai gata nan kin ganta ai" Jalila tace "Nana kinga yadda kika zama lukuta kuwa, me kikeci haka wai" Maama tace "ku zauna mana se kace kun shekara baku hadu ba" Ai basu tsaya a parlor ba suka wuce dakinsu na gidan, komai yana nan, taaf da shi ana gyara dakin, suna zuwa Nana ta cire hijjabin jikinta tace "ga abunda yasani kiba nan, se naga na zama mummuna ko Baby?" dariya Jalila ta sha cikin Nana ya fito sosai tace "Allah sarki rayuwa, kaman ba tare muke shiririta a dakin nan ba wai Nana ce da ciki, wallahi ba wani muni da kikayi, kinma fi kyau a haka" Nana tace "wallahi Habibi ma cewa yake cikin yamin kyau" Dan ya mutse fuska Jalila tayi tace "waye kuma Habibi?" "mijina mana, ko an gayamiki kowa irinkune? Ana so ana kaiwa kasuwa" Dariya Jalila tayi tace "ina wane mu, wannan abu ai se su Hajiya Nana manya, to ya Yaya Mahmud da Anty Salma? Ya kuma England da masu jajayen kunnuwa" Nana tace "suna lafiya, wannan tambayoyi haka" Jalila tai murmushi tace "masha Allah, Nana cikin nan da nauyi kuwa, wallahi yayi miki kyau sosai?" Hararta Nana tayi tace "ki bari in yazo kanki seki ji" Haka Jalila taita tsokanar Nana, Abba yayi murna ganin yadda yaga Yaran nasa kowacce cikin nutsuwarta. Da daddare ma hira sukaita yi, Jalila ta kunna data taga Jalal online, nan ta manta da batun Nana suka dinga chatting da Jalal har Nana tayi bacci Jalila ta turawa Jalal "bakajin baccine?" "banaji, nakasa baccin ma gaba daya?" "me yasa?" "Am missing your body warm, that make me fall asleep" "hmm, Performe Ablution, recite qur'an, and hug your pillow, goodnight 😘" Murmushi ya dinga yi,  ya duba agogonsa karfe biyu da rabi na dare, ya tura mata "ni kike cewa in rungume pillow ko? Zan kamaki ne, let's meet in your dreams" ya rufe data ya kwanta. Washegari bayan sun kammala breakfast suka dau haramar tafiya bauchi, tunda gari ya waye take trying lambar Jalal amma taki shiga, har suka tafi bauchi layinsa ya dena shiga. Har sukaje garin bauchi Jalila ji take kaman bata da lafiya saboda takasa samun Jalal a waya, "dama da gaske yake semunyi sati biyu ba muyi waya ba?" A status dinta ta rubuta "I miss you zaujee" Se la'asar suka isa, sun gaji sosai, musamman Nana ga tsohon ciki ga gajiyar tafiya, suna fitowa daga Mota taga Yaya Jawwad "Yaya Jawwad i miss you wallahi, dama zakuzo kuma wannan surprise haka ba wanda ya gayamin" Jawwad yayi murmushi yace "Ai gara da mukayi surprising dinki, Jalal yasan zamuzo ai shine yayi miki lefi" Jalila tace "yaya ina Hanan?" "muje kya gani" suka rankaya zuwa ciki abunda yayiwa Jalila dadi be wuce tozali da Hanan da tayi ba  da nata katon cikin itama da gudu ta rungume Hanan Jawwad yace "A'a Baby ayi a hankali kar aimana barna mun kara yawa" Nana ta bude baki tana jinjina kai yaushe Yaya Jawwad yazama mara kunya? Jalila tace "Allah yabada hakuri, zan kula" Nan gidan yau dau shewa, hatta Mummy Hanan da daddynta sunzo, Daddy yayi mamaki yadda yaga Jalila tayi kalau da ita, kaman ba ita aka dinga fama da ita tana kukan bata son Jalal ba. Jalila tace "bari inje inga Innata" Anty fiddo tace "Inna tana lazimi bata son aje dakinta in tana lazimi se dai anjima" daga nan suka baje suna ta hira. Nana tace "ni Yaya Jawwad yabani mamaki, ga yadda yake salihi ga kunya, amma waishi ke cewa za'a musu barna, tab matar Yaya Jawwad da ciki abun mamaki" Dundu Haanan tayi mata tace "Nana zan miki rashin mutunci akan mijina, ina ruwanki damu" Jalila dariya take musu Yusuf ne ya shigo shima dan gaisawa da su Abba, ya tarar da su Nana a parlor suna ta hira, yaga Jalila tsaf da ita ta dan kara kiba ma, Hanan da take dan danna waya ta dago tace "waike Jalila daga rabuwarku jiya hada wani status wai you miss him, sarkin gulma ashe kun jone? Kamar bake kika dinga kuka kina ba kya so ba" Jalila ta Harare ta tace "da kika ce yanzu ina son abuna ai mutu ka raba" shewa sukayi gaba daya Nana tace "dan bakiga hotunan da sukeyi a wayar ta ba, soyayya suke sha abunsu, ahh komai lokaci ne hakuri me tadda rabo" Yaya Yusuf yayi gyaran murya, suka nutsu gaba daya sukayi tsit suka gaisheshi ya wuce. Anty fiddo tafito tace "ku taho dakin Daddy akwai magana" Jalila taji dam "Allah yasa lafiya" Suka mike suka nufi part din Daddy, Jalila na gwada yadda su Nana ke tafiya. Suka shiga da sallama, gaba daya iyayen nasu sun hallara, Jalila kanta a kasa ta nemi guri zata zauna daga kan da zatayi ta sauke su cikin idanuwan Ummi da ta kura mata ido. Zumbur ta mike ta fasa zamana tana kuma zaro idon ta waje. Maama tace "Jalila ki zauna mana" Wani irin yawu Jalila ta hadiye tana nuna Ummi tareda dan ja da baya zatayi magana Amma taji numfashin ta na sauka da kyar cikin huhunta ta dena ganin komai se duhu. Da sauri Ummi ta mike ta karasa inda Jalila take, kafin tayi wani yunkuri Jalila ta silale kasa sumammiya a gurin Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724  🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 5️⃣8️⃣111 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                     _MY FIRST NOVEL _ Ummi ta rungume Jalila sosai a jikinta, Jawwad ya dakko ruwa me Sanyi a fridge aka shafawa Jalila ruwan a fuska, a hankali Jalila ta bude ido tareda jero ajiyar zuciya ta sauke idonta akan Ummi, kara kankame Ummi tayi tareda sake fashewa da kuka. Maama tace "Jalila ba kuka zakiyi ba, kamata yayi ki godewa Allah ganin mahaifiyarki da kikayi" Abba yace "hakane yakamata ki godewa Allah sannan ki godewa mijinki da danginsa" Kallon Abba tayi cike da rashin fahimtar abunda yake nufi Daddyn Hanan yace "gaskiya kam, mijinki ya cancanci yabo, da shi da danginsa, kuma kafa da kafa zamuje domin nuna godiyar mu da farincikin abunda sukayi" Sam Jalila bata san inda zancen nasu ya dosa ba. Ummi ta share hawayen fuskarta tace "tabbas bayan godiya ga Allah daya nuna muku naku ahalin, zanyi godiya ta musamman bisa Jajircewarku da kulawa da tarbiyya yarinya ta, nagode Allah yasa ku dauka a gidan Aljanna, Jalila bata tana kukan rashin mahaifi ba sanadiyar tarasa wani abu ba nagode kwarai. Tabbas Jalal yasan inda nake, lokacin dana bar ku nayi sallama domin zuwa garinmu, motar mu ta tsaya domin musulmin cinkinmu su gabatar da salla, bayan nayi salla ne na tsallaka wani restaurant na sai Abinci, na fito zan tsallaka titi mota ta bigeni, mutane suka fara taruwa a gurin, wanda ya bigeni dan sanda ne, dan haka ya nuna musu id card dinsa ya daukeni ya tafi dani. Ya kaini wani Asibiti na kudi, inda aka tabattar masa dana samu matsala a kashin bayana, sannan nasamu internal injury akaina, lokacin da labarin bata na ya iskeku Jalal ya shiga zuwa offisoshin yan sanda domin an gaya masa dan sanda ne ya bigeni, Allah ya temake shi yasamo wanda ya bigeni yaje har Asibitin da nake, koda yaje yaga halin da nake ciki, yai magana da mahaifin sa akayimin visa zuwa Dubai a wani Asibiti, na dade ina jinya saboda aikin da'akayimin Kashi kashi a bayana saboda matsalar dana samu. Dana fara samun sauki Jalal yai magana da Hajiya Salma aka maidani Can England gurinta take jiyyata aka cigaba da bani kulawa a can. Hajiya Salma ta zauna dani kaman 'yar uwatta, a gurinta na warke gaba daya, tun ina Asibiti Jalal yaso ya bayyana muku inda nake amma nahana shi saboda ina cikin mawuya cin hali, bayan na warke nai shirin dawowa Nigeria nacewa Jalal bana son kusan inda nake musamman Jalila, idan har Jalila tasan ina raye bazata taba yadda ta zauna a gurin Abban Jawwad ba, nikuma bana son Abunda ze shafi Addinin ta, Yarenta, da Al'adar ta, saboda ni dangina nada banbancin Al'adu da Addini, kuma yin hakan kaman na saba Alkawarin da nayiwa Aliyu ne kafin ya koma ga Allah. Jalal da mahaifinsa, Hajiya Salma, wanda ya bigeni da Mijin Antyn Jalal me sunan Abeenki su sukamin rakiya har masarautar mu, Abunda ya bani mamaki be wuce yadda masauratar suka karbeni kai tsaye ba cike da kauna da girmamawa, sannan na tarar anbawa mutanen dake gidanmu damar kowa yayi Addinin da yake so ciki hadda musulinci, mahifiya ta ta musulun ta, kakana kuma ya rasu, Yaya na ke mulki yanzu" Ummi ta kalli Jalila tace "Jalila ban guje ki ba, a duniya ina matukar sonki ke nake kallo in tuna Aliyu, nayi haka ne domin gyaran rayuwar ki, nayi haka don ki tsaya da kafafunki ko ba kowa tareda ke zaki iya rayuwa keka dai, kin koyi darusan rayuwa daban2 da nake ta nuna miki a baya kika kasa ganewa, lokacin da Jalal ya gayamin an daura muku Aure amma kince bakya sonsa, na shiga damuwa sosai, dan tuntuni nake miki Addu'ar samun miji nagari, kuma koda Ina jinya Jalalya gaya wa Hajiya Salma ta gayamin yana sonki, banji ina kin abunba saboda nasan kina son Jalal kema" Ummi ta kalli Jalila tace "Jalila tsawon lokacin dana dauka bana tare dake kowane lokaci kina raina ina miki addu'a a duk inda kike, zaki shiga damuwa idan kika ga halin da nake ciki na jinya, Amma Alhamdilillah naji dadin yadda naganki, Allah ya albarkaci rayuwar ku gaba daya" Daddyn Hanan yace "Masha Allah, Kinga abunda muke gaya miki tun a wancan lokacin ko 'yar Baba, yanzu da kin wulakanta Jalal da wani ido zaki kalleshi, ba ke kadai kikayi masa halacci ba, shima yayi miki, da fatan zaki kara rike mijinki ki kula da shi, duk da halayen Jalal na ki, Amma mutumin kirki ne, Abun mamaki duk yadda yake da Jawwad be sanar masa ba, se last month ya fada, watan mahaifiyar ki guda a gidan nan, kuma har can garin nasu muma munje, sannan munje maiduguri ma, Insha Allah a satin nan zamuje dake maiduguri kema ki musu godiya sannan muje kiga 'yan uwan mahaifiyar ki su ganki, dan munji dadin yadda suka karbemu cikin girmamawa da mutunci" Jalila kasa magana tayi, yanzu take tabattar tayi wauta, da ta cigaba dayi wa Jalal rashin mutunci da wani idon zata kallesu, ta tuno yadda ta kusa bijirewa Auren, Allah sarki dukda halin bakin ciki data shiga a wasu lokuta a baya, Amma ga karamci da kauna da wasu mutane da bata hada dangi da su ba sukayi mata ba tareda ta sani ba, ga jajircewa da wannan dattawa da kokari da suke tayi a kanta da Mahaifiyar ta Abba da kuma Daddy Hanan. Mikewa tayi ta tafi gaban Abba ta zube akan gwiwowinta ta riko hannunsa amma takasa magana sema wani kuka da ya sake kwace mata. Ba wanda beji tausayin Jalila a gurin nan ba dan Hanan da Nana ma kukan suke taya ta. Abba yace "Jalila kukan ya isa haka, ai murna yakamata kiyi ba kuka ba, kar kanki yayi ciwo sarkin kuka kawai" Jalila cikin kuka tace "Abba narasa me zance, Allah ya biyaku ladan dawainiyar da kukayi dani, Ummi dan Allah ki bawa su Abba hakuri, naso na bijirewa maganar Auren da sukayimin a baya, Abba dan Allah kuyi hakuri ku yafemin, Sannan shima a bashi hakuri abubuwan da nayi masa" Abba yace "Ai baki bijire mana Ba Baby na, ba abunda kikayi mana, kinmana biyayya yarinya ce ke me matukar hakuri da biyayya, Allah baze tozarta ki ba Jalila, halinki daya da mahaifinki, sadaukarwa da kawaici Allah yayi masa rahama" Daddy yace "in ce ko yanzu kina son nashi dai?" Daga kai tayi alamar eh, seda ta basu dariya, amma babu Alamar Jalila zata sassauta kukan da take yi. Maama tace "zanyi Amfani da wannan damar in baki hakuri Maryam, na cutar dake da Jalila a baya, Amma nayi nadama, sharrin shedan ne da kuma zigar 'yar uwata, Amma daga baya nayi nadama, wallahi samun yarinya me halin Jalila se an tona, bata taba min rashin kunya ba duk abunda nake mata, dan Allah Maryam ku yafemin " Ummi tace "Haba Zainab, wallahi kin gama min komai a rayuwa, tunda kika zauna da Jalila kika rike ta, abubuwan da suka faru da ni da ita itace kaddarar mu, kuma ko yanzu Alhamdilillah, karki damu ni ban rikeki da komai ba, Allah ya yafe mana gaba daya" Suka amsa da Ameen gaba daya, Babu alamar Jalila zata dakata da kukan nan, dan da kyar take jan numfashi ma. Daddy ya kalli Anty fiddo yace "fidausi ku kai yarinyar nan daki ta kwanta ta huta, wannan kukan ze iya jamata matsala" Haka akayi suka kama Jalila zuwa daki suka kwantar da ita, suka kukkuna mata fanka, tana ta sauke numfashi. Yusuf yayi mamaki, yaji labarin rayuwar Jalila da kuma waye Jalal, tabbas babu wanda ya dace da Auren ta se Jalal. Seda aka kira likita yayi mata allura tayi bacci dan bata gane waye akanta, dan kukan da tayi ya saukar mata da zazzabi me zafi da ciwon kai. Ilham ta shirya ta tafi gidan su Yaseera, tana zuwa tayi sa'a yaseera tana nan, suka gaisa da babar su yaseera sannan suka wuce Dakin ta, suna shiga yaseera ta kalli Ilham tace "Ilham abun har ya kai haka? Kinga yadda kikayi duhu, kin wani rame ko baki da lafiya ne?" Ilham tace "wallahi Bani da lafiya yaseera, Amma ban damu da rashin lafiyar ba, ina cikin damuwa kuma mafita nake nema cikin gaggawa ko wace iri ce" Yaseera ta gyara zama tace "ina jinki, nasam dai ta tsuniyar gizo bata wuce koki, akan Jalal ne ya ake ciki? Har yanzu baki hakura ba?" "ta yaya zan hakura yaseera, kinsan son Jalal ya zame min bala'i?" "ban gane ya zame miki bala'i ba, ina dama can soyayya ta shiri ce zakuyi dan ya aureki?" "yaseera wallahi ashe son gaskiya nakew Jalal ban san hakan ba seda yayi auren nan, Yaseera yarinyar nan muguwar player ce, wallahi soyayya suke kamar ya hadiye ta, Yaseera uwar sa fa yake gayawa wallahi ko a gaban waye se ya fada yana son matar sa, Yaseera zan iya rasa raina saboda yadda soyayya Jalal ke kara ruruwa a raina" "tabdijan Ilham kinga da Jalal yana jin maganar mahaifiyarsa to tabbas zata tirsasashi ya aureki, amma yadda yake din nan a duniyar nan babu me iya raba shi da ita, ni tun a baya na fuskanci abun nan nasu akwai soyayya a ciki, Amma nayi gudun in gaya miki saboda karki ji haushi" "to yaseera meye abunyi yanzu?" Yaseera tace "wane kokarin ummanki take akan lamarin" Dan tsaki Ilham tayi tace "itafa kawai burinta ta dauki fansa, bata tausayawa halin da nake ciki, itama Mummy bata ni take ba, kawai burinta ta raba Auren" Yaseera tace "to mafita daya ce a yanzu, Amma ban san yazaki kalli abun ba" "nidai gayamin koma meye zanyi" "kin san da bakinki kika gayamin asiri baya tasiri akanta, sannan tunda Jalal ya riga ya aure ta nasan sun hada shimfida, abu daya zuwa biyu zakiyi yanzu, ki cigaba da hakuri kiyi duk yadda zakiyi ki tabattar babarsa ta raba auren nan, sannan kije ki karya sihirin da kukayi masa, idan har ya karye zeji maganar mahaifiyarsa, in yaso se kiyi kokarin kiyi wani asirin da duk yadda zakiyi mahaifiyarsa ta tirsasashi ya aureki " Murmushi Ilham tayi tace "kin kawo shawara Yaseera nagode sosai" "Amma kije kiyi magana da Umman kiji me zata ce" Dan zare ido Ilham tayi tace "wace Umman, wallahi bazata yadda ba tabdijan, tunda naga kowa kansa ya sani nima kaina zanwa fafutuka, ta taba bani labarin inda taje akayi asirin, zan Lalla bata ta kara gayamin yadda abun yake, sena karya asirin dan burina ya cika, nagode sosai yaseera" Yaseera tace "shikenan Allah ya temaka" daga nan Ilham ta samu relief ta saki jiki suka sha hira. Kiran sallar Asuba da'akayi ne yasa Jalila ta farka, Addu'a tareda fatan Allah yasa ba mafarki bane, Allah yasa Ummi ce da gaske, ta bude idonta ta juya, kamar yadda ta saba gani wasu shekaru da suka shude, Da gudu ta sakko daga kan gadon dukda ciwo da kanta yake ta rungume Ummi gam. Cikin kuka take cewa "Allah yasa ba mafarki nake ba, Allah in bacci nake Allah kasa in dawwama inayinsa, Allah kasa a jikin Ummina nake, Ya Allah.. Ya Allah... Ummi tasa hannu ta dago ta, dukda Ummi hawaye take sharewa tace " Haba Babyna, ba bacci kike ba, nice Ummin kice, kalleni nice" Kara rungume Ummi tayi dan ji take kaman in tayi wasa Ummi zata kuma tafiya ta batta. Dakyar Ummi ta lallaba Jalila tayi salla tana idarwa ta kuma kwanciya a jikin Ummi tace "Ummi meyasa kikaki ki bari in san inda kike, inyu jinyarki da kaina? Na shiga damuwa na shiga kunci, Nayi kuka a lokacin da babu me rarrashi na Ummi, meyasa Ummi?" Ummi ta numfasa tace "Jalila a lokacin da nake jinya ko kinzo bazan ganeki ba, i partially loose my memory" Mikewa zaune Jalila tayi tana kallon Ummi, Ummi ta jinjina kai tace "tabbas Jalila na manta da abubuwa da yawa a wannan lokacin, But Alhamdilillah idan bani na fada ba, babu me gane  hakan se su Jalal da suka san nayi, da Mahmud tunda a gidansu nayi jinya" "yanzu Ummi Yaya Mahmoud ma yasan inda kike amma aka rufeni, shiyasa ranar da ya fara ganina yace nice Jalila?" "sosai makuwa, sannan duk iya shegen da kika dinga yiwa dana nasani, Inda Allah ya temakeki kema kinyi rawar gani gurin sauya rayuwarsa, Tun kuna kanana na fuskanci Jalal yana matukar sonki, Har Abeenki yace Insha Allah in dai yana raye in har kina son Jalal ze bashi, Abun Allah, Allah ya kaddara ke rabonsa ce, Jalila duk mutumin daze soka tun baka san kanka ba wannan shine masoyi na gaskiya, babu abunda ze sameki ya guje ki" "Amma Ummi me yasa baki gayamin a baya ba?" "ta yaya zan gaya miki? Kina fama da rashin ji da tsiwa, a lokacin ma ga abunda kike masa inaga na fada miki, Jalila hatta mafarkin da kike da Jalal nasani, kiyi ta surutai cikin bacci, nidai na dage muku da Addu'a ne" Dan murmushi Jalila tayi "tabbas Ummi Addu'a ki bata fadi kasa ba, Amma Ummi na sha wahala wallahi, naga kalubale daban2" Nan ta labartawa Ummi wasu daga cikin gwagwarmayar da tayi, daga karshe tace "Ummi da muna mutunci da Mummy sosai, Amma tunda Jalal yafara nuna yana sona ta tsaneni Ummi, kinga cin mutuncin da takemin kuwa?" "Jalila Kamar yadda Allah ya tsamoki daga cikin kaddara daban2, karkiyi tunanin shikenan, dole ki fuskanci wata kaddarar, Allah yana jarabtar bayinsa da yake sone dan haka ki gode Allah kiyi fatan Allah yasa ki cinye dukkan jarrabawar ki.   