[5:07PM, 7/13/2017] ‪+234 706 196 7803‬: 1) A DAREN FArko kotun ta yi tsit, kowa ya yi jigum, ana sauraran abinda xai fito daga bakin alkalin wanda yasunkuyar da kansa yana rubuce- rubuce. Lauyoyi dasauran ma,'aikata wadanda suke da alhakin zama a kotun sbda sauraron shari'ah, kowanne yana xaune a mazauninsa daya dace dashi,haka yan kallo da iyayen yarinyar da ake gudanar da shari'ar a kanta al'amarin yan ba kowa tausayi shiyasa indai mutum yakalli fuskokin kaso tara cikin goma na mahalarta kotun sai kaga kowa cikin matsananciyar damuwa musamman wadanda abin yashafa, iyayenta da yan uwanta knan. Mai shari'ah usman muhammad yadaga kansa a hankali yadubi wacce ake ka ra tana tsaye inda ake tsaida wadanda ake tuhuma hannayenta biyu sanye da ankwa. Bakar rigace a jikinta da bakin hijjabi sanye akanta, ba dankwali idanuwanta sunyi wani irin ja saboda tsabar kuka, ba ta son dago kai tadubi kowa saboda tsanar kanta datayi don haka ma da alkalin yakira sunanta bata dago kanta ba ta dai amsa cikin dashashiyar murya wadda da kyar ake iya jin abinda ake fada. Alkalin yakuma cewa "Fatima Musa" Ta amsa "Na'am" "Ke kika kashe doctr Abubakar saddik wanda akafi sani da doctr khalifa??? Fatima tayi shiru alkali yana maimaita tambayar har sau uku batayi magan ba, yadda kasan kotun ba kowa saboda tsabar shiru, koda fatima da mai shari'a yake kallo ana sauraron abinda fatin xa tace amma taja bakinta tayi shiru kamar dam chan yadda Llah yahalicce ta ba ta da bakin magana. Mai shari,'a Muhammad Bamaina yana magana cikin yanayi na tausasa harshe yace "Fatima kotu tana tuhumarki da laifin kashe mijinki Dr. Khalifa kamar yadda ka kamaki da gawarsa shiyasa muke son ki bayyanawa kotu gasjiyar al'amari da bakinki tunda ke ba bebiya bace kuma ba kurma bace kina jin abinda muka fada kuma kina iya magana. idan ke kika kashe shi kifadawa kotun sannan kifadi dalilin dayasa kika kashe shi, idan ba ke bce ba to kidanyi magana kiyi bayani. Fatima tadago kanta a karo nafarko tadubi duk jama'ar kotun suka hada ido da mahaifiyarta wadda tazuba tagumi dukda nisan dake tsakaninsu da Fati, Fati ta san kuka take wiwi tana girgiza kai, Fati tadubi mai shari'a sai kawai taj kanta yana juyawa kafafunta suka shiga rawa, hakan yasa suka gaza cigaba da daukar gangar jikinta tazube a gun, nan take mai shari'a Usman M Baina yadaga shari'a zuwa uku ga watan gobe idan Allah ya kaimu. Kotu tarude da hayaniya, koke koken iyayan fati da yan uwanta ya cika kotun ga uar uwarsu a matsananciyar hali amma ba yadda xa ayi su taimaketa, sunaji suna gani wasu yan sanda mata suka daga fati aka fice da ita da gaggawa sbda numfashinta ne yake sama saa kamar zai dauke. *******×*×***********×***×******×** Yammaci ne akalla za mu iya kiran lokacin karfe biyar na yamma dawasu mintuna, ummi na zaune gefen tabarma ta hada kai da guiwa tana kuka kamar ranta xai fita, goggo Abu ne gefenta itama tana goge hawaye cikin yanayi na tsananin damuwa kobaka sansu ba kaga halin dasuke ciki sai ka tayasu wnnan kuka dasuke, ko ba a maka bayani ba ka san damuwar daxata sa a yi irin wannan kuka ya isa a tayashi kuka. Malam musa yashigo da carbi a hannunsa yayi sallama yatsaya chan daga bakin kofa yana kallonsu tsawon mituna biyar sanan ykaraso inda suke ,Allah sarki bawan Allah mai saukin kai wanda bai dauki duniya a bakin komi ba, fuskarsa cike da tausayi da karaya yake kallonsu ya ka sa magana, xuwa chan goggo Abu tagoge hawayenta cikin karfin hali tace "Malam ka dawo?? sannu daxuwa. Ya daga mata hannu yace ba na son gaisuwar ta kui tunda idanuwanku baxasu daina xubda hawaye ba akan abinda ba xai yi mana amfani ba. kokuwa wannan kukan xaiyi mana magani akan damuwar damuka samu kanmu aciki?? Goggo Abu tace "Mala to yaya xanyi tunda abinnan yfaru ummi bata daina kuka ba. na yi lallashin duniyar nan yarinyar nan ta ki daina kuka har na rasa wacce kalma xan gaya mata wanda xa yasa tayi hakuri. Malam yace "Ummi kiyi hakuri ko mu damuka haifi fatima babu abinda xa mu iya akan wannan lamarin sai dai addu'a. Cikin matsananciyar damuwa Ummi tace "Shin baba shikenan daga hakuri babu abinda xa ku iya gaya min wanda xan samu sassauci a xuciyata game da halin da fatima take ciki??? Wyyo Allah kaicon rayuwata ni ummi in har xan xauna ina rayuwa a cikin tunannin fatima na kulle a kurkuku ana tuhumarta da laifin dani daku daduk duniya sun san baxata taba iya aikata shi ba. Ya ya xa ayi ace fatima xa takashe rai, kisan ma ace tarasa wanda xa takashe si mijinta? kadubi wannnan al'amari ayi wani abu akai har yaushe muna zaune fatima na cikin mummunan zargi irin wannan". Malam. musa yai xaman dirshan a wurin yace "Ummi toh yaya xamuyi? Saboda girman Allah me kike ganin xa mu iya yi kinsan indai ace muna da bakin yi din da yanxu ba wannan xancen akeyi ba. kinsan mudai ba kudi garemu ba, kuma ko idan mutum na da kudi idan akace case din me xafi ne da tsanani irin wannan ba ka da tacewa, kudinka ba xa suyi amfani ba dan ba xa su sayi ran da aka kashe ba balletana kasiya domin ko da ke biyan diyya idan wani yakshe wani ba a irin wnnan yanayin ake biyan diyya ba kinsan ita shari'a sabanin hankali ce, duk yadda kaje tunaninta ta wuce nan. Kuma idan ma muna da abin yin a yanxu ba xa mu iya ba idan Fatima ba ita takashe docta Khalifa ba tai magana man a kotu, kinaji kina gani daxu a kotu ka sa magana tayi ,tayi shiru tabude bakinta tace ba ita takashe shi ba tafdi yadda abu yafaru akalla idan ma akwai abinda za a yi ai a yi tunda tayi shiru me za ace?? Yagirgiza kai cikin dan zuciya yace "Allah kadai yasan yadda wannan abu yakasance sai kuma fatima. Ummi taciji yatsa har yanxu kuka take mai ciwo a rai tace "Shi kenan baba shikenan goggo tunda kuma kun yarda fatee ita takashe doctor sai kusa ido itama a kasheta ba tare da hakkinta ba, amma dai inaso kusani ko ku kuka haifi mutum to ba kune kuka halicceshi ba yadda kake da hakkin yayi ma biyayya haka shima yanada hakinsa akanka idan kadanne Alah subhanahu wata'ala xai tuhumeka baba. Nikam ba xan bar maganar fatee tawuce haka ba ,ba xan bari acigaba da xalintarta akan abinda bata aikata ba, zan shiga infita ko xan rasa zanin daurawa sai na taimaki Fati Insha Allahu. Malam yace ummi ba na shakku akan abinda kika fada mun tabbatar xa ki aikata fiye da abinda kik fada akan fatima kaunar dake tsakananin ku ya wuce a fadadeta da baki, Allah kadai yasan iyakacinta, sai dai inason kisani ba wai mun yarda cewa fati itace ta aikata kisan ba, kifahimci wani abu day ummi ba mu da kudin daxamu iya daukan lauya daxai kare fati, ba ki da bukatar mugaya miki halin damuke ciki na kaka ni ka yin rayuwa a gidannan kinsan kome da ina mukaga halin daukar lauya sannan idan ma mun dauka dawacce hujja xa mufidda fati daga wannan zargi tunda ta ki magana? wannan shi ne a dalilin dayasa muka mikawa Allah lamuranmu, idan fati ba ita takashe likita ba insha Allahu Llah xai bayyanar da gaskiyar alamari Allah xi kawo mana mafita. Ummi duk wanda na sa yashiga matsanancin hali irin wannan ya gama kwanciyar hankali kada kidauka bamu dmu da ita ba illa iyaka shi lamari irin wannan idan kaga kanka acikinsa ba ka tsananta damuwa wadda ita dama rayuwa jarravawa ce acikinta, idan Allah yajareba ka dawani alamari kagode masa kawai karokeshi yabaka juriyar cin wannan jarbawa dayayi maka domin ba wanda ya isa yakaucewa jarabawar Ubangiji . kiyi hakuri ummi. Ta jinjina kai yace "Na hakura baba, na hakura dakuka na hawaye, tunda ba ka son ganin hawayen saidai ba xan iya hakuri da fati ba ko da nima xan shiga halin datake ciki, ko nima xan rasa raina, idan ba halin daukar lauya ai muna da halin daukar akwai guraren da ake taimako a samu agaji su taimako ne a gabansu kawai a gabansu ba kudi ba, su ake kira gatan mara gata" Goggo tace"Allah shi ne gatan mara gata shi xai xama gatanmu, Ummi kiyi hakuri" Tayi murmushin karfin hali tace goggo nakanyi mamakin masu cewa inyi hakuri akan maganar fati, wa yace banyi hakuri ba? Tabbas na yi hakuri domin na hakura daduk wani farin ciki Insha Allahu akan nemawa fatee hKkinta sai inda karfina yakare ko da hakan shi xai kasance abinda xan aikata nakarshe a rayuwata". *********************************** Suna a wani dan daki mara girma Ummi da Barrister Nuruddin ,aka bude kofar dakin wani kakkauran dan sanda ne a gaba fuskarsa ba fara'a, fati na biye dashi a baya kamar kamar koyaushe bakar rigar nan ce ajikinta da bakar hijabi kai ba dankwali ta rame sossai ta yi duhu idanuwan nan kamar gauta saboda jan dasukayi, hannayenta biyu cikin ankwa, wani dan sanda a bayanta saidai shi fuskarsa akwai sassaucin ra'ayi. Fati tadubi ummi tayi murmushi cikin dasasshiyar muryarta tace "Ummi ku ne? Dan sandan yace "mintunanku ba su dayawa ku gaggauta yin abinda yakawoku dan kar kuyi asarar lokacinku". Ummi tagirgiza kai hawaye wasu na bin wasu ta ta so tadafa kafadar fatima tace "sannu Fati da izinin Allah zai kawo mana mafita a cikin alamarin nan, mun shiga tashin hankli da dmuwa akan halin dkike cki fati inajin ciwon damuwarki kamar xuciyata xa ta buga sbda tashin hnkali. WNnan shine barrister Nuraddin Mustapha,na daukeshi ne dan yazamo lauyan dazai kare ki a kotu. Fati inaso kibamu hadin kai duk tambayoyin daxai miki ki bashi amsa sannan idan anje kotu a zama nagaba kibude baki kiyi magana. Fatima tayi murmushi hade da hawaye tace "Ummi bansan dawani kalamai zanyi amfani gun gode miki ba ,komi nafada ba zai wdatar dxuciyata ba hai inji cewa na nuna miki godiyata kan soyayyar da kikemin dakuma kokarinda kike don ganin kin ceci ryuwata daga wahala. Saidai inaso kifahimci wani abu duk yadda kaso yankewa mutum wahala idan Allai bai kaddara lokacin yankewar wannan wahala ta sa ta yi ba ba za ka iya yanke masa ba. na godewa Allah daya kaddara min shiga wannan hali ina fatan wannan jarabawar da Allah yayimin tazamo kaffara agareni, ummi inaso kisani ban tsananta bakin ciki akan halin danake ciki ba ni a karan kaina wannan kukan dako dayaushe za aga idanuwana na yi inayinsu ne sbda tausayin iyayena daku yan uwana a Bisa halin dxaku shiga ba bakin cikin halin dana tsinci kaina a cikinsa, dkuma uwa uba rashin mijina wanda xuciyata ba ta da juriya akan wadannan abubuwa biyu, wannan damuwar ba zanyi kuka ba inhar akan halin danake cikibne. Zaman danake ummi ina jiran ranar da za ayanke min hukuncin kisa ne inbi mijina. idan har akwai taimakon danake da bukata daga gareku ayanxu shi ne ku taimaka ayanke min hukunci inhuta wannan damuwar kuma kuhuta domin idan an kasheni kun daina ganina dole watarana kuhaura idan ko ina raye haka xa kuyi taxama cikin damuwa. Wannan shi ne dalilin dayasa naki magana a kotu kuma ina nan akan bakana na ba xance komai a kotu ba don ba ni da abin cewa duk abinda xan furta bai wuce ince ba ni nakashe doctor ba, idan nace ba ni nakashe shi ba in neman kariya knan wadda e nufin inci gaba da rayuwa alhali ni kaina banga amfanin rayuwata a duniya ba. Umi kiyi hakuri kiba iyayena daduk yan uwana hakan kirokar min su gafara kowa yayi hkuri yamanta dani ba na bukatar taimakon kowa agareku sai addu'a, na gode kwarai dagaske kada kisake wahalär dakanki gun dauko min lauya....... Ummi takatseta cikin huci tace "Fatima kin amince kidauki laifin daba na ki ba, kin amince kikashe kanki,? wayake kin taimako kin amince kijawa dukkan zuri'arki abin fadi? kina zaton wannan ba zai zama mugun aibi ga zuriarki ba? wanda xaija adinga aibata muku zuri'a mata surasa mazajen aure? Kina zaton idan ankashe ki wani zai sake zama lafiya acikin iyayenki da yan uwanki? To kisauya tunani lauya tunda kince ba kya so na janye shi, amma ko shakka babu kuskure ne babba wanda xa kitafka idan har kikayi ikirarin kece kika kashe docto khalifa alhalin ba ke kika kashe shi ba. Fatima tace toh idn ni nakashe shi fa ummi? Ummi tayi murmushin takaici tace ba ke ce kika kashe docta ba, dankuwa ba ki da dalilin kasheshi, kina fadin hakanne kawai dan kin gaji da duniya ba kyason rayuwa a halin da kinason ki gaggauta barinta, shiyasa kike furta abinda xai raba ranki da gangar jikinki". Dan sanda yace "Lokaci ya yi" Ummi tace kayi hkuri ina fada mata abinda xai amfaneta ne. Yace ba shi da amfani gareta da saita karba kidaina wahalar da kanki. Ya tisa keyar fatee, kallon data waiwayo tayiwa ummin tawuce shiya sa tsigar jikin ummi tashiga tashi tazube a kasa tarika kanta da hannu bibbiyu. Shi kansa barrister nura jikinsa ya yi sanyi, ya jima xaune agun yana kallon ummi daga can yadan ja numfashi yace "Tashi mutafi ummi tun anan na tabbatar yarinyar nan fati ba ita takashe docta ba dukda Cewa ta ki amincewa daduk wani taimako daxa abata ta rufe duk wata kofa takariya daxa a ba ta, bawani abune kuma yasatayi hakan ba ta yi ne kawai sbda bakin ckin dake damun xuciyarta wanda yake tafarfasa xuciyarta yasa rayuwa tafita a zuciyarta. Hakan yasa taki mgana a kotu sannan taki yarda da taimakon da za a ba ta, ba komi Llah yana tare damasu gaskiya, sannan ba ya goyon bayan zalinchi, indai ba ta da hakki dasannu xa kiga hukuncin da Allah xaiyi. " Ummi bata kuma cewa komi ba har suka fice daga gun. [5:07PM, 7/13/2017] ‪+234 706 196 7803‬: A DAREN FARKO 2 dasauri yagoge hawayen dake zuba a idonsa jin sallamar matarsa, goggo Abuwa tazauna sharaf a gabansa jikinta na rawa ta ajiye flask d'in abincin datazo kawo masa, yadda jikinta ke rawa haka muryarta take rawa, tace "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un malam kuka kake? Yayi d'an murmushi yace "haba dai kuka ba kuka nake ba Zainabu. " Tace "Dom Allah karkace haka malam bayan na gani da idona kana kukan kuma na ji shasshe'kar kuka, malam idan kayi kuka akan wannan al'amari mu kuma yaya za muyi da ranmu? Kai kake nuna mana muyi ha'kuri bisa fushi dayin Allah me zai sa kai kayi. " Malam musa yace "Zainabu al'amarin nan yana matu'kar bani mamaki da d'aure min kai, ya ya za ayi fati ta iya kashe mutum? idan munce ba ita takashe shi ba wa ne yakashe shi? alhalin da Ita sai shi a gidan d'akin a rufe da sakata taciki. Meyasa fati takashe Dr. khalifa me yayi mata? Meye iyayen khalifa basu yimana ba? shi kansa khalifan meye bai yi mana ba? Ace fati tarasa tukuicin dazata saawa wad'an nan bayin Allah saida wannan mummunan aikin? " Goggo Abu tace "malam ka yarda fati ita takashe Dr. khalifa? Yace "to zainabu idn a ita bace waye? daga ita sai shi a d'aki yashiga yarufe 'kofa shi zai kashe kansa ne zainabu? " Tayi shiru na lokaci mai tsawo, daga bisani tajinjina kai tace "ko shakka bbu acikin wannan al'amari akwai rikitar da 'kwa'kwalwa sannan duk wanda yayi wannan aikin wanda yasan sirrin gidan ne, tabbas fati ba ita takashe dr. khalifa ba don ba ta da dalilin kashe shi ko tanada dalilin kashe shi ba ta da 'karfin halin dazata aikata wannan mummunan aikin, saboda zuciyarta tanada sau'ki akan al'amura, Allah kad'ai yasan yadda al'amarin nan yakasance. " Cikin sanyin murya malam yace "Zainabu nima abinda yake damuna knan kowa ma haka yake fad'a su kansu iyayan khalifa haka suke cewa basu yarda fati takashe shi ba, to amma meyasa ba za tayi magana akotu ba idan akaci gaba da tafiya a wannan hali za asamu mafita ? Tunda ba ita bace tayi magana mana " Goggo tace "wannan shi ne abinda yadamu kowa ma ba kai kad'ai ba malam. " ************************************ Kasancewar mahaifin marigayi Dr. khalifa babban mutum,d'aya daga cikin masu fad'a aji a cikin gwamnatin garin yabasu damar ganin fatima cikin isashen lokaci batare da tsayawar 'yan sanda ba, ko kuma ankwa. Alhaji Muhammadu Nazif mahaifin marigayi Dr. khalifa da hajiya maijidda mahaifiyarsa suna zaune a wani babban d'aki da aka 'kawata da kujeru, Malam musa da goggi suna zaune gefensu sai babban wansu fatima dakuma ummi da Barrister Nuraddeen, fatima na tsakiyarsu kanta a 'kasa ba kuka takeba su d'in ne baki d'ayansu ke sharar 'kwalla sakamakon matsanancin tausayi da bayanin datake furtawa yabasu Alhaji muhammad yace "Fatima abinda nakeso kigane shi ne dukkanmu nan mun san ba ke kika kashe Dr. khalifa ba sbda kamar wanda zaiyi kisan kai ya fita daban, ko da auren dole akai maki dashi ba za ki iya kashe shi ba balletana anyi auran nan ne da amincewarki, ke yarinya ce mai biyayya ga iyayenki, wadda kike zaune dakowa lfya kowa na yabon kyawawan halayenki tayaya za ayi Muyarda kin kashe Dr. khalifa. Ki bud'e bakinki fatima nan ba kotu bane mu ba lauyoyi bane mu iyayenki né duk duniya ba wanda kike dashi wadanda suka fimu idan rufin asiri ne ba rufin asirin dayafi na Allah, ba wanda zai rufa miki asiri bayan mu, kigaya mana saurin lamari waya kashe Dr khalifa ?? Falon yayi tsit kamar ba kowa sai 'karar A. C ko motsi fati batayi ba ballantana tabasu amsa, malam yace "fati dame muke magana kigaya mana yadda akayi idanma ke kika kashe khalifa ya ya za muyi dake ? khalifa dai ya mutu kuma ba zai dawo ba, fad'a mana gaskiya shi yafi dacewa, kullum hankalinmu a tashe yake fati ba mu da sukuni idan mun kwanta don muyi bacci bacci ba ya yiwuwa, abinci ba ya ciyuwa, muna cikin matsananciyar damuwa ,bansan dawani ido zan kalli iyayan khalifa ba, bansan da wanne ido zan cigaba da kallon 'yan uwansa ba damutanan unguwa, ba wani abu ne ma ba fatima shirun dakikayi har yau baka fad'i Wata magana wadda za a kama ba akan maganar nan kin mana adalci, dukkan 'yan uwansa da masoyanki kowa yana cikin damuwa. " "Ni na kashe shi baba. " Akayi tsit kowa yazuba mata ido, maijidda kallonta kawai take ta yi tagumi d'ansu da suke mutuwar so khalifa ta sake rushewa da kuka, Goggo Abu tace "shikenan tunda kince ke kika kashe shi to lallai ne kidaina wahalar da mutane idan anje kotu kifad'i dalilin dayasa kika kashe shi, kin san ba wai kice ke kika kashe shi kiyi shiru ba dole ne kifad'i abinda yasa kika kashe shi. Ummi tari'ke hannun goggo tazaunar da ita tace "goggo me mye amfaninki yi hushi da fati alhalin kowa anan ya san takura matan da akayi da maganar nan yasa tace Ita takashe shin to haka idan ma akaje kotun aka takura Mata abin da za tace knan 'karshe idan tace ita takashe shin dole tayi shiru tunda ba ta da dalilin dazata fad'a wanda yasa takashe shi. " Goggo tace "shikenan ummi haka za muyi tazama cikin damuwa tunda ba ita takashe shi ba idan anje kotu ta fad'i Iya abinda tasani mana. " Fatima tana kuka tace "kiyi ha'kuri goggi ba'kin cikin damuwar danasa ku ya fi damuna fiye dakowa sai dai ba yadda zanyi, goggo ba zan iya cewa ba ni nakashe Dr. khalifa ba sbda gaba d'aya bayanan sun tabbatar dacewa ni nakashe shi." Kuyi ha'kuri shirun danayi a kotu wannan shi ne abin da yafi damuwa na, idan nace zanyi magana bansan abinda zan fad'a ba 'karshe dai na san duk abinda shirun na wa zai haifar bai wuce a yanke min hukuncin wanda yayi kisan kai bane a kashe ni. To dama abinda nake jira knan, ni kam rayuwa ta 'kare a guna sai dai sai dai jiran lokaci ko ba'a kasheni ba ba'kin cikin halinda iyayena kuka shiga a sanadiya ta da ba'kin cikin rashin mijina shi zaisa zuciyata tabuga in mutu ba zan iya cigaba da rayuwa ba shi yasa ba na bu'katar taimako tako wani fuskar lauya don ku'butarwa idan akwai abinda nafi bu'kata bai wuce addu'a ba, wannan ba sai na ro'keku ba na san kuna yi min. Dan Allah kuyi ha'kuri kuyafe min babu abinda zan iya cewa a kotu. Aliyu yayan fati yayi mgana a karon farko tun zamansu a d"akin yace "fatima bamu amince kici gaba dayin shiru a kotu ba dole kiyi magana. " Tace "shi knan yaya zanyi magana. Alhaji muhammadu dakowa yafi sani da, abba yace "kar kice ke kika kashe shi fati". Tace "Abba idan nace ba ni nakashe shi ba waye? idan kuma akayi bincike aka gane ni d'in ce abinda ake gudu shi zai faru, kuna fad'in hakane don fa kusamar min mafita wadda za ta ba ni damar ci gaba da rayuwa a duniya, yayin da ni kuma ba na son rayuwar ta fita daga raina so nake na mutu na bar duniya yadda mijina yabarta. " Aliyu yace "Anya fati baki samu ta'bin hankali ba? " Tace "lafiya 'kalau nake yaya ".kowa yarasa abin fad'i a kayi shiru. ********************************************* ********* Da sassafiyar ranar daxa a koma kotu hajiya maijiddah da akafi sani da mama tana kwance kan faffad'an gadonta na alfarma tunani da ba'kin cikin duniya ya isheta tarasa abin dake mata dad'i, tana mutuwar son D'anta an kashe mata shi wata 'kanwarta dake tayata zama wato anty sadiya tashigo d'auke da abincin karin kumallo tazauna kusa da ita suka gaisa tace "kidaure ki sha ko da ruwan sanyi ne zama da yunwa ya fi komi illa duk abinda yafaru rubuttaccen alamari ne babu wanda ya isa yago ge shi. " Tami'ke zaune tazubawa anty sadiya ido tace "anty sadiya kina ganin haka yadace mu zubawa lamarn nan ido kullum Alhaji yana cewa fatima ba za ta kashe khalifa ba toh ni so nake agaya min wa yakashe min d'ana? Anty sadkya tace "tabbas kam fatima ba za ta iya aikata wannan mugun aiki ba abinda yake da sar'ka'kiya shi ne daga shi sai ita a d'akin to waye yashiga yakashe shi? Mama tace "ke sadiya idan ma ba ita takashe shi da hannunta ba to da had'in bakinta aka kashe shi sbda ana ganin ubansa yana da dukiya d'ansa d'aya ne ko don a mallake dukiyar ubansa za ta iya yimasa haka. Anti sadiya tace "kigafarce ni amma ban tari numfashinki ba to amma idan haka ne da had'in bakin fatima ya ya za ayi ita data kasheshi ko ta had'a baki aka kasheshi bata gudu ba har akazo aka kamata? Allah (SWT) dasu kuma mahukuntan tunda Allah yabasu basiran gano gaskiyar wannan alamari cikin hikima da izinin Allah za su gano mana wanda yakashe mana d'a jininsa ba zai tafi a banza ba. A bisa hanyarsu tazuwa kotunne cikin mota mitar da mama ke tayi wa abba kenan yayi tsit yana jinta ko tari vaiyi ba ya yi tagumi yana jan charbi. Suna shiga su malam da goggo suka shigo suka gaisa, Abba yace"malam bana jin dad'i Yadda kake kaucewa had'uwa dani tunda wannan abu yafaru. " malam yarufe fuskarsa da babbar riga dan kar abba yaga fuskarsa yace "haba alhaji me, zan ce dakai? menake dashi wanda zan gaya maka dahar zaisa intsaya in kalleka, kaico. Ina ba'kin ckin faruwar wannan alamari har ina cewa ina ma ace banzo duniya ba da dai ace 'yar cikina ta kashe d'an mutumin kirki kamar kai d'in nan Alhaji muhammadu. Abba yaja hannunsa suka wuce cikin kotu ba tare dayace komi ba, wuri d'aya suka zauna mutane suna mamaki sosai yadda suke ganin iyayan wanda aka kashe da iyayan wacce ake zargin ta yi kisan. wannan abu yana matu'kar baiwa mutane mamaki haka zakaga jama'a na kallonsu, yai d'in ne ma dai hajiya maijidda tasauya fuska sama sama suka gaisa ba wani magana dasukayi fuska tamau ko da aka shigo da fatima ma ko kallon inda take batayi ba. ummi kamar ta fi su kansu fati shiga tashin hankali ta rame ta lalace . Fati na shigowa kotu da ummi suka fara ido sannan tadubi iyayanta dasauri tad'auke idonta xuwa 'kasa tashin hnkali datake ganin iyayanta a ciki ko wannan ma ya ishi mutum tashin hnkli da ba'kin ciki ina amfanin rayuwarta. Yau kam duk abinda zai faru sai dai yafaru lallai sai ta kawo 'karshen wannan zaman kotu. Bayan da akayi abubuwan daya dace ayi aka zauna mai karanta 'kara yakaranto, tuhumar da akewa fati na ta kashe mijinta a ranar da aka d'aura musu aure a daren farko. Mai shari'a Usman Muhammad Bamaina yace "fatima musa kinji tuhumar da ake miki a karo na biyu? " Ta gyad'a kai tace na ji ya mai shari'a, yau kowa na jin muryarta sosai, kuma kowa ya ji dad'in yadda tayi mgana har alamun natsuwa a fuskar iyayanta da 'yan uwanta musamman ummi wadda har tsima jikinta yake a ranta tana fad'in yawea fati gara ki yiwa kanki adalci da iyayanki damu masoyanki.Mai shari'a yace "fatima musa me za ki iya Fad'awa kotu akan haka? ma'ana kin amince ke kika kashe mijinki Dr. khalifa.? Kai tsaye fati taware muryarta tace "Eh ni na kashe shi ya mai shari'a. [5:07PM, 7/13/2017] ‪+234 706 196 7803‬: A DAREN FARKO 3 Gabad'aya kotu tarud'e da sallalami kowa na fad'in albarkacin bakinsa ,iyayan fati dasu kansu surukan suka rud'e, ummi kuwa hannu tad'ora aka tana fad'in "wayyo Allah na wayyo fati meyasa kikace ke kika kashe Dr. khalifa bayan ba ke kika kashe shi ba. Mai shari'a yayi tsawa akayi tsit sai dai kukan 'yan uwan fati da ba ya 'karewa, ita kuwa fatin yau tana tsaye 'kyam ko gezau gadukkan alamu zuciyarta ta fara soyewa, idanuwan amma ba kuka take ba zafin zuciya ne, ba ta son takalli iyayanta taga mummunan tashin hnkalin dasu ke ciki, dama chan ita mutum ce mai tsananin tausayin mutane balletana iyayenta. Mai shari'a yace "fatima kotu tanason kiyi mata bayanin dalilin dayasa kika kashe mijinki a daren tarewarku. Fati tace "ban san dalilindayasa kika kashe mijinki a daran tarewarku". Fati tace "bansa n dalilin dayasa nakashe shi ba, ba abinda nao na zai iya furtawa a kan haka ya mai shari'a ina ro'kon wannan kotu mai alfarma Data taimaka min tayanke min hukuncin kisa a yau in bar duniyar nan inhuta, ba na son bugawar da zuciyata keyi yazamo sanadin mutuwata na fi son a yanke min hukunci dai dai da laifi na. Tanumfasa tana kallon al'kalin daga bisani tad'auke idanunta daga kansa zuwa kan jama'ar dake kotun, gaba d'ayansu su ma ita suke kallo kowanne da abinda zuciyarsa ke sa'kamasa game da ita. Tayi shashe'kar ajiyar zuciya tace "iyayena da 'yan uwana da dukkan masoya na ina ro'konku don girman Allah kuyafe min wannan yanayi dana sa ku nadamuwa sannan kuyi min addu'a rayuwa ta fita daga raina minti d'aya ba na son in 'ka ra yi a duniya na fi son inbi mijina. " Tayi shiru kamar yadda kotun ma tayi tsit kai ka ce ba kowa a kotun, al'kali yana 'yan rubuce rubucensa, haka a 'bangaran lauyoyi wasu suna rubutu wasu shiru kawai sukayi suna kallon fatima. Taci gaba da fad'in "ya mai shari'a a karo na biyu ina ro'on a taimaka a yanke min hukunci daidai da laifina na amsa laifina ni ce nakashe mijina". Wani daga cikin lauyoyi yami'ke yanemi izinin magana daga gun mai shari'a yace kanada daman magana. Yayi godiya yadubi fatima yace "sunana barrister Abbas Mukhtar inason kare wadda ake 'kara sbda na fahimci ba ita tai kisan ba ina nufin fatima musa ba ita takashe mijinta Dr. khalifa ba ina ro'on wannan kotu mai adalci data ba ni damar yin cikakken bincike a kan wannan al'amari, kuma inason a ba ni damar dazan yiwa fatima tambayoyi akan abinda ake tuhumarta dashi. " Mai shari'a yace "kanada damar yin haka. Yayi dariya yana d'an murmushi ya'kara maida fuskarsa ga fatima wadda itama shi take kallo fuskarta a tsuke, yace "malama fatima musa 'karfe nawa aka kaiki gidan mijin kuma a wace rana ce. " Fatima tayi shiru kamar ba da ita ake magana ba, Barrister Abbas ya'kara maimaita tambayar tare da ro'kon kotu data tursasa fati tayi magana". Mai shari'a yayi hakan amma Fatima cewa tayi "nagode da kake burin taimakona a bisa halin danake ciki, sai dai inason kayi ha'kuri gaskiyar magana ba zan iya ba ka amsa ko d'aya ba a bisa tambayar dakake min sbda ba so nake in ku'buta daga halin danake ciki ba, wanda yake bu'katar lauya shi yakeson yatsira nagaya muku ba na bu'katar rayuwa dan Allah kuyafe ni. Mai shari'a Usman muhammad Bamaina yadubi wani dogon d'an sanda dake tsaye gefe yace "Za a gwada 'kwa'kwalwar fatima don mu tabbatar da mai hankali muke shari'a, idan munyi zama na gaba za mu ji sakamakon sannan mud'ora a inda muka tsaya. Daganan aka d'aga 'karar zuwa mako biyu idan Allah yanuna mana,amma kotun ta ba wa 'bangaran lauyoyi guda biyu damar suyi duk binciken su akan yadda al'amarin yakasance don ba da kariya dawadda ake zargi. Yau ma kamar wancan karon kotun ta tashi da hayaniya kowa na fad'in albarkacin bakinsa akan kafiyar da fati tayi a shari'ar mamakin da take bawa yawancin mutane shi ne tayaya za ayi mutum yace shi ya fidda rai kwata kwata da rayuwa mutuwa yake muradi, wasu suna ganin wannan ya isa kowa ma ya amince ba ita tayi kisan ba, yayin dawasu ke ganin dan ace ba ita bace shi yasa tasallama tami'ka wuya, idan ba ita bace waye? Gida su biyu kachal ba kowa d'aki a kulle su biyu in har ance ba fati takashe Dr. khalifa ba to sai dai ace shi yakashe kansa, hatta hajiya Maijidda mahaifiyar marigayin dayawa daga 'yan uwansu abinda suke gani knan wannan kukan da take abinda suka d'auke shi kukan munafinci ne kawai. A harabar kotun kafin sutafi gaida malam musa ya tsaida barrister Abbas yana masa godiya a bisa 'ko'karinsa nakare 'yarsa, barrister yayi murmushi yace, "Ba komai kada kadamu baba na yi wannan ne domin Allah da tsananin tausayin da fatima ke ba ni tun randa aka fara tsaida ita a gaban shari'a na tabbatar ba Ita tayi wannan kisan ba, duk wanda yakashe Dr. khalifa na gida ne wanda yasan sirrin gidan insha Allahu da izinin Allah zamu gano ko waye,sai dai inason kataimaka min fatima tadinga ba da amsa a kotu sannan xanje inganta kutaima ka min tayimin cikakken bayani duka tambayoyin da zan mata dan insan yadda zan 'bullowa al'amarin. Malam yace "To ni na rasa me yasa fati take tsuke bakinta komi sai tace ba za ta iya fad'a ba sbda rayuwar ta fita Daga ranta. Barrister yayi murmushi yace "bako mi tsananin damuwa ne yasa take fad'in haka, matsayinku na iyayenta ku yadace kulalla'bata tafad'i yadda akayi. Malam yayi masa godiya mai yawa bayan tafiyarsu malam d'in barrister na xaune a motarsa shi kad'ai yana nazarin alamuran fatima tausayin ta har ya yi masa yawa a zuci.,daurewa kawai yau yayi ya zo kotun tun a wancan zaman da akayi hankalinsa yatashi sosai gameda al'amarin yarinyar, tun lkcn abinda yake d'aga masa hnkali matsalar d'aya matsalar kowama ita ce shirun da fati tayi tana neman mutuwa ido rufe ta 'ki ba da had'in kai ballantana a samu mafita. ********************************************* A hankali ummi tafito daga motar tabi bayan mama zuwa cikin gida, kowanne zuciya ba dad'i , a falo suka zauna gaba d'aya yayin da ita ta dawo dabaya zuwa ainihin d'akin Dr. khalifa na gidan har yanzu mukullan d'akin yana hannunta ita kad'ai take bud'ewa tashiga tunda ga lokacin daya mutu zuwa yanzu, komi na nan yadda yake wani irin 'kamshi mai dad'in gaske yana tashi a d'akin, gaba d'aya kayansa nasawa suna jere a cikin wardrobe gwanin ban sha'awa manyan hotunansa da akayi enlargement d'insu guda biyu na gefe da gefe na gadon ya yi kyau ba na wasa ba. Tazauna a gefen gadon tanasa hannu tad'auki hoton tarungume kam kam idanunta a rufe hawaye wasu na bin wasu zuwa chan ta ajiye tashiga bud'e durowowin jikin madubin hotunan bikinsa da fatima ne birjik musamman ma gun lunching da dinner dayawa yarungume fatin ne 'kam 'kam a 'kirjinsa wasu kuma tare da abokanansa maza da mata. Kan cinyar ummi yaji'ke dahawaye kamar ruwa aka zuba mta a cinya tun ranar da aka kashe Dr. khalifa take kuka amma bata ta'ba kuka irin na wannan rana ba, har sai dataji numfashinta kamar zai d'auke. Ba za ta ta'ba mantawa da abinda yagya mata ba a yammacin lahadin daza akai fatima gdansa wanda kuma a wannan rana ce aka kashe shi bai sake kwana a gidan duniya ba. Yana tsaye a harabar gdansu tare da manyan abokansa biyu wad'ana baida aminai kamar su. Manyan likitoci Dr. Hafiz Bala Muhammad da Dr. Mustapha Abubakar kura, yana tsakiyarsu suna hira, sai ita ummi tafito daga cikin gida tana ganinsu tahau yimusu hoto a wayarta, Dr khalifa yaharareta yace "wai meyasa kike daraina mutane ne ummi ni kikewa hoto? Sai Dr. Mustapha yace "kaima kanada saurin hushi khalifa ko wacce rana idan an maka abu za ka 'bata rai banda wannan rana wadda tazamo ta auranka da matar dataza mo allura cikin ruwa kaine kaxamo mai rabon daka zu'kota. " Dr. khalifa yarausayar dakai yana murmushi tare da lumshe ido yace "ka fad'i gskiya Dr. Mustapha tabbas ni ne na cafko wannan allurar data zamo tamai rabo ce, a daidai lokacin dana fidda rai da ita sai najita kawai a hannuna ,tabbas wannan rana ta dace tazamo ta farin cikina, ranar dazan sadaukar da komi na wa sbda Fatima. " Ummi tay murmushi tace "shiyasa nima nake maka hoto domin ka yi min kyawun daban ta'ba ganin ka yi shi ba a duniya dukda cewa kai d'in me kyau ne kullum kyau kake da ado. " Dr. Hafiz Bala yace "har bayan hoto yanada kyau ma yayi miki kyauta ta musamman ummi." Dr. khalifa yayi murmushi yace "ko shakka babu a wannan rana ina cikin farin cikin daban ta'ba samun kaina a cikin shi ba, sai dai kasan tun safiya gabana ke fad'uwa bansan dalili ba wannan yayi sanadin dayasa tun ruwan shayi danasha rabin cup d'azun bayan d'aurin aure ban iyacin komi a bakina ba. Ummi tayi wal da ido tace "fad'uwar gaba kuma Dr. a irin wannan rana? ni dai na san ko kusa bakayi kama da wanda mace za ta ba wa tsoro ba ballantana ince firgita kayi sbda fatima. Dr. Mustapha ya bugi kafad'arsa yace "wa wannan? ni tunda ake ma gwargwadon bud'ewar idanuna ban ta'ba ganin namijinda yayiwaa mata farin sani irinsa ba, farin ciki ne yayi masa yawa sbda soyayyarshi yasa ma gabansa yake fad'uwa....... " Tunanin ummi yakatse a nan lokacin da mama taturo 'kofar d'akin tatsaya tana kallon ummi kukan datake yabata tsoro ta'karaso dasauri ta kamata takwashe hotunan dasuka ji'ke da hawaye ta mayar, takamo hannunta tafito da ita tarufo d'akin takar'be makullin tace "daga yau ko 'kofar d'akin nan ba na so kisake zuwa, haka kada ki 'kara zuwa kotu ba xa muyi biyu babu ba, mun rasa Dr.khalifa muna cikin ba'kin ciki mai tsanani kema damuwa na neman xama ajalinki to B xai yiwu ba. Cikin kuka ummi tace "Don Allah mama kada kiharamta mini shiga d'akin likita, yin hakan ne kad'ai zaisa zuciyata ta sassauta daga damuwar danake ciki, na rasa d'an uwana ga aminiyata na cikin matsancin zargi na bi duk hanyoyin daya kamata inbi don ganin fatima ta ba lauyoyi had'in kai ta 'ki burinta akasheta meyasa ba zanyi kuka ba mama? mama tayi tsaki tace "ina mamakin yadda ke Da Alhaji kuka d'auki damuwar duniya kuka d'orawa kanku akan fatima shin dakuke cewa batace komi ba me za tace, fatima ba ta da abin cewal shiyasa tai shiru, ko a hankalce kun san 'karyane ace akwai. mutumin da ake tuhuma irin hka ya'ki amsar taimako daga lauyoyi don kawai yana burin mutuwa. kinta'ba ganin wanda yazauna yana jiran mutuwarsa kuma yana maraba da ita, saidai fa in ta zo a kar'beta don ba yadda za ayi da ita. Ummi tasaki hannun mama tazubla mlatla ido muryarta a dashe tace "mama shin kina nufin kin amince fati za ta iya kashe likita? Mama tayi murmushi tace "ummi ummi kiji tsoron duk wanda kika taimakawa. Akoda yaushe idan za ki taimakawa mutum to kitaimake shi kai tsaye don Allah ba wai don zai saka maki da alherin dakika yimasa ba, shi dama mutum bbu abinda yake cika cikinsa sai 'kasa shi. mai butulcewa mahaliccinsa ne ma ballantana ace wani gama garin mutumin don hka ba abin mamaki bane ga mutumin daka d'auko shi daga rana kadawo dashi inuwa shi kuma yaturaka ranar,a cikin mutane mutumin dayake salihi ko mai shiru shiru irin fatima mutane ba sa zarginsa da mugun abu sbda yanayinsa amma Allha (SWT)daya halicci zuciya shi yasan abinda ke cikinsa. Ummi tayi shiru na lokaci mai tsawo daga bisani tace "Mama kina nufin kin amince akashe fatima akan kisan likita? " Tace "ummi ba ni da masaniyar abinda shari'ar za tahaifar, sbda ita shari'a macece da ciki ba wanda yasan abinda za tahaifa sai Allah mudai mun mi'ka kukanmu ga Allah yabayyanar da gaskiya. " Tayi gaba tabar ummi tana binta da ido jikinta yayi sanyi 'kalau, da'kyar tad'aga 'kafa tabita cikin gida. . . [5:08PM, 7/13/2017] ‪+234 706 196 7803‬: A DAREN FARKO 4 maganganu sunyi yawa a kan abubuwan dasuke faruwa a kotu, wasu sun fara yarda tunda tace takashe Dr. khalifa yayin dawasu har yanzu suna ganin ba'kin cikine yahanata magana dukda cewa su d'inma suana gnin fati ba ta da hujjar da za tasa taja bakinta tayi shiru ta 'ki cewa komi. Kwana biyu a zauna kotu malam musa da mahaifiyarsu fatima da da ummi da Barrister Abbas suka isketa a inda take tsare abisa alfarmar dom mahaifin marigayi Alhaji muhammad amma fa akwai sa idon 'yan sanda guda biyu. Fatima tarusuna tagaida mahaifinta ciwon rai ya'kara damunta sakamakon ramewar dataga ya dad'a yi ya fita hayyacinsa kaida gani ka san yana cikin matsananciyar damuwa da takaici, sannan tagaisa dasu ummi da barrister. Malam yace "fatima. Ta amsa 'na'am baba. Yace "fatima wannan shi ne zuwa na 'karshe dazanyi gunki akan in ro'ki kiyi bayani a kotu idan kinga dama kiyi magana fati idan baki ga dama ba kicigaba dayin shiru tunda kinfi 'bukatar mucigaba dazama cikin tashin hnkali darashin sanin abin yi. A yau na zo ne ba dan in ro'ke ki kiba lauyoyi da al'kali amsar duk tmbayar dsuka bu'kata agunki ba zuwa nayi in ba ki umurni a matsayina na mahaifinki idan ya cancanta kiyi min biyayya kiyi fatima idan kuma ban isa ba kici gabadayin shiru kamar yadda kika saba. Fatima tace "baba idan nayi bayanin zai sauya 'kaddara ne? ko kuwa bayanin na wa zai dawo da rayuwar Dr. khalifa izuwa gidan duniya, baba idan ni ce nakshe Dr. khalifa idan ma ba ni bace Allah SWT ya san haka tunda shi yake ganinmu a lokacin damuke kulle mu biyu acikin d'aki ni da Dr. khalifa, ni dai abinda nakeso ayi amfani dashi shi ne tunda naji na gani na amince ni ce nakashe shi na yi i'kirari da bakina a yi min hukunci dai dai da laifina shiknan shari'a sai a gaban Allah (SWT) wannan itace rana daza a tsage gskia ranar dakowa zaiyi bayanin abinda ya aikata da ga'bo'binsa bama da bakinsa ba kuma itace dawwamammiyar rayuwa wadda va za ta'kare ba har abada. Don Allah baba kayi ha'kuri kada kayi fushi dani akan hka bbu abinda bakina zai iya furtawa a lamarin kisan nan. Ummi tace "fati mahaifanki sun kasance suna masu alfahari dake a bisa biyayya da kike musu, baki ta'ba yin musu dasu ba, ba'a ta'ba samun wata rana da suka baki umurni kika sa'ba ba, meyasa a wannan karon za kisa'ba musu? Ba ki da hujjar dazakice rayuwarki ta zo 'karshe fati, ko kuma dan kina jiran mutuwa shiyasa kike ganin biyayya ga iyayankinya va ta da amfani? To bari in tunatar dake wani abu guda d'aya ance akwai mutumin dazai ta aikin alheri wanda yake share masa hanyar tafiya aljannan sai 'karshen rayuwarsa tazo sai kawai ya aikata wani abu wanda zai kaishi wuta sai ya shiga wuta. Yayin dawani zaita aikata aikin dazai kai shi wuta gab da mutuwarsa siya aikata abinda zai kaishi aljannan saiya shiga janna. Fatima ina ro'kon ki kiyi abinda iyayanki suka bu'kata ba ki da hujjar dazaki sa'bawa umarninsu, ba ki da tabbacin kwann ki ya 'kare mutuwa zakiyi fatima. Barrister kallon fatima kawai yake yarasa yadda xaiyi da tausainta a zuciyarsa, yamatso daf da ita muryarsa 'kasa 'kasa yace "fatima 'karfe nawa aka kaiki gidan Dr. khalifa? Ta amsa 'karfe biyar da rabi Zuwa shida a wannan d'an tsakanin ba'a wuce haka ba. Gaba d'aya sai da fuskokinsu suka nuna jin dad'in had'in kan data fara badawa, barrister yace a wace rana knan fatima? Ta amsa "A ranar lahadi biyar ga watan uku" Ya gyad'a kai yana murmushi yace "fatima suwa dawaye suke cikin motar da aka kaiki? Tayi d'an jim daga bisani tayi murmushi tana kallonsu tace "ummi za ta fini snin suwaye a motar da ka kaini sbda ni fuskata a rufe take ba wanda zan iya shaidawa a lokacin sai dai tabbas na san ina tare da manyan aminai na guda biyu kamar ita ummin da d'ayar aminiyar ta wa Jiddah. Barrister yace "yawwa ko za ki iya tuna 'karfe nawa kowa yawatse acikin gidan aka barki ke d'aya lkacin dakike jiran ango kamar yadda al'adar amare take a ranar da aka kaisu d'akunan mijinsu,? Tace 'lallai kam ba zan manta ba bayan an yi sallar isha'i wuraren 'karfe takwas nadare su ummi da maijidda dawasu 'kannan mahaifiyata biyu kad'ai suka rage a gidan inda mukai sallar isha tare dasu sannan sukayi shirin tafiya suka tafi gaba d'ayansu. Barristr yace "bayan haka waye yashigo gidan kafin zuwan ango dr. khalifa? " Tajima tsit tana nazari tace "gaskiya ba wanda yashigo kuma banji motsin kowa ba ni kad'ai nazauna. Barrister yace "zaman minti nawa kikayi 'kiyasi kafin dai zuwan ango ? Tace "tace ba'ayi minti sha biyar ba naji tsayuwar motarsu shida manyan abokansa guda biyu wad'anda sukayi masa rakiya. Barrister yace "kafin dai zuwan angon ba wanda yakiraki ko da awaya ne? Tagirgiza kai ba wanda yakirani in barda shi angon Dr. khalifa. Me yace miki? "Cewa yayi inyi ha'kuri suna hanya " Ke kuma me kika ce masa? Cewa nayi to Allah yakawosu lfya. Yace "dukda haka bakiji ko da alamar motsi a gidan ba har lokacin da dr. khalifa da abokanansa suka iso. Tagirgiza kai gaskiya babu wani alamun motsin danaji saifa lokacin dasuka shigo. "Su nawa suka shigo. " Barrister yaci gaba da tambayar har yanzu idanuwansa na kanta. Tace su uku wato shi da abokan na sa guda biyu. Yace "yaya sunayensu.Ta amsa "daya sunansa Dr. Mustapha kura d'aya Kuma Dr. Hafiz. B. Muhammad. " Yace kafin auranku yaya ala'karku dasu abokan na sa? ina nufin sun amshe ki a matsayin matar abokin su ko kuwa ba sa yi dake? Fatima tace "Nikam alhmdlh Dr. khalifa da iyayansa da abokansa da yan uwansa ko sau d'aya babu wanda yata'ba nuna min wata 'kyama ko wani abu wanda zai sa ince lallai wane ba ya 'kaunata, daidai gwargwado ina samun had'in kai daga garesu to sai shi kuma abinda yake na nasani mutum yakeda masaniya akai abinda yazamo na bad'ini Allah kad'ai ke da masaniya akansa sa sai dai mubarwa Allah ikonsa". Barristr yace "to fatima za ki iya gaya mana maganar dasuka yi lokacin da za suyi sallama daku a wannan dare? Tace "eh gaba d'aya tunda sukazo nasihohin zaman lfya suke mana bayan hka sun mana addu'o i na neman zaman lfya bayan haka sukayi mana sallama suna mana barkwanci irin na abokan ango ranar siyan baki irin wannan. To daga nan sai me yafaru? Tace "saiya rakasu" Ke kuma kina ina? Ina zaune akan gado ko motsi banyi ba kamar yadda suka sameni, bayan ya rakasu saiya dawo yazauna kusa dani yana d'an zolayata. Barrister yace "dukda haka a lokacin ba wani motsi a gidan sannan shi d'inma bai nuna miki ya ji motsin wani abu ba ko kuma ke kin fahimci wata razana a fuskarsa? " Tace "gaskiya banga komi ba yana cikin nishad'i sosai yadda yakamata ango yakasance a irin wannan dare. " Daga nan fa? Sai yace dani kinga hayaniya tayi yawa a kaina ko sallar isha'i banyi ba nayi 'ko'karin inyi kafin mutaho su mustapha suka daman akan inyi sauri su garin za subari a daran. "Garin za subari? inji barrister yafad'a yanayinsa yasauya. Tace "haka dai yace daganan kuma bai 'kara fad'ar wata magana wadda tashafi wad'annan abokai na S ba yatashi yafita bansan ina yaje ba saiya dawo. Ya yi kamar minti nawa dafita kan yadawo? Tace zaiyi kamar minti goma saiya dawo yacire babbar rigar jikinsa ya Ajiye kan gado yace ya kamata inyi sallar nan dashi kuma inajin yunwa tun d'azu anti take ce min ga abinci na ka sa zama inci sda jama'a gaba d'aya na ji abincin ya fita daga raina ba na sha'awarsa sai yanzu nakejin yunwa,amman bari inyiwa mama waya tasa akawo mana abincin hatta kazar amarcinki ma tana gun mama ita tace za tagasa dakanta akwai tanadin datayi miki a ciki. Duk yayi wad'annan maganganun ne a tsaye yana murmushi tare da daddana wayarsa tahannu yakira maman bayan sun gama wayar sai ya ajiye wayar akan madubi danufin yashiga toilet sai aka kirashi yayi magana mai tsawo dawanda yakirashi d'in sannan yakashe yadubeni yace "idan mutum yana harka da jama'a sai ha'kuri, tashi kema kiyi alwala idan nayi sallar isha'i sai muyi Nafila ko bari inyi tawa a d'akina sai intaho da littafina daganan saiya fice waje Nikuma nashiga toilet na idar da alwala na fito ne na iske gawarsa akan gado. Barrister yagirgiza kai cike da tausayi yace "fatima. " Yanayin fuskarta ba d'ad'in gani sbda tamkar lamarin datake bayarwa yana fama mata wani gyambo nazuciyarta wanda yake mata tsananin zugi a zuci yake rabata da duk wani zaman lfya da walwala a zuciyarta, hatta kallon datayiwa shi barristan lokacin daya kira sunanta ya firgita shi zuciyarsa tabuga yayi mata tsai da ido don yana son taci gaba da bashi amsar tambayoyin dayake mata. Yace "fatima kin kai minti nawa a toilet d'in lokacin da kika shiga danufin yin alwala. Tace "minti kamar goma don na d'anyi wasu abubuwan kafin in gabatar da alwala. To sai kika fito inda kika ga gawar mijinki Dr. khalifa shimfid'e akan gado, haka ne? Tace "eh ina daga band'aki naji motsin bud'e 'kofa sau biyu dakuma motsin bud'e kwaba ko me zan kawo a rainadon na ji wannan motsin, d'auka zanyi shi ne tunda ba kowa a gdan a iya sanina dagani sai shi. Yace "kuma ba motsin gudu? Tace "Gaskiya banji wani motsi wanda yake tabbatar da rashin gaskiya ba ko kusa. Yace "to bakiji 'karar mijin na ki ba ko wani abu da yayi kama da haka a lokacin da za a kashe shi? Tace "nidai banji komi ba yadda nagaya maka naga gawarsa haka nagan shi ba wani abu da na sani bayan wannan. Yace "dame aka kashe shi? Ta amsa "wu'ka ce 'karama. kin ta'ba wu'kar? Tace "eh lokacin danafito daga band'akin hankalina yayi mugun tashi natafi dagudu nad'aga wu'kar daga cikinsa domin wu'kar tana kan cikinsa ne bayan an luma masa sai aka zareta aka d'orata akan cikin na sa nikuma danazo saina d'aga wu'kar shi ne dai dai lokacin da 'kaninsa isma'il ya 'kwan'kwasa 'kofa jin ina ihu innalillahi wa inna ilaihir raji'un saiya danno 'kofar yashigo da food flask d'in abinci a hannunsa wanda mama tabashi yakawo mana. Barristr Abbas yace "fatima lokacin dakika iso kan mijinki dr. khalifa yanada sauran rai ko ya mutu? Tace "dasauran ransa don kuwa har yana d'an juya kansa yana cewa ta kasheni ta kashe ni har lokacin dashima isma'il yashigo d'akin yana magana ganin yanayin da ya iskemu aciki yasa isma'il d'in yawatsar da abincin hannunsa ya isa kan d'an uwansa a gefe ana fad'in, ya ya wa yakashe ka, yakasa hannuwansa daidai bakin dr. khalifan yana cewa don Allag gaya min wadda takashe ka nima yanzu inkasheta. Ban san yaya akayi ba ko shi Dr. khalifan a lkcn bansan waye a kansa yake masa magana ba ne ban sani ba naji Da kunnena dai lokacin Da dr. khalifa ke cewa Fatima ta kasheni, fatima ta kasheni. Fatima tayi shiru zuciyarta na bugawa kamar lokacin abin yafaru, daga barrister har malam da ummi dashi kansa d'an sandan dake tsaye a kansu sun ji'ke sharkab da gumi sbda tsananin tausayi da tashin hnkali. Idanuwan fatima sun 'kafe ba zancan hawaye sai tsananin zugi da rad'ad'i dasuke mata 'kirjinta kuwa kamar zai 'balle dan azabar zafin da yake mata numfashi na fita da'kyar. Tunda al'amarin yafaru yau ne ta iya bud'e baki tabada labarin yadda abubuwan suka wakana. Sun jima zaune shiru tuni lokacin daya dace sufita yawuce shi kansa d'an sandan ya kasa cewa sufita hnkalinsa shima a tashe yake.. Barrister abbas tagumi kawai yayi da tambayoyi a bakinsa, bakin ya yi masa nauyi la'b'bansa sun bushe da'kyar yake iya numfashi tare dacewa, shi cikakken lauya ne Kum 'kwararre mai cin gashin kansa don tuni ya jima da 'kasaita akan aikinsa sbda matakin daya ta ka nakaratu, irin wadannan abubuwan ba bakin al'amura bane gareshi, aikinsu nako yaushe jin abubuwan tashin hnkali amma bai ta'ba fuskantar alamarin dayake tsananin d'aga hankalinsa da ba shi tausayi irin wannan ba, ya damu da mGanar 'kwarai dagaske. Kafin ma yayi mata tmbaya taci gaba da fad'in "Abinda bakinsa ke furtawa knan har yabar duniya, wato ta kasheni fatima, takasheni Fatima. Isma'il yana ihu akansa yana cewa "yaya fatima ce takashe ka? fatima ce takashe ka? bai 'kara motsi ba yaci gaba da jijjigashi ko shurawa baiyi ba, tuni jini yayi faca faca akan gadon. Wu'kar tana hannuna ina tsaye har izuwa lokacin da isma'il yasake shi yafita baice min komi ba, ban ajiye wukar ba sai lkcin da yan sanda suka shigo d'akin wani acikinsu yalulku'be hannunsa da safa yakar'bu wu'kar daga hannuna. Tayi ajiyar zuciya tace "ba wani abu dana sani bayan wannan ,bbu kowa a gidanmu lokacin da aka kashe Dr. khalifa sai mu biyu a gidan ni da shi ni kaina na shaida banji motsin kowa ba, idan ba ni nakashe shi ba wa zance ykashe shi? Idan nace ba ni nakashe shi ba dole inyi bayanin wanda yakashe shi to waye? sannan ni akazo aka iske da wuka a hannu haka nan bakinsa gana furta takasheni ,idan akace wa sai yace fatima.. Fati tarushe dakuka mai tayar da hankalin mai imani tace "kaicon rayuwata na yi nadamar zuwa wannan duniya ace an wayi gari a rasa wanda zai kashe Dr. khalifa sai ni ni fatima me xanyi da rayuwa.. me zan tsinta a cikinta, wane farin ciki zanyi a gaba? Don Allah kudaina yun'urin kareni kuyarda ni nakashe Dr. khalifa a kashe ni in huta da wannan ba'kin cikin rayuwata ba ta da amfani. Wannan bayanin da nayi iyakarsa zan iya fd'a ba zan ta'ba bud'ar bakina a kotu ince wani abu ba game da ranar da dr. khalifa ya bar duniya, hukunci kawai nake jira kuyi ha'kuri kuyafe min. Barristr Abbas yace "to shikenan munji ke kika kashe Dr. khalifa gaya mana meyasa kika kashe shi? Ta amsa "ni ma bansan dalilin dayasa na kashe shi ba. Ba wani laifi dayayi miki? Bai min komi ba sai alheri, ba komi tsakanina dashi sai alheri, ban sani ba ko alkairin ne yasa nayi masa sakayya da kisan kai. [5:08PM, 7/13/2017] ‪+234 706 196 7803‬: DAREN FARKO 5 TSAKIYAR dare ne za mu iya kiran lokacin 'karfe biyu da rabi nadare, fatima na zaune kan dandayyar siminti ana muku mukun sanyi ne a lokacin amma ita ta ji'ke sharkab da gumi sakamakon matsanancin halin tashin hnkalin da gararin darayuwarta ke fuskanta. Ita kanta yadda alamuran suka faru suna matu'kar ba ta mamaki, koyause tambayar datake wa kanta itace waye yakashe Dr. khalifa? Me yayiwa wanda yakashe shi? Meyasa ba'a kashe shi ba sai a daren su nfarko A DARAN FARKO na amarcinsu aka biyo shi har cikin gida akan gadonsu aka kashe shi, tabbas duk wanda yakashe Dr. khalifa ya isa azzalumi, ita da Dr.khalifan ne baya so shi yasa aka kashe shi a sigar da duk wanda yagani zaice itace takashe shi. Ita da Dr. khalifa mesuka yiwa wani daya daidaici irin wannan dare a gunsu yakashe mata miji? Wannan itace tambayar datake wa kanta tun lokacin da aka kulleta a wannan guri, itace tmbayar da ciwon dayake mata a zuci ke barazanar sa zuciyarta tabuga ta tadda mata ajalin sbda tsananin damuwa, Allahu akbar ashe ko kwana d'aya ba za tayi a