Sannan ba abun mamaki bane dan bata sonki, tunda inkika tuna abunda tayiwa kanwarta da suke uba daya, ke a wa daba zatayi miki ba? Tsoronta daya kar a mallake mata da, shiyasa take ganin ke matsala ce a rayuwar danta, duk kirkinki Jalila baze taba yuwuwa kowa ya soki ba, dole wani seya kiki, karki taba tunanin kowa seya soki, wani ze nuna a fuska yana kaunarki, Amma zuciyar sa babu wadda ya tsana kamar ke, sedai Jalila kiji tsoron Allah, yadda kika dauki aniyar sauya rayuwar Jalal karki sa ya kauce hanya, kar son da yake miki yasa kisa yaci gaba da fito na fito da mahaifiyarsa dan bata sonki, ki rike mijinki Jalila, Shi Aure idan ka samu wanda kake so ka iya tafiyar da shi yadda shari'a ta koyar, babu abunda ya kaishi dadi, shiyasa har gobe bazan manta Aliyuna ba" "kai Ummi ko kunya ta ba kyaji?" Ummi murmushi tayi tana girgiza kai,. Jalila ta dan bata rai tace "ummi Jalal tun kan ya tafi Lagos yace kar in kirashi har sati biyu wai bazata shiga ba, ashe abunda ya shiryamin kenan, dan Allah ki kiramin shi a waya, nasan ke ze daga naki Kiran" Ummi tace "A'a abunda yake so shi nake so, dan haka se kiyi hakuri se lokacin da yace, ai gara ya rama shima" Jalila ta dan sunkuyar da kai tace "Ummi ina son ine nemi afuwar Jalal, tun kafin in san dawainiyar da yayi min dake, ina jin nauyinsa idan na tuna abunda na dinga yi masa a baya, dan ma wani abun baki sani ba" Hira ce sosai Ummi da Jalila suka cigaba dayi, wani lokacin suyi kuka, wani lokacin suyi dariya, Ummi na ta kara yiwa Jalila nasiha, har gari ya waye yayi haske har kusan goma suna tare, aka fara shigowa duba Jalila, aka tarar Jalila ta ware tanata hirar ta da Ummi. Warewa sukayi aka cika dakin suna ta hira da Ummi, Ummi se lallaba Su Hanan takeyi, Jawwad ji yake wani bangare na farincikin iyalansu sun dawo, koba komai Ummi ba abar yarwa bace, dan itace uwar rainonsu shida Jawwad, Amma shi kansa Jawwad ya sha mamakin abunda Jalal yayi. Jalila tayi2 wayar Jalal ta shiga amma taki shiga, ta tura masa messages amma shima babu response, abun ya fara damun ta sosai, Harta E-mail dinsa ta tura masa sakkonni amma shiru. Jalal kam yana sane yayi mata haka, in bahaka ba yasan halinta ta dinga tuhumar sa kenan, koma taita koke2 se ya dawo, wani lokacin ya kan bude system dinsa ya duba sakkonin Jalila, "zaujee pick my calls please, i have a lot to say" ire iren messages din nan dayawa a Gmail dinsa, murmushi yayi yace "Baby na sarkin rigima, dama akwai ranar da zatazo kidinga nuna missing dina haka?" Murmushi ya kara yi yace "Yarinya se na rama tukuna, gara kema ki dana abunda nake ji" Ya dauki wata wayar tasa daban ya kira Jawwad, yana kira Jawwad ya dauka, suka gaisa Jalal yace "Jawwad ina matata ne? Fatan tana lafiya?" "ban sani ba, ai kafini kusa da ita, ka wani kashe waya kana wahalar min da 'yar uwa" Jalal yace "ba ruwanka, kai waya dameka kai da matarka, kawai kuyi kallo, dan Allah Jawwad tana ina me take yi yanzu?" "Wallahi tana cikin damuwa Jalal, tayi murnar ganin Ummi sosai, Sannan a gaban mutane take kuka tana a baka hakuri, har gurina tazo tana tambaya ta ko ina samunka a waya? Ba yadda na iya ka sanayi mata karya" Hanan da take gaban Jawwad yana bata Abinci tace "Jalal ka temaki sister na, ta horu fa, kullum se tayi zancen ka babu Adadi," Allah sarki Jalal dina, ko yaci Abinci? Ko yayi Adhkar dinsa? Da yana nan dai dai yanzu muke cin Abinci, Allah ya dawomin da shi in bashi hakuri" haduwar ta da Ummi be sa ta manta da kai ba, tana kewarka sosai fa" Ajiyar zuciya yayi yace "Allah sarki masoyiyyata wallahi nafi missing din ta, banyi haka dan ta shiga damuwa ba, wannan shine burina, Jalila ta hadu Ummi, bayan Ummi ta warke, nasan Jalila tana sona, Kaman yadda Hanan ke fada ne, tana da taurin kai, bata fiye yadda da abunda zuciyar ta tazo mata da shi ba, Hanan dan Allah ki cigaba da rarrashin ta, in dai na daga wayarta nasan kuka zata yi min, nikuma kukan ta yana tabamin zuciya, naji gobe in Allah ya kaimu zaku tafi garin su Ummi, Allah ya kaiku lafiya ya dawo da ku lafiya " Jawwad yace " Ikon Allah, ji yadda ya wani kashe murya yana gayamin yayi missing din matar sa, kaman ba shine me cewa Mata matsalane, soyayya shirme ce, to yanzu kuma mene? " Jalal yayi murmushi yace "a bayan ma duk basaja nakeyi in gaya maka, da zaka tona zuciya ta seka tausayamin, nayi zaton cire soyayya abune me sauki daga zuciya, amma duk lokacin da nayi yunkurin cire son ta a raina, se naji kaman ina kara azabtar da zuciya ne, gashi a lokacin bana ganin komai se kiyayya ta a idon Jalila, se kuma daga baya da Hanan ta nunamin son da Jalila takemin ne yasa take fada da kowa akaina, kishina da take yasa take bani Kariya da dukkan mummunan abun da ya tinkaroni, shiyasa na samu karfin gwiwa na cigaba da kaunar ta, ina son Jalila sosai, kai se anjiman ku, zan fita gurin aiki" Jawwad yace "har ka gaji da zubar? Da labarin soyayyar taka?" "ina fa? Ai labarine sakanni, awanni, da wuni, sati, watanni ko shekaru bazasu bada damar gama wannan Labari, me dadi da ban tausayi ba se an jimanku" Murmushi Jawwad yayi "A da in aka cemin Jalal yana wannan zazzafar soyayyar zan rantse ince karya ne, yau gashi kunne na yaji min" Hanan tace "Ain dama tuni nasan yana kaunar ta, kuma itama tana sonshi, shiyasa nai tayi musu Addu'a, nikuma na kafa tawa soyayyar" Jawwad yayi murmushi yace "gashi nan an kafa min ita inda ba wanda ya isa ya ganta balle ya taba, mata ta abar Alfahari na, Allah ya rabaki da cikin nan lafiya dake da Nana" "Ameen my lovely Haidar" Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 5️⃣9️⃣112 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                     _MY FIRST NOVEL _ Shiri sukayi sosai don tafiya garinsu Ummi, da farko akace baza'aje da su Nana ba saboda larurar ciki, amma sukace baza'ayi babu su ba suma suna son zuwa garinsu Ummi. Shiri sukayi sosai, suka dau motoci suka nufi kwara state. Tunda suka shiga garin Jalila ta kara tabattar da lallai Akwai banbancin Addini da al'ada. Jalila tayi mamakin irin kyau da tsaruwar masarautar su Ummin ta, lallai Ummi ta cancanci yabo da jinjina, da ta iya tsallake wannan daular ta zabi Addinin musulunci da kuma soyayya. Su nasu masarautun basa amfani da doki, se manyan motoci, ga barori nan nata kaiwa suna komowa, gasu da matukar biyayya, duk inda suka ratsa zubewa ake ana girmama su, musamman Ummi. Seda suka shiga cikin gidan ta kara tabattar da lallai Ummi ba karamar 'yar gata bace ba, Tangamemen hoton Mahaifiyar Ummi ne sakale a wani katon guri kamarta daya sak da Ummi, duk da ta manyan ta seka dauka ya da kanwa ne. An karbesu cikin girmamawa da mutuntawa, Seda suka huta, Aka dinga gabatar musu da kayan Abinci, Seda aka jima suka huta sannan Mahaifiyar Ummi ta fito, Mahaifiyar Ummi na ganin Jalila ta rungumeta cikin harshen turanci tace "ko ba' a gayamin ba nasan wannan itace jikata" Ummi tayi murmushi tace "Eh itace" Mahaifiyar Ummi ta kalli su Hanan ta kalli Jalila tace "wannan 'yan uwanta ne?" Jawwad yace "Eh duk' yan uwanta ne" "to wace matar Jalal kenan?" Nana tace "Jalila ce matarsa" Mahifiyar Ummi ta jinjina kai tace "Sunan ta da mijin ta  suna kama, mijinki yana da kirki sosai lokacin da mamanki ta dawo gida yana zuwa nan" Maman Ummi tana da kirki sosai, nan aka dinga gabatar da su gurin mutanen gidan, 'yan gidan sunyi murnar ganin yarinyar' yar uwasu, bayan tsawon shekaru 'yar uwatasu bata tareda su. Sarkin da yake mulki a wannan lokacin wanda yakasance Yaya ga Ummi shima ya nuna farincikin sa da jin dadi, na ganin su Jalila. Daddare suna hira, mahaifiyar Ummi take cewa su Jalila, "nayi dana sanin hana marry ta auri wanda take so a wancan lokacin, dukda ba laifina bane, laifin kakanta ne, yana ganin na auri bahaushe musulmi zaman beyi dadi ba, nayi kewar ta sosai tsawon wannan lokaci, bana iya bacci, sannan mahaifina yace be yadda in tura kasar hausawa a nemo ta ba, duk abunda yafaru da ita babu ruwan wani. Ban taba zaton marry zata iya jure zama tsawon wannan lokacin ba ba tare da mu ba, bayan rasuwar mahaifina shekaru biyar baya, Yayanta ya karbi mulki, shi da kansa yasa a bincika koza'a gano ta amma abun be yuwu ba, na koma Addinin musulinci, Yayana yaba wa kowa damar yayi Addinin da yake so, abun mamaki akan marry na yadda musulmi kuma hausawa mutanen kirki ne, lokacin da ta dawo gidan nan nayi mamaki, labarin da ta bani akan yadda rayuwar hausawa musulmi yake, da kuma karamcin da suka nuna mata, musamman wannan dan kyakywan yaron me dogon hanci, yana burgeni matuka yana girmama ta kaman ta haifeshi, kuma da ta gayamin alakar dake tsakaninsu naga babu wani babbar alaka da suka hada amma yake ta dawainiya da ita shida iyalansa" Jalila ta kunshe kai tana dariya taji ance Dan kyakywan yaro me dogon hanci Hanan tace "Dallacan se wani murmushi take dan ance mijinta kyakywa, nima mijina kyakywa ne, dan mijina farine tas" Nana tai caraf tace "nima mijina yana da kyan ai, tunda kanin mijin Jalila ne" Sukaita hira suna dariya, mahaifiyar Ummi tana da kirki da sanyin hali kamar Ummi gata da faran faran babu ruwanta. Amma duk abun nan Jalila hankalin ta yana kan Jalal, ta damu sosai rashin ganin sa, ba karamin missing dinsa take ba. Kwanan su hudu a garin, sun sha yawo, garin yana da kyau, sun sha hotuna, gasu da yalwar dazuka, Akwai fulani a garin, da babur amma yawancin su yarabawa ne, suma mutane masu kirki da kyakywar mu'amala. A kwana na biyar suka fara shiri domin tafiya su bar garin. Mahaifiyar Ummi taji babu dadi, seda tayi mita "marry meyasa bazaki barmin yaran nan ba su dan kara kwanaki, wallahi sun shiga raina sosai naji dadin zama da su" Ummi tace "kiyi hakuri zasu dinga kawomiki ziyara, matan aure ne yaran nan, yakamata su koma gidajen Auren su, sannan Zamuje maiduguri gidan Su Danki Jalal, Abban Jawwad zasu jira mu a can" "Shikenan amma ba haka naso ba, naso  kara zama damu, yanzu na kara tabattar da abunda ake fada akan hausawa musulmai ba haka bane, kuna da kyakywar mu'amala da kuma girmama mutane, Jawwad amma kaima zaka dan dinga zuwa ko?" Jawwad yai murmushi yace "karki damu, dukkan mu ma zamu dinga kawo miki ziyara, amma kema muna fatan zakizo mana" "zanzo mana, tunda ina daku, Insha Allah nima zanzo muku" A kwana na biyar suka karasa shiri zasu tafi, An musu alkhairi me tarin yawa. Suka yi harama Jawwad ya dauke su suka baro garin suka nufi borno state. A motar ma se hira suke, suna kara yaba kirkin mahaifiyar Ummi da kuma barkwancin ta. Suka karasa maiduguri a gajiye, bayan la'asar sosai suka karasa, Antyn Jalal tayi murnar ganin su kwarai, musamman da ta gansu tareda Ummi cikin fara'a tace "kai masha Allah, bakin ba zata, Ummi Kice keda iyalan naki gaba daya kike tafe" Ummi tace "Aikam dai gasu nan" "sannunku da zuwa Jawwad, dazu Jalal ya bar garin nan, nasan be san zaku zo ba" Jalila a ranta taji dama tun dazun sukazo, "meyasa Jalal yakemin hakane? Duk na damu yaki bari mu hadu sam, why?" Anty tace "Jalilan Ummi, gaki ga Ummi, dazu Jalal yabar garin nan, albarkacin ki yasa ya kan leko mu ya kawo mana ziyara, bashi da aiki se yabon matarsa ko kunya ta bayaji" dan murmushi Jalila tayi ta sunkuyar da kai. Jawwad yayi alwala ya tafi masallaci, Suma sallolin su suka gabatar, Anty se lallaba su Hanan take saboda ciki da suke dauke da shi. Jalila tace "Anty ina Husnah ne da Amal?" "Husnah ta koma gidan ta, Amal kuma tana gidan kanin Babanta" Daddare mijin Anty ya dawo, yanayin yadda suka gaisa da Ummi ze tabattar maka da sun san juna, nan Ummi take gaya masa daga kwara State suke, ya nuna farincikin sa da jin dadin sa akan hakan, gefe guda kuma ya dinga tsokanar Jalila "matar so inji mijin ta, ya akayi kukayi sabani da mijin naki ne? Shi ya tafi dazu kekuma kinzo yanzu, ya akayi hakan ta kasance? Gayamin sirrin mana daughter, banda zancenki ba abunda Jalal yake in ya zauna" Jalila dai kasa magana tayi, kowa tsokanar ta yake saboda Jalal. Itakam Hanan ana wannan hirar ta silale ta tafi masaukin Jawwad daga ta kai masa Abinci bata dawo ba se bayan karfe daya, Jalila ta dinga ce mata mara kunya. Washegari wajen Azahar Abban Jawwad da Daddyn Hanan, se Maama da Mummy Hanan suka iso, gida ya dau harami ya cika da baki. Suna zuwa da suka huta ba tare da bata lokaci ba Daddy ya gabatar da abunda ya kawo su na zuwa su jadadda godoyar su akan karamci da dawainiyar da sukayiwa Ummi. Abee yace "babu bukatar ku cigaba dayi mana godiya, duk abunda Jalal yayi wa Wannan baiwar Allah be fadi ba, musamman shima dawainiyar da soyayyar data nuna masa a lokacin da shi da mara uwa kusan daya, mun riga mun zama daya da mu da ku, dan Allah batun godiyar nan a barshi, Allah yakara hada kanmu ya kara mana kaunar juna, Allah ya Albarkaci rayuwar yaran mu, Amma babu godiya a tsakaninmu" Suka Amsa da Ameen gaba daya. Kwana daya su Abba sukayi, suka kama hanya zuwa bauchi, kafafuwan Hanan duk sun dan kumbura saboda zaman mota, hakan yasa Jawwad ya damu yace a bauchi ze barta ta huta, in yaso ya biya kudin jirgi su koma Abuja. Tun suna hanya Mahmoud ya kira Nana a waya yace mata yana bauchi, Nana se murna take yi, yau zata ga mijin ta, Jalila ta danyi shiru tana tunanin nata mijin. A gajiye suka koma garin bauchi, a yan kwanakin nan sun sha yawo, da suka isa bauchi Jalila wanka tayi ta nemi guri ta kwanta tana baccin gajiya. Jalila bata tashi ba seda Ummi tazo ta tasheta "ki tashi haka kiyi salla kici Abinci mana, baccin ya isa haka uwar bacci ashe har yanzu baki dena wannan baccin ba" A shagwabe tace "Ummi wallahi a gajiye nake shiyasa" "ki tashi haka dai baccin ya isa" Jalila ta tashi tai salla ta zubo Abinci ta zauna kenan ta fara ci Nana ta shigo, ta kalli Jalila tace "se yanzu kika tashi kenan? In kin gama akwai surprise" "Suprise kuma? Suprise din me?" "sekin gama tukuna" Jalila tace "shikenan" Jalila ta cinye Abincin ta, tanemi guri ta kashingida tana danna waya. Nana ta dawo dakin ta tarar Jalila tana danna waya, ta dan hade rai tace "wato baki damu da Suprise din ba ko?" Jalila tace "ai naga baki da niyyar gayamin ne" Nana ta dakko powder da janbaki tazo gaban Jalila ta zauna. Jalila ta kalleta "wannan na menene kuma?" "fita zamuyi, yaya Jawwad yace mu shirya" Jalila ta dan bata fuska tace "haba dai muje ina? Banda wannan gajiyar" "ni dai ba ruwa na, shi yace mu shirya zamu dan fita" ta shashsha fawa Jalila powder da jan baki sunayi suna fada Jalila tana mitar ita gaskiya bata son kuma fita  a gajiye take Hanan ta shigo tace "Jalila har yanzu baki je ba?" Cikin rashin fahimta Jalila tace "nifa ban gane muku ba, inje ina kuma?" Nana tace "kije BQ ki duba Suprise din yana can" "nifa Nana nakasa gane miki, kince Yaya Jawwad yace zamu fita kuma kince zakiyi surprising dina" Hanan tace "dan Allah kije ki gani mana, ke ba kyacin ribar abu, ga mitar tsiya" Jalila tace "saura inje inga shirme, sena muku rashin mutunci" Hanan tace "in kuma akasin shirmen kika gani fa?" Jalila tace "Bari dai inje in gani tukuna" ta dauki gyale ta yafa akan riga da skirt din jikinta ta fita Da taje inda Nana tace taje bata ga kowa ba se Yaya Jawwad a parlor Jawwad ya kalle ta yace "Baby ya akayi ne?" ba tace masa komai ba se dai dan shiru da tayi tana nazarin dakin, tana kokarin gano wani abu, kaman kamshin turaren Jalal take ji, Jawwad yayi murmushi yace "duba wancan bedroom din yana ciki, nasan shi kika biyo" Ba tareda tace komai ba ta nufi dakin da Jawwad ya nuna mata da sauri, ga mamaki kuwa tana zuwa tatarar Jalal yabawa kofa baya, sanye da dogon wandon jeans da vest a jikin sa yana waya, da gudu ta tafi ta rungume shi ta baya, dan murmushi yayi yai sallama da wanda yake wayar da shi, ya aje wayar ya juyo da ita suna fuskantar juna, har hawaye ya wanke fuskarta. "Ohhh am sorry dear, waye ya gayamiki ina nan ma tukuna?" Shigewa jikinsa ta kumayi ta kankameshi kamar wani ze kwace mata shi ta sake fashewa da kuka. Jalal yace "Subhanallah Kin san bana son kukanki, gayamin me yasa min ke kuka?" A hankali ta fara magana cikin kuka "Am sorry Jalal, Am sorry" "Aini bakimin komai ba, kidena kukan nan please" Kasa denawa tayi, Hawaye ne wani na bin wani keta zuba daga idon ta. Jalal yace "Am sorry My love, ni nayi miki laifi, tsawon wannan lokaci dana boye miki nasan inda Ummi take, am very sorry ba laifina bane" Tasa hannu ta toshe masa baki tareda girgiza masa kai. "Nina yi maka laifi zaujee" A hankali ta durkusa akan gwiwowin ta, ta rike kafafuwan sa tareda fadin "Jalal nagode, bani da kalaman dan zasu nuna maka godiya ta, Allah ya biyaka da gidan Aljanna, sannan Kayi hakuri Jalal abunda na dinga yi maka a baya please forgive me" Ba karamin mamaki abunda Jalila tayi ya bashi ba, da hanzari ya dagota ya zauna ya rungumeta a jikinsa, cikin sigar rarrashi ya fara magana "Jalila laifin me kikayi min dana cancanci haka? Nima Ummi uwata ce" Cikin tsokana yace "yarinya seda Ummi ta sameni sannan ta haifeki fa, kidena min wata godiya abunda nayi kaina nayiwa, sannan ni ba abunda kika yimin dana cancanci ki durkusa kina bani hakuri haka, ni yakamata in durkusa in miki godiya, Bayan Jawwad ban taba tunanin akwai wanda ze damu da al'amurana kamar ke ba, kalli rayuwar da nayi a baya, kalli wadda nake a yanzu, kinsaka rayuwar ki a cikin hatsari saboda ni, wani nasani wani ban saniba, abubuwam da kikayi min a baya kuruciya ce, kuma kinyi ne saboda kina kyamar mummunar Rayuwar da nakeyi, Thank you very much for all what you did for me, kin kawo canji mafi girma a rayuwar ABDUL JALAL, I love you so much my wife " Ta kara kankame shi tareda fadin "I love you too, Zaujee" Yadda tayi maganar yaji wani abu ya tsirga tundaga kansa har tafin kafarsa. "Jalila Do you really mean what you say?" Jinjina masa kai tayi "I mean it zaujee, I love you" Jalal yaja numfashi yace "Kalamai masu girma dana dade ina expecting a gayamin, gayamin yaushe kika fara sona ne?" Murmushi tayi tace "hmm wani dogon zamani da ya wuce, da farko dai na dauka kishi ne da tausayi daga baya kawai aka shammaceni aka jani fagen soyayya" Dariya Jalal yayi yace "waye ya jaki fagen soyayyar?" "Mijina mana daya tamkar da dubu" "dan Allah ki dan kara cewa kina sona mana" "I love you Zaujee" Ya dan kashe mata ido yace "dan kara fada mana" "Anki din bazan sake fadan ba cikani in tafi" Kara riketa yayi yana dariya, abu kaman wasa Jalila taji Jalal yana neman wuce gona da iri dan haka ta rike hannunsa, tareda kiran sunansa da dan karfi "Jalal" Ya bude idonsa yana kallon ta "Dan Allah ka kyaleni ba fa a gida muke ba" "Au a daji muke?" Kaman zatayi kuka tace "Ina nufin ba'a gidanmu muke ba, Yanzu Ummi zata iya nemana fa" "Shikenan karkimin kuka Sarkin kuka, Amma Jalila yakamata mu koma gida fa, yaushe zamu koma?" "duk lokacin da kake so" Ya dan lumshe ido yace "ko yanzu?" Jinjina masa kai tayi alamar eh "Shikenan ki koma ciki, da safe Insha Allah zan shigo in gaida Ummi, ki shirya gobe zamu fita yawo" "ina zamuje?" "Allah ya kaimu gobe zaki gani, in kinyi Salla ki hau online" Hararsa tayi "bazan hau ba din, kuma ba yawon dazan bika, kusan sati biyu nayi a cikin damuwa da kewar ka, nima sena rama" "Haba matar kiyi hakuri, banyi hakan da gangan ba, nasan dana bar wayata a kunne, kirana zakiyi tayi kina koke2, nikuma bana son inji kina kukan nan shiyasa, Allah yabaki hakuri" Mikewa tayi ta dau mayafinta tace "kaga na tafi seda safe" kafin yayi wata magana tai waje abunta. Tana zuwa ta tarar Ummi tana sama ita da Maama a dakin Inna, dan haka kai tsaye dakin da sukw ta wuce taje ta tarar da su Hanan sunyi kwadan garri suna ci. Tana shiga Hanan kalleta tace "lallai matar so, se yanzu?" Jalila ta harareta tace "ban sani ba" Nana tai dariya tace "Jalila ina Jan bakin?" Cikin ko in kula tace "mun shanye abinmu" Hanan tace "wallahi Jalila baki da kunya" Jalila tace "har na kaiki rashin kunya, kudena gulmar nan ku maida kai kuci garrin kwakinku" Nana tace "zakiga mu maida kai muci garri, kema zezo kanki ne" Jalila tana idar da sallar isha'i tai Azkar, suka fara waya da Jalal. Duk soyayyar da Jalila tayi Abaya yanzu take tabattar da shirme ce yanzi ta gane menene hakikanin soyayya, yanzu ta gane se yanzu ta shigo fagen soyayya, Jalal yana tarairayar ta da nuna mata tsantsar kulawa. Da suka gama wayar ma da Jalal chatting suka koma yi, da kyar sukayi wa juna sallama suka kwanta. Kusan kullum idan yamma tayi, su Jalal se sun dau matansa sunfita yawo. Jalal seda ya kyale Jalila takara kwana goma da Ummi sannan yace yana son sukoma Gida, Nana da Hanan duk sun riga sun tafi. Jalila tunda taji yace su tafi tasan ya mata kara, amma seda tayi kuka, ana gobe zasu tafi Ummi ta kirasu ta zauna da su taita musu nasiha a karshe tace "Jalila ga amanar dana nan, ki kulamin dashi, kiyaye hakkokinsa ki guji abunda ze bata masa rai koya sa shi yin fushi" Jalila ta dan tura baki tace "to shi bazaki ce masa ga amana ta  ba"? Ummi tai murmushi "Jalila ai bazaki taba canza hali ba, ni Jalal ne dana dole in jadadda miki ki kulamin da shi" Jalal ya dinga yi mata dariya, Jalila tace "Ummi wai bazaki bimu mu koma kano ba?" Ummi tace "in biku in muku me? Gidan mu zan koma nima, se an kwana biyu zanzo in ga dakinki, nidai fatana Allah ya zaunar mana daku lafiya a daku nan ku" Sam ba haka Jalila ta so ba, nan da nan ta fara kuka, Gaba daya yanayin Jalal ya sauya ganin yadda Jalila ta fara kuka Ummi tace "Jalal tashi ka tafi kyleta, gobe insha Allah zaku tafi" Haka Jalal ya tashi ya tafi. Washegari gurin karfe sha daya na safe suka baro Bauchi zuwa kano ba dan Jalila taso ba dan sam bata gaji da ganin Ummin nata ba, ta sha kuka sosai kafin su taho. Bayan Azahar suka isa gida, Jalal ya tafi masallaci Dan la'asar ta gabato, ita kuma Jalila ta shiga gida da kayan su. Ta bude Dakin ta ta shiga ta tarar da Akwatina a ciki, set uku blue, silver, da purple kowacce uku da kit. Mamaki ne yakamata tareda tunanin waye ya kawo wannan kayan? Kuma na menene. Bata taba su ba, ta ajiye kayan da suka dawo dasu, tai salla ta shiga gyaran gida, saboda duk yayi kura kusan wata guda kenan bakowa a ciki, ta share ko ina tai mopping ta wanke toilet da glasses na window harta gama tana tunanin kayan nan. Seda akayi sallar magariba Jalal ya dawo hannunsa da ledoji, a parlor ya tarar da ita tana kallon zee world "Waike ba kya gajiya ne, daga dawowarki kin tsiri aiki" Batace komai ba se murmushi da tayi ta karbi kayan hannunsa "ina ka tafine haka?" "na tsaya nayi salla ne, sannan naje nayi mana siyayya abunda zamuci base kinyi girki ba" Jalila ta dan numfasa tace "Akwatinan me ka ajiye a dakina?" "Nakine na lefe ko ba suyi miki bane?" "Amma Jalal.... Yatsan sa ya dora akan lips dinta yace "Shhhh bana bukatar sharhi, tuhuma, ko godiya, a cigaba da yimin kwalliya kawai, babu bukatar kimin wata godiya dakko plate da cup muci Abinci" Jiki a sanyaye ta dakko plate tazo ta ajiye ya zazzage ledar kaza ce da dogayen kwalayen madara, ya zuba a plate ya mika mata yace "feed me" Gaba daya ya lura a tsorace take da shi yau, da dane da yanzu watakila ta haye cinyarsa tana tsokanar sa, Amma yau ko kusa dashi taki zuwa karshe dai shi ya dinga bata amma taki ci se kyaleta yayi. Bayan ta idar da sallar isha'i tai wanka ta haye gadon ta tai kwanciyar ta dan tana jin bacci sosai harta fara bacci taji an kunna wutar lantarkin dake Dakin ta, dan rintse ido tayi, sannan ta bude a hankali ta sauke akan Jalal Murmushi yayi yace "shine yau ko azo muyi azkar din ko? To ni nazo muyi" Janyo bargo tayi ta shige ta rufe har kanta ta dunkunkune, ba karamin dariya ta bashi ba, ya kashe fitilar ya hau kan gadon yace "ni kike gudu haka ko Baby?, fitowa zakiyi" Ya fara kokarin janye bargon nata, "nifa bacci nake ji ka kyaleni" Banza yayi mata seda ya cirota daga bargon, gaba daya Jikin ta yayi sanyi, "Jalila ni kike gudu haka ko? Hada shigewa bargo, ance ana sona amma ana guduna haka akeyi, burina ya cika ummi na ta warke, Baby na ta hadu da Ummin ta, yakamata a tausayamin haka Baby na azabtu fa" Haka yai ta mata surutai, Bata gama firgita ba seda taji abunda Jalal din ke kokarin yi ya shallake tunanin ta, Yau dai Jalila baki ya mutu, ko kwakwaran motsi takasa se kuka da kiran Ummi, duk yadda take tunanin abun ya wuce tunanin ta, seda Jalal fanshe soyayyar sa ta tsawon shekaru. Kaman ba Jalal din nan me mugun jin kai da hade rai ba. Bayan komai ya lafa Jalal ya rungume Jalila tsam a kirjinsa yana so yayi magana amma sam yakasa, a hankali taji jikinsa na daukar zafi fiye da kima, ganin yakasa magana yasa shi sakinta ya juya mata baya, Ji tayi kamar ana girgiza gadon da suke kai, juyawa tayi taga jikin Jalal ne yake karkarwa, ta kai hannunta jikin sa taji kamar wanda aka hurawa wuta bata taba jin jikin dan adam yayi zafin haka ba. Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 6️⃣0️⃣113 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                     _MY FIRST NOVEL _ Da sauri ta janye hannunta daga jikinsa, da kyar ta mike zaune ta janyo rigarta ta saka, a hankali ta sakko daga kan gadon, dan duk wata gaba ta jikin ta ciwo take mata, ta kunna switch haske ya gauraye dakin gaba daya, ta kalli inda Jalal yake har yanzu karkarwa yake kamar wanda ake girgizawa, a hankali ta tako ta zauna a kusa da shi ta dan dora hannunta a goshin sa zafin karuwa yake fiye da farko, a hankali tace "Jalal meyake damunka ne?" Shiru yayi be ce komai ba, gaba daya jijiyoyin kansa kaman an kumbura su har jijiyoyin fuskarsa seda suka tashi, ta tashi ta debk ruwa a container da towel me kyai ta dinga tsoma towel din a ruwa tana shafa masa tareda karanto duk addu'ar da tazo bakin ta, bude ido yayi yana kallon ta, seda gaban ta ya fadi ganin idon sa yana caccanzawa kaman yadda ta taba gani yayi kwanakin baya, salati ta dingayi "Jalal ko Daddy zan kira ne?" girgiza mata kai yayi ya mayar da idonsa ya lumshe, MP ta dakko ta kunna karatun Alqur'ani ta dora akan mirror. Ta cigaba da shafa masa ruwa, a hankali jikin sa yafara sanyi ya fara sauke ajiyar zuciya alamar bacci ya dauke shi, seda ta tabbtar yayi bacci ta mike ta tafi toilet dan gyara jikin ta, ji take kaman zata fadi gaba daya jikin ta babu kwari, ga ciwo da jikin ta yake mata, ta gargasa jikinta da ruwan dumi ta fito ta canza kaya, ta koma gurin Jalal ga mamakinta taga ya mike zaune amma har yanzu idonsa wani iri, takarasa gabansa tace "Sannu ya jikin naka?" Kallon ta yayi yai shiruu kaman wanda akayi wa dole yace "zan sha giya" "giya kuma? Amma kasan gidana ba club bane ko?" Kokarin mikewa ya keyi tai sauri tace "tsaya ina kuma zakaje? Bari in dakko maka ai inada ita" Ya nemi guri ya zauna, ta fita ta dakko zamzam ta dawo ta tarar ya kashimgida idonsa a lumshe tace "bude bakinka" ba musu ya bude ta fara zuba masa zamzam din nan me dauke da tofin Al'qur'ani a ciki ya dinga sha ba tareda yasan menene ba, seda ya shanye shi tsaf kawai yafara Tari abu kaman wasa ya dinga tari kaman ze shide, zuwa jimawa kuma yafara amai, wani irin abu yake amayarwa baki kirin me kauri, tun Jalila na iya gogewa ta gyara gurin harta gaji ta zubawa sarautar Allah ido, ta koma gefe ta zuba masa ido tana hawaye. Seda Jalal ya kusa fita hayyacinsa gaba daya, ya dinga aman nan ba kakkautawa, sedai in yayi yayi, ta goge, yayi awa yana aman nan baya hutawar minti biyar beyi wani aman ba. Ba Jalal ba hatta Jalila ta galabaita, ga wahalar da ta sha a hannun Jalal shikuma ga wannan rashin lafiyar, da aman ya dan lafa masa ta dakko zuma   ta dinga bashi da spoon yana karba. A hankali ta kira sunan sa "Zaujee" juyo yayi ya Kalle ta idonsa ya koma normal yace "Na'am my love" "ya jikin naka? Kana jin wani aman ne?" Girgiza mata kai yayi yace "A'a bana jin aman yanzu" "Masha Allah, yanzu yakamata kaje kayi wanka" Ya Kalle ta ya dan kashe mata ido yace "wankan me zanyi?" Jalal kenan yana fama da kansa amma tsokanar Jalila yake, ta tura baki tace "nima ban sani ba" Murmushi yayi yai kokarin mikewa amma yaji jira yana dibarsa, ya dake ya dafa bango, cikeda damuwa Jalila tace "Zaujee anya bazamu tafi Asibiti ba kuwa? Na tsorata da abunda ya sameka fa" "ba se munje ko'ina ba aina warke, karki damu zan shiga inyi wankan im fito" Haka ya dake ya nufi toilet, Amma gaba daya jinsa yake wani iri garin yana juya masa, kan ya fito Jalila ta tattara kayan da ya bata da amai ta tafi toilet din parlor ta wanke su tas, ta canza bedsheet ta dakko masa wasu kayan, ta kunna burner ta saka turaren wuta saboda karnin aman da yayi, Jalal ya jima a toilet be