gidan miji ba, bala'i zai fad'a musu A DARANSU NA FARKO. Sai kace ana tariyo mata rayuwarta da abinda yagudana a tarihin rayuwarta gaba d'aya haka yarin'ka wanzuwa a zuciyarta da 'kwa'kwalwarta kamar shirin fim. *******************************,****** Malam haruna shi ne mahaifin malam musa wanda yakasance shi ne mahaifi ga su fatima. Asali malam Haruna bafullatanin gombe ne yawon neman karatu yakawo shi kano kasancewarsu fulani ne na jame inda yazauna a hannun wani shahararran malami mai babbar tsangaya anan kano, Allah ya yi malam haruna mutum ne mai tsananin ha'kuri da biyayya malamin nan da iyalinsa suna matu'kar jin dad'in zama dashi inda a sanadin haka ne suka d'au d'iyarsu Maryama suka ba shi auranta ita kuma tahaifa masa 'ya'ya maza har bakwai, malam musa ne autansu. Bayan rasuwan malamin, malam haruna shi yazamo magajinsa don duk acikin almajiransa na wannan lkcin ba wanda yakaishi sha'kuwa dashi, ga kaifin basira yaci gaba da jagorantar tsangayar kuma shi yari'ke iyalan malam har zuwa shima lokacin da Allah (SWT) ya kar'bi ransa sai d'ansa malam musa yagajeshi a lokacin ma bai dade da auran fari ba inda matarsa zainab tafito itama daga zuri'ar tsohon malamin marigYi malam Yakubu, an ce na ji dad'i shi ne gari ba na saba ba. Malam musa yayi kyakyawan gadon hali na hakuri datsananin juriya irin na mahaifinsa, mutum ne mai matukar saukin kaida sanin yakamata, hka itama matarsa zainabu bbu abinda yadameta da zafafawa kanta game da rayuwar duniya. Suna zaman su lfya a dan karamin gidan da yake haya kusa da makarantarsu basu dogara da kowa ba sai Allah mutane ne dako kadan va su da kwadayi, mutanan unguwar sunajin dadin zama dasu sosai ana zaune lfya. Aliyu shi ne d'a na farko da goggo Abu tafara haifawa malam sai mai sunan malam Yakub suna cewa dashi malam, sai rukayya sai fati sai mai sunan malam Haruna suna cemasa baban gida sai muhammadu nazifi sai nuraddeen ba su da wadata da dukiya rayuwa ce tarufin asiri amma akwai wadatar zuci da son juna, rayuwarsu tana yawan ba wa mutane sha'awa yadda suke kamun kak da tarbiyya da girmama jama'a da 'ya'yan gidan masha Allahu hka suke amma ba kamar fatima, itace tafi fad'a kowa d'auko halayyar mahaifinsu kamar yadda tafi kowa kama sak da mahaifinsu don hkane tafi kowa kyau a gidan. kaf zuri'ar marigayi malam haruna kyawawan gaske ne har kwatance ake dashi a garin sbda kyaunsu ga uwa uba farin jini dukda cewa ba masu kud'i bane ba su da komi sai rufin asirin Allah. Tun fati tana 'yar mitsitsiyarta ake mata shaidar hkuri dasau'kin kai duk inda fatima tashiga sai an yaba halayyarta, balletana biyayya ga iyaye wad'anda takeji kamar tayi musu numfashi don tsananin so da 'kauna ko kuma takwanta sudinga bi ta kan ruwan cikinta don biyayya. Hka a makaranta malamanta ke ji da ita bayan maida hankali akan karatu da gudun fitina ga biyayya da tsafta. Fatima kyakyawar gaske ce daga ganinta ka ga bafulatana sak zai wahala mutum yagaji da kallonta sbda Allah ya yi mata baiwar kyau mai tsayawa a zuci. Bayan auran yayarta rukayya da shekara biyu wata rana da daddare malam musa yana zaune kan tabarmarsa goggo Abu tana gefe itama kan tata tabarmar yayin da fatima ke zaune kusa da su tana yi masa firfita. Yace "zainabu yaya batun d'an gidan rukayya ya warware ko? Ta ce "Alhamdulillah jiki kam dasau'ki yau danaje na iske shi yanata wasa da yara. Yace "Masha Allah, sannan yagyara zama yadubi fatima yace "fati yaya batun haddarki ta jiya kin haddace" Tace "na haddace har d'azun na ba da a gaban malam musbahu ya dad'a min wani. Yayi murmushi yace "Alhamdulillah yana daga cikin ni'imar da Allah yake yiwa mutane shi ne yabasu 'ya'ya na gari salihai wad'anda zasu zamo farin ciki a gareka, fatima ina matu'kar alfahari dake sbda kinada hankali da biyayya ban ta'ba shakku akan biyayyar da kike mana ba wannan shi ne dalilin dayasa kai tsaye ko shawara banyi dake ba na daukeki nabawa malam musbahu auranki sbda na fahimci halayyarku ta zo d'aya. Shi ma mutum ne da Allah yahore masa ha'kuri dasanin yakamata tunda nake dashi bai taba aikata min wani abu na assha ba, sai dai ajizanci irin na d'an adam wanda yake kai mutum ga kuskure. Amma dukda hka ina neman yardarki, idan kin yarda ba wani abune mai girma agareni ba don ina da ya'kini da kwanciyar hnkali akan hakan, idan kuma kin ce baki yarda ba ma'ana ba kya son shi ina mai yimiki rantsuwa da girman Allah ba zan damu ba na san Allah ne bai 'kaddara musbahu mijinki bane shi yasa kika'ki amincewa dashi. Fatima kanta na 'kasa ta shiga shararar 'kwalla batace komi ba, malam yace "fatima kada wannan magana tad'aga miki hnkali balletana tajefa zuciyarki cikin damuwa. Cikin shashe'kar kuka fati tace "dole indamu baba ban ta'ba tunanin akwai watarana dazakayi tunanin zan bijirewa umarninka ba, har inada abinda zanyi wanda zaisa inyi gaban kaina ba tare da umarninka ba. Wlh idan har akwai watarana wadda za tazo in bijirewa umarninku ba na fata tarismeni ina numfashi a duniyar nan gara in mutu da in ganta sbda haka baba ba na bukatar ka kara neman yardata a bisa wani bu wanda kake nufin zartarwa a kaina. Na amsa malam musbahu hannu biyu biyu kuma zan yi masa biyayya bakin iyawa ta. Malam musa yagirgiza kai yace "Allah yayi miki albarka fatima, Ubangiji Allah yasa kigama da duniya lfya, biyayyar dakikayi mana Allah yasa 'ya'yan dazaki haifa suyi miki wadda tafita, dukda haka ina mai tabbatar miki dacewa hakkinki ne in nemi amincewarki akan auranki da malam musbahu kamar yadda nayi miki bayani a baya ba wai dan ina shakkun amincewarki a gareni ba sai dan in ba ki hakknki a matsayina na mahaifinki. Yadda nake miki wannan magana haka na zaunar da musbahu nace dashi musbahu yau fiye da shekarar ka goma a hannuna tun lkcin dakazo da sassafe kana kuka kana ce min in taimakeka inje in ba wa kawunka hakuri matarsa ta yi maka sharri zai dake ka natambayeka abinda kayi mata kace min cewa tyi dashi na yi mata sata, malam musa yace "fatima a lokacin ne nasa musbahu a gaba har gidan kawunsa wanda yake bayan wannan layin na mu, kasancewarsa maraya, mahaifiyarsa ta rasu tun yana yayayye, yayin da mahaifinsa yarasu bayan shekara d'aya tsakani wannan shi ne dalilin dayasa kanin mahaifinsa yadaukeshi yabawa matarsa wadda ita kuma tadauki tsanar duniya ta dora masa, take wahalar da rayuwarsa. Abunda yasa musbahu yazo guna shi ne "lokaci lokaci kawun na sa yana zuwa dashi nan don daukar karatu da magriba kuma ya san akwai fahimtar juna tsakani na da kawunsa. Lokacin damukaje gdan nayi sallama da kawun yafito yana ganina tare da musbahu ya hau fada ko gaisawa bai bari munyi ba inda yake shiga ba nan yake fita ba, dakyar nasa yayi shiru nace "Alhaji Habibu ba haka ake lamarin duniya ba, idan mace tagaya maka magana saika bincika kafin ka dauki mataki, sha'anin mata idan akace ba su suka haifi d'a ba sai a hnkali ballantana d'an dayake maraya. Albaji habibu yace "duk abinda yagaya maka karya ne don ya ji Kawai ana cewa maraya ne duk abinda aka ajiye a gidan nan saiya sace yasiyar sannan idan nayi masa magana sai ytafi yana hadani da muatane ana cewa muna cutar dashi alhali shi maraya ne don ba mu muka haife shi ba. Ina dalilin wannan, haka kawai an ba ni ajiyar kudade masu yawa yabi dare ya bi rana har dakina ya sace, to ba zan iya ba yan sanda zansa sukama shi su kulle in huta ko kuma in kai shi gidan kangararrun yara ka ga na huta. Na dubeshi tsam sai da yagama fadace fadacensa nace"to ni kam ba zan bari kakai musbahu gidan kangararrun yara ba tunda shi ba kangararre bane, idan kai ba za ka iya rikon shi ba dan kawai ba kai kahaife shi ba ni zan iya, sai dai ina son kadinga Tunawa wannan yaron maraya ne kuma maraya ne a gareka, idan kaci amanarshi Allah ya tambayeka kamar yadda yazo acikin hadisin ma'aiki(SAW) ,sai ya tambayi kowa akan abinda yaba shi kiwo, maigida mai kiwo ne Allah sai ya tambaye shi akan iyalansa ya yatafiyar dasu.......... Ya katseni cikin hushi yace "Ni bance kayi min wa'azi ba tunda nan ba makaranta bace, ka ce za ka iya rike musbahu, ka ga gashinan kuje kukarata idan yagwada maka mugun halin sa za ka koreshi ne, da kai ka kama da sannu zan ganku a rana. " Nace "Insha Allahu ba za kaganmu a rana ba, kai ne dai za kayi nadamar abinda kayi masa, da sannu za kaga sakayyar da Allah zaiyi masa kuma da sannu za kagani watarana zai zama abin taimako gareka da iyalin na ka ma wadanda kuka hada kai dasu kuka walakantashi. A lokacin kawun musbahu yashiga dakin da musbahu yake kwana a zaure yadinga watso masa kayansa yana masifa a haka nataya shi mu*a kwaso kayan, wannan shi ne dalilin zaman muśbahu a gidan nan lokaci lokaci dangin iyayansa na uwa dana uba sukanzo guna suna yi mini godiya shi ma yana ziyartarsu. malam musa yaci gaba dacewa fatima lkcn dana gama tunasar da musbahu wannan lbri kansa na kasa nakara da fadin "musbahu lkci ya yi dazakayi aure shekararka ashirin da bakwai a duniya, kana bukatar ajiye iyali tunda kke baka taba cemin ga wata mace dakakeso ba sbda kunya dakake da ita da kawaici. Musbahu ka rayu kana hidima gareni vakin iyawarka, allah kadai yasan kaunar danake maka, wannan shiyasa nadauki diyata mafi soyuwa a zuciyata nabaka ita dan tazamo matarka uwar yayanka. Yayi saurin fadin fTima yana me dafe kirji da fiddo idb stories A DAREN FARKO 7 A babban falon alhaji aka sauki iyalan malam, falon da ba kamarsa a gdan duk wani kasaitaccan bakon da zai gana dashi a gidan nan yake sauke shi, aka kawo musu abubuwan ci dana sha na alfarma. Alhaji da hajiya maijidda suka fito aka gaisa, malam yagabatar dasu ga iyalansa aka shiga yi musu godiya mai yawa, alhaji hace "malam kwarai dagaske na ji dadi matuka da zuwanku gidan nan, sbda dama wannan gda ne na mutane ba mu da 'ya'ya in banda d'a guda d'aya da Allah yabamu amma idan kashigo koyaushe za ka iske mutane da yawa a gdan ko da yaushe muna godewa Allah kalar jama'a kam ba wadda ba ma gani a wannan gida sai dai a gefe guda banji dadin wannan zuwa na ku ba da sunan godiya don banga abinda nayi ba, wlh da ace malam za ka baiwa 'dana khalifa auran 'yarka da na yi murna duk dan kusan d'aya muke da kuwannan dukiyar da Allah yabani ba ta gabana ballantana har in ga wai na fi wani. Malam yayi shiru yana tunanin maganganun Alhaji muhammadu, shi kam vai taba burin kai diyarsa irin gida na aljahi muhammadu ba hakan yasa hnkalinsa yatashi sosai jikinsa yayi sanyi. Bayan sun dawo gida suna zaune a tsakar gida da da daddare zainabu tace "malam ai kuwa a dazu rukayya take ce min tunda alhaji yanemi aure a gdan nan mai zai hana abashi fatima. Sai ya bata rai yace "shi yasa hnkali na yatashi lokacin da alhaji yafurta wannan magana a gabanku, sbda ku mata ne karamin tunani gareku, tunanin ku ba ya wuce karan hancinku, ko da yaushe kyale kyale na duniya kan dauki hankalinku ku aikata abinda zuciyoyin ku suka raya muku sai daga baya azo ana nadama sbda haka ba na son wannan magana daga yau, shi yasa ko amsa ban ba wa alhaji ba lokacin da ya fada, ba na ra'ayin diyata tayi auran dukiya, idan alhaji ya kasance mutumin kirki mai taimakon talakawa sai akace muku shi dan na sa da sauran danginsu haka suke? da zaran mun dauki fatima mun ba su shikenan kowa ma cewa zaiyi kwadayi yakaimu ba za ace su suka nemi auran ba cewa za ayi ni ne nanemi khalifa ya auri fatima duk gorin da akanmu da duk walakancin da akayi mata mu muka jawo. Goggo Abu tace "kuma hakane fa malam bbu wanda yayi wannan tunanin acikinmu kowa kirkin Alhajin yake kallo. ************ Tun daga wannan lokacin aminci mai karfi da zumunci yashiga tsakanin mutanan da iyalansa da alhaji da hajiya maijidda a lokacin nan shi khalifa yana kasar germany inda yake karatunsa na likita. Alhaji bai da abokin shawara sai malam haka hajiya maijidda ta dauki goggo Abu kamar yar uwarta tajini, dukda cewa alhaji muhammadu bai ka ra nuna wa malam yana son yabawa dansa khalifa auran 'yarsa fatima ba tun daga wannan lomacin hankalin malam bai kwanta ba ba wai don yana kin alhajin ba, malam yana matukar kaunar alhaji har cikin zuciyarsa kamar yadda shi ma alhajin yake nuna masa kauna ta tsakani da Allah, auran fati ne kawai ba ya son yabawa khalifa sbda abinda zai je yazo. Bayan shi kansa alhajin akwai mutane wadanda suke da kima a idon malam suna nuna sha'awarsu akan malam yaba 'ya'yansu auran fatima sbda kamun kai na yarinyar da uwa uba kyawun halittarta bai taba furtawa wani ya ba shi ba, sai dai yayi dariya kawai yace aure nufi ne na Ubangiji. A ranar da alhaji yazo wurin malam da daddare bayan sun gama karatu da addu"o i yace dashi "malam idan Allah ya nuna mana rana itayau khalifa zai dawo daga kasar germany. Gaban malam yafadi amma bai bari alhaji ya fahimci fargabar da zuciyarsa ke ciki ba, ya fadada fara'arsa yace "masha Allah ya kammala karatun knan. Alhaji yace "kwarai kuwa karatu ya kammala lfya don ya samu cikakkiyar takardarsa ta shaida ya kammala karatun sa a matsayin cikakken likitan mata. Malam yace "mun godewa Allah, Allah yasa anyi a sa'a kuma Allah yadawo dashi lfya. " ***************** Shi kansa malam baisan dalilin dayasa hankalinsa yatashi sosai da maganar dawowar Dr. khalifa ba, tun da alhaji yashaida masa zancen dawowar yashiga damuwa sosai ko goggo Abu bai gayawa ba, shi kadai yake tunani a ransa karshen tunaninsa shi ne ba abinda yadace yayi wanda yawuce yaba auran fatima kafin dawowar Dr. khalifa ko da alhaji ya tada maganar idan yagaya mai ya bada ita shikenan an huta. Wannan ahi ne dalilin dayasa yadauki fati yaba amintaccan almajirinsa kuma d'ansa wanda yayarda dashi fiye dakowa,a 'ko'karinsa na ganin iyalansa sun zauna lfya a gidajan mazajansu, tun ranar daya shiga gdan alhaji yatabbatar wannan rayuwar ta fi 'karfin fatima ba za ta iya ba me zaisa yada'u d'iyarsa yakaita inda za tashiga wani hali rayuwar da mutum ya sabayi ita yake iyawa,idan yaje inda aka fi 'karfinsa wahala zai sha. ***************'Karfe bakwai daidai na yammacin litinin jirgin IRS yasauka dasu Dr. Abubakar Assadiq wanda aka fi sani da Dr. khalifa a filin jirgin saman Malam Aminu kano dake nan kano wanda yad'aukesu daga filin jirgin saman murtala muhammadu dake birnin ikko jihar lagos, bayan da jirgin da jirgin daya d'akkosu daga jamus ya ajiye su da asubahin wannan rana. Dr. khalifa dogon matashi ne kyakyawan gaske irin mazan nan da ko wace mace ke burin mallaka ba wai don shi da mahaifan sa sun mallaki abun duniya ba sai dan haduwarsa na gwarzon namiji wanda ya isa a kalleshi a san cewa shi d'a namiji ne abin kwatance acikin mazaje. Yana da madaidaiciyar 'kiba wacce tadace da tsawonsa ma'ana 'kibar da tsawon basuyi masa yawan dazasu sa shi muni ba. Babu inda yabar mahaifinsa alhaji muhammadu a kyau kamanninsu d'aya har tafiyarshi dai bambamcin halayyar abbansa mutum ne mai matukar kirki da sau'ki kai da son mutane yayin da Dr. khalifa yakasance miskili tun yana yaro bai da son magana sai dai 'kar'karfar mutum ne kuma gwarzo wanda ba shi da tsoro ko kad'an. Dr. khalifa ya taso cikin gata da kulawar iyaye bai san wani abu wai shi babu ba duk abinda yakeso shi akeyi masa, hakan ne yasa yagirma cikin izza da isa da raina mutane, sai dai yana raina wanda yashiga harkarsa ne, idan baka kalli inda yake ba ba ruwansa dakai, kuma bai ta'ba damuwa da yawan alherin dayake yi wa mutane ba idan ma Allah yayi mutum yana da rabo idan kazo neman abu gun abbansa sai yabaka abinda yafi wanda abban zai ba ka ma'ana dai shi kyautar sa taganin dama ce kuma sa'a ce. Bayan ya kammala karatun sa na secondary yafara karatu anan jami'ar bayero dake kano. Inda Allah yataimake shi shine dukda gatan da yakeda shi na iyayansa bai wasa da karatu kamar yadda sauran 'ya'yan gatan ke shagwaba suyin karatu sbda iyayansu suna da dukiya. Dr. khalifa tun yana nursery yake da kaifin basira wannan yasa yake da farin jini a gun malamansa har izuwa jami'a inda anan ne yazamo kamar jinjiri wata sha kallo sbda farin jinin dayake dashi, bayan dai tsabar kyau da iya dressing da Allah yahore masa. Kaifin basirarsa yana burge kowa sannan ga 'barnar dukiya dayake wa abokai maza da mata,shi yasa duk inda Dr. khalifa yake sai ka ga mutane ana wata irin shafta mai dad'i. A cikin Bayero 'yan matan dasuka shiga mawuyacin hali akan son Dr. khalifa Allah kadai yasan yawansu yayin dashi bai san suna yi ba, wasu suna ganin sbda dukiyar ubansa ne suke sinsa, kasancewarsa dan gata ahi kad'ai suka mallaka duk wannan tarin dukiyar da Allah yaba mahaifinsa shi ne mai mallakarta to kuma shi akwai 'ya'yan manyan masu kudi suna matkar sonsa, su ba abinda suke nema dashi sai shi kansa, shi mutum ne mai saurin d'aukar hankalin d'iya mace sbda Allah ya ba shi surar da mata keso wadda take burge su. Sai dai kash babu soyayya acikin ra'ayin Dr. khalifa, babi wata d'iya mace daya taba kallo yace yana ao da bakinsa wadanda suke nuna masa soyayyarsu ma share su yake kamar bai gane ba, a lokuta da dama har tambayar kansa yakanyi wai meye so? Ta yaya kake ganewa ka kamu da son wance? Shekarar sa hudu da kammala digiri dinsa nafarko a Bayero mahaifinsa alhaji muhammadu yace "yayi shirin tafiya germany inda yakeson yayi karatun zama cikakken likitan mata. Lokacin dayake gaya masa wannan magana suna zaune ne a falon abban na cikin gida dasafe suna breakfast tare da mamansu hajiya Maijidda. Dr. khalifa ya ajiye cup din shayi yana kallon abbansa yace "abba na ji koda yaushe fa kana gaya min bbu abinda kafi bukata wanda yawuce inzauna kusa dakai in kula maka da harkokin kasuwancinka. Abba yayi murmushi yace "ina sane da wannan khalifa sai dai hakan ba zai hana in yi abinda ydace ba, ina burin kazamo likita don in gina maka babban asibiti anan kano wanda zan sadaukar dashi sbda Allah a dinga taimakawa bayin Allah wadanda ba su dashi. Yace "abba toh kasuwancin na ka fa? ba ka son in taimaka maka akansa? Yace "kada kadamu da wannan saddik ina bukatarka a kusa dani a ko da yaushe sbda abubuwa suna mini yawa sannan yaran danake dasu ba kowane yakeda amana ba, sannan ina samun matsalar rashin masu sa ido a kan abubuwa dukda kokarin danake da ganin na basu hakkokinsu gudun samun matsala irin wannan toh amma matsalata ba za tasa in ki taimakon al'umar musulmi ba, na hakura da amfanuwar da kasuwancina zaiyi dakai kaje kayi wannan karatu don ka taimakawa al'ummar musulmi 'yan 'uwanmu. Mama tace "to amma abba kafin yatafi yanada kyau yayi aure yatafi da matar ko? Dr. khalifa tadafe 'kirji tare da fiddo ido yace "aure mama? sghekaruna duka duka ashirin da biyu ina ni ina maganar aure? don Allah karki 'kara wannan maganar mama ni tun da nake ma ban ta'ba ganin wata mace da zuciyata ta ta'ba so ba, wadda har nakejin zan iya aure. Mama ta ta'be baki tana harararsa tace "kai da Allah rufe mana baki ni za kacewa ba wata mace daka taba so, duk 'yammatan dake biyoka har gidan nan ba 'yan matanka bane? kokuwa kana zaton ba ni da masaniya kan abinda kake? Yalangabar dakai yace 'Alah mama ba budurwata ko daya aciki? su duk wacce kikaga ta zo gdan nan nemana kawata ce ina nufin abokan karatu. Abba yayi murmushi yace "to ko ma dai meye za katafi germany a haka ba tare da aure ba amma idan Allah ya dawo dakai lafiya za ka yi aure insha Allahu ka fahimta ko? Kansa na kasa bai ce komi ba shi kan baya so ko zancan aure a yi masa don ba batun soyayya a gabansa ama batun kawaye wadanda ake debe kewar rayuwa dasu ai babu wadda babu. Bayan fitar khalifa abba yabata rai yana kallon mama yace "ba na son kina matsawa yaron nan kan batun aure tunda ba shi da ra'ayi har 'kwara nawa khalifan yake da za ace dole sai ya yi aure. Mama tace "Alhaji ai kaine dai bakasan abinda ke faruwa ba, dukiyar daka sakarwa yaron nan tasa yanayin abinda duk yaga damar yi masa auren shi ne abinda yafi dacewa. Ya kara tsuke fuska yace "ni fa ba na son zargi irin wannan muci gaba da dagewa da addu'ar damuke masa insha Allahu Allah zai tsare mana shi. Tace "shikenan alhaji kuma bayan haka kana sane da maganar yarinyar nan zainab tana matukar son khalifa amma 'ki'ri'kiri yake nunawa ba ya son ta ka ki yin wani abu a kan wannan maganar dakayi inason kabani goyon baya ne don ayi auransu da zainab har kunyar mahaifiyarta nakeji yadda fa yake d'angata itama 'yar gata ce mahaifiyarta na sonta kaga...... Abban yace "Don Allah kihutar da bakinki da fad'in abinda ke kanki kinsan ba zai yiwu ba. Daman na ce miki mahaifiyar zainab ba ta son ta ne, kokuwa kin ta'ba ganin wanda yahaifi d'ansa yace ba ya so? kawai dai kud'i ake nunawa da so? kinfi kowa sanin cewa ba zan ta'ba tursasawa d'ana auran matar da ba ya ra'ayi ba don muna da dangantaka da iyayanta, kamar yadda nima ba zanso a tursasawa wata d'iya ta auri khalifa ba alhali ita ba ta so. Inaso idan khalifa yatashi aure ya auri matar dayake matukar so itama tana matukar sonsa, insha Allahu zanyiwa khalifa bikinda za a jima a garin nan ba a ga biki na d'an gata irin sa ba. Farin cikina da kwanciyar hnkalina bai wuce auran soyayya bane don hka idan khalifa yanason zainab zai aureta a lokacin daya nuna yana son aure, idan kuma ba ya sonta zai auri wadda yake so ne bbu dlilin dazaisa don tana son shi ace dole sai ya aureta, hkan na nufin ita an mata adalci shi kuma an tauye masa hakki nsa knan? Tace "shknan ya wuce. A DAREN FARKO 8 Ummi d'iya ce ga Hajiya Hauwa yayar Abba wadda take bin babbar yayarsu Hajiya jummai duk da cewa kafin tasowar ummi hajiya Hauwa ba sa shiri da mama don tana cikin masu zakewa 'yan gaba gaba a kan sai abba ya yi aure tunda ita maman ba haihuwa take ba, in banda hajiya jummai datafi karfinsu ita kuma tana matukar son mama sbda kirkinta yayin dasu hajiya hauwa gani suke duk kirkin dasu jummai ke cewa tana dashi na kissa ne da munafunci don ta mallakesu su da d'an uwan tare dacewa babu abinda alhaji muhammadu ba ya musu hatta saudiya shi yakai hauwan ita da mijinta kasancewar duk cikin 'yan uwan nata ma itace ta auri mai karamin 'karfi sai dai tsananin soyayya, kayan abinci da kudi akai akai yake musu aike dukda haka hajiya hauwa ba ta gani kawai sbda ba ta son matarsa hajiya maijidda, yan biyu hajiya hauwa tafara haifa sannan tahaifi wani namijin mai suna Abdulrasheed tahaifi wasu 'yan biyun su kuma mata ummi ce d'iyarta ta biyun 'karshe inda taci sunan mahaifiyar abbansu ake cemata ummi daga ita sai dan autansu umar. Hajiya hauwa na matukar son ummi kasancewarta mai halayya irin ta ta, tun tana yar karama take abokiyar shawara gareta ,ba laifi itama tanada kyau da d'an gwargwadon abinda yasa ake dad'a ganin kyaun ummi bai wuce yanayinta ba da kuma bkin tsiwarta tsiwar kanta tan yi mata kyau, tana burge mutane da dama. Bata fiye zuwa gdan abba ba sai ana wani sha'anin sbda ba shiri take da mama ba, tanada d'abi'ar duk wanda hajiyarsu bata shiri dashi itama baza tayi shiri dashi ba, tana biyewa ra'ayi da son zuciyar hajiyarta shi yasa ra'ayinsu ya zo d'aya. Ummi na aji hud'u na secondary Allah yayiwa mahaifinsu rasuwa kuma a gun zaman makokin ne wata irin soyayya tashiga zuciyar ummi da Dr. khalifa farat d'aya a lokacin ummin shekarunta goma sha shida kacal a cikin 'yan maan ma bata ri'ka ba shi ne lokacin dasuke tasawa. Ranar da aka kwana bakwai da rasuwar suna zaune a d'akin hajiya hauwa ita da babbar aminiyarta kuma makotansu wato jidda khalifa yashigo tare da sallama fuskarsa a tsuke yake amsa musu gaisuwa yace "ina hajiya? " Jiddah tace "tana gaisawa da ba'ki a sit room d‹in baba. Yace "to idan ta fito kice mama ta ce maganar sa'kon nan zatayi mata waya yanzu dai bai samu ba ni sauri nake ba zan iya jira tafito ba. Bai saurari abinda za suce ba ya fice su ma basuyimagana ba ya ga toh dasuka hada baki suka fada lokaci guda. Bayan Fitarsa jiddah tadubi umi tana murmushi tace "Oh ni tunda nake ban taba ganin mutum mai jin kai da isa irin yaya khalifa ba ko dan yana ganin ya had'u ne. Ummi tayi ajiyar zuciya tace "lallai kam ba abinda yake sashi ta'kama wanda yawuce haduwarsa sai kuma dukiyar mahaifinsa wadda yake takama da ita kina ganin duk tsadar mota khalifa zai hauta da zarar an shigo da mota sabuwar yayi 'kasar nan komi tsadarta abbabnsa zai siya masa ya hau, kuma dan wani karin jin kai da alfahari ma ba zai yawo a mota d'aya ba sai ya jera motoci goma yana tsakiya tare da abokansa yana homa daga bisani ne surutu yayi yawa a dangi da abokan abbansa ya tsawatar masa a kan yadaina fita da motoci da yawa haka shi ne yanzu yake fita da motoci biyu ko uku. Jiddah tace "duk abinda yayi ya yi daidai don ya isa yayin, ni kam yaya khalifa yana matukar burgeni ina mai ba ki shawara ummi in har za ki iya shiga zuciyarsa kada kibari ya subuce miki. Ummi tayi ajiyar zuciya tace "jiddah kin san dai yaya khalifa kuma kinsan yadda rayuwarsa take, nima kinsan gwargwadon wayewata da fahimtarki da rayuwa kina ganin zan iya shiga xuciyarsa ina nufin kina ganin ina da nagartr da zai so ni? Jiddah tace ummi kina da kyau kuma kina da wayewa, meye zai gagareki idan kika bar wannan damar tawuce miki za kiyi nadama. Ummi ta jima tana nazari kanta na 'kasa tace kada kijefa min damuwa a zuciyata kan abinda samuwarsa gareni zaiyi wahala. Jiddah tace "idan kika sa wa zuciyarki damuwa akan samuwar khalifa gareki to lallai wahala zai zame miki, yayin da idan kika sa wa zuciyarki abu ne mai sauki mai sauki ne kada kidamu da jin kan yaya khalifa ko haduwarsa da takamarsa kina da hanyar da za ki iya mallakar zuciyarsa cikin sauki mata irinmu da ba mu da alaka ta jini tsakaninmu shi ne zai mana wahalar samuwa ke kuwa uwa daya uba daya iyayanku suke gdanku gdansu ne haka gdansu gdanku ne, kitashi tsaye ki mallaki miji na fita kunya mijin da za a iya shiga dashi ko ina a kalleku bayan kyau ga dukiya ga uwa uba ilimi ba jiya kikace min zai tafi germany karatun likita ba? Cikin sanyin murya ummi tace "jiddah na yi mamakin wannan magana ta ki sai jace kin shiga zuciyata, wlh jiddah tun kafin in mallaki hankalin kaina insan waye namiji insan menene so nake matukar so da sha'awar yaya khalifa duk sanda na ganshi nadinga kwatantashi a matsayin mijina abinda yas nakasa kusantar kaina gareshi sbda miskilancinsa kina gani ko gaisawa akayi sama sama yake amsawa, ban taba gaida khalifa ya yi min murmushi ba al'amarin har tsoro yake ba ni, amma khalifa shi ne nakema son dana tabbTar babu wani d'a namiji da zanwa ko da rabin son danake masa, tabbas a wannan rana kin fama min inda ke min 'kai'kayi a da na kwantarwa da zuciyata soyayyarsa dake raina amma yau kin tayar min da ita insha Allahu sai inda karfina yakare xan nemi soyayyar yaya khalifa bakin raina zanyi duk abinda zan iya don ganin na mallake shi ba zanyi sakaci wata d'iya mace tarabani dashi ba ko ta halin 'ka'ka. Tami'ke a hankalin ta tsaya gaban madubin dake bango tana kallon kanta tun daga sama har kasa, doguwar rigace a jikinta wadda tafito da zahirin suffar jikinta, gashin kanta ya sauka har gadon bayanta, kamar yadda take doguwa mai kyau siffa tana daga cikin abinda yake dauker hankalin maza tare da ummi shi ne gogewar fatarta, ba fara bace 'kal 'kal amma tana da haske sosai, fuskarta tanada daukar hankalin mai kallonta, sannan tana da daukar dressing in dai za tasa kaya sai sun amsheta sbda ba zai yiwu tasa kayan dabasu dace da kalar jikinta ba, haka duk d'inkin dazatayi sai ta tabbatar zaiyi mata kyau sbda ita Allah ya yi ta da iya zabar kaya dan shi kanshi telanta daban ne shi yake mata tsala tsalan dinkuna nagani, duk kayan daza tasa sai an tabbatar an yi matching dan a birge ai kuwa tana birgewar, ko a salon iya tsara magana aka tsaya musamman ummi za tatafi da imanin mutum yatsaya yasaki baki yana kallonta yadda za kaga tana tsara xance daya bayan daya mai shiga cikin wannan ne yasa takeda mutane a gida da makaranta, hatta malamansu sun santa kan tsananin iyayinta da son gayu duk kudin da hajiyarta tasamu akan sayawa ummi sutura mai tsada da kayan kwalliya suke tafiya kowanne kya sai an hada mai mayafi, takalmi da fashion don ace dai an yi kyau. Ummi tana matukar jin kanta ba kowani d'a namiji take kulawa ba duk da dumbin masoyan dake nuna mata zahirin kauna ba wani d'a namiji daya taba burgeta sai yaya khalifa. ************** Jidda ce kawai ta 'kud da 'kud kuma aminiya ga ummi tun suna yara ba ajin kansu kasancewar katanga ce kadai taraba gdansu kafin rasuwar mahaifin ummi baida abokin shawara kamar aminin daya wuce babansu jiddah shi ne dalilin dayasa zumuncin na su yakara kwari, duka makarantun dasuke zuwa guda uku a kowacce rana duka ajinsu daya kullum tare suke wuni babu abinda yake rabasu sai bacci, kullum shawararsu daya banbancinsu shi ne jiddah ta fi ummi tanada tsiwa da jin kai da raina mutane, yayin da jiddah ke da girmama mutane da gudun zuciya. Iyayan jiddah hamshakan masu kudi ne su biyu suka haifa daga ita sai yayanta Habibullah wanda yake kasar england karatu, itama jira suke takammala secondary su fidda ita kasar waje tayi karatun ta na jami'a dukda cewa ta ce babu inda za taje sai fa in za a hadasu da aminiyarta ummi, lokacin data fadi haka mominta ta yi murmushi ne tace "jiddah manya, jiddah aminiyar ummi, idan har ummi da iyayanta sun amince za ta outside karatu mai zai hana dady dinta yabiya mata insha Allahu indai kinga ummi baku tafi tare da ita ba ,ita ko iyayanta suka ce ba za ta ba. Cikin tsananin farin ciki jiddah tashigo gdansu ummi dagudu ta isketa cikin dakin hajiya tana kwance bisa gado tana karatun littafin hausa tafisge littafin ta watsar tace "Albishirinki. Ummi ta lumshe ido tace "kina burgeni jiddah sbda koyaushe ina ganin ki cikin nishadi da wahala mutum ya fahimci wata damuwa a zuciyarki. Tace 'hakane ummi ban cika sa wani abu a azuciyata ba ballantana yadameni ina daukar raywa da sauki dan kada in dami zuciyata zuwa nayi in gaya miki insha Allahu idan mun gama secondary tae za mu tafi outside karatu. Ummi tayi shiru batace komi ba fuskarta ko walwala babu ballantana tanunawa jiddah ta ji dadin maganarta, itama jiddar gimtse far'arta ayi tace "ummi yaya ni dana taho da batu mai dadi gareki ina mai gaggawar yi miki albishir sai inga fuskarki ta ahiga damuwa kamar wadda tazo miki da labarin tashin hankali ? Ummi tayi doguwar ajiyar zuciya tace "jiddah ba wai farin cikine banyi ba ba yadda za ayi ayiwa mutum albishir irin wannan yakasa farin ciki sai dai inason kiyi hakuri jiddah na gode kwarai da gaske da kaunar dakike min wadda tasa har kike jin ba za ki iya tafiya wani gari kiyi rayuwa babu ni ba, iyayanki suka amince miki akwai haka tare Dacewa kudi za su kashe ba na wasa ba, babu inda za ayi haka sai in akwai kauna mai yawa kuma kauna wadda take ta gaskiya sbda Allah to sai dai inda gizo ke sakar shi ne jiddah kiyi hakuri, zuciyata ta yi nisan kiwo a cikin soyayyar yaya khalifa, ba zai yiwu bayan kammala secondaru din mu in bar kasar nan zuwa wata kasa ba ba tare da na san matsayina a zuciyarsa ba. Ba tare dani ba duka hanyar da ta dace nabi don in nemi soyayyarsa ba don in nemawa kaina masauki na din din din a zuciyarsa. Tagyara zama har yanzu idanuwanta na kallon jiddah taci gaba da fadin "jiddah zuciyata tana yiwa yaya khalifa wani irin so wanda ban taba tunanin akwai irin son a duniya ba, ba zan iya bayyana miki irin yadda nake jin ciwon sonsa a zuciyata ba. Kullum dashi nake kwana in tashi kullum soyyayarsa karuwa take a zuciyata ban kuma samu mafita ba akan yadda zan bullowa lamarin har gashi tafiyarsa germany ta matso. Tun a yanxu ban samu mafita ba inaga in yatafi tafiyar dazata dauke shi shekaru hudu. Ina matukar tausayawa rayuwata jiddah ban san halin da zuciyata za takasnce ba yayin dana rasa yaya khalifa.... . Jiddah takamo hannunta cikin tausaya wa tace "ki kwantar da hankalinki ummi in dai yaya khalifa mijinki ne da izinin Allah za ki aure shi, in har baki auri khalifa ba to Allah ne bai kaddara aure ba ba za ayi ba, shi ne amfanin daukar rayuwa dasauki. Ummi hakika na san yaya khalifa miji ne abin so gakowacce irin d'iya mace kowa cece ita kuwa, ko ni kaina din nan abinda yasa nake nesanta kaina daga burgewar da yake min na san ya yi min nisa ne ba zan same shi ba, ke din ma bansan za ki tsanantawa zuciyarki matsananciyar soyayyarsa har tashafi duk rayuwarki ba, da tun farko ban zungure ki da maganarsa ba, ko dacewa kina sonsa daman chan a baya tun kafin in tuntubeki da maganar amma tuntubar danyi miki ita tajefa ki a wannan damuwar. Ummi ina mai ba ki shawara ta gaskiya akan ki dauki rayuwa dasauki duk abinda kika zafafa shi zafi zaiyi gareki Kuma ba wanda zai dagawa hnkli sai ke din. Ki cigaba da fafutuka akan neman soyayyar yaya khalifa har kiga kin aure shi amma dan Allah kada kibari damuwa ta lalata miki tunani ki dogara ga Allah sai komi yazo miki dasauki. Ummi bata kara cewa da jiddah komi ba har aka fara kiraye kirayen sallan magriba tayi mata sallama takoma gdansu, dakyar tatashi tayi sallah taci gaba da zama a daki kan daddumar datayi sallah tana jan carbi tayi tagumi idanunta sunyi jawur. Hajiya hauwa taahigo dakin ta sha adon ta kamar yadda tasaba kai bakace ita ta ajiye manyan samari irin su hassan ba, mace ce mai son gayu shi yasa ummi ke samun daurin gindin gayu da kece raini a gunta. Tayi sororo tana kallon diyar tata tace "ummi wai lafiya kike kuwa kwana biyun nan kin sauya ko ba ki da lfya ne? Ummi tadago ido zuciyarta ba dadi tace "hajiya zauna kiji wata magana. Dasauri tazauna ummi tace "hajiya barin kashi a ciki ba ya maganin yunwa, yau zan fayyace miki damuwata dan kisamo min mafita a cikinta, hajiya zuciyata ta kamu da tsananin son yaya khalifa inaso kigaya min hanyar dazanbi yasoni. Hajiya tadafe kirji tare da fiddo ido tace "ummi kinsan maganar dakike fada kuwa? a duniya kirsa wanda za ki so sai khalifa? Kara gaya mini ko dai ba khalifan dana sani ba kika ce kina so? Ummi tamatso kusa dai tadora kanta akan cinyarta tace "hajiya babu wani khalifa dazan yi magana akansa wanda yawuce na mu ba zan iya raba zuciyata da son sa ba kuma ba na bakin ciki da son da zuciyata ke masa insha Allahu ba xanyi nadama ba mafita ce ban sani ba ita nakeso kisanar dani hajiyta. ************ Maganarta tadamu hajiya hauwa yau dai ba ta son mahaifiyar khalifa haka shi kansa khalifan ba kaunarsa take ba, a daran takira kanwarta hajiya sauda wadda ita ke binta ko gaisawa bata bari sunyi ba tace "saude tashin hankali ne ya saman a daran nan. Hajiya saude tace "har gabana ya fad'i "meya faru yaya hauwa? Tace "wai ummi tarasa wanda takeso sai wannan yaron mai shegen girman kan tsiya wanda ko kallo mutane basi ishe shi ba. Hajiya sauda tace "wai waye ne ?duk kin rikitani. Hajiya hauwa taja dogon numfashi cikin takaici tace "waye in banda khalifa. Hajiya sauda tace "to sai me dan ummi ta ce duk duniya babu wanda takeso sai khalifa, kada kibani kunya mana yaya hauwa kamar ba ke ba ko in ce kamar ba mu ba? Hajiya hauwa tace "uhm saude dole hankalina yatashi kina kallo fa yadda rayuwar yaron nan yake, ko kallo mutane basu ishe shi ba, gaisuwa da yake mana ma dan ya zama dole ne a gareshi, in banda haka khalifa bamu isa yagaidamu ba ni kam ba khalifa da uwarsa na tsanesu ba zan taba kaunarsu ba shiyasa da ummi tabudi baki tace min ba ta da gwani wanda yawuce khalifa hankali na yayi mugun tashi nayi gaggawar kiranki a waya dan musan abin yi. Hajiya sauda tayi murmushi tace "Allah sarki yaya hauwa ni ko da kika gaya min maganar nan sai naji zuciyata ta yi 'kal 'kal, na jima banji maganar data faranta min rai irin wannan ba. Hajiya hauwa tayi tsaki tace "ke da Allah ana ga yaki ke kina ga kura me za muyi khalifa, yarinyarn nan ummi duk dan abinda na samu a gun kayan kwalliya suke tafiya don dai musamu gallelen alhajin birni mu darje amma ta lalace kan khalifa, wannan sangartaccen yaron da bai san yafita neman na sa ba sai dai dukiyar ubansa dasuks jiku a ciki shi da uwarsa. Hajiya hauwa tace, "to sai me idan khalifa bai nnemi na sa ba sai na ubansa? dama me muke nema ne? burin mu dama aibai wuce musamu wani ba ko d'an wani, to bamu samu wanda yake wanin ba ai a karan kansa sai dan wani to dawani da d'an wani in dai za mu shaki dukiya ai mu burinmu ya cika. Hajiya saude tayi ajiyar zuciya tace "to in banda abinki saude taya za mu iya mallakar wannan yaron mai masifar girman kan tsiya, zancan danake miki fa a satin dazai kama idan Allah ya kaimu zai tafi germany karatu sai ya yi shekaru hudu zai dawo, na ji uban abban hajiya yana gayawa jummai wai so yake yazama cikakken likitan mata, don haka karatu yakeso yayi a germany mai zurfi. wlh saude idan kinji kudin da muhammadu yakashe akan wannan tafiyar na khalifa sai kin rike baki sai hankalina ya kasa karba inda zai zauna ma tsawon wannan shekarun hudun da aka zuba akan su ya ishe irin mu mumore mun gama arziki a duniya dai. Wai amma jummai maimakon tai mashi fada yarage kashe kudi haka akan khalifa sai fadi take ya yi daidsi. Hajiya saude tayi murmushi tace "to ko anan za kisan lallai auran ummi da khalifa shi zaisa mu mallake dukiyar alhaji muhammadu cikin sauki kinsan ana cewa daka haifa gwamna gwara kahaifi matar gwamna saita kawo maka gwamna har gida sai ka shekara kana yawan neman ganin gwamna ma baka ganshi ba amma idan kabi takan matarsa lokaci guda sai kaganshi ba tare da ka samu matsala ba sbda ita mace mace ce daban take, yanzu idan muka bi duk hanyar data dace gun cusa ummi a zuciyar khalifa shikenan mun mallaki khalifa, idan muka mallaki khalifa sai yadda mukayi dashi ko uwarsa bata isa tayi yadda takeso ba sai mu din dai. Da ba a so muci arzikin slhaji muhammadu kinga munci dan bakin ciki sai dai yamutu. Kuma anan ne za mu fanshe haushin da mukeji na hajiya maijidda uwar khalifa, tana ji tana gani za mu aurawa khalifa ummi za mu mallake shi 'kaf shi da dukiyar uban na sa tunda dama alhaji muhammad ba shi da tunani sai khalifa, idan ummi ta auri khalifa shi kuma zai kasance ba shi da tunani sai na ummi sai yadda mukayi dashi da dukiyar ta shi, hajiya maijidda tazama yar kallo yadda tamaida mu yan kallo mu da dukiyar dan uwanmu ba mu da iko akanta muna gefe sai abinda aka sammana me zai hana muyi farin ciki akan soyaygar da ummi ke wa khalifa, wannan itace hanya daya tilo da burinmu zai cika kuma za mu nunawa maijidda ita ba komi bace hancin gauta ce bata isa komi a miya ba. Hajiya hauwa tace "tabdijam amma fa kinyi tunani saude shi yasa ake cewa mai shawara ba ya aikin banza, tabbas gaskiya kika fada sai dai abinda nake jinjinawa shi ne tayaya za mu mallaki khalifa kidinga tuna masifar jin kansa fa. Hajiya saude tace "kash yaya hauwa ni kunya nakeji kamarki wannan maganar kalaman nuna karaya da gazawa suna fitowa daga bakinki, khalifan banza khalifan wofi har meye shi, wa yayi ma ballantana yafi wani ko za murasa zanin daurawa sai mun mallaki khalifa, sai mun shiga ko ina zamu shiga dan mu tura ummi gdan khalifa, matakin farko dazamu fara dauka shi ne ummi za takoma gdansu khalifa dazama, hikimar yin hakan shi ne a matsayinta tamace wadda takai mace muka dade muna koyar da ita kissa da kisisinar jan hankalin namiji tabi hanyar duk data dace tafara kafa gwamnatin ta a zuciyar khalifa kafin tafiyarsa germany a wadannan gajerun kwanakin 'kididdigaggu, ko yaya ne mu tabbatr khalifa ya bar kasar nan ne da tunanin ummi ba wai soyayyarta ba. Kafa soyayya a zuciyar wanda kwata kwata hankalinka ba ya kansa abu ne mai wahala sai a hankali, lamari ne da ba ayi masa gaggawa a cikin lamari irin wannan to ko shakka babu ba zai ci nasara ba, ana kaddara cewa mutanen dasuke cin nasarar abubuwan dasuka sa gaba na rayuwa su ne masu hakuri a dukkan lamarinsu. Sbda ita nasara kafad'a da kafad'a suke tafiya da hakuri, ballantana lamari irin wannan ba abu bane mai wahala amma fa ga mace datasan abinda take wadda takaranci halayyar d'a namiji, kada ki jinjinawa ummi jin kan khalifa har jikinta yayi sanyi, ki kashe mata guiwar taji cewa ba za ta iya ba ,ko da tanajin cewa ita d'iya mace ce da za ta iya jan hankalin d'a namiji ko waye shi, idan kika jinjina al'amarin itama girmama zaiyi a zuciyarta daga nan sai ta kasa yin komi sai asarar tashafe mu baki d'aya. Amma idan kika nuna mata ba kowane khalifa face namiji kamar kowa shikenan saita ka ra samun kwarin guiwar kokarin janyo hankalinsa har muyi nasara. Yadda za ayi takoma gdansu khalifa da zama kuwa wannan sai idan Allah ya kaimu wayewar gari gobe lfya idan nazo sai musan abin yi. *************** Ba kowa a gidan sai fatima ita kadai, sauran kannanta suna makaranta yayin da goggonsu Abu tatafi barkan haihuwa da akyi musu, ta karasa tankadan garin tuwon datake takai kitchen tashare gidan tadora ruwan tuwon sannan takoma kan tabarma tadauki wani littafi na addu'a tana dubawa maisuna Du'a'ul mustajaba. Zuwa can ta ajiye ta kwantar danta kan pillow tana tunanin auran da za ayi mata da malam musbahu nan da lokaci kadan har yanzu dai malam bai yanke lokacin da za ayi bikin ba haka zalika musbahu bai taba kiranta da sunan zancan ba, kunyarta yakeji kamar yadda ita matake bala'in jin kunyarsa, kafin malam yafurta cewa zai hada su aure, malam musbahu ba wanda yafi shiri da shi a yaran gdan sai ita, tun tana karama musbahu ya fi kaunarta fiye da kowani d'a a gidan nan duk abinda yasamu kafin yaba kowa sai ya ba ta har sai da mutane suka shiga zargin ko dai son ta yakeyi, ganin bai furta ba yasa aka watsar haka itama take bala'in kaunarsa tun lokacin da bata sani ma musbahu ba dan gdansu baneballantana data mallaki hankalin kanta tagane musbahu maraya ne yahadu da zaluncin matar kawunsa har malam ya amshi ragamar rigimar rikonsa, sai tausayinsa yasa take ka ra kaunarsa suka rike shi tamkar dan gdansu, in banda wannan lokaci da malam yake gayan mata, da ya gayawa mutanensa cewa zai ba wa malam musbahu auran diyarsa fatima sannan dayawa wasu suka san ba malam bane yahaifi musbahu ba sbda yadda malam din da ita goggo Abu din da yayansu ke matukar ji da musbahu shi ma haka yazamo dan halak agaresu ya sadaukar da rayuwarsa gaba daya gun soyayya a garesu, kyautata musu tamkar su suka haife shi, koda yake ako da yaushe yana gayawa malam cewa bai taba kaunarsa a matsayin iyayan riko ba kullum a matsayin mahifa yake daukarsu wanda ba shi da kamarsu a duk fadin duniyar nan kamr yadda yake da tabbacin suma haka suka dauke shi, rayuwa suke a gdan mai dadin gaske ga shi dai ba su da abin duniya sai rufin asirin Allah, abinda yakesa suke jin dadin rayuwa shi ne girmama junansu da kaunar juna da ake sbda Allah da tarbiyyar data ratsa duk d'an dayake na gidan ne, nisan da fatima tayi cikin tunani yasa har ruwan data d'ora bisa wuta ydinga tafsa tamanta dashi sannan mutum na tsaye a kanta bataji takunsa a lokacin daya shigo ba ballantana sallamar da yayi mata saida yatsuguna gabanta yace "fatima wani irin tunani kike haka kina yarinya karama mai kankantar shkaru haka ina ke ina wannan tunani? Kafin yagama rufe baki fatima tatashi dagudu jikinta na rawa za ta shige daki, musbahu ya mike shima yana murmushi yatare kofar dazata shiga yana murmushi yace "fati haka za mu zauna koda yaushe kina guduna kamar dodo tunda malam yace ya ba ni ke ban kara magana dake ba ko gaida ni ba kya zuwa kiyi ina dalili. kan fatima na kasa kamar za ta nutse a gun sbda kunya, tarufe fuskarta da tafukan hannayenta yace "je ki kigama tuwon kuma kada ki kona mana tuwo amma fa lallai yau ke za ki kawo mana tuwo ni da abokina mansur, idan har bazaki kawo mana da kanki ba ba na cin tuwon, idan kinyi kada ki aiko dashi zan kwana da yunwa, bai saurari abinda za tace ba yafice yabarta tsaye kamar an zare mata jijiyoyin jikinta tana kallon yadda ruwa ke tafarfasa akan wuta amma ta kasa tashi tayi talge, hankalin fati ya tashi kwarai da gaske idanunta suka cika da kwalla har ji tayi kirjinta ya yi mata nauyi numfashinta yana sama sama kamar zai dauke . Tun tasowar fatima babu wani d'a namiji daya taba cewa yana sonta ta amsa mai ballantana maganar soyayya ta had'a ta dashi shekarunta goma sha shida da haihuwa ajinta hudu a secondary, tun tana shekara sha biyar ake cewa ana sonta kasancewar ita yarinya ce da Allah yahorewa kyau ba na misali ba abin sai wanda yagani sannan tana da shiga rai yadda kasan wadda aka tsuma ta da maganin farin jini, in dai namiji zai ga fatima sai ya yi shaawar ace matarsa ce. sbda bayan kyaun ga natsuwa ko magana fati take ka san ta samu tarbiyya irin wanda duk d'a namijin arziki yake burin mallka a matsayin matar aure. Shigowar goggon ta Abu yasa tatashi dagudu tawuce 'yar rumfar kwanon dake gaba kitchen dinsu inda suke hura wuta, goggo tarike baki fatima yau me ya sameki sai yanzu ake talgen tuwo? kina sane dacewa ba na son ayi tuwon dare a gidan nan, fati bata saba karya ba don haka tai saurin kallon idanunta kadai, goggo dai ta san akwai abinda ke damunta yau abinka ga babba ballantana wanda yahaifeka, ta jima tana nazarin fuskar fatima sannan ta gyada kai tawuce daki. Har fati tagama tuwo a sanyaye jikinta yake ko magana akai mata dakyar take amsawa hatta shi kansa bakinta ya yi mata nauyi, bayan sun idar da sallar isha tana zaune kusa da goggo sanye da hijjabinta da charbi a hannun ta tana ja hawaye sai neman xubo mata sukeyi tana maida su dan kar goggon ta gane tayi mata tambayar da za ta gagara amsawa amma ina dole tatashi daga gun tashiga dakin dasuke kwana da kannanta tazauna tana sharar kwalla, har goggo tashigo tazauna kusa da ita cikin saryin murya da tausayawa irin na d'a da mahaifi tace "fatima na san duk abinda zai dameki bai wuce maganar auranki da musbahu ba, fati kada kicutar da kanki idan ba kya son musbahu kina sane malam bazai matsamiki ba, shi ma tunda farko abinda yasa yace ya ba shi ke kai tsaye dan ya san dakake har musbahu babu wanda ba zai yi masa biyayya ba. Sannan ya yi la'akari dacewa ke da musvahu akwai kaunar juna mai karfi a tsakaninku tun kafinn ku mallaki hankalin kanku kusan ku waye ku a rayuwa. Fatima tace 'goggo inason yaya musbahu sbda ba shi da makusa da mace za ta ki shi hasalima banga abinda baba na zai bakata in ki yi masa ba, inji ina kinsa a matsayinku na iyaye na, biyayyarku a gareni wajibi ce, wannan damuwar tawa ba ta da nasaba na kin yaya musbahu sai dai ni kaina bansa abinda yashiga xuciyata ya tsunduma ni a bakuntar rayuwa a yau din nan . Goggo tayi murmushi tace "ai baki shiga bakuwar rayuwa ba fatima sai randa kika shiga gdan aure kika zamo matar aure lokacin ne za kishiga cikin bakuwar rayuwa wadda baki santa ba amma da sannu saiki zama 'yar gari har wata rana kigaya wa wasu yadda aka gaya miki, kowacce mace sai da tashiga irin wannan bakuwar rayuwar. Tashi maza ki kaiwa musbahu abinci daga yau haka za kidinga yi. Bayan goggon ma cigaba tayi da zama ta kasa tashi har sai da goggon taleko takara yimata magana sannan tafita tadauki abincin tanufi dakin musbahu dake zaure, ta yi sa'a ba kowa a dakin ta ajiye dasauri za tafita sai ga shi yafito daga toilet yace "to dawo kidana murna dodon na ki yananan, har wani rawar jiki kike za kigudu ko? Tayi murmushi tatsuguna daf da gado tarufe fuskarta da hijabi, yazauna akan kujera yace "fatima ki rufe fuskarki yadda kikeso sbda kina da abin rufewar, mace kyakyawa irinki ta isa tayi irin kowacci yanga ga kowane d'a namiji ko waye shi ballantana almajiri kamar ni. Fatima tun lokacin da baba yabudi baki yakira sunana har sau uku hankalina a tashe nadinga amsa masa sbda bansan wace magana zai gayamin ba wadda har tasa yayi min irin wannan kiran. Tun kafin yagaya min na san duk abinda zai gaya min din magana ce da muhimmancinsa ta isa. Fatima malam yabude baki yace dani "musbahu na ba ka auran fatima, wlh fati ban taba kwana a zaune ba, yadda naga rana haka naga dare hnkalina ya tashi kwarai dagaske ba dan komi ba sai dan tunanin dame zan rike mace kamar ke fatima. Ina sane dacewa mutane da dama suna tunanin inasonki ne sbda yanayin shakuwar mu tun kina karama nima ina karami to Allah yasani fatima ina matukar kaunar ki sbda haduwar jini da Allah kan hada tsakanin mutum da mutum amma Allah ya sani tun da nake ko da wasa ban taba kallonki da wata siffa ko da wata manufa ba, bayan kanwata ina kallonki ne a matsayin kanwata wadda muke ciki daya. Yana magana ne cikin yanayin tausayin kai muryarsa kasa kasa yana mata wani irin kallo, lamarin yajefata ckin sabon tashin hnkali da rudani idanunta suka kama zubar da hawaye, fatima ban taba tunanin akwai lokacin da xan iya zama in miki maganganu makamantar wannan ba sbda kallon ki nake kamar kanwar damuka fito ciki daya. Shi yasa nayi ta jinjinawa yadda zaman aure zai kasance tsakanina dake. To amma a safiyar yau abokina mansur yasauya min tunani akanki ya ce dani 'tunda aure bai haramta tsakanin ka da fatima ba ba yadda za ai kunya tahana muku nishadantar da zuciyarku ta hanyar soyayya, shi aure dakuke gani ba bu abinda yake rike shi yazauna lfya sai soyayya. Ya jawo abinci yakama ci yana cewa "fatima har na rasa dawata kalma zanyi amfani a bakina kan yiwa Allah godiya daya azurtani da mace kamarki, fatima in sonki wlh don Allah ni ma ki ce kina so na inji dad'i. Bai aune sai kawai yaga ta tashi ta faki idonsa ta fice daga dakin a guje ya kyslkyale da darya har da tafa hannu yace Allahu akbar, fati manya shi abinda yake ba shi mamaki shi ne wai an wayi gari shi da fatima sun zamo masoya soyayya kuma irin ta aure. Tabbas Allah ya amshi ran mahaifinsa ya zamo maraya sai dai shi maraya ne wanda yai rashin mahaifa amma ba wanda yarasa iyaye ba, a rayuwa iyaye suna da daya wa mahaifa ne kwara d'aya kachal, shi kam Allah yai masa baiwa da iyaye nagari yagirgiza kai yana murmushi. ****************wannan page goron jumma'a ne gareku ba ki d'aya,,,, daga jiddan nan dai 'yar mutan A DAREN FARKO 9 karfe goma da minti hamsin hajiya saudat ta faka motarta a kofar gdansu ummi, ta sha ado da wata galleliyar shadda maroon colour, ta yi kyau kasancewar su kam Allah ya hore musu kyau da son gayu. ita mijinta