fito ba, dan yana shiga toilet din yaji wani aman, ya kunna shower yadda Jalila bazataji karar aman da yake ba, gaba daya tausayin ta yake ji, be so wannan dare yazo musu a haka ba, wannan karon hadda jini a cikin aman da yayi. Jin shirun yayi yawa yasa Jalila tazo kofar toilet din tai knocking tare da fadin "Zaujee ya na jika shiru ne? Lafiya dai ko?" Ya galabai ta amma cikin karfin hali yace "lafiya kalau, kiyi kwanciyar ki yanzu zan fito" Maimakon ta kwanta guri ta samu ta zauna a bakin gado tana jiran sa, seda aka jima sannan ya murda kofar toilet din ya fito jikinsa daure da towel, da sairi ta nufo shi tace "Jalal Allah yasa ba aman ka kuma yi ba, gaba daya kammaninka sun canza dare dayan nan baka ga yadda ka rame ba" Dan Murmushi yayi mata yace "Ashe haka ake sona aka damu dani, nace karki damu ban kuma aman ba ai, wanka nayi na fito" Haka ta kyaleshi ba dan ta yadda ba, ya tsane jikin sa ya dauki jallabiyar da ta dakko masa ya saka, ya haye kan gado amma ga mamakin ta ya kai hannu ya kashe MP din da amon karatun Al'qur'ani ke tashi. Kallon sa tayi cike da mamaki tace "ya haka kuma? Meyasa ka kashe?" "Naki nake son ji, ke zaki karanta min da sautin muryarki me narkamin zuciya ya sani nutauwa har inyi bacci" Jalila idon ta har mannewa yake saboda tsabar gajiya da baccin da take ji, Amma haka Jalal ya kwanta a jikin ta, ta fara rero karatun Al'qur'ani cikin suratul Ibrahim da muryarta me dadin sauraro, ta nayi tana shafa sumar kansa. lumshe ido yayi yana sauraron ta, bacci ne ya dauke Jalal, Abunda ya firgita Jalila be wuce ganin hayaki na fitowa daga hancin Jalal ba. "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un" shine abunda Jalila keta nana tawa, ta shiga jero dukkan Addua da ta zo bakin ta, shikam Jalal kara kankame ta yayi yana baccin sa. A hankali hayakin ya dena fita, mamaki ne ya cika Jalila, ta yaya Hayaki ze dinga fitowa daga jikin dan adam haka? Tana cikin tunanin ne bacci barawo yayi awon gaba da ita ba tareda ta shirya hakan ba. Ko da Asuba Jalal ne ya tasheta daga bacci, da kyar Jalila ta iya tashi tai salla, da ta idar da sallar ko Addua ba tayi ba ta kwanta akan sallaya ta cigaba da bacci, seda Jalal ya dawo ya same ta akan dadduma a kwance tana bacci, carbin hannun ta ya zare wanda hakan ya sata bude ido Jalal yace "kin kwanta a kasa se wuyanki yayi ciwo ko? Tashi muje ki kwanta" Hamma tayi tareda yin miki cikin muryar kasala da jin bacci tace "Zaujee ya jiki?" "Aina warke ni, kece baki da lafiya tashi muje ki kwanta" Mikewa tayi Jalal ya rike ta ya cire mata hijjabin, har kan gado ya kaita ya kwantar da ita, tana kwanciya bacci ya kuma dauke ta, zama Jalal yayi ya kura mata ido, gaba daya tausayin ta ya kama shi, ta sha wahala sosai, dan murmushi Jalal yayi yace "Babyn Ummi ta girma, Allah karka bani ikon cutar da wannan baiwar taka ko da kiftawar ido" Ya rungume ta a jikin sa yana shafa gashin kanta. Ilham kam kwanan ta biyu bata gida, ta cewa Mummy za taje gidan su, Amma ba gidan ta tafi ba gurin malamin da umman ta kwatanta mata, can boarder tsakanin Nigeria da kamaru, a can ne malamin da ya yiwa Jalal Asiri yake, taita bugun cikin umman nata tana bata Labari, ta shirya ta tafi. Mummyn Jalal tana zaune tana breakfast aka kira ta a waya, daga wa tayi tareda yin sallama "salamu Alaikum dan Allah Hajiya khadija ce?" Mummy tace "eh nice" "Dama Umman Ilham ce aka wayi gari takasa tafiya, bakin ta ya karkace an kaita Asibiti amma babu kowa a gurin ta" "Subhanallah, ina Ilham din?" Me kiran wayar tace "Ilham bata nan" Mummy tace "shikenan nagode" Gaba daya jikin Mummy rawa yake yi, ta tafi part din daddy bacci yake ko farkawa beyi ba ta tashe shi. Daddy ya tashi yace "deeja lafiya kuwa? Yana ganki a haka?" Cikin damuwa tace "Daddy, Saudat na Asibiti wai ba ta iya tafiya bakin ta ya karkace" "Subhanallah wani Asibitin ne?" "Nima ban sani ba sedai muje mu gani" Haka suka shirya suka tafi gidan Saudat daga can aka gaya musu Asibitin da take suka tafi. Koda sukaje Asibitin idonta biyu an sama ta ruwa, bakin ta ya karkace se zubar da yawu take, fuskarta duk ta kumbura, ta kara duhu kafafun ta kamar an shanye, gaba daya halittun ta sun sauya kamar ba ita ba. Khadija na ganin ta ta fa she da kuka tana fadin "Saudat meye sameki haka? Garin yaya haka ta faru dake?" Babu baki sedai ido da take binsu da shi, Mummy tai kuka har idon ta yayi jawur. Daddy ne ya dinga rarrashin ta Yace "Wai ina Ilham ne?" Se a lokacin Mummy ta tuna bata ga Ilham ba, waya ta dakko ta kira Ilham, ta kira ya kai sau biyar sannan ta dauka Mummy tace "Ilham kina ina ne?" "ina gidan mu mana" A fusace Mummy tace "karya kikeyi, gamu a Asibiti tare da Mahaifiyar ki an kwantar da ita ba lafiya" Da sauri Ilham tace "na shiga uku, Meya same ta?" "ban sani ba, gidan ubanwa kika tafi" Kuka Ilham ta fara yi tana fadin "shikenan na makara, dan Allah meya same ta?" "in kinzo kya gani" Se shadaya na safe Jalila tai juyi ta farka daga bacci da sauri ta sakko daga kan gado tana fadin "Subhanallah" Jalal baya dakin ya fita Toilet ta tafi tai wanka tai brush, ta fito ta gyara gadon sannan ta fito parlor. Koda ta fito Jalal yana danna waya ya dago ya kalle ta yayi murmushi, seda ta dan tsorata da ganin Jalal, ya rame sosai idonsa yayi zuru zuru, Jalal ya taso ya riko hannun ta zuwa kan kujera, ya zaunar da ita yace "good morning my Angel, ya jiki?" Dan murmushi tayi tace "Lafiya ta kalau ai kai zanyi wa ya jiki?" "Kin tabattar lafiyar ki kalau?" yai maganar yana kashe mata ido. Tura baki tayi "ni cikanizaka canza min magana, baka tashe ni ba gashi rana tayi bamuyi breakfast ba, ya kake ji a jikin ka yanzu ka rame sosai wallahi, na damu sosai da halin da ka shiga jiya" Jalal yace "gani nan dai wallahi Jalila ji nake kaman bacci nayi na tashi, gani nake duk abunda ya faru a baya kamar a mafarki, kamaman an sauke min wani nannauyan abu da yake rinjaya ta a kaina, ko kuma dutse haka nake ji" Jalila ta rike hannunsa tace "Jalal yakamata mu tashi tsaye anema maka magani, nifa jiya hayaki na gani yana fitowa daga hancin ka fa" "Hayaki kuma?" ya tambaye ta "Eh hayaki, hayaki nagani yana fita daga hancin ka jiya kana bacci" Jalal ya kyalkyale da dariya yace "i see that you enjoyed yesterday night, bacci ya miki dadi in ba haka ba ta yaya hayaki ze fita a hanci na, mafarki kikayi" Jalila kaman za tai kuka tace "Jalal ba fa abun wasa bane" Ya dan Harare ta yace "bazaki dena cemin Jalal ba ko?" "Yi hakuri bazan kara ba, Amma ka dau magana ta da mahimmanci" "Jalila ki kyaleni da maganar na, yanzu na dafa tea na siyo bread bari in dakko muyi breakfast" Riko hannun sa tayi tace "To ko Asibiti muje a dubamin kai, ka rame da yawa jiya ka sha wahala sosai, ni nayi mamaki ma da ka iya tashi har kake harkokin ka" Dan noke kafada yayi kaman wani karamin yaro yace "Kece likita na ai, ni ba Asibitin da zanje lafiya kalau nake jin jikina, bayan abunda ya shiga tskanin mu ji nake kaman nasamu wani immunity ne daga gareki, gayamin meye sirrin" Hannayen ta biyu tasa ta rufe fuskarta tace "dan Allah ka dena wannan zancen, ni ka dakko mana kayan breakfast din ni yunwa nake ji" "Dole inyi wannan zancen, Jalila ba haka naso daren jiya ya zo mana ba, Amma babu yadda muka iya da kaddara, A koda yaushe kokarin ki shine ganin kin tabattar da farinciki a cikin rayuwa ta, dukda yanayin da kika kasance a jiya be hanaki nuna tausayi da jin kai a gareni ba, Jalila " ya karasa maganar da kiran sunan ta, ta dago ta Kalle shi "Allah ya saki a madaukakiyar Aljannah, kada Allah ya kawo second din dan zan cutar da ke a rayuwa ta, ina kaunar ki Jalila" Ta amsa da "Ameen" Ya kai bakinsa kunnen ta yace "you deserve a gift from me in return of what you gave me yesterday" Idan har ta biye wa Jalal ba zasu karya ba, gashi yanzu sha biyu saura, ba shida niyyar sassauta kalaman da yake zubowa, ture shi tayi ta mike taje ta hado kayan breakfast ta ajiye a gabansa. Haka sukayi breakfast cike da nishadi da kaunar juna. A haka cikin hirar ta su, Jalila take bashi labarin irin miyagun mafarkan da ta dinga yi akan sa a lokutan baya. Jalal ya sha mamaki yace "that's why I said our souls are destined to be together, ke garkuwa ce ga ABDUL JALAL" Wayar sa ce ta fara ringing, ya sa hannu ya dauka Muryar Daddy yaji dan haka ya kara nutauwa suka gaisa. Daddy yace "Jalal muna Asibiti fa" "Asibiti kuma Daddy waye ba lafiya?" "maman Ilham ce, bata da lafiya sosai bata san waye akan ta ba, yakamata in ka samu lokaci kuzo ku duba ta" Jalal yace "Allah ya bata lafiya Amma bazan zo ba" Daddy yace "Jalal meya sa kake hakane? Narasa me baiwar Allah nan tayi maka ka tsane ta, rashin lafiya ce kuma bata wuce kan kowa ba, At least in kazo ka duba ta mamanka ma zata ji dadi, tunda muka zo ta kasa sakewa tana ta kuka ne" "Daddy idan fa nazo bani zan bata lafiya ba, kuma bani na dora mata ba, meye dole sena zo, nima bani da lafiya fa, dan Allah kayi hakuri kayi mata sannu Allah ya sawwake" Jalal ya kashe wayar sa, girgiza kai Daddy yayi yace "Allah ya shirya" Mummy dake gefe tace "Kaima kasan baze zo ba, da dai kanwar uwar Jalila ce ze tafi ko bangon duniya ne a kafa, ai na riga nasa masa ido yaje yayi abunda ya ga dama tunda bani da mutunci a idonsa, na barwa Jalila shi dadi mata yaje yai duk abunda yake so kafin in waiwayeshi" Daddy yace "deeja bana son wannan maganganun da kike yi fa, ina ruwan Jalila a cikin wannan abun? Naga tun kafin ya auri Jalila basa wani jituwa da Ilham da mahaifiyar ta, kuma in kikayi hakuri watakila kiga yazo, amma be kamata komai Jalal yayi ki dora alhakin akan matarsa ba" "Eh dole kace haka mana tunda kai ka aura masa ita, da Ilham ya aura nasan duk wannan bakin cikin da ban ganshi ba, yanzu se 'yar mulki taga dama tasa baki sannan zezo" Mikewa Daddy yayi yace "Sekuma kiyi ke ka dai, ni zan wuce gida" Dauke kai tayi tai masa banza har ya fice daga Dakin Jalila tace "Zaujee waye ba lafiya ne?" Dan bata rai yayi yace "wai babar su Ilham, shi kuma Daddy wai inje in duba ta, in duba ta ince mata me? Nima ba lafiyar ce dani ba ai" "haba Zaujee meye a ciki dan munje mun duba ta? Dan Allah zakayi kuma Mummy zataji dadi, Akwai lada me yawa a ziyarar mara lafiya, karka duba wai tayi maka wani laifi kowani abu ka duba girman Allah da manzon sa, duba mara lafiya umarnin manzon Allah ne salallahu alaihi wassalam, kuma koyi da sunnar sa ne, zuwan ka da rashin zuwan ka baze canza komai ba, Amma mara lafiya zeji dadi kai kuma zaka samu lada" "idan na dau carbi ma kona karanta Al'qur'ani zan samu lada" Jalila tai murmushi tace "Annabi salallahu alaihi wassalam yasan da hakan yace muyi zumunci, kuma yace muje ziyarar mara lafiya, please Zaujee ko minti kadan ne muje a duba ta" "to naji amma se nayi shawara" "haba mijin so be kamata kayi jinkiri a aikin lada ba, a temaka zuwa gobe in Allah ya kaimu muje" "shikenan Allah ya kaimu goben lafiya" "Ameen ya Allah, ko kai fa har naji dadi" Mummy duk ta sanar da 'yan uwa abunda ya faru, ana ta zuwa duba ta, Se bayan isha'i Ilham tazo Asibitin nan, gaba daya ran Mummy ya gama baci, Ilham na zuwa Mummy ta rufe ta da fada "wai daga gidan ubanwa kike? Tun jiya mahaifiyar ki bata da lafiya amma ba kya gida, ina kika tafi?" Ko sauraron Mummy Ilham ba tayi ba ta nufi gadon da Umman ta ke kwance, tana zuwa taga yadda kamanin Umman ta suka koma, ja da baya tayi ta fasa ihu tana fadin "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, munshiga uku, wayyo Allah na umma meya sameki haka? Shikenan komai ya warware a haka zaki zauna kenan? Na shiga uku Umma na" Mummy tace "Ilham kiyi hakuri mana, dare ya fara yi ga marasa lafiya kiyi hakuri, likitoci sun bada tasa tasai duk anyi amma sunce basu ga komai ba, ni ban san meya same ta haka ba" Banza Ilham tai mata ta cigaba da kurwa tana surutai. Wajen goma Mummy ta tafi gida, ta bar kanwar Saudat da Ilham a gurin ta. Da safe Jalila ta lallaba Jalal suka shirya suka tafi Asibiti domin su duba mahaifiyar Ilham. Da sukaje Asibitin Jalal ya kira Daddy a waya ya kwatanta masa dakin da aka kwantar ds ita, koda sukaje Daddy yana nan ya kai Mummy be tafi ba. Mummy na ganinsu ta hade rai kaman bata san wani abu dariya ba, Jalila tana gaisheta amma ta dauke kai. Jalila ta gaida Daddy sannan suka gaisa da 'yan uwan Mummy dake dakin Jalal ya nemi guri ya zauna ya dora kafa daya kan daya ba tareda ya kula kowa ba yace "Mummy ya me jiki?" Daga ido Mummy tayi ta kalleshi tace "Uwar taka ta barka kazo kenan?" "wa kenan"? Jalal ya tambaya "Matar ka mana" Cikin ko in kula Jalal yace "Badan Jalila ta takura ba babu abunda zesa inzo duba wannan matar wallahi, Allah ne ya tashi kamata shiyasa ya maida ita haka" Daddy yace "deeja bana son irin wannan abubuwan, daga zuwa dubiya kin fara surutai ga mara lafiya a kwance" Daddy na cikin fadan ne Ilham ta shigo dakin hannun ta dauke da ledar pharmacy, tana ganin su Jalila tayi jife da ledar ta nufi Jalila tana zazzaro ido tana magana cikin ihu Jalal yai maza ya mike yasa Jalila a bayan sa "Wallahi baki isa ba Jalila saboda ke koma meye ya samu mahaifiya ta, wallahi kema bazaki rayu cikin dadin rai ba sekin wulakanta kuma sena ciki burin mahaifiya ta koda hakan yana nufin rasa raina" Jalila ta fito daga bayan Jalal tace "Ilham har yanzu baki hankalta ba ko? Abunda ya sameki be zama darasi a gareku ba? Ashe kuwa zaki kare rayuwar ki a wahala, zuwa yanzu ya kamata ki san baki da abunda zaki iyayi ki cutar dani, wallahi Ilham na miki zarra kuma na riga na miki illa, ya rage naku ku nemi yafiyar wanda kuka cutar, ko Allah ya sassauta muku wannan iftila'in, bakar aniyarki da ta mahaifiyar ki ce ta koma kanku, yanzu seki dau damarar zaman jinya, dama shi Allah ba Azzalumin sarki bane" Cikin ihu Ilham tace "wallahi karya kike kiyi galaba akaina, sena kasheki na kashe Jalal din" Jalila tace "sedai ki kashe kanki, Allah maji rokon bawa, Allah be bar gwagwarmayar da nayi a banza ba, Allah ya shiryi mijina kuma ina miki albishir da abunda kukayi masa ya bar shi" Ganin Jalila ta fara daukar zafi yasa Jalal janye hannun matar sa sukayi waje. Mummy da Sauran 'yan uwansu da ke dakin kam daskarewa sukayi suna mamakin irin musayar kalaman da suka shiga tsakanin Ilham da matar Jalal me hakan ke nufi? Mummy tace "Wai Ilham ban gane inda maganganun nan suka dosa ba?" A fusace Ilham tace "dalla malama khaleni, kece silar komai, kece sanadiyar shigar mahaifiya ta wannan halin wallahi bazan yafe miki ba makira maci amana, kuma wallahi kema sekin ga yadda karshenki ze kasance. Wata Jaka Ilham ta dakko a cikin jakar ta ta zazzage a gurin, layu ne da wasu tarkacen kayan shirka hada bawan kwai dauke da sunan ABDUL JALAL Share please 07063065680 What's App only Watpad Ayshercool7724                                     🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 6️⃣1️⃣115 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                     _MY FIRST NOVEL _ Mummy tace "kai gidan Jalal fa nace zaka kaini" Driver ya ƙara risina kai yace "eh Hajiya shi din fa, Jiya da daddare yazo layin nan shida matarsa, yace inje in kaisu filin jirgi yau, ɗazu na dawo daga kaisu" Bata tsaya ta ƙarasa ji ba ta koma cikin gida kirjin ta yayi mata nauyi take tambayar kanta "wace irin tsana Jalal yayi min har yazo layin nan ya tafi be ganni ba, be leƙo mun gaisa ba? Yazo shida matarsa suje gidan su matar sa amma suka kasa shiga su gaisheta, take ta kara jin wata muguwar tsanar Jalila tasan tabbas wannan makircin Jalila ne" Da ta sake tuna cewar Daddy zeyi aure setaji gaba ɗaya duniyar tayi mata zafi, tarasa me yake damun ta, kowa ya guje ta ya juya mata baya ciki hada dan cikin ta, ga dukiya tari guda, dukiyar da take ta hari tana kwaɗayi gata nan a jibge amma sam yanzu hankalinta ba'a kan dukiyar yake ba, da anjima kuma idan ta sake tuna irin masifar shaye2 da Jalal yayi, da yadda take riƙe da Ilham kaman ita ta haifeta ta tuna Abunda Saudat ta aikata mata se taji kaman a duk duniya ita ka ɗai aka tsana tarasa me zatayi taji daɗi, bacci ya ƙauracewa idanun ta, bata jin yunwa ma balle tasaka ran zata ci Abinci, idan tasa Abinci a gabanta za taci kuwa ji take babu test babu daɗi, bata da aiki se tunani da koke koke, Ankwace mata miji, wata ta kwace mata ɗanta ɗaya tilo se yadda tayi da shi, gashi 'yar uwatta data yadda da ita taci amanar ta tayi mata cutarwa mafi muni, ga ba wanda yake son rabarta saboda izzarta da jin kai da wulaƙanta mutane, nan da nan abubuwa sukayi mata yawa, ta fara fama da wani matsanancin ciwon kai da yake sakkowa har wuyan ta ko gani bata iyayi sosai, tunda Daddy ya tafi ko message be mata ba balle ya kira ta, saɓanin da da idan ya tafi se suyi waya sau biyu zuwa uku, yanzu ya tattara ta ya watsar ya shiga harkokin sa da shirye shiryen maida Auren sa. 7 hours cif su Jalila suka shafe ana tafiya a jirgi sannan suka isa London babban birnin England, Jalila ta gaji sosai tun ana tafiyar ta marmari tazo ta gaji, ta fara yamutsa fuska daga karshe ta kwanta a jikin Jalal tai bacci. Jalal ya tashe ta suka sakko daga jirgin, yanayin weather garin ce ta tabattar mata lallai ta baro Nigeria, wani irin sanyi ne me ratsa jiki taji yana dukan ta, ta ɗaga kai tana kallon yanayin garin dukda dare ne amma tasan akwai banbanci da gida Nigeria, komai nasu cikin nutauwa da tsari, bayan sun gama clearing komai Jalal ya ja hannun ta sukayi gaba, wajen wata mota suka nufa kafin su karasa inda motar take aka bude motar na cikin motar ya fito. Mahmud ne mijin Nana yazo ɗaukar su. Cikin fara'a yace "Sannunku da zuwa bros nasan kun sha hanya, da ganin idon Jalila a gajiye take" Jalal yace "wallahi kuwa a gajiye take sosai, muje ka kaimu gida seta huta gaba ɗaya" Seda suka shiga motar sannan Jalila ta samu damar gaisawa da Mahmud har take tambayar sa Nana, dan a gajiye take sosai ga sanyi da a take ji gaba ɗaya ta dunƙule guri ɗaya a jikin Jalal. Ya kaisu gidan daya kasance nan ne masaukin su, ya kawo musu Abinci daga gidansa sannan yai musu sallama ya tafi. Jalila dai wanka tayi da ruwa me zafi ta shafe jikin ta da mai tasa ka kayan sanyi dan ta rage sanyin da take ji, shikam Jalal ko a jikin sa dan shi ya saba. Lumshe ido yaga tana yi alamun bacci take ji Yace "matar yakamata kici Abinci kafin kiyi bacci" Tayi miƙa tare da tura baki gaba tace "ni ka nunamin ɗakina bacci nake ji" "A waje zaki kwana idan baki ci Abinci ba" Ya takura mata ya zuba Abinci ya zauna ya fara bata a baki, ji tayi gaba ɗaya Abincin babu daɗi, amma ta daure kar Jalal yaji babu daɗi taci kaɗan tace ta ƙoshi, shima be wani ci dayawa ba ya ajiye sukayi shirin kwanciya. A zaton Jalila Jalal ze saurara mata ganin gajiyar tafiya da suka sha, amma tun a lokacin ya fara nasa honeymoon din, da ƙyar ta samu tai bacci Jalal ya tara mata wata gajiyar da bata shirya mata ba. Abun mamaki Jalila se juyi tayi taga Jalal baya ɗakin, tsoro ne ya kamata ta tashi zaune tana rarraba ido, can se gashi ya shigo ya dube ta yace "ba'a yin salla ne? Ko baki san Asuba tayi ba?" Cikin tsiwa tace "Eh bana yi shiyasa jiya ka...." se kuma tayi shiru, dariya Jalal yayi yace "ƙarasa mana, ya kika yi shiru?" Ta ɗan murguɗa baki tace "bazan ƙarasa ɗin ba, Amma dan Allah ina kaje ne? Nifa har na tsorata" "Sarkin tsoro, naje masallaci ne" "Masallaci kuma? Dama akwai masallaci a wannan ƙasashen" "Akwai masallaci hada na juma'a, ai suna da musulmi suma, akwai musulmi sosai a unguwar nan" Jinjina masa kai tayi ta sakko taje tayi alwala tazo ta tayarda sallar Asuba. Gari yayi haske sosai amma Jalila ba ta dena jin sanyi ba har yanzu, Yanzu ma Mahmud ne ya kawo musu Abincin safe suka gaisa sannan ya tafi, da Jalila ta fito tana kallon yanayin tsaruwar gidan, ba irin fasalin gidajen mu ne na Nigeria ba, hotunan Hajiya Salma ta gani a falon da su Mahmud tace "Zauje nan gidan Anty Salma ne?" "Eh gidan ta ne, a nan Ummi tayi jinya ma gidan mijinta ne da ya rasu, Lokacin da yayi jakadanci anan aka bashi wannan gidan" Jalila ta jinjina kai tace "to yana ga ban ganta ba?" "ta tafi Maiduguri, Ranar Friday za'a maida Auren ta da Daddy, zata koma can Dubai gurin Daddy" Jiki a sanyaye Jalila tace "dama dagaskene Daddy ze maida Auren nan? Allah sarki Mummy koya za taji? Dama baka bawa Daddy wannan shawarar ba, da ka bari da kansa in yayi niyya ya maida ita" "Baby look, Daddy yayi haƙuri a zamansa da mahaifiya ta ni na sani, girma ya fara kama shi ya kamata ace ya huta, Mummy mahaifiya ta ce, Amma Soyayya kawai ta iya amma bata san wani abu respect ba, kuma Ya kamata Daddy ya maida Anty Salma saboda hakan shine dai2, yana son ta har yanzu, ko kin manta tun farko gidan tane Mummy ta shiga ta fidda ita? " "Hakane Zaujee, Amma kishi babu daɗi, akwai ciwo me raɗaɗi" "Jalila karki zama me son kai ban sanki da haka ba, Mummy a yanzu bata bukatar a tausaya mata, kamata yayi ta karɓi horo akan abunda ta aikata daga duniya" "A'a zaujee, Macen da ta rasa soyayya da biyayyar ɗanta ya kamata a tausaya mata, please zaujee ka yafewa Mummy ka bata haƙƙinta na mahaifiyarka" Ɗan lumshe ido Jalal yayi ya buɗe yace "Jalila a shirye nake da na karɓi mahaifiya ta in danne zuciya ta in manta da abunda ya wuce, Amma Abunda nake nuna miki har yanzu Mummy ba ta ɗau darasi ba, yanzu ina raɓarta zata fara kawo min abubuwa na son zuciya ta tursasni tace se nayi, ni kuma bazan biye wa son zuciyar ta ba, Jalila duk lalacewar ɗa yasan uwar sa, ko lokacin da nake shaye2 ina kaunar mahaifiya ta halayen ta ne bana so, sune suke ɓata min rai, halayen ta ne suka sa nake gudun ta ko inda take bana son zuwa, ko yau Mummy ta dena halayen ta marasa kyau zan mata biyayya, sedai bazanyi biyayya ga abunda nasan ze cutar dani ba" Jalila ta yunƙura za tayi magana Jalal ya katse ta ta hanyar ɗora yatsan sa akan lips ɗinta yace "bana son jin wata magana, muci Abinci" Haka Jalila tayi shiru ta kyaleshi. Seda suka kwana huɗu sannan Jalal ya kai Jalila gidan Nana, babu nisa da inda suke da ƙafa sukaje. Nana tayi matuƙar farincikin ganin su, da ƙyar Nana take tafiya cikin ta yayi nauyi sosai. Nana tace "Yaya Jalal tun ranar da kuka zo nake zuba ido amma baku zo ba se yau" Jalal yace "yanzunma ba daɗewa zamuyi ba kuje minti biyar kawai ku gaisa zamu koma gida" Mahmud yace "Haba dai brother ai ba zamu cinye maka ita ba" yai maganar yana murmushi Suka dinga hira kaman wanda suka yi shekaru basu haɗu ba. Jalal da kansa ya bawa Mahmud labarin abunda ya faru a Nigeria. Nana ta kaɗu da jin abunda Ilham sukayi ita da Mahaifiyarta, Nana tace "Allah sarki ashe shiyasa bata son Jalila ta tsane ta, kullum cikin faɗa suke" Mahmud yace "Ai brother ka Auna Arziki, dama da mamaki ace lokaci ɗaya fa ka canza gaba ɗaya aka kasa gane kanka kasha wahala" Jalal yace "munsha wahala dai, dani da Jawwad da Jalila, wato idan ina tuna wasu abubuwan da Jawwad yayi min a rayuwa har tunani nake anya Jawwad ba waliyyi bane? Jawwad ya wuce aboki a gurina, jinsa nake tamkar wani ɓangare na rayuwa ta, ya bani gudunmuwa a rayuwa ta, uwa uba matar so 'yar Aljanna wato wani abun idan na kalle ta har mamaki nake yi a ƙarancin shekarun ta ba kowace ƙwaƙwalwa ce zata iya tunani irin nata ba" Sun sha hira sosai wuni sukayi a gidan Nana se dare suka tattaka suka koma nasu gidan. Zuwansu ƙasar nan ba karamin yiwa ma'auratan daɗi yayi ba, suna more soyayya yadda suke so, Jalal ya kai ta gurare da dama na shaƙatawa da buɗe ido, wata irin soyayya yake nuna mata me cike da ban sha'awa, yayin da ita ma take dukkan ƙoƙarin ta gurin ganin ta faranta masa rai, gaba ɗaya sun manta da damuwar da suka baro a Nigeria, babban abunda yake damun Jalila be wuce yadda ba ko yaushe take samun irin Abincin da take so ba. Kamar yadda Daddy ya faɗa ranar Friday ya maida Auren sa da Hajiya Salma, Mummy tana kwance tana fama da kanta wata ƙawarta wadda tasan wasu a family su Daddy ta kira ta, ta sanar da ita Auren Daddy hada bata labarin abunda Jalal da danginsa sukayi wa  mahaifiyar Jalila ai Mummy bata gama jin kanun labaran ba ta ajiye wayar ta miƙe zaune, kamar wata mara hankali ta kuma Janyo wayar ta hau danna lamabar Jalal amma seta tuna ba zata shiga ba tunda baya ƙasar, kenan ta tabbata Daddy yayi aure? Ji tayi numfashin ta yana sama yana ƙasa kaman ze ɗauke gaba ɗaya, ta lalubi wayar ta ta kira likita. Kusan awa guda kafin likitan tazo, "kiyi haƙuri Hajiya Khadija muna kan wani aiki ne shiyasa banzo da wuri ba, me yake damunki ne?" Mummy babu baki sedai Nuni, likitar tayi gwaje gwajen da ya dace ta gano jinin Mummy yayi mummunar hawa, idan bata kula ba idan ta faɗi zata iya samun shanyewar ɓarin jiki. Ta zauna taita bawa Mummy shawarwari amma sam Hankalin Mummy baya kan likita harta gama surutan ta tai mata allurai Mummy bata san me likitan tayi ba, ita dai tasan tana cikin tunani bacci ya kwashe ta. Ilham an sallami mamanta daga Asibiti saboda ciwon ta bana Asibiti bane, Ilham tattar duk abunda suke dashi tana kai Umman ta gurin wasu 'yan tsibbun ko zasu dace amma abu yaƙi, daga ƙarshe ta ɗauki umman ta zuwa gurin wanda yayi Asirin farko shima ya tsufa sosai ko gani baya iyayi ya bayyana musu cewar "Yawan karatun Al' qur'ani da kuma, zumar da Jalila ta dinga bawa Jalal ce ta illata Aljanin, sannan Jalila tana da tsari a jikinta sabo da riƙo da Al'ƙur'ani, shiyasa Aljanin ya samu nakasa kuma ya koma jikin Saudat, da an karya Asirin kafin Jalal ya haɗa shimfiɗa da Jalila da baze koma kan umman ta ba" Ilham tace "Yanzu babu wata dabara ko wani abu dazaka iya yi mana akan wannan larurar" "yarinya babu wanda ze iya yiwa mahaifiyar ki komai, sedai kukoma ga Allah ku zuba mata ido a haka, duk wanda yace ze muku magani ƙarya yake yi, tun a baya da yarinyar nan ta fara bibiyar sa na nusar daku, Amma kuka gaza ɗaukar wani ƙwaƙwaran mataki, yanzu se dai kuyi haƙuri" Haka Ilham ta tattaro suka dawo gida, ba wani me basu wani taimako musamman idan akaji abunda sukayi, yayan Ilham yana prison baban su kuwa idan ya shura ya bar gida se ya shekara uku be zoba, ga dangi da 'yan uwa dama ba wani jituwa ake ba, Saudat bata ganin kowa da mutunci dan haka ba wanda ya damu da halin da suke ciki, a hankali komai nasu ya fara ƙarewa saboda jinya, ga Ilham ta fara gajiya taita hantarar Umman ta wasu lokutan, idan tayi ba haya ko fitsari a zaune setai tafiyar ta ta barta a gurin se ta daɗe cikin najasa sannan tazo ta kula da ita. Abubuwa suka cakuɗewa Ilham abunda za suci ya fara nema ya gagare su, da dane da sedai tayiwa Mummy waya ta turo kuɗi, banda wanda zata sata ta kawo gida, se yanzu take dana sanin abunda tayi, da ta sani da ba ta ga yawa duniya su sukayi wa Jalal Asiri ba da koba komai baza su rasa Abunda za suci ba. Jalila tana kwance a jikin Jalal tana chatting taga surutun da ake a group ɗinau na makaranta yayi yawa dan haka ta sauka ta shiga domin ganin surutun me sukeyi haka? Sameera ce da Saleema 'yar gidan oga KB aka kuma kamawa a gidan karuwai suna aikata miyagun laifuka har an kaisu kotu an yanke musu hukuncin shekaru biyar a gidan gyaran hali. Da sauri Jalila ta miƙe zaune tace "Zaujee kaga" Ta nuna masa ya karɓa ya gani yace "Allah ya kyauta" Jalila tace "Zaujee Saleema 'yar Oga KB ce, shi yana prison itama yanzu zata tafi prison na ɗauka tun a wancan lokacin ta shiryu" Jalal yace "Jalila dan Allah karki saka damuwar wasu a ranki ki hana mana jin daɗi, shiyasa fa ban gaya miki su Hannah ma an kaisu prison ba, Sannan Jeje yayi rashin lafiya lungs cancer yai ta fama a prison ga rashin kula watansa guda da mutuwa, shima oga KB yana Aisbitin cikin prison paralyze ya kama shi" "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un" Shi Jalila ta dinga nanatawa ta kalli Jalal tace "Zaujee me Jeje zeje ya cewa Allah, mutuwa ake tsoro dama, Allah ya karɓeka ba zato ba tsammani ba tareda ka shirya mata ba, Allah ya jiƙan musulmi" "Ameen ya Allah, bance kuma ki zauna ki damu kanki ba, in kuwa naga kin damu na dena baki labari" "to bazan damu ba" ta faɗa a sanyaye, amma ƙasan zuciyar ta so take tayi kuka Seda sukai wata guda a UK sannan suka fara haramar tafiya, dama tana kewar Nijeriya sedai suyi waya da 'yan gida, ga shi tayi missing wasu abincin Nijeriya, dukda sun sha yawo sunsha soyayya sunyi ƙiba sunyi kyau daga ita har Jalal ɗin, sukaje suyiwa su Nana sallama. Jalila tace "Yaya Mahmud yaushe Zakabar Nana tazo Nigeria gara ta haihu a Nijeriya" Mahmud yace "Injiwa? Gara ta haihu anan semu taho Nijeriya" Jalal yace "Sarkin wayo so kake yaronka ya zama citizen ɗin UK kenan?" Mahmud yace "Ashe ka gane bros" Haka sukayi sallama suka koma gida, Washegari ƙarfe goma Mahmud yaje ya ɗauke su ya kaisu airport sukayi sallama shi yakoma. Maimakon  su sauka a Kano se suka sauka a Abuja gidan su Jawwad, Jalal be gayawa Jalila ba, ya dai ce mata ze kai ziyara Abuja sam bata kawo gidan su Hanan zasu ba. Tana ganin Hanan suka rungume juna, cikin Hanan har yafi na Nana fitowa da girma. Jalila taita tsokanar Hanan tana gwada yadda take tafiya, Jawwad kansa yaji daɗin ganinsu, gaba ɗaya sunyi ƙiba, Jalal kamar ba shine me yawo da Sarƙa, da askin banza a ka ba yayi ƙalau da shi ya zama babban mutum. Jawwad ya ja Jalal suka fice suka bar su Hanan a gida, dukda ranar suka sauka Amma Jalila seda tayiwa Hanan gyaran gida da sauran abubuwan da bata iyayi, saboda tana shirin zata koma gida haihuwa. Jalila se santin gidan Hanan take yi, ta fita ta ɗan zaga ta samu ƙanan guava sun faɗo ko nuna basu yi ba, take taji ranta ya biya ta tsinto tazo saka a leda ta jefa a jakarta, Hanan har mamakin ƙibar da Jalila tayi take "Jalila anya ba'a gamu ba kuwa? Kinga yadda kika zama wata uwar mata" Jalila tace "Aka gamu dame?" "ciki mana" Hanan ta bata amsa "An gaya miki kowa irinku ne, bani da komai hutawa ta nake" Hanan tai murmushi tace "to me yake hanaki cin Abinci se kin zaɓa?" Jalila ta ɗan yamutsa fuska tace "ke nifa ba abunda yake damuna, ni ba laulayi nake ba, bani da komai tunda muka bar Nijeriya komai ya dena min daɗi ne kawai Abincin su bana jin daɗin sa ne" Hanan ta ƙyale Jalila dan tasan ta da taurin kai. Kwanan su Jalila uku suka baro Abuja zuwa kano, Hanan kuma  ta tafi Bauchi a can zata haihu, tunda suka taho Jalal yake lura da Sam Jalila bata son Abinci se dai ciye ciyen shirme, ga bacci kamar wata kasa duk inda ta samu bacci, abu kaɗan ze mata ta fara kuka yanayin nata ya ɗan fara damunsa daya takura taci Abinci seta fara kuka ga yawan complain na ciwon ciki da take yi. Haka suka dawo gida, kwanan su biyu da dawowa Jalila ta matsa masa suje yaga halin da Mummy take ciki, ba dan yaso ba ya shirya da daddare suka tafi. Abunda ya basu mamaki be wuce yadda ta rame ba, da ƙyar take iya