ba wani mai wadatar zuciya bane sosai kusan itace mai kudin don yar kasuwa ce, daga kasar dubai ake kawo mata kayan sa wa na mata, koyaushe gdan ta cike yake da mata business takeyi ko ta ina. Ita kam Alhaji muhammad ne asalin ba ta jari amma duk da haka ba sa gani. Taahigo uwar dakin hajiya hauwa tana kwance kan gado ummi na kwance gefenta zancen khalifan dai suke, saude tace "kitashi mana tun yanzu kifara shirya kayanki don da kaina yau zan kaiki gdan alhaji muhammadu chan za ki zauna ni zan xan gaya masa cewa tunda Allah yayiwa mahaifinku rasuwa ya zama dole a tallafa yaya hauwa a gun rikonku, na san dai idonsa da kunya ba zaice ba za ki zauna mai a gda ba sannan ita hajiya maijidda na san za tai farin cikin xaman ki a gdanta, don za ta ga cewa haka zaisa tasamu fada a gunmu ke Kuma idan kinje ba cewa akayi kisaki jiki kina bacci ba, yakin neman zuciyar khalifa za kiyi ko ta halin kaka sannan ki dage dun kyautatawa uwarsa, yin haka ne zai sa in yadawo daga germany ko bai sonki da kansa ita za takalli kyautatawar da kike mata ta tursasa shi ya aureki, kin san son uwa shi ne son d'a, Hajiya hauwa tace "wannan shi ne hanya mafi dacewa. Zuciyar ummi fari kal san da tagama sanya kayanta suka nufi gdansu khalifa, . A bisa hanya hajiya sauda atana ta wassafa mata yadda za tai amfani da damarta duk san da take dashi don jan hnkalinsa. Ummi jin ta kawai tana dura mata a zuciyarta, daga alhajin har hajiya maijidda sun nuna jin dadin zaman ummi a gdan daman fada ne ba na so nayi a samu matsala in ba haka ba in ba haka ba idan hauwa da duk yaranta sukace za su zauna a gdan nn, rikesu xan iya insha Allahu. Daki guda aka warewa ummi a gdansu khalifa kusa da na mama, akwai gado da dressing mirror da toilet acikin dakin, tun a ranar da taje gdan aka gama wannan mama maijidda tace da ita '"gdan nan gdanku ne kin sani ki dauki kanki fiye da yadda kike rayuwa a gdan iyayanki, duk abinda kkeso akwai su idan ma babu kada kigawa kowa kigaya min in har da kudi za a siye shi zan saya miki ummi. Batazo gdan nan dan cutar da khalifa ko iyayansa ba dan haka za ta nemi soyayyar khalifa a bisa hanya ta gaskiya da tsakani ga Allah. Ta tashi tabude kofar sakamakon kwankwasawar dataji ana yi, daya daaga ckin yan matan dake aiki ne tace da ita, "Mama ta ce in zo in ce miki an gama sanya abinci a tebur kifito kici. Ummi tace "ki ce ina zuwa. Har yar aikin ta tafi ta kirata tace "meye aikinki agdan nan? Tace wanke wanke wani lokaci ina yin girki. Ta jinjina kai tace "wa ye yakedafa abincin da yaya khalifa yake ci? Tace"yana da kyankyami bai yarda da abincin mu ba shi da abbansa mama ke dafa musu abinci sai dai mu tayasu shirya tebur kawai Tace "yanzu ya dawo? Tace "eh yana falon dasuke cin abinci shi da iyayansa. Cikin zumudi ummi takoma daki gaban katon madubi ta tsaya tana kallon surar jikinta, daga sama har kasa tana tmbayar kanta shin tana da tagomashin da zata iya jan hnkalin namiji kamar khalifa? Tafito falo cikin yauki khslifa yana zaune kusa da abansa kan kujerar zaman mutum uku sanye yake da bakar kot, da wandonsu. Zahiri da badini khalifa ya yi kyau ba na wasa ba kamar yadda yake kyau a idon kowacce mace ballantana ummi data mutu acikin soyayyarsa. Ta gaidasu gaba daya, kallo daya shi ma khalifan yayi mata yamaida kansa ga jaridar da yake dubawa kafarsa daya tana kan daya, mama ce tace dashi khalifa ga kanwar ka nan ummi ta dawo gdan nan da zama. A nan ne yadan ajiye jaridar akan cinyarsa yakalli ummi suka hada ido yayi mata murmushi takaitacce yamaida ganinsa ga mama yace "ya yi dai dai hakan kinga kin samu mai tayaki zama. Tsigar jikin ummi yadinga tashi sakamakon murmushin khalifa da ta gani kuma ita yayiwa murmushin. Karfe taran dare khalifa yatashi yawuce dakinsa ya kara yin wanka yasauya zuwa blue din jeans da farar t shirt yazuba wani mai tsadar takalmi ga farin gilash dan siriri ya manna ya fesa turare yadawo falon da iyayansa ke zaune yarusuna daf da abbansa yace"abba ba ni aron makullin motarka za ni unguwa in dawo. Ba musu yazaro key din ya damka masa yakalli mama yace "mom sai na dawo. Ta sha kunu sosai tace ina za ka a wannan daren? Yadubi agogo yace "mom wani abokina zan duba a asibiti da asubahi za a tafi dashi egypt. Tarasa abinda za tace sai kallo tabisa dashi har yafice kamar yadda itama ummi ta lalace kan kallon sa. Tabdijam ashe jan aiki ne a gabanta ********** Khalifa bai dawo ba sai biyu da rabi na dare, yana shiga dakinsa yafada bisa gado bacci yai awon gaba dashi . Da sassafe ummi tariga kowa tashi agdan tayi wanka tatsala ado za tashiga kitchen sa'ar da tayi ita gwanar iya girki ce da kwalliya ta yi cos din wadannan abubuwa guda biyu a gun hajiyarta. Mama tafito wurin karfe bakwai d rabi tana shirin hadawa abban kayan tea sbda fitar da zaiyi dawuri, sai taji kamshin girki ya game dakin. tashiga kitchen suka hada ido da ummi tarike baki tana murmushi tace 'oh sannu da himma ummi irin wannan kamshi hka? Ummi tatsuguna tana murmushi tagaida tace "ummi ke za kidinga girki a gdan nan, girki ba zai hanaki bacci ba a lkcn da kowa ke hutawa ko yan aikin nan a yanxu haka suna chan suna bacci idan ba abban ne zai fita da wuri ba sai karfe gomaake gama abinci sannan aci. Ummi tace "mama ai daga wannan rana dana dawo gdan nan da zama insha Allahu ruwan shayi ba za ki sake dafawa da kanki ba sai fa in ba na nan, kuma yau ma na tashi da wuri ne jin abban ya ce zai fita dawuri. Mama tagyada kai tace "ya yi kyau lallai na san za ku shirya da yayanki khalifa don yana son abinci mai dadi. Gabanta yadan fadi tayi murmushi kawai. A kwanaki shida da ummi tayi a gdan kafin tafiyarsa germany sai da tayi kokarin da khalifa yake kulata a kalla yana amsa mata gaisuwa cikin fara'a har yakan ja ta da magana a wasu lokutan. Ranar laraba da asuba ta kama tafiyar khalifa germany a daran talata bai shigo ba sai sha biyun dare yan can wurin abokansa da yamatansa da sunan sallama. Mama tana zaune a dakinta ita kadai bayan ta idar da sallar shafa'i da wutiri da casbi a hannunta, ummi tashigo da food flask a hannunta tatsuguna gaban mama tace "mama yaya khalifa ya ce amala yau yakeso da miyar kubewa ya ce a gama da wuri, na yi masa tun magriba ga shi har yanzu bai dawo ba. Mama tace "na yi zaton ma kinyi bacci dama tun dazu kina falo jiran khalifa? lallai baki san gararin khalifa ba, idan yaga dama in yazo yaci idan baiga dama ba cikinsa. Tace "mama ko dai injira in ya ce bazai iya ci va ya yi sanyi in dafa mai wani abun. Mama tace "habadae sai kace kin zamo baiwarsa, tashi ki mayar da abincin falo kitafi ki kwanta. Ummi tadawo da flask falo maimakon taje takwanta sai ta zauna tayi tagumi a daidai wannan lokaci shi khalifa na daki tare da ramcy a yau ta kare mai gida taviyo shi har gdan ubansa, kamar yadda tasha gaya masa ta ce "duk abinda zai faru in dai a kaina ne ta dauka ba gudu ba ja da baya. Khalifa ya rasa yadda zaiyi da ramcy yau ta rikice msa yini guda yayi a gidanta tun safe har dare bata barshi ya motsa ba amma da dare yayi bai san yaya akayi ba har ta biyo shi a motarta ba, sbda shi kansa a yau ckin natsuwa yake sbda alhinin rabuwa da gda ba wasa bane tun safe jikinsa yake a sanyaye dan hka yinin dayayi a gdanta ma ba abinda ya iya aikatawa sai kwanciya tana kallonsa kawai. Sa'ar da yayi shi ne lokacin da zata biyo shi ta yi shigar mutumci ta sa dogon hijjabi mai hannu har kasa yana shiga da motarsa itama tasa tata motar mai gadi zai mata hayaniya kasancewar dare yayi kuma bai taba ganin motar a gdan ba khalifa yace yakyaleta bakuwarsa ce. Suna shiga daki yarufe ta da bala'i yace "ni za ki walakanta haka? baki san uwata da ubana suna gdannan ba? me kike son a daukeni dakika biyoni, toh abinda xan gaya miki shi ne na barki kin shigo nan dakinnan ne don kar inyi hayaniya dake a waje wanda bai san abinda ake ciki ma ba yasani, ki tashi kikoma inda kika fito... Sai tayi wuf takamoshi tarungumeshi kam kam tana masa kiss, wannan ne dalilin dayasa khalifa ba ya hada ramcy da wata dan wata hanya ta kan shawo kan namiji ta sani komi fushin da yayi kuwa, tace "khalifa me na rasa ne? meye mahaifina bazai iya mallaka min ba a rayuwa? sai kai kai ne kadai mahaifina bai da ikon yamallaka min sbda kudi bazai siye ka ba to yaya zanyi da raina khalifa? Jikin khalifa yayi sanyi kwarai da gaske bai taba tausayin wata diya mace irin yau ba, musamman yadda take me kuka da hawaye. Dai dai wannan lokaci ummi ta gaji da zama a falo tana takaicin ace khalifa bai ci wannan abincin ba yadda tzauna ta tsara shi hakan yasa ta kasa juriyar tafiya ta kwanta ta zuba abincin ta jera a plate tanufi dakinsa tunaninta shi ne tabar masa a dakin nasa tunda tana da makullin dakin shi da kansa yabata sbda yanajin dadin yadda take gyara masa komi a dakin a tsaftace. Tana isa kofar dakin tasa makulli ta bude, abinda tagani yasa gabanta mugun fadi, yaya khalifa rungumeda mce tana sanye da hijjabinta, bayan Runguma ba wani mummunan abu da ummi tagani amma duk da haka sai da abincin hannunta yasubuce ya tarwatse a gun takoma ckin gida da gudu tana haki, wani abin takaicin tahadu da mama a falo za ta sashen abba. Gaban mama yafadi tatsare ummi da tambaya, hnklin ummi yatashi tarasa abinda za tace wani karya za tawa mama, mama tawuce tabarta jiki na tsuma. Khalifa ture ramcy yayi yace shkan hnklinki ya kwanta kin tona min asiria gdan mu ko? Za tayi magana yadaka mata tsawa yace, "kawai kifita idan kikaci gaba da tsayuwa anan komi zai iya faruwa dake tunda asirina ya tonu ba na fargabar komi dn haka kama gabanki. ******** Karfwme dayan dare tayi khalifa ya kasa runtsawa, ganin da umi tai masa rungume da mace ya tayar mai da hnkli matuka bai san wani irin kallo yarinyar za ta ci Gaba da yi masa ba a yadda take ba shi girma shknan ta daina ganinsa da kima bayan wannan za ta iya gayawa mama daga nan maman za ta iyasa wa ai masa aure da diyar da maman ke son ya aura itace 'yar aminiyarta mai suna ummi. Yamike cikin tsananin mutuwar jiki cikin sanda ya kwankwasa dakin ummi a hnkli ya san dai da wahala su abba su ji. ummi tamike ckin tsoro tace waye? A hankali yace ni ne khalifa, dasauri tamike ko kayan bacci yau bata sa ba, kayan jikinta ne hijjabin datayi sallah, ta tsaya jikin bango tana kallonsa, cikin kakkausar murya ta jaruman maza yatsare ta da idanunsa. A wannn lokaci hnkalin ummi yai matukar tashi yace "ummi Murya na rawa ta amsa yace me ya kaiki dakina dazun? Tace abinci kawai naje kai maka na ga ka jima baka dawo ba ni kuma ba na so yakasance baka ci abinci ba sbda tun azahar na shiga kitchen nahda maka shi. Ya danna mata harra kamar zai shaketa yace 'damaa a dakina nasaba cin abincin? Sai dai na zo ne dan in gargadeki dan kisani kada wani yaji kinga wata mace a dakina. Idan kuma naji ko da wasa wani ya furta ta ko shakka babu na san ke kika fada, saiki saurari matakin dazan dauka wanda ba zai taba yimiki dadi ba. Sannan maganar soyayya tsakani na dake bbu, ni ba sa'anki bane, idan naji kince da mama ko abba ko wani cewa kina sona xa kisha mamakin matakin dazan dauka akanki, idan wannan ce gulmar da kika dakko kikazo gdan nan da ita sbda ni to kikoma don ba xa kiyi nasara ba, yaja tsaki cikin hushi yafice daga dakin. ******* Tabdijam su duka biyun bbu wanda yayi bacci a wannan dare, abinda yadaga hnkalin kowa daban kowa tunaninsa daban. Bayan fitar khalifa ummi tatashi ckin tashin hnkali tayi kuka kamar ranta zai fita tadubi agogo karfe biyu da minti ashirin bata ga nisan dare ba takitra mahaifiyr ta a wannan dare tana kuka wayar a kashe, hajiya sauda itama a kashe, takira babbar aminiyarta jiddh bata kashe waya ba, jiddah tadauka a figice tana fadin "inalillahi wa inna ilaihir raji'un. tadaga wayar abinda tace shi ne "ummi waye yamutu? Musanman kukan dataji ummin na rusawa kamar ranta zai fita, tace ni ce na mutu jiddah mesa kuka ban kwarin guiwar in so wanda ba zai so ni ba? Jiddah tayi ajiyar zuciya tace "ummi yau kwananki nawa a gdansu khalifa? Tace "shidda. Ta j tsaki tace "gaya min abinda yasa kika kira kanki matacciya gashi kina raye. Cikin sanyin murya ummi tabayyanawa jidda abubuwan dasuka fru a wannan daren, jiddah tace "kin ban kunya da hushi ummi kuma kin kashe kanki a wurin khalifa. jiddah tace "ummi ita nasara tare suj tafiya da hakuri, tunda khalifa tafiya zaiyi abu daya yarage miki shi ne kiyi kokarin yin abinda zai matukar ba shi tausayi tyadda idan yaje jamus abin zai tsaya masa a rai, . Khalifa na sanye da bakar kot ya tsuke sosai fuskar nan ba fara'a ya sha kunu, mama tana dakinta ko fita batayi ba, ummi ta bishi dasauri ta tsaya daga baya a langabar da kanta a jikin bango tana kallon khalifa yana taku dai dai. Lokacin dazai shiga motar ne ya waiwayo sai karaf kuwa suka hada ido da ummi, sai yayi cak yana kallonta bai shiga motar bazuciyarsa tashiga harba wa, ganin haka sai ummi tadaga hannu sama da nufin tana masa addu'a kuma tashiga yi masa bai bai da hannu tashiga ckin gda da gudu. Khalifa yafada mota abbansa na kusa dashi direbansu yahaya yaja motar zuciyar khalifa ba dadi abubuwa da dama suka cunkushe masa a zuciya. Tausayin ummi suka kamashi har suka isa filin jirgin saman malam Aminu kano hannunsa biyu tallafe a kumatunsa, abubuwa da dama suka tsaya mai a rai, abokansa da yammatansa ba wanda bai nunawa tsananin damuwa ba ama ba wanda yatsaya mai a rai irin ummi. Ya kwana yanajin zafinta a ransa a tunaninsa ma yarinya karama dako secondary bata gama ba tatsaya gaban namiji tace tana sonsa. Lokacin dazai shiga jirgi yarike hannun mahaifinsa yace "abba kayi min addu'a zan bar kasar nan cike da kewarku zuciyata ba dadi. Abban yarufe me baki yace "a duk lkcin da mutum zaiyi tfya abinda yake tsirga mishi shi ne abinda yafaru lkcn rabuwarku. Kamar yau danazo maka rakiya insha Allah kamar yau xanzo taryarka in dai muna raye. Kazauna da kowa lfya kaji tsoron Allah gun muamularka da mutane sannan kariki gskiya da amana ba za ka tabe ba kuma ba za kayi asara ba insha Allahu Duk dauriyar xuciya irin na namiji khalifa sai da yashiga jirgi yana goge hawaye abbansa yabishi da kallo yana murmushi A DAREN FARKO 10 Ummi tagyara zama tare da jan dogon numfashi tace "jiddah khalifa ya tafi ba tare da na amfana da zaman da nayi a cikin gdansu ba, face bacin rai da mugun gani da idanuwa na suka gani. Jiddah tabata rai tana yimata wani irin kallo tace "wai me yasa kika fiye gaggawa ne ummi, anya za ki rinka cimma nasara a kan abubuwa, idan kika dubi tsarin khalifa gaba daya da yadda kike ba abu ne mai sauki ba mallakar zuciyarsa sai anyi da gasken gaske. Ummi tace "to in banda abinki jiddah tawace hanya zan samu nasara idan nayi hakuri, kada kimanta fa shekaru hudu khalifa zaiyi a germany kafin yadawo kasar nan, yana chan Ina nan zan iya jan hankalinsa jiddah, dole xuciyata takaraya, ke bari in gaya miki wani abu daya da ban yi zaton zan gayawa wani ba, ina cikin gdan nan fa ina kokarin jan hankalinsa na ganshi da mace rungume a jikinsa a dakinsa, idan zan iya jan ra'ayinsa zai kawo mace gdan nan ina cikinsa? Jidda ta ja dogon tsaki tace "daman kina tsammanin ko khalifa a karan kansa yake sonki za ki rabashi da yammata ne, namiji irin khalifa ko baice yana son 'yanmata, za su yi tabinshi tun bai kula ba watarana sai ya kula, don hakama shawarar da zan ba ki itace idan kinyi nasarar mallakar khalifa to ki sanya hakuri mai yawa a zuciyarki akan 'yanmatan da za suyi ta bibiyar khalifa don ba namijin mace daya bane. Ummi tajinjina kai tace "tabdijam hakika zan girgiza kowa a kan khalifa ba zan hada miji da wata ba, ba zan yi tarayya da wata macen a dakin khalifa ba. Jiddah takyalkyale da dariya tace "ummi manya har khalifan ya zo hannu da za ki wannan cika bakin. Ta lumshe ido tace "kuma fa hakane maganar dakika fada ne naji kamar har na mallake shi na ji tsananin takaicin hadashi da wata da zanyi a sunan kishiya . ************* Malam musbahu yana cigaba da karfafa zuciyarsa ga kaunar fatima tare da tattalin farin cikinta sai dai ba ya samun hadin kanta sbda tsananin kunyarta, ba ta iya sakewa dashi hakan yasa tadaina sakewa a gidan duk abinda take idan yashigo sai taji kamar za ta nutse a kasa don kunya hakan na takura shi shima don ya fi son tasaki ranta auyi soyayyar da za su fahinci juna kafin lokacin auransu. Ranar laraba da safe inna ta tursasawa fatima kaiwa musbahu abincinsa a kokarin innar na ganin sun shaku ta fuskar soyayya kamar yadda tafahimci basu sake da junansu ba, fatima ba ta son shiga dakin musbahu sbda maganar soyayya da yake mata na daga mata hankali alhali bata saba ba. ********** Lafiya kalau khalifa yasauka a kasar germany inda zai zaman karatun likita ,har yanzu damuwar daya taho da ita daga nigeria yana makale a ransa ga kewar iyayansa tamkar bai taba tafiya ba sai a wannan lokacin, yana shirin shiga motar dazata kaishi masaukinsa kamar daga sama yaji an rike mai hannu, yajuyo dasauri yazu bawa yarinyar ido, Anisa? Yafada cikin shakku dan ba shi da tabbacin ko daidai yafada sunan. Tayi murmushi tace "amma na ji dadi daka iya kiyaye sunana. Yace "nikam mamaki nayi dana ganki a kasar nan yaushe kikazo? Tace "sai mun zauna zan ba ka labari yanzu muje naga masukinka ko za ka fara zuwa ganin na wa masaukin? Yace "ah ba komi inga waya ba sai mun tafi ba. ta langabe kai tace "kada ka sanyaya min jiki bayan na yi farin cikin ganinka kayi murnar ganina. Yace "hakika na yi farin cikin ganinki domin ina bukatar abokin debe kewa a wannan kasa da nazo. Tace"to kayi hakuri mutafi mana. Yace "to muje. Sashensa daban a gdan da zai zauna, falo guda daya da bedroom ba dai wani girma bane amma akwai kayatarwa, kitchen kamar na mace sbda tsaruwar da yayi shi kansa saida yayi sha'awar ace yanada matar aure wadda za tarika dafa masa abinci irin na mamansa, wadda yayi mugun sabo dashi, a zaman da yayi da mamansa bai da matsalar komi ta fuskar abinci duk abinda yakeso shi ake masa, duk yawonsa da gararinsa bai iya cin kowani abinci sai a gdansu sbda shi mutum ne mai kyama da kuma son cin abinci mai dadi duk dadin abinci bai iya ci sai a gdansu ko a halin yanzu yunwa sosai a cikinsa bai san yadda zai yi ba tunda bai iya girki ba ko ruwan tea bai iya dafawa ba, hakan yasa tunda ya zube akan gado bai kara motsawa ba dan ko takalmansa anisa ce tazare masa. Tana zaune daf dashi tace "khalifa bayan gajiya kana tre da damuwa kataimaka kagaya min. Ya lumshe ido yace "Anisa ba za ki iya magance min matsalata ba shi yasa nace kar ki biyoni, ba za ki ga walwala ta ba a wannan lokacin. Ta marairaice kamar za tai kuka tace "dan Allah kafada min Abbakar. Yace "Anisa yunwa nakeji kuma ba za ki iya dafa min irin abincin dazai gamsar dani ba. Ta bushe da dariya tace "Abbakar idan yau ban dafa maka abincin daya gamsar dakai ba to mata na rako duniya, kuma har yanzu bakasan wacece ni anisa ba, ko ka san cewa sbda na ji labarin kana matukar son abinci mai dadi na shiga fafutukan koyon girki ko ta ina? Ya fiddo ido yna kallonta, tamike tace banga tazama ba kafin kagama nazarin maganata bara in dafa ma abincin. Ido yabita dashi har ta fice yamaida idonsa kan rufin dakin. A wani party suka fara haduwa wanda wasu dalibai suka shiga sbda nishadi, a lkcn bata dade dafara xuwa mkarantar ba, tana zaune tare da kawarta nafisa, suna hira wasu samari suka tskoanesu har nafisa za tayi magana anisa tahanata tace "kyalesu dan mu kulasu ne zo mu bar gun. Za suci gaba da binsu shi kuma khalifa yana kallonsu ya aika a gaya wa wadannan samarin su shiga hankalinsu su kyale su anisa ko yasa a musu tsirara a gun, samarin wanda sakon yafito daga gareshi yasa sukayi nasu gurin, ya aika akira mai anisa. Mamaki yakamata jin ance wai wani ne yake kiransu kamar wasu 'ya'yansa taduvi dan aiken tace "kaje kace a za mu zo ba. .. Nafisa tayi saurin rufe mata baki tace kinsan waye Abbakar muhammad? zo muje kawai. Anisa tace "to me zai mana da har zai ce muzo? Idan wani abu yakeso garemu mai zai hana shi yazo da kansa? kai je kace bazamu zo ba. Dan aiken khalifa yace "idan kika kara furta kalma mara dadi akan maigidana zanje in gaya mai idan kuwa nagaya mai daga wannan rana kin daina farin ciki a wannan makarantar. Ga dukkan alamu ita kawarki ta san shi ke kuwa bakuwa ce shiyasa nayi miki uzuri. Anisa takara fusata sosai za tayi magana nafisa tarufe mata baki ta ja hannunta tace zo muje. Har anisa ta dage akan ba ta zuwa sai kuma taga bara taje taga abinda wannan mai gadarar yake takama dashi tabashi mamaki. Khalifa na zaune kan kujera tare da abokansa, Anisa da Nafisa sukazo gabansu, Nafisan ce tayi musu sallama ita kuwa anisan bakinta ne yayi nauyi duk abinda nayi niyyan fada masa ya gagara sai ido data bishi da shi. Yayi murmushi yanuna musu gun zama yace "kuzauna 'yammata. Bata san sanda tazauna ba, gayen ya gaji da haduwa ya yi mata ya burgeta anya kuwa ta taba ganin matashi mai kyaun wannan a rayuwarta? Tun daga wannan rana suke gaisuwar mutunci da shi da abokansa, zuciyar Anisa ko yaushe a cike yake da kuncin son khalifa batasan yadda za ayi tasamu soyayyar ta sa ba, hatta nafisa duk yadda suke ba sa boyewa juna sirrinsu amma ta kasa gaya mata . Lokacin dataji cieon so na neman hallakata ne ta sanar da nafisa halin datake ciki, tayi dariya tace "haba sister na san halin dakike ciki boye min din da kikayi ne yasa na nuna miki ban sani ba. Tace ni dai na ji ina mafita? Anisa kai tsaye zance ba za kisamu khalifa ba, ba za ki iya mallakarsa ba sai dai in Allah ya sa ravonki ne amma sai kinyi hkuri mai nisa kafin kicin ma nasara, kada kifito kigaya mai kina sonsa saidai kici gaba da hakurin bin wasu hanyoyi dan kija ra'ayinsa. Anisa taci gaba da binciken rayuwar khalifa daki daki me yakeso da wanda bai so, har a gdansu, abinda yatsorata ta shi ne mata dayake mu'amula da su sannan ba shi da niyyar aure. Lokacin daya kammala karatunsa na Bayero duka shekararta biyu a nata karatun, anan ne hankalinta yatashi sosai ganin bbu hanyar da zata kara ganinshi kuma tashiga binciken ina yasa gaba a rayuwarsa, aiki zai fara ko ci gabada karatu, bata samu cikakken byani ba sai da aka dade tana fama da azaban ciwon sonsa a zuciyarta, tadagawa mominta hankali akan sai an maidta kasar germany ta karsa karatunta acan, momin tadube ta cike da mamaki tace "ke kuwa sbda me? Kasancewar nisa ce diya tafari a gun mahaifiyarta kamar kawa da kawa haka suke bata iya boye mata duk wani sirrin daya shafeta ko meye shi, taciro wayarta tanuna mata hoton khalifa tare da bayyana mata halin datake ciki a kansa, tace "momi tsawon shekaru biyu zuciyata ta rayu ckin azabtacciyar soyayyar har wani lokaci inaji a raina kamar mutiwa zanyi idan ban mallakeshi ba, mom ba zan iya rayuwa bbu khalifa ba ke kadai ce za ki iya min wannan taimakon. Hnklin mmin yatashi sosai ta tausaya wa Anisa, ta jima tana kallonta sannan tayi ajiyar zuciya tace, "Anisa ba zan ga laifinki ba dan kin kamu da soyayyar wanda kikeso tunda ba mutum ne yake dorawa kansa so ba kuma zan yi iya kokarin inga burinki ya cika. Zan sa abanku yashirya maki zuwa germany kiriga khalifa zuwa, zanyi ta binciken tafiyar shi da saukar shi a kasan, inaso ki kasance a filin jirgin lkcn dazai sauka domin kibashi mamaki, dan zai sauka ckin kewar iyaye da abokansa Na gida tabbas sai ya yi farin ckin ganinki. Abu guda daya zan rokeki Anisa shi ne kitsare mutuncinki, kada kiyarda soyayyarsa tasa kibiye mishi ya lalata miki rayuwa. Ta gyara zama tace "mom ban taba kallon khalifa da wata manufa ba mara kyau burina shi ne muzama miji da mata, ba zan iya bata rawana da tsalle ba akan khalifa. Mom tayi murmushi tace "anisa duniya fadi gareta abinda kika sani shi kika sani wanda baki sani ba baki sani ba, na san mutumcin soyayya kuma ina darajata, ni ce mace ta uku da mahaifin ki ya aura kinsan da wannan ko? To ina mai tabbatar miki da cewa ni ce mace tafarko daya fara so a rayuwarsa". ries : A DAREN FARKO 11 anisa tafiddo ido tace "to momi me ya hana yafara auranki har sai da ya auri su hajiya da mama? Momi tayi murmushi tare da girgiza kai tace "Anisa tun ina 'yar shekara goma sha daya mahaifinki yake so na, so ba na wasa ba tun muna ganin d wasa yake har kowa ya amince so yake min na gas*iya,yadinga hidima dani, duk abinda yasami niyake ba mawa, hr na kammala secondary dina lokacin aurena ya zo knan ba na kula kowa. Lokacin daya tuntubi babana da mganar aurenmu lokacin na yi candy sai yace ydaka ta masa sai ya yi shawara da 'yan uwansa, hnklin abbanku yatshi yanuna min damuwarsa akan haka nace yayi hakuri na san babana bazai ba mu matsala ba. Ahe kuwa matsala na tare damu domin babana biris yayi har takai ga ya kira abbanki yace yadaina zuwa guna dan kuwa ya yi min miji,munga tashin hankali abban ki Ibrahim a wannan rana domin kuka da hawaye yadi? ga yi yana rokin abbana yayi hakuri yarufa mai asiri kada yacuce shi da chan ba a hana shi ba sai yanzun, ba afi sati ba babana yadaura min aure dawani d'an d'an uwansa wanda yace shi yzaba min a matsayin miji. Wannan abu yajefa abban*u cikin matsanancin tashin hnkli domin kuwa ba karamin so yake min ba kowa ya san da wannan. Hakan yasa yan unguwa akayi ta zagin babana ana cewa bai kyauta ba anci amanar ibrahim, wannan ne dalilin dayasa mahaifiyar ibrahim tayi fushi tazo har gida tana gayawa babana bakaken maganganu yace da ita ai ba maryam ce kadai diya mace a duniya ba, bai ba wa ibrahim diyarsa ba ai ba wani yahaifa masa ita ba, idan anyi hushi ta aurawa ibrahim mata biyu koma hudu a rana daya shi ne zai tabbatar ita mai zuciya ce. Ai kuwa abinda yafaru knan, hajiyar ibrahim ta nemo mai 'ya'yan aminanta biyu itace hajiya hauwa uwar gidan abbanku ta yanzu da hajiya hafsa dakike ce ma mama. Ibrahim yayi namijin kokarin ba wa mahaifiyarsa hadin kai dan kada yakunya ta ta a idon duniya ganin walakancin da akayi mai a kaina,ya amince da auran hauwa da hafsa wadanda aka daura auransu rana daya aka fara kai hauwagdan da hajiyar ta sa tagina mai daga bisani bayan sati daya aka kai hafsa ,yayin da ni kuma bayan wata daya da daurin aurena da Aminu aka kaini gdan iyaynsa dake bayan layinmu. Na yi kuka na yi bakin ciki mara misaltuwa sbda ko ido ba na sn in buda in ga Aminu. Sai daga baya zance yabayyana cewa mahaifin Aminu ne yake bin babana wasu kudade masu yawan gaske yabukaci yabashi abinsa ba shi dashi, mahaifin aminu yace "tunda lokacin damuka yi za kabiya ya yi kuma babu to sai dai kabaiwa Aliyu auran maryam in ba haka ba kuwa zaiyi kararshi ne kuma nan take dole yabiya sa kudinsa, yace wadannan kudi in dai yabada maryama to sune a matsayin kudin aure da kayan lefe, sadaki kawai zai biya a daura aure, hnklin babana yatashi sosai sbda ya san dai da kunya yahana ibrahim auran maryam lokaci daya yabawa Aminu bayan lokaci mai tsawo ibrahim yadeba yana hidima da maryam tabbas ya san sai duniya ta zageshi, yayi duk tunanin dazaiyi dan yasamu mafita bai samu ba, kudi kuma bai da hanyarsu, hakan yasa yarufe idonsa yana takaici yaba Aminu aurena, lokacin daya ga damuwar goggona ya yawaita ne yasa yagaya mata yadda akayi shi ne nikuma tagaya min. Hakan danaji yasa zuciyata tadan sosu tadamu na tausayawa babana domin ko yaushe tunanina shi ne yadda babana ke son ibrahim meyasa yahana shi aurena rana tsaka ,bayan babana mutumun kirki ne ba mutum ne mai kwadayin abun duniya ba. : Shekarata biyu a gdan Aminu kowatan bata ban taba yi ba, shi da mahaifiyarsa suka shiga min walakanci suna cewa ba na son Aminu shiyasa naki yarda in haihu, ni kam ina iya kokari na duk da ba son Aminu nake ba ina mai biyayyaya shikuma yana wahalar dani kasancewar ba wani mutumin kirki ne sosai ba halayyarsa ba masu kyau bane. Watarana ina kwance a dakina yace dani "in fita inje gdanmu ya sakeni ba zai iya cigaba da zama dani ba, ba ni da wani amfani sai inci inyi kashi, natafi gda na fadawa babana daya tuntubi mahaifin Aminu kan maganar sai yakama fada yana cewa kar a gaya mai zancen banza mana maryama ce tahura wa Aminu wuta sai ya saketa gar da yi masa gori cewa ita ba shi takeso ba kuma tunda an yi masa haka kudinsa dinnan dai sai an biyashi tunda baiga amfanin auran maryama ga aminu ba, babana yace bai isa ba tunda dai yakafa sharadi kuma anyi auran a bisa sharadin daya kafa zancen kudi kuwa babu shi sai dai in kara zaiyi. Momi tadan yi shiru tana kallon fuskar anisa wadda tazuba mata ido tana mamakin labarin da take ba ta tace,"to momi yaya akayi har kika auri babana? Momi tace "Anisa hakika abbanku ya san darajar soyayya kuma ya mutunta kaunar dake tsakanina dashi; ahaifin Aminu yayi karar babana yace sai ya biyashi kudinsa tunda dai diyarsa maryam ta ki zama da Aminu, kiri kiri alkalin nan yagoyi bayan mahaifin Aminu bayan ni da baba na mun bayyana a kotu yadda abubuwa suka kasance wai sai alkalin nan yace sai na kawo shaidar mutum daya kwakkwara wanda zai min shaidar cewa Aminu ne yasake ni da kansa ba ni nace yasakeni ba, nace banda shaida sai Allah dan shi ne masanin dukkan abubuwan dasuka faru,, alkali yace dole sai babana ya nemo kudin Aminu ya biyashi lamarin daya tayar da hnklin kowa a gdanmu har kuka sai da babana yayi, kwasam Allah mai iko bayan kwana biyu dayin hakan sai ga abbanku ibrahim ya zo gun babana yakawo mai kudin da sukafi wanda baban Aminu yake binsa, mamaki yakamashi da kunya yarasa abinda zai ce, Ibrahim yace karka damu baba ni fa kaunar dana kewa maryam Allah kadai yasan iyakarta, duk abinda yashafe ni ya shafeku, Allah ne bai kaddara itace matata tafarko ba shiyasa abubuwan dasuka faru suka faru. Babana yabiya baban Aminu kudinsa kuma yace bai yafe masa ba, ina kammala idda aka daura aurena da Ibrahim, ban cika shekara daya ba na haifeki a cikin shekarata ta uku a gidan nan na haifi kaninki mahmud, kuma a wannan shekarar ne Allah yadaukaka arzikin mahaifinku wanda izuwa yanzu shi da kansa bai san abinda ya mallaka ba. Har yanzu iyayena ba su da abin Kauna kamar ibrahim kamar yadda nima ban iya hada shi da kowa, abinda nakeso inkaiki gareshi guda daya ne Anisa mahaifinki dani kaina mun san martabar soyayya muna mutunta ta. Mahaifinki ya nuna min kaunar da ban taba jin wani da namiji dayai wa mace halacci irin wadda ya min ba ko da kuwa a labari, shi yasa ban wasa da duk abinda yasha fe shi. Duk da kasancewarsa adali a tsakanin matansa amma kowa ya san soyayyar dayake nunamin ba karama bace shiyasa hajiya da mama suka tsaneni to amma ba su da ikon komi akaina sbda sanin halayyarsa. Wlh Anisa ni kadai ce matar da zan tunkareshi da kowace irin bukata yayi min ko baida ra'ayi don hka zan umarce shi da ya shirya miki tfya xuwa kasar germany don ki karasa karatun ki a chan. Anisa ina rokon ki kiji tsoron Allah a wannan tafiya da zakiyi kada kija min bacin rai,duk rintsi duk wuya kada ki lalata rayuwarki idan ban gani ba Allah ya gani ki min alkawarin tsare mutuncin kanki. Anisa tace "mom na maki wannan alkawari insha Allahu. Kowa yayi mamakin batun tafiyar anisa har kasar germany da sunan karatu tun da babanta dai ba shi da wannan ra'ayin ko babban dansa da hajiya hauwa tafara haifa anan kasar yake karatunsa na jami'a hakan yasa aka dauki hassada aka daura akan anisa amma dan ita abin bai dameta ba cikar burinta ne kawai damuwarta har a ranar da za tabar gida nigeria zuwa jamus batun mominta guda daya ne. "Anisa kiji tsoron Allah kada ki zubar da mutuncin ki baki da takamar data wuce budurcinki a gun mijin da za ki aura duk abinda zai rudeki kiji tsoron Allah kada ki biye masa bbu inda zai kaiki face ga nadama wadda zai sa kiyi ta kunkan da ba ki da ranar dazaki daina, duk abinda d'a namiji zai aikata a rayuwarsa ado ne mace ce a cikin hadari da bakin ciki idan batayi taka tsan tsan da rayuwarta ba. A cikin jirgin anisa ta hada kanta da guiwa ne tana tunanin wadannan maganganun na mahaifiyarta wadanda suka tsaya mata a rai, hawaye suka dinga zuba a idonta wani na bin wani, taji tausayin kanta da iyayan ta jikinta yayi sanyi sosai batasan yadda rayuwarta za takasance a wannan kasa ba. *********** Jiddah zaria Babban magana wai namiji dasuna Hajara, anya kuwa Anisa za ta iya cika wannan alkawari na mahaifiyarta???? ni ma dai jiki na ya yi sanyi amma dai ga mai fili ga mai doki........ karku gaji dai kukasance kuna biye dani a baya ganin yadda za takaya.... Ni ce dai 'yar mutan zazzau. Hawwa umar. a.k.a jiddah zaria. A DAREN FARKO 12 Kamshin da khalifa yaji ya halarci hancinsa yasa yamike xaune yana kallon Anisa, tace "ga abincin nan tashi kaci kayi wanka kayi sallah. Ya fubi abincin cike da gamsuwa yace "amma fa nagode Anisa kin fara ragemin damuwata zauna kigaya min dalilin zuwanki garin nan. Tayi murmushi tace "karatu nazo yi nima, rakiya nayo wa wata kawata za tayi tafiya kamar daga sama na ganka. Yajinjina kai yace "na godewa Allah daya kawoki daidai lokacin da zama ya kamani a nan. Farin ciki ya mamaye zuciyarta ta fara jiyo kamshin nasara a cikin muradinta duk da cewa ta san akwai aiki ja a gabanta. ******** Ruwan sama akayi kamar da bakin kwarya tun safe har gab da za ayi sallar azahar sannan yadauke, garin kano yadauki sanyi mai dadi kasancewarba sanyin takurawa jikin bil'adama ba. fatima tagama shiryawa cikin atamfarta maroon mai adon ja da fari, ta yi mata kyau sosai tadauki littafanta za tafara karantawa inna tadubeta ta ce "Ajiye littafin nan za ki yi ki kaiwa hajiya maijidda wamcan man shanun na soyashi tun daren jiya naso akai mata. Ta dan bata rai tace "nikam inna ba na son shiga wannan godan. Inna tarike baki tace "me mutanan gdan suka yi miki mutane masu kirki da mutunci wai ke meyasa ba kya son mutane ne fatima? Tace "ba haka bane inna kin sani duk abinda mutum yakeyi ana kallonsa idan ina yawan zuwa gdan karshe ace kwadayi ne yake kaini. To a fada din mana "inna tafada a fusace sannan tadora da fadin "idan har za kibiyewa surutun mutane ba abinda za ki aikata a rayuwarki dan duk abinda ka aikata din mutane ba fasa magana za suyi ba. Fatima ta dakko hijjabinta tasa ta dauki bokitin man shanun tanufo gdan abba. Hannu bibbiyu mama ta amshe ta suna zaune ita da ummi a falo suna hira, ta tsuguna ta gayar dasu tamika mata bokiti tace "Gashi inji inna. Tace "Oh Allah sarki inna da hidima take na gode Allah saka da alheri zauna sai anjima kya tafi ke in kin shigo gidan nan sai kace ana korarki na rasa sanda za kisaba da mutane fatima. A haka ta dan zauna a darare sai kace akan kaya tazauna, ummi tadubi ta da fara'a tace "fatima kin iya kitso ko rannan naga na kan kanwarki Aysha tace ke kikayi mata yaushe zanzo ki min irinsa? Tace 'idan kin shirya yanzu ma sai in miki. Tace "yawwa kamar kin san kan yadameni da yawa ina kuiyar saloon, tadkko kibiya da mai da komi tace "xo mu shiga daki kimin ma yi hira ma. Mama tayi murmushi tace "Ayi hira ko gulma idan ba gulma ba me zai hana a yi kitson a nan falon sai an shiga daki. Ummi tace "mama wannan hiran ai ta sirri ce. Tace 'gulma dai knan. Fatima na mamakin jin dadin da ake a wannan gida ita kanta ummi ace an shirya mata kasaitaccen daki irin wannan, tfara mata kitso suna hira tana ba ta labarin makarantar ta wadda saura shekara daya ta kammala, ummi tace "fatima amma idan kin gama za kici gaba da karatunki ko? Tace "a'a aure za ayi min in barda ma inna ta so inyi candy ai da yanzu anyi bikina da malam musbahu. Ummi tace "ba dai malamin ajinmu na islammiyr yamma ba. Tace "shifa ai dan gidan mu ne. Ummi tasake kallon fatima tana rayawa a zuciyarta yaya za ayi yarinya tanada kyau na garari irin wannan takare gun wani malamin islamiyya.,kwata kwata fati ba ajin malam musbahu bace, domin kyaunta yasa wasu har ce mata suke beauty, dukda cewa ba ta da sakin jiki da mutane ba ta ayyanar da tsabar kyaunta ta fi zama da nikab a fuskarta amma dukda haka kallonta ake ana zuzuta kyaunta, sbda zahiri Allah yayi mata kyakyawar sura tadaukar hankali da ace fati irin wayayyun 'yan matan nan ne masu budaddan ido ba karamin kudin maza zataci ba sbda in dai batun kyau ake fati ta fi gaban kwatance abin sai wanda yagani, ita kanta ummi aduk sanda tadubi fatima ji take kamar takwace kyaunta, tabbas ace tanada kyaun fati khalifa bai isa yace ba ya sonta ba, hankalinta bai kara tashi da fati ba sai watarana dataje gdansu fatima ta isketa ba dan kwali ta fito daga wanka tana taje gashin kanta, ummi taga yadda bakin gashin nan ya kwanta lanban a bayan fatima yana daukar ido kamar irin yammatan indiyawan nan, ga kirar jikinta abin sha'awa irin wadda ake cewa coca cola shape, ita kanta ummi datake mace saida taji tanason fatima sbda kyaunta kyaunta yayi mata ga tadai yar talakawa ba wani kayan ado dazai fiddo da itatake samu ba hakanan ta ki tawayar da kanta ,duk da haka fati ta isa abar kallo, kyaunta gdan wani hamshakin maikudi inda za ta jiku da jin dadi lallai za ayi kallon mace anan. Bayan ta gama mata kitson ummi taja hannunta zuwa kan dressing mirror tarike kugu tana kallonta tace "fatima kinga acikin kayan kwalliyarmu mata babu nau'in kalar da babu anan na baki dama ki zabi duk abinda kikeso wanda za ki dinga kayatar da kanki dashi gun ado, don Allah fati ki sani jikinki domin inason kizamo wayayyar mace mai ado za ki zama abar kallo fati, Allah ya yi miki baiwar kyaun sura wadda duk wata diya mace za taso ta mallaki sura irin wannan, dan banga abinda kika rasa ba fatima. Fatima tace "Nagode ummi da kaunar da kike nuna min, sai dai ina son kiyi hakuri ba zan dauki komi ba anan dan idan nadauka narabaki da abinki ba zan yi amfani dasu ba. Ummi tagyada kai tace "fati na fahimci kyamar dukiyar nan gdan kike yi. Fatima tace "haba ummi kada kiyi min muguwar fahimta mana. Ta tareta dasauri tace "me zai hana in fadi haka ba muguwar fahimta bane gskiya nafada miki. Ta girgiza kai tace "kiyi hakuri ba haka bane. Tace "to in dai ba haka bane zan hada miki kayan kwallia dakaina dan Allah kidaure kidinga amfani dasu. Tayi dariya tace " to na ji ummi amma dai zan tunasar dake abu daya wanda kwalliya ana yinsu ne dan afita kinga dai ni babu inda nake zuwa in banda makaranta,kuma ba wasu maza ke zuwa guna ba kinga dai ba su da amfani a gareni. Ummi tace "to in banda abinki fatima shi malam musbahun ba ya da bukatar yaga kwalliyarki, gskiya kanki a duhu yake dayawa kibani hadin kai in wayar miki dashi kada kiyi aure a cikin wannan yanayin dukda kasancewar malam musbahu malami ne amma xa ku iya samun matsala acikin zaman auranku idan kika cigaba da tafiya a wannan tsarin na ki, namiji dakika ganshi ko wani iri ne yana bukatar matarsa tayi masa ado yana bukatar matarsa takasance wayayya mai iya lura da abubuwa na jan hankali, idan akace mazan suke waje kadai za ayiwa ado banda na mazajen aure hakika kwalliya bata biya kudin sabulu ba knan, mace in har ta amsa sunan mace to tattalin rayuwar mijin auranta take domin shi ne na ta, wata kila kina ganin misbahu malami ne kuma dan gdanku ne ba ya bukatar sai kin masa wata kwalliya ta jan ra'ayi, wannan kuskure ne idan ma ra'ayinki ne haka to kisauya domin misbahu namiji ne kamar kowa rayuwar da zakuyi ta aure tanada banbanci mai yawa da wadda kukayi a gida, dole sai kin ajiye wannan kunyar da kke fama da ita domin tuni na fahimci kunya itace tahana ki sakin ranki ki zama wayayyiya mace, idan nace wayewa ba ina nufin kizamo mara kunya ba a'a kizamo mai wayewa ta fuskar rayuwa, matukar baki bin wannan hanyar dana ke son doraki a kanta ba, za kisamu matsala ba za kiji dadin zaman auran ba. Fatima tayi shiru tana tunanin abinda ummi tafada mata, ummi taci gaba da fadin "kiyi nazari sosai za kiganoinda nasa gaba, kinada kyau fatima kyaunki kadai ya isa yamallaka miki da namiji to amma fa masu iya magana kan ce in kanada kyau ka kaara da wanka,, dan Allah kisaki ranki da misbahu kidinga tsala ado sosai kina tsayawa kuna hirar soyayya za kiga yana dada rudewa akanki, a tunanina babu wani abun Burgewa ga mace wanda yawuce mijinta na aure yayi ta sonta ya kasance kullum hankalinsa na kanta, matukar kuwa bata bi hanyoyin dazata rike shin ba ba zata samu yadda takeso ba daganan sai kiga anata samun matsalar rayuwar aure a dalilin a dalilin hakan za kiga aure ba ya danko kiyi taganin kananan zawarawa a gari, wadannan abubuwan da matan mu na hausa ba sa kulawa dasu suna taka muhimmiyar rawa gun lalacewar zamantakewar aure. ****** A DAREN FARKO 13 Har fatima tadawo gida tana tunanin maganganun ummi wadanda suka jefata a wasi wasi amma tana karfafa kanta dacewa gaskiya ne mamakinta shi ne yadda ummi tasan wadannan abubuwan ba tare da ta yi rayuwar auren ba ballantana tasan matsalolinsa da abubuwan da ke haifar da matsalolin, koda yake kallo daya inkayiwa ummi za kasan kanta a waye yake sosai ta fuskar rayuwa haka karance karancen datake na littafin hausa suna taimaka mata sosai nagano abubuwa da dama da suke ckin rayuwar auren. Fatima na zaune a dakin da suke kwana ne a wannanlokaci da bai wuce karfe takwas na dare ba sallar isha'i ta idar tadauko kayan da ummi tahada mata na kwalliya tana dada kallonsu har da kayan sawa materail ne kala biyu da mayafinsu da fashions da agogi ga turarruka har kala uku, kuma taroke ta idan gari yawaye tadawo daga makaranta tazo zata rakata saloon u gyara mata gashin ta, a dazun da wayo da wayo sai da ummi taja hankalin fatima takai la'asar a gdansu tana cusa mata maganganu na jan ra'ayi don dai ta samu ta aminta da maganganunta har sai da taci nasarar da fatin tasaki jikinta take ba ta labarin yadda shi kansa malam musbahu yake nacin son tadinga sakin jikinta suna hirar soyayya tadaina gudunsa, tace wani lokacin har tausayi yake bata idan yafaye mata magiyar tayi mai hirar soyayya ko kaka ne dan yaji sanyi a zuciyarsa, amma ina tsabar kunya yasa ba ta iyawa, ko hada ido ba ta yi dashi, ummi tace "kinji ko ? " Tace "wannan idan baki bar wannan halin ba idan anyi auran yagaji zai dinga kula wasu yammatan ko yadaina baki kulawar dakike bukata kema. Lokacin data dawo gida innarta rike baki tayi tace "Tabdijam kece kika yini yau a gdan hajiyar ? Tace "uhm ummi ce tatsareni da magana kinga kayan ma data ba ni. Inna taduba tayi godiya. Fatima ta san cewa ummi na kaunarta kawai don Allah, don haka tasaki jikinta da ita sosai tana kokarin kwatanta abinda take gaya mata, tadaina dari dari da ummin zama take suyi hira sosai tazamo tazamo kamar irin aminan nan dasuka jima da shakuwa da juna, ita kanta fatin ko dayaushe idan takalli irin alherin da ummi take mata da yadda tadamu da ita tana nuna mata tsantsar kauna sai ta dinga mamakin kaunar da take mata, yakasance ko yaushe ummi na gdansu fatima ko ita tana gdansu suna hira, malam musbahu yana matukar jin dadin kawancen fatima da ummi sbda ta samu cigaba mai yawan gaske a cikin rayuwar fatima, hakan yasa yake mutunta ummi tazamo abokiyar shawararsa kan abin da shafi fatima, duk abinda yataso ita yake fadawa. ,kuma ckin ikon Allah sai ta nusar da fatima hanyar data dace nan da nan abubuwa suka dawo daidai kunyar nan ta fati duktazama tarihi har tana iya caba ado tatsaya suyi hira sosai da malam musbahu. ******** Yadda Anisa tashiryawa khalifa abincin safe hka ta tsara mai na dare wanda yafi na safen dadi yana can yana baccinsa ya iske an shirya tebur sai kamshi mai dadi ke tashi tana zaune kan kujera tana kallon wani fim da ake haskawa ya dubeta yana mur. mushi yace "godiya nake ranki yadade. Tace "na fika farin ciki da yabawarka Abbakar dan haka ni yafi dacewa in yi godiya gareka bisa karbar bakunci na dakayi a gdan ka, idan ka kammala zan koma masauki na abokaina na karatu suna jirana yanzu muka gama waya dasu. Ya rausayar da kai har yanzu da murmushi a fuskarsa yace "bakiyi laifi ba idan kin tafi dole in barki ki tafi domin bansan zan sameki ba na hadu dake amma dai va zan ji dadin tafiyarki yau ba me zai hana ki daure ki tayani kwana. Ta lumshe ido tare da ajiyar zuciya takwantar da kanta tana kare mai kallo lokacin daya zauna yabude abincin yana fadin "A bisa ra'ayinki za ki kwana a hidan nan idan gari yawaye sai muje nima inga na ki masaukin, amma idan kinga da takura sai muje yanzu ba na son inyi abinda xan matsawa mutum. Bai jira abinda za tace ba yafara cin abincinsa, idanunta a lumshe taje tunanin abi ? da kwananta a gidan zai haifar, har yau idan sunyi waya da mominta rokon da take mata shi ne tarike mutuncin kanta kada tayarda wani ya yaudareta ya lalata mata kuka yaja mata abinda za tayi kukan da ba ranar karewa., ance idan mace da namiji suka kebenta a wuri daya su biyu na ukun su shaidan ne, soyayyat da takewa khalifa ita kanta har tsoro yake ba tazuciyar ta ta tsananta da ciwon so mai zafi da tsanani shin akwai abinda zai nema a gareta ta hanashi. Bayan ya kammala cin abincin ya wuce dakinsa ya zuba wasu kananan kaya da suka kama jikinsa kam kam sun mai kyau abin har ba a magana, kamshin turarensa ne yafara baibaye Anisa kafin yabayyana gareta, hawaye suka taru a ido? ta Allah ya taimaketa suka koma ba tare da sun zubo ba amma duk da haka idanuwan ta sunyi jawur zuciyarta ta kuntata tunda take rayuwa da ciwon sonsa dake hana zuciyarta sakat bata taba jin abinda taji yau yana mata yawo a zuciyarta ba, hakan ne yasa tamike dasauri tace "bari in dakko jakata muje in wa sisters di na bayani sai mudawo. Yanayin muryarta yakarantar dashi wasu abubuwan game da ita, ko da yake yana sane dacewa tana son shi duk wasu alamu ta nuna masa ya dai ki nuna mata ya fahimci inda tadosa ne sbda tausayin ta yakeji. Ganin bata fito ba yasa yazauna kan kujera kafarsa daya kan daya yana tuna watarana a b. u. k aboki? sa bukhari ke ce masa "khalifa kafito kanunawa yarinyar nan anisa ce ba ka ra'ayin ta don tadaina wahalar dakanta son da take maka ba kadan bane. Ya ja tsaki yace "wai ku mesa ba kwa rabuwa da gutsiri tsoma, ita anisan ce tace ma tana so na? Buhari yace "kai da Allah kar ka raina min wayo ka fi kowa sanin son da take maka idan kuma za ka iya ba ta soyayyarka to kabata fuskar da za ta bayyanar ma da abinda ke ranta. Yayi murmushi yace "Buhari tausayin anisa nakeji sosai a zuciyata, ban shirya batun aure ba ba ni da ra'ayinsa idan nayi soyayya da ita naravu da ita wahala za tasha gara tayi hakuri dani a yanxu akan ta shaku da soyayya ta a gaba ta rasa ni, shiyasa nake nuna mata kamar bansan abin da takeyi ba. Anisa ce takatse mai tunani lokacin data murda kofar dakin tafito rataye da yar madaidaiciyar jakarta tace "inaga ba sai mun fita ba na yi masu waya sun taho nan din yanzu. Yace "ba laifi. Suka zauna shir7 kowa tunanin dayake kara kaina a zuciyarsa, lokaci zuwa lokaci takan kalleshi tashare kwallan dake taruwa a idonta, ta kagu sisters dinta su zo tahuta anya za ta iya kwana a gda daya da khalifa? Namijin data kwallafa rai akansa take masa son da batayi tsammanin anawa wani d'a namiji ba, suka kirata a waya sukace ga su a kofar gdan tamike dasauri taje tashigo dasu. Fadilat da Ramat su ne abokan anisa wanda take ji dasu komi na su tare suke aiwatarwa gida daya suke zaune wanda yake kusa da makarantarsu, amincewar da iyayanta suke nuna mata yake tsoratata yasa take matukar kiyaye rayuwarta, Fadilat da ramat suna rayuwar dasuke so da samari? su yayin da ita ba ta da sakewa da mazan. Ita kanta anisan bata ji dadin irin tarbar da khalifan ya yi wa su Ramat ba, ta dai daure tagabatar dasu a gareshi sannam taya musu cewa za ta taya shi kwana ne, basu jima sosai ba sukace xa sukoma tabiyo su don yi musu rakiya, suna fitowa fadila datake ta fi ramat zafin kai ta hau ta da fada tace "dama haka Abbakar din yake kika gayyato mu gdansa? kina sane da cewa a rayuwata babu ab8nda natsana kamar walakanci, meye dalilin na nuna mana isgilanci haka? Tace "kuyi hakuri nima banji dadin abinda yyi mukun ba haka halinsa yake bai da son magana. Ramat tace "halinsa yake bai da som magana kuma to haka kike tsammanin za ki iya mallakarsa, gskia anisa jikina ya yi sanyi da yanayin khalifa dole ki sassautawa zuciyarki burin da kika ci akansa. Jikin anisa yayi sanyi tace "ina bukatar ku tayani da addu"a xuciyata ba wanda za taso bayan shi, fadila tayi tsaki tace "aikin banza wai dole sai kin rayu da khalifa? Suka tafi suka barta tsaye, ta jima a gun daga bisani takoma ckin gdan, a nan falom data bars&i ta tadda shi yana magana da iyayensa a waya har sai da barci ya dauketa, bayan ya gama da iyayansa yai tunanin ckin yammatansa wa zai kira tadebe masa kewa, yanajin wani iri ne a ransa zaman anisa a gdan ya taimaka masa amma hakanan yake jin tausayinta ba zai iya maidata abokiyar debe masa kewa ba yayin da kudirin datake dashi a kansa ba zai yiwu ba. Yakoma cikin daki yafidda kayan jikinsa yabar gajeran wando kawai yahaye gado sai kuma ummi tafado masa yayi murmushi yakira laila daya daga cikin yammatan na sa, wayarta a kashe, yaja tsaki yakashe wayar ya kama barci. ********* Posting a yan kwanakin nan sai hakuri a dalilin muna ta hidimar biki, duk yadda aka gani a hakura da hakan. A DAREN FARKO 14 GIDAN ainihin iyayan ummi yau hajiya saude tayi ma tsinke ta iske hajiya hauwan tana shirin fita tace "yanzu kuwa nake shirin kiranki a waya inji ko kina gida in biyo ki min rakiya. Saude tace "ai zuwa nyi inji labarin inda aka kwana da batun ummi da khalifa, wai shin har yanzu babu wani labari? Hauwa tace "uhm wani labari ne ban da na takaici saude? wannan yaron zai wahala mu cimma nasara kansa yana da jin kan tsiya. Saude tace "shi din banza, ke fa yadda uwarsa taraba mu da dan uwanmu haka za mu rabata da danta, ba za mu samu wannan damar ba har sai khalifa ya auri ummi. Hauwa tace "to tana can dai tana faman bautar girki a gdan idan yadawo ma san abin yi, yanzu kam sai hakuri tunda ba ya nan. Saude tace '"duk da haka bai dace muyi kasa a guiwa ba da safe ake kama fara idan mukayi sakaci wankin hula yakaimu dare bazamu samu yadda muke so ba. Hauwa tazauna gefen gado tace "to me za muyi yanzu? Tace "gun boka za muyi duk abinda yadace a yi a ja ra'ayin khalifa ga ummi