miƙewa ma bata da lafiya sosai. Duk tsaftar Mummy amma gidan duk yayi ƙura, ko magana bata iyayi. Suka ɗauke ta zuwa Asibiti, likitoci suka rufu akan ta saboda a galabaice take. Jalal suna reception suna jira, ya hango doctor Salis ya miƙe yaje suka gaisa cikin fara'a doctor Salis yace "Jalal keine ka koma haka? Kayi ƙalau da kai se jin labari nayi wai kayi aure daga kai har Jawwad ba labari" Jalal yace "Aini nawa Auren ne yazo ba shiri, Mummy muka kawo Asibiti babu lafaiya, kuma muna tare da madam ɗinma kuwa dan Allah ka dubamin ita na kasa gane kanta" Jalal ya nuna masa inda Jalila ke zaune tana danna waya, suka ƙaraso inda Jalila take doctor Salis yace "kai wannan ai Jalila ce, ita ka aura Jalal" "Eh itace" "Allah sarki ashe shiyasa aka dinga yimin hanya2 ashe kaine a gurin, masha Allah, Allah yasanya Alkhairi ya baku zaman lafiya" Suka amsa da Ameen Suka bi doctor Salis office ɗinsa ya tambayi Jalila me yake damun ta tace "ni lafiya ta ƙalau, wannaan gobar da nake ci ce baya so" Jalal yaiwa doctor Salis bayanin abunda take yi ya rubuta musu tests, yace suje lab ayi, da safe suzo su kawo masa  result ɗin. A daren aka fito da Mummy, likita yai musu bayanin cewar hawan jini ke damun ta kuma ya fara taɓa mata zuciya dan haka tana buƙatar kulawa, ba ƙaramin damuwa Jalila ta shiga daa jin hakan ba, a daren Jalal ya maida Jalila gida yace bazata kwana a Asibiti ba bata da cikakkiyar lafiya. Da safe Jalila tayi girki ta taho Asibiti bata jira Jalal yazo ɗaukar ta ba, da ta je ɗakin Mummy ba kowa a ɗakin, Mummy na kashingiɗe tana tunani, Jalila ta shigo da sallama tana gaida Mummy Amma Mummy tayi mata banza, Jalila ta zuba mata Abinci ta zauna a kusa da ita tace "Mummy ki daure kici Abinci seki sha magani" make plate ɗin Mummy tayi tace "ke wace irin mayya ce bazan ci ba, kina so ki ƙarasa ni kiji daɗin mallake min ɗa ko? To baki isa ba ki tashi ki bani guri" Jalila ta girgiza kai tace "Mummy wallahi ni bawani abu da nakeyi dan in mallaki Jalal, ina ƙoƙarine kawai inga ya gyara rayuwarsa, Amma wallahi ni ba wani abu da nake yi in mallake miki ɗa" Jalila na cikin maganar ne Jalal ya shigo ɗakin yana murna gaba ɗaya ya manta da Mummy a gurin yace "sweet heart yanzu naje gida ba kya nan, congratulations you are soon to be a mother" Kallon shi tayi da mamaki "mother kuma" "yes matar so you are 3 months pregnant" Mummy ji tayi kaman ta mari Jalal taji tamkar ya soka mata mashi a ƙirjin ta. Asalam Alaikum warahmatullah 'yan uwa da masoya masu nunamin ƙauna ina godiya, masu bina private in tura musu daga farko ina sakawa a watpad masu neman part2 kumin afuwa ku dinga tambaya a group abubuwa sunmin yawa nagode sosai da kawar ku Allah ya bar zumunci Vote, Comment and Share please I want comments not stickers or just thanks Daga alkalamin Aysher cool 🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️ What's app only 07063065680. Follow me onWatpad @Ayshercool7724          🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 6️⃣2️⃣116 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                     _MY FIRST NOVEL _ Jalila ji tayi kaman tayi tsuntsuwa ta gudu dan kunya, sam Jalal ko a jikinsa ya ci gaba da magana "Jalila na rasa me zanyi dan farinciki, ɗazu na karɓo result ɗin na kaiwa doctor Salis yace muje office ɗinsa nida ke" Jalila zata yi magana ya janyo hannun ta sukayi waje. Mummy ji tayi tamkar zuciyar ta tsage, a gaban ta ɗan ta yake rawar ƙafa akan wata mace alhalin ita baya wannan rawar ƙafar akan ta. Office ɗin doctor Salis sukaje, yana ganin su ya faɗaɗa murmushin sa, suka samu guri suka zauna, doctor Salis ta dube su yace "Congratulations once again Mr and Mrs Jalal, you are expecting your baby in the next six months Insha Allah, a scanning ɗinki cikin ki ya shiga wata na huɗu, ya akayi ke ba kiyi noticing kina ɗauke da juna biyu ba?" Ɗaga kai tayi ta kalli Jalal ta sunkuyar da kai. Jalal yai murmushi yace "ya zaki kalleni? Ki bada amsa mana" Shiru tayi ba tace komai ba, nan doctor Salis yaita counseling ɗinsu, tare da basu shawarwari kuma ya jadaddawa Jalal cewar se yayi haƙuri da wasu halaye da ze ga tanayi wanda ba tayi masa a baya, yanayin ciki ne zesata yin hakan. Sun kai kusan minti talatin a gurin doctor Salis, sannan ya rubuta mata magungunan da zatayi amfani dasu kafin ta fara zuwa awo. Suka baro office ɗin doctor Salis sam bakin Jalal ya kasa rufuwa saboda farinciki, ɗakin da Mummy take kwance suka koma. Jalila tace "ko zaka bawa Mummy Abinci da kanka na bata Abincin ta ƙi ci" Jalal yace "kinga ki ƙyale ta nima idan na bata baci zata yi ba haushi na take ji, tun ɗazu nake fama taƙi ci munyi waya da Daddy jiya anyi sa'a yana Maiduguri yace yau zezo" Jalila tace "A'a yakamata ka gwada mata ko yaya ta samu taci" "Ke wai ina ruwan ki dani ne? Dole ne bazanci Abincin ba cikin ki ko nawa? Kinibabbiya kawai" Tsawar Da Mummy tayi seda Jalila ta ɗan tsorata, Jalal yace "Wannan yana daga cikin abunda yasa bana zuwa gurin ki, yanzu me tayi miki dan kawai tace kici Abinci? Haba Mummy zuwa yanzu yakamata ace kindena irin wannan abubuwan da kike yi" "ka rufamin baki tun banci mutuncin ka ba, naji duk abunda ka aikata, uwar matarka ta fini tunda har ka iya ɗaukar ta aka fita da ita tai jinyar shekara biyar, ka sa uban ka ya maida tsohuwar matarsa saboda tana ƙaunar matar ka, yanzu ba ko kunya kazo gaba na kake faɗar matar ka tana da ciki, ka je kayi duk abunda kaga dama Jalal, indai kaine na sallamawa mace kai, kaje ta maida kai cikin ta tsabar ƙauna" Murmushi Jalal yayi yace "Mummy Allah yana son bayinsa masu godiya, idan yayi maka ni'ima ka gode masa seya ƙara maka, karki manta a baya ko kwatankwacin haka baki samu ba daga gare ni, kowa harkokin sa yake yi ba ruwa na dake, na rasa dalilin da yasa har yanzu baki ɗau darasin rayuwa ba, yanzu kome zan miki baki da taka maimai dalilin da yasa kike ƙina da Jalila, matar da kika so in Aura a baya Ilham kin gani da idonki abunda suka yi min, so sukayi su kassara rayuwa ta saboda ke, kin taɓa tunanin meyasa nake gudun ki nake kyautatawa wasu? Idan duniya da gaskiya ya kamata ki tuna Ummi ta riƙeni ta maida ni ɗa lokacin da kika ajiyeni kika tafi neman duniya, ko kin manta waye Jalal ɗin naki,? kin Manta halina ne a baya? Ba wanda zeso ya raɓeni saboda mugun halin Shaye2 da rashin girmama ɗan adam, Rayuwa ta fa ta rushene saboda ke Mummy, Abaya bama shiri da Jalila amma kin taɓa tunanin wani dalili ne yasa na ɗaukaki soyayyar mata ta da mahimmanci? Me yasa baki tsani Jawwad haka ba se Mata ta?" Jalila tace "ka tausasa harshe Zaujee Mummy ce" Ɗagawa Jalila hannu yayi alamar tayi masa shiru ya ci gaba da magana "A baya in ba mutum ya sanni ba ko yaji sunana ba se a ɗauka Arne ni saboda yanayin saka suturata ma sam beyi kama da na musulmi ba, Yanzu kalleni Mummy Allah ya shiryeni, da kinsan gudunmuwar da Jalila ta bawa rayuwa ta da koda wasa bazaki mummunar magana akan ta ba, a gabanki akace sanadin ta Asirin jikina ya karye, Mummy ko a lokacin da aka ɗaura mana Aure da Jalila ina shaye2 ban fasa ba, Amma ba wanda ta kaiwa ƙara ta, tayi aiki ba dare ba rana dan ganin na shiryu, ni wani irin butulu ne da ba zan nunawa duniya ina sonta ba, Mummy haifa ta fa kawai ki kayi, Tarbiyya ta da sauran Al'amurana mahaifina da duniya ce sukayimin, wallahi Mummy idan baki dena butulci ba abunda ya faru da Umman Ilham kema ze faru dake" Da sauri ta ɗago tana kallon Jalal, Amma ba tayi magana ba. Ta wani fannin Jalal gaskiya yake faɗa, Mummy wata irin mace ce ma kafiya da taurin kai, gata da riƙo wata irin zuciya ce da ita yanzu take ganin lallai Daddy yayi haƙuri a zaman sa da Mummy. Daddy ne ya turo ƙofar ɗakin ya shigo da sallama. Amsa masa sukayi tareda gaishe shi, yayin da Mummy ta juya baya ta rufe idon ta, gefen gadon daddy yaje ya zauna ya kai hannun goshin Mummy yace "Sannu deejah me yake damunki haka?" Shiru tai ko motsawa ba tayi ba balle tai masa magana. Ƙara matsawa Daddy yayi ya riƙo hannayen ta yace "deejah fushi kike dani haka? Me yake damunki haka,? kin rame sosai" Jalal yace "hawan jini ne yake damun ta ya hau over, ko Abinci taƙi ci, mu zamuje gida mu ɗan huta" Daddy yace "shikenan ku gaida gida, Jalila zanzo a kwance jaka dani ba abani tsaraba ta ba" Murmushi Jalila tayi tace "shikenan Daddy insha Allah da kaina zan kawo maka har gida" "to shikenan Allah ya huta gajiya" Su Jalila suka tafi gida, Daddy kuma ya zauna zaman rarrashi Amma kamar yana tunzura Mummy taƙi saurarsa, likita ya sallame ta tareda bata magunguna Daddy ya ɗauke ta suka koma gida. Ilham fa Abubuwan babu sauƙi, ta rasa inda zata saka ranta, basu da komai komai ya ƙare musu, gashi ita kanta Ilham ɗin cikin dare tsorata ta akeyi, taita gane2 da jin sautuka marasa daɗi, ta fara gajiya da jinyar mahaifiyar ta, babu wani ci gaba kullum jiya i yau ga babu wani me kawo musu tallafi koda na hatsi ne Ilham kuma tasan bata isa ta tunkari gidan Mummy ba. Kwanan Daddy biyu a kano amma Mummy bata saurarsa, gashi komai a hankali take yi, saboda idan ta fiye aiki se taji kaman numfashin ta ze ɗauke. Yanzuma Daddy yana ta lallaɓata taci Abinci Su Jalila suka zo dubiya, Amma ba Jalila ba hatta inda Jalal yake bata kalla ba, Jalila tazo da manyan kwalayen turare ta bawa Daddy sannan ta bawa Mummy tace "tsarabar su ce" Jifa Mummy tayi da jakar kayan tace "ke nifa bana son jaraba, na meye dole sekin min shishigi? Shegiyar yarinya makira sekace mayya, a baya ma dana yadda dake ban ɗauka haka kike ba, jarababbiya in dai Jalal ne gashi nan kije ki cinye shi, daga yau in zezo inda nake karki ƙara biyo shi, shi na haifa bake ba bana son salon munafunci bazan taɓa ƙaunrki ba, bazaki taɓa wani abu ki burgeni ba, yadda Asirin da'aka yi masa ya karye haka wanda kika yi masa ze karye, in ba aikin Asiri ba ya za'ayi namiji kamar Jalal ya dinga rawar ƙafa akan yarinyar da ta dinga ci masa mutunci a gaban uwar sa, ba miyagun kalaman da bata yi amfania dasu gurin muzanta Jalal ba, Amma mara zuciya ya liƙe mata se kace ita kaɗaice mace, ni ban yadda son da Jalal yake mata na tsakani da Allah bane, tunda uwatta beyerabiya ce ta shiga ta fita an......... "Enough Mummy" Jalal ya katse mahaifiyarsa daga maganar da take son ƙarasawa, ita kuwa Jalila ta shi tayi ta bar falon tana kuka, dan taji zafin maganganun Mummy ba kaɗan ba kai tsaye ta fice ta tafi gidan su. Daddy ma ya fusata da abunda Mummy tayi dan haka yace "Khadija ke kam bansan me zaki gani a rayuwa da zesa ki dawo hayyacin ki ba, ina ni mijinki ne nima fa wata ce ta haife ni kika aura, kika rabani da 'yan uwana da kowa nawa, kin auri ɗan wata kin mulkeshi dan me ke baza' a auri naki a mulka ba,? ki gode Allah ke ta hanyar data dace a ke juya naki ɗan ya kike gani in da za'a miki abunda ke kikayi? Kina dama da kanki amma kina kishi da matar ɗanki wannan wane irin abun kunya ne? Hakan baze ja miki komai ba se zubewar mutunci " Jalal yace "tunda ba kya ƙaunar ganin Jalila nima ba kya ƙaunar ganina, sannan dan ta muzanta ni a gabanki a bayan idonki dubun ta sun muzanta ni, dukda kina mahaifiya ta idan na biye miki na cutar da Jalila se Allah ya saka mata, kin san baƙar wahalar da ta sha akaina kuwa? Dukda tana muzanta ni, Amma a bayan idonki baki san gwagwarmayar da tayi akaina ba, duk wanda yake ƙin Jalila ni yake ƙi, sannan tun bani da hankali mahaifiyarta tayi ɗawainiya dani ta kula dani, duk abunda ya faru a baya da Jalila tayi min ƙuruciya ce kuma ya wuce, Sannan ɗaya daga cikin manyan maƙiya ne da yayi kwangilar ɓata min rayuwa da shi da uban gidansa Oga KB Jalila ce tai sanadiyar zuwan su prison don ta nesanta su dani in dena shaye2, kullum muka haɗu ƙoƙarin ta da nasihar ta be wuce in dena wulaƙanta iyaye na ba musamman ke, kuma kinsani duk lokacin da ta gayan muguwar magana to tabbas ta kamani ina aikata abunda be dace bane, ni wani irin baƙin butulu ne da zan tozarta ta? So kike nima inyi dana sani inzo ina cizon yatsa kaman yadda kika yi, duk me son ya so Mata ta da dangin ta, sunmin abunda dangin uwa ta ba su yi min ba" Jalal ya ƙarasa maganar kaman yayi kuka, ya nufi hanyar fita ya tsaya ya juyo yace "Insha Allah Jalila bazata ƙara zuwar miki gida ba balle ki ɓata mata rai, har ga Allah a yanzu ma banji daɗin abunda kikayi mata ba" ya juya ya fice zuciyar sa a cunkushe Jalila kam tana fita ta shige gidan su, Maama tana parlour tana shan tea Jalila ta shigo tana kuka, seda gaban Maama ya faɗi tace "Jalila lafiya meyafaru haka kike kuka?" Seda Jalila tayi kuka me isar ta sannan tace "Maama wai dan Allah da ba a yafiya a duniyar nan da zamu cigaba? Da Allah baya yafe laifukan mu da zamu kawo iyanzu muna morar ni'imomin sa?" Maama ta girgiza kai tace "A'a Jalila, Kullum cikin laifi muke Allah yana yafe mana, ba dan yana yafe mana ba da tuni ya kawar damu ya halicci wanda zasu bauta masa ba tare da sun saɓa masa ba" Jalila ta goge hawayen ta tace "Maama meyasa Mummy bazata yafe laifukana na baya a idon ta ba, ta tsaneni bata ƙaunata, kullum se tayi mitar a baya na muzanta ɗan ta a gaban ta, Maama Jalal da bakin sa ya yafe min abunda nayi masa, Amma kullum se Mummy taci mutunci na" Maama tace "Jalila shiyasa a rayuwa dan mutum yana aikata kuskure be kamata ka dinga yi masa gatsali kana cin mutuncinsa ba, kin gama yi masa rashin ta ido ƙarshe ya zama mijinki wanda yake matuƙar ji dake, Amma mahaifiyarsa bata ƙaunarki, duk abunda kikayi wa ɗan ta na kirki ko akasin haka uwa bata mantawa, Nima ƙaunarki ga 'ya' yana ce tasa na dawo hankalina na gane kuskure na, dan haka ko nan gaba ki kiyaye muzanta ɗan mutum a gaban iyayen sa, sannan be kamata ta cigaba da ƙinki ba dan ƙoƙarin da kikayi akan rayuwarsa yafi laifukanki, ya kuma ci ace ta yafe miki" Cikin kuka Jalila tace "bana tunanin zata yafe min ta tsaneni yadda ba kya zato na rasa ina zan saka rayuwa ta, kuma tun a wancan lokacin da ta tsawatar min ta nuna min bata son abunda nake wa Jalal da bazan kuma ba" Maama tace "Hakane Amma kiyi haƙuri, ba'a taɓa kyale ɗan adam ba'a jarrabashi ba" Yarone yayi sallama Maama ta amsa, yaron yace "wai Jalila ta fito su tafi gida inji mijin ta" Maama tace "to kace tana zuwa" Jalila na miƙewa ta zura da gudu ɗakin su. Maama tabi bayan ta tana faɗin "wannan wane irin sakarci ne kuma? Ki taso kije ku tafi" Cikin kuka Jalila tace "ni ba inda zani bazan bi shi ba, Mummy ta zaɓa masa matar da take so ya zauna da ita" Maama tayi tayi amma Jalila ta ƙeƙashe tace "ba inda zata" Jalal ya gaji da jira dan haka yazo yana ƙwanƙwasa ƙofar parlourn Maama tazo ta buɗe, Jalal ya durƙusa ya gaishe ta, wanda da se su kusa karo a hanya baze kula ta ba alhalin a gidan ta yake wuni tareda ɗan ta, tabbas idan Mummy ta dage gun raba Auren su Jalal zata tafka kuskure mafi muni. Bayan sun gaisa Maama ta nuna masa ɗakin da Jalila ta shige tace "tana ciki tunda ta shigo bata kulani ba bansan me ya faru ba" Jalal ya jinjina kai ya nufi ɗakin da Jalila take, ta ƙule akan gado tana ta sharar hawaye, Jalal yaje ya zauna a kusa da ita yace "Jalila ki taso mu tafi gida" Shiru tayi ba tace komai ba. Yasa hannu ya ɗago ta gaba ɗaya yace "kiyi haƙuri kizo muje gida se muyi magana" "ni ba zan biki ba ka ƙyaleni, ka bari Mummy ta samo maka matar da take so ka aura" Ɗan ƙura mata ido yayi kafin daga baya kaman wanda aka yi wa dole yace "har kina tunanin akwai macen da zata iya zama dani bayan ke? Kin sanni fiye da yadda kowa yasan halina, Jalila just recently kika gama gayamin cewar duk tsanani bazaki rabu dani ba, yanzu har anzo tsananin da zaki karya Alƙawarin da kika yi? Duk ƙoƙarin da nake yi ba kya gani? Mene makomar rayuwar mu da ɗan da yake cikin ki idan muka rabu? Anya Jalila kina min son da nake miki?" Ɗagowa tayi fuskarta sharkaf da hawaye tace "Jalal idan har ina maka son gaskiya ne, to zanso in kasance da kai har cikin Aljannah, Jalal bazan so Allah yayi fushi da kai saboda saɓawa iyaye ba, Amma nima nasan tabbas zan shiga mawuyacin hali idan na rabu da kai" Ta ƙara sa maganar tareda rungume Jalal ta fashe da kuka ta cigaba da cewa "Jalal nayi wauta abubuwan da nayi maka a baya, Amma dan Allah Mummy tayi haƙuri karta rabani da kai, hukunci mafi tsauri da zata yi min shine rabani da kai, in aka rabamu zuciya ta ba zata iya ɗaukar hukuncin ba ina sonka Jalal, nayi dana sanin abubuwan da nayi maka  a baya Amma dan Allah ku yafe min " Tausayinta ya mamaye ilahirin jikin Jalal, gaba ɗaya jikin sa yayi sanyi ya ɗago ta suka fuskanci juna yasa hannu ya share mata hawayen fuskarta "Babu me raba wannan soyayyar se ubangijin da ya haɗata, lokaci ne Mummy zata yi nadamar abunda ta aikata, Amma kuskure mafi muni a gare ni shine kice zaki rabu dani, Akwai hatsari a cikin aika ta hakan, ki dena kuka kar kisa Baby na cikin damuwa" "kafi damuwa da Babyn ka dani ko?" Jalal yace "ni na isa ina sonku gaba ɗaya, ku ɓangare ne me girma a tare da ni, Allah ya raba ku lafiya" Jalila ta amsa da "Ameen" Jalal yace "tashi mu tafi gidan mu" Maƙale kafaɗa tayi tace "sedai in zaka saimin goba me tsami" Murmushi yayi yace "shikenan tashi mu tafi" Ta ɗauki mayafinta suka fito, Suna fitowa Maama tace "zaku tafi ne? Jalila ina da fura zo ki karɓar muku" Jalila tabi Maama Jalal kuma ya fita. Maama tace "Jalila shi lamarin Aure haƙuri ake yi, karki ƙara cewa zaki rabu da mijinki akan abunda be kai ya kawo ba" "Insha Allah Maama bazan ƙara ba" Tabawa Jalila fura da Nono suka yi Sallama suka tafi. Daddy kam faɗa ya cigaba da yiwa Mummy, Mummy ta nisa tace "waini abunda ya bani mamaki shine ya'akayi yarinyar nan tasan Kabiru har tayi sanadiyar zuwan sa prison? Ko dai kuna rainamin hankali ne kawai kaida ɗanka?" Daddy yace "se kije ki bincika, abunda ya dace kiyi kenan tun farko ba shirme da son zuciya ba" Daddy beyi mata wani bayani ba ya tashi ya ƙyale ta. Jalal ba ƙaramin tausayin Jalila yake ba, cikin na wahal da ita ɓangaren Abinci wataran da Asuba haka ze farka ya ganta a zaune tana cin biscuit ko goldenmorn wataran ko brush ba tayi ba, bata laulayi sedai zazzaɓin dare da yawan ciwon ciki. Jalal ya fara shirin komawa Lagos dan hutunsa tuni ya ƙare, ya ƙara ma sosai, Jalila se rigima take baze tafi ya barta ba, ya rasa inda ze sa ransa se rarrashin ta yake amma fafur taƙi se koke koke take, ta koma masa kamar wata 'yar ƙaramar yarinya yace "ze tafi da ita Lagos tace ba zata ba makaranta zasu yi final exams" Saura kwana ɗaya ya tafi, tana kwance a jikin Jalal tana ta zuba shagwaɓa, ya biye mata yana ta rarrashi, Wayar Jalila ce ta fara ringing Jalal ya miƙo mata wayar tasa hannu ta karɓa taga Ummi ce, zumbur ta miƙe zaune ta ɗaga wayar "Ummi na ya kike?" "lafiya ƙalau ya me jiki kuma?" "lafiya ƙalau Ummi, jikin ta da sauƙi" "Masha Allah dama zamu zone gobe insha Allah" Tsalle Jalila tayi tana murna "Allah yakawo ku lafiya Ummi na" Ta ajiye wayar tana tsalle daga wannan kujerar zuwa waccan tana rawa, Jalal kallon ta kawai yake yace "Ayi a hankali dai, kar ki illata min yarona dan Allah" Zuwa tayi ta zauna kan cinyar sa tace "Ummi ta fanshe ka mijin so, a tafi Lagos Allah ya kiyaye hanya se an dawo, gobe insha Allah zasu zo" "Allah ya shirye ki, da su Ummi baza su zoba haka zan ci gaba da fama dake ko, kiyi ta bani wahala?" Ɓoye fuskar ta tayi a ƙirjinsa tana dariya tace "kaifa ranar kace Yaya Jawwad dole ya kula da Hanan tunda ɗansa ne, kaima yanzu tunda naka ne sekayi haƙuri damu" Dariya Jalal yayi yace "ba kya mantuwa ko? Zaki ramawa Jawwad" Dariya tayi tace "daɗin ta dai kai ka faɗa ba wani ba" Washegari da wuri Jalal ya tafi Lagos, su Ummi kuma suka zo da Yamma, Jalila tayi murnar ganin su Ummi, Ummi da mahaifiyar ta da wasu 'yan uwan ta suka zo, Jalila ta rasa inda zata sa ranta dan murna, tai musu kyakywar tarba da Abincika kala2, Ummi taji daɗin inda Jalila ke zaune kuma ga dukkan alamu Jalila na cikin kwanciyar hankali a gidan Auren ta. Ummi ta kalli Jalila tace "Baby wannan ƙiba haka?, kice in fara tara kayan yara, Babyna girma yazo" Jalila ta kalli cikin ta ta rufe fuska tace "ni bani da komai, sedai in kayan teddy wasa na zaki saiwa" "hmm kinkusa ɗaukar teddy me rai ai, Allah ya raba ku lafiya" "in ba da  hanjina zamu rabu lafiya ba ni ba komai a cikina" Ummi tace "Jalila baki da kunya, ko kunya ta ba kyaji ko ni zaki kalla kiyi wa wayo Allah ya shirye ki" Rufe fuska Jalila tayi tana dariya. 'yan uwan Ummi basa jin hausa, se yarabanci turanci, da fulatanci kaɗan kaɗan. Jalila ta sake ta sha hira da Ummi, ta gaya mata halin da ta ke ciki da Mummy, Ummi taita rarrashin ta tana bata haƙuri. Ƙarfe goma na dare Abba ya turo da mota yace a ɗakko su Ummi, Jalila tayi tayi su Ummi su kwana a gidan ta suka ƙi suka tafi gidan Abba. Washegari da safe Jalila ta kira Jalal a waya tace masa tana so tabi su Ummi gidan Abba ba ta jin daɗin zaman gida ita kaɗai, Jalal ya batta da safen ta shirya ta tafi gida itama. Ummi ta shiga duba Mummy, Sam tarbar da Mummy taiwa Ummi bata ji daɗin ta ba amma ta danne ta ƙyaleta. Kwanan su Ummi uku Jawwad yai waya "Hanan ta haihu ta haifi mace", Jalila kaman ita akace ta haihu ta dinga murna. Maama tace "Allah ya raya, saura Nana itama Allah ya raba lafiya Jalila kuwa dama da saura" Kwanan Hanan biyar da haihuwa Nana ma ta haihu, Itama mace ta haifa, sedai Nana seda aka mata aiki aka ciro yarinyar. Ba'ayi suna ba seda aka jira Nana ta zo Nigeria, aka shirya gagarumin taron suna a garin Bauchi, sunan Jaririyar Hanan Zainab, ta Nana kuma Ummu Salma sunan Hajiya Salma. Jalal yayi bajinta shi yayiwa Jarirai abun yanka, banda kyautuka da ya basu, se bayan suna Ummi ta koma garin su. Jalila tasha labarin labor a gurin Hanan hakan yasa ta ƙara tsorata sosai, Jalal ya ɗakko Jalila suka dawo kano. Komai ya ƙarewa Ilham, gidajen masu kuɗin unguwarsu take bi tana musu wanke2 da wanki ana biyan ta sannan ta samu na Abinci, gashi yanayin rashin lafiyar mahaifiyar ta da firgitar da take cikin dare yafara taɓa ƙwaƙwalwarta, wani lokacin da rana tsaka ma se taita zabura kaman zata zura da gudu, Abun ya haɗu ya yamutse mata, gaba ɗaya ta koma wata iri ta koma kamar wata tsohuwa gaba ɗaya a firgice take. Jalila ciki ya fara tsufa, ta kammala makaranta zata yi service ɗinta a kano, Seda Jalal ya shirya mata walima a gida akaci aka sha ga cikin ta nan yayi girma gwanin sha'awa yayi mata kyau, 'yan uwa da abokan Arziki sun halarci taron sosai. Har yanzu Mummy a ƙule take da Jalila, bata sonta sam bata ƙaunar yadda Jalala ke nan nan da Jalila, haka dangin Daddy ma suna matuƙar ƙaunar Jalila tanada kirki ga kyauta, ɓangaren Daddy ma yanzu ya dena ɗaukar abunda Mummy ke masa a baya, duk sati uku yana zuwa ya ganta amma halinta yake sawa yaji baya son zuwa inda take, Hajiya Salma kam tana ta ƙara ƙoƙari gurin ganin ta kyautata wa Daddy, Sosai hawan jini ya taso Mummy a gaba, yanzu ko gani bata yi sosai seda glass hawan jini ya taɓa mata zuciya da kuma ganin ta, ga dukiyar a jibge amma bakomai take iya ci ba, ba ko ina take iya zuwa ba saboda yanayin larurar da take ciki. Jalal koya tafi Lagos baya iya daɗewa saboda hankalinsa yana kan Jalila, yana tausayin ta bakomai take iyayi ba cikin yayi girma, dan haka ya ɗauke ta ya tafi da ita Lagos yaci gaba da kula da ita. Wani labari ne ya iske Mummy daga kamfanin Jalal abun ya matuƙar girgiza ta ya ɗaga mata hankali hakan yasa ta kira Jalal a waya tace lallai yazo tana son ganin sa, ya sanar mata yana Lagos tace "lallai ya bar abunda yake yi ya dawo" "Mummy a ƙarƙashin wasu fa nake aiki, haka akeyi kawai in taho ba tare da izini ba, idan na samu matsala fa?" "Jalal dole ka bar wannan banzan aikin ka dawo ka kula da dukiyar ka akwai matsala, bazan lamunci abunda ke shirin faruwa akan dukiyar ka ba" Cikin rashin fahimta Jalal yace "meke shirin faruwa akan dukiyar tawa?" "idan kazo ka ji" Comment yayi ƙasa fa ko kun gaji ne, nima se in tafi hutu se kun ganni 😡😡😡😡 Share please 07063065680 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 *ABDUL JALAL* _Story, writing and edited _ By AISHA HUMAIRA ( _Daddy's girl_) *PERFECT WRITER'S* *ASSOCIATION*🌞 (𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪) /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A*✍️ PART 2 _PAGE 6️⃣3️⃣117 Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam. Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba. Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina 07063065680 Or email address @ www.humaira17@gmail.com Watpad @Ayshercool7724                     _MY FIRST NOVEL _ Ajiye wayar Jalal yayi tare da dafe kansa yayi shiru, Jalila tace "me yake damunka ne, Ina fatan dai lafiya ko?" Cikin damuwa yace "Mummy ce ta kirani wai lallai in koma tana son ganina, Akwai abunda taji yana shirin faruwa akan dukiya ta" "Subhanallah Allah yasa dai lafiya? Yaushe zamu koma kenan?" "ba inda zani" Jalal ya bata amsa "Saboda me? Kiran mahaifiyarka ne fa" "Nasani Jalila nasan akan abunda take magana, indai zan biye wa Mummy bazan taɓa abun Arziki a rayuwa ta ba, shiyasa bana son raɓarta komai nata na son kanta ne" Jalila cikin sigar rarrashi tace "Jalal me yasa kake me tausasawa ga wasu can bare amma baka iya tausasa wa mahaifiyarka, duk wanda yakamata ya more ka a bayan ta yake, kayi haƙuri da yadda Allah yayi ta ka cigaba da yi mata Addu'a wataran se labari, kai ka ɗai ne ɗan da ta mallaka, be kamata a ce kana mata irin wannan halayen ba" Kaman ze kuka cike da zuciya da ɓacin rai yace "nika ɗai take dani, kuma nika ɗai take azabtarwa" "Jalal ya za'ayi mahaifiyar ka ta haife ka sannan kace tana azabtar da kai, baka fahimce ta bane.... " Enough Jalila kidena pretending kaman baki san komai ba mana, Jalila bana jin daɗin Alaƙata da mahaifiya ta, ina kulle kaina inyi kuka da hawaye na saboda rashin soyayya da kulawar mahaifiya, ban san jin ƙai na tsakanin ɗa da uwa ba, kullum tunanin Mummy burin ta kowa ni abu da take hange ya cika, bata tunani makoma ta, duk lokacin da nayi niyyar in shiga jikin mahaifiya ta in bata kulawar da zan iya, se ta bijiromin da wani abu da yake saɓanin tunani, me yasa yaushe Mummy za ta gane inda rayuwa ta dosa,? shi kansa Daddy yanzu bata gaban sa, shekaru talatin da uku yana haƙuri, Jalila har yanzu ina ganin lokacin da mahaifiyar Daddy ke zubar da hawaye saboda halayen mahaifiya ta yaushe Mummy zata canza tunanin ta se yaushe? Yaushe zata gane mutunci da soyayya gaba suke da dukiya? " Jalal ya ɗau zafi sosai dan har jijiyoyin kansa sun fara miƙewa ya zuciya da yawa. Ƙara matsowa kusa da shi Jalila tayi tace "Jalal a duk lokacin da mutane zasu zauna da junansu ba dan Allah bato tabbas wannan zama ba shi da wani amfani, wanda suka zauna da Mummy a baya ba masu ƙaunarta bane, masu son abun hannunta ne, Baka tunanin in kayi haƙuri da ita kai mata biyayya a hankali ta shiryu? Rayuwarmu da mukayi a baya da wadda muke da kai a yanzu misali ce a gareka, Jalal baka da uzuri a gurin ubangiji idan ka mutu kana ɓatawa mahaifiyar ka rai, abubuwan da tayi tsakanin ta da Allah ne, Amma kai zaka yi aikin gyara halayen Mummy idan kaso" "ta yaya?" "ta hanyar bata matsayin ta na uwa, ka girmama ta, duk lokacin da tazo da abunda ba dai dai ba ka gyara mata cikin sigar rarrashi, kuma kaga yanzu bata da cikakkiyar lafiya tana buƙatar kulawa Amma kai baka shiga sabgarta Daddy ma ya ƙyaleta dama bata wani jituwa da 'yan uwan ta me kake tunani ze faru da ita?". Haka Jalila ta cigaba da lallaɓa Jalal da yi masa nasiha har ya amince zasu tafi Kano dan yaje yaji neman da Mummy ke masa. Koda yaje kiran da take masa ba akan komai bane face wasu daga cikin ma' aikatansa za suyi ritaya, ya ware wasu maƙudan kuɗi domin ya sallame su, tun yana ƙaramin yaro suke juya masa dukiyarsa sunyi wa kasuwancin sa bauta, dan haka ya ware kuɗi masu yawa akan cewar ze basu, sannan ya bawa kowannen su vacancy na mutum biyu ze ɗauke su aiki, shine Mummy take faɗa akan danme ze bayar da wannan kuɗaɗe masu yawa haka? Ƙarshe dai haka ya taho ya bar gidan ransa a ɓace tare da dana sanin zuwa gidan da yayi, yana mamakin wannaan hali da zuciya na mahaifiyarsa be san meze sa zuciyar ta tayi laushi ba. A kwana a tashi tunda cikin Jalila ya shiga wata takwas zuwa tara aka yiwa Jalal ƙarin matsayi akai masa transfer ya dawo kano gaba ɗaya, Jalila tafi kowa farinciki da wannan transfer. Jalila bata da aiki se ɗora yaran su Nana a status ɗin ta, Jaririyar Hanan kamarta ɗaya da Jawwad Jalila taita tsokanar su da "gidan Jajaye, uwa Ja uba Ja 'yarsu ma Ja" Jalal na shan wahala tunda cikin Jalila ya shiga wata tara yau tace nan ciwo gobe tace can, ba ƙaramin tausayin ta yake ji ba, wataran se dare zata tashe shi tace "ita ta kasa bacci" haka zeta faman rarrashi. Ummi ta gayawa Jalila kayan da zata shirya na haihuwa da alamomin da za taji wanda zata gane naƙuda ne. Gaba ɗaya jikin Jalila yayi sanyi dan tana matuƙar jin tsoron haihuwa sam ta kasa bacci, ga shi a satin nan tana ta fama da ciwon baya da ƙafafuwa, ga ciwon mara da yasa ta gaba ya hana ta bacci sam. Juyawa tayi ta kalli Jalal yana ta baccin sa ita kam bacci ya ƙauracewa idon ta, tashin Jalal tayi ya kalle ta yace "Baby lafiya kuwa?" kamar zata yi kuka tace "na kasa bacci fa" "to kiyi haƙuri zakiyi baccin Insha Allah, ba abunda yake miki ciwo dai ko?" "Jalal ina jin tsoron haihuwa, Hanan tace min akwai wahala fa" "haba Jarumar mata, ita Hanan ɗin da suka haihu ba gashi ya wuce kamar ba'ayi ba, kiyi ta ambaton Allah komai zezo da sauƙi Insha Allah, da kinji ciwo kimin magana" Jinjina masa kai tayi tace "to ɗan kwanta, se in kwanta a bayan ka" Ya juya ya kwanta ta tada kai da bayan sa, ta ɗora ƙafafuwan ta akan pillow, A hankali yaji tana sauke numfashi alamar tayi bacci. Ɗan girgiza kai Jalal yayi, lallai mata sun cancanci a girmama su kodan Albarkacin wannan ɗawainiyar da suke yi Allah ka ɗai yasan me suke ji, ko iya tashi da ƙyar da juyi ya ishi abnun tausayi, dan wani lokacin idan tana bacci ya kalli cikin yana ganin yadda cikin yake motsi, Yana wannan tunanin shima baccin ya ɗauke shi. Juyi Jalal yayi akan gado yaga bata kan gadon ya kunna fitilar ɗakin can ya hango ta durƙushe a gaban gado tana ta haɗa gumi dukda fankar da take ta juyawa a ɗakin amma Jalila gumi take, da sauri ya sakko yana kiran sunan ta. Kasa magana tayi sedai juya kai a hankali tace "Jalal bayana ze ɓalle" Riƙota yayi yace "Sannu bari in saka riga mu tafi Asibiti" A daren ya ɗauki Jalila suka tafi Asibiti, amma koda suka je aka sanar da su labor take yi amma da sauran lokaci. Ba Jalila ba shi kansa Jalal seda ya ɗan karaya duk wannan wahalar ace da sauran lokaci. Haka suka kwana a Asibiti, yana ta nafila da Adduoin Allah ya sauke ta lafiya. Da safe yaje gida ya dafa Abinci da kansa ya kawo mata, tana zaune kaman ba me labor ba. Zama yayi suna hira ya haɗa tea ya bata tana sha suna hira, wata nurse tace "gaskiya ba haihuwa zakiyi yanzu ba soyayya ma kike yi zaki ci ƙaniyar ki ne" Jalila dai ba tace komai ba ta cigaba da shan tea ɗinta, Ba yadda Nurses ɗin basu yiba Jalal ya fita ba yaƙi, tana cikin shan tea ɗin tayi jifa da kofin hannun ta, ta riƙe rigar Jalal tana ambaton Allah gaba ɗaya Jalal ya ruɗe da ƙyar ya ƙwace rigarsa duk ta yamutsa ta, tun daga nan Jalila take fama kasancewar haihuwar fari ce. Jalal ya kira Maama a waya ya sanar mata suna Asibiti, ya kira Hajiya Salma ya gaya mata suyi wa Jalila Addu'a suna Asibiti. Befi minti Arba'in da wayar da Jalal yayi wa Maama ba tazo Asibitin. Jalal ya fito harabar Asibitin yana ta kaiwa yana komawa, kallo ɗaya zakayi masa kasan hankalin sa ba'a kwance yake ba. Suka gaisa da Maama ya rakata ƙofar ɗakin da Jalila take, suna iya juyo Jalila tana ambaton Allah daga inda suke. Maama taita kwantarwa da Jalal hankali, suka ci gaba dayi mata Addu'a. Jalila tun karfe biyun dare suke Asibiti se karfe sha ɗayan daren Washegari ta haihu, ta haifi ƙaton jariri namiji su kansu ma'aikatan seda sukayi mamakin girman jaririn. Seda suka kintsa Jaririn da Jalila tsaf sannan suka sanar da Maama Jalila ta sauka lafiya. Wata irin ajiyar zuciya ta yi tare da fadin "Alhamdilillah" Jalal ta kira a waya tace  yazo tana son ganinsa, sam Jalal ko Abinci be iya ci ba, gaba daya tausayin mata ne ya mamaye zuciyar sa be taba zaton mata na shan wahala iirn haka idan zasu haihu ba, ya dauka abun ba wuya. Yana zuwa Mama ta sanar da shi Jalila ta haihu kasa magana yayi se murnar tareda sauke ajiyar zuciya kafin daga baya yace "Alhamdilillah" Suka shiga dakin da Jalila take, tana zaune an hada mata tea tana sha, kaman ba itace ta ke ta shan wahala ba. Jalal ya kalli Jalila yace "Sannu Jalila ya jiki? Ina ne kuma yake miki ciwo?" Tai murmushi tace "Alhamdilillah ina haihuwa na dena jin ciwon komai" Maama tace "Sannu Jalila" Jalal ya karasa gadon Baby ya dakko shi, jaririn kato dashi kaman Jalal yayi kaki ya tofar saboda kamar da suke yi. Jalal yace "Maama yanzu wannan nawa ne? Ni Allah ya bawa?" Maama tace "naka ne Jalal, Allah ne yaba ka" Ya ƙanƙame yaron a kirjinsa ya tafi gadon Jalila ya zauna a gefen ta yace "Masoyiyya kalli waini ni ne da ɗa yau" Maama ta fita ta basu guri. Jalila tace "Zaujee ya zama Daddy" Ya haɗa da jaririn da Jalila ya rungume su yace "Jalila ban taba zaton zan samu wannan Ni'imar ba, Allah ya shiryeni ya bani mace ta gari, yanzu kuma ya bani ɗa, Alhamdilillah" Jalila ma rungume shi tayi tace "Zaujee kaga wahalar nan dana sha? Watakila Mummy ta sha wahala fiye da wadda na sha a gurin haihuwar ka, shiyasa Annabi salallahu alaihi wassalam yace  "abi uwa sau uku sannan yace uba" dan haka zaujee dan Allah ka gyara tsakanin ka da Mummy " "Jalila ina ƙaunar mahaifiya ta kamar yadda kowace halitta ta keyi, halayen mahaifiya tane bana son zuwa inda take" Maama ta dawo ɗakin tace "Jalal ya kamata ka tafi gida dare yayi, gobe in Allah ya kaimu in an sallame mu se kazo ka dauke mu" Da ƙyar Jalal ya yadda ya tafi gida. Washegari da safe aka sallami su Jalila suka wuce gidan Maama, aka dinga sanar da 'yan uwa da abokan arziki Jalila ta haihu. Nan da nan gidan Jalila yafara ciki da mutane, kowa ya ɗauki Yaron nan seya yaba kyansa. Jalal bewa yaron nan huduba seda Jawwad yazo, yai masa huduba da sunan Jawwad Aliyu Haidar. ' yan garin su Mummy sunzo, mutanen Bauchi da Maiduguri ma duk sunzo, Hajiya Salma ma kwana uku da haihuwar tazo, dan taya su Jalila murna, kowa se yaba girma da kyawun jaririn yake, babu wanda yayi zaton Jalal ze samu canjin rayuwa daga tsohuwar Rayuwar da yake a baya. Ranar suna ƙaton hall Jalal ya kama saboda taron suna, taron Sunan ya tara jama'a masu tarin yawan gaske, akaci aka sha jariri yaci sunan mahaifin Jalila kuma sunan babban Amin Jalal, Jawwad. Kamar yadda kuka sani dama dangin Jalal Akwai bajinta haka suka dainga yiwa jaririn nan da mahifiyarsa kyautuka, kowane bangare yayi bajinta daidai gwargwado. Akwatuna Jalal yayiwa Haidar da kuma Jalila ya bata kujera me girma a kamfanin sa, tare da rantsatsiyar motar hawa, (mhmmm Abun manya dai na manya ne) " Jawwad yaji dadin karar da Jalal yayi masa, nasakawa dansa na fari sunan mahaifin Jalila kuma sunan Jawwad. Kullum se Jalal yazo gidan Maama dan ganin Jalila da Haidar, Daddy ma ya zazzo ganin Jariri yayi masa Adduoi tare da bashi kyautu ka. Tunda akayi haihuwar nan Mummy bata taba zuwa taga me aka haifa ba, musamman da taji abunda Jalal yayi, Abun ya damu Jalila matuƙa. Dan haka da daddare da Jalal yazo ganin Jalila ta saka masa kuka "Zaujee kwana goma da haihuwa ta, Koba danni ba yakamata Mummy tazo taga jikan ta, Jalal ina cikin matukar damuwa akan lamarin nan" Jalal yace "Jalila zaki tausayamin idan kika san kuncin da nake ciki na halin ko in kula da mahaifiya ta ke nunawa akan al'amura na, ko baki fada ba dama nayi niyyar insha Allah da kaina zan kaiwa Mummy Haidar, da safe zanzo muje" Jalal yaita rarrashin ta yana kwantar mata da hankali, Sam Jalal baya kara akan dansa, ji yake kaman ransa yaita kallon Haidar yana cewa "yanzu ni Allah ya bawa ɗa, dukda tarin laifukana a gare shi Alhamdilillah" Tun daren Jalila take Addu'a tana fargabar me zata tarar in suka je gurin Mummy. Kamar yadda suka shirya da safe, Jalal yazo ya dauki Haidar Jalila tace Hanan ta raka ta da yake bata koma ba, sukabi bayan Jalal zuwa gidan su. Suka tarar da Hajiya Salma a gidan da Daddy, Mummy kana kallon ta zaka san ta rame saboda rashin lafiya, Amma har yanzu tana nan da gayun ta, hannun ta yasha lalle Ja, kanta ba ɗan kwali tai parking din gashin ta, wani abu take sha a cup kamar bata san da zaman Daddy da Hajiya Salma a gurin ba se kaɗa ƙafa take abun ta. Su Jalila suka yi Sallama, Su Daddy ne suka amsa banda Mummy, Hajiya Salma tace "Jalila me yasa kika fito kina ɗanyen jego" Tuni Jalila ta fara kuka tace "Anty Salma, Daddy dan Allah ku saka baki Mummy ta yafe min abunda nayi mata, dan Allah kar laifina ya shafi Haidar, kwana na goma da haihuwa bata ga abunda na haifa ba" Har ƙasa Jalila ta zube tana cewa "Mummy dan Allah kiyi hakuri kidena fushi dani, ki yafemin abunda nai miki kar laifina ya shafi jikan ki dan Allah" Gaba daya tausayin Jalila ya kama su, ita kanta Mummy jikin ta seda yayi sanyi, ta ajiye kofin hannun ta ta dauke kai taƙi kallon Jalila, A hankali Jalal ya tako yazo gaban Mummy shima ya durƙusa akan gwiwowin sa ya ɗora Haidar akan cinyar Mummy yace "Mummy na, ga Abunda aka haifa min ba danni ba ba dan halina ba ki sawa jikan ki Albarka, koba komai ke kika haifi ABDUL JALAL ɗanki ɗaya tilo, kuma wannan jininsa ne, sannan zanyi Amfani da wannaan dama gurin neman Afuwar ki akan Abubuwan da nayi miki a baya, Mummy na, tabbas Jalila ta fini gaskiya duk abubuwan da kikayi min a baya, be kamata in saɓa miki ba duba da irin wahala da ɗawainiyar ciki da haihuwa ta da kikayi, ban taɓa ƙinki ba ke mahaifiya ta ce, halayen kine bana so, Mummy na kuɗi da ɗaukaka ba komai bane abubuwa ne da suke fararru ƙararru lokaci daya se Allah ya ƙwace abunsa, Amma soyayya da mutunci basa taɓa gushewa indai anyi sune dan Allah, Ki yafemin sannan dan Allah ki dena ƙin Jalila saboda haakan yafi komai cutar da zuciya ta, Mummy Jalila bata da wani laifi da ta aikata miki da ta cancanci ƙiyayyarki, kin manta alkhaiaran ta a gare ki? Kidinga hukunta mutum da alkhairin sa ba sharri ba" Ƙurawa Haidar dake hannun ta Ido Mummy tayi, sak Jalal lokacin yana Jariri, ta tuna yadda Daddy yake bin ta Jalal yana kuka, Daddy yana haɗa ta da Allah ta shayar da Jalal, kamar Mummy na da Jalal yayi Amfani da ita ya tuna mata yadda In tazo hutu Jalal yake bin ta yana Mummy na dan Allah karki tafi ki barni, dan Allah ki zauna a gida ki dinga bani Abinci. Ta tuna yadda ya taso me biyayya daga baya rayuwarsa ta tarwatse sanadiyar sakaci da kuma kwaɗayin ta, dama Jalal ze shiryu har ya iya durƙusawa ya nemi Afuwar ta? tabbas ita ya cancanci ta nemi Afuwar sa dan tun bashi da wayo ya sha wahalar kadaicin rashin kulawar uwa. Take taji ƙaunar Jaririn ya mamaye ta, inama da zata dawo, inama Jalal taiwa wannan kulawar lokacin yana kamar Haidar Rungume Haidar tayi ta fashe da kuka. Daddy yace "ba kuka zakiyi ba, yara na durƙushe a gaban ki, rashin kyautawa dai kinyi ta tunda har seda suka zo suka kawo miki jariri da kansu" Mummy tace "Jalal ɗina ni namaka laifi tabbas, ba inda yaron nan ya barka a kamanni irinsa sak na haife ka, sedai na gaza cika haƙƙina na uwa akanka, nabi son zuciya, ruɗin duniya da kuma ƙawaye na ajiye ka na tafi neman duniya, ƙarshe ga duniyar ta samu amma Alhakin Mutanen da na ɗauka ya dinga bibiyar ka yanzu kowa ni yake jin haushi kowa laifi na yake gani, Haihuwar yaron nan ya tunamin abubuwa da dama da suka gabata" Kuma fashewa tayi da kuka tana shafa gashin kan yaron tace "Jalal am sorry forgive your Mum please" Jalal ya zauna kusa da Mummy yace "Mummy na babu buƙatar ki nemi yafiya ta, wahalar da kika shiga kafin inzo duniya ya isa in duba ta in miki biyayya amma idona ya rufe, Alfarma ɗaya nake nema a gurin ki yanzu" Ta kalleshi alamar ina jinka "Mummy so nake ki ɗauki soyayyar da nakewa Jalila a matsayin tawa ƙaddarar kuma sakayya akan abunda kikayi a baya, Mummy ni kaina ban san wane irin so nake mata ba, Amma Mummy Jalila ta cancanci in so ta ne, Mummy kin san waye ni a baya, kin san irin ƙazamar Rayuwar da nayi, amma kalleni yanzu, jajircewar tace ta saka na gane ni me laifine nazo na durƙusa ina neman afuwar ki, baki nasha faɗar Jalila itace silar haske a rayuwa ta amma baki ɗau hakan da mahimmanci ba, Amma zan gaya miki dalilin da yasa bazan iya cutar da ita ba nake matuƙar son ta, Mummy idan duniya da gaskiya be kamata in wulaƙanta 'yar da Ummi ta haifa ba, dukda ba kya garin nan Daddy yasan komai yasan ita ta maye min gurbin uwa a lokacin da kikayi nesa da ni" Nan ne ya zauna ya dinga warwarewa Mummy zare da abawa, Daddy yana tuna masa abubuwa da dama, har kawo lokacin da Jalila tazo kano suka haɗu, hatta ɗuren hayaƙin sigari da yayi wa Jalila seda ya faɗe shi, ya bata labarin gwagwarmaya da fama da Jalila ta dinga yi da Ilham akansa da wahalhalun da ta sha da abokan da suke sashi shaye2, Hanan ma seda ta faɗin abubuwan da shi kansa Jalal ɗin besan anyi su ba. Shiru Mummy tayi ta sunkuyar da kai, ta kasa ɗaga kai ta kalli kowa a falon. Jalal yace "dan Allah Mummy ki tayani son abunda nake so, idan kikayi yunƙurin rabamu banyi mata adalci ba, ban kyauta wa Ummi ba kuma naci amanar Abee, Mummy Jalila ta sha wahala ta, in dake ta, in zage ta in ranƙwasheta har hayaƙin sigari na bata saboda tana takura min, Amma bata karaya ba, ta cigaba da bani kariya da kulawa, itama in hakane ya kamata ta ƙini saboda abunda nayi mata, please Mum kiyi hakuri ki kyaleni da matata wallahi ina sonta " Hawaye Mummy ta cigaba da gogewa amma ba tace komai ba. Daddy yace "Deejah kiyi magana mana" "Daddy mezan ce, inajin kunyar abunda na aikata, nayi kuskure masu yawan gaske tabbas sakayya ce tasa Allah ya jarabci Jalal da son matarsa, da a tunani zan iya kaucewa ayimin abunda nayi shiyasa naso in zaɓo masa mace da kaina, Amma ba'ayi wa Allah wayo, Alhamdilillah Jalal ka samu sauyin Rayuwa, ina matuƙar jin kunyar ka da matarka, tabbas matar ka ba ta dukiyar ka take ba, kaine a gaban ta da rayuwar ka, tabbas itada Jawwad sun taka mahimmiyar rawa a rayuwar ka, wanda ni ban sani ba, dan Allah kuyi hakuri ku yafe min" Murmushi Jalila tayi ta sunkuyar da kai tana share hawaye tace "Nidai Mummy in dai kin yafe wa Jalal shikenan" Haidar ne yafara motsi zeyi kuka, Jalal yace "Mummy kawo shi" "A'a Jalal ka ƙyalemin shi mana, zan iya rarrashin sa ai Gani nake kaman kaine lokacin kana jariri" Jalal yace "A'a Mummy ke ɗanki ya girma, wannaan ɗana ne idan kina so to kimin ƙani" Hannu tasa ta talle ƙeyar Jalal tace "sannu mara kunya" Hajiya Salma tace "Masha Allah, naji daɗin faruwar hakan, ina fatan zaki dena zarginmu akan mun aurawa ɗanki yarinya bada izininki ba, ba muyi hakan dan cutar da shi ba, wanda be guje ka ba lokacin mutane suna gudun ka ba, to tabbas shine masoyin gaskiya" Mummy tace "Hakane kema Salma kiyi Hakuri dan Allah ki yafe min, tawa tayi kyau da Allah be jarabce ni kamar yadda ya jarabci 'yar uwa ta Saudat ba, Daddy dan Allah ka tayani neman Afuwar family ɗinka, tabbas na aikata kurakurai masu yawa a rayuwa ta" Jalila tace "Mummy aishi Allah me Rahama ne da jin ƙai babu ruwansa da girma da yawan laifukan ka, indai harka roƙe shi afuwa ze yafe maka" Mummy tace "Jalila ban san haka al'amuran suka faru ba, na miki wulakanci na ci mutuncinki dan Allah ki yafe min" "bakomai Mummy abunda yafi komai yimin daɗi be wuce ganin dai daita warki da Abban Haidar ba" Sosai Mummy tayi nadamar abunda tayi, sega Mummy da kanta take neman yafiyar wanda taiwa laifuka, Sosai take nunawa Jikan ta ƙauna ta ɗauki son duniya da tattali take wa Haidar. Ummi tayi Aure, ta Auri wani ɗan uwan ta a can garin su. Ilham kuwa seda aka kaita Asibitin masu tabin hankali saboda zabure zaburen da take yi, Umman ta kuma se gidan gajiyayyu aka kaita a can ta rasu. Yaya mairo ma komai ya kwaɓe mata, Naja ta zama tantiriyar 'yar ƙwaya kuma karuwa, Sa' adah kuwa tana can gidan yari. Farinciki ya shiga tsakanin iyalan, duk wata hayaniya da abubuwan da Mummy tayi ta sauke su a gefe ta rungumi carbi tana tuba ga Allah ga kuma jinyar larurarta na hawan jini da ciwon zuciya ga ciwon sugar. Dukiya gata a jibge amma babu lafiyar morarta yadda ya kamata, ga shekaru sunyi nisa. Daddy ya dawo Nigeria domin ya huta girma ya kama shi, ya ɗora Jalal akan al'amuran ya cigaba da kula da komai, ya canza gida ya haɗe Mummy da Hajiya Salma a gida ɗaya. Seda Jalila ta haifawa Jalal yara shida, Haidar kam gurin Mummy ya koma da zama saboda ƙaunar da take nuna masa. Haka Nana da Hanan suma sun hayayyafa suka Cika gida da 'ya'ya ga soyayya da ƙaunar juna da ya wanzu  a tsakanin iyalan TAMMAT BIHAMDILLAH ALHAMDILILLAH ALA KULLI HALIN DUKA DUKA ANAN NA ƘARƘARE WANNAN LITTAFI ME SUNA ABDUL JALAL ALHAMDILILLAH  ƘWARIN GWIWARKU DA ƘAUNAR KU CE' YAN UWA DA MASOYA TA KAINI GA KAMMALA WANNAN LITTAFI. JINJINA DA GODIYA TA MUSAMMAN GA IYAYENA DA ABOKAN ARZIKI NAGODE DA KULAWA DA ƘAUNAR KU ABDUL JALAL NOVEL FANS GODIYA TA MUSAMMAN BAZAN MANTA DA GUDUNMUWAR KU BA INA ƘAUNAR KU, KUN ZAMA WANI ƁANGAREN FARIN CIKI NA RAYUWA TA. PERFECT WRITER'S ASSOCIATION ƘUNGIYA DAYA TAMKAR DA DUBU, GODIYA TA MUSAMMAN A GAREKU 'YAN UWANA, ALLAH YAKARA MANA KAUNAR JUNA YA KAIFAFA ALƘALAMINKU. INA FATAN AN AMFANA DA SAƘONIN DA DARUSSAN DAKE CIKIN WANNAN LABARI, KURA KURAN CIKI DAGA GARENI NE INA FATAN ALLAH YA YAFEMIN INA FATAN DUK WANDA NA ƁATAWA RAI, KO WANI LAIFI DAN ALLAH YAYI HAƘURI YA YAFEMIN. INSHA ALLAH ZUWA BAYAN SALLA IN ALLAH YA KAIMU ZAN SANAR DA KU LOKACIN DA ZAN CIGABA DA KAWO MUKU SABABBIN LITTATTAFAI NA ƘOFATA A BUƊE TAKE DOMIN KARƁAR GYARA SHARHI, ƘWARIN GWIWA KOKUMA ƘORAFI. TAKU HAR KULLUM AISHA HUMAIRA DADDY'S GIRL WACCE KUKAFI SANI DA AYSHERCOOL WHAT'S APP 07063065680 WATPAD @ AYSHERCOOL7724  WWW.HUMAIRA17@GMAIL.COM Nafara wannan littafin July 2020 Na kammala a April 2021 Alhamdilillah