idan ma ta kama muhana shi zaman jamus din gaba daya yadawo ya aureta ba matsala. Zuciyar hajiya hauwa ta karfafa sosai tace, "wannan shawara ce mai kyau tashi mune. A daidai wannan lokacin babbar aminiyar ummi wato jiddah tana wurin ummi ta je yimata sallama don lokacin tafiyarta london karatu ya yi. Suna zaune dakin ummi su biyu fatima tashigo sanye da doguwar rika baka after dress ta yi mata kyau sosai, malam musbahu ne yasayo mata da sukaje kaduna da malam, suka gaisa da jiddah. Ummi tace "kinyi kyau mutuniyar bari in yi miki hoto ,Allah yasa dai angon ya ganki na san zai yaba wannan kwalliyar. Tayi wal da ido tace "shi ne ma ya aiko ni da kwan zabi yace in kawowa hajiya sunje kauye da malam sukayo tsaraba, bari ma inje yana jira na anjima zan dawo insha Allahu. Ummi tace "muje kitchen in ba ki wani lemo dana hada hirar taku za tafi armashi idan kunayi kuna sha.. Fati tace "kai antina kina shagwaba mu dayawa. Tace "haka yadace. Bayan tafiyar fati tadawo daki gun jiddah tace "Allah ya sani ina matukar son yarinyar nan fatima sbda kyaunta da halayenta masu kyau. jiddah tace "ai na ga alama za a iya dawo da ita gidan nan idan tafiya tayi tafiya. Tace "ai da za ta dawo din ai da na ji dadi mama da abba ba su da matsalar komi gdansu gdan jama'a ne suna son suga mutane suna ta zuwa gdan nan. Ta ce "ai hakan yana da kyau shin kuna waya da khalifa? Tarike baki tace "wane ni? Tunda yatafi suke waya da iyayansa bai taba tambayata ba, gaskiyar magana jiddah ina ci gaba da zama a gdan nan ne dan inajin dadin zaman gdan a dalilin kirkin mama da abba amma ba na jin zan samu khalifa ya fi karfina. Jiddah tace "ni abinda yake hada ni dake saurin karaya har yanzu dasauran batu, idan da rai da rabo idan kikayi hakuri watarana za ki cimma nasara akan khalifa, kidaure kici gaba da zama a gdan nan a matsayin mai yakin neman zuciyar masoyinki idan kika ci gaba da kyautata masa zai iya auranki musamman dayake kin shiga zuciyar iyayansa duka biyun. Tace "toh Allah yasa inafa cigaba da addu'a na san bbu abinda yafi karfin Allah. Jiddah ta mike da niyyar tafiya ta ce "ina takaici da zanyi wannan tafiyar ni kadai ba tare da ke ba soyayyar khalifa ta nisanta ki da kowa. Suka fito suna ci gaba da tattauna maganar shawarar da bata wuce abinda yashafi khalifa ba daga karshe ummi tace "jiddah soyayyar khalifa tayi min yawa a zuciyata abin har tsoro yake ba ni ,ina ta kokarin ganin na fidda shi a zuciyata don in huta amma abin ya ki yiwuwa, ina jiyewa kaina abinda zan iya aikatawa akan kowa idan narasa shi, idan na rasa khalifa bai auri wata macen ba nasan zan iya hakura abu daya ne ba zan taba iya hakura akaiba shi ne khalifa ya auri wata macen, ina nufin idan zai zauna haka ba na ganin mace a tare dashi shike nan. Jiddah taja tsaki tace "ni wannan shirmen na ki ne ba na so, wadannan maganganu? ba za subaki khalif ko su hanaki shi ba. Tace "ni fa ki sani haka jidda ina gaya miki ne dan ki san abunda ke ckin zuciyata wannan shi ne abin tsoron. Bayan tafiyar jiddah gdansu fatima tanufa ta iskesu ita da musbahu a zaure suna hira, wani yaro yashigo da sallamarsa yace "wai wani a waje ya ce don Allah wadda tashigo yanzu tazo. Ta tsuke fuska tace "kai tafi kace ba za tazo ba. Malam musbahu yace "haba ummi bai dace kiyi haka ba mu maza ba ma son muga anawa yan uwanmu haka. Fatima tace "malam ko kaje mana kaji me ke tafe dashi. Kafin malam yadawo suka shige cikin gida innarsu fati ta je unguwa a tsakar ida suka zauna kan tabarma, fati ta bata rai tace "ummi duk abinda nayi kina bata rai akan banyi daidai ba meyasa ke nake ganin ba kya iya sauraron duk masu kaunarki? shin ke abunda kikeyi daidai ne? ko kuma dan komi ke ce kika iya;? Malam musbahu yashigo cike da fara'arsa yana fadin "don Allah ummi kizo kugaisa da mutumin nan na san shi mutumin kirki ne sosai. Tace "don Allah malam kasallame shi yatafi kace an yi min miji kun taba ganin na saurari wani? Yayi dan jim sannan yace "to ba zan matsa miki ba amma zan shawarce shi akan yanemi shawra a gun abbanku. Bayan fitarsa fatima ta ci gaba dayi mata kallon tuhuma ranta a bace take fadin "baki ba ni amsar tambaya ta ba. Ummi tayi murmushi tace "fati knan kin more mijinki ma ya mori mace duk abinda kikayi kyau yake maki batan ran ma da kikayi yanzu bakiga yadda kika kara kyau da haduwa ba. Fatima takara fusata tace "ni ba wannan na tambayeki ba dole sai kin ba ni amsa ta gaskiya bisa tambayar dana yi miki idan kuma ba haka ba nima na daina yin abinda ki ke umarta ta. Ummi tana dariya tace "idan kin kwantar da hankalinki ko baki bata rai ba zan fada miki komai. Ta mike zaune suna fuskantar juna tace "fatima a cikin rayuwa bbu abinda ba ya samun mutum wani yasamu yadda yakeso wani akasin haka, wanifarkonsa yana ckin jin dadi karshensa wahala, yayin da wani zai taso ne cikin wahala karshensa yasamu jin dadi, fatima ni kam bbu wanda zanso a rayuwata bayan mutum daya da zuciyata ke muradi. Waye wannan? Na san ko baki san khalifa a ido ba hotunan da kike gani a gdansu zai sa ki shaida shi idan kin gan shi a fili, khalifa shi ne mutumin da zuciyata ta rataya da soyayyarsa, wannan shi ne dalilin dayasa ba na kula kowa dalilina shi ne duk wanda na kula bata mai lkaci zanyi domin zuciyata ba za ta so shi ba, me ye amfanin in yaudari mutum in nuna amincewa na gare shi alhali zuciyata tana tare da son wani, in dai ba yaudarar mutum zanyi ba to gwara in kyaleshi bbu wanda zan mallakawa zuciyata bayan shi, bbu wani da namiji da zai samu farin ciki a tare dani sai shi domin shi ne nake da kwarin guiwa dazan farantawa zuciya ko ina so ko ba na so sbda karfin kaunar danake masa ba mai misaltuwa bace, son danake masa ba zai bari in yi abinda zan bata masa rai ba, wannan shi ne dalilin dayasa nake ta burin ace shi na aura don in samarwa kaina farin ciki da kwanciyar hnkali a auran, kuma insamu tsira a gaban Allah idan nayi mai biyayya, fatima ina zaton wannan shi ne dalilin dayasa ake ba ma'aurata daman zabar wadanda suke so yayin neman aure, wanda zuciyar mutum ta aminta tana so shi take iya bi. Fatima tace "toh ummi an yi maganar auranku ne da khalifan kan tafiyarsa ? Tayi murmushi "fatima in banda khalifan iyayansa ma basu san ina masa wannan son ba, ya gargade ni akan kar in sanar da iyayansa ballantana a matsa masa kan ya aureni, khalifa ba ya so na ni ce dai zuciyata ba ta iya hakuri dashi. Fatima ta girgiza kai"anya kuwa za ki ce kai tsaye bai son ki ummi ? shin meye abin ki a tare dake, ko halayyarki ta arziki ta sa mutum yaso ki. Tace "Allah sarki fatima ke ce kime ganin haka, ai ita soyayya ba ruwanta da kirki ko rashinta, idan kana son mutum to kana sonsa idan ba ka so kuma ba za ka so shin ba koda ya fi kowa kirki. Fatima tace "to yanzu meye abinyi ummi ni bar na ji na tsani khalifan sbda rashin tausayin daya nuna miki, bai dace ka watsawa wanda yake sonka kasa a ido ba ya dace yatausaya miki, ni kam ina bakin cikin wannan damuwa ta ki inama inada halin taimakonki wlh da sai inda karfina yakare. Ummi tace "fatima idan kika biyewa damuwata za kiyi tazama cikin damuwa ne domin kuwa damuwa ba ta kare mini don lokacin dana fara son khalifa nake kuka nake zama a cikin damuwar da har sai da nasaba da ita, inata kokarin raba kaina da soyayyarsa don in huta amma ko yaushe soyayyarsa karuwa take a zuciyata abin ko sauki ba ya yi, tunda har aka kai wannan lokacin khalifa bai waiwayeni ba ba zai tausaya min ta fuskar soyayya ba kuma dagaske yake bai sona, ban isa in tursasawa khalifa ya aureni ba dole knan in hakura da auransa, amma ba zan iya hakuri dashi ba, ba zan auri ko wanne namijj ba ba zan hakura da khalifa ba. ******** Khalifa ya fara karatu mai zafi a kasar germany cike da zuciya mai karfi da cikawa mahaifinsa burinsa na ganin ya zamo cikakken likita dan yataimaki al"umman musulmai, Anisa tana tre dashi a gdansa ta zamo tamkar kukunsa itace abincinsa na safe da yamma a bisa ka'idarsa na cin abinci guda biyu kamar yadda ya tsarawa kansa, ko kusa Anisa batayi niyyan zaman gdan khalifa ba illa soyayya data rinjayi zuciyarta wadda ba ta barinta tayi tasiri a tare dashi, duk abinda yace mata dashi take amfani, yana matukar gamsuwa da nau'ikan abincin da take shirya masa kuma yana yaba mata tare da nuna mata jin dadinsa, lamarin dayayi mata dabaibayi knan take jin cewa data sabawa dr. khalifa gara ita ta matsawa kanta, babbar abin mamakin shi ne duk irin yadda ake neman soyayar mace ga da namiji zuciyar anisa ta gama nisan kiwo a ckin son khalifa amma a takure take da zaman gdan na sa sbda bbu abunda yake hadata dashi sai hirar duniya ba batun soyayya, idan gari yawaye tagama masa abin karyawa zai fita zuwa makaranta itama za taje ta ta, idan tadawo sai tayi abincin yamma, in dare yayi zai shirya ya dau ado yafice yawon zaga gari yayin dazai barta a gida kamar wata yar jiran gdansa, sai ya gama gararin ta zai dawo yabarta a falo yashige dakinsa, anan take kwana, wani lokacin tanaji zaiyi ta hira da yammatansa taci kukanta tagaji tahakura, idan tayi yunkurin barin gdan sai taga wata dai sabuwar damuwa ce za ta hada kanta da ita idan ba ta ganinsa. Yau ta tashi da kasala zuciyarta bbu dadi tahada abincin safen kamar yadda tasaba tashiga falon fuskarta bbu walwala, dr. khalifa na zaune teburin cin abinci bai fara cin abincin ba magana yake a waya tazauna tana mai kallo, a kullum shi me kyau ne amma kyaun dayayi yau na daban ne, wani irin abu taji ya kara turnike mata zuciya, idanuwanta suka kada jajur tazauna kan kujera taci gaba da kallonsa yanata hirarsa a waya cike da nishadi abubuwan dayake fada suka cigaba dasa zuciyarta a wani yanayi tadinga jin cewa meye amfani zamanta a gdan khalifa kullum ranta na baci, bata san inda tadosa ba, ya kamata tayiwa kanta fada. Bayan ya kashe wayar ya kawo ganinsa gareta yace "ya akai sister an tashi lfya ko,? Wani irin kallo tayi masa wanda bai taba gani ba tare da ita yataso zuwa gabanta yatsaya hannayensa zube ckin aljihun wandonsa yana kayataccen murmushin nan na sa mai kayatar da zuciyarta amma yau takaici ne yakara rufeta, hawaye suka taru a idonta tai sauri tashige daki. Khalifa yatsaya shiru yana kallon kofar dakin nata cike da mamakinta, ko dayake bai kamata hakan yazamo abun mamaki ba gareshi don yanada tabbacin son da Anisa ke masa ne yasa tayi shahadar zama a gdansa tare da sadaukar da kanta gun hidimar dafa abinci da gyara mai gida, hatta gadonsa ita ke gyarawa za tawanke mai toilet tagyara mai kayan sawar sa da komi na sa, in banda ya dage akan bai so tai masa wanki da gugar kayansa da tuni ita ke wankewa don har ta fara ya yi mata jan ido yace ba zai yiwu ba ayyuka za suyi mata yawa, ita ba lada zai biyata ba ballantana yadinga biyanta kudi ,damuwarsa itace bai san dawani ido zai dubeta ba ranar data gaji ta bayyana mai batun soyayya da bakinta tare da bukatar aure, alherinta yanada yawa a gareshi. Bai jima da fara zuwa makaranta ba yasamu aboki guda daya mai suna Faisal wanda yafito daga gda Nigeria jihar kaduna, Faisal tantirin matashi ne mai budaddan ido yadda khalifa ke da farin jinin yammata haka faisal yayi fice a wannan fannin, sa'ar da akayi shine faisal na da kokarin karatu, wannan shi ne dalilin dayasa khalifa yaji dadin abota dashi bayan haka faisal ba bako bane a kasar germany ya saba zuwa kuma yanada yammata da yawa, tun da suka fara abota khali:a yasaki ransa sosai ko yaushe suna tare sai lokacin barci suke rabuwa anan fa 'yammata suka fara kawo kansu ga khalifa, son karatu dayake yasa bai son su shiga jikinsa sosai don kada su shagaltar dashi. A yammacin jiya bayan sun kammala da makaranta wata budurwar khalifa mai suna shukura dasuke cewa 'shu baby'ta nace akan sai ta biyoshi gdansa yau dai ta tayashi kwana tace in kuma bai sonta yafito yagaya mata, yace "nikam ba na bukatar kwananki a gidana kiyi hakuri. Tace "ni na rasa dalilin dayasa kake min haka ko dai matar aure gareka a gdan. Faisal ya ja tsaki yace "ke ce kika kwallafa ranki kan wannan wahallaln ina mamakin dabi'unka khalifa har yaushe kanada matsayi irin wannan a rayuwa za ka takura kanka. Khalifa yace "faisal na fi shu baby bukatar ta a gidana ina kaucewa hakan ne sbda Anisa. "Anisa ? Faisal yafadi ckin mamaki. Ya amsa mai da fadin "Anisa mana, anisa ta cancanta in kaucewa abinda zai bata mata rai tana hidima dani sosai. Faisal yace "ka ga tunda ba ka iya debe kewar rayuwa da ita kasallameta daga gdan mana kadauki yaron gda wanda za ya dinga maka duk hidimar da Anisa ke maka tunda ba kudin dazaka biya karasa ba, yaya za ayi kazauna kana shakkar sakewa a gdan ka sbda Anisa, gskiya kasauya tunani. Tausayin anisa yakeji sosai a ransa shi kansa yana bukatar mai debe me kewa a gidan ba zai yiwu yadinga kwana shi kadai a gado ba bayan yanada ikon yin hakan. Yayi ajiyar zuciya yamike da niyyar yaci abincinsa yabar gdan, sai yakasa yanufi dakin data shiga yabude tana kwance rub da ciki bisa gado tana kuka, yahaye gadon yakwanta kusa da ita yana shafa bayanta da fuskar ta cikin muryar nan tasa mai taushi da kayatar da zuciya yace da ita "bansan dalilin wannan kukan naki ba Anisa in dai ina da matsayi a gunki na hadaki da Allah ki bayyana min damuwarki. Tabude idonta zuciyarta a karaye tace "Abbakar ba za ka iya min maganin damuwata ba da za ka iya da bamu kawo wannan lokacin cikin wannan yanayi ba. Yace 'haba anisa Allah musuru gareni da zan san damuwarki har in magance miki ita alhali baki sanar dani damuwar ta ki ba. Tamike zaune tana goge hawayen dasuka cigaba da zubo mata tace "Abbakar meye dalilin zamana a gdan nan? Ya amsa "kauna. Me yasa kace kauna? Ya amsa "Na san babu abinda zaisa ka zauna da mutumin da ba ka kauna, dan haka kaunar da kike min ce tasa kika zauna tare dani. Bayan wannan za ka iya rantse min da Allah akan cewa bakasan wani abu a zuciyata ba game da kai. Yace "to in banda abinki anisa akwai wanda yasan abinda ke cikin zuciya bayan Allah? Ya matso jikinta sosai yakamata yarungume yayi mata kiss yace "kidaina sawa zuciyarki komi game dani kidaina bari ranki yana baci duk abinda kike bukata zan miki. Ya yi hakan ne dan yahanata fadin abinda yasan tana daf da fadinsa, yashga shashafa mata bayanta da cinyoyinta nan da nan jikinta yayi sanyi tadinga jin wani irin abu na yi mata yawo a jiki, so ya yiso a zuciyarta kallon kyakyawar fuskar khalifa ya hanata ta hanashi aiwatar da abinda yake mata alhali nasihohin mominta na ta kai kawo a zuciyarta, zuwa can khalifa yadinga fidda numfashi dasauri dasauri yana cakudata yadda yaso, abin yafara ba ta tsoro tayi kokarin janye jikinta daga na sa yayi wuf yakamota yana fadin "kar ki gujeni a wannan lokacin ke ce kika ja ra'ayina ba zan iya hakura dake ba ki daure kibani hadin kai zan maki maki duk abinda kikeso. Ya kwantar da ita bisa gado yadanneta da faffadan kirjinsa yarufe ta ruf yana mata kiss, gabadaya hankalinta ya tashi sosai sai jikinta yake rawa, a haka dai khalifa yasan ta diya mace yayi mamakin yadda yasanta a matsayin sabuwar budurwa wadda bata taba sanin da namiji ba, dama "yammata suna kaiwa wannan lokacin da budurcin su? A DAREN FARKO 15 yamike yayi wanka yafito falo cike da nishadi yaci abincinsa bai koma dakin ba yafita abin da yasawa ransa shi ne ashe yanada abar hutawa a gda tun farko yaki ba ta kai . Anisa tayi kuka tayi kuka har taba uku lada, zazabi da ciwon kai suka rufeta takasa tashi, takira number ramat tace "ke ni fa ba zanzo gdan wannan abin jin kan tsiyar ba ke dai da kike mayen sonsa kikaga za ki iya zaman gidansa sai kiyi tayi, ni dai ina ba ki shawarar kidauke ranki akan khalifa ba za ki iya mallakarsa ba ke ko kin mallake shi wahala za kisha dan namiji ne me garari da tsada. Anisa ta jefar da wayar taci gaba da kuka sam dawani ido zata dubi mominta ko da ta san cewa ba za tasan abinda yafaru ba abin takaici ne ace ta karya alkawarin datayi wa momin ta ta na cewa za ta rike mutuncin kanta, shin ina makomarta a gun khalifa, shin meye amfanin zuwanta germany ne? **** Bayan tafiyar jiddah london karatu abunda su hajiya sude suka maida kai shi ne yawon gdajen malamai da bokaye wai su burinsu khalifa yaso ummi ko ta halin kaka, mafi yawan malamai na bayyana musu cewa khalifa fitinannen yaro ne mai jarabar kwadayin mace amma bbu batun aure ko kadan a zuciyarsa, haka shi mutum ne da ba ya son raini da ace yanada sausaucin ra'ayi zai iya kula ummi da sunan soyayya tunda da sha'awa mai zafi amma a bisa la'akari da yadda yanayinsa yake bazai iya baiwa ummi fuskar soyyaya ba dan gudun kada tarai na shi tunda yana ganin ta ne a karamar kanwarsa, malamin daya fara shaida musu wannan batu ya tabbatar musu da cewa wannan shi ne hakikanin ra'ayin dr. khalifa wanda yake tafiya akai, hajiya hauwa tace,"to malam ba za a iya tankwasa zuciyarsa yasota ba ko ya ki ko ya so, malam mahaifin yaron nan dan uwanmu ne matarsa ta asirce shi bai jin maganar kowa sai tata duk wannan uwar dukiyar daya tara idan bbu shi ita da khalifa za su mallaketa. Malam yayi murmushi yace "akwai hanyar hakan amma ba zai yiwu ba har sai ya dawo kasar nan dazama sbda za muyi amfani da kasar daya taka ne muyi masa aikin da mukewa lakani da bita zai zai, zaita bin ummi sai yadda tayi dashi, anan ne suka dan yi murmushi hnkalinsu yafara kwanciya. "Yace suyi hakuri nasara sai a hankali da hakuri ake samunta ba da gaggawa ba,. **** Fatima da jiddah daga can london din ke damun ummi akan tadinga neman khalifa a waya da sunan za ta gaida shi bai dace tabar damuwa a cikin ranta haka ba, suna ba ta wannan shawarar ne saboda ganin yadda hnkalinta ke tashi musanman fatima da ke kusa da ita tana ganin yadda ummi ke kuka akan rashin khalifa tun tana boye wa har kukanta ya bayyana ita kanta mama ta fara gane damuwar da ummi take ciki, dukda cewa ba a san abinda ke damunta ba idan ta tambayeta sai tace bakomi, mama ba ta son takurawa ummi sbda tanajin dadin zama da ita. Rannan dai da fatima ta matsa mata akan sai ta kira khalifa a waya tayi murmushi tace "fati idan yabamu amsar da za ta daga mana hankali fa? da muguwar rawa ai gwamma kin tashi, fatima tagirgiza kai tace "wannan hujjar ta ki ba za tasa mi ta zama ckin damuwa ba, idan kin ce da muguwar rawa gwamma kin tashi ai kuma kar ki manta ance a rashin kira karen bebe ya bata kuma a rashin tayi akan bar arha, ummi tajawo wayarta ba tare da ta ce komi ba ganemo nomban khalifa takira ckin sa'a tashiga. Bata jima ba tana ringing yadaga cikin kasaitacciyar muryarsa yai sallama gaban ummi na faduwa tasa hands free dan fatima taji da kunnanta. Ta gayar dashi ya amsa tace "ka gane me magana yayana? Yace "na gane mana ba ummi bace. Tace "ni ce kira nayi dan mu gaisa na ga tun tfyarka kana tmbayar kowa a gdan nan amma ban da ni, bansan laifin da nai maka ba, . Yayi dan jim kamar ba zai amsa ba, daga bisani yace "ina cewa kowa lafiya? idan nace kowa lafiya kina ciki. Ta ce "shi knan nagode yaya karatu.? Ya amsa "karatu Alhamdulillahi. Za takara magana taji dif ya kashe wayar tayi murmushin takaici tace "kin ji ko? Wadannan abubuwan ne suka sa ba na son bugawa khalifa waya, ba wai dan ba na jmson jin muryarsa ba kullum farin cikina ko da a waya ne in dinga hira da khalifa ina jin muryarsa amma ba zan samu wannan hadin kan daga gareshi ba, sbda ba ya bukatar soyayya dani. Hawayen dasuka zubo mata yahana. ta cigaba da magana, hankalin fatima ya kartashi taji tsanar khalifa ya kara kamata, wai wani irin mara imani ne wannan tasa dankwalin ta tana sharewa ummi hawaye, tace "ki yi hakuri insha Allahu khalifa zai zamo mallakinki. Ta ina? Akwai wanda zai yiwa khalifa auren dole? idan har kuwa ba auren dole za a yi masa ba to ba zan same shi ba don baya sona, rokon dazan miki daya neduk yadda mama za tayi miki akan ki gaya mata abinda yake damuna kada kisake tasan cewa khalifa nake so. Fatima tayi mata wani irin kallo tace "matsalarki knan ummi banga ta inda za a samu mafita ba ana wannan boye boyen. A DAREN FARKO 16 .Sai da dare yayi sosai khalifa khalifa yadawo gdan tare da shu baby yau ta yi masa nacin da dole ya amincewa kwananta. agdansa, ahi kansa bai san dalilin dayake gudun kawo mace gdansa ba sbda anisa, tun daga nau'in kayan jkin shu baby za kasan lalacewar ya yi yawa, a ranta tace "tabbas yau sai na ga abunda khalifa yake tsoro, tabi bayansa zuwa ciki, anisa na kwance a bisa kujera a fali tana kallon wani film a wayarta, duk zamanta a gdan bata taba ganin khalifa ya zo da mace ba duk da ta san yana tare dasu sai fa yau, suka dubi kowa ita da shu baby kowacce tashaki wani masifaffan kishi a zuciyarta, anisa ta maida kanta tana kallonsu suka wuce dakinsa, bby tace "sbda wannan figigiyar yarinyar dama kake kin kawo ni gdanka? Yamata wani irin kallo yace "kiyi abinda ke gabanki shuu wannan kanwata ce ba na son.... Bai cigaba da maganar ba yashige toilet yayi wanka yayi alwala, bayan ya idar da sallar dake kansa yaleka falon yace "anisa wannan da kika gani abokiyar karatuna ce ki kawo mana abinci daki kuma ina so ki gaisheta. Yawan kukanta yana ba shi haushi ganin ta fara share kwalla yasa ya koma cikin daki, tunanin da anisan tayi shi ne wai ita wacece ne a gun dr. khalifa da har zai gujewa bacin ranta, tunda takawo kanta zama a gdansa dole tahakura da duk abinda za taji ko tagani, a sanyaye tamike tashirya abinci a tray tashiga dakin da sallama tatsuguna ta gaisar da baby tafita, kallon daya bita dashi yakara baiwa baby haushi taja tsaki tabude abincin taxuba a plate tafara ci, dandanon abincin ya burgeta ga takaici da kishin wadda tadafa, shima yazuba na sa yana ci yana fadin "kai aniaa ta iya girki mijin ta ya mori mace. Sun kwana suna morar junansu ta hanyoyi daban daban wadanda suka kware a kansu ko wannenau ba baya bane a wannan harkar, sun gamsu iya gamsuwa hakan yasa kowanne zuciyarsa wasai ba damuwa, khalifa na son yayi bacci sosai amma yunwa ta hana shi baccin dole yafito falo sai dai tebur wayam yaleka kicin ba abinci bbu anisa yadawo dakinta ya iske doguwar takarda mike bisa gado tun kafin yakaranta ya san abinda ta kunsa yace"shikenan shukura ta ja min asarar mai dafa min abinci da kula da gdana. Salam. Abbakar ina maka ban kwana tare da fatan allah yasa kagama karatunka lafiya ka koma gda lfya, xamana a gdanka ya kare ba tare da na gaji da ganinka ba sai dai yin haka shi yafi mana ni da kai, na gode kwarai dagaske da masuakin daka ba ni a gdanka duk da cewa hakkana bai cimma ruwa ba na samun masauki a zuciyarka wanda shi ne makasudin zuwa na wannan kasar, amma dai na godewa Allah daya ba ni ikon aikata abinda natabbatar zai wahala ka manta dani har ka koma ga mahallincinka, ina rokaonka a duk sanda katuna dani kai min addu'ar alheri. khalifa na zo wannan kasa ne dan neman soyayyarka da take ta cin zuciyata tun daga ranar da idanuna suka fara ganinka na yi suk kokarin da zan iya na ganin na ja raayinka banyi nasara ba, tun daga gda nigeria har izuwa yanzu dana tabbatar ba zan same ka ba, daga karshe ina maka fatan dukkan alherin duniya dana lahira. Ni na san bbu namijin dazanso bayan kai, Anisa.... Iya abinda takardar takunsa knan, har gumi yaji yana keto masa sbda tsabar tausayin anisa, yadinga jin wani iri a ransa yana tunanin rayuwar dasukeyi wadda ba ta da wani amfani a garesu, idan suna gaban iyayansu sai su dinga nunawa su na kirki ne amma a bayan idon iyayan na su suna aikata abinda suka ga dama. Shin tsakanin iyaye da Allah wa ya fi dacewa aji tsoro, in har suna boyewa iyayansu halin dasuke cki ne don suna tsoronsu, Allah daya halicci mutum shi yafi dacewa a ji tsoro, kuma Allah yana kallon mutum a ko wani hali yake. Wannan nasiha da khalifa yaiwa kansa yasa yaji nan take komi ya fice mai daga rai ya tsani yan matan dayake tare dasu na holewa, yana bukatar yazamo natsatsen mutum wanda yake biyayya ga Allah da manzonsa, takaicin abubuwa da dama suka kamashi har yaji kyamar kansa da kansa yakeji, yamike jikinsa ba kwari yafito daga dakin yadawo dakinsa, ya isje shu bby har yanzu baccinta take cike da nishadi da kwanciyar hankali, yasa hannu yagirgizata dakarfi tabude ido tana fadin "bacci ke damuna,yace " ba na iya juriyar yunwa. Tace "ina yar aikin gdan nan? Yace "ba ta nan. Ba abinda shukra tatsana irin girki amma da yake khalifa ne haka tadaure tadafa ruwan tea da dankali da plantain, ba wani kwarewa tayi da girkin ba yunwa ce tasa kawai yaci. ***** A DAREN FARKO 17 Tun daga wannan lokaci rayuwar khalifa ta sauya gaba daya yadaina sauraror kowacce mace har da ita kanta shuu babyn, hatta fAisal ya watsar dashi sbda ya yi ya yi yaja hankalinsa don shima yadawo hanya tagari faisal ya yi masa wani irin kallo shekeke yace "kai kiwa meya sameka da za kace mudaina rayuwarmu, tajin dadi mu takura kanmu, ko mafarki kayi ka mutu an sa ka a wuta? Khalifa yace "ko kusa banyi wani mafarki ba na dai yi wa kaina fada ne dan na fuskanci gaskiya, na ga yakamata inja hankalinka kaima damu daina wannan rayuwar kafin ranar nadama tazo mana. ko wata amsar kirkifaisal bai ka ra bashi ba yamike yavarshi a gurin,hakan yasa khalifa ya janye jikinsa yakoma rayuwarsa shi kadai, yanemi masu dafa masa abinci da gyaran gida bai zuwa ko ina sai makaranta inya dawo yakan kulle kansa a dakinsa yayi ta nazarin abinda yake karantawa ko karatun alkur'ani mai girma wanda a baya ko bude shi ba ya yi sbda shagalta da rayuwa da ya ya mata dayayi, sai yake jin dadin rayuwarsa a haka hatta hotunan sa da nambobinsa ya goge, yayi ta karfafar zuciyarsa tare da neman gafarar Allah yana rokon Allah yataimake shi yaraba shi da wannan rayuwa. A haka a haka har Allah yataimake shi yakammala karatunsa yakawo shi inda ya fito da kyakyawan sakamako zuwa babban likitan mata a lkacin ya dada kasaita irin mazan nan ne da dole idan aka kallesu a kara sbda cikar zatinsu, kwarjini da ilimi, 'yammata sun yi sunyi suja ra'ayinsa kowacce tana fatan yasota amma ya ki bada kai, matar aurance har yanzu baiga wadda yagamsu yaji ta yi masa zai zauna da ita a matsayin matar aure ba, amma dai mace ta holewa ya yi alkawarin insha Allahu ya daina. Kafin ranar dawowarsa gida nigeria ya yi ta neman yadda za ayi yaga anisa ya rasata haka a kano bai san a ina zai ganta ba, yana yawan jin tausayin ta tare da yimata addu'a duk sanda yatuna ta. Tunda ya daura damarar tahowa gida damuwarsa itace yarinyar nan ummi ya san ta yi girma yanzu sosai ta kara wayo a baya ma ta iya budar baki tace tana son shi ballantana yanzu, bayan shi ba wani sakar mata fuska yakeyi ba ballantana ace shi kwata kwata ba ya da ra'ayin auran zumunci kuma ko yana dashi ma ummi bata cikin lissafinsa, cikin hikima yatambayi mamansa a waya ko an yiwa ummi aure, tace ai bata fidda da mijin ba ma ba ta sauraron kowa tun da tayi candy abban k7ma ya ce ya dace ta fidda mijin aure tunda mutane dayawa suna nunawa suna sonta in ya so taci gabada karatun a gdanta sai tace wai wanda takeso din ya yi doguwar tafiya idan yadawo za ta gabatar dashi. Wannan yafadarwa dr. khalifa gaba ya tabbatar yarinyar nan in baiyi da gaske ba zata zame masa matsala, har ranar dawowar tasa tunanin da yake fama dashi a xuciyarsa knan, yarinyar tashiga ran mamansa za a iya cewa sai ya aureta ko da yake bai da matsala da abbansa, maganar mamansa kuma da karfi a kansa baya son bata mata rai. ***** Karfe sha biyun rana fatima tagama shiryawa cikin wata blue din batik mai haske riga da zani ne amma kai kace siket ne sbda yadda kayan suka zauna a jikinta suka yi mata kyau abin har ba a magana, ita da kanta ta yi sha'awar kanta sbda kayan sun mata kyau, telan dayayi dinkin ya gwanance a fagen tsarawa mata dinki, ta jima tana gyara gashinta ya dau kyalli ta tsara daurin dankwalin sosai yadda yadace da adonta tazuba fashion da mayafin da suka dace da kayan, ummi ce ta bukaci taraka ta gdansu yau wato gdan iyayanta, fati bata fiye son xuwa gdansu ummi ba sbda jininsu bai haduwa da hajiyarsu ummin ba tare da ta san abinda tayiwa hajiyar ba, tana cin darajar diyarta ummi ne kawai sbda a halin yanzu ummi tanad\ matsayi lamba daya a zuciyar fatima ba ta da na biyu kowacce irin alfarma fatima za ta iya yi akan ummi. Innar tana zaune a kofar dakinta tace "inna sai mun dawo. Tace "adawo lafiya a gaida su. Tayi sallama a kofar dakin malam musbahu yadago yadubeta sai yayi saurin bude idonsa gaba daya yace "kai fatima wacce irin kwalliya ce wannan? kin ga yadda kikayi kyau kuwa? Ta lumshe kyawawan idanuwanta tana murmushi tace "ka manta na gaya maka za muje gdansu ummi. Yace "fatima gskiya in banda ummi na da matsayi mai girma a gareni ba zan iya barinki fita cikin wannan kwalliyar ba ban taba ganin ranar dakikayi kyau a ido irin wannan rana ba, fatima ina fatan Allah ya mallaka min ke. Tace "malam ai ya mallaka ma saura kadan yarage komi lokaci ne. Ganin zai tsaida ita da maganganu na santin kyaun datayi yasa tawayance tafice tabarshi yana hadiyar yawu kamar yabi ta yayi ta kallonta yau kyaun datayi masa daban ne. Bayan sun gaisa da mama tawuce dakin ummi ta iske ta tana shiryawa tace "mutuniyar kin hadu kayan nan sun yi miki kyau bana wasa ba. Fatima tace "kai wai ke ba kya gajiya da yaba kyau na ne? kullum sai kin cena yi kyau. Tayi dariya tace "to ai yabon gwani ya zama dole kinyi kyaun ne ba na gajiya da kallonki fatima, don Allah idan kinyi aure kada kidaina kwalliya kina matukar yin kyau da kwalliya dukda cewa idan ma bakiyi kwalliyar ba kyau kike yi ke kam Allah ya yi miki baiwa da yawa fatima. Tace "don Allah kiyi sauri mutafi kadda yamma tayi ba kya gajiya da surutu. A cikin mota suna tafiya ummi tana tuki fatima tana gefenta suna hira, tace "duk inda muka wuce fa sai an kalleki fatima ina kallon wani dazun da danja ta tsayar damu sajra kadan yabuga wa wani sbda kallonki, kidinga sa nikab kidaina daukar hankalin mutane. Ta dubeta tace "su sukaga za su iya ni bance wani yakalleni ba duk wanda wani abu yasame shi a dalilin kallona to shi yadauki alhakin kansa, muyi wata hirar. Tace "yawwa ai kuwa yau zan miki gagurumin albishir. Fatima tace "Allah sarki ai kuwa ni bani da wani labari da nake son ji mai faranta rai daya wuce in ga khalifa ya dawo ya amince da batun auranki da shi, wlh a wannan rana bansan farin ckin dazanyi ba, bansan yadda zan fassara wannan rana ba, gskiya anty ummi ina kaunar khalifa ne sbda son da kike mishi., duk da cewa na tsane shi tawani fannin sbda ba ya da tausayi. Ummi tayi dariya tace"ummi misali idan ke ce wani namijin yazo yana miki irin son danake wa khalifa za ki tausaya mai kiyarda da auran ko da ba kya sonsa ? Fatima tace "ummi ni mutum ce da ba na son ganin musulmi dan uwana a cikin damuwa in dai har na san yana zubda hawaye akan ciwon so na irin yadda kike zubda hawaye akan son khalifa zan tausaya mishi. Ummi ta girgiza kai "to albishirinki soyayya ba haka take ba. Tayi saurin katseta da fadin "ko ma yaya take ummi, khalifa ba shi da kirki, ba shi da tausayi, ya kamata mutum yaso mai sonsa, ya kamata mutum yakasance mai tausayi, nikam ba zan taba yiwa khalifa uzuri ba, duk da haka don Allah ina rokon idan khalifa yadawo kasar nan...... " Ummi tayi fakin a kofar gdansu tace "ki kwantar da hankalinki idan Allah ya kaimu gobe khalifa zai dawo kasar nan. Tadafe kirji tare da fiddo ido tace "don Allah dagaske kike ? Tace "kada kiyi shakkar hakan kizuba ido gobe za kiga dr. khalifa. Ita kantaa ummi bataji dadin samun hajiya saude a gdan ba sbda a fili suke nuna ba sa son fatima, yayin da ita kuwa ta tsani mutum ya nuna mata ba ya son fatima, tana matukar kaunar fatima a ranta. Fatima tatsuguna har kasa tagayar dasu su ka amsa kowacce fuska ba fara'a suka ja baki suka tsuke, wayar fatima tafara ringing tamike tayi sauri tafita ganin sunan malam musbahu, nan da nan hajiya saude tazubawa ummi harara tace "wai me kike nufi da yawo da wannan kodaddiyar yarinyar, duk inda za ki sai da ita za ki, sai da ita za kizo gdan nan ma kin dauko ta kina nufin duk abinda xa mu tattauna akai sai dai muyi a gabanta knan ba mu da wani sirri sai ta ji ? Hajiya hauwa tayi tsaki tace "ba ma wannan ne abin haushin ba saude sai yadda ummi take bata rai idan munce muna son magana da ita wai lallai sai duk abinda za a fada a fada a gaban fatima. Bayan ita fatimar idan sun tashi na su sirrin da ta ta uwar tafiya take gdansu suyi maganarsu ba a gaban ummin ba. Hajiya saude tace "ai ummi ba ta da wayo na rasa wacce irin soyayya takewa fatima kamar wadda ta asirceta, ga ta dai a haka kamar wata mai wayo nan kuwa ba komi a ranta sai wauta, mu da mukeso mu mallaki khalifa ta jawo wannan mai kama da aljanu ta jawota gdan kullum a gdan take yini idan yadawo ba kya jin ba zai ce fatima yake so ba ? Ummi tace "hajiya ya ya za ayi khalifa yace yana son fatima bayan an kusa bikinta, kwanaki kadan suka rage akaita gdan mijinta. Hajiya tace "wohoho ummi sai yaushe za ki fahimci halayyar mutane ne kidinga taka tsan tsan dasu, ki guji sharrin wanda kika taimaka wa, lokacin daka tausaya wa mutum kadakko shi daga rana kayi masa gata kadawo dashi inuwa bbu wanda zai tura cikin rana sai kai. Kin ga dai ke ce kika wayar da fatima da iya kwalliya da komi hatta magana ke kika koya mata amma babu wanda fatima za ta fara yiwa illah sai ke, tabbas idan bakiyi taka tsan tsan ba sai kin ce na gaya miki. A DAREN FARKO 18 Ummi takwana tana jujjuya maganganun su mahaifiyarta tana musanta duk abunda suka fada, ita kam ta yarda da fatima dari bisa dari bazata cutar da ita ba ta tattara duk maganganun na su ta watsar, ta fuskanci ranar dazata fuskanto ta wato ranar dawowar mutumin da ba tasan abinda sakamakon dawowar ta sa za tahaifar mata ba, farin ciki ko bakin ciki dole a daya biyu ne don haka a wannan daren bacci ta ragagge ne duk sanda tafarka sai ta ji gabanta ya fadi. Da sassafe takira fatima a waya tace don Allah tazo, tace lafiya, tace "banjin dadin jikina ne da zuciyata inason ki zo miyi hira. Fatima tace "don Allah ki kwantar da hankalinki khalifa fa ba wani bane illa mutum kamar kowa, meye na(aga hankalin ki akansa ? Tare da fatin suka shiga kitchen lokacin dataxo gdan wuraren karfe tara na safiya, ko da yaushe mama na yabawa yadda suke tsara girki da tebur a halin yanzu fatima dai da iyayanta sun zamo yan gda sosai a gdansu mama, suna yawan yi musu alheri na kayan abinci da sutura, wani lokacin mama dakanta take zuwa gun innar su fatima suyi hira sosai tanajin dadin shawarwarin datake ba ta akan rayuwa, sun shaku dayawa haka malam da abban khalifa sun zamo aminan juna ,idan kashiga gdan za kace fatima 'yar gdan ce sbda sakewar da takeyi, ci mai kyau da sha mai kyau ga kayan ado hakan yasa fatima tayi kyau ba na wasa ba kamar a taba jikinta jini yafito ta zamo kamar irin taurarin matan nan da suke zamowa ababan kallo a duk inda suka shiga, mafi yawan mazan dasuke shige da fice a gdansu mama idan sunga fatima sukan nace suna sonta, ba ta sauraron kowa duk kudin mutum da kasaitarsa, fatima ba ta bari yashiga ranta sbda alkawarin datayiwa babanta na auran malam musbahu yana tsaye a zuciyarta, bata taba wasa da maganar iyayanta ba koyaushe farin ciki ? su shi ne ranta. Gargadin karshe dasu hajia hauwa suka yiwa ummi shi ne "ta sallami fatima daga gdansu mama kafin khalifa yadawo kasar nan in ba haka ba tai kuka dakanta, ta jiye ma kanta abinda zaisa ta tayi kuka ba iyaka, bbu maganar data kama ummi aciki face ma dariya dasuka bata, magana daya tayi musu inda tace "su kwantar da hankalinsu da ace fatima za tayi soyayya da wani da tuni ta yi kafin ma khalifa yadawo sbda mazaje dayawa masu matsayi da takama da dukkan abinda da namiji yake takama dashi sunce suna sonta bata taba sauraron wani ba, ta rike maganar iyayanta dagaske ,tunda dai fatima bata yi soyayya da wani da namiji ba ba za tayi da khalifa ba. Hajiya saude tace "haka kike gani, ke mesa kikace ba kya son kowa sai khalifa ? Tace "wannan kuma daban soyayya gamon jini ce bai zamo dole don ina son wani yakasance wance itama shi tame so, masu iya magana ma kance abincin wani gubar wani. Gaba daya ummi ta san basu gamsu da hujjojinta ba, hankalinsu a tashe yake a bayan azahar in yau sai da hajiya takirata tana tmbayarta "in ce ko fatima ba ta gdan nan, na ji ance khalifa ya iso gda nigeria yana Lagos yana shirin isowa kano. Ummi tace "hajiya itace take tayani hada mai abinci, kin san yana son abinci mai dadi. Taja tsaki takashe wayar har tarasa yada za tayi da ummi. Karfe hudu na yamma dun abubuwan ci da na sha da sukaiwa khalifa sun hada a tebur, gida ya dau kamshi an gayare mai dakinsa fes yanata kamshi, bayan fati Ta idar da sallar la'asar tazura dogon hijjabin ta da nufin tafiya gda. Ummi ta fito daga wanka tace "zan tafi idan bakon ya isa ki ce muna masa sannu da zuwa. Ummi tace "ai kuwa baki isa ba dole ki tsaya kiga khalifa ya dace kigan shi. Tace "To ai na sanshi a hoto duk wanda ke shigowa gdan nan ko bai taba ganinsa a fili ba ya san shi a hoto ko ina a gdan nan fa hotonsa ne. Tace "ai na san da hakan nace kitsaya kigan shi duk yadda yake a hoto ya fi nan. Fatima tayi dariya tace "na san zaifi haka ummi idan za ki lura ai ban taba cewa kinyi laifi don kin wa dr. khalifa son da kike masa ba, ya cancanci a so shi dan ya hadu kowa yana son abu mai kyau, ba laifi bane don mace ta so mijinta yakasance mai kyau irin dr. khalifa sai dai bbu ,gskiya yi hakuri ba zan boye miki ba ba na farin ciki da gani ? khalifa, ina tayaki murnar dawowarsa ne kawai don shi ne farin ckin rayuwar ki ina son abinda zai faranta ranki ummi fiye da farin cikina, da ace dr. khalifa ya amince ya karbi soyayyarki da zan kasance cikin dumbin farin ciki mai yawan gaske amma duk da haka.... Ta katseta "fatima in dai dagaske kina son farin cikina tsaya dr. khalifa yazo don Allah. Fati bata sake magana ba tafidda hijjabinta tahaye gado takwanta, doguwar rigar shadda ce a jikinta ruwan powder, daga sama ta matseta yayin da tayi fadi daga kasa, babu kwalliya fuskarta gashin kanta ne dai ya sha gyara yakwanta a kafadarta ,a cikinsu babu wanda tasan khalifa ya shigo gdan. Ummi tace "don Allah fatima dako min ragowar furar dana rage a fridge. Fatima tafito a yadda take ko dankwali babu tashiga kitchen din falo tadakko furar kwatsam suka hada ido da dr. khalifa daya fito daga dakin mamansa, abbansa na biye dashi da manyan abokansa biyu dr. hafizu da dr. bashir, gaba daya taji kunya ya kamata cikin karfin halin gaske tarusuna tace "barka da isowa. Kallon da yayi mata yasa jikinta ya hau rawa ta wuce dasauri cikin dakin ummi tace "ke ai mutumin na ki sun shigo. Ummi tadafe kirji tace "don Allah ? furar da bata sha ba knan tazuba wata doguwar riga amma ita ta atamfa ce tayafa dankwalin a kanta ta fesa turare ta fito falon, tuni har sun haye tebur sun fara cin abinci. Fatima tabude dakin taleko don taga kallon da dr. khalifa zai yiwa ummi, ai kuwa fuskarsa baa fara'a yake amsa mata gaisuwa, su dr. hafiz ne masu zolayarta, shi kam gogar na ka ya yi dif abinci kawai yake durawa cikinsa. Wani irin takaici yakama fatima kamar taje tashake dr. khalifa tahuta an masa abinci ko yabawa ba zai yi ba yana walakanta wadda tayin. Wai wane irin mutum ne haka, nan da nan tayi takara tsanar sa, taja tsaki takoma kan kujera taharde . Ummi tashigo dakin harara tafara samu a idon fati tace "mi yiwa Allah ki daina son dr. khalifa ba shi da kirki. Ummi jikinta a sanyaye tazauna tayi tagumi tace "kiyi hakuri haka halayyarsa yake har in mutu ba zan daina sonsa ba, shi kadai nafara so a rayuwa rata, ba na iya hadashi da kowa ko bai aureni ba ba zan hakura dashi ba kitayani addu'a kawai. Fatima tafigi hijjabinta tace "to gaskiya ni ba zan iya ci gaba da zama a gdan nan ina ganin wanna abin haushin ba. Bata ji kiran da ummi ke mata ba tafice, sai dai abi ? takaicin dole tawuce ta falo gashi ba ta son kara ganin dr. khalifa yayin da shikuma dr. din kamar an ce yadago idonsa sai yadago karaf akan fatima za tafita, shi kansa bai fahimci muryarsa ba lokacin daya ke ce wa, "ke zo nan" Tayi dan jim, ba wata a falon lallai ta san da ita yakeyi, ya dace ta walakanta abin da ummi ke so, ranta a bace ta nufo inda suke ta tsuguna a gefe kanta na kasa tace "Ga ni . To bai san dalilin dayasa yakirata ba, ballantana yasan abinda zai gaya mata, ya samu kan shi da zuba mata ido shi dai bai san ta a gdan ba, Dr. hafiz ne yace "yammat don Allah ya sunanki ? Fatima kawai tace. Kafin wani cikin su yakara magana tamike dasauri tabar gdan. Dr. khalifa ya ajiye spoon din hannunsa yayi ajiyar zuciya yace "fatima. Kai wannan yarinya Allah ya hore mata kyau. Dr. bashir ya kyalkyale da dariya yace "likita knan bokan turai nan kuma kagano ance inda baki yakarkata nan yawu ke zuba. Fitowar mama takatse maganar tazauna suna hira, dr. khalifa yace "mama ina kuka samo fatima ? Tace "yarinyar nan makwabtan mu ne wanda kuka gaisa da babanta a waje dazun wanen malam musa. Ya basar da maganar kamar bai damu ba sukaci gaba da wata hirar. ***** Tun a daren masu zuwa yiwa dr. khalifa sannu dazuwa suka fara cika gdan yawanci tsoffin abokansa ne musamman na B. U. K da 'yan'uwa da abokan ckin dangi, wayoyin sa ma kashe wa yayi don yahuta, bai samu kansa ba sai sha biyun dare yahada ruwa mai zafi yai wanka yafesa turare yahaye gado, tunanin bai samu masauki a zuciyarsa ba yahau bacci sallar asuba ma sai da abbansa yatayar dashi suka nufi masallacin tare, ita kanta sallar idanunsa a rurrufe yayi ta suna dawowa yakoma wani sabon barcin. Yayin da ummi takwana ckin fargaba da kai komo a zuciyarta da tunanin tayaya za ayi dr. khalifa ya aureta ? zancen haduwa yanzu ba a magana, a tsaya bayyana tsarin kyau da Allah ya hore wa dr. khalifa bata baki ne, zuciyarta takara rudewa, sabuwar soyayyar data ninka ta bata ta karu akan ta da, ummi ta ji kanta tamkar tsawa tsawa yake mata. Da sassafe kamar yadda tasaba tashiga kitchen tafara hada abincin dr. khalifa na musamman, mama ta fita tace mata takira fatima a waya tazo tataya ta domin akwai wasu abokan dr. khalifa daza suyi breakfast tare nan da karfe takwas. An yi sa'a fati ba ta kashe waya, lokacin da ummi tabayyana mata bukatarta amsawa kawai tayi ba dan ranta ya so ba, hakanan take jin wani irin abu a zuciyarta jininta bai hadu da dr. khalifa ba, kallon da yayi mata ya firgita ta kwarai dagaske, ba ta da matsala da inna da babanta akan zuwa gdan mama, hijjabinta dogo har kasa tasaka tafito zuciyarta cike da sake saken abinda zai je ya xo. Aikin suke kowacce da abinda zuciyarta ke sakawa, karfe takwas komi yakammala a tebur suka debi na su sukayi dakin ummi. Kinga dr. khalifa ko fati ? Ummi tayi tmbayar tana kallon idon fatima wadda tagyada kai fuskarta a tsuke tace "eh na ganshi meye. " Ummi tasa gefen mayafinta tana sharar kwalla takasa cigaba da magana, zuciyar fati ta kuntata sosai yadda abincin yaki ciyuwa a gun ummi itama kasa ci tayi, tace "ummi ko zuwa zanyi in rokeshi yasoki. Tace "karki yi haka ya gargade ni akan kada in fadama cewa ina son shi, dole in kiyaye dokarsa in dai inason in zauna lfya. Fatima tace "to yanzu haka zamuyi ta zaman damuwa ? Ummi tace "damuwa ta kam ba zata gushe ba amma na ci alwashin ba zan bar dr. khalifa ba ba zan yarda in rasa shi wata tasame shi ba. Tunda ummi take irin wadannan kalaman jinta kawai fati take ta san me za ta iya ? hakuri ne yazame mata dole in batayi ba tayi tashan wahala idan so cuta ne hakuri kuma magani ne. ***** A wannan rana malam musa mahaifin su fatima yafidda bayanin cewa sati biyu rak za ayi bikin fatin da musbahu akai tagdansa, har inna tace "malam bai yi wuri ba har yaushe aka gama shiri. Yace "shi kam wannan lokaci yasanya kuma ba zai daga ba, fatima na dawowa gda malam musbahu yatare ta da zancen yana cikin farin ciki mai yawa, itama ta nuna gamsuwarta tare da fatan alheri garesu baki daya, yatambayeta abinda za tayi da kawayenta na shagalin biki tace ta fi sha'awar walima a ranar jumma'a da yamma amma dai za tayi shawara da antinta ummi. Data shiga ckin gda takira ta a waya tashaida mata, ummi tarangada guda tace "amarsu ta ango knan wannan sai mun zauna an tsara yadda za ayi, zanso ganinki ranar wannan biki za kiyi kyau na jan magana. Fati tace "fatana aure dai Allah yasanya mai alheri da albarka ba na na so inga anyi aure anyi shagali aure na soyayya amma auren bai je ko ina ba sai kiga ya lalace ko ayi ta samin matsala a rasa laifin waye mazan ko matan ? Ummi tace "kowa na da laifi fati a tsakanin mazan da matan ko wanne akwai rawar dayake takawa gun haifar da matsaloli ckin auran da rabuwarsa, amma dake insha Allahu za kuzauna lafiya da malam musbahu domin aure ne da aka gina shi a bisa kyakyawar turba, kuma za ayi shi ne don Allah,. Bayan ummi ta kashe waya tafito falo, ganin dr. khalifa ya hakimce bisa kujera wata lafiyayyar shadda a jikinsa maroon colour dinkin da matasan zamani ke yi yayi, ya yi kyau har ya wuce misali, farin gilashin idone a fuskarsa bai damu da zaman ummi a gun ba yaci gaba da fadin "mama kinsan maganar aure tana bukatar nazari da bincike, wlh a rayuwata bbu auran dana tsana irin je ka kadawo, ayi aure ana farin ciki da zarar an je an zauna a kasa fahimtar jin dadin dake ckin zaman auren, kullum kana ckin damuwa matarka na ckim damuwa meye amfanin hakan, amma idan aka natsu za asamu kwalliya tabiya kudin sabulu sbda na sani bbu wanda ya isa yakaucewa abinda Allah ya hukunta masa. Yayi shiru anan yana nazarin fuskar mama don ya fahimci yadda tadauki maganar, batace komi ba tajuyo tadubi ummi tace "'yammata yaya akayi ne yau fatin batazo tayin hira ba ? A sanyaye tace "batazo ba waya tamin yanzu tace malam ya ce idan Allah ya kaimu nan da sati biyu za ayi bikinta. Mama tatsuke fuska tace "wani irin sati biyu kuma ? Tace "haka dai tace. Tace "to je ki kiramin fatin har yaushe akayi mata shiryen shiryen amaren. Dasauri ummi tabar gun tafada daki don tasamu damar yin kukan data ke ta hadiyewa. A falo kuwa dr. khalifa ne yaji wani irin abu ya tsirga masa a cikinsa zuciyarsa takama bugawa. Fatima Za ayiwa aure nan da sati biyu ko kuwa wata fatin ce daban, nan da nan yanayinsa yasauya gaba daya yawaiwayo tare da zare space din sa yadubi mama yace "mama wace fatin za ayiwa aure ne ? Tayi murmushi "fatima yarinyar nan dai ta makotanmu daka gani jiya. Yace "doyar malam musa ? Tace "yawwa ita kuwa. Abinda yafito daga bakinsa shi kansa ya ba shi mamaki don bai san sanda yace "Lallai da sake". ****** A DAREN FARKO 19 Mama tayi masa wani irin kallo tace "me kake nufi ? Anan ne yadan shiga natsuwarsa yace "mama wannan yarinyar nakeso na aura don gskiyar magana ita neke ganin ta dace da rayuwata da tsarina haka nan zuciyata ta aminta da soyayyar ta dari bisa dari don... Ckin zafin rai mma tadaga mai hannu tace "kai ya isa haka, saita bakinka kasan abinda kake fada, fatima an yi mata miji tsawon lokaci mai yawa kuma ba za a fasa ba shi a ba ka ba. kada kasoma sanyawa zuciyarka soyayyarta wahalar da kanka za kayi don baza kasame ta ba. Bai ce komi ba yamike yabar faol zuwa daki ? sa yakira dr. hafiz yace "kana ina ? " Yace"ina asibiti yanzu muka fito daga meeting.. Yace "to ina ka dosa ? Yace "gida za ni akwai magana ne ? Yace "kwarai kuwa magana ma babba ba karama ba. Yace "kasameni a gida mana. Mota yadauka yanufi gdan dr. hafiz da ke hotoro ya iske ya rigashi isa, yace "matar gdan fa da yaran ? Dr. hafiz yatabe baki yace "ai mata ba su da matsalar data wuce biki, sunan wai kanwa ta ce data haihu tun karfe bakwai tabar gdan nan ko abinci ba a tanadar min ba kuma yunwa nakeji sosai, yanzu sbda Allah a irin wannan tsarin idan munce, za muyi aure munyi laifi ? ko yanzu da zance zanyi aure sai ka ji bala'i na tashi nakan rasa su mata wane iri ne. Dr. khalifa yabushe da dariya yace "na san duk yunwa ce tasaka wannan surutun ai kai da sauki ma tunda ka iya shiga kitchen ka sarrafa abincinka kaci ni ko tea ba na iya dafawa. Dr.hafiz yace "to ai kuwa ka koya mata ba su da tabbas surutu da soyayya a waje suka iya idan an shigo gdan sai a hankali musamman idan an fara ajiye yara, bara in dafa indomie kaina har ciwo yake sbda yunwa. Bayan ya gama dafa indomie din suka mike a kasa suna ci yace "mutumina wai wace babbar magana ce ? Yace "ina fatan ka gane fatima" Dr. hafiz yace "ba zan kasa fahimtarta da wai ba domin na fahimci zuciyarka ta amsheta da gaggawa. Yace "kwarai ba ka yi fahimtar kuskure ba, kallo daya nayiwa yarinyar naji zuciyata ta aminta tazamo mata ta. Dr. hafiz yace "to ai bbu matsala yarinyar datake rayuwa a cikin gdan ku na yi farin cikin han. Dr. khalifa yace "kai dakata saura sati biyu bikinta. Dr. hafiz yace "to ba sai a lalubo wata ba abinda ga matan nan dayawa dakansu suke cewa ma suna so. Dr. khalifa yace "kai likita mata suna suka tara, duk yawan dasukayi irin su fatima daban suke, a iya budewai idona da yawace yawace na ban taba ganin mace mai kyaun fati ; a ba, tare da kyaun fuska ,dubi yadda tsarin halittar jikinta yake,habawa wannan ai itace mace mutumi na. Dr. hafiz yayi dariya sosai yace "kai wani irin kayatarwa fatima tayi maka, ne karude haka ? Haba likita kada kabari fatima taji za ta rainaka ka ga yarinya ce karama ko ka mance kana cewa ba ka son karanar yarinya ? Dr. khalifa yace "kai tafi chan wannan lokacin ya wuce ba zan iya hakura da yarinyar nan ba. Dr. hafiz yabata rai yace "kai Abbakar muyi magana ta gaskiya yarinyar daya rage saura sati biyu bikinta yya za ayi kace kana sonta ? ko a shari'ance ba kyau nema cikin nema ,kayi hakuri kawai mace in dai mace kake bukata za kasamu wadda tafi fatima kyau sai dai in fa fatima kake nema. Dr khalifa yadan marairaice yace "haba dr. hafizu yaya za ayi ka sanyayar min da jiki ? bayan ka san ban taba nuna maka wata diya mace dana damu da ita ba ballantana har in nuna damuwata akan sonauranta, tunda nagaya maka ai ka san dagaske nake ya kamata kataimake ni da shawarar dazan samu mafita ba kasace min guiwa ba. Dr. hafiz yace "to ai ni banga hanyar mafitar bane Abbakar, sati biyu fa yarage biki sai kuma muce muna so ? wannan ai son kai ne da zuciya, kuma kasani son kai da zuciya ba dabi'a ce ta mutan arxiki ba. Dr. khalifa yace "knan so kake kace min sai dai inyi hakuri da fatima ? Yace "Don Allah kayi wannan hakurin sai Allah yabaka wacce tafita.... Dr. khalifa yace "kai hafiz daina min wannan maganar da wuya in za tayiwu bakasan menake ji bane game da wannan yarinyar, ban taba sanin haka so yake ba. ****** Tun a wannan rana mama tafara shirya amarya fatima da kayan gyaran jiki na mata suka tunkari lamarin dagaske, batasan rikicin da dr. khalifa ke ciki game da matsananciyar soyayyar fatima da ta damki zuciyarsa ba, a wannan daren yakasa sukuni yakwana yana tunanin tawace hanya zai samarwa kansa mafita. Abin da dai yasawa kansa shi ne ko ta wani hanya zai mallaki fatima babu yadda za ayi yayi sakacin dazai rasa ta, bai san haka ciwon so yake ba sai yau. A gdan fatima takwana suna tattauna yadda biki zai kasance, abinda fati take jaddadawa ummi shi ne "ta sani khalifa sbda ba ya da tausayi, tace "ni kam ummi na rasa yadda zanyi da takaicin dana ke ji a raina game da yaya khalifa, ko ganinsa ba na son yi sbda kawai ya nuna ba ya sonki. Ummi tayi murmushi tace 'to yaya zanyi na zubawa sarautar Allah ido na zubawa dr. khalifa ido, na tabbaatarwa raina ko ban samu dr. khalifa ba to zan tabbatar wata diya mace bata same shi ba, idan narasa shi sai dai kowa ma yarasa . Fatima tace "kina nufin za ki hanashi aurene ? yaya mutumin da ka kaasa jawo ra'ayinsa yasoka za kasawa ranka cewa za ka iya hana shi aure ? Ummi ta girgiza kai "ba aure xan hana shi ba ban isa in hanashi aure ba ni dai na ce sai dai kowa yarasa . Riga da zani na atamfar egyptian ce a jikin fatima tana tsaye ita kadai a kitchen tana suyar kosai, kawai ganin mutum tayi a kusa da ita yana fadin "fatima aiki ake yi ne ? A firgice tawaiwayo tadubi dr. khalifa yana sanye da doguwar riga fara kal kamshi mai dadin gaske yana tashi a jikinsa, ta matsa gefe ganin yadda yatsaya daf da ita kamar zai taba ta, yayi murmushi yace "ya kike matsawa haka kamar kinga wani dodo ? zo ki kwashe kada yakone. Ta katsa motsawa sai gabanta ke faduwa a lkacin ummi tashigo tana fadin "fatima kin gama ? Ganin wanda ke tsaye a kitchen din yasata tsayuwa turus tana kallonsa shi da fatima, ganin ummi yasa yatsuke fuska yafice daga kitchen din ummi takwashe kosai tana fadin "yau kuma meya kawo doctor kitchen din nan ko wani abu yake nema ? Kokarin da fatima tayi shine na daidita muryarta don kada ummi tazargi wani abu a ranta tace "ni ma gani nayi ya shigo. Kallon da ummin tayi mata shi ne yasa tafahimci kuskuren ta a bisa abinda tafada, to sai dai kuma batasan abinda za tafada din ba in ba hakan tafada ba, jikinta yakara sanyi sosai ganin ummi bata sake magana ba, takwashe kosan tace tadakko kunun gyadan dasuka dama zuwa falo. Bayan sun gama shirya tebur din ne tadubeta tace "ki je kigayawa doctor an gama shirya tebur kada yai sanyi yakasa ci. Cikin dacin rai fati tace "ni ce ma zan fadi mai ? kin taba ganin na nufi hanyar dakinsa. Ummi ta tabe baki tace "ai ba abin zafi bane gani nayi ya fi son yi miki magana fiye dani amma kar ki damu bari ni inje in gaya mai. Fatima taja tsaki tawuce daki, yayin da ummi tanufi dakin dr. khalifa ta kwankwasa yace "waye ? Tace "ni ce ummi. Ga mamakinta sai yace "shigo" Ta bude jikinta ba karfi yana kwance bisa gado yanuna wata kujera yace "zauna in miki tambaya. Ummi na son kallon fuskar dr. khalifa yana yawan burgeta nan da nan taji hawaye ya taru i donta tayi kasa da kanta, yana sane da halin datake shiga idan tana kusa dashi yashare domin shi ma din a halin yanzu abin tausayi ne duk yadda take son sbi ya fita son fatima kuma ya fita shiga hadari domin kuwa gab yake da yayi babbar asarar rasa fatima. Ke ummmi gaya min dangantakar ki da fatima". Abin da yace da ita knan lamarin dayasa tadago cikin sauri zuciyarta na bugawa sosai tace "ban gane ba yaya khalifa. yamike zaune bai ce komi ba, tunanin da yake kai komo a zuciyarsa shi ne shawarar da dr. bashir yaba shi duk a daren jiya lokacin daya same shi a waya yabashi labarin halin daya ke ciki yace "Bash don Allah kada ka kashe min guiwa ba zan iya hakuri da fatima ba ni kadai nasan halin da zuciyata ke ciki. Dr. bashir yayi shiru kamar ba zaiyi magana ba. Khalifa yce "ya ya naji ka yi shiru. Bashir yayi ajiyar zuciya yace "Abbakar ta yaya xa a maido wannan aure a kanka bayan sati biyu yarage kace ayi mata aure. Yayi tsaki yace "amma dai ni ne nafada maka saura sati biyu ayi bikin ko ? ka ga ba na bukatar kasanar dani shawara dai nanemeka bashir. Yace "to shi me rai ba ya rasa motsi, hanya daya ce wata kila idan munbi za mu iya dacewa. "Fadi inji" Bashir yace "ta hanyar ummi da mama ne kawai za mu iya yin nasarar jan hankalin fatima idan da rabo sai ayi nasara. Ummi tace Bashir ? Ya amsa "ita nace dalilin dayasa nace ita kuwa inada labarin cewa fatima ba ta da kawa aminiya abokiyar shakuwar data wuce ummi, ummi na iya sauya ra'ayi da tunanin fatima sbda yarda da amincin dake tsakaninsu, yayin da mma ke da girma a idon ummi ba ta iya musa maganar mama. Dr. khalifa yajinjina labarin a ransa yace "hakane Bashir to amma fa kada ka manta ba wanda ummi ke so sai ni, ban amince da auranta ba ta yaya za ayi ta amince da wannan batu ? Ba ka ganin za tayi amfani da wannan damar gun lalata min al'amarina da fatin ? Bashir yace "to ai daman ba kai tsaye za kagaya matan ba sai ka bi tawasu hanyoyin na hikima wanda zaisa ta fahimci kana sassauta zuciyarka akanta,ma'ana kadinga sakar mata fuska kuna hira kuma karara kanuna mata cewa kana bukatar ta taimaka maka akan fatima za kayi mata duk abinda take so, idan kayi mata za ta amince tunda tana sonka ba ta son damuwarka, sannan ita kuma mama ka marairaice mata sosai kanuna mata ba za ka iya rayuwa ba fati ba, so so ne amma son kai ya fi da sannu za ta tausaya maka tagoya ma baya. Dr. khalifa yakashe wayar kansa a daure tamau yana jinjina yadda zai iya jan hankalin ummi har ta taimaka masa, bayan magana ma ba yi mata yake ba, ya kwana yana tunanin abin ga dumbin ciwon so na karuwa a zuciyarsa har yana jin ina ma zai iya fidda son fati daga ransa ya huta, amma ina duk yanayin dazai shiga in dai zai mallaki fatin dole yajure tunda mallakar ta shi ne kadai kwanciyar hankalinsa da farin cikin rayuwarsa, amma fa yana takaicin hakan bai damu da lallaba mama ba ya san tana sonsa da tausayinsa, ummin ce dai matsalarsa kuma ya amince ta hanyar ummi zai iya cimma nasara.. Wannan shi ne dalilin dayasa da gari yawaye yanufi kitchen ya san ummin ce ke dafa abincin safe a gdan ga mamakinsa sai yaga gimbiyar ce a kicin din... Yakatse tunaninsa anan yadawo da ganinsa ga ummi wadda tayi tagumi tana goge hawayenta wadanda tayi kokarin tsaida su suka ki tsayuwa takyalesu suyi ta zubar lokacin su ne. Ummi" Muryar dr. khalifa ya ratso kunnanta da sassan jikinta tadago kai suka kalli juna tace "Na'am". Ina son ki yi min wani taimako daya za ki iya ? Idan bai fi karfina ba insha Allahu zanyi maka, fada min inji" Ummi "inason kawarki fatima. Inason in aureta za ki iya taimaka min ki ja min ra'ayinta a fasa ba musbahu auranta a bani ? Wai shin mafarki ne wannan ko gaske ? Dr. khalifa datake tsananin so ne yake gaya mata da bakinsa cewar fatima aminiyarta yake so ya aura har yana neman ta taimakeshi. wane irin raini khalifa yake mata, wani irin cin fuska ne wannan ? Hawayen idanuwan ummin suka kara ballewa tashiga kuka kamar ranta zai fita, Dr. khalifa yace "ummi idan ba za ki iya taimako n ba kitashi ki ban guri. Tace "ya ya khalifa ba ka da tausayi kuma baka san darajar soyayya ba, baka san ciwon so ba, da ka san zafi da dacin rai dake cikin ciwon so da baka nufeni da wannan maganar ba, ka san yadda nake ji a zuciyata kuwa ? tamike tsaye idanunta tazuba kansa wadanda suka kada jawur tana huci tace "khalifa na sani ba ka so na, ba zan yi maka dole kaso ni ba, kuma ba zan taba bin wata hanya don kaso ni ba,, ni kam ina sonka son da ba zan taba dainawa ba, abu daya nake son tabbatar maka wanda shi ne ba zan taba barwa wata kai ba sai dai kowa yarasa ni kam na ami ? ce na rasaka.... Amma ba zan hakura ba. A fusace tabude kofar tafita, yabiyota dasauri yasha gabanta ya sausauta murya yace "haba ummi kitsaya ki fuskance ni da kyau mana na yi miki alkawarin zan miki duk abinda kikeso matukar na mallaki fatima. Murmushi tayi masa tace "ka yi kuskure babba doctor daka fuskance ni da wannan maganar. Ta zagaye shi tashige cikin gida. Abba da mama ne kawai a falo suna breakfast, tashige dakin dasauri dan ba ta son sukalli idonta. Ba karamin faduwar gaba fatima tayi ba ganin ummi ta shigo tana kuka, tamike tariko ta tana tambayarta lafiya ? me khalifan yayi miki ? Ta ja hannunta suka zauna tana goge mata hawaye, ummi tace "ummi babu abinda dr. khalifa yayi min fyace ya shaida min cewa yana sonki yana son in taimake shi yasamu auranki. INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. fatima kefadi muryarta na rawa tace "bai san an kusan bikina bane, ke ko ba a kusan biki na ba ina ni ina shi. Wani irin abu ummi taji ya tokare mata zuciya, kirjinta yamata nauyi, kanta ma yashiga sarawa nan da nan taji jiri ya fara dibarta, tadaure tatashi tadauki hijjavinta tayi sa'a abba da mama sun shige daki tafice daga gdan taja mota sai gdan mahaifiyarta. Hajiya Hauwa na barci ummi tafada jikinta tana kuka mai tsanani, a rude hajiyar tatashi tana tambayar lafiya lafia ? Wa ye yamutu ? Tace "hajiya na ga takaina na shiga uku, wai khalifa ne yau din nan yakirani yana shaida min cewa ba macen da yake son aura sai fatima. Yana son in taimake shi yasamu hadin kan fatima. Hajiya tace "yawwa abinda nake gayan miki ya auku ko ? ai lokacin da muke gaya miki gani kike ba zai taba yiwuwa ba, bayan mu munsan faruwarsa abu ne mai sauki, idan kika kalli fatima da tsarinta mace ce da maza ke burin mallakar irinta, ta yaya khalifa yana ganinta a gdan zai hadiye maitarsa. Ummi kuka take tana karawa fargaba da takaici sun sa ta kasa samun abinda za tace yayin da hajiya ke ta fadace fadacenta inda take shiga ba nan take fita ba, takira hajiya saude a waya tace "kinga abinda muke gudu saida ya auku, taurin kan yarinyar nan zai ja mana asara. Bayan saude ta saurari abinda ke faruwa daga bakin hajiya hauwa tace "kujirani za mu yi maganinsu dukkansu wannan karon sai mun bude musu wuta duk tsawon lokacin da muka dauka ya tashi a banza knan ? wannan abu ne da ba zai taba yiwuwa ba. Ba afi minti daya ba hajiya saude tayi dirar mikiya a gdan tadubi ummi tace "kukan banza da wofi idan mutum bai aiki da shawarar na gaba dashi yana tare da nadama, gun malam za mutafi yanzun ba za mu rangantawa khalifa ba. Hajiya hauwa ta tabe baki "ba sai in za tayi abubuwan da aka ce mata ba. Tace "to kada ma tayin batayi ba ta isa tazo tana mana kuka anan ? Har suka isa gdan malam din kuka sosai ummi takeyi ita takaicin ta ace dr. khalifa yarasa wa zai so sai aminiyarta fatima, tunda su hajiya suke gaya mata abin da zai iya fruwa ganin take bazai taba yiwuwa ba ashe kuskure tayi babba, hajiya hauwa da hajiya saude ke ta tattaunawarsu kan matsalar ita kam ta sunkuyar da kanta tana tunanin yadda za takasance in har fati ta amshi soyayyar dr. khalifa koda yake abu ne da take ganin kamar zaiyi wahala sbda koyaushe fatima na tabbatar mata da cewa bbu abinda zai hana yi ma iyaynta biyayya, tanayin wannan magana ne idan wasu daga kawayensu suna cewa"kyaun halittarta ya fi karfin ta auri malami almajiri irin malam musbahu wanda ba wayewa a tare dashi, to anan ne take tabbatar musudacewa "malam musbahu ya fi kowanni namiji a gunta tunda shi iyaynta suka zabar mata dole tayi iyayya gasu sbda yardar Allah take nema a cikin al'amuranta ba wai kyale kyalen duniya da abinda ke cikinta ba. Ummi tana cigaba da gasgata abubuwan da fatin ke fada ne ganin yadda bata kila kowani irin da namiji duk matsayinsa, hakan ne yasa ummi ta tabbatarwa kanta cewa ko dr. Khalifa yadawo ya ce yana son fati bazata amince da batunsa ba, sbda akidar biyayyar iyayanta data sawa zuciyarta to in dai haka ne ma me zaisa in daga hankali na ? Ta tambayi kanta in dai fatima bazata amince da dr. Khalifa ba me zaisa ta tayarwa kanta hankali, to a daidai lokacin da wannan tunanin ke tasiri a zuciyar ummi har tafara jin saukin zafin da zuciyarta tadauka sai kuma dai wani gdfen na zuciyarta yafara tunasar da ita cewa fa dr. Khalifa kyakyawan namiji ne ga ilimi ga naira, mata kuwa ba abinda suke so a gun da namiji wadanda suka wuce kyau da naira ballantana abin yahadu da ilimi da wayewa, kadan ne suke la'akari da addini da kyawawan dabi'u, fatima kam tanada banbanci da sauran matan zamani, iya zaman ta da ummi ta tabbatar za ta mata wadannan kyawawan shaidar a ko ina fatima ba ta da kwadayin abin duniya don da tanayi da dr. khalifa bai dawo yasa meta, wannan tunanin duk yake kara kuna a zuciyar ummi sunada tasiri mai karfi don ta tabbatar da hakan. Ummi na wannan dogon tunani ne kafin malam yabasu damar shigowa, hajiya suka shaida masa abinda ke tafe dasu, yajawo wani rairayi dake bayansa yafara zane zane yana tambayarsu wasu abubuwan dasuka shafi dr. khalifa da fatima da iyayanta. Malam yajinjina kai yace "hakika khalifa ba karamin so yakewa fatima ba, kai hasalima bai taba jin son wata diya mace a ransa kwatankwacin yadda yake son fatima ba, kuma ya yi dammarar auranta ko tawani hali. Wannan bayanin na malam yasa ummi tunani kamar kirjinta zai tarwatse sbda faduwar gaba, hajiya hauwa tace "to malam yanxu knan khalifa ba zai auri ummi ba, kuma kana ganin auransu da fatima mai yiwuwa ne dukda cewa an kusan bikinta ? Malam yace "to ni dai na gaya muku abinda nagano tar da khalifan ne, batun yiwuwar auransa da ummi idan kun bi abubuwan dazan tsara muku anyi an gama, fatima kuwa zan fatattaki soyayyarta ne daga zuciyarsa, amma gskiyar magana ba aiki ne mai sauki ba. Hajiya saude tace "malam indai za asamu nasara wahala mai sauki ne kuma me wucewa ne me ake bukata ? Malam ya gyara zama yace "dafarko kamar yadda nagaya maku a baya za ku kawo min kasar da khalifa ya taka, za ku kwao gashin kansa da hankicinsa da hularsa da hotonsa, za ku biya kudin fararan raguna guda uku, jajayan akuya guda uku, jajayan zakaru bakwai, sauran abubuwan kuma mu za mu samo su, kudin aiki dubu dari, ku zuba ido za kuga aiki da cikawa. Suka tsaya akan cewa bayan kwana biyu za akawo duk abinda aka bukata har kudin, suka dawo gda da shawarar yadda za asamu kudin dasuka kama har kusan dubu dari biyu, a karshe dai Alhaji muhammad mahaifin dr. khlifa aka buga wa waya suka mai karyar cewa asibiti za su yace zai aaiko musu da kudin dama sun saba dahaka duk abinda suka bukata zai musu iya ikonsa amma ba sa gani, su dai matarsa da dansa ne ba sa so dashi kansa sai dai dukiyarsa A DAREN FARKO 20 Fitar ummi yakara dagawa fatima hankali sosai takifa kanta a cinyarta tana sharar kwalla, meyasa dr.khalifa zai mata haka, ya ya za ayi yarasa wadda zai fadawa cewa ma yana sonta sai ummi wannan ba karamin cin fuska bane da walakanci, duk abinda zai sa ummi tayi hushi da ita abin ya yi yawa ko da yake ta san dole ne ummi tayi fushi da ita akan dr. khalifa, ba wanda ummi ba za ta iya juyawa ba sbda son datake masa ba kadan bane, ta gaji da kukan bakin ciki da takaici tatashi a sanyaye. zata tafi gda taci karo da mama a harabar gida tana magana da ado me musu wanki da guga, yanayin ta da mama tagani yasa tayi saurin matsowa daf da ita tace " 'yammata lafiya ? kukan me kikayi haka ? Ba kuka nayi ba wani abu ne yafada min ido. Tace "ina ummi ? Tace "ta fita ban san ina taje ba. Tace "ke ina za ki yanzun ? Tace "gida za ni yanzun xan dawo. Kamar zata hanata tafiya sai tayi tunanin bai dace ba batasan abin da za tayi ba don haka ta kyaleta tatafi tadawo falo tazauna. Dr. khalifa yashigo cikin shirin fita yazauna suka gaisa tace "ba za kaci abincin bane naga ka yi shirin fita ? Ya girgiza kai"ba zan iya cin komi ba xuciyata tana ckin damuwa bansan mafita ba a cikin halin danake ciki. Mama tayi murmushi tace "khalifa Allah (SWT) daya halicce mu cewa yayi "ban halicci mutum da aljan ba sai don su bauta min, to ni dai a ganina ba wani abinda zai dagawa mutum hankali akai in dai ba bautar Allahn nan ba, to ita kanta bautar Allah ba zafafa mana akai ba, Allah ba ya daurawa wata rai sai abinda za ta iya, in kuwa haka ne bbu abinda zai zamo mai tsanani a cikin wannan rayuwa ko meye shi kuwa, musanman ida mutum yana la'akari da rayuwar duniya, wadda fararriya ce kuma kararriya, duk wani abu dakasani dayake a cikin duniyar nan a dayan biyu yake, ko dai ka kare kabar shi ko shi yakare yabarka, to meye dalilin damuwa. Khalifa yayi ajiyar zuciya yace "mama na san za ki yi min shaidar hakuri da kau da kai a cikin al'amarin rayuwa idan yataso min, mama a wannan karon na samu kaina a yanayin dana kasa mallakar kaina, don na sa hakurar da zuciyata tayi hakuri da abinda take nema. Wallahi ji nake k ; ar zan mutu sbda ciwo fmda radadin da nakeji a zuciya ta. Mama tayk mai zumu da ido tana kallon fuskarsa, tabbas yanayin fuskarsa ta nuna tabbatar da abinda yake fada haka ne, tausayin sa yakamata amma tjure don kada ta dada karayar mai da zuciya tace "khalifa daman akwai abinda ba za a iya hakura dashi ba a duniyar nan ? a matsayin mu na musulmi munyi imani da cewa dukkan abinda yasa me mu haka Allah ya kaddara mana kuma ba mu da ikon kaucewa abinda Allah yakaddara mana ,kadaure kayi hakan mana. Yace "mama ba zan iya hakuri da fatima ba, don Allah ki taimake ni duk yadda za kiso alheri a gdan wanda za a ba auran fatima ba kamar a gdan nan ba. Mama ta jima kanta a kasa tarasa abinda za tace, Dr. khalifa yaci gaba da fadin "wlh mama babu abinda zan iya aiwatar wa a rayuwa ta in dai ina cikin wannan yanayin ni dai kisha min kan yarinyar nan da iyayanta ina matukar kaunarta. Tace "khalifa wace irin son zuciya kake son mu aiwatar ne ? don Allah kayi hakuri. Ya tareta dasauri yace "don Allah kada ki ba ni umurnin yin hakuri ina son fatima dayawa zan iya kowani irin hali idan ban mallaketa ba, ke za kiyi hakuri ki taimakeni ba wai ni zanyi hakuri ba waye zai iya hakuri da abinda yake so mama" Tace "ahi ke nan kabani kwana biyu zanyi tunani. Nan take mama tgano dalilin kukan da fatima ke yi knan, to kuma meye dalilin fitar ummi da safen nan ba tare da ta sanar dakowa inda za ta ba, ta kira wayar ummin a kashe takira hajiya hauwa ita kuma tana ringing ba a daga ba, ta aje wayar a gefe tayi tagumi tunani ya sha mata kai, shin yaya za ta yi da wannan al'amari, tana bukatar shawara, ko dayake duk wata shawara ba ta wuce ta lallashi khalifa yayi hakuri ba domin wannan son zuciyar ba yiwuwa zaiyi ba. Takira sadiya kanwarta dake tayata zama a gdan a dalilin mutuwar auranta tashaida mata abinda ke faruwa. Sadiya tace "tabdijam wannan ai babbar magana ce. Tace "to sadiya nima haka nagani, na rasa ta ina zan gano mafita. Sadiya tayi murmushi tace "to amm fa mama so so ne sonkai ya fi, tun kafin khalifa ydawo kasar nan idan nakalli fatima nakanji sha'awar ina ma itace khalifan zai aura, hakan yasa ba na so ma in ji ana hirar auranta me zai hana tunda dai khalifa ya nuna wannan damuwa ta sa mu san yadda za muyi ya aureta dama ance matar mutum kabarinsa wani bai auran matar wani. mama tagirgiza kai tace "kai anty sadiya anya wannan maganar ta yi daidai kuwa ? Sadiya tace "ta yi dai dai mana mama abinda yasa nace dake haka, idan khalifa bai samu auran fatima ba ba zai maida kansa kan aure ba sannan tunda ita yakeso in ya aureta hankalinsa zai kwanta sosai, yarinya ce mai hankali da natsuwa, gskiya mama kada muyi wannan sakacin daga karshe mu zo muna nadama. Mama takwantar da kanta bisa kujera idonta na kallon silin, sadiya ma ta zo da maganar daya cancanta a duba, abin ne da nauyi dole kam tsan abin yi in banda wannan matsalar ta fi kowa son khalifa ya auri fatima sbda fatima mace ce tagari to ya ya za tayi tadubi fati tace tafasa auren musbahu ta auri khalifa ??? ****** Tunda fatima tashiga gdansu bayan gaisuwa datayi da iyayanta bata kara cewa kowa kmi ba tashiga dakin innarta takwanta tana ci gaba da hawaye. Inna ta tambayeta damuwarta tagaya mata komi tace "tabdijam abin da malam ke gudu ne yafaru kin san shi Alhaji baban khalifan ya taba cewa yana son malam yaba dansa auranki yace ya riga ya ba da ke. Fatima tace "to ai inna ko da ba a bayar dani ba bazan taba amincewa khalifa ba, sbda aduniya dai banga da namijin da ummi ke so irin sa ba, ummi ba ta da burin daya wuce mallakarsa, ta kwallafa rai a kansa tana matukar so da kaunarsa. Matsayin ummi gareni ya wuce in yi mata haka, don Allah inna kada ki saurari maganar khalifa ba shi da tausayi bai da adalci. Tace "to ina ma za ayi haka ? dole yahakura. Fatima tadinga nacin kiran ummi a waya wayar a kashe take, dole taje ta lallashi ummi, ummi ta fi komi a gareta. Bayan sallar azahar tashaidawa inna za ta gdansu ummi tace sai ta dawo, ko ganin gdansu dr. khalifa ba ta son yi ,sbda takaicin ya cuceta ya hadata da babbar aminiyarta abokiyar shawararta. Tana tsaye bakin titin kan layinsu tana neman adaidaita sahu kawai sai ganin mota tayi ta yi fakin a gabanta, bakaken gilashin da aka zuge yabata damar ganin wanda ke ckin motar. dr. khalifa ne gabanta yafadi tsmatsa dasauri tana masa wani irin kallo, yace "ina za ki ne fatima. " Tayi shiru kamar ba da ita yake ba, yace "don Allah kigaya min inda za ki in kaiki. Anan ne ta hasala tace "ina ruwanka da inda za ni, ni ba neman taimakon mota nake ba. Yakashe motar yafito yana kare mata kallo daga sama har kasa, yana murmushi a wannan lokacin ne yadada tabbatarwa kansa yana son fatima kuma ba zai iya sakacin dazai rsata ba insha Allahu wannan yarinyar matarsa ce ta sunnah. Kwatsam adaidaita sahu ta tsaya a gabansu, ummi ce tafito idanunta fes akansu bata ce komi ba tabiya dan adaidaita kudinsa tawuce za ta tafi, fatima tabita tana fadin "ummi ai gdanku za ni Allah ne yataimaka bamuyi sabani ba. Ummi tajuyo suka hada ido ,kallon datake mata yana dagawa fatima hankali, tawuce dasauri tabar gun, ta tsaya sororo tabi ummin da kallo. Dr. khalifa ya iso gabanta yace "fatima don Allah ki tsaya ki saurareni, zuciyata tana matukar so da kaunar ki don Allah ki tausaya min. A fusace tace "ai kai ba abin tausayi bane, babu wani dalilin dazaisa a tausaya maka, tunda kaima ba ka tausayin mai sonka, tun yaushe ummi take fama da ciwon sonka a zuciyarta amma ka ki kadubeta kake walakanta ta sbda kawai tana sonka ? Yazuba mata ido yana murmushi wai shi yarinya kamar fatima ke wa tsiwa haka, son da yake mata ya yi tasiri da isarsa ta namiji ba zai yi komi a kanta ba, a iya rayuwarsa bai taba samun kansa a yanayi irin wannan ba. Tayi tafiyarta tabarshi a gun yana binta da kallo, gumi yana yanko masa har ta bace sannan yashiga motarsa yaja zuwa gdansu. Baiyi tunanin nan gdan na su fati za tazo ba sai yaganta za tashiga yayi murmushi kawai ,tafizge kanta tashiga ckin gda tayi sa'a mama ta fita anguwa sai 'yan aikin gdan suna hidimomin su, ta iske ummi a daki tana hada kayanta . Ta amsa sallamar fatin ba tare da ta kalleta ba, fatima tazauna a bakin gado muryarta a kasa kasa takira sunan ta, ta waiwayo tace,"na'am fati. Tace "ummi meye laifina akan wannan al'amarin lokaci daya za kijuya min baya ki tsane ni ? shin ni na budi baki nace ina son khalifa ? ko zuwa nayi sashensa naja ra'ayinsa don yasoni ? Ummi tayi mata wani lalataccen kallo tace "ke ki kama kanki, kin san dai ban tare ki dawata magana ba akan khalifa, don haka ba na bukatar kiyi ta nemana dawasu maganganu. Fatima tadaga murya tace "wlh ummi ko kusa bakiyi min adalci ba, na yi zaton a gun ki zan fara samu shaidar wani da namiji va zai taba samun masauki a zuciyata ba, ko ina son khalifa ko babu maganar musbahu a kaina ba zan taba ba, dr. khalifa fuska ba sbda na san waye shi a gunki, ballantana kwanaki suka rage a daura min aure, hakanan ba na son shi ba na ra'ayin shi to meye na damuwa, don Allah ummi kada kidauki alhaki na kada ki watsa mana zumunci ki kwantar da hankalinki insha Allahu ta hanya ta za ki iya mallakar dr. khalifa in dai Allah ya kaddara mijinki ne zan yi amfani da damar dana samu a kansa in ja ra'ayinsa gareki amma fa sai in na samu hadin kanki. Ummi tayi dif tan juya maganganun fatima wadanda sukan saurin fisgar hankalinta tadawo natsuwarta, idanunta da zafin kishi yasa suka rufe suka bude domin ta fara jiyo kamshin nasara a maganganun fatima. Ta taso tadawo kusa da fatin tazauna muryarta a hankali tace "kiyi hakuri fatima a cikin gaba daya al'amura na ba na wasa da dr. khalifa sbda soyayyar danake mishi, ban taba jin za a wayi gari watarana inji ba na san na budi ido in ganki ba sai ranar da dr. khalifa yabudi baki yace min "ke ce mace daya dayake so ya aura a duk fadin duniyar nan, a wannan lokacin ji nayi na tsaneki fatima duk da na san ba laifinki bane ba ke kika sa yasoki ba amma wannan baiyi tasirin daya Hana inga laifinki ba. Fatima tayi murmushi tace "ke ma ba ki da laifi ummi domin ba laifi bane don mutum ya yi kishin abinda yake so, ballantana soyayya irin ta ki ga dr. khalifa, hnkalina ya tashi don sabon danayi dake ta ina zuciyata xa tasake kin juya min baya, ummi inason ganin kin mallaki dr. khalifa don haka zn daure shi da jijiyoyin jikinsa tunda ya ce yana sona to ya kawo kansa garemu, kiyi hakuri da duk abinda za kiga yana nuna mini na so, kafin mu cimma burimmu, kuma kibashi hadin kai a duk maganar dazai miki a kaina ki nuna mai kin goyi bayansa, xai kasance yana son magana dake sbda hirata da kuke. Nan take ummi taji zuciyarta ta yi mata wasai, kaunar fatima takaru a zuciyarta, tafasa hada kayanta tabar gdan kamar yadda tayi nufin yi, bayan tafiyar fatima gda takira wayar hajiyarta tashaida mata yadda sukayi da fatima, hajiya tace "anya kuwa dagaske take ummi ? kada fa tayaudare ki, sai wahala ake awai wata manufa a zuciyarta. Hajiya tace "to ki dai yi taka tsan tsan kuma kisan yadda kikayi kika kawo mana abubuwan da malam yace a kawo wadanda suka shafi khalifan. ****** Cikin dacin rai fatima tadawo gida tana takaicin son zuciyar dr. khalifa duk da ta san ba zaiyi nasara a kanta ba amma abin yana ba ta haushi sosai, ga mamakinta sai ta iske mama da anty sadiya a gdan na su suna hira da inna ga zogala a gabansu suna ci. Ta fadada fara'arta tace "lah mama dama nan kika shigo. Tace "eh amma mun biya kasuwa kafin mushigo nan din. Inna tatashi tace "bari in tuka tuwon nan in hada miya in dawo. Mama ta ji dadin fitar inna tace " 'yammata na zo ki zauna anan kiji wata magana. Daf da ita fati tazauna tace "wannan zuwan na ki ne don gunki muka zo. Tace "ni mama. Tace "kwarai kuwa fatima ko baki kai matsayin daza muzo gunki ba. Tayi kasa da kanta tana girgiza kai, mama tace "fatima munzo da kanmu ne nan dan kidauki abinda mukazo miki dashi da mahimmanci, a wani lokacin idan za kagawa mutum abu mai muhimmanci to kadubi yanayin dazaka fada masa dan yafi kama batun da daraja. fatima na san matsayin uwa nake a gunki ckin gdan nan na san bbu abunda xan nema in rasa shi sai fa in ba ku dashi. ko da yake maganar danazo miki da ita mai nauyi ne amma duk da haka nauyinta ba zai hana in gaya miki ba, sbda na san wacece ni a gunki, ba kuma ina nufin yin amfani da wannan damar bane in tursasa ki ba a'a alfarma ce nake fatan kiyi min. Fatima dan uwanki khalifa ne ke neman alfarmar ki amince mai ya aureki sbda ke kadai ce zuciyarsa ke so, kuma ta aminta ya aura. Tunda mama tafara magana fatima tasan inda tadosa, dataji ta yi shiru tace "mama duk abinda kika fda haka yake, kuma alfarma kowace iri zan yiwa kowa a gdanku amma a wannan karon sai dai in ba ki hakuri mama abu guda daya ne zai hana in amsa wa yaya khalifa soyayyarsa itace ummi. Ummi kuma fatima ? Me ya kawo ummi ckin wannan maganar ? Fatima tagyara zama tace "mama ummi itace za tayiwa yaya khalifa shamaki dani domin kuwa ta fi karfin in auri wanda maitar so da farautar nema, ummi tana tsananin so da burin auran dr. khalifa ,da wani ido xan dubeta in na aureshi,in banda haka da a yau dinnan xan tabbatar miki da matsayinku a gareni mama ta hanyar amsar bukatar dr. khalifa, kiyi hakuri mama ki taimaki rayuwar ummi ki ceto zuciyarta daga halin datake ciki ta hanyar sa khalifa ya aureta, mama kin zo gdan nan ne nasan sbda ttausayn sa di kikeji da gudun fadawarsa wani hali idan bai samu yadda yake so ba, mama to kisani ummi ta fidr. khalifa kuncin zuciya don shi a cikin kwanaki kalilan yake fama da ta shi damuwar yayin da ita tadade tana fama da damuwa, akwai daran datake kwana kuka akwai ranakun da ko abinci ba ta iya ci, ,kullum ciwon rai ke damunta akan dr. khalifa, in dai akwai abin tausayi ta fannin soyayya to ummi ce, kiyi hakuri mama kituno hadisin manzon rahama (SAW) da yace imanin dayanku ba ya cika har sai ya kasance yana sowa dan uwansa abinda yake sowa kansa. A DAREN FARKO 21 A cikin uwar dakin mama ita da anty sadiya ne ke zaune suna fama da magana daya dai dataki karewa, khalifa yashigo fuskarsa ba walwala yazauna kan stool yana fuskantar mama yace "gani" Tace "khalifa don Allah kayi hakuri da batun fatima ba za ta amince da batun auranka batunda dai har nataka kafata har ckin gdansu na roki alfarmarta bata amince ba, karshe ma tashiga kawo min wa'azi wai yadda naji tausayinka a matsayinka na da na har nake fafutukar ganin ka samu abun da kake bukata to itama ummi in tausaya mata in taimaketa ta aureka. Khalifa yaja dogon numfashi yace "wlh mama ni ma bansan abunda ke damuna ba, na kasa hakuri da yarinyar nan wani irin abu nake ji a cikin zuciyata kamar idan ban samu auranta ba mutuwa zanyi, ina jinjina wannan yanayi danake cki mama, a ni kaina ba na ra'ayin auran zumunci ba zan auri ummi ba, fatima kuma yanzu nafara sonta ki ci gaba da kokarin taimakona da addu'a da duk abinda za ki iya mama. Wayarsatafara ringing yatashi yafita, mama taja tsaki tadubi sadiya tace "to yanzu me za muyi, nikam ban san abinda za a zarge ni da son zuciya, ba na son in ja wa kaina zagi. Sadiya tace "kidaina damuwa mama in fa fati matar khalifa ce sai ya aureta, dole muci gaba da jan ra'ayin fatima tunda ita yakeso itace farin ckinsa. Bayan dr. khalifa yagama wayar da aka kira shi dakin ummi yanufa tana zaune tana duba wani littafi, ta amsa mai sallama cikin fara'a, yazauna gefen kujerar dake gaban madubi ya amsa gaisuwar tayi masa yace "ina fatima? Tana gdansu. Ya gyada kai "ummi" Ta amsa "na'am yaya khalifa. "Ba ki da wata hanya daza ki iya ja min ra'ayin fatima, ina sonta dayawa fa. Ba karamin namijin kokari ummi tayi ba gun shanye damuwarta da tsananin kishi? ta tace "yaya khalifa tunda dai kana son fatima zan taim*e ka kasameta, ko ba komi dai na godewa Allah dayasa kakejin irin abinda masoya keji a zuciyarsu yayin dasuka rasa masoyansu. Bata jira abinda zaice ba tamike tace "bari ma inje in zo maka da fatin. Ya bita da ido har tafita, ya ji ciwon maganar data fada masa na karshe amma babu yadda zaiyi soyayyar fatima ce taja masa, in bar da haka har ummi ce ta isa tagaya mai magana, yaja tsaki yayi tagumi. dr. bashir ne ke dada karfaf masa lallai yanemi taimakon ummi maganarta na da tasiri sosai a gu? fatima kada yadamu da abinda zaiji yagani domin duk abinda kake neman nasara a kansa sai ka yi hakuri, ba abi? da yatsana irin raini, Allah yasa ba alhakin 'yammatan daya wahalar ke bibiyarsa ba. Yana ckin wannan tunanin fatima da unmi suka shigo dakin idanunsa akan fatima yaji wani irin sanyi a ransa kamar yatashi yarungumeta nan take yakara sallamawa al'amari ummi a gun fatima, bai dada tabatar da haka ba sai da fatin tarusuna ta gayar dashi tace "ga ni yaya khalifa. Ummi tace "yawwa nikam na gama aikina, ke fatima kinsan dai yaya khalifa yayanmu ne. Ta gyada kai tace "na gane anty ummi. Bayan fitar ummi, dr. khalifa yakamo hannun fatima ya mikar da ita tsaye ya kura mata kyawawan idanuwansa masu laushi da daukar hankali, nan take yafara jefa mata wani bakon al'amari a zuciyarta, nan da nan tayi kasa dakanta tana jan numfashi dakyar, lamarin dayasa takasa cigaba da tsayawa ta janye hannunta ta zauna, yazauna daf da ita yace "haba fatima dago idonki kidube ni mana, wai meye aibuna da ba kya son kallona? Ta maraice murya tace "don Allah yaya khalifa kaji tausayin ummi ka amsa soyayyarta tana sonka dayawa, kayi hakurin fiddani daga zuciyarka, an riga an ba da ni kwanaki kadan suke rage nazamo matar wani.... Yasa hannu yatoshe mata baki yace "in kina son in a; hi batunki dago ki kalli kwayan idanuna. Ba ta son kallon idonsa sbda idon na sa daban yake dana sauran maza, amma bukatarta datake son tabiya yasa dole tawatsar da abinda takeji tawarware idonta ta dubeshi, ya lumshe ido yana mata kyakyawan murmushi, tamaida kanta kasa yace "fatima idan fa kina son in yi miki yadda kike so sai dai kiyi ta kallona har sai na ce kidaina. Tun fatima na zamewa kallon na sa har tafara rikicewa domin wani irin yanayi tafara ji a jikinta wanda bata taba jinsa ba, yakara matsowa daf da ita yasa hannayensa biyu yadafa kafadarta, "wlh ina sonki fatima inajin kihar ckin jijiyoyin jikina don Allah fati kada kibari kirasa ni kada kibari in rasaki, fati duk wanda yayi ceton rai... Yakasa cigaba da maganar sakamakon wasu siraran hawaye dasuka shiga zubo masa, lamarin dayasa fati tarude tana fadin "meye abin kuka khalifa ? Yace "ke ce bakiga abin kuka ba. Yasaketa yamike, tamike itama tatsaya a gabansa takasa magana, sun jima a haka daga bisani yafice daga dakin yana cigaba da sharar hawayensa, yawuce mama a falo yafita, gabanta na faduwa sbda ta ga yanayin daya fito nan take tsoro ya mamaye zuciyarta. A cikin dakin fatima sororo a tsaye tana tunanin khalifa, karo nafarko dataji tausayinsa ya kamata, ta yaya za tayi da wannan al'amarin, abinda yatsaya mata a rai shi ne hawayen khalifa da kyakyawan murmushinsa,dr.khalifa ya zamo namijin farko dataji lallai tanason taji ta a jikinsa sbda burgetan da yyi. Ta kwanta bisa gado tayi luf, a lokacin ne ummi tashigo dakin da zumudin jin yadda sukai ganin kwanciyar da fatima tayi da yanayin jikinta yasa gabanta yafadi sosai. Ko dai khalifa ya fara wa fati tasiri a zuciya, a sanyaye tzauna daf da ita muryarta cikin wani irin yanayi tace "fati yaya akayi naga kin zama wani iri. Fati tayi firgigit tamike zaune idnuwanta a waje tana kallon ummi tace "an samu nasara domin kuwa ya fara amsa min zai min duk abinda nake bukata. Ummi tayi ajiyar zuciya "fatima lallai idan kika ceci zuciyata daga halin da take ciki kin yi taimako. Tadafa kafadarta tace "ba komai kidaina yawan damuwa. ****** Tsakiyar dare ummi takira jidda dake londn ta fayyace mata abubuwan dake faruwa, jiddah tace "Dr. khalifa na son fatim Tace "kwarai kuwa jiddah soyayya kuma ba gama garin soyayya ba original one, domin kuwa tunda yadora idonsa a kanta gaba daya ya rikice ya rasa sukuni, kin san dai yadda khalifa ba ya sakar min fuska ko ? To a halin yanzu sbda in masa kamfen a gun fatima za kiyi mamakin yadda yake ja na a jiki ko kunyata ba ya ji. Jidda tayi ajiyar zuciya tace "anya kuwa umi ko dai dr. khalifa tsammani yake son wasa kike masa. Tace "haba jiddah wani irin wasa kuma, da dai ace mun saba wasa ni dashi to zaiyi tunanin haka, mutumin da bai min ko kallon arziki za kiyi mamakin yadda yasauya akan son fatima abin har tsoro yake ba ni jiddh. Ta jinjina kai tace "to yanzu wani mataki kika dauka akansu ? ko kin hakura dashi ? In hakura jiddah ? Tabdijam ai idan kika ga na hakura da khalifa to numfashin karshe nayi a duniya, ma'ana rayuwata ta kare amma idan ba haka ba matukar ina numfashi ba zan hakura da doctor ba. Jiddah tace "to ummi ta wce hanyar za ki mallakeshi bayan kin san ko da akewa maza auran dole a wani lokaci ba za ayiwa dr. khalifa ba. Tunda kinfi kowa sanin cewa mahaifinsa yana fifita shi akan komi yana kara akan komi banda khalifa. Ummi tace "eh nima bance za ayi mai auran dole ba kawai dai ba zan bar ma wata shi ba. Jiddah tace "ko da fatiman ta ki ta aura ? Tace "wannan ne abinda yafi daga min hankali ban so yakasance dr. khalifa fatima yake so ba sbda kaunar da nakewa fatima ba na son wani abu na bacin rai ya sameta, in da nake dan samun natsuwar zucia shi ne fatima ba son dr. khalifa rtake va, bayan kasancewar saura kwanaki kadan a daura auranta, fatima tanada burin biyayya ga iyayanta shi yasa bata kula kowanne da namiji, wannan yanuna kwanciyar hankali. A DAREN FARKO 22 Gaban abban yafadi ras yayi wa dr. khalifa wani irin kallo yace "ai an kusan bikinta da musbahu. Yace "na sani abba ai aaure nufi ne na Allah idan matata ce sai kaga.... Ya katse shi yace "kai khalifa wannan abu ne da ba xai yiwu ba nima na so auranka da fatima domin yarinya ce mai hankali da sanin ya kamata,to amma ta ina xanje in ce a fasa ba musbahu aure a ba ka, gskiya sai dai kayi hakuri Allah yabaka wata. To shima khalifan ya san abun da nauyi soyayyar dayake mata ne yasa yarufe idonsa yakeso ya mallaketa kota wani hali, bai ka ra cewa ko ; i ba, abba ya bishi da ido jikinsa gaba daya yai sanyi ba ya son dan na sa yanemi wani abu yarasa a rayuwarsa. Nan da nan yanayin abba ya sauya ganin damuwar da ke tare da khalifa, yamike yashiga dakin mama, tamike dasauri daga kwanciyar da tayi tace "daman ka fito Alhaji ? Fuskarsa ba walwala yace "na fito, khalifa ne yazo min da maganar data dagan hankali. Mama tace "uhm Allah yasa ba maganar fatima yakawo maka ba",. Ya dada bata rai yace "af daman kinsan da zancen baki fada min ba ? Mama tace "to Alhaji idan na fada maka me za kayi !? abinda zai yiwu ahi ake, ta yaya khalifa zai samu auran fatima idan kuwa ba zai samu ba meye amfanin tattauna maganar. Alhaji yazauna gefen gado yana fadin "to haka za mubarshi a ckin damuwa hajiya ? gaskiya ba zai yiwu ba. Mamaki yakama mama ganin yadda abba ke neman rufe ido kiri kiri yayi son kai, tace "alhaji gskiya sai dai hakuri domin ni da kaina naroki yarinyar tanuna min gskiya ba zai yiwu ba,ni abinda ke hadani da Khalifa shi ne idan yakallafa ransa kan son abu ba zai iya hakura yabi abin a hankali ba, sai dai ydga hankalinsa yadaga wa wani hankali. Abba yace "ba dole yadaga hankali ba, in bai gaya mana damuwarsa ba wa zai gayawa, kin san zafin soyayya kuwa ? Tace "hakane ban sani basai ka nema mai auran nasan dai sai da amincewar yarinyar da iyayanta za ayi ko ? Abba yace "Gaskiya ba zan bar yaron ckin damuwa ba, dole in bi duk hanyar dazan bi don ganin na samar mai dafarin ciki a rayuwarsa. Yajuya yafita yayin da mama tabishi da kallo cike da takaicin yadda abba ba ya son nunwa Khalifa yadda rayuwa take. **** Fatima ce zaune a runfar innarta ta yi tagumi ta kasa cin abincin dake gabanta, innar tana dakin malam, sauran kannanta duk sun tafi makaranta, musbahu yashigo da sallamarsa, tadaga ido ckin ladabi ta amsa muryarta a sanyaye tace "ina kwana. Idanuwan daya kafa mata yasa tayi kasada kanta yazauna kusa da ita yace, "fatima a kwana biyun nan kin sauya kamar ba ki da lfya sai ramewa kike ko dai fargabar auran ne ? Ya fada yana dan murmushi a kokarinsa na kwantar mata da hankali, itama murmushin tayi tace "lafiya kalau. Yajawo abincin gabanta yafara ci yana fadin "kai abincin nan yayi dadi da yawa na san ke kikayi. Bata ce komi ba, yaci gaba "gaskiya fatima Allah ya yi miki baiwa da yawa shi yasa zuciyata ke kara sonki don Allah nima ki soni kuma kidinga tausaya min wahala zan sha idan nasamu sauyi daga gareki. Anan ma shiru tayi masa don bata san abinda za tace dashi ba, wani iri takeji a jikinta ko kallonsa ba ta iya yi, yace "ftima don Allah kiyi min magana ko zanji dadi mana kin san ina sonki. Fatima bansan abinda zai same ni ba hakanan nake jin zuciyata tana cik e da fargaba idan nakwanta bacci kuma sai in ta mafarkai barkatai marasa dadi wanda yafi daga min hankali shi ne wanda nayi yau da asuba wai wani ya kwace min ke ta karfin tsiya, shi ne jikina duk yakara sanyi. Ga mamakin ta sai taji hawaye ya taru a idonta, tatashi dasauri tashige daki tace dashi "ina zuwa . Misbahu yabita da kallo har yagaji dazama yatashi bata dawo ba bai san meke faruw aba baiyi tunanin binta ckin dakin ba yafice daga gdan. Itama inna data shigo dakin kallon mamaki tabita dashi ganin yadda take saharar kwalla tace "lfya fatima? Tace "ba komi inna Ba komi kike kuka? Takasa magana domin itama batasan dalilin kukan na ta ba ballantana ta bayyanawa inna, inna ta jima a tsaye tana kallonta daga bisani tadaga kai tafita . Wayar fatima tafara ringing tadauko ta bakuwar lamba ce, tadaga tare da sallama, daga can bangaran aka amsa mata "Khalifa ne. Gabanta yafadi "ko baki fahimci khalifan bane? "Na fahimta. "To ai na ji kinyi shiru. Tace!"bansan abinda zan ce bane. Yayi dariya "za kisani yanzu kuwa, so nake kizo mugaisa tun da natashi idanuwa na ke son ganinki zuciyata na azalzala min da yawa don Allah kidaure ki zo. Tace "haba khalifa meye ma'anar zuwana gareka? me ganin zai haifar maka, me yasa kke mantawa na kusa zama matar wani ne.... Ya katse ta. Don Allah kidaina gayamin wannan maganar ki daure ki zo muyi wa kanmu maslaha. Shi knan a ina zan sameka? 'Yawwa tawan ina kofar gdanmu ckin mota ta. Hijabi tasa wanda yazo har kafafunta ydda idanunta ke kode sunyi ja haka tafita bayan ta shaidawa innarta cewa za ta gun ummi.. Ta wuce musbahu a kofar gda tare da wani abokinsa mai suna Aminu, khalifa yana hangota ya bude mata kofar motar tarike kofar tana kallon sa tace "idan na shiga mota ina zamu? ko a cikin motr za muyi magana? Yace "inaso kiyi min rakiya wani wuri. ne ba nisa. Ta waiwaya tadubi musbahu ita yakafawa ido, ta dawo da idon ta kan khalifa tace "kn ganin hakan y dce? "Eh ya dace mana kowa ya sanba na satar mutane, Fatima maslaha muke nemawa kanmu ina bukata kema haka in haka ne ki shigo mutafi. Bbu abinda ummi ke kallo sai rayuwar ummi wannan ce damar da zatayi amfani dan tallafawa ummi, sai ta zuke fargabarta tshga motar tarufo. . Ta gabansu musbahu, kbalifa yawuce idon ta ckin na musbahu taji gabanta ya fadi an ya ta yi dai dai kuwa. Gdan dr. bashir yanufa da fatima, matar dr. bashi ta asheta hannu biyu zuwa falonta takawo musu abinci da shayi, dr. khalifa yahada tea yafara sha, dr bashir ya harare shi "wato haka Za kadinga son kai ko ita amaryar fa. Don Allah ku rufa min asiri ina tare da matsaloli ko yanzun ma na biyo shi ne domin in fahimtar dashi. Farida tahada mata shayin taja hannunta zuwa ckin daki tace "fatima don Allah dagaske ba kya son Khalifa? Fatima tawaro ido tace "me son na shi xai amfana min, a rayuwata bbu abin da na tsana irin in yi abu in dawo ina nadama. Farida tace 'dr khalifa yadaga hnkli akan tsananin sonki, da za ki amsa soyayyarsa xa ki mori rayuwar aure, irin su tsada garesu. Fatima tace kin san kyaun mijin daxan aura da halayansa? an masa adalci in nabarshi na auri Khalifa? aminiyata na tsananin son khalifa ya kamata in watsar da batunta in aure shi? abinda khalifa ke nunawa fa son kai ne kuma ba dabi'ar musulmin kwarai bane, ya kamata kidnga fadwa Khalifa wadannan, don ydinga sa hkuri a zuciyarsa a rayuwa ba komi mutum ke so yake samu ba. Farida tarasa abin da xa tace sbda hujjojin fati sun daure mata jijiyo tamike tadawo falo tace da Khalifa da wuya fati ta amince yahakura kawai. Khalifa yace kai ba zai yiwu ba turo min ita, ban taba neman abu na rasa ba ba xan fara akan fatima ba, fatima ba ta ckin matan da za a iya hakuri dasu. **** Tun daga ganin yanayin fuskarsa ta san ba lfya, bayan sun gaisa ta tambayeshi "yace "ummi don Allah ko kin san wani abu tsakanin ummi da khalifa? Tace "wani abu kagani? Yace "kwana biyun nan na fahimci wani abu na damunta ta ce min ba komi, daxun kuma naga ya dauketa sun fita a motarsa, na kira wayarta bata daga ba. Ummi ta fiddo ido "fatiman? yace itafa abin ne nima yabani mamaki da yawa shiyasa nakasa aurewa sai sun dawo nazo inji ta bakinki na san kin san komi. Ummi tayi shiru kanta na kasa ". Lamarin daya dada firgita musbahu gabansa yashiga faduwa yashiga rokonta da Annabinsa in ta san wani abun kada taboye masa..... A DAREN FARKO. 23 Dr. khalifa yaci gaba da cusawa fatima maganganu a cikin kunnuwanta, suka dinga ratsa mata zuciya ga hgangar jikinta, lamarin daya sa ta kuma jin tsigar jiki? ta tana tashi tarabu da marsh war zuciyarta ,lokacin da dr. Khalifa ya fahimci ya yi ntasirin jan hankalinta sai ya saketa ya zaunar da ita gefen gadon yazauna a kasa. yace "fatima kiyarda in zama mijinki zan shayar dake zumar soyayya, zan dandana miki wata rayuwa wadda mafarkin ki bata taba ba ki ba, duk wani jin dadi da kwanciyar hankali da diya mace take fatan samu a gdan mijinta zan ba ki shi ba dan komi ba sai don ina sonki, ni kaina na san zuciyata tana sonki ba zanyi wasa da duka abinda yshafe ki ba. Abinda ke tafiyar da fatima shi ne son kallon fuskar Khalifa da idanuwanta ke nacin yi, idan kuma takalle shin sai taji wani irin abu nai mata yawo a cikin zuciya d jiki, ckin kasalalliyar murya tace "wai don Allah ya kakeson in yi da matsallina ? yaya xanyi da musbahu da ummi. Yaja tsaki yace '"don Alah ki ce kin amince dani kina sona za ki aureni, musbahu na san yadda zanyi dashi, unmi kuwakadaki kara min maganarta tunda nace ba na sonta ban sonta ba zan auri matar da ba na so ba. Tace" amma docter ya dace katausaya mata yadda kake son kaima. a tausaya maka yadda kake kokawa a bisa soyayyar dakake min tana wahal ma da zuciya, kowa fa yataimake wani Allah zai taimaka masa. Ya dan harare ta yana murmushi. "To na ji sarkin iya wa'azi. Takara langabe kai "to baka ce komi ba. Yace "to wai so kike in hakura dake in auri ummi ,ko kuwa in aure ku tare. Yana tsaye ne kyam a gabanta, kai wannn bawan Allah dakyau yake Allah ya yi halitta anan, ta hadiyi yawu tace"ni dai ina so ka aureta. Yace "to baki amsa ba in hakura dake ko in aureku tare ?ki je kiyi tunani ki zo min da amsa nan da gobe tashi mutafi gida. A hanyarsu ta komawa gda yatsaya a wani makeken super market yadinga zabar mata kayan kwalliya masu tsadar tsiya da burgewa sannan yajuya kan ciye ciye da na masarufi sai daya jibgesu a kujerar baya tana kallonsa. Wannan karon ma musbahu yana zaune shi kadai a kofar gidansu fatima kan benci, khalifa yayi parking, sakinbaki yayi yana kallonsu har suka fito tashige cikin gida dasauri yayin da khalifa yashiga kwasar kayan da zai iya, yakira wasu yara suka dinga deban buhunhunan shinkafa da kwalaye suna shiga dasu, duk wani abu na kurewar jin dadi a fannin ci da sha khalifa ya siye shi ba kadan ba. Inna tana tsaye a tsakar gida tana kallon ikon Allh ana ta jibge kayn tatmbayi yaran sukace khalifa ne yace a kawo. Fatima kam daki tashige, xuwa chan dr. khalifan yashigo inna takarbe shi da fara'a zuwa rumfarta "duk dawainiyar da ke damu bata isa ba si anyi wata. Yace "don Allah kar ku damu inna ni dai fatana a yi mana addu'a. Tace "addu'a kam dare da rana bata yankewa daga bakinmu, Allah yai muku albarka, Allah yara ba ku da duniya lafiya,Allah yaraba ku da sharrin makiya da mahassada. Khalifa yadinga fadin "amin amin inna ngd. Yana son magana ya kasa bayyana wa inna abi? dake tafe dashi ya dan jima zaune shiru daga bisani yayi mata ama yafice daga gdan. Malam misbahu yavishi da kallo zuciyarsa ckin matsanancin kishi da kunci, me khalifa da fatima ke nufi dashi ? saura kwana takwas kachal yarage a daura musu aure amma yana jan fatima a mota yana fita da ita a mota, ba Khalifa ne abin mamaki ba fatin ce, kowa ya san ta da kyawawan dabi "u ya za ayi akan khalifa tasauya lokaci daya haka ? Yatuna yadda sukayi da ummin dazu a gdansu Khalifa lkcn da yayi ta rokon ta da Allah tafdi masa abinda tasani game da mu'amalar fati da Khalifa ,ya hadata da girman Allah akan kada taboye masa gskiar abinda tsani. Ummi dakyar ta iya rike kanta a lokacin itama ta kanta take ji ta fi musbahu shiga tashin hankali, jin cewa wai dr. khalifa da fati sun fita a mota ina za su ? meye dalilin fitar ta su ? da wace manufa fati tabishi ? shin ta bi shi ne dan taci gaba da jan ra'ayinsa akan yaso ita ummin ko Khalifa ya ja ra'ayin fatin ne ta fara son shi ? abubuwa da dama suka dawo mata game da yanayin jikin Fatima dake sanyi a duk lkcn da suka kebeda Khalifa idanuwan ta sukan yi jawur me yakawo. haka, itama lallai tana bukatar wadannan tambayoyin da gaggawa. Wannan tunanin ne yahana ummi magana ga musbhu ya tsareta da ido hnkalinsa a tashe yana ckin fargaba, da. kyar ta iya bude baki tace mishi "kayi hakuri fatin tadawo zanji ta bakinta. Kina nufin baki san komj ba ? Kadafa ki manta na hadaki ne da girman Allah. Tace "ban ce maka ban sani ba kayi hakuri akwai wasu bayanai danake son tattarawa xan gaya ma gskiyar dana sani amma ba yanzu ba. Dakuar ummi ta lallabashi yahakura yatafi, tunda yadawo gida yakasa zaune yakasa tsaye, tunaninsa me fati da khalifa suka fita yi a mota? kuma fatin tana ganin shi a tsaye ko kunyarsa bataji ba suka wuce meye hadin ta da khalifa? har zaiyi wa inna maganar yaga bai dace ba, shi ne fa tun da yafito waje yazauna bai iya tashi ba har su fati suka dawo, ganin dukiyar da ake shiga da ita gdan yakara rudewa, ga fati ta wuce ko sannu batayi masa ba yadinga fadin "Lahaula wala kuwwata illa billahil azim. Babu tunanin da bai yi ba a wannan lokacin hnkalin sa ya tashi sosai. A DAREN FARKO 24 A rikice ummi tashiga gdansu tazube a gaban hajiyarta hauwa tana shaida mata cewa ga dukkan alamu fatima za ta ba wa khalifa hadin kai, ra'ayinta ya fara karkata gare shi. Hajiya tace "to ai dama ke ce kika yarda da ita, fatima karya take tace za taki khalifa akan wannan musbahun, wa yaki dadi? ballantana daula irin ta gdansu khalifa ga shi dan gata, ke ce baki da wayo yaudararki kawai take tana gaya miki cewa za ta taimake ki yasoki, soyayyarsu suke yi, dan kada kijuya mata baya ne take miki haka, kinga dai ke ce kika wayar wa da fati kai amma tafi ki wayon, iya zaman duniya da mutanan ckinta. Ummi ta jinjina kai tare da cije lebe tace "Amma lallai fatima ta tafka babban kuskure idan har ya tabbata yaudara ta tayi bata yaudareni ba kanta ta yaudara, do min kuwa sai na nuna mata cewa duk wanda yariga ka bacci sai ya rigaka tashi ba zan barta ta mallaki khalifa ba, domin ban cancan ci yaudara a gun fatima ba. Hajiya tace "to ki dai san abin yi bai dace wannan wahalar damuke sha yatashi a banza ba. Tace "karku damu in dai ban samu khalifa ba to na hakura dashi to bbu wacce za tasame shi ko zan rasa raina na amince akan khalifa. Ta fiddowa hajiya guzurin kayan data yi musu itama tace abban khalifa ya aiko mata da kudin don haka suka yiwa gdan malam tsinke da tsakiyar rana. Hajiya ta jadadda masa cewa ayi wa khalifa aikin da uwarsa ma bata isa dashi ba sai ummi, tace "malam muna so mu mallake shi shi da dukiyar tasa gaba daya data uban. Malam yayi dariya yace "ai kar ku damu tunda kuka kawo wadannan abubuwan ai an gama. ku sa ido za kuga yadda khalifa zai zamo a hannunku. **** Kwance take laga laga tana cike da tsananin shaukin jikin dr. khalifa da son jin muryarsa,komi na ta ya suaya fatima ta tsinci kanta a wani irin sabon yanayi na bukatar rayuwa,tunda take rayuwa a duniya bata taba jin abinda taji yau ba game da Khalifa,, kamshin sa har yanzu yana tare da jikinta, kyakyawar surarsa tadinga gani a idonta, ta hasko mijin da za ta aura rana ita yau musbahu, nan take taji ta tsane shi, daman bata taba jin tana son shi ba biyayya biyayya ce kawai. Lallai a yau ta fuskanci meye so, don kuwa ta samu kanta cikin irin yanayin da ummi ke bayyana mata tana shiga a kan soyayyar khalifa. khalifa kam ya isa miji abin so da burgewa . Tamike zaune tazuba tagumi shin yaya za tayi da musbahu da ummi, ko shakka ba ta yi a halin yanzu tana son Khalifa kuma shi za ta aura, musbahu da ummi fa? mutane ne masu kima da daraja a idonta me za tace dasu? Duk bata san inna ta dade tsaye a kanta ba sai data yi mata tsawa tadago da sauri ta dubeta, a fusace inna ta tsare ta da ido tace "tunanin uban wa kike tun dazu nake tsaye akan ki ina magana? Fati tayi shiru takasa magana, inna ta jinjina kai tace "tabdijam amma kina da jan aiki fatima, da can wani namiji bai ja ra'ayinki ba sai yanzu, yau din nan fa za a fara rabon goron bikinki, to karkace kunnuwanki da kyau kiji idan ma son khalifa kike to kishiga taitayinki, kisan abinda kike, kinsan dai mu ba kwadayayyu bane duk abinda iyayan khalifa suka mana mun gode ba za muce bamu gode ba amma dai ba rokonsu mukayi ba ba za mu kai kammu inda Allah bai kai mu ba, dan mu tsira da mutumcin mu, ni kaina na gamsu duk abubuwan da iyayan Khalifa ke mana sunyi ne don Allah to amma mutanan dake gefenmu kallon kwadayi suke mana, kin ga dai su suka ja mu a jiki amma yanzu da zarar an ji wata magana ta fito fassarar kwadayin nan za a yi mana, sbda haka kisan abinda kike kada ki soma daukar dabi'ar da ba ta ki ba ki sa wa ranki wahala, kitsaya a matsayin da Allah ya ajiye ki sai ki zauna lafiya. Bayan fitar inna, fati tayi shiru tana tunanin maganganun inna, wadanda akan hanya da gaskiya suke, sai dai kash zuciyarta ta kamu da soyayya farat daya hankalin ta da tunanin ta sun dawo kan Khalifa, tana jin sa a ko ina a jikinta. **** Ummi da hajiyarta da hajiya saude sun dawo gida zuciyarsu cike da tabbacin abinda malam yagaya musu zai auku har tadinga jin kamar ma ta mallaki khalifan ne, sai fatima ce dai a ranta ita ke daga mata hankali. Takira jiddah a waya ta gaya mata abinda ke cigaba da faruwa. Jiddah tace "ummi in tambayeki mana" Tace "Allah yasa na sani. Tace "wai shin dama a baya khalifa bai taba wata budurwa ba sai fatima? mesa za ki daga hankalin ki haka akan fatima? bayan kina sane da cewa duk inda yake "yammata natare dashi. Ummi tace "ke jiddah tsaya kiji duk wata 'ya mace dake tare dashi ita ke nace masa bai damu dasu ba fatima kuwa shi yake sonta, tarihin rayuwarsa ba macen daya ke nunawa zai shiga kowani irin hali a k anta sai fatima, wannan al'amari yana matukar daga min hankali da ba ni tsoro jiddah. Jiddah tace "kai wani irin soyayya ce wannan? ko da yake fatin da khalifa duka ababen so ne, hakika ba abin mamaki bane dan namiji ya shiga kowani irin hali akan fatima, wannan yarinyar Allah ya hore mata kyau me shiga zuci, sannan khalifa Allah ya hore masa kyau na daukar hankali, fatima za ta iya kamuwa da son khalifa haka Khalifa zai iya kamuwa da son fatima fiye da duk yadda kike kwatantawa, amma shawar da zan ba ki itace kiyi hakuri kiyi hakuri idan Allahyakaddara fatima matar khalifa ce kiyi hakuri kiyi hakuri Allah yabaki wanda za kifi so fiye da son da kikewa dr. Khalifa. Tace "jiddah idan nahakura ya ya zanyi da son danake wa dr. khalifa? Tace "ummi tun a fari ni ce na sa ki a hanyar ki so khalifa, amma hakan bai hana a yanzu in ba ki shawarar kiyi hakuri da Khalifa ba sbda maslahar zuciyarki, ummi yanada kyau kisani duk abinda Allah bai kaddara makasamunshi ba ba za kataba samun na sa ba har abada sbda Allah ya kaddara ba rabonka bane, kitsaya akan wannan don ki zauna lfya. Ko kusa shawarar jiddah bata samu karbuwa a zuciyar ummi ba, domin abu ne da ba zai taba yiwuwa ba, ji take har gwamma ta sallamawa wata khalifa in da za ta iya yin hakan akan ta sallamawa fati. Su hajiya ma sun tsaya tsayin daka akan sai ummi ta mallaki dr. Khalifa ko da yake su dukiyarsa kadai suke kwadayi. Dab da sallar magriba ummi ta iso gdansu khalifa, ta iske shi suna alwala tare da dr.bashir ,ta tsaya suka gaisa abin mamaki fara'a ce karara a fuskar khalifa yana fadin "yawwa kanwata daman ina son ganinki, bari in dawo daga masallaci. Ta shige gida cike da zargi iri iri a zuciyafmrta, musamman ganin yadda fatima tadaina neman ta ko da a waya ne, tabdijam ckin dakin mama tafara shiga ta iske ta ta tayar da sallah ita dayake ba sallar za tayi bata watsar da jakarta da mayafinta tazauna gefen gado tayi tagumi. Mama ta idar da sallah tazuba mata ido tace "sai yanzu ? Ta sauko kasa suka gaisa tace "mama yaushe rabon fatima da gdan nan ? Tayi murmushi tace "ai fatima ta dauke kafarta daga gdan nan ne sbda mun zamo surukanta. Tace "kamar yaya mama ? Tace "uhm kina nufin baki san meke faruwa ba ? Tace "mama idan ma na sani ina bukatar karin bayani daga gareki. Mama tace "ummin hankalina a tashe yake domin abbanku ya goyi bayan son zuciyar da khalifa yazo dashi karara bayan ya san hakan bai cancanta ba. Bakin ummi na rawa tace "mama kina nufin abba ya goya ma khalifa baya ya auri fatima. Tace "wannan shi ne damuwata. ina tsoron kallon da mutane za suyi mana musamman kasancewar musbahu talaka khalifa me kudi abin da kowa zai ce shi ne anyi amfani da dukiya gun dannewa musbahu hakki don ba shi da dukiya, ya kamata abba ya takawa Khalifa burki yanunamasa jan ido tunda ba shi za ya daurawa kansa auran ba, dole yahakura amma ya ce ba xai hana shi yin abinda ba ya so ba ina jiyewa khalifa rayuwar da abba yasa shi bai san bbu ba bai san yanemi abu yarasa ba sai dai duk abinda yanema sai ya samu, wace irin rayuwa ce wannan ? idan khalifa bi san rayuwa ba yanzu sai yaushe zai sani ? Cikin nauyin baki da takaici ummi tace "mama to ke kin amince ? Ta amsa "to yaya zanyi ummi ? ina da ikon yiwa abba musu akan wani abu daya tsara akan khalifa ? Ummi tajinjina kai a zuciyarta tace "gaba dayanku kunyi kuskure wato cikinku babu wanda yadamu da damuwata sai damuwar danku ? Hakika son zuciyarku da kanku ya zame muku damuwa daman ance son zuciya bacin ta. Tabude baki za tayi magana wayarta tafara ringing, khalifa ne tadaga yace da ita "taho mana da abinci mana dakina. Ta tambayi mama abincin na su tace yana kan tebur. Wani iri ummi take jin zuciyarta kamar ba ita ba, tadauki abincin tanufi dakin na sa, bayan ta zauna Khalifa yace "ina kawar ta ki ? Tace "fatima. Yace "eh. Tace "ai ina zaton a halin yanzu ka fini sanin inda take tunda ka fi ni kusa da ita. Yace "um um ummi ba haka bane kina da matsayi babba a gun fatima koyaushe tana maganarki da kokarin ganin ta nema miki mafitar da za ta haifar maki da kwanciyar hankali,kada wani abu yarufe miki zuciya ki zargeta da abinda bai dace ki zarge ta dashi ba. Gaba daya taji takaici da bakin ciki sun kara rufeta maganganun sa kara mata damuwa suke, meye amfanin abunda yake fada mata kan ftima, tamike da niyyar tafita yakira sunanta yace "zauna. Takoma ta zauna tana kallon sa yace "ummi ya zamo dole in miki godiya domin kin taimaka min akan fatima, zuciyarta ta karkata a gareni ta amince ta amshi soyayya ta duk da cewa wasu abubuwan suna firgitata wadanda sune suka hanata sakin ranta sosai tabani hadin kan daya dace, ina miki godiya ne ummi sbda kin taka muhimmiyar rawa akan hakan. Tayi masa wani irin kallo cike da mamakin abinda yake gaya mata, ba ta son tayi kuka sbda lokacin kuka ya wuce gareta, ta dade tana kuka akan khalifa lokaci ya yi da za ta daina kuka, don da ace kukan zai mata maganin damuwarta da ya yi abinda yadace da ita shi ne tanema wa kanta mafita kawai ko ta wani hali, tadubi khalifa tace "a takaice daikwalliya ta biya kudin sabulu fatima ta amince da soyayyar ka ko ? Ya amsa "eh hakane abu guda daya zuwa biyu ne damuwarta ke da musbahu tana jinjina yadda za ku kalleta, shiyasa nakiraki yanzu dan in roke ki kinunawa fatima ba komi kuma kisaki ranki sosai da ita kamar yadda kuke rayuwa a baya, yin hakan ne kawai zaisa ta kwantar da hankalinta tabani hadin kan danake bukata. Kai khalifa da wauta yake. Abinda ummi ke fadi a ranta knan ko da yake gani yake ya fi karfin komi tabbas khalifa ya rainata, shi yasa ko wani irin danyar magana sai ya tareta da ita to kuwa za ta shayar dashi mamaki daga shi har fatima da iyayansa masu son zuciya. A fili kuma dubansa tayi tace "karka damu zanyi yadda kace. Yayi murmushi yace "nagode ummi zan miki kyauta mai ban mamaki". A DAREN FARKO 25 Tsakiyar dare ummi ta kasa barci tana tuna abubuwa iri iri ta saka wancan ta kwance, tun tana ganin auran fati da khalifa ba mi yiwuwa bane har nesa tafara matsowa kusa, abinda ya faru da karfe goman daren yau ne yatabbatar mata da haka. Wato ta zo za ta shiga dakin mama ta tsinkayi muryar mama da anty sadiya suna hira da daga murya soai, anty sadiyance take fadin "to wai mama idan Allah ne yakaddara fatima matar khalifa ce fa ? kin san dai babu wanda ya isa ya shirya wannan al'amarin sai Allah ko ? tunda ita kanta yarinyar ta amince to meye na damuwa ? kin san babu yadda za a yi abba ya sauya ra'ayinsa, kada ki jawo abin da zai zamo na rigima. Mama tace "haba sadiya yanzu ko a hankalce wannan ya yi dai dai, da kunyar son da ummi ke masa zanji ko da malam musbhu. Anty sadiya tace "duk ki kwantar da hankalinki ki kaddara cewa Allah ne yakaddara faruwar hakan ki toshe kunnuwanki daga duk wani surutun mutane idan kika biyewa mutane babu wani abun alherin dazaki kulla a rayuwarki, ki kyaleshi ya aureta Allah yasa haka shi yafi alheri itama kuma ummi Allah yabata wani haka shima musbahun. Abin da ummi taji mama tafada ne takara tsinkewa da al'amarin cewa tayi "sadiya ni ma na fi son Khalifa ya auri fatima fiye da kowacce mace, sbda tarbiyyarta da nagartarta, na san inaha Allahu za yi alfahari da auranta, Allah yasa haka shi yafi alheri. Anty sadiya tace "to Alhajin ya yiwa mahaifin fatiman magana ? ni na fi son ayi komi a gama hankalin kowa yakwanta. Mama tace "eh da magribar dazu ya ce idan yafita masallaci zaiyi wa malam maganar zan tambaye shi in ji yadda sukayi, na san dai da wahala in za su ki. A hankali ummi taja jikinta tadawo dakinta zuciyarta na azalzala mata tamkar za tafashe, tabude wayarta ta binciko wani kyakyawan hoton khalifa data faki idonsa ta dauke shi bai sani ba tadauke shi a falo, yana sanye da kananan kaya dasuka matukar karbar jikinsa, murmushin da yayi ya dada kayatar da kyaun hoton. wata rana tazauna tazubawa hoto ido, fatima ta iso kanta bata sani ba, ta jima tsaye tana kallonta ganin bata motsa ba fatima tazare wayar tana fadin "wa ki ke kallo haka ? Ummi tamike takwanta bisa gado tana dariya tace "wa kika san zan kalla in banda sahibi na. Fatima tadubi hoton tace "yayi kyau kam amma zan ba ki shawara. Tace "tame fa yar kawata ? Tace "ummi ina matukar jin tausayinki game da al'amarin khalifa, kina sonsa da yawa kada ki ja wa kanki wahala yayin da so ya tsananta a zuciyarki don Allah ki dinga bi a hankali yadda za ki iya daukar duk abun da zai faru me dadi ko akasin haka. Murmushi ummi tayi tace "hakane fatima amma za ki iya fada min dalilin dayasa kika min wannan nasihar ? Tace "ba wani abu ne yasa nace haka ba illa la'akari da yanayin khalifa anya wannan zai tsaya kan mace guda daya ? idan ma bai ce yana so ba sai ance ana son shi, wata rana idan bai amince ba watarana zai amince amfanin shawarar dana ba ki itace idan kin bi komi a hankali sai komi yazo miki da sauki. Ummi tace "fatima wai don Allah kina ganin zan samu dr khalifa. Tace "ummi wannan lamari ne na Allah babu w ? da ya isa ya yanke hukunci sai shi, za ki iya samun sa za ki iya rasa shi, ba komi mutum yake nema yasamu ba Ummi ta rausayar da kai tana dan murmushi tace "fatima don Allah idan ke ce xa kiyi hakuri da khalifa akan soyayyar danake masa ? Fatima tayi dariya sosai tace "ummi kin ganni nan wallahi har yanzu ban san meye so ba. Ummi tafiddo ido "fati wace irin magana ce kike haka ? meye matsayin musbahu a gunki knan idan dai baki san meye so ba. ? Fati ta tabe baki tace "musbahu zabin iyayena na, ba na fatan ganin ranar da zan sabawa umurnin su, shi yasa na tallafe shi hannu bibbiyu kuma na yi damarar rike shi da kyau in dai batun so za ayi to ban san me akeyi idan ana son mutum ba. Ummi tace 'Don Allah dr. khalifa ya taba birgeki ? Tayi mata wani irin kallo tace "ni dai na yarda har zuciyata khalifa ya isa namijin da za a so shi, ko da nace bn san so ba, na san cikakken namijin kuma na san namijin dazan kalla in ce ya hadu, shi yasa ba ni ganin laifinki don kina damuwa da khalifa face ina jan hankalinki don ki dauki komi dasauki... Ummi ta buga kwafa, lallai ba abin mamaki bane don fatima ta amince ta amshi soyayyar khalifa, sai dai ita tana tausaya mata don ba karamin kuskure tayi ba. A DAREN FARKO 26 Ba karamin tashin hankali inna tayi ba lokacin da fatima da kanta ta zauna tana yi mata wani mamaki wanda yabata mamaki, kallon fatin take kamar ba ita ba, tun tana fada har ta dawo yi mata nasiha amma fati ta murje idanunta kukan da take ma yau batayi ba don tsakaninta da Allah so take inna ta amince da abinda take fada mata. Inna tayi tagumi tana kallonta tace "maimaita min abinda kika fada. Fatima tace "inna kiyi hakuri ni na san wannan magana ba za tayi muku dadi ba amma kuyi hakuri ku karbeta a matsayin abinda Allah ya kaddara mana ni daku, inna don Allah kiyi hakuri kada kuyi fushi dani nima ban taba tunanin zan bijire wa auran malam musbahu ba sai a wannan lokacin dana samu kaina a cikin yanayin da ban taba tsammaninsa a gareni ba, tayi shiru ta kasa ci gaba da magana ganin yadda inna ta tsareta da ido kamar za ta shaketa. Fuskarta a tsuke alamun fushi da zuciyarta ke ciki, jin shirun ya yi yawa inna tace "kici gaba mana tunda bakiji kunyar fara fadar wannan maganar ba ba wani dalilin dazai sa kiji kunyar karasawa. Kan fati na kasa bakinta ya mata nauyi ga maganganu na cinta ta kasa karasawa bayan ta zauna a gaban innar ne cike da azamar fada din sbda ance barin kashi a ciki bai maganin yunwa. A daran jiya ne da barci ya gagari idanuwanta ta kwana tana juyi kamar zuciyarta xa ta tsage, ta yanke shawarar idan gari ya waye za ta tari inna da maganar duk abinda zai faru yafaru, itama a halin yanzu tasan meye so ta san abinda ake nufi da ciwon so. Bayan tayi duk sallar asuba tazauna shiru tana tunanin ta yadda za tadubi tsabar idon inarta ta shaida mata cewa su yi hakuri su bata khalifa shi take so, ba wata manufa data wuce hakan amma akwai tashin hankali mai yawa a cikin al'amarin da ban tsoro, iyayanta suna matukar kaunar musbahu kamar su suka haife shi, ba sa wasa da abinda ya shafe shi, kamar yadda shima yake matukar sonsu da kula da al'amarinsu, ko da su suka haifeshi ba zai yi musu biyayyar da tafi haka ba ko da yaushe malam yashiga yafita maganarsa musbahu, duk abinda za ayi a gdan musbahu ne zai ce yayi, shi kuma ba ya kasa a guiwa gun aiwatar musu da abin da suke so ko meye shi kuwa, in dai ba wanda yasani ba ba mai cewa musbahu ba dan gdan bane, ta ina iyayanta za su amince da damuwar musbahu, damuwa kuma irin wannan. Idan fatima takalli girman son da takewa Khalifa sai ta tuna matsayin musbahu a gun iyayanta ba karamin tashin hankali bane a yanzu tace zata juyar da ra'ayin iyayanta daga auran musbahu zuwa khalifa. Tana cike da wannan rashin kwarin jiki da karayar zuciya taci gaba dakulla shawarwarin yadda za ta tunkari inna da maganar kafin ma malam yaji wanda yafi kowa son musbahu. Da gari yagama wayewa tafito tsakar gida duk sanda suka hada ido da inna sai gbanta ya fadi, lokaci lokaci takan faki idon inna tagoge kwallar dake taruwa a gefen idonta, innar ce tagaji takira ta daki tazaunar da ita tace yau sai ta gaya mata abin dake cin zuciyarta wanda yasa tadaina walwala. Ta mayar da kanta kamar bakuwa a gdan, da farko shiru fatin tayi tana sharar kwalla, inna tace "uhum ta yaro kyau take ba ta karko, babu abi ? da zai sa ki tashi a gun nan sai kin min bayanin abinda ke rufe min zuciyarki.... A kofar gdan malam musa, Alhaji muhammadu mahaifin khalifa ne zaune kan tabarma, shima malam din suna hira, musbahu yafito musu da kunun ayar da inna tahada musu yayi sanyi sosai yana ta kamshin kayan yaji, suna sha suna ci gabada hira. Abba yana son gayawa malam abin da ke tafe dashi kunya ta kamashi yarasa ta ina zai faro maganar, bai yi tunanin zaiji nauyin maganar da take ta damun zuciyarsa ba, bai san me xe ce da Khalifa ba idan yakoma gda a haka har suka gama hirar yabar gurin zuwan gdansu, ai kuwa khalifa ya iske shi a falo tare da mama ta tare shi da tambayar "Abba ya kuka yi da malam din!? Ya fidda babbar rigarsa da hula ya ajiye yazauna. Khalifa naje na kasa gaya masa, ban san dalili ba naji bakina ya rasa yadda zai furta maganar khalifa me xai hana ka daure kayi hakuri komi na Allah ne. Mama tayi farat tace "yawwa abba don Allah kadinga nuna masa hakan irin wannan son kan ba shi da dadi. Khalifa ya kwantar da kan shi a jikin kujera yace "abba ni zanje dakaina in sami mala.m din in gaya masa, ni bakina ba zai ji kunyar fada ba, wannan yarinyar ba zan taba iya hakura da ita ba a rayuwata don Allah kuyi hakuri ku ci gaba da tayani addu'ar Allah yasa auran fatima alheri ne a tare dani. Yamike zai fita abba yace "kayi hakuri kar kaje zan kara yin tunanin akan al'amarin. Murmushi yayi yafice. Yana fitowa harabar gdan yakira fatima a waya yanayin dayaji muryarta ya tabbatar itama tana fama da damuwa. Bayan sun gaisayace "a ina zan ganki? "kazo gdammu kawai ina son kowa yatabbatar ina snka kuma na amince dakai. An gama gimbiyar mata. Inna da malam, zaune a tsakar gida suna hira ,khalifa yayi musu sallama, cikin fara'a sosai suka amshe shi ya tsuguna suka gaisa nan da nan kamshin turaransa ya game gdan, farar shadda ce a jikinsa sai walwali yake, yace "inna yaya naganku a duhu? Tace "khalifa ai ka san ba kullum suke kawo wutar ba? Yace "ba injin a gdan nan? Sukayi shiru, yace "idan Allah ya kaimu gobe za a kawo muku injin. Malam yace "Don Allah khalifa kudaina mana hidima haka abin ya yi yawa. Yace "haba abba meye amfanin arzikin da ba za a taimaki al'umar musulmi dashi ba, mu dai a dinga sanya mu cki? addu'a yanzu ma bukata nazo da ita gareku. Malam yace "in dai bata fi karfinmu ba insha Allahu za muyi maka kai da mahaifinka kunfi karfin komi a gdan nan. Kansa na kasa yace "baba dazun abba ya zo gdan nan da nufin isar da sakon dana turo shi dashi gunka amma ya koma yace min ya kasa gaya ma, shi ne ni nazo in fada maka kuma in roko alfarmarku. Malam musa yayi murmushi, "amma alhaji ya ba ni. mamaki yanzu har akwai abinda zai ce yaji nauyin gaya mana, ni dashi ai mun zama daya fada min khalifa ko meye in dai mallaki na ne zan maka shi. Khalifa yaji sanyi a ransa guiwarsa takara karfi yace "baba auran fatima nake son kabani. Gumi yashiga karyowa malam kansa na kasa yayi shiru yakasa magana, itama innar shirun tayi yayin da fatima ke cikin daki a zaune tana jiyosu sai gabanta ke faduwa. Zuwa can malam yadago kansa yace "ikon Allah, khalifa ban taba zaton bukatar da za kazo min da ita ba knan, ko dayake ba abin mamaki bane don ka so fatima Allah ne mai hada zukatan bayi su so juna kuma na ji dadi sosai na gode da son da kakewa fatima, amma ina ba ka hakuri na riga na ba da fatima, a inda ba zan iya karbota in ba ka ba, in banda haka wallahi zan ba ka fatima khalifa kayi hakuri insha Allahu za miyi ta maka addu'ar Allah yabaka matar datafi fatima. khalifa yayi shiru kansa na kasa lokaci lokaci yana sharar gumin da yake tsatsafo masa, gdan ma ya yi tsit kamar ba kowa a gdan, daga bisani yamike dakyar ko ina a jikinsa ya yi mai nauyi yace "to na gode baba Allah yasanya alheri. Malam yamike yabiyo khalifa kofar gda suka tsaya, malam yace "Abbakar ina matukar bakin cikin hanaka auran fatima amma kayi hakuri Allah ne bai sa matar ka bace, akwai abubuwa da dama da Allah kan jarrabi bawansa don yagwada imaninsa, idan yajure yayi hakuri sai Allah yamusanya mai da abinda yafi wannan alheri sakamakon hakurin da yayi da abinda Allah yajarrabe shi dashi. Duk kokarin da dr. khalifa yayi na mayar da hawayen da suka taru a idonsa don kada malam ya gani abin yaci tura, domin sai da yadinga sharar kwalla yana jan numfashi da kyar, daga karshe kasa ci gaba da tsayuwa yayi sai durkusawa yayi, hankalin malam yatashi sosai tun yana iya magana har yayi shiru ya zurawa khalifa ido, yaji tausayinsa a wannan lokaci ,tausayi mai tsanani, zuwa can khalifa yatashi yatafi gida ba tareda yakara cewa da malam komi ba. Malam ya jima yna kallonsa sannan yashige ckin gida ya iske inna itama na ta jikin a sanyaye, yazauna yace "kai yaron nan dagaske yana son fatima. "Itama tana sonsa malam ". Inna tafadi tana kallonsa. Yace "wane irin tana sonsa kuma da maganar musbahun a kanta take son wani. Tace "wallahi kuwa fatima ta yi abinda ban taba zato ba a yanayin rayuwarta, tadubi idona tace a yanzu ita khalifa take so tana son mu fasa ba musbahu auranta mu bata shi in bar da tana son sa za tayi haka? tunda tagaya min wannan maganar jikina ke rawa hankali na yatashi sosai, ni dai yin wannan rana na yi shi ne kawai amma zuciyata tana cike da sarkakiya da damuwa, sbda fatima ta ban mamaki ta ba ni tsoro, duk abinda fatima za ta budi baki tayi magana akansa ba karami bane, tana da kunya sosai da zurfin ciki, tunda harta iya magana to da gaske tana son khalifa, yawan kukan datakeyi shi yake dada dagan hankali har na rasa yadda zan bullowa lamarin. Malam yace "amma wannan zancen banza ne, ni za ta mayar karamin mutum, sa rai da ci shi ke kawo jin yunwa in barda ta sa soyayyar ta sa ai ba za ta daga hankalinta akan shi ba, tun yaushe aka sa wa musbahu rai da batun auran ta, ya saki jiki itace matarsa kawai sai ta dawo tace ga wanda take so, a gun nan nafada mata idan ba ta son musbahu ba zan mata dole ba tace ta ami? ce, yanzu ya kike zaton mutane za su daukeni idan nafasa ba musbahu naba khalifa, kwadayi? Babu ta inda zan fidda kaina a gun musbahu da yan'uwansa dasauran jama'an gari na sayowa kaina zagi. Inna tace "wallahi malam ni ma ban goya mata baya ba don na san son zuciya ne karara tazo dashi. Haushi yakara kama malam ya kwalawa fatima kira, tafito tana rabe rabe ta tsuguna ybuga mata harara yace "na fahimci cewa ke ce kika ba khalifa fuskar yazo gdan nan yazo min da batun auranki alhalin kina sane da musbahu, kin ba ni mamaki fatima ban taba shakku akan lamarinki ba sbda biyayyar ki garemu kada ki bamu kunya kada kija abinda zai ja mana damuwa alhali muna zamanmu lafiya. Fatima tayi doguwar ajiyar zuciya tace "kuyi hakuri baba ni ma banyi tsammanin zan wayi gari ckin wannanyanayi ba, ni kam ina son khalifa don Allah ku ba musbahu hakuri.... "Salamu Alaikum Muryar musbahu knan, suka daga kai a razane suka zuba mai ido fuskarsa a cunku she yazauna jagwab kusa da malam muryarsa na rawa yace "Baba hakika na ji duk tattaunawar ku da fatima kuma na ji matsayina a gunku, ba ni da abi? da zan ce muku sai godiya, kyautatawar dakuka mini Allah ne zai biyaku domin don shi kukayi. Baba na san ina son fatima soyayyar da tasa nake jin cewa idan na rasata zai wahala in yi aure domin bansan ta yadda za ai in so wata mace ba bayan ita, ko da yike komi na Allah ne amma wannan soyayyar danake mata ba za tasa in aureta alhali na san ba ta so na ba, kayi hakuri baba kaba fatima khalifa... Cikin zafin rai malam musa yace "yi min shiru musbahu, wannan yarinyar bata isa tasauya min ra'ayi ba, tunda tun farko da amincewarta aka sa bikin auran nan kadarra cewa ma ka auri fatima ka gama. Ranar da aka sanya za a daura wannan auran ba fashi, insha Allahu za a daura in dai ka ga ba a daura ba sai dai in ranar ce tariskeni ba na numfashi, za a daura auranku kuma za a kaita gdanka, a ranar tahadiya zuciya tamutu a kawo min gawarta. Musbahu yabude baki zaiyi magana malam yayi mai tsawa yace "in dai kaima ba so kake kabata min rai ba kayi min shiru, idan Allah yakaimu gobe kaje ka amso katunan daurin auran a kaiwa kowa. Yatashi yafice ,musbahu ma yabi bayansa, itama innar tashige daki tabar fatima tana kuka. Tunda take bata taba batawa iyayanta rai ba ballantana suyi fushi da ita sai yau, shin me ya shiga zuciyarta ne tasauya haka, a duk lokacin da ake magana, soyayyar khalifa ce take karuwa a zuciyarta, kamar ana hura mata wuta, idanuwanta suka kada jawur tarasa yadda za tayi da ranta. Soyayyar dr. khalifa ta gama rufe mata zuciya ji take kamar ba xa ta iya rayuwa ba in ba shi, gabaki daya ta watsar da batun ummi ta kanta kawai take, tana ji a ranta in dai ta auri khalifa duk abinda zai biyo baya me suki ne, iyaka dai ummi tadaina kulata ita in dai tana tare da khalifa bukatar zuciyarta ta biya, matsalarta yanzu iyayanta wadanda sun dau zafi dayawa. Ta daga kai ta amsa sallamar musbahu, haushi yakara kamata tabishi da ido har yatsuguna gabanta yace "fatima. Bata amsa ba sai kallo yace "kiyi hakuri. Ta mike tashige ckin daki a zuciyarta tana fadin ai kai hakuri yakama ba ni ba. Musbahu yayi zaman dirshan a gun yazuba tagumi da hannu bibbiyu shin wani irin iftila'i ne yasa me shi haka?da can bai rasa fatima ba sai da yagama sakin jiki bai da mata sai ita, yakasa juriya yabita dakin na su, ya isketa a kwance tana kuka. Yace "fatima baki min adalci ba don Allah ki kwatanta idan ni nayi miki haka za ki so? a ce a irin wannan lokaci in ce na fasa auranki wata zan aura? Ya tsuguna a gabanta kamar mai neman gafara yace "don Allah fatima ki taimake ni wlh ba karamin so nake miki ba, ni ban isa in ce kwadayin duniya ne yasa kike son khalifa ba idan akwai kwadayi ba za ki tsaya akaina ba, masu kudi dayawa sunce suna sonki baki ba su hadin kai ba. Fatima batayi niyyar yi ma musbahu magana ba dan ita kanta ta san ba ta da abinda za tace musa, amma a bisa wannan maganar tasa da taji ya dace tace wani abu a kokarinta na samin mafita. Tace "Nagodewa Allah dayasa da kanka kayi min shaidar ba kwadayi yasa nace ina son khalifa ba, ka san cewa soyayya ce don Allah, ina son kayi hakuri kayi min adalici, soyayya Allah ne me sanyata a zuciya ba mutum ba. Ya katseta zuciyarsa cike da daci yace "fatima ki fito a gaban ido na kawai ki ce ba kya so na, khalifa kikeso, na gode fatima nagode. Yamike dasauri yafice yana goge hawaye. Fati tace "innalillahi wa inna ilaihir raji'un. A DAREN FARKO 27 izuwa wannan lokaci ummi ta tabbatar fatima ta daina yi mata aikin komai ita takewa kanta, ta fahimci soyayya suke shimfidawa da dr. khalifa ta gaske duk da cewa rigima ake tafkawa a gdansu, ga katunan daurin auren yau an fito dasu har an kawo na Abba gdan, a kalla kwana uku kachal a daura auran musbahu da fatima, har takaici da kishi ya yiwa ummi yawa, yaudara ita take fassara fatima ta yi mata tunda gashi ta fita hanyarta tunda gashi ta fita hanyarta gaba daya ko neman ta ba ta yi lallai mutum abin tsoro ne. Ta iso gdansu da katin daurin auran ta nunawa hajiyarta tace "to ai zance ma ya kare in dai aka mata aure aka kaita dakin mijinta ai dole khalifa ya hakura da ita duk maitarsa . Unmi tace "kayya dai hajiya khalifa yana son fatima in kinga abin da yake nunawa za kiyi mamaki. Tace "duk ihu yakeyi bayan hari shi zai bawa kansa auran na ta? ki kwantar da hankalinki malam yana nan yana buga mana aiki da kafarsa khalifa zai zo gdan nan. Ita dai ummi hnkalin ta ya ki kwanciya son da khalifa ke nunawa dmfatima kadai ya isheta takaici, ita ko kallon ta ba ya yi tamkar ba aiki ake yi a kansa ba. ***** Ummi ce take sha'aninta khalifa bai san an fara rabon katin auran fatima ba sai da yamma daya dawo daga asibitin su dr. hafiz ya iske katin a hannun abbansa, yana gama karantawa yazube a gun. Abba yatashi a firgice yana jijjiga shi tare da kiran sunan sa da karfi ina khalifa ko motsi baiyi ba numfashinsa yatsaya cak, abba yafita dagudu yakira mai gadi yace yazo sudauki khalifa ba lfya, mama da anty sdiya ma suka fito daga daki ganin yanayin khalifa yatashi hankalin kowa sun shiga dimauta, suka nufi wani asibiti mai zaman kansa har suka isa khalifa ko motsi abba salati yake yana fadin "shike nan Khalifa ya mutu akan son ftima na ga takaina. Likitoci suka amshe shi ckin gaggawa suka kaishi wani daki suka fara ba shi taimakon gaggawa, dakyar suka lallashi abba y tsaya a waje dan cewa yayi sai ya shiga dakin, gani yake kamar khalifa ya mutu, mama datake mace ma ta fi abba karfin hali, itatadinga ba shi baki tana nuna masa cewa ba mutuwa khalifa yayi ba, yadinga kai komo a kofar dakin ba likitan daya fito, yagaji yashiga buga kofar yana fadin "ku fito min da gawar khalifa na san ya mutu. Wani bakin likita dogo siriri yafito yaja hannunsa suka shiga dakin yaba shi kujera yazauna daf d gadon da aka kwantar da dr. khalifa yace "Alhaji duba kagani yana numfashi ko? Anan ne abba yayi doguwar ajiyar zuciya, ashafi fuskar khalifa zuwa wuyansa yaji sanyi kalau, numfashinsa yadawo normal amma lokaci daya yarame fuskarsa takara haske. Likitannan mesuna dr. mansur yadan rusuna kusa da abba yace"ka gamsu bai mutu ba ko? Yace "hakane amma nikam likita jikina na ba ni mutuwa zaiyi, khalifa ba zai yi dogon kwana ba a duniya... Dr. mansur yarufe me baki yace "haba alhaji ya za kadinga wadannan maganganun a matsayinka na musulmi? mutuwa daban ciwo daban, kayi hakuri mun sha kan matsalar khalifa dimuwa ce kawai takai shi ga shiga wannan halin in dai ku? yi kokarin magance masa damuwarsa shi knan komi zai tafi yadda yakamata. Su mama ma an ba su damar shigowa ita da anti sadia, gaba daya suka zubawa khalifa ido cike da damuwa jikinsu ya gama sanyi da al'amarin . Abba yagirgiza kai yace "hajiya wani irin tsari ne haka, shi knan akan mace mutum yadaga hankalinsa kamar zai bar duniya,ni wallahi har na rasa yadda zan bullowa al'amarin na khalifa tunda ga wanda iyayanta suka yiwa kawari na yi na yi yayi hakuri ya ki fahimta,ban taba ganin abinda khalifa ydga hankalinsa akan sa ba sai akan fatima, wacce irin soyayya ce wannan, daga ganin katin daurin aure. Mama tagirgiza kai tace "wallahi abba nima tunda khalifa yafara maganar yana son fatima hankalina a tashe yake, sbda yanayin daya ke nunawa abin fargaba ne, in an yi magana yace wai a kyale shi b a san abinda yake ji bane, to rayuwa za tatafi a haka, wani abun idan mutum yana so yana samu wani abun kuwa duk maitarsa da kaunarsa da abin ba zai same shi ba sai hakuri. To shi khalifa ji yake kamar ba zai ci gaba da rayuwa ba idan bai mallaki yarinyar nan ba,. Suka yi shiru kowanne idonsa kan khalifa, daga bisani abba yaja numfashi yace "wai yaya za mu bullwa lamarin nan ne? Mama tace "to yaya za muyi kuwa abba in barda muyi hakuri dole fa khalifa yahakura da fatima. Abba yace "kai hajiya a irin wannan yanayin, dubi fa yadda yake. Tace "to idan bamuyi hakurin ba ta karfin tsiya za mu ba shi fatima? ***** Ga dai lokacin biki ya zo gadan gadan amma gdansu fatima yanayin babu dadi domin kuwa ango da amaryar suna cikin damuwar dataja jikin kowa ya yisanyi babu mai walwala,Fatima ce zaune kan kujerar zaman tsakar gida da wayarta ta hannu ta kurawa sakon daya shigo wayarta ido zuciyarta na azalzala sako ne daga khalifa yace. Fatima soyayyarki xa ta hallakani bbu wani taimako daza kimin don Allah kiji tausayi na kada ki bari iyayanki su bawa musbahu ke wallahi na fi son ki fatima. Tagoge hawayen dasuka gangaro mata tayi ta maimaita sakon tana girgiza kai, ta tashi tashiga dakinsu tacimma katunan gayyata na biki da musbahu yakawo mata da la'asar din dazu, ganin idon katunan sun tsaru sun yi kyau amma ita bakin ciki ne yakara turnuke mata zuciya data gansu, ganin katunan yakara kusanto mata lokacin bikinta knan kuma lokacin rabuwarta da masoyinta dr. khalifa, kuma idan tayi wasa wankin hula na daf da kai mata dare. Shi kansa musbahun lokacin daya kawo mata katin sai da yabata tausayi, tana sallah yashigo yatsuguna bakin kofa kamar me neman gafara, data idar bata kalleshi ba tajawo pillow ta kwanta, a sanyaye yace "fatima ga katinan gayyatar. Tadube shi wani iri tace "to ajiye anan. Ya matso daf da ita ya ajiye, uace "ko kina bukatar wani abu daya danganci bikin? Ta ki magana sai da yayi ta mata naci sannan tace "Ni fa ba abinda nake bukata. Yace "shi knan sai anjima. Yamike yafita yayin da tabi bayansa da ido cike da takaici. Gabadaya dr. khalifa ya sauya mata yanayin rayuwarta, kafin dawowarsa tana zaune lafiya ba ta damuwa da komi babu abinda yake tayar mata da hankali sai daya dawo. Tun randa dr. khalifa yafara cewa yana snta bata kara samun kwanciyar hankali ba, gabadaya ya jefata a ckin damuwa da rudani kullum tunani, ta zamo abar tausayi akan kanta domin yanayin da zuciyarta ke ciki ba dadi, ba ta jin dain halin data sanya musbahu sbda babu abinda yayi mata, ya rayu yana tattalin abin da take so tun tana yar karama yake tattalin rayuwarta har maganar aure ta bullo a tsakaninsu, ya dauki son duniya ya daura mata kullum kamar zai lashe ta, ba ya son abinda zai daga mata hankali, kowa ya shaidi musbahu da kyawawan dabi'u ababan so ga kowacce mce, dari bisa dari ta amince da batun auransa, shi yasa bata tava kallon wani da namiji da sunan so ba, sbda ita dai yardar Allah kawai take nema a rayuwarta, bata taba damuwa da kyale kyalen duniya ba, bbu kwadayi ko son zuciya tsarinta, shi yasa tafiyarsu da musbahu yaxo daya svda shima akan wannan tsarin na ta yake tafiya. kowa yana kyautata zaton za su zauna lfya a dalilin kowannen su ya dauki rayuwa dasauki, iyayanta suna cike da murnar auran ba su da fargabar komi, sai da abin yazo daf dr. khalifa ya bayyana cikin rayuwarta shi knan zuciyarta tasauya. ***** A DAREN FARKO 28 Tana cike da jin nauyin musbahu, soyayyar dr. Khalifa ce take da karfi a zuciyarta shi yasa takasa tuna komi. A bangare guda da ummi, ummi ta taka muhimmiyar rawa a kanta ta hanyar nuna mata kauna da aminci na gaskiya takuma haifar da cigaba a rayuwarta, a daidai lokacin datake kokarin taimakon ummi don ta cimma kufurinta a kan dr. khalifa soyayyar khalifan yakama zuciyarta, wanda a wannan lokacin ne ta fahimci meye so tasan zakinsa da dacinsa kusan wahalar da zuciya ke sha akan ciwon so, tausayin ummi ya yawaita a zuciyarta domin ta dade tana fama da ciwon son khalifa, alhali ba ta da tabbas din komi a kansa, ga misali itama dayake son ta tanayin ciwo me zafi a rayuwarta na son sa ina ga ummi da ta tabbatar ba ya sonta ,kowannansu kam abin tausayi ne, ama dai ita ta fi zama abun tausayi tunda ita tana sa ran samun khalifa wani abu ne yake neman yi mata shamaki dashi, ummi kuwa dama tana sa rai ne tana cire ranta, tunda ta san bai karbi soyayyarta ba. Wannan shi ne tunanin fatima. ***** A bisa wani dan benci dake kofar gdansu fatima,musbahu ne zaune ya yi tagumi lokaci lokaci yana fidda nannauyar ajiyar zuciya wadda ke cike da damuwa da dacin rai,idanuwansa sun kada jawur ,yau so yake yi ma yayi kuka ya kasa, wai shin me ke faruwa dashi ne, da can bai fuskanci matsala da fatima ba sai yanzu, an ya ba mafarki yake ba, fatima ce tadawo ko ganinsa ba ta son yi, a baya ko yaushe in suna magana idan ya kutso mata maganar rayuwa takan bata rai tace ita kuwa me za tayi da wani namijin bayan ga zabin da iyayanta suka yi mata, ta kance k kwantar da hankalinka ba ni da abin da yafi iyayena in dai zuciyarsu za tayi haske to ni burina ya cika ba ni da damuwa . Ire iren wadannan maganganun suke ba shi cikakkiyar natsuwa da kwanciyar hankali, musamman a bisa la'akari da rayuwar fatima ba mai tsada bace in ban da haka kallonta kadai ya isa hnkalinsa yayi ta tashi sbda kyawun halittar da Allah yayi mata zai dinga jan hankalin mazan zamani kanta, to kuma si gashi abubuwa sun sauya a lokaci guda fatima tajuya masa baya khalifa take so, yadinga jin wani azababban kishi da takaici yana tafarfasa zuciyarsa kamar zaiyi hauka, iyakar tunanin sa bai san yadda zai bullowa al'amarin fatima ba haka zai aureta hankalinta na kan khalifa ya girgiza kai, inama sai da akayi auransu khalifa yadawo, da ba zai ganta bama ballantana yace yana sonta har yadaga mata hankali yadagawa kowa. Yashiga harar kwalla, sai yanzu yaji zuciyarsa ta yi masa dama dama daya samu hawayensa suka zubo, tabbas yana son fatima amma yanzu fati tsoro take ba shi "kukan me kake musbahu? A firgice yadaga kansa yadubi malam wanda yake tsaye a kansa yana kallonsa, yaci gaba da sharar hawayensa ba tre da y ce komi ba, malam yace "Biyoni ckin gida. Ckin sassarfa musbahu yake tafiya suka shiga dakin malam din suka zauna, yakara maimaita mai tambayar "kukan me kake? Muryarsa a dashe yace "baba ban san yadda za ayi in shawo kan fatima hankalinta yadawo kaina ba, ina jiyewa kaina tsoron abubuwa da dama game da fatima. Malam yace "musvahu ni ne fa na haifi fatima ni ne na yarje ma auranta, har a halin yanzu ina dada tabbatar maka da cewa in dai ranar daurin auran nan tazo ina raye ba zan daurawa fati kowa ba sai kai, to meye na tayar da hankalinka kan fatima in dai in dai tana ckin gdan nan tana karkashin ikn mu za a kaita gdanka kuma dole ne tayi biyayya gareka in har tana son zaman lafiya damu, ita kanta ta san ba na kwadayin abun duniya bana son zuciya a kanta kuma ba zan fa ra ba. ***** A son ran ummi tayi zamanta a gdansu kada takoma gdansu khalifa wai a tunanin ta hakan zai sa hankalinta yakwanta, ta huta da bakin ckin dr. khalifa da fatima ke haifar mata amma ina lokacin da dare yayi dare sai taji hankalinta ya tashi sosai khalifa kawai take bukatar gani. Tabdijan ashe dai tana da jan aiki a gabanta ace duk sanda ba ta gdansu hnkalinta ne zai ding tashi haka, knan va za ta iya rayuwa ba sai tana ganin khalifa? ta mike zaune zaman ya gagara tamike tsaye anan ma tashiga sunturi ta dauki wayarta tayi kiran nomban khalifa bai daga ba bata san abinda za tace masa ba amma dai in taji muryarsa watakila tasamu tayi bacci ta huta, in dai a haka xuciyarta za ta tafi tana da babbar matsala. Takira nomban fatima bugu daya fatima tadaga tayi mata sallama da siririyar muryarta, tace "fatima bakiyi barci ba? "Eh banyi ba. "Meya sa? Tayi shiru. Tayi murmushi tace "na san tunanin dr. khalifa ne yahanaki bcci, don Allah haka ne. Fatima tayi ta maza tace "Na san kin san haka ne unmi shiyasa kika fada. Tayi ajiyar zuciya tace "fatima da ma na san ba za ki iya kaucwa soyayyar dr. khalifa ba duk da cewa a baya na mi? ce har ckin zuciyata za ki taimake ni a kan dr. khalifa to sai ga shi kema.... Haushi yakama fatima ta tabbata soki burutsun na rashin abin yi ne yasa ummi ke mata wannan shiriritar dan haka takashe wayarta. Mamaki yakama ummi ta jima tana kallon wayarta wai yau ita fatima ke ma haka, bata ma da lokacin saurararta, hakika ya zamo dole ta dauki mataki mai kwari akan fatima. Da gari ya waye da sassafe ta tashi tayi wanka ko tunanin cin abinci batayi ba tashirya tace da mahaifiyarta "na tafi gdansu khalifa. Hajiya na zaune a kicin tana suyar wainar fulawa tayi mata wani irin kallo tace "wai me ke daminki ne ummi, abin ci ma ba za kidinga tsayawa kina cinsa ba sbda khalifa? wannan wainar ma sbda ke nake yinta na san kina sonta amma ki ce tafiya za kiyi? Tace "don Allah hajiya barni in tafi hankali na a tashe yake ko barci banyi ba jiya. Tana tuka mota tana wasi wasi a haka har ta iso gdan masu aiki suka tarbeta da mummunar labari a asibiti dr. khalifa yakwana ba shi da lfya, tayi saurin kiran nomban mama tayi mata kwatancen asibitin dasuke tafigi mota ta nufi can. Hankalin ummi yakara tashi ganin yadda taga dr. khalifa mike isa gado, yana wani irin bacci wanda ga duk alamun bai san a inda kansa yake ba, mamane zaune bisa dadduma a kasa sadiya a gfenta abban na zaune kan wata kujera dake gefen gadon khalifa yazuba masa ido kawai. Ta tsyguna ta gayar dashi tare da jajanta masa ciwon khalifa ta zauna kusa da mama tana tambayarta "me ye musababbin ciwon ne? Mama ta tabe baki tace "katin daurin auren fatima yagani. Ummi tafiddo ido gabanta na faduwa tace "don ya ga katin daurin auran fatima yashiga wannan halin? Mama tace "kwarai kuwa tunda muka kawo shi asibitin nan bai farka ba har yanzu, nasarar da akaci dai nu; fashinsa ya dawo dai dai sabanin lokacin da muka kawo shi dan ko numfashi bbu, ni zatona ma ya mutu. Jikin ummi yakara mutuwa murus takoma jikin bango itama tayi shiru har tarasa abin da za tace. Wato wannan soyayyar har ta kai zafin haka, ina aikin da malamin su yace zai musu mai zafi wanda yaci musu alwashin zai raba soyayyar fatima da khalifa da ta duk wata diya mace sai ita ummin,. Amma abin mamaki kamar karawa dr. khalifa soyayyar fatima ake, me malamin nan ke nufi knan, aikain yake musu ko yaudararsu yake" Ta jinjina kai a baya kam ta san dr. khalifa yana son fatima haka yanayinsa yanuna, to amma yau ne yadada tabbatar da soyayyar nan ba ta wasa bace duk inda ake tunanin abin ya wuce nan,fidda soyayyar fati daga zuciyar khalifa abu ne mai wahalar gaske. Tadubi mama tace "to yanzu me likitocin suka ce? Mama tace "cewa sukayi a samar masa da abinda yasaka a ransa yana so din idan ana son rayuwarsa. Tace "to wani mataki aka dauka? Mama tace "har yanzu bamu san abinda za muyi ba. fatima dai tunda ba mu da ikon ba shi ita ai sai hakuri . Ta jinjina kai tace "To Allah ya sawwaka bari inje gda in kawo muku abinci ko zai farka ya bukaci wani abu. Mama tace "ga abin cin nan na asibiti an kawo. Tace "ai khalifa ba zai iya cin abincin asibiti ba bari dai in dafo wani abun. Lallai dr. khalifa ya yi nisa ba yadda za ayi yaji kira, gdansu fatima tafara shiga sai ita kadai a rmfar inna tana fama da waya, inna tana dakin malam suna hiran bikin fatima. Ta amsa sallamar ummi ckin fara'a tamkar ba wani abun, tukukin bakin ciki yakara turnukewa ummi zuciya, tayiwa fati kallon sama da kasa lokacin datake ce mata zauna mana anty ummi. Tace "ba zama nazo yi ba zuwa nayi in tamvayeki ina amsar taimakon dakika dauka za kimin a gun dr. khalifa.? Nan fatima tarasa abinda za tace tayi shiru, ummi tace "dama na san bbu abinda za ki iya cewa, tunda ba ki da abin fada din kinyi amfani da damar dakika samu kinja ra'ayin dr. khalifa har soyayyar dayake maki ta kaishi ga kwanciyar ciwo, to yana asibiti bai san inda kansa yake ba a dalilin ya ga katin daurin auranki da musbahu, sai kije ki duba shi kafin yakarasa mutuwa. Tajuya za ta tafi fati tajawo hannunta tace "Don allah ummi kar ki tai zauna ki taimake ni nasamu kaina a wani irin hali. Wani taimako zan maki fatima? ni van taimaki kaina ba wa zan iya taimakawa? in kura na maganin zawo me yasa batayi wa kanta ba?. Fati na kuka tace "ai rai ba ta rasa motsi ummi tasaya kiji. Ta jingina da bango tare da rungume hannayenta a kirjinta tana kallon fatima, fati tace "a wane asibitin khalifa yake? Tace "idan za ki wuce muje. Gaba dayansu sun rasa abinda za su cewa junansu kowacce tana neman taimakon 'yar 'uwarta ne ,unmi tace "tunda baki da abin fadi nima na rasa abinda zan ce miki kisameni a gda zan hadawa khalifan abinci sai muje asibitin, dasauri tfice daga gdan. Yayin da fatima tanufi dakin babansu ta durkusa tashaida musu cewa za su je karbar dinkin tada mama tayi musu na biki da ummi, sukace a dawo lfya. Ta sauya kaya ko wanka batayi ba tafice daga gdan, musbahu na kallonta tashige gdansu khalifa ba shi da ikon yi mata magana sai kallo, fatima ta fi karfin sa yanzu. Ummi na kicin tana ta hada abincin cikin gaggawa, fatima ta yi zaune a falo tana ta kallon hoton khalifa gabanta sai faduwa yake, wani babban hotonsa ne yakewa mutum maraba da zarar ka shigo falon, murmushi yayi a hoton murmushin dayayi matukar kayatar da fuskarsa, takagu ummi tagama su tafi taga halin da masoyin ta ke ciki. Bayan ummi ta kammala komi a mota tashiga dakinta da niyyar yin wanka ganin ta jima bata fito ba a fusace fatima ta bita ckin dakinta tashiga buga kofar toilet din tana fadin 'haba ummi wane irin jan rai ne haka? kinsan fa jiranki nake. Ummi tace "to don kina jira na ba zanyi wanka ba, karki dameni malama asibitin ma ganin damar kaina nayi ko kin sani ne ba sai da na gaya miki ba. Fatima tarasa me za tace da ummi don haushi, kuma karin haushi ne yasa bata kara ce mata komi ba sai da tagama abinda take a toilet,sannan tafito tafara shiryawa,fatima takara fusata a karo na biyu tace "ummi idan ba za ki rakani asibitin nan ba ki gaya min in yi tafiyata. Ummi tarausayar dakai tana murmushi tace "yi hakuri taso mutafi. A cikin mota tafiya suke kamar wasu kurame, kowacce da abinda take fama dashi a zuciyarta, da suka shiga harabar asibitin tasamu wuri tayi parking fatima ta tayata diban kayan abincin suka shiga dakin. Abba ne yakama fara'a yana fadin "fatima ke ce da kanki? Kunya da tausayi suka kamata lallai abba na cikin damuwa ta tsuguna tagayar dasu tare da tambayarsu mai jiki, Abba yace "to fatima mai jiki dai ga shi nan sai yadda Allah yayi, soyayya ce mai wahalarwa ya hdu da ita, sai dai hakuri. Mama dai shiru tayi tazuba tagumi tana ganin ikon Allah, magana in dai ta khalifa ce abba ba ya kawaici akanta, yaci gaba da fadin "fatima dubi halin da khalifan yake ciki har yanzu bai san wanda yake kansa ba, ni wlhi ban taba ganin inda akewa mutum irin son da khalifa yake miki ba, ga shi ba mu da ikon bayar dake gareshi, shin yaya za muyi da wannan tashin hankalim. Kukan fatima yafito karara tana juya kanta mama tace "Alhaji bai kamata kadinga fitowa da fatima irin wadannan maganganun ba sbda aikin gama ya gama alkalami ya bushe, hakuri dai khalifa zaiyi Allah yatashi kafadunsa. Cikin sanyin murya abba yace "ai nima ba wani abu nace ba. Fatima tace "Abba don Allah karoki babna ya janye mganar aurena da musbahu yana jin maganarka tare da girmama bukatarka, wlh nima khalifa nake so. Mama tarike hannunta tace "fatima mun san kina son khalifa Allah ne bai kaddara Khalifa mijin ki bane shiyasa duk abinda yafaru yafaru, wannan son zuciya ne karara idan har muka nacewa iyayanki da rokon su bawa khalifa ke,sbda shima musbahun yana sonki ba ya son yarasaki, idan mukayi amfani da wata dama da muke da ita muka rinjayi iyayanki suka ba khalifa auranki bamuyi amfani da hadisin manzon Allah dayake cewa imanin dayanmu ba ya cika har sai ya kasnce mun so wa yan uwammu abinda muke so wa kanmu, sannan na biyu mutane za su zagemu don a zahiri munyi rashin adalci mu mun san iyayanki basu hana mu auranki dan kiyayya ba sai dan girman alkawarin dasuka wa musbahu. Fatima takara rikicewa da kuka tana kallon dr. khalifa take cewa wallahi mama ba na son musbahu, khalifa nake so, ba ina fadin hakan bane don a gabanku ne ina son shi ne kawai don shi ne ra'ayina na amsa wa iyayena auran musbahu a lokacin da ban san meye so ba, yanu na fahimci inda rayuwa ta dosa don Allah mama kutaimaka ku fahimtar da iyayena kada su dauran auran da ba na so xan iya shiga ko wani hali idan ban auri khalifa ba. Aka yi tsit dakin kukan fatima kadai ke tahi, ummi kallon iyayan khalifa da fati kawai take tana girgiza kai ta ji dadi da hawayenta basu zuba ba domin ta gaji da kuka lokacin kuka ya wuce a gunta illa neman mafita, son kai ba musbahu kadai ake naman yi mawa ba har ita gara ma musbahun da yake so ake kwace masa matr ana ta nanata yadda za ayi dashi ita kuwa ba wanda yadamu da damuwar ta idan ma mutuwa za tayi tayi ta mutu, wai fati ce ke kuka a gaban iyayan khalifa tana rokonsu ita dai tana son khalifa, takallesu gaba daya tagirgiza kai tare da cije lebe. Anty sadiya tace "mama kinga abinda nake gaya miki wai meye amfanin yin shirun da akayi alhalin an san halin da zuciyoyin yaran nan ke ciki. ya kamata ayi musu adalci, shi musbahu bai san aure nufi ne na Allah ba, a zaunar dashi a yi mas bayanin kudubi halin da khalifa ke ciki daga ganin fa katin daurin auranta yashiga wannan halin ina ga idan an wayi gari yasan an kaita gdan musbahu? Tagirgiza kai. Gaskiya mama a san abin yi kada fa azo ana nadamar da ba ta da amfani gara tun kafin lokaci yagama kurewa a yi wani abin. Abba yace "maganarki haka take sadiya tabbas a yau din nan zan bi hanyar data rage tarage don ganin ankawo karshen wannan matsalar wannan lamarin na khalifa ya fi karfin a sa ido dole a yiwani abin a kai. Kofar dakin tabude dr. mansoor yashigo tare da wata nurse a bayansa ya isa gaban gadon dr. khalifa yace "har yanzu bai farka ba. Abba yace "ai ko motsin kirki ba ya yi nifa in banda ina ganin numfashinsa da yanzu na ce khalifa ya mutu. Dr. mansoor yadaga hannun khalifa ya mayar ya ajiye, yadakko wata karamar na'ura yadaura mai akan kirji yana latsawa tare dasa wani abu a kunnansa, zuwa can yacire yajuyo yadube su gaba daya yakira sunan nurse din da ke tare dashi mai suna jamila yace "ki lura dashi sosai. Tace "ba damuwa sir. Yamaido ido ga abba yace"kuyi hakuri Alhaji insha Allahu khalifa zai samu lafiya ni yanzu xan tafi gida. Abba yace "haba dr.yaya za kace za ka tafi bayan har yanzu ko farkawa khalifa baiyi ba. Dr. mansoor yace "Alhaji kada kadarra cewa samun lfyar khalifa yana hannuna wannan hukunci ne na Allah,Allah yahore mana taimakon al'umma ta hanyar ilimi daya azurta mu dashi a bisa yardarsa muke yin komi ,nan da dan lokaci kadan likitan daya karbi aiki zai shigo yaci gaba da kula dashi, Allah shi ne me ba da lafiya, kafin dai in tafi inaso idan da hali ayi duk kokarin da za ayi a nemo abinda zai sanya khalifa farin ciki yayin daya farka ma'ana da zarar ya bude idonsa yakasance ya ga wani abu dazai faranta masa rai, wannan zai taimaka gun sanya natsuwa a zuciyarsa. Abba ya waiwayo yadubi fatima sannan yamaida kallonsa ga likitan yace dashi "ka ga wannan yarinyar? Dr. mansoor yadubi fatima dake tsugune gefe tana sharar kwallah abba yace "to itace yarinyar da khalifa ke so kuma iace silar fadawarsa cikin wannan halin. Dr. mansoor yace "Alhaji kana nufin itace fatima. Dasauri Abba yace "itace kuwa likita ina kasan sunanta? Yace "a jiya da kuka kawo khalifa lokacin da numfashinsa yafara dawowa bayan salatin Annabi da yayi sunanta muka ji yana ambata tun daga nan muka kaddara cewa a dalilin mace yafada ckin wannan damuwar, to tunda ga ta meye abin tashin hankali ba sai a bashi auran na ta ba kowa yahuta. Abba yayi murmushin takaici yana girgiza kai yace "Likita wannan yarinyar tafi karfin khalifa, kudi ba sa sayan mutum da ace kudi na sayan mutum ko nawa fatima takai sai na siyawa khalifa dan in rabashi da wannan damuwar dayake fama da ita, saura kwanaki biyu kachal awa 48 fatima tazama matar wani ban san halin da khalifa zai shiga ba, Inalillahi wa inna ilaihir raji'un. Dr. mansoor ya jinjina kai yace "gaskiyar magana abba tunda halin da khalifa yashiga ya kai haka to kanemi iyayan yarinyar nan ku daidaita magana su zo suga halin da danka yake ciki su taimaka kowa yataimaki wani Allah zai taimake shi, kada kabari wani ya auri fatima alhali khalifa na ckin wannan halin. Akayi shiru gaba daya har Dr. mansoor yafita bbu wanda yasake magana. A DAREN FARKO 29 Karfe daya daidai Abba yace zaije gida yayi wanka yayi sallah yadawo. Mama ta biyo shi har mota tana rokon yadaure yaci abinci. Ya dubeta da jajayen idon sa yace "cikin nawa ne bbu dadi tun dazun nake jin zuciyata na tashi kamar zan yi amai ga kaina na juyawa. Tace "kayi hakuri ka kwantar da hankalin ka komai na Allah ne, duk wadannan abubuwan dake fruwa idan Allah ya yi fatima matar khalifa ce zai aureta, za kaga yadda Allah zai juya al"'amarinsa daga damuwa izuwa farin ciki, babu abinda ya gagari Allah shi ne me yadda yaso a lokacin daya so, yayin da duk damuwar da za ayi da duk halin da za a shiga idan Allah bai kaddara matarsa bace sai dai mutari muyi hakuri muyi fatan alkhairi. Abban yadora kansa a kujerar da yake kai idonsa na kallon sama ,sun samu shiru daga bisani yace "Hakane sai na dawo. yaja motar ita kuma tadawo ciki. Tace "Fatima ku ci abinci kutafi gida ku huta don Allah ki daina yawaita wannan kukan ba zai yi mana maganin komi ba sai addu'a da hakuri. Cikin shashekar kukan tace "ni kam mama a idanuwa na ba za su taba daina zubar da hawaye ba sbda tashin hankalin da take ciki. Mama tace "kiyi hakuri fatima kada ki ja abin da za ki bata da iyayanki bayan a baya kuna zaune lfya kullum inna tana yabon halayyarki, iyaye suna da kima sosai a gun dansu in dai da yana son a gama da duniya lfya to yabi iyayansa, na tabbatar ba za su so ace ba ayi auranki da musbahu ba sbda shi ne xabinsu, hakan ba yana nufin suna kin khalifa ba, idan muka ce iyayanki ba sa son khalifa ba muyi musu adalci ba tundamuna sane da yadda al'amuran suke. Fatima duk da cewa ni na haifi khalifa na fi kowa jin ciwon da tashin hankali halin nan dayake ciki, idan a son raina ne izuwa yanzu yakasance kina dakin khalifa a matsayin matarsa sbda son da yake miki kowa ya san bashi dawani farin ciki wanda yawuce ya mallae ki, yanayi ne wanda kowa yasan khalifa bai taba samun kansa a ciki ba, ai wannan dalilin ne yasa kowa yake tabbatar da son da yake miki na gskiya tun yana fada da baki har gashi yau a gadon asibiti bai san waye a kansa ba, to amma duk da haka ba zan rufe ido a kan abinda ba ma gskiya da adalci ba na hakura na zubawa sarautar Allah ido idan Allah ya yi khalifa zai rayi zai tashi, ni dai na san rayuwa cike take da jarabbawa iri iri, komi lokaci gare shi duk yadda tsanani ya tsananta insha Allahu akwai sauki da zai biyo bayansa, a ckin alkur'ani mai girma ma Allah (SWT) yana fadin, dukkan tsanani suna tare da sauki. A wannan lokacin fatima dora kanta tayi bisa cinyar mama tana kuka har sai da hawayenta suka jikawa mama zaninta, lamarin dayasa itama mama takama sharar da kwallah duk kokarin data dinga yi gun hadiye hawayenta tun safe abin ya ci tura, wannan karon kuka take sosai, sai anty sadiya da ummi ke basu hakuri. Mutmryar khalifa tasa suka mike gaba daya a rude suna kallonsa, idonsa yabude yana fadin "Lahaula wala kuwwata illa billahil azim. Gaba daya suka iso kanaa suna masa sannu. Bai fahimci a inda yake b kansa a rude yake don haka yamaida idonsa yarufe, rudewa tasa Fatima ta manta tana tare da mahaifiyar khalifa takamo hannun khalifa tana fadin "Don Allah katashi daga barcin nan ya isa haka. Kamar a mafarki yake jin muryar fatima, sai yayi saurin bude idonsa, ai kuwa fatin ce a kansa ya zuba mata ido har yanzu dai a tunanin sa rayuwar mafarki yake, yace "Fatima. Ta amsa "Na'am khalifa. Ya matse hannunta yace don Allah fatima kada ki auri wani ba ni ba mutuwa zanyi idan na rasaki, mafarki nayi wai na ga katin daurin auranki fatima bai dace ki yi min haka ba ko so ki ke in mutu? Ni kadai iyayena suka haifa, ko su ya dace ki tausaya wa. Fatima tarufe me baki tace "ka kwantar da hankalin ka insha Allahu za ka mallakeni kasan nima ina sonka. Bayan khalifa ya yi sallolin dake kansa yana zaune kan darduma fatima thada mai ruwan shayi shi kadai yace zai iya sha gaba daya jikinsa yayi sanyi kallon kowa yake kadan kadan yake iya bude idonsa, kowa yazamo dan kallo, fatima ce ke da bakin magana a gun, shayin ma ita ta matsa masa tace sai ya sha gudun kada tayi masa hushi yasa ya hakura zai sha, amma bbu abunda yake sha'awa. Kofar dakin tabude, abba da malam musa mahain fatima da musbahu da inna suka shigo. Fati tatashi zumbur daga gaban khalifa domin zaune take sosai a gaban na sa tana rokon ya daure ya dan ci abinci ko kadan ne, kunya ce takamata sosai musamman ganin kallon da iyayanta ke mata duka fuskokin su ba walwala, ballantana musbahu wanda yake jin kamar ita kanta fatin ya shaketa kowa yahuta. Bayan sun gama gaisawa da tambayar jikin khalifa, musbahu yadubi malam da Abba yace "Don Allah ku yi hakan baba a kawo karshen wannan damuwar a yau, har abada hankalina ba zai taba kwanciya ba idan ya kasance dan uwana musulmi yana ckin damuwa a dalili na kuma zan iya taimakawa gun magance masa damuwar. Musbahu yayi shiru yakasa ci gaba da fadin abin da yayi niyyar fadin sbda wani irin abu da yaji ya tokare masa kirjinsa da makwagaronsa haka bakinsa yayi masa nauyi idanuwa sun yi jawur, dakin yayi tsit kowa kallon tausayi yakewa musbahu sbda matsananciyar damuwar data bayyana a fuskar sa. Da kyar yaja dogon numfashi yaci gaba da fadin "Baba na san ina son fatima har ga Allah ina jin daci da ciwon rabuwa da ita amma ba yadda zanyi kukan ya zame mini dole sbda in da baki yakarkata nan yawu ke zuba, in ji masu iya magana, tun kafin mukawo ga wannan halin na tabbatar wa zuciyata fatima khalifa take so, na auna abubuwa dayawa na ga dai hankalinta ya karkata akai wannan ne yasa na tilasta kaina nabar masa ita, na barwa khalifa fatima don Allah baba ku ma kuyi hakuri ku ba shi ita, ku dubi yanayin dasuke ciki ku kauda tunanin komi mu kaddara haka Allah yanufa, wannan rana da aka sa za a daura mana aure da fatima a daura da khalifa ina fatan Allah yasa haka shi yafi alheri gare mu gaba daya. Mama tadaga mai hannu tace "gaskiyar magana ba za ayi haka ba musbahu, tun yaushe kake son fatima, tun yaushe aka ma alkawarin an ba ka ita, amma lokaci daya a rufe ido a yi maka kwace, wane irin kallo mutane za suyi mana knan? fassarar da kowa zai mana ita ce ta rashin adalci, khalifa ne zai yi hakuri da fatima. Musbahu yayi murmushi tare da girgiza kai yace "mu wuce wannan gun mama tunda har fatima ta amince khalifa take so shi yadace a aura mata, ita diya mace in har ana son a zauna lfya da ita a bata wanda take so. Ya kasa ci gaba da maganar sbda wani abu dayake jin yana tokare masa makoshi, kirjinsa yana mai nauyi gudun kada suga hawayansa yatashi yafice daga dakin yanufi hanyar fita daga asibitin cikin sauri yasamu wata hanya a bayan asibitin yashiga yazauna a kasa yajingina dawata katanga yahada kai da guiwa yana ajiyar zuciya, a lokacin ne yasaki hawayen da yake ta boyewa yakama kuka mai ciwo da karfi, hannunsa daya dafe da kansa, kai da ganinsa ka san yana ckin tashin hnkali mai yawa da damuwa, tabbas yau ya san ya rasa fatima ya rasa yarinyar daya ke matukar so so mai yawan gaske, yarinyar da bai taba hadata da wata diya mace ba ballantana yakalli wata da sunan so bayan ita ba, hakika ba ka sanin kana son abu sai sanda karasa shi, wannan ciwon dayake ji a ransa ya san har ya mutu ba zai barshi ba, amma wajibi yayi hakuri fatima ba ta son shi abinda yayi shi yafi masa. A DAREN FARKO 30 A wannan rana aka sallami dr. khalifa daga asibiti duk da ba jin sauki yayi ba ko a ganin ido idan ka dubeshi ka san yana fama da ciwo irin na zuci wanda fuska ke bayynar da shi, bbu wanda ya samu bakin tattauna wata magana sai da suka dawo gida gaba daya. Jikin fati a sanyaye ta bi iyayanta zuwa gdansu gaba daya a razane take domin fuskokin iyayanta sun nuna mata akwai babbar magana wadda ba za ta taba yi mata dadi ba, ta zauna lakwas a rumfar inna tana jiran abinda za ace mata musamman ganin yadda malam musa yazauna ya lankwashe kafafu yace "fatima ai kamata yayi tunda kin zabi khalifa sai ki koma gdansu da zama a yi bikin na ku a can ko? Inna tace "Ni ma haka na gani malam. fatim tace "Don Allah baba kuyi hakuri kada kuyi fushi dani, ba ni nace musbahu yafurta ya hakura dani ya barwa khalifa ba shi yayi niyyar kansa. Inna tace "ke da Allah rufewa mutane baki waye sa'anki a nan da za ki zo mana da wannan maganar ta bnza da wofi, da ace ba ki nuna ra'ayin khalifa kike ba musbahun zai fadi haka, misbahu ya san ciwon kansa kuma yana kishin kansa dole yace ya hakura domin ba zai zauna a walakanta shi a banza ba. Malam yabude baki zai yi magana wani kanin fatima me suna ibrahim yashigo yashaidawa malam cewa ga abba can a waje yace yana son ganinsa. Tsaki yayi yamike yafito, ya umurçi Abba daya shigo zaure, ibrahim yadebo kujerun zama na roba suka zauna suka ka ra gaisawa. Alhaju mahammadu yace "malam na yi wa khalifa iyakar nasihar dazan masa Alhamdulillahi kuma ya fahimceni ya amince da nasihata ya hakura da fatima, na yi hakane sbda dogon nazarin da nayi a kan al'amarin don Allah malam kuyi hakuri kada kuyi fushi da fatima, fushin iyaye ba ya taba gyara sai illa, a bata goma daya bata gyaru ba, idan kukayi fushi da fatima al'amarin ne gaba daya zai lalace ba za asamu mafita ba, idan dai za muyi hakuri mu klli rayuwar yadda take tafiya cikin yaran bbu wanda yake da lifi face haka Allah yakaddara, kowane mutum da Allah ya halicce shi yarubuta abinda zai faru dashi a rayuwarsa kuma babu wanda zai kaucewa wannan kaddarar tasa. Kan malam na kasa nauyin maganar Abba sun masa nauyi aka har sai da yaji kunya ta kama shi sosai wato Abba ya fahimci ba sa son ba wa khalifa auran fatima shi yasa yadanne damuwarsa duk yadda yake son khalifa ya auri fatima ya hakura, ko kusa bai cancanta suyi wa Alhaji muhammadu haka ba duk yadda mutumin kirki yake mai son mutane da kula da hakkin makotaka yakai Alhaji sai son barka yana samun yabo a bakunan mutanan unguwar, su kam alhaji babu abunda bai yi musu ba ko kusa bai cancanta suki dansa ba. Ya daga ki yace "Don Allah alhaji kar kayi tsammanim hana khalifa fatima nake son yi. Abba ya katse shi da sauri yace "wallahi ba haka nake nufi ba, ko a baya damuwar da khalifa ke ciki tasa idona yarufe na shagala daga baya nayi nazari na sawa zuciyata hakuri. Malam yace "Alhaji na gamsu da bayananka na yi fatan Allah yasa haka shi yafi alheri garesu gaba daya, na bawa khalifa fatima. Abba yace "don Allah abba kada kayi hushi da ita albarkar auran nan ake nema in dai kuna fushi da fatima wannan albarkar ba samuwa za tayi ba. Sai a lokacin xuciyar malam ta dan sassauta daga damuwar da yake fama da ita, bayan tafiyar Alhaji ya dawowa inna da bayanin abinda abin da abba yazo mai dashi, inna tace "kai ni dai kam ba zan fasa fadar cewa wannan abu bai yi min dadi ba, to idan ma naboye ban bayyana a bakina ba Allah na gani xuciya b dadi . Malam yace "ba komi. mu barshi a haka Allah yakaddara din mu yi fatan alheri ,fushi ba namu bane. fushin mu ba zai yi maganin matsalar ba face yakara jagula al'amarin, duk yadda zamuyi ba za mu ba musbahu fatima ba tunda Allah bai kaddara matarsa bace. Tace "to malam yanzu ina musbahun? Yace "Ni tunda yafita daga asivitin nan ban kara ganinsa ba, ban san ina yayi ba wayarsa ma gashi a kashe take tun da muka dawo banganshi ba nake ta kiranta bata shiga ba. Inna tayi tsaki tace "Duk fatima ce taja tun farko in da bata ba khalifa fuskar yaso ta ba zai so ta? mutumin da ya san an yi masa baiko ina shi ina kula wani namiji. Fatima ta ban mamaki Allah malam wannan halayyar arota kawai tayi ba ta ta bace, ina matukar jin kunyar yaron nan yagama sawa ransa ba shi da mata sai ita lokaci guda ace yarasa? haba ai abin da ciwo. Fatima dai na daga dakinsu tana ji bata ji dadin abubuwan a ranta amma soyayyar da takewa khalifa tasa tashare komi in dai za ta samu cikar burinta akan dr. khalifa xancen ya kare. Yawan kuka datayi ya haifar mata da zazzabi da ciwon kai, tasamu babban zani ta kudundune kanta a ciki tana wasi wasi wayarta tafara ringing ganin nomban khalifa yasa tadaga dasauri. Muryarsa a sanyaye yace "Fatima me ki ke yi yanzu? Tace "A kwance nake zazzabi ne yarufeni. Yace "Subhanallahi *in sha magani? Tace "yanzu dai zan sha. Yace "zan iya zuwa in ganki? Tayi shiru, yace "ko akwai matsala? Tace "Gani nayi ba ka da lfya. Yace "na ji sauki tunda na sameki dama rasaki da naga da gaske zanyi ne yaja min ciwo, lokacin danaga wannan katin na tabbatar na rasaki sai naji gaba daya duniya ta min kunci, abin cikinta ma ya min kunci, hankalina ya tashi gaba daya na kasa mallakar kaina, ,na yi kokarin in daure damuwa ta ta kai matakin data kai amma da yake ba ni ne nasa kaina a damuwar ba hakan bai yiwu ba gareni dole sai da kowa ya fahimci matsalata da farko na yi zaton mfarki nake ashe gskia ne don Allah fatima ki nemar mini iso gun inna da malam su amince in ganki zuciyata ba ta da juriya a kanki ba zan iya jurewa rashin ganin ki ba. Fati ta runtse ido tabude tace "Ba komi kazo gdan kuma zan fito zaure kaganni. ***** A gdansu Dr. khalifa xanceb da ake ta nanatawa knan za a daura auran khalifa da fatima nan da kwana biyu masu zuwa, reshe ya juye da mujiya ,nan da nan Abba yashiga kiran abokansa da yan uwa a waya yana shaida musu batun daurin auran dan lelen dansa biki daisai bayan sati daya domin ba abu ne na wasa a tare dasu ba, auran khalifa abin alfahari ne a tare dasu sai kowa yasan ana yi, mama ce dai bata nuna farin cikinta sosai sbda ta tsani abinda za ace ta yi son kai ko son zuciya wanda tabbas ta san sai an fada,anty sadiya tai ta tsaki a ranta. Ko yushe tananuna mata cewa aure nufi ne na Allah babu wanda za ya auri matar wani, Allah yayi fatima matar dr. khalifa ce dole shi zai auri matarsa, surutun mutane ba karewa yake ba duk yadda kaso da taka tsantsan dinka sai an yi surutun, idan b a yi maka akan wani abin ba sai an yi a wani abin shiyasa idan mutum yagane to yasa*i ransa yayi komi kansa tsaye kawai yahuta, mutum ya fuskanci Allah a cikin al'amarinsa to karya damu da surutun mutane. Mama tace "kai sadiya duk fa yadda za ki kare abin nan ba zan fasa cewa Khalifa yayi son kai ba. Tace "to mama shi yace sai an ba shi ta karfin tiya? muna zaune fa aka ce an bashi to sai ya ki karba don kada mutane su ce ya yi son kai? A bisa dole mama tahakura don bata samu goyon baya ba ta kowanne fannin, dayake harka ce ta masu kudi duk da kasancewar baa gayawa yan uwa ba tun auran da wuri ba amma daga lokacin da aka fara bada sanarwar daurin auran gdan yafara cika da mutane maza da mata yan taya murna. Ummi tana gdansu tun lokacin da dr. khalifa yafito daga asibiti ta tabbatar za a yi auransa da fatima ta karasa rikicewa hankalinta a tashe tajewa hjiyarta da labarin, ta bayyana mata duk yadda abubuwan suka faru tace "Hajiya mama da abba babu abunda suke sosai farin cikin dansu, Abba da kansa yaje ya sanar da mahaifin fatima halin da dansa ke ciki a kan yarsu, suka taho asibitin da niyyar dubashi lamarin dayasa musbhu yace ya barwa khalifa fatima sun manta ina son khalifa tun kafin yaso fatima, bbu wnda yadamu da hlin danake ciki ana nan an fara shirye shiryen auran gadan gadan. Hajiya tashare mata hawaye tace "Daina kuka ummi in dai ina raye a gdan duniya nan zanyi miki maganin damuwarki, ba zan taba cewa kidaina son khalifa ba don ita zuciya ba a rabata da abinda take so a zauna lfya, idan har muka hakura da khalifa to mata muka rako duniya, wannan dogon lokacin damuka dauka muna nemansa ba zai tashi a banza ba, tashi mu koma gun malam. Ummi tadanyi jim sannan tace "hajiya bai dace mucigaba da wahalar da kammu a gun zuwa gdan mlami ba da wahala idan hakan zai amfanar damu tun da a baya bai mana amfanin kmi ba. Hajiya tafiddo ido tace "ke saurara nsara a hankli samunta idan lokacin samuwarta ya zo za kiyi mamakin aikin malam, ke de muje muji ta bakinsa, motsi ai yafi labewa, bari in karasa miyar can yunwa nake ji.A DAREN FARKO 30 A wannan rana aka sallami dr. khalifa daga asibiti duk da ba jin sauki yayi ba ko a ganin ido idan ka dubeshi ka san yana fama da ciwo irin na zuci wanda fuska ke bayynar da shi, bbu wanda ya samu bakin tattauna wata magana sai da suka dawo gida gaba daya. Jikin fati a sanyaye ta bi iyayanta zuwa gdansu gaba daya a razane take domin fuskokin iyayanta sun nuna mata akwai babbar magana wadda ba za ta taba yi mata dadi ba, ta zauna lakwas a rumfar inna tana jiran abinda za ace mata musamman ganin yadda malam musa yazauna ya lankwashe kafafu yace "fatima ai kamata yayi tunda kin zabi khalifa sai ki koma gdansu da zama a yi bikin na ku a can ko? Inna tace "Ni ma haka na gani malam. fatim tace "Don Allah baba kuyi hakuri kada kuyi fushi dani, ba ni nace musbahu yafurta ya hakura dani ya barwa khalifa ba shi yayi niyyar kansa. Inna tace "ke da Allah rufewa mutane baki waye sa'anki a nan da za ki zo mana da wannan maganar ta bnza da wofi, da ace ba ki nuna ra'ayin khalifa kike ba musbahun zai fadi haka, misbahu ya san ciwon kansa kuma yana kishin kansa dole yace ya hakura domin ba zai zauna a walakanta shi a banza ba. Malam yabude baki zai yi magana wani kanin fatima me suna ibrahim yashigo yashaidawa malam cewa ga abba can a waje yace yana son ganinsa. Tsaki yayi yamike yafito, ya umurçi Abba daya shigo zaure, ibrahim yadebo kujerun zama na roba suka zauna suka ka ra gaisawa. Alhaju mahammadu yace "malam na yi wa khalifa iyakar nasihar dazan masa Alhamdulillahi kuma ya fahimceni ya amince da nasihata ya hakura da fatima, na yi hakane sbda dogon nazarin da nayi a kan al'amarin don Allah malam kuyi hakuri kada kuyi fushi da fatima, fushin iyaye ba ya taba gyara sai illa, a bata goma daya bata gyaru ba, idan kukayi fushi da fatima al'amarin ne gaba daya zai lalace ba za asamu mafita ba, idan dai za muyi hakuri mu klli rayuwar yadda take tafiya cikin yaran bbu wanda yake da lifi face haka Allah yakaddara, kowane mutum da Allah ya halicce shi yarubuta abinda zai faru dashi a rayuwarsa kuma babu wanda zai kaucewa wannan kaddarar tasa. Kan malam na kasa nauyin maganar Abba sun masa nauyi aka har sai da yaji kunya ta kama shi sosai wato Abba ya fahimci ba sa son ba wa khalifa auran fatima shi yasa yadanne damuwarsa duk yadda yake son khalifa ya auri fatima ya hakura, ko kusa bai cancanta suyi wa Alhaji muhammadu haka ba duk yadda mutumin kirki yake mai son mutane da kula da hakkin makotaka yakai Alhaji sai son barka yana samun yabo a bakunan mutanan unguwar, su kam alhaji babu abunda bai yi musu ba ko kusa bai cancanta suki dansa ba. Ya daga ki yace "Don Allah alhaji kar kayi tsammanim hana khalifa fatima nake son yi. Abba ya katse shi da sauri yace "wallahi ba haka nake nufi ba, ko a baya damuwar da khalifa ke ciki tasa idona yarufe na shagala daga baya nayi nazari na sawa zuciyata hakuri. Malam yace "Alhaji na gamsu da bayananka na yi fatan Allah yasa haka shi yafi alheri garesu gaba daya, na bawa khalifa fatima. Abba yace "don Allah abba kada kayi hushi da ita albarkar auran nan ake nema in dai kuna fushi da fatima wannan albarkar ba samuwa za tayi ba. Sai a lokacin xuciyar malam ta dan sassauta daga damuwar da yake fama da ita, bayan tafiyar Alhaji ya dawowa inna da bayanin abinda abin da abba yazo mai dashi, inna tace "kai ni dai kam ba zan fasa fadar cewa wannan abu bai yi min dadi ba, to idan ma naboye ban bayyana a bakina ba Allah na gani xuciya b dadi . Malam yace "ba komi. mu barshi a haka Allah yakaddara din mu yi fatan alheri ,fushi ba namu bane. fushin mu ba zai yi maganin matsalar ba face yakara jagula al'amarin, duk yadda zamuyi ba za mu ba musbahu fatima ba tunda Allah bai kaddara matarsa bace. Tace "to malam yanzu ina musbahun? Yace "Ni tunda yafita daga asivitin nan ban kara ganinsa ba, ban san ina yayi ba wayarsa ma gashi a kashe take tun da muka dawo banganshi ba nake ta kiranta bata shiga ba. Inna tayi tsaki tace "Duk fatima ce taja tun farko in da bata ba khalifa fuskar yaso ta ba zai so ta? mutumin da ya san an yi masa baiko ina shi ina kula wani namiji. Fatima ta ban mamaki Allah malam wannan halayyar arota kawai tayi ba ta ta bace, ina matukar jin kunyar yaron nan yagama sawa ransa ba shi da mata sai ita lokaci guda ace yarasa? haba ai abin da ciwo. Fatima dai na daga dakinsu tana ji bata ji dadin abubuwan a ranta amma soyayyar da takewa khalifa tasa tashare komi in dai za ta samu cikar burinta akan dr. khalifa xancen ya kare. Yawan kuka datayi ya haifar mata da zazzabi da ciwon kai, tasamu babban zani ta kudundune kanta a ciki tana wasi wasi wayarta tafara ringing ganin nomban khalifa yasa tadaga dasauri. Muryarsa a sanyaye yace "Fatima me ki ke yi yanzu? Tace "A kwance nake zazzabi ne yarufeni. Yace "Subhanallahi *in sha magani? Tace "yanzu dai zan sha. Yace "zan iya zuwa in ganki? Tayi shiru, yace "ko akwai matsala? Tace "Gani nayi ba ka da lfya. Yace "na ji sauki tunda na sameki dama rasaki da naga da gaske zanyi ne yaja min ciwo, lokacin danaga wannan katin na tabbatar na rasaki sai naji gaba daya duniya ta min kunci, abin cikinta ma ya min kunci, hankalina ya tashi gaba daya na kasa mallakar kaina, ,na yi kokarin in daure damuwa ta ta kai matakin data kai amma da yake ba ni ne nasa kaina a damuwar ba hakan bai yiwu ba gareni dole sai da kowa ya fahimci matsalata da farko na yi zaton mfarki nake ashe gskia ne don Allah fatima ki nemar mini iso gun inna da malam su amince in ganki zuciyata ba ta da juriya a kanki ba zan iya jurewa rashin ganin ki ba. Fati ta runtse ido tabude tace "Ba komi kazo gdan kuma zan fito zaure kaganni. ***** A gdansu Dr. khalifa xanceb da ake ta nanatawa knan za a daura auran khalifa da fatima nan da kwana biyu masu zuwa, reshe ya juye da mujiya ,nan da nan Abba yashiga kiran abokansa da yan uwa a waya yana shaida musu batun daurin auran dan lelen dansa biki daisai bayan sati daya domin ba abu ne na wasa a tare dasu ba, auran khalifa abin alfahari ne a tare dasu sai kowa yasan ana yi, mama ce dai bata nuna farin cikinta sosai sbda ta tsani abinda za ace ta yi son kai ko son zuciya wanda tabbas ta san sai an fada,anty sadiya tai ta tsaki a ranta. Ko yushe tananuna mata cewa aure nufi ne na Allah babu wanda za ya auri matar wani, Allah yayi fatima matar dr. khalifa ce dole shi zai auri matarsa, surutun mutane ba karewa yake ba duk yadda kaso da taka tsantsan dinka sai an yi surutun, idan b a yi maka akan wani abin ba sai an yi a wani abin shiyasa idan mutum yagane to yasa*i ransa yayi komi kansa tsaye kawai yahuta, mutum ya fuskanci Allah a cikin al'amarinsa to karya damu da surutun mutane. Mama tace "kai sadiya duk fa yadda za ki kare abin nan ba zan fasa cewa Khalifa yayi son kai ba. Tace "to mama shi yace sai an ba shi ta karfin tiya? muna zaune fa aka ce an bashi to sai ya ki karba don kada mutane su ce ya yi son kai? A bisa dole mama tahakura don bata samu goyon baya ba ta kowanne fannin, dayake harka ce ta masu kudi duk da kasancewar baa gayawa yan uwa ba tun auran da wuri ba amma daga lokacin da aka fara bada sanarwar daurin auran gdan yafara cika da mutane maza da mata yan taya murna. Ummi tana gdansu tun lokacin da dr. khalifa yafito daga asibiti ta tabbatar za a yi auransa da fatima ta karasa rikicewa hankalinta a tashe tajewa hjiyarta da labarin, ta bayyana mata duk yadda abubuwan suka faru tace "Hajiya mama da abba babu abunda suke sosai farin cikin dansu, Abba da kansa yaje ya sanar da mahaifin fatima halin da dansa ke ciki a kan yarsu, suka taho asibitin da niyyar dubashi lamarin dayasa musbhu yace ya barwa khalifa fatima sun manta ina son khalifa tun kafin yaso fatima, bbu wnda yadamu da hlin danake ciki ana nan an fara shirye shiryen auran gadan gadan. Hajiya tashare mata hawaye tace "Daina kuka ummi in dai ina raye a gdan duniya nan zanyi miki maganin damuwarki, ba zan taba cewa kidaina son khalifa ba don ita zuciya ba a rabata da abinda take so a zauna lfya, idan har muka hakura da khalifa to mata muka rako duniya, wannan dogon lokacin damuka dauka muna nemansa ba zai tashi a banza ba, tashi mu koma gun malam. Ummi tadanyi jim sannan tace "hajiya bai dace mucigaba da wahalar da kammu a gun zuwa gdan mlami ba da wahala idan hakan zai amfanar damu tun da a baya bai mana amfanin kmi ba. Hajiya tafiddo ido tace "ke saurara nsara a hankli samunta idan lokacin samuwarta ya zo za kiyi mamakin aikin malam, ke de muje muji ta bakinsa, motsi ai yafi labewa, bari in karasa miyar can yunwa nake ji. Ummi tace "ni don haushi ma ko yunwa ba ta damuna. ina mamakin son kan da ake nunawa kowa akan khalifa amma ta watsar da komi ta kanta kawai take ko kunyar idona ba ta ji. Hajiya tace "duk ki kyalesu son zuciya bacinta da sannu dukka za sugane kurensu. Ummi ta tashi tashige dakin hajiya ta tsaya a gaban madubi tana karewa kanta kallo tare da tuno siffofin fatima a idanuwanta tajinjina kai tare da ajiyar zuciya tace "ba komi. Sai bayan sallar isha'i suka isa gdan malam shima yana mamakin ganinsu a wannan lokacin ya san ba lfya. suka baje masa bayanin komi. Unmi ta marairaice tace "Don Allah malam kataimakeni xan rayu ckin bakin ciki mai tsanani idan narasa dr. khalifa dole in yi kishin fatima domin ta san sirrina ta san abinda ke ckin zuciyata, ko zan hakura dr. khalifa yarayu da wata diya mace ba dai fatima ba, na amince in rasa shi amma kada wata ta mallake shi. Malam yabushe da dariya yaja ra'ayinsu ya fara zane zane yana bajewa lokaci mai tsawo suna kallonsa sannan yadago kai ya dubesu yace "haba ko da naji ai uwar Khalifa ce tashiga malamai aka tsare mata jikin khalifa don kada wata macen tasamu damar asirce shi ta rabata da shi, tunda tasan yammata za su so shi da yawa ita kanta fatiman don soyayyar da yake mata ta ra'ayin kansa ce shi yasa duk ayyukan da muke jifansa dasu ba su tasiri akansa, to amma ba komi akwai aljanin da zamu hada shi da shi sai yayi tasiri a kansu shi da fatiman kuna zaune za kuga ya tsaneta hankalinsa ya dawo kan ummin, amma sai an sayi sa babba wanda za a yanka shi a yi aikin a kan sa aiki irin wannan karfi gareshi sai an yi yanka. Ganin sun yi jim yasa yaci gaba dayi musu dadin baki tare da kwadaitar dasu amfanin aikin idan an yi, yace "wa kukaga ya ji dadi ba tare da ya sha wahala ba, duk wadannan abubuwan tarihi za su zama idan Khalifa yazo hannu sai ya baku tausayi ku dai ku daure. Suka dawo gida suna tattauna yadda za su nemo kudin sa, sun yi ammana aikin malam zaici, ummi tace "Hajiya dole ne in saki jiki wurin gudanar da al'amarin bikin nan xan nuna kamar bbu wani avu a zuciyata xa ayi komi dani, amfanin hakan shi ne dan in samu kudin da za muyi amfani dasu. Hajiya tace "Lallai kin zo da dabara, idan har kika nunawa khalifa cewa kina son auran sa da fatima komi za musamu a jikinsa da abbansa, kin ga knan mun jefi tsuntsu biyu da dutse daya. A DAREN FARKO 31 Ana ya gove daurin auren fatima da khalifa wasikar musbahu ta iske mallam inda yake shaida masa cewa kada su daga hankalinsu a dalilin rashin ganinsa ya kauracewa gdan ne don ya samar da zaman lfya da walwala yayin bikin fatima, a cikin wasikar yace. "Malam idan naci gaba da zama kana ganin damuwata za ku dinga jin zafin fatima yayin da ni kuma zuciyata ba za ta taba yi min dadi ba in dai yakasance kuna jin ahushin fatima a sbda ni da ace da ace zan iya shanye damuwata da zan dawo amma hakan hakan ba zai yiwu gareni ba, zuciyata ba ta da wannan karfin. Baba da inna ina rokon ku yi hakuri don Allah ku dauki wannan al'amarin a matsayin kaddara kada kuyi fushi da fatima, fushinku matsala ce babba ga rayuwarta ina nan ina ta mata fatan alheri, insha Allahu da zarar an gama bikin an kaita gdanta zan dawo. Sun ji tausayin al'amarin kwarai da gaske sai dai ba yadda za suyi al'amarin kaddarar nan dai da kowa ke fada itace dole ayi hakuri a karbeta, surutun da ake gudu shi ake tayi a cikin unguwa da dangi, kwadayi kwadayin abin duniya shi ake tafada musamman lokacin da sanarwar daurin auran ta cika gari ta hanyar kafafan yada labarai dake arewacin kasar nan ba ma nan kano kadai ba tare da sanarwar za ayi gagarumar wlima bayan daurin auren da yamma amma na maza zalla,tuni aka cikawa malam gdansa da nau'ikan kayan abinci na alfarma wanda za ayi amfani dasu a gun bikin, hatta nama kala kala aka kawo, kayan da amarya za tasa lokacin biki mama da anty sadiya suka tsara mata su gun kwararrun telolinsu dake tsara musu dinki, kaya ne msu tsadar gaske haka dinkunan sun sha kudi amma fa sunyi kyau sun dace da amaryar, kayan lefene suka ce sai an gama hidimar daurin aure ango da amaryar za su tafi da kanta za ta xabi irin kayan da take so da kanta. Anty sadiya ta hurawa mama wuta akan lallai su za su gyara amarya tun daga kan fatarta da abubuwan da ake sha masu kawo ni'ima ga amarya, mama tarike baki tace "sadiya wannan ai na su ne na iyayanta da yan uwanta ina dangin miji ina gyaran amarya. Sadiya tace "Tabdijam ai kuwa mama anan ne ma yadace ki yi gyaran da hujja, me yasa kikayi mata a baya lokacin da za ta auri musbahu, kika gyara don dan wani ma ballantana na mu, ai ajiye kunya za muyi mi tattalin farin cikin danmu zamanin duhun kai ya wuce ina innarta za ta iya irin wannan abub tana fama da kunya. Mama tayi dogon tunani taga gaskiyar fa sadiya barin kashi a ciki bai maganin yunwa, musamman yadda taga khalifa yana cike da tsananin farin cikin auran daya samu ko kawaici bai iya yi. Lokacin da ummi ta iso gdan da safe tashaida mata cewr tana son tadan yi dabarar da dan ja hankalin fatima tadawo gdan nan tazauna a yau, duk abinda aka fada akan fati sai ummi ta ji tsigar jikinta ya tashi, sai dai bata bari a fahimci damuwarta ta saki ranta sosai, a wannan lokacin ma fadada fara'arta tayi tace "Ba damuwa mama ai ke ce uwar amarya uwar ango mu kuma mune kirjin biki. Bayan sun gama cin abinci tanifi gdansu fatiman ta iske su ita da ango dr. khalifa a soron gdan suna hira, tarike baki tana murmushi tace "to ai dai aski ya zo gaban goshi yaya khalifa meye na mannewa anan? Ni na dauka ma ka fita. Ya bata rai yana harararta yace "ke wai ni abokin wasanki ne xan dauki mataki akanki idan baki shiga taitayinki ba. Tace "a'a yi hakuri kamaida wukar ni dai katayamu murna Allah yasa rakiya tayi nisa. Suka bushe da dariya gaba daya ita da fatiman tawuce cikin gida tana fadin "Bari mugaisa da inna kafin kugama. Khalifa ya matso kusa da fatima yana dan rausayar da kai fuskarsa dauke da murmushi yace "Wallahi fatima har na rasa wacce hanya zan nuna miki soyayya duk abin da nayi miki don in tabbatar maki da soyayya sai in ga ya yi kadan matsayinki ya wuce nan. Ta kwantar da kanta a jikin bango tana kallonsa, shadda ce a jikinsa ruwan kwai, iya guiwa rigar ta tsaya masa ta dan matse me jiki, fuskar nan fes fes tamkar kullum kyau ake kara masa, bbu wani da namiji da fatima take tsayawa tamasa kallon kurilla sai jan gwarzanta Abbubakar saddik, sbda ahi take kallo taji sanyi a ranta, duk damuwar datake ciki in dai za taga khalifa sai taji sanyi a ranta kuma sai taji lallai ta gamsu ta ga da namiji cikakke wanda in dai ka kalleshi ka san ka ga da namiji. Khalifa yaci gaba da fadin "Fatima Allah ne yayi ke rabona ce shi yasa nadawo gida a dai dai wanna lkacin, godiya nakewa Allah daya ba ni ke, domin da na rasaki ban san halin dazan samu kaina ba fatima. Wani irin kallo take masa tana dan lumshe ido tana budewa tare da marairaice fuskarta domin za tayi kuka, lamarin daya dagawa dr. khalifa hankali sosai yakasa rike kansa yakara matsowa daf da jikinta yakai bakinsa kunanta yace "Don Allah fatima zo mu shiga dakin nan in dan ji dumin jikinki zuciyata za ta fashe yanzu. Tayi wal da ido ta waiwaya gaba da baya ba kowa. Ko me yasa bata iya musu da dr. Khalifa tana sane dacewa bukatarsa gareta bata dace ba amma ba za ta iya kaucewa abin da yake so ba, sai kawai tabishi suka shiga dakin musbahu wanda yake zauran gdan, dasauri ya rungumota sannan yayi ajiyar zuciya mai karfi yayi mata kiss, ya saketa yace "to zo ki shiga gida. Mamaki yasa ta tsaya galala tana kallonsa, yakama dariya yace "ai dama ba wani abu mai yawa zan miki ba soyayya ce ta yi mini yawa, shi yasa idan idan ina gabanki bana iya jurewa, ki yi hakuri daga gobe idan Allah yakaimu na zamo mijinki za ki ga abubuwa da dama a tare dani, kada kidamu soyayya ce wadda za takasance abar alfahari gareki, sai kinyi tsammanin kin fi kowace mace sa'a a duniya, zan tabbatar miki ina sonki, zan baki kaina kiyi yadda kika ga dama dani fatana dai kiji tsoron Allah, kiyi min adalci kada kiyi amfani da wannan damar ki wahal dani, kiyi hakuri mu zauna lfya shi ne kadai abinda zai sa in samu farin ckin rayuwata. Babu abinda fati ke iya ce masa sai kallo da ido, abubuwan datake ji game dashi a zuciyarta ya fi karfin ta iya fda masa da baki sai dai tabarwa zuciyarta, ita dai ta san tana son dr. khalifa kuma in dai haka soyayya take hakika masoya suna fama da wahala, meye wahala? wahalar ciwon so daban ba kamar kowacce wahala bace, in da wahalar take shi ne in dai mutum bai ga wannan masoyin na sa ba to zuciyarsa na cikin fitina da garari. Yarike hannunta kam kam yayi mata kiss, sannan ya saketa ya fice, ita kuma tashiga gida ta iske ummi da inna suna hira. A cikin daki ummi tadubi fatima tarike kugu tana murmushi tace "amarsu ta ango in ji ko dai dr. khalifa ya fara latsa jikin ki ne.? Tafiddo ido tace "Ban son sharri ummi. Itama ta tsareta da na ta idon tace "ke fatima kada ki mayar dani yarinya karama mana daga lokacin da soyayya ta tsumu a zuciyar mace budurwa mai tashen kuruciya irinki har takai namiji ya fata tabata sai ta sauya. Duk da kyau da ki ke dashi a baya amma yanzu kina da bambamci, idan ke baki san yanayin jikinki ya sauya ba ni na san ya sauya. Fatima taja doguwar ajiyar zuciya ta zauna gefe tana kallon immi, takasa magana. Ummi ta kyalkyale da dariya tana tafa hannuwa tace "Daman akwai lokacin da za ki iya soyayya ? Tadan yi murmushi tace "Anty ummi ai dr. khalifan ne ya isa a so shi ya hadu. Ummi taji wani dam a jikinta da zuciyarta kamar za ta shaki wuyar fatima tace "tashi ki shirya fita zanyi a yi miki gyaran jiki mun dai makara jibi a cigaba. A kofar gdansu dr. khalifa, fatima ta kafe akan ba za tashiga ba ita kunya take ji, ummi tace "ki rufa wa kanki asiri idan mama taji kin ki shiga fushi za tayi dake, idan ma kin sa wa zuciyarki surukuta da kunyar mama to wahala za ki ba kanki tunda kin san ita wayayyar mace ce bbu ruwanta da irin wadannan abubuwan. A harabar gdan suka ci karo da mama ta yowa baki rakiya, bata amsa gaisuwar fatima ba sai harararta datayi tace ke kin dauke kafarki daga gdan nan wai ke suruka ko ? Fatima ta sunkuyar da kai tana murmushi, ta gayar da baki, tawuce ckin gda da sauri jin mama tana fadama bakinta cewa wannan ce amaryar khalifa. Ai kuwa suka fara fadin "kai msha Allahu wannan yarinya da kyau take ya more mace ga kyau ga kuruciya. Daya daga ckin bakin tace "to ai ta fishi morewa a wannan zamanin samun namiji irin da na khalifa sai an tona kinga kuwa mu za muyi yanga va mu za a yiwa yanga ba, tunda duk inda danmu yake rububinsa ake. Bayan sun tafi mama tadawo ckin gida ta samesu a falo tare da anty sadiya ,tace "yawwa "yammata a zo a dafa ma abba abinci saura yan mintuna kadan bakinsa su iso. A ? ty sadia tace "mama munada abubuwa da yawa da za muyi fa lokaci zai kure mana. Tace "ai komi za ayi dole a tsaya a yiwa mai gidana abinci in kuma ba haka ba a fasa fitar. Ummi tace "tabdijam ai kuwa mama a yadda muke ji da amaryar nan tamu yau ko tsakar dare za mukai a gdan mai gyaran jikin nan xa mu kai, mai kunshin ma daukarta za muyi mutafi da ita. Mama tace "Lallai abin naku nayi ne sai ku kira angon a waya yazo yabada kudin kunshin don kuwa bbu wanda zai biya masa kudin kunshin matarsa tunda don shi za a yin. Anty sadiya tace "Eh ko zai bayar kema sai kin bayar da wani abu mama kudin fa da yawa. Tace 'Au tausayin khalifa kukeyi ni baku tausayi na ? duk fa abubuwan nan da ake yi ko sisinsa bai kashe ba hatta walimar nan da za ayi idan allah yakaimu goben su dr. hafiz ne suka dauki nauyi da wani abokinsa da sukayi karatu a jamus, to ko nawa yabayar gun kunshi ai ba wani abu ko ? Ummi takirashi a wya tace "yaya kana ina ne ? Yace "mun fita dasu dr. bashir. Tace "To muna bukatar kudin kunshin amarya da gyaran gashinta. Yayi wani mur. ushi yace "Da kyau ummi idan har aka yiwa amaryar nan tawa adon daya birgeni ni nasan kyautar da zan miki ko nawa ne zan biya a yi mata in dai zai yi kyau. A DAREN FARKO 32 Ummi tayi dariya tace "yaya knan in dai batn kyau ne yau za mukai amaryarka in da za ka kasa gane ta sbda kyaun da za tayi. Khalifa ya kyalkyale da dariyan da bata taba jin ya yi ba yace "kia ina ja fa ummi amaryata fa me kyau ce shi yasa na zabeta a cikin dubban mata nace ita kadai zan aura sbda dogon nazari nayi a kanta tun daga lokacin da idanuwa na suka fara gani? ta. Ummi ta cije lebe tare da runtse ido har wani gumi taji yana tsiyayo mata sbda daci da ciwon maganganun da khalifa yake yaba mata, ji take kamar ruwan zafi ake watsa mata a jiki, shi yasa nan take tajike da gumi, a hankali tace "yaya khalifa wai don Allah me yasa kazabi fatima ka fifita ta akan duk wata diya mace, har kabata matsayi me girma a zuciyarka? Yace "Ummi na ji dadin wannan tambayar da kika yimin domin ina son in ji ina fadawa wanda yashafi fatima matsayin fatiman a zuciyata don yarinka karfafa mata xuciya tana sanin cewa dagaske nake. Ummi tace "to in banda abinka daman yaya khalifa ai fatima ta san kana sonta ,yanayin soyayyar dakake nuna mata ne ma yake karfafa mata zuciya take kara sonka tare da sakin zuciyarta ta yarda da son da kake mata, in ban da haka fati za ta iya sanya shakku a zuciyarta game da kai sbda yanayinka. Khalifa ya dan tsuke fuska yace "sbda me kika ce hka ummi? wannan magana ta ki ta ban mamaki don Allah yi min karin bayani. Tace "yaya khalifa a yanayin rayuwa irin na fatima dole taji tsoron sakin jiki dakai idan tana kallon yadda rayuwarka ke tafiya, kayi mata nisa nesa ba kusa ba, amma dayake kana nuna mata soyayya mai karfi ta yarda dakai ta amince akan kana mata so na gskiya, ina ganin idan haka ne ba ka da bukatar wanda zai ci gaba da nusar da fati soyyarka gareta. Khalifa yace "kuma hakane amma duk da haka ina bukatar taimakon ku fatima yarinya ce. Bayan sun yi sallama ummi ta ajiye wayar a gefe tayi tagumi, wannan soyayyar da dr. khalifa kewa fatima tana da yawa, fidda fati daga zuciyarsa abu ne mai wahalar gaske, wace hanya za tabi knan, ta ina za tasamu khalifa? Duk kudin da suke kashewa a gun malamai abin ya ci tura tamkar suna asirin karawa dr. khalifa soyayyar fatima ne, aiki ne ja a gabanta tun da ta tabbatar wa ranta ba za ta hakura tasa ido wata diya macen ta mallaki khalifa ba in dai tana raye. Tayi kwafa tamike tabi fatima da anty sadiya inda suke girkin abincin Abba. Suna ckin shirya tebur khalifa yashigo gdan cikin sauri tare da dr. Bashir, kai tsaye suka wuce tebur din wai dama yunwa sukeji, mama ta harare su tace "ai duk yunwar ku ba za kuci wannan abincin ba. Khalifa yaduvi fatima zai yi magana mama tace "oh za kace mini matarka ce tayi ko? Yarufe baki yana dariya, fatima dai tabar dakin dasauri tanufi dakin ummi suka yi sallar azahar ummi tashigo musu da abinci suka ci a tsatsaye. Kudin da dr. khalifa yaba ummi na gyaran jikin amarya sai da suka firgita su sbda yawansu, ta yi murna sosai domin abin nema ya samu a ranta tace "ka ba da kudin da za a yaki soyayyar fati a zuciyarka da sannu za kagane kuskurenka. Mama ma tadada musu kudin tace su sayo duk abu! uwan dasuke bukata har na su ma kansu ita da anty sadiya. Da yake lamari idan nakudi ne bbu matsala suna zuwa gdan gyaran jikin aka watsar da kowa a ka dukufa akan fatima babban guri ne kamar wata ma'aikata, ayyuka sukeyi kala kala, cikin awa biyu xuwa na uku fatima ta sauya gaba daya ta dauki walwali abin ba acewa komi, anayi ana turara mata jiki da turaren wuta masu kamshi mai sanyi da shiga rai ga humra ana mulkawa. Bayan an gama da nan aka zuba mata kamshi kafa da hannu masu gyaran gashi na tsaye sunayi fatima tazamo tamkar tauraruwa a cikin taurari hatta su ummi da sadiya lalacewa sukayi gun kallon fatima sbda kyau datayi ya wuce misali, ga wani kamshi mai dadin gaske na tashi a jikinta, basu dawo gda ba sai karfe sha dayan dare, tuni angonta yadamu da son ganinta yanata kiransu a waya suna mishi dariya. Yana tsaye yana waya dawasu abokansu yan kaduna yaga shigowar motarsu, yayi saurin katse wayar yace zai kira yafito. Kafin ya iso garesu anty sadiya taja hannun fatima suka shige gida, suka turata toilet wai tayi wanka ba ta son dr. khalifa ya ganta lokaci guda yarikice. Jikin fatima kawai yake bukata, yashiga dakin mama tana zaune tana hada wata zuma da tsimi da za taba fatima. Tayi mai wani irin kallo ganin yanayin daya shigo dashi tace "kai kuwa lfya? Yace "Mama ina fatima? Tayi tsaki tace "wai kanka daya kuwa? da tsakar daren nan kake nemanta me za tayi maka? Ya dan langabar dakai yashiga in ina yarasa abinda zai cewa mama, karshe yace "wai da indomie za tadafa min. "To da basu dawo da ita nan gdan ba fa? Wa zai dafa maka? ta watso mai tambayar tana harararsa tace "to bace min da gani kaje kace ummi tadafa maka. Zaiyi magana tace "Allah idan kana matsa mata xan hanaka ganinta. Yafice zuwa falo abinda yasawa ransa shi ne ba zai iya barci ba sai ya rungumi fatima a jikinsa ko ta halin kaka. Anty sadiya tafito daga dakin dasu fatin suke za tashiga dakin mama ganin shi a tsaya yasa tace "yaya akayi boy? Ya tsareta da ido fuskarsa ba walwala yace "ina fatima? Tace "wanka take. Bai ce komai ba yasa kai dakin ummin, ta bishi da kallo tana jinjina kai tashige dakin maman tazauna kusa da ita tace "in kin gama ki ban in ba ta tasha ba za tasaki jiki tasha a gabanki ba. Mama tamika mata a sanyayae tace "kazar "yar sokoto ta kawo ma yana kitchen idan za ta iya ci ki hada ki bata wannan fitinannan yaron za a sha matsala dashi dole sai an gyara fatima, sai dai ni kam jikina ya yi sanyi wannan soyayyar da khalifa ke nunawa fatima ta yi yawa, kada fa idan sun je aun zauna tayi amfani da wannan damar tadinga juya shi kamar waina. Anty sadiya tace "don Allah mama kada ki sawa ranki irin wannan damuwar kowa da lokacinsa kuma a yanayin fatima ba za tayi haka ba yarinyar ta samu tarbiyya me kyau. Mama tace "uhm sadiya mutum ba a shaidarsa mace tana da wani irin hali yayin da da namiji yadaga hankali a kanta yana sonta dayawa shike nan tasamu damar yi mai yadda taga dama maimakon tayi amfani da wannan damar gun rikeshi da kyau sai tadinga murza kambunta yadda taso. Sadiya tace "mama ki yarda da Allah ki yarda shi ne me komi, addu'ar da kikewa khalifa ke da abbansa ba zai taba faduwa a kasa ba, insha Allahu bbu abunda zai faru da aurensu sai alheri, kidauki fatima kamar "yar dakika haifa sai Allah yakalli kyakyawan niyyarki yatsare khalifa daga dukkan wanda zai masa abin da zai gusar da hankalinsa, idan kaji tsrom Allah ka kyautatawa 'ya'yan wasu Alkah zai dubi na ka zuri'ar ko ba ka da rai. mama tace "Hakane anty sadiya ina kaunar fatima dayawa nima yanayin soyayyar da khalifa ke nuna mata ne yayi yawa ni na rasa me yakeji a zuciyarsa game Da ita, in dai akan fatima ne to fa zuciyarsa ba ta da sukuni, zai iya hakuri akn komi banda ita. Duk su mama na wannan tattaunawar ne dai dai lokacin da fatima tagama wanka tafito daga toilet daga ita sai dauri kirji sai ko dan tawul din data yafa a kafadarta bata san khalifa na dakin ba, ganin shi kawai tayi tsaye jikin madubi ya kuma zuba mata wadannan fitinannun idon na sa masu tsananin kyau da laushi, tatsaya sororo tana kallonsa kamshin dayaji yana tashi a jikinta yaji kamar ana fizgarsa zuwa jiki? ta, lamarin dayayi sanadiyar daya kasa rike kansa sai da ya isa gabanta yaja hannayenta biyu yahadata gam da jikinsa yasa harshensa yana lasar lebbenta, gaba daya jikin su yadauki rawa ita tsoro takeyi kada wani yashigo ya iskesu a haka yayin da shikuma jikinsa na rawa ne sbda wata fitinanniyar shawa data jefa shi a cikin yanayin da bai taba shiga ba a rayuwarsa, yakama kunnuwanta yana gaya mata kalaman dashi kansa bai san yana fada ba, har sai da fati taji tsigar jikinta na tashi tasa hannu tarufe mai baki. Kwatsam ummi taturo kofar dakin tashigo, khalifa yasaki fati yajuyo yayi wa ummin wani irin kallo yafice, ta ajiye abin cin data zubo musu kamar ba abinda tagani tashiga jan fatin da hira nan kuwa zuciyarta kamar za ta tarwatse sbda wani azababben kishi da taji ya tokare mata kirji, sama sama fatima ke iya magana, hira ta ki yiwuwa domin hankalin fatiman ba ya tare da ummin, Dr. Khalifa angonta ne kawai a gabanta shi take muradin kasancewa tarea dashi. ***** Tunda sassafe wasu yayyan innarsu fatima suka iso gdan duk da ba yau ne za a kai amaryar ba sai sati ya zagayo amma za su dafa abinci sbda 'yan'uwa maza daza su zo domin auran. Yaya kubura tace "Ina amaryar ne? Inna tace "Tana gdansu angon amma yanzu za tazo. Gaba daya suka rike baki sukece "wani irin tsarin banza da wofi ne haka? Yaya kubura ce tafi sauran fusata tace "Ni na taba jin irin wannan? yaya za ayi ace amarya na gdansu ango? Ke ba kya tsoron ace kwadayi ne yasa ta tattare a gdansu angon? Yaya rabi tace "ke kike wannan xancan kubra tun yaushe ake cewa kwadayi ne yasa ciki sati daya aka fasa bawa musbahu aure aka bawa khalifa don kawai babanaa yanada farcan susa, to ballantana yanzu ace tan gdan wai acan ma takwana, in barda zuvarwa kai daraja meye wannan? Inna tace "Ai ba wani abu yasa taje ba sbda kunshi ne da gyaran gashi. Yaya kubra tace "duk wani gyara ita batasan inda za taje ayi mata ba sai ta tafi yawon tallan kanta a gdan surukan, To Allah dai ya sawwake amma gskiya kidinga lura kuna jan mutuncin ku irin wannan abu ne ke sawa a dinga wa mutum gori daganan mutumci yazuve. " Inna dai tana jinsu bata sake cewa komi ba, itama kanta ba a son ranta fati takwana gdan su Khalifa ba mutumcin mama ne yasa ba ta iya musu da ita, sun nuna suna son fati daywa, hakanan fatima tasauya ra'ayin ta gaba daya akan Khalifa. Wuraren karfe takwas da rabi su fati suka shigo tare da ummi, tun kafin matar da aka dauka musamman dan tayi mata kwalliya tazo fati har ta fara daukar ido abin gwanin ban sha'awa, kowa yakalleta sai ya kara, fuskarta dai ce ta dan kumbura sakamakon rashin barcin da bata samu ta yi sosai ba a daren jiya, tsabar tunanin khalifa da kaunarsa da asuba ne bayan sun idar da salla tazauna jugum tayi tagumi. Ummi tajanye hannun na ta tace "haba matar yayana tunanin yayan ke damunki? Tayi mata wani irin kallo tadauke kai bata ce komi ba, ummi tayi murmushi tace "Ba kiyi laifi ba dan kin kasa sukuni akan dr. khalifa, ni na san tabaki yake yana dandana miki zuma a baki, shiyasa hnklinki ke tashi dayawa, fatima ba ki da laifi don kin damu da yaya Khalifa, bai dandana wa mace irin wannan zumar ba ta rikice akansa ballantana ke da yake nuna miki so irin haka har yana hada jikinsa da naki'. ***** Karfe goma sha dayan safiyar lahadi daruruwar alummar musulmi suka shaidi daurin auran Dr. Abubakar Saddiki Muhammad da Fatima Musa, daurin auran daya samu halartar manya manyan mutane tun daga kan manyan yan kasuwa da sunan su yayi fice a fadin kasar nan zuwa manyan yan siyasa da kusoshin gwamnati da jiga jigan malaman da ake ji dasu a jihar mu ta kano, hatta bangaran sarauta sun halarci daurin auran ballantana likitoci da abin yazama nasu maganin a kwabe su, maroka suka rinka yayata sunan ango da amarya da iyayansu yayin da gdajan rediyoyi ke ta bayyana yadda abubuwan ke gudana, sai shiga ake ana fita da nau'ikan abubuwan ci da na sha na alfarma daga gidansu dr. khalifa da gdansu inna. Angon ya sha ado ya yi kyau daya wuce misali, abin sai wanda yagani shadda ce mai tsadar gaske fara kal riga da wando da babbar riga sai akayi aikin babbar riga da blue din zare, hula kansa ma ya kasance fara da blue takalminsa blue, a ckin gda amarya fatima irin shigar ango aka mata fari da blue, ba a iya tantance wa yafi kyau tsakanin angon da amaryar kowanne ba baya bane ko ina masu hoto ne da bidiyo ke daukar ango da abokanansa sannan suka shigo gda tare don gaida iyayan amarya.. Gdansu fatima ma cike yake da mata anata rangada guda d sanya albarka, fatima ta zamo matar dr. khalifa rana ba ta karya sai dai uwar diya taji kunya, farar tukunya mai fidda farin tuwo, kirari iri iri maroka suke tayi musamman a gdansu khalifa inda anan ne ake facaka da kudi kamar ba nemansu ake ba. Abba yadinga kyautar muhimman abubuwa yana fadin "ai wannan rana ce ta farin ciki garesu ranar auran dansu daya. To fa. Ina su hajiya hauwa da hajiya saude kannan abba iyayan ummi? wadanda duk wani burinsu a wannan rana bai wuce ace da diyarsu ummi aka daura auran ba, amma hakan bai yiwu ba, khalifa da iyayansa basu damu da damuwar kowa ba sai ta su. Da farko basuyi niyyar zuwa gdan ba a yau daga bisani saude tace gara suje karshe a zo anayi damu ai idan baka iya kama barawo ba kai sai ya kamaka. Ba za ka iya shaida bacin ran dake tare dasu ba amma zuciyarsu fal bakin cki da takaici, da isowarsu a safiyar abba yaraba musu sabbin kudi rafa rafa yace suyi liki, duk da haka ransu ba dadi tunanin su shi ne da da ummi aka daura auran nan ai sun more irin wannan dukiya haka. Bayan gama daurin auren suka kebe a ckin wani daki, saude tadubi hauwa tace "ke wadannan mutanen ba na wasa bane sun fi mu shiri. Hauwa tace "Yo ba kiji abin da malam yace jiya ba? yace ai uban fatima ne yahada wani gagarumin asiri ya dabaibaye zuciyar khalifa yadda b ya son kowacce mce si yarsa fatima shiyasa muke tayin aiki aikin ya ki kama khalifa, yace. a wani lokacin yana so ya so ummi sai asirin yayi tasiri a zuciyarsa yakasa katabus yaji kamar ba ya da iko a kansa sai son fatima. Hajiya saude tace "Haba ko da naji ni nasan arina wai an saci zanin mahaukaciya, wannan aikin da malam keyi ba zai tashi a banza ba da mugun abinda da sukayi, duk mu mun manta uban fati malami ne sai da yayiwa khalifa asiri duk iyayan ya gama dasu anma ba komi jiya da dare na je na kaiwa malam kudin bajimin sa dayace a kawo za a zubar da jini yace musa ido za muyi kallo dakansu sai sun gane kurensu kowa yaci tuwo damu miya yasha. A DAREN FARKO 33 Mama tana iya kokarin ta akan bawa su hajiya hauwa 'yanci a gdan dan dai kada ayi korafin amma bata tsira ba duk inda tayi binta suke da harara suna kwafa. Karfe hudun yamma angwaye da wasu daga ckin mutane aka fara daukan mutane zuwa inda akayi gagarumar walima maza zalla, ana kiran slar magriba aka tashi kowa yana farin ciki da sanya alheri. Karfe tara da rabi na daren dr. khalifa ya fito daga wanka a dakinsa abokansa biyun nan Dr. Bashir da Dr. Hafiz su biyu suka rage bayan kowa ya watse,yafada bisa gado yana mai da numfashi da kyar. Dr. Bashir yadubeahi yana dariya yace "Ango na amarya, amaryar ka ta yi kyau yau abin har ba a magana sai dai kwalelen ango, ko ganinta yanzu ba damar yi. Dr.khalifa yace "Ba komi ai komi lokaci gareshi rana ita yau iyanzu babu wanda zai mini shamaki tsakanina da ita zamu kwana a daki daya sai yadda naga dama da ita. Kafiz yace "Oho dai ba haka aka so ba wai kanin miji ya fi miji kyau, ko in je in dauko maka ita? Dr. khalifa yace 'Rufa mini asiri dazun nan mama takirani dakinta tana gaya mini idan taji na je gdansu fatima sai ta batan rai don Allah kaji wani danyan hukunci mutum da matarsa. Dr. Baahir yace "Ai ta yi ma haka ne don ta san halinka, a gdan iyayan na ta ma sai kabita ka matseta kai ba kunyar mutane kake ji ba. Yace "kai ba a irin gdansu fati ake wannan ba ka san akwai inda ake barin halak don kunya. Dr. Hafiz yace "To kai ka san kunya ne Abbakar? ko dayake yanzu ka sauya kamar ba kai ba, son fatima ya sauya ka dayawa kamar bakaji tashan 'yN mata ba, tunda kadaura idonka akan fatima kadaina tunanin 'yammatan ka, tun wasunsu na damuwa suna damun mu har sun hakura. Yace "Kai ni ai babu sauran wata diya mace a zuciyata tunda na mallaki gimbiyar mata fatima ta rufe kofa gaba daya. **** Da gari ya waye mama tazo da kanta taroki inna da malam akan a bata fatima akwai shirin da za ayi mata, a zuciyoyinsu basu ji dadin haka ba har ita kanta fatiman sbda ta san dr. khalifa matsamata zai yi a gidan amma mama tafi karfin komi garesu, iyayan khalifa suna da kimar da za su iya yi musu komi surutun mutane ne yake damun su fassarar nan ta kwadayi ita take damin inna komi akayi idanuwan mutane na kai kuma sai sun yi magana. Bayan tafiyar mama abinda inna da malam ke tattaunawa knan, Fatima na dakinsu na yara a kwance tana fama da barcin gajiya ita kanta ta san a yanzu ta canja, ta baza kunnuwa tana addu'ar Allah yasa kada malam ya amince da komawarta sai dai kash sai ji tayi malam din na cewa ta tafin kawai. Amma dai kija mata kunne tasan abinda takeyi, kuma tasan kanta. Ya sa kai yafita. Inna ta kwala mata kira ta fito ckin rashin kuzari kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki tazauna daf da ita, tace "To malam dai ya amince da zan ki a gdansu khalifa, jan kunne da zanyi miki shi ne ke diya macece ki san darajar kanki idan har kina son ki samawa kanki kima a gun khalifa na san yadda kike biyewa al'amarin khalifa sbda son da kike masa, to kisani namiji sai ana taka tsan tsan da al'amuransa dole mace Tayiwa mijinta biyayya domin aljannarta. na karkashin kafarsa amma kada ki zake karki ja wa kanki abin fadi. Jin tayi shiru yasa fatima a sanyaye tace "Inna don Allah kibarni anan nima ba na son zama a gdan nasu. Tace "to yaya za muyi kin san ko a yanzu khalifa ya fimu iko dake in dai aure ke sa ayi iko da mace tunda an daura kasancewar ba a kaiki gdansa ba ba zai hana dokar Allah aiki a kanki ba a cikin hakkokinsa da Allah ya jarabta akanki, kai mace daki ba shi ne sharafin biyayyar aure ba shaidu da sadaki sune aure in dai an yi su ya zama dole mace tayiwa mijinta biyayya ko a ina take kuwa kinga in dai haka ne dole mu amince da zuwanki gdansu khalifa. Fatima taji zuciyarta ta karaya bata ankara ba kawai sai jin hawaye na xubo mata, ,ita kanta bata san kukan metake ba batasan ma'anar kukan na ta ba. Inna tayi murmushi tace "To meye na kuka, khalifa zabinki ne fatima kin manta yadda kika dinga kuka kina rokon a bashi ke? Duk abinda khalifa yazo dashi dole kiyi biyayya domin aure kikayi na soyyaya na zabin ranki da zuciyarki,ban taba zaton xan ga hawayenki ba bayan kin zamo matar khalifa fatima, ki share hawayenki ki mike kafafuwanki kiyi walwala kin auri wanda kike so. Fatima tayi jugum ta san magana ce irin ta gugaz zana inna take gaya mata akan abinda tayi akan musbahu ,taci gaba da kuka sosai ,taci gaba da kuka sosai inna ta tashi tashiga hidimomin gabanta tana fadin "Ai sai kiyi. Fatima ta koma ckin daki ta kwanta bata san abi? da ya daga mata hankali ba hawayanta suka ki tsayawa, ummi ce ta yaya lavulan dakin da sallama tayi turus tan kallonta tace "Kukan amarci kike tun yanzu fati ko wani abu aka miki? Babu Babu amsar da za ta iya ba ummi don ita kanta bata san kukan da take ba. Ummi tace "to koma dai meye kisaki kukan tashi kiyi hakuri kiyi wanka ki shirya tafiya za muyi ango yana jiranki za mu fara fita hada kayan sayan baki kafin na lefe shi khalifan ma ya so ace Dubai za aje a hado har kayan dakinki mama ta ce babu inda zai tafi dake ba tare da an kaiki gdanki ba. Fatima dai ba ta son magana ta tashi tayi wankan, ummi tagama shirya mata kayan ta, suka yi sallama da inna suka nufi gdan mama, dogon hijabi da nikab tasa suna shiga harabar gdan fati tayi sauri tashige ciki don kar su hadu da khalifa ta zauna a falo a kunyace tagaishe da abba da mama ko kanta ba ta iya dagawa. Sai mama ke mata dariya tace "in har wannan kunyar za ki sawa ranki za kiyi ta wahalar da kanki ke kawai ni dai ba suruka na dauke ki ba a matsayin diyata kike har yanzu, tashi ki wuce daki idan kin huta akwai girke girke na abokan mijinki. Da zarar an kra dr. khalifa mijinta sai taji wani iri a jikinta, tana jinjina alamarin kamar a mafarki ,duk yadda ta so shi a ranta take tsananin son tadinga ganinsa a ko yaushe sbda burgetan da yake yau tsoron ganinsa take, fatanta kada yashiga gdan suhadu, tayi sa'a kuwa har magriba tayi bai shiga ba tuni suka gama hada abinci mai rai da lfya suka shirya kan tebur tashige daki tayi wanka tasa doguwar rigar shadda koriya takara gyara gashinta tayi sallar isha'i tana shirin hawa gado takwanta aka turo kofar cikin tattausar muryar nan tasa yayi mata sallama. Khalifa ne.. A figice tadago idonta taxuba masa yana ckin wata lafiyayyar shadda brown me haske an mata aiki da dark brown din zare irin dinkin tazarcen nan, kamshin turaransa yadinga ratsa mata zuciya, ya fidda gilashinsa ya baibayeta da fitinannun idonsa ba walwala sosai a tare dashi yace "Fatima. Duk kokarin da tayi na tsayuwa ta kasa svda rawar da kafafunta suka shiga yi, ta durkusa a gun tadafa gado. Ya kara kirn sunanta a karo na biyu a nan ne ta amsa, yace "Tun karfe nawa kikazo gdan nan? Muryarta na rawa tace "sha biyu. Yace "Amma ba ki san hanyar dakina ba ballantana ki zo ki gaisheni. Gabanta yafadi tadago ido a tsorace tana dubanshi abinda ta gani a cikin kwayar idonsa yasa tayi saurin maida kanta ksa, yace "kin yi daidai knan? A hankali tace "kayi hakuri. Yayi saurin katseta yace "Ba zan yi hakurin ba. Tabude baki cike da mamaki tana kallonsa abin ya ba shi dariya ya iso gabanta ya kamo hannunta yamikar da ita tsaye, kai tsaye yahadata da jikinsa ya matseta yadda ba za ta iya motsi ba, ya cusa bakinsa ckin nata yadinga tsotson lebbanta ckin wani irin salo na gwanancewa a harkar sarrafa mace har jikinsa yafara rawa yafara manta a ina yake. Kwatsam yaji mama na kwalawa fatin kira daga falo dasauri yasake ta yafito falon, mama tayi mai wani irin kallo fuskarta a tsuke tace "Daman kana ciki? Yayai dan murmushi yana sosa keya yace "Yanzu na shiga. Ta harare shi tace "To me ka shiga yi? Yace "A'a gani nai dai ban ga fatin a falo ba shi ne na bita ciki. Mama taja tsaki tace "ka ji dashi dai ina fatiman. Yace "Kayanta take swa, ya wuce tebur yana bude buden kayan abincin yace "mama asa su fatima su kawo mana dakina muna da yawa. Tace "kai kafita daga idona khalifa babu abunda zai kawo fatima dakinka kuma idan baka saurara dashiga dakinsu ba zanyi maganin ka. a zuciyarsa yace "a baya ma na taba fatima ballantana yanzu, ai zancan ace kada in taba ta ma bai taso ba, mutum da halak malak. Unmi ce ta taya shi kai abinci tana zolayarsa yana dariya, ummi tana mamakin yadda khalifa yazamo mai mata walwala akan fatima ya dawo kamar ba shi ba, mutumin da murmushi ma a baya tsada yake masa, shi ne yanzu ake hira dashi yana dariya, in dai kana son ganin walwalar khalifa yi masa zancan fatima, wannan lamari yana taima zuciyar ummi tare da gigita ta, abinda ta tabbatarwa ranta shi ne na raba zuciyar Dr. khalifa da son fatima sai dai mutuwa idan ransa yabar jikinsa amma ba dai wani boka ko malam ba. A DAREN FARKO 34 Abokansa suka tsare su dtambayar ina amarya tunda an ce tana gdan dole suna son ganinta, khalifa ya marairaice fuska yace "to ya zanyi !? Mama ta yi ruwa ta yi tsaki ta ce fatima ba za tazo dakin nan ba, ni ban taba ganin irin wannan tsarin ba mutum da matarsa a dauki ido a dora mai ko kallon fatima nayi mama sai ta hau fada na rasa dalili bata san jin zuciyata nake kamar za tafashe ba idan tana hanani ganin mata ta. " Wani a cikinsu mai suna Nura yace "Ai mama tayi min daidai sanin halinka ne yasa tayi ma haka,idan aka kyaleka za ka iya kwana da fatima a dakin nan da safe kuma kayi mirsisi kana kallon idon mutane. Khalifa yakara fusata yace "Kai da Allah kar ka dada batan rai haramun ne dan na kwana da matata. Dr. Bashir yabushe da dariya yace "Wannan ihu ne dai bayan hari in ka isa katafi dakin mama kayi mata wadannan fadace fadacen karshe tace sai bayan wata uku za a kaima amaryar in ga kuma yadda za kayi. Khalifa yayi dariya yace "Tabdijam ai kuwa da na basu mamaki nima in ga yadda za ayi dani. Nura yace "Uhum ka bisu dai a sannu idan kai baka ba su mamaki ba su subaka mamaki. ***** Mama tayi tsayuwar daka gun gyara amarya da abubuwan da za sukawo mata ni'ima a jikinta, ita dai burinta hankalin danta yakwanta,. Fatima ta cika ta batse ta kara wani irin kyau kyaun ma mai ban sha'awa, tayi fresh babu abinda ke damunta. Mama ta hanata fita ko ina don kar ta shiga dakin khalifa sai dai shi in ya shigo su gaisa iya fali. Ya yi fushin ya yi mitar har ya gaji ya zuba ido shi kadai yasan damuwar da yake fama ita a zuciyarsa, a ranar da fatima tayi kwana biyu a gdan ana ya jibi za a kaita gdan Dr. Khalifa aka kai kayan lefenta gdansu, lefen da aka dinga surutun karya tayi yawa, wannan ai almubazzaranci ne da dukiya kamar ba masu neman taimako da za a kashe dukiya irin wannan a lefe,? Abinda 'yan'uwan abba sukayi ta fada knan, daga bisani wannan yazamo ba abin surutu ba lokacin da aka kaisu ganin gdan dr. khalifa da fatima za su zauna wanda yake court road, da irin kayan alatun da aka dankara a gdan abin sai ya wuce ayi magana da baki sai gani da ido, duk wani abinda za a kawata gda dashi a kalla asan ya yi kyau sai da akasa a cikin wannan gda, komi ya kammala amarya kawai ake jira. Washegari ranar asabar wanda yakasance saura kwana daya akai fatima gdanta tatashi da ciwon kai abisa dole mama tace khalifa yashiga dakinsu ya dubata, shi bai ma san ba ta da lfya ba svda hushi yayi yadaina shiga harkar mama da ita kanta fatin, idan ma yashigo falon ta gayar dashi fuska a tsuke yake amsawa sbda ya gaji da jan ran da ake masa kawai don an ga ya damu. Lokacin daya shiga falon suka gaisa da mama yawuce kan tebur zai ci abinci ta dubeshi tace "Yau baka tambayi matar ta ka ba. Ya dan tabe baki kamar bai damu ba yace "Oh tana ina ne ? Tace "Tna daki ba ta da lfya. Yaji wani irin abu ya dakar masa zuciya duk da haka yashare bai bari mama ta fahi ; ci halin da zuciyarsa tashiga ba, yayi zamansa yafara tsiyaya tea a kofi yana fadin "Me ya sameta ? Ta amsa "Tashi tayi da ciwon kai da amai idan kagama kashiga kaduba ta. To kawai yace yaci gaba da cin abincinsa, da ya gama din ma maimakon yashiga dakin au fatima sai yadauki hanyar fita. Mama tace "Ba za kaduba fatiman bane ? Yace "Af har na manta. Yamurda kofar dakin tana kwance bisa gado nannade da bargo, idanuwanta a rufe, yazauna kusa da ita yayaye bargon data rufe, ya taba wuyanta zafi sosai, yace "Subhanallahi. Nan da nan yaji tsigar jikinsa ta kama tashi, yakira dr. hafiz a waya ya gaya masa irin magungunan dazai aiko masa dasu, yafita dan yadan hada mata abinda za taci sbda allurar da zai mata. Mama tace "za su fita da anty sadiya yanzu za su amso dinkunan fatima tunda ba kowa a gdan yazauna yalura da ita. Zuciyarsa tayi mai fari kal 6au ya sami dama amma sai yadan kanne yaduba agogo yace "Da fita zanyi kuwa. Tace "Kadan jira mudawo bai dace a barta gda ita daya ba sai 'yan aiki alhali ba ta da lfya. Bayan fitar su mama yahada mata shayi ba madara yazuba mata dankali shi kadai yanufi dakin, yazauna gefen gadon yajawota jikinsa yana lallabata kamar kwai yarungumeta yana bata shayi tana dan sha a hankali tace ita dai ta koshi. Wata daga cikin ma'aikatan asibitinsu dr. hafiz takawo magungunan yabata tasha yayi mata allura guda daya tana zuba shagwabarta yadda taga dama, hankalin khalifa yakara tshi zuciyarsa ta tsimu komi na jikin fatima ya bayyana a gareshi, domin wasu riga da siket ne a jikinta marasa nauyi takara zama fara kal, ko idanunsa bai iya daukewa a kanta ba, itama tana son tadinga kallonsa duk da tanajin nauyinsa, ganin ya fara shafa mata cinya da ciki yasa tadan janye jikinta ta matsa, yayi narai narai da idanuwan nan na sa yana mata wani irin kallo mai daga hankali. Yace "Haba fatima kin san matsayinki a guna bai dace ki biyewa mama kina wahalar dani ba, wai ace fatima tsakanina da ke sai gani da ido daga nesa,. Ni fa mijinki ne ina da hakki akanki ko kin manta ne ? Doguwar ajiyar zuciya tai tace "mama ce ba ta son in zo gunka nikuma ba zanyi abu ? da zai bata mata rai ba. Yace "ai dama ba cewa nayi ki bata mata rai ba, amma ya dace ace ko da daddare ne kina dan fakar idonta kizo dakina kitayani hira ki debe min kewa tunda kin san dole ina fama da damuwa a zuciyata ko ? tunda kika dawo gdan nan dazama kullum dare ba na iya barci sbda kewarki fatima, ina son ko kakane in dinga jin dumin jikinki, ko rungumarki nayi na miki kiss ai zan ji dadi a zuciyata ko ? Amma ke ba ruwanki sai ki biyewa mama ki shareni sai dai in shigo in ganki kyaunki na karuwa zuciyata tayi ta fama da kewarki ya kamata ki tausaya min Fatima. Ya kamo hannunta yakara janta jiki ? sa yarungumeta sosai yaci gaba da cewa "Wallahi fatima ina sonki son da ban taba zaton zan ma wata diya mace a duniya ba, sbda kafin ke ba zan iya tantance miki meye soyayya ba, nidai nasan ina mu'amula da mata amma ban taba damuwa dawata diya mace ba saida nafara ganinki nadin ga jin tamkar zan mutu idan ba na tare dake, duk wata natsuwa takan gushe mini idan ban ganki ba, shi yasa na rikice na gigice lokacin danaga katin daurin auranki da musbahu, Fatima idan ciwon sonki ya tsananta a zuciyata sai in dinga jin kamar ba zan yi doguwar rayuwa dake ba, fargaba takan kama mini zuciya in rasa yadda zanyi da raina, fatina dan Allah,. Yayi shiru yakasa cigaba da magana. Tausayin sa yakamata sosai taji ciwonta ya sauka gaba daya babu abinda ke gabanta sai khalifan tadinga jin wani so da shauki yana ratsa mata zuciya kamar yau ne tafara sanin khalifa, a wannan lokacin da kanta tasa hannayenta biyu tarungumi dr. khalifa kam kam a jikinta tana hawaye. Yasa harshensa yadinga lashe hawayen na ta yana fadin "fatima, fatima kukan me kikeyi. Ta tura bakinta cikin kunnuwansa tace," kukan farin ciki ne kada yadameka. Yadda tayi mai shima haka yayi mata yace "Farin ciki kala kala ne fatima don Allah fassara min yanayin farin cikin daya sa ki kuka. Tace "Babu wani farin ciki ga masoyi wanda yawuce mai sonsa ya soshi, hausawa kan ce son maso wani koshin wahala ne, idan mutum yana son wanda ba ya sonsa ya gamu da wahala idan kuwa mutum yana son wanda yake son sa yana ckin farin ciki da kwanciyar hankali, a yau ban san wanda yafini farin ciki ba shiyasa nake kuka. Khalifa yayi murmushi yace "Allah sarki ashe in dai hakane za kiyi ta kuka tunda ni yanzu nafara nuna miki so da tattali har zuwa ranar da Allah (SWT) zai karbi rayuwata. Fatima ina fatan Allah yasa in mutu in barki sbda nasan insha Allahu za kiyi tamin addu'ar neman gafarar Allah. Bayan haka ina jimantawa kaina halin da zan shiga idan na rigaki mutuwa, mutuwata sutura ce a gareni idan yakasance kin mutu fatima don Allah ki dinga yi min addu'a. Ta katse shi ckin damuwa tace "Don Allah kadaina batun mutuwar nan haka. Yace "kyaleni in yi fatima duk mai rai mamaci ne duk yadda muka kai ga son rayuwar duniya sai mun mutu, tuna mutuwa shi kesa mutum yayi wa kansa hisabin ayyukansa yadinga sanin cewa zai hadu da Allah kuma zai ga abinda ya aikata me kyau ko kishiyarsa. Tace "To nidai na ji don Allah mubar wannan maganar. Yayi murmushi yace "Shikenan na barta, yaci gaba da dan latlatsa mata jiki har sai da yayi nasarar kashe mata jikin gaba daya ya kasance ba ta da wani kuzari, sai yadda yayi da ita, duk zazzabin da take fama dashi sai da taneme shi tarasa sai tsabar tsananin son khalifa da shaukin sa. Ya zare jikinsa yamike yasawa kofar key yakara rufe lavulayen dakin yayi dan duhu duhu, tsoro yacika zuciyar fatima ta tsahi zaune tana rokon don Alla ya taimaketa kada yayi mata wani abin, yace "kiyi hakuri kawai fatima nima ba na son yimiki wannan abin anan gdan sai a gdanmu amma a halin yanzu zuciyata ba xa ta taba iya hakuri ba, kada kijefa nin ckin fushin Ubangiji kisa in je in aikata sabon Allah, kada kijefa kanki kema ckin fushin Allah kuma kinsan matsayin matar datake gujewa mijinta. Jikin fatima yadinga rawa ganin yadda yanufo ta gadan gadan sai kawai ta sallama zuciyarsa ta gama karaya ta tabbatar idan bata bashi hadin kai ba zaiyi ta karfin tsiya, tunda idanuwan sa sun rufe hankalinsa a tashe yake sosai. Kokarin da khalifa yayi shi ne ya saita kansa sanin cewa fatima budurwa ce wadda taba taba sanin da namiji ba, sannan yarinya ce karama in barda haka da yau fati ta yabawa aya zaki ? ta, duk ilahirin jikinta saida khalifa yabi yalashe, yajuya ta nan yajuya ta chan tading jan numfashi dakyar don kafin a kai ga bbabban al'amarin fatima ta galabaita, lokacin datafiya tai nisa yasamu nasarar rabata da budurcin ta bata san lokacin data saki wani kara mai karfi ba sbda zafi da taji ya ratsa mata har kwakwalwar kanta, tafita hayyacinta hatta numfshin ta sai da yayi daukewar yan mintuna sannan yadawo, khalifa yana sane da halin da take ciki sai daya gamsu son ransa sannan ya kyaleta. ***** A DAREN FARKO 35 Tuni zazzabin fatima yadawo jikinta yadauki zafi sosai, yayi saurin dagota yakaita bandaki yasa tawul da ruwa yadinga shafa mata a jikin sannan yace tadaure tayi wanka. fatima kuka take sosai da kyar tayi wankan, gaba daya jikinta ciwo yake mata ba karamar wahala tasha ba. Idanuwanta suka yi ja, bayan ta gama wankan tadaura zaninta tazauna jugum tayi tagumi tana tunanin wannan azabar ake sha idan an yi auran ? shin haka khalifa zai yi ta gwada mata karfi yana gana mata azaba, kai gskiya da sake. Yaturo kofar bandakin ya shigo, a tsorace tamike har abin ya bashi dariya daya fahimci tsoronsa take ji, shi kansa ya san ya ba ta wahala, ya matsa dab da ita yace "kiyi hakuri fatima kowace mace da kike gani tana rayuwa da mijinta sai da tasha wannan wahalar, ki kwantar da hankalin na lokaci daya ne daga yau ba za ki kara jin zafi haka ba. Tadinga sharar kwalla yace "Don Allah kidaina kuka in dai ba so kike nima in miki kukan ba. Wannan abin na yi miki ne don ina sonki, bai dace yazamo abun damuwa a zuciyarki ba kinga gdan nan ba mu kadai bane idan su mama suka dawo suka ga kina kuka kinsan za tadamu don Allah kiyi hakuri kidaina tunda ba kyaso ba zan ka ra yimiki ba. Ya lallabata yakara rungumeta a jikinsa yana gaya mata kalamai masu sanyi har zuciyarta ta dan lafa, tafito daga toilet din ta taras ya sauya shimfidan gadon da kansa, mutumin da ba abinda yasani a rayuwarsa sai yahuta komi yimasa ake yi. Bayan ya gama yafito lokacin ta gama sa kayanta ta haye gado har yanzu idanuwanta jawur suke, ta ki yarda su hada ido da khalifa a bisa dole ya kyaleta yakoma gefe yazuba mata ido yana murmushi, shi kadai yasan abinda yake ji a zuciyarsa game da ita, shi dai kam yau ya san ya kwanta da mace ya gamsu yafara sanin meye sirrin dake tare da matar aure ta sunna wadda ke da banbanci data bariki, wadda a baya suka dauka itace rayuwa ta cinyewa da burgewa, ashe duk wani sirrin kwanciyar hankali na tare da matar aure, hakika zai rike fatima dakyau domin yau kam ya san ya yi aure na birgewa da morewa, yadaga hannunsa yna ma Allah godiya daya bashi fatima. Yamike yadan shafi fuskarta ba ya son fita daga dakin amma haka yadaure yafita, hankalinsa a kwance ganin hr yanzu su mama basu dawo ba, sai dai yana fitowa yaci karo da motarsu ta shigo, a tsatsaye yayi musu sannu dazuwa ta tambaye shi jikin fatin yace da sauki yadau motarsa yabar gdan. Dakinsu fatima yafra shiga, jin zafin da jikinta yayi fiye da dazun yasata kira dr. khalifa a waya ta hau shi da fada tace "Ya naji jikin Fati da zafi haka ? Baka ba ta magani bane ? Gabansa yafadi yayi zaton ko wani abu tafahimta, ya san halin mamansa da wayo, Har allura nai mata mama zai sauka ne. Tace "wane irin xaxxabi ne wannan an auna jininta ? Yace "Ina zuwa za mu zo da Br. Bashir yanzu mu auna. Ya iske Dr. Bashir a office dinsa a asibiti ba aiki yake ba kulle kansa kawai yayi yana hutawarsa, Dr khalifa yace "Ka taso muje ka auna min jinin matata zazzabi yake damunta. Idanun Bashir a lumshe yace "Kai me kakeyi da baza ka debo jinin kataho dashi nan a auna ba, don Allah ka kyaleni barci nakeji jiya kwana nayi ba barci shi yasa naki tafiya gda don ba za subarni in yi barci ba idan naje. Dr. khalifa yace "Don Allah taso muje mama sai fada take min. Dr. bashir yatashi yana mita yadauki wasu kayai aiki suka shiga motar dr. khalifa suka danno gdan. Fatima bacci take sosai sai mama ce a kanta ko da jin yanayin fitar numfashinta ka san tanajin jiki, mama tafice tabarsu. Dr. khalifa yazauna kusa da ita yadakko hannunta yadora kan cinyarsa ya amshi sirin jin yasoka mata akan jijiya zai debi jininta tasaki kara mai karfi, yavuga kafa da karfi yace "Oh my God ka ga abinda nake gudu ko. Dr. Bashir ya amsa jinin yana harararsa, yasaka a cikin waya 'yar na'ura daya riko a hannunsa, Fatima ta tashi takama kuka. Dr. khalifa ya kara rudewa yarungumeta yana lallashinta, Dr. Bashir yace "Ka ga idan ba za ka saketa muyi aikin da zamuyi ba zan yi tafiyata, haba mutun sai nacin soyayya tamkar akanka aka fara aure. Ya maida idonsa ga fati yace "Ke fatima karfafa jikinki ba na son shagwaba tashi kiyi tafiya in gani. Fatima takara narkewa a jikin mijinta cike da shagwaba tace "Ni kafata ciwo take ba zan iya tashi ba. Dr. bashir yafiddo ido yace "Ai ko dole kitashi idan baki mike ba ya ya zan fahimci ciwonki. Khalifa yace "Ni fa ba na son iskanci duk ciwon da za kagani za kagani a jikinta ba za ka wahalar min da mata ba ko don ciwon ba a jikinka yake ba.. Dr. Bashir yace "Allah ta tashi kaine kake kara shagwaba yarinyar nan. Khalifa ya lallaba fatima ta tashi tafara tafiya da kyar takai bango tadawo za ta zauna, Dr. Bashir yace "a'a bai isa ba cigaba da tfya. Khalifa yafusata yace "Kada Allah yasa kadubata in dai sai ta cigaba da wahalar tfya kana gani fa dakyar take tafiya. Bashir yayi murmushi yace "Abbakar kaine ka haifarwa da fatima wannan ciwon. Yaja tsaki "To ina ruwanka kai dai kayi aikin ka mana ni ban son sa ido. ***** An yanke shawarar sai an kai fatima gdan wanda yahada da yini da party guda biyu amma a ranar da za akaita da yamma za ayi kamu hade da walima, ta dai ji sauki sai abinda ba a rasa ba, tun a safiyar yau lahadi tadawo gdansu, a gdan dan hausa aka shirya za ayi kamun, ango da abokanansa ma za su halarci gun domin za ayi kamun ango daga karfe hudu zuwa biyar xa ayi komi a gama, dan haka karfe uku da rabi na yamma aka fara daukar mutane zuwa gdan dan hausan, mawakan zamani na ta cashewa ana wasa ango da amarya da iyayansu mama da abba da inna ma sun halarci gun malam ne yace va zai je ba. Yau shigar ango da amarya ta kasnce dark da light brown, shi shadda ita less, abin ba a magana kyau an yi shi sai wanda yagani duk wanda yake gun ya yabawa haduwar ango da amarya sbda sunyi kyau na daukar ma'ana ayau an ga abinda ake kira matching, kalandar da aka raba a gun ta ja hankulan mutane da yawa domin anyi hoton ne a wani irin yana yi me ban sha'awa wanda yake tabbatar wa da jama'a tsananin so da kaunar dake tsakanin ango da amaryarsa. Lokacin da mawaki yanemi fitowar ango da amarya filin rawa don su taka rudewa gun yayi domin cewa yayi zai ga wanda zai riga wani mikewa tsakanin ango da amarya. Fatima tayi wuf tariga dr. khalifa mikewa, gaba daya aka shiga tafa mata, mawaki yace "kyautar fatima tafarko ce sannan ta dr. khalifa tunda ta rigashi mikewa. Lokacin dasuka iso filin rawan, iyayansu da abokai da dangi aka dinga yi musu ruwan kudi har ya kasance babu abunda kake gani a gun sai sabbin kudi suna tashi sama da kasa. Karfe biyar da rabi akayi kamun amarya karfe shida kuma akayi kamun sngo, shida da rabi aka rufe taro da addu"oi na musanmman daga manyan kuma shaharrarun malamai, bakwai saura kwata aka tashi. Karfe takwas aka shiga wata liyafar inda malamai mata suka yiwa ango da amarya fadakarwa ta awa daya kachal yadda za su zauna da junan su, karfe taran dare aka dauki amarya zuwa dakin ta bayan iyaye da yan uwa da abokan arziki sun yi mata nasihar zaman lfya tare da addu'ar Allah yasanya wa aurensu alheri tare da albarka. Duk inda amarya tagifta sai kamahi mai dadi da sanyaya zuciya ke tashi. ***** Wannan shi ne asalin labarin masu karatu sai kuyi jimirin biyoni kuji yadda aka kaya, an dai kashe Dr. khalifa a DARANSU NA FARKO da aka kai fatima, shin waye ya kashe Dr. khalifa ? shin ina labarin musbahu ku biyoni. ***** Karfe shida daidai na yammacin Alhamis jirgin da ya taso daga Lagos yadire Jidda a airport din Malam Aminu Kano dake birnin kano, tana rataye da jakarta ta hannu, tashiga motar gdansu da aka zo daukar ta, tana shiga gdansu aka rude da murnar ga jiddah ga jiddah, ta zauna a falom mahaifiyarta suka gisa tare da tambaye tambayen 'yan'uwa da abokan arziki. Ummansu tace "ke dai jiddah idan kika sawa ranki abu sai kinyi shi har yaushe kikaje london din da za kice sai kin zo hutu ? Tace "wallahi umma nima banyi niyyar zuwan ba haka kawai a wannan satin naji gaba daya hankalina ya tashi da zaman london din ga mafarkai ina tayi marasa dadi nayi nayi in jure na kasa kwana biyun da suka wuce ko barci bana yi sosai. Umma tace "To Allah yasa alheri, Allah yarabamu da muagun ji da mugun gani. Tace "Amin, ina Abba ? " Tace "Ya fita amma tunda yamma tayi yana hanyar dawowa. Tace "Bari in yi sallah in je gdan su Ummi wai tana shigowa kuwa na san rashin kirkita. Umma tagirgiza kai tace "Wayyo Allah ai ummi gaba daya ba ta ckin natsuwarta hankalin kowa a tashe yake sakamakon wani abin tausayi daya faru. A firgice jiddah tace "Mr ye umma ? ko shiyasa idan namata waya ba ta shiga a kwana biyun nan ? Tace "ai idan kikaga ummi sai kin tausaya mata sbda firgicin data shiga ai na yi zaton ta gaya miki a waya ma ? Jiddah tace "wai me yafaru ne umma ? Umma taja dogon numfashi tace "Uhum ai jidda a ranar aka kashe Dr. khalifa da Fatima ,yanzu haaka zancen danake miki fatima na kulle ana tuhumarta da laifin kashe Dr. khalifa. Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un. Jiddah ke maimaitawa jikinta na rawa tabugi kirji tace "Mama an kashe khalifa ? Ta amsa cikin tausayi. '"An kashe Khalifa jiddah kuma fatima tana cikin mummunan zargi don ita da kanta ta amsawa kotu cewa ita ta kashe shi. Jiddah ta girgiza kai ta mike tsaye tace "Fatima ba za ta kase Dr. khalifa ba, ko da ace ba ta son shi ba ta da dalilin kashe shi akwai wadda na sani wadda ke da dalilin kashe shi kuma shi ta kashe shin ni ce zan fasa kwan, nasan waye yakashe Dr. khalifa. Alhamdulillahi. Masu karatu a yi hakuri ayi jimirin biyoni a littafi na hudu kuma na karshe don jin ya zata kasance, waye yakashe Dr. Khalifa ? A DAREN FARKO 36 NI na san wanda yakashe Dr. khalifa da dalilin dayasa aka kashe dr. khalifa.Jiddah taci gaba da tayar da maganar wanda yasa mahaifiyar ta ta cikin tashin hankali, ta zaro idanuwanta gaba daya cikin kaduwa take kallon jiddah tace "Ke 'yar nan kin san abinda ki ke fada kuwa ? Na sani Ummah, "kin sani jiddah ? "Eh na sani mana umma, idan babu rami babu abunda ke kawo batun rami, wannn maganar da idan mutum yadauketa ya san abinda yataka, haka kawai baxai fada ba sai yana da hujjah hujjar ma mai karfi. Umma ta jinjina kai har yanzu fuskarta a razane tace "Jiddah ki yiwa Allah da Annabinsa kada ki kara furta wannan maganar ballantana wani yajita kija bakinki ki shiru. Jiddah tai murmushi tace "Ummah na yi zaton za kitambayeni inda nasan wannan maganar me cike da gagarumin sirri ba wai ki dinga rokar kada in fada ba, yaya lallai in boye wannan maganar ko kuma kiyi shakkar inda naji ta. Umma ta girgiza kai tace "Jiddah tsoron hadarin dake cikin maganar ne ya firgitani yasa narude ni din ma dakike fadawa tsoro nakeji ballantana idan magana tafasu kowa yaji, kin san irin wannan maganar gagurama ce kuma ni banyi shakka don na ce kina da masaniya akan kisan khalifa ba sbda bazai yiwu kifadi hakan ba face lallai kin sani, mamaki na shi ne a ina kika sani ke da ba ki a kasar, to amma tsoron danaji yasa maganar mamaki ta kau a zuciyata nake roko ki rufawa kanki asiri ki rufa mana. Da zarar kin furta wannan maganar za a shiga tuhumar mu. Jiddah tace "Umma yaya za ayi ina ganin gskiya kiri kiri a rufeta, yanzu sai kisa ido a kashe Fatima ? Alhali ba ita takashe khalifa ba dole in bayyana wanda yakashe khalifa yau din nan, tamike tsaye. "Umma ki kwantar da hankalinki babu abinda zai same mu sai alheri insha Allahu, itama umman mikewa tsaye tayi tace "ta ina zan kwantar da hankalina jiddah ? ai hankali ya bar kwanciya in dai kika fasa wannan maganar ni dama na sani ban fadi miki ba. Tace "Ummah ko baki gaya min ba zanji ke dai ki tamin addu'ar neman kariyar Allah ahine me kowa da komi, tarike hannunta lokacin data yi hanyar fita tace "jiddah kar dai kijefa kanki ckin hadari, takatse ta umma bazaki tambaye ni wanda yakashe dr. khalifa da dalilin kashe shi ba sai rayuwa ta kike neman karewa to bari kiji, "Kariya tana gun Allah ban taba tunanin zan dawo nigeria a wannan lokaci ba haka kawai ina zaune hankali na naji ya tashi, Allah ya dawo dani ne don yatoni asirin wadanda sukayi wannan kisan . Allah ya dawo dani ne don ya kubutar da Fatima kinga kuwa ba ni da dalilin dazai sa in rufe bakina don in kare rayuwata, jin an yi kiran sallar magriba yasa jiddah tafita tana fadin "ina zuwa ummah. Hankalin ummah yatashi sosai zuciyarta tashiga harbawa, kar fa yarinyar nan tajawo mana fitina ya kamata in sanar da babanta halin da ake ciki, wannan maganar me hadari wa zai sa kansa a ciki don wauta ? Tana cikin wannan tunanin babansu jiddah yashigo tare da babban yayansu Alhaji Nazifi, tace "Yawwa Alhaji gara da Allah yaka wo ka jiddah dai ta dawo mana da fitina tana neman jefamu ckin zargi. Yace "me ya faru daga dawowarta ? Ta bayyana masa duk abubuwan dasuka tattauna da jiddah, hankalinsa shima yatashi, Nazifi har ya fi abban na su fusata yace "kin ga yarinya mara hankali ? wa yagaya mata ana irin wannan ? Alhaji yce "Dakata, tanada dalilin fadin hakan, ta gaya miki ? Umma tace "Yo Alhaji ni da hankali na yatashi ina na tsaya tmbayarta wanda take nufi ya yi kisan. Yace "yanzu tana ina ? Tace "ta fita nasan dai ba za tawuce gdansu dr. khalifan ba ko gdansu fatima. Yadubi Nazifi yace "maza nemo mini ita a waya, zo muje masallaci mudawo, Alhaji Nazifi yayi kwafa xuciyarsa cike da haushi nomban jiddah tana dagawa yace "Ke fitinanniya munji maganar dakika zo da ita sai ki zo kiyi mana bayani. Bai jira jin abinda za tace ba yakashe wayar. Suka yi alwala suka nufi masallaci. itama umma alwalar tayi tai sallah zuciyarta cike da fargaba sai a yanzu take son jin hujjar da jiddah ta taka take furta cewa ta san wanda yakashe dr. khalifa. **** A harabar gdansu ummi, jiddah ke tsaya tana neman wata waya kiran yayanta yashigo, don haka tafasa shiga gdan tadawo da baya zuwa gdansu kafin baban na ta sudawo daga masallaci itama tayi ta ta sallar. Kannanta duka suna falon da abokiyar zaman umanta hajiya zainab da suke cewa Anti, Abba da Nazifi suka shigo har gara fuskar Abban tana nunawa zai karbi maganar da fahi ; ta. Nazifi kuwa gallawa jiddah harara yake kamar ya shaketa yahuta, ya tsani ana zaune lafiya a tado da ftina. Jiddah na zaune gaban abbansu ta lankwashe kafafu kanta na kasa tana mai bayanin daya daurewa kowa kai, babu wanda yakatse ta sai da tayi shiru. Nazifi yaja tsaki yace "kai jiddah ni duk da haka inain wannan abubuwan dakika fada bai isa ya zamo hujja akan wannan gagarumin magana ba,. Shari'a fa sabanin hankali ce kuma ita an yi mata lakani da mace mai ciki ba a san abinda za ta haifa ba, sannan hausawa sunce idan baka iya kama barawo ba barawo sai ya kamaka, eh abubuwan da kika fada mana ya isa a dubesu a yi nazari amma ba zai isa gamsashiyar hujjar da za a tunkari kotu da ita ba kai tsaye sai an yi dogon bincike da taka tsan tsan sbda kotu ba gun wasa bane. wannan maganar saita jefamu a wahala. Umma tayi farat tace "yawwa alhaji abinda nake son ka kalla knan mutum yana ckin zaman sa lfya bai dace yadauko ma kansa abinda zai zama fitina gunsa ba, wannan magana ce me sarkakiya. Jiddah tace "ki kwantar da hankalinki insha Allahu Allah zai fitar damu ni dai addu'arku nake nema, ina ji a jikina wani nauyi ne ya hau kaina wanda ya zamo dole in yi magana a cikin wannan lamarin idan nazauna inajin tsoro za ayi kwaba. Gaba daya suka yi shiru kowanne zuciyarsa bata gamsu da abunda jiddah ke niyyar yi ba a son ransu abba ya hana amma ga mamakin su sai ga abban na cewa "Allah ya taimake ki jiddah, Allah ya tsareki. Dama kowa ya san fatima ba ita tayi kisan nan ba fatima ba za takashe khalifa ba. ***** Daga wanna rana rayuwar Jiddah ta kasance a boye babu wanda yasan tana kano sai 'yan gdansu har zuwa ranar da kotu za tazauna don yanke huku ? cin karshe tunda dai wadda ake zargi ta amsawa kotu karara cewa ita tayi kisan. A ranar fatima fuskarta ba tashin hankali sosai idanuwan ta ba hawaye sai dai jawur dasuka yi. Yau kotun ta cika makil, 'uyan'uwan fatiman har wadanda basu taba halartar kotun ba yau sai da suka zo. Ummi na zaune kusa dasu inna kamar yadda tasaba kanta na kasa. Fatima na tsaye kan minbarin amsa kara bayan mai karanto kara ya karanto. Kafin kowa yace komi sai akaji barrister abbas ya tashi ya nemi izinin magana. Alkalin yace "yana da damar yin hakan, yayi godiya sannan yashaidawa kotu cewa yau ya zo da babbar hujjar da zata gamsar da kowa cewa ba fatima ce tayi wannan kisan ba, aka bashi izinin yagabatar da hujjarsa. Wata kofa ce tabude jidda ce tafito, lamarin dayasa kallo yakoma kanta ana shirin ganin abinda zai faru, itama fatiman kallon jidda kawai takeyi cike da mamakin lamarin kamar yadda fuskar kowa a kotun yanuna ckin wadanda suka san jidda, kowa ma knan ballantana babbar aminiyarta ummi. Barrister abbas ya gabatar wa da kotu jidda da kuma rokon kotu tabawa jidda daman gabatar da bayanin datake dauke dashi, ake ce duk za a iya yin hakan. Bayan jiddah ta yi sallama tafara da fadin "Ina gdan da nake zaune birnin london wani yamaci naji wayata na ringi ? g ina dakkowa naga nomban babbar aminiya ta ummi, hakan yasa nadaga dasauri muka gaisa na tambayeta labarin gida da rayuwa. Tace "komi lfya jiddah, sai dai ni ina cikin matsanancin tashin hankli wanda yasa rayuwat ma gaba daya ta fita daga raina. Nace "Subhanallahi me ke damunki kike fadin haka ummi. Tace "eh to jidda a iya saninki dai kin san tun tasowa ta ma'ana lkacin da na mallaki hankalin kaina babu abinda yake barazana da duk wani farin ciki na rayuwata wanda yawuce dr. khalifa ko ? Na amsa mata "eh na sani ummi. Tace "To dr. khalifa shi ne matsala ta ko kin san cewa zancen auransa da fatima ya tabbata. Nace "to kiyi hakuri mana ummi, ni dai na san duk abinda ke faruwa Allah ne yahukunta hakan zai faru sai dai kiyi hakuri domin kuwa lamari na Ubangiji yadda yakaddara haka zai faru, cikar imanin musulmi yadda da kaddara cikin abinda yayiwa mutum dadi ko akasin haka. Ummi taja dogon numfashi tace "Jidda kina nufin in hakura da dr. khalifa ? duk lokacin dana bata ina jiran dawowarsa daga grmany ya tashi a bansa knan. Nace "Bai tashi a banza ba idan har za kiyi aiki da shawarar dazan ba ki, abinda nake so kigane shi ne idan zuciyar mutum tadamu da son wani abu kuma bai samu ba yadan gana ga Allah yayi hakuri, yakaddara cewa Allah ne bai kaddara abin nan da rabonsa bane to Allah zai dubi niyyarsa ya musanya masa abin nan da wanda yafishi, don a lokuta da dama mukan so abunda ba alheri bane garemu, abinda nakeso inkaiki gareshi ummi shi ne ki kaddara dr. khalifa ba rabonki bane a bisa abinda Allah ne yakaddara ba wani ba, domin wani ko wata bai isa ya kwace maka abinda Allah yakaddara rabonka bane, in dai kin yarda da haka to saikiyi hakuri na san abinda ciwo amma in kin daure kin yi hakuri don Allah, zai miki maganin damuwar ki, ance idan so cuta ne hakuri magani ne. Ummi taja dogon numfashi tace "jidda hakika shawararki itace akan hanya anma wannan hanyar binta ba zai yiwu ba idan nabita mutuwa zanyi. Nace 'Haba ummi ya ya za ace wanda yabi hanyar gskiya yamutu. Tace "jiddah ba zan taba iya hakuri da dr. khalifa ba idan kuwa nace zan hakura dashi to mutuwa zanyi. Nace "To ni dai kuma ban san abinda zan ce miki ba ummi ba ni da abinda zance sai dai kiyi &akuri. Tace "Ba zan yi hakur ba jiddah na yarda na rasa dr. khalifa amma yadda na rasa shi sai dai kowacce mace tarasa shi, babu macen da za ta moreshi. Na ce "ummi me kike nufi da fadin haka ? Kai tsaye tace "Kashe shi zanyi. A nan ne jidda tayi shiru. Yayinda jama'ar kotu suka rude da hayaniya ana fadin "Lahaula" wasu na salati, sai da aka tsawatar sannan kowa yai shiru. Mai shari'a ya dubi jiddah yace "kotu ta ji abinda kikace, akwai karin bayani ko shi knan hujjar ta ki ? sannan kuma akwai shaidar da za ki tabbatarwa da kotu cewa kunyi wannan magana da wadda kika kira ummi. Ta gyda kai tace "Ina da kwakwarar hujjah ya mai shari'a. Cikin rudani na tambayi ummi "kashe shi za kiyi ? Tace "Abinda kunnanki yagaya miki shi nake nufi tare da kara tabbatar miki da hakan kar ki dauka da wasa nake...... Na katseta nace "ummi an taba irin wannan maganar da wasa ? Tace "Yawwa gara da baki wahal da kanki gun shakkar abinda nafada ba. Nayi ajiyar zuciya nace "ummi meye dalilin da yasa za ki furta wannan maganar mai tada hankali ? Tayi dariya tace "na gaya miki idan har na rasa khalifa to sai dai kowa yarasa shi har iyayensa da kowa nas. Nace "amma lallai yau ummi na tabbatar ba ki da hankali kuma ba ki da tunani. Tace "in dai akan son dr. khalifa ne ba damuwa duk abinda za ki kirani kinyi dai dai. Idanuwana a makance suke babu abunda zan hango illa abunda nasa gaba zan aiwatar wanda shi nake ganin zai bani mafita, haka kunnuwana a toshe suke ba zan iya sauraron kowani nasiha ko gaskiya ba da ace zan vi hanyar gskiya wannan hanyr da kika nuna mini ba zan kauce mata ba tunda hanya ce ta hakikanin gskiya. Na marairaice murya "ummi bakin ki ne ke furta wannan kalma na ta'addanci ki ji tsoron Allah kidaina fada ni har kin sa tsoro ya kamani. Tabushe da dariya tace "kidaina damuwa jiddah babu wanda nataba fadawa wannan maganar sai ke, kuma na gaya miki ne sbda ke din sirrina ce babu maganar da ba zan iya gaya miki ba duk nauyinta kuwa. Nace "meye amfanin gaya min din tunda na ba k8 shawara kin ki dauka, har da bakinki kince abinda nafada gaskiya ne kiyi wa Allah ummi kiyi hakuri da dr. khalifa kada soyayyarsa tasa ki haukace, don ni na fara zargin kin samu tabin kwakwalwa ne, lfya kalau kike ba za kidinga furta wannan mummunan lafazin ba. Tace "Lafiya ce ta sani furta wa kuwa jidda zan kuma aikata. Na ce "to meye laifin khalifa don bai so ki ba, ana soyayya dole ? ke yanzu za a tursasa ki son wanda ba kya ra'ayinsa ? Tace "Nima bance miki dr. khalifa ya aikata min wani laifi ba, zan kashe shi ne don kowa yarasa shi sbda sun nuna min rashin tausayi shi da iyayansa sun san ina son khalifa amma lokacin daya dawo daga germany ya rikice akan cewa fatima yake so sai suka watsar da komi ba sa kallon kowa sai dansu suka fifita bukatar sa akan ta kowa aka bashi fatima sbda gata ana bukatar farin ckinsa, idan har khalifa zai kasance ckin fari ciki to basu damu da kowa ba da komi ba wannan ne dalilin dayasa zan kashe shi kowa yarasa. Nace "kai lallai ummi kin cika mara hankali, to na ji za ki kashe shi ba kya tsoron kema kar a kashe kin ? kinsan fa hukuncin wanda yai kisa kashe shi akeyi ko bakisan da haka ba. Dariya sosai tayi tace "na sani mana jidda ai ni mutuwa hutu ce gareni da akan rashin khalifa, ke bari in gaya miki wani abu matukar ina cikin duniyar nan ba zan bar khalifa yarayu da wata diya mace ba ne ko zan yi hakuri da auran khalifa ba dai fatima ba don fatima ta ci amanata ta yaudareni na gama gaya mata sirrin zuciyata da niyyar ta taimake ni tasama mini fada a zuciyar khalifa amma ina maimakon tayi min hakan ganin son da khalifa yake mata sai tayi amfani da wannan dama tabi hanyar data mallake zuciyarsa har yadinga nunawa tamkar zai mutu ne idan yarasat., duk fa fatima da khalifa sun san halin danake ciki basu tausaya min ba, jidda ko ke din nan bakisan sirrin zuciyata cikin abinda yashafi khalifa ba yadda fatima tasani, ta san ydda nake kwana ba na barci, ta san yadda nake kwana idona na zubar da hawaye, ta san yadda nake yini ba ci ba sha, duk sbda na rasa khalifa, amma fatima tashare tashiga fafutuka akanta, har sai data mallakeshi, ita kadai yake kallo, itace a gabansa, wannan shine dalilin dayasa nace yadda narasa shi itama tarasa shi. Nace "Don Allah ummi me zan gaya miki ki fuskanci cewa wannan kuskure ne babba za ki tafka ? duk wannan abubuwan da kike fada ba hujja bane wanda za tasa ki raba fati da khalifa ta wata hanyar m bllantana ta wannan mummunar hanyar, don Allah ummi kiyi hakuri. Tace "Jiddah karki bta bakinki da ace, zan iya yin hakuri da tuni na ba wa kaina hakuri. Nace 'na ji ki bi duk hanyar da za ki bi don ganin kin rabasu amma ba wannan ba. Tace "jidda kudimmu dayawa sun salwanta akan in raba fati da khalifa in ja hankalinsa sai yakasance ma kamar soyayyarta ake kara masa, babu wata hanya da za tayi tasirin rabasu sai wannan hanyar da zan bi, dole in bita kiyi hakuri kawai Nace "To naji tawace hanya xa kibi ki kashe shin ? ashe ke yar ta'addace ban bansani ba ? Tabushe da dariya tace "duk lokacin dakika samu labarin an kashe dr. khalifa, ni ummi ni na kashe shi, idan kin dawo kya ji bayanin hanyar da zan bi.... To nan ne takashe wayarta. Tun daga wannan rana ban sake samunta a waya ba, hankalina ya tashi sosai idan nayi yunkurin kiran wani sai in ji a jikina kamar ba da gaske ummi take ba ko kusa ban yarda za ta iya aikata kisan kai ba, to kada yakasance nafada ita kuma ba gaske take ba dana rasa yadda zanyi sai nayi shiru naci gaba da addu'a. Ba a dade dayin haka ba wata rana da safe wani matashi yazo gdan danake zaune a london yace sako ke tafe dashi yana son magana dani, nace "daga ina ? Yace "Daga kano, na zo miki da wani muhimmin abu amma na roki yazamo sirri a gareki. . **** Jiddah zaria,,, to ko wani sirri ne kuma wannan ??? A DAREN FARKO 37 Duk da cewa zuciyata bata kwanta da mutumin ba amma na daure nace ba kmai shigo muka zauna a falo yana duba na yamiko min wani memory card, nace "Na meye. Yace "karbi xan miki bayani. Na jima ina kallonsa sannan nace "kana tunanin zan karbi abinda ba ni da masaniya akan sa. Yayi murmushi yace "don Allah kar ki damu wannan abin ba zai taba zama abin cutarwa gareki ba face yazamo abin amfani na tabbatar ba za ki taba mantawa da zuwana ba yayin da kika fahimci muhimmancin wannan abin a gunki idan bukatar sa ta taso. Nace "to ai ni bansan daga ina kake ba, ban san meye a cikin sa ba ballantana in san dalilin daya sa ka ban shi, ka fada min mana idan kana son in karba. Yace "jidda kiyi hakuri dai ki karba wannan memorin ba wani ya shafa ba illa aminiyarki ummi. Yajefo min kan cinyata yamike tsaye yana cigaba da kallona yace "na daina lallabaki akan ki karba idan kin ga dama ki jefar dashi nidai ai na kawo miki, ina son kisani lokacin da ummi tayi miki wayatace za ta kashe dr. khalifa ina zaune duk wani bu da kuka fada yana ckin wannan memory daga bisani za kiga wasu muhimman abubuwa da xai miki amfani a ciki, in kuma har yanzu baki gamsu ba za ki iya jefar dashi. Yana gama fadar haka ya kama hanya zai fice, na dauki memodin jikina na rawa nabishi ina rokon yadawo yagaya min sunansa kuma yayi min karin bayani don ba karamin rikitani yayi ba. Yace "Babu wani bayani dazan kara miki, jin sunana kuma ba ya da amfani gareki a yanxu tunda dai kikaji nafadi haka kin san wannan memorin yanada amfani gareki, kiyi hattara ki kiyaye kada ki bude shi sai bukatar hakan ta taso. Iya abinda yafada min knan yafice yabarni tsaye da memory card a hannuna jikina na rawa. Jidda tayi shiru. Kowa ma a kotun shiru yayi ana kallonta, masu rubutu na yi masu nazari na yi. fatima na tsaye kyam inda aka tsaida ta ko motsi ba ta yi ba, kallon dakowa yake wa jidda itama shi take mata. Ummi kuwa da kai tsaye ita abin yake shafa tana zaune tadaura kanta bisa cinyarta itama dai bata motsa ba, mutanan da basu sn ita abin yashafa ba basu kalleta ba iyayan marigayi dr. khalifa da iyayan fatima fatima da wadanda suka san itace umin da ake nufi sun dawo da kallonsu kanta, ina zaton shi ne dalilin daya sa ta sunkuyar da kanta bata dago ba, to ama dayake hankalin mutane na kan jidda da mahukunta suna son jin yadda al'amarin ya kaya sai basu motsa da wani abu ba suka fuskanci jiddah don jin yadda za ta kasance cikin wannan al'amari mai ban mamaki, aka ba ma jidda umarnin taci gaba bayyana labarin datake bayyanawa, tadora da fadin. Bayan tfiyar wannan mutumin nazauna shiru ina tunanin al'amarin nayi shawarar in bude wnnan memory a wautata in ga meye a cikinsa, haka kawai sai naji tsoro ya kamani, kamar wadda akayi wa dabaibayi nakasa budewa kuma nakasa bayyanawa kowa al'amarin, nayi masa ajiya mai kyau har zuwa lokacin danaji gabaki daya na kasa samun natsuwa idan nakwanta bacci sai bacci ya gagareni, in kuwa nasamu barcin zan yi ta fama ne da mafarkai masu ban tsoro, dole tasa nabaro london ina ckin karatu na nadawo, a ranar dana dawo din nasamu lbrin an kashe dr. khalifa lamarin daya tayar mini da hankali sosai, nana da nan natuno hirar da mukayi da ummi a waya wanda tun daga wannan rana ban sake samun ummi a waya ba sannan itama bata sake kirana ba, a wannan lokacin ne nadakko wannan menoryn nabude naga abinda ya kunsa. Jidda takara tausasa lafuzanta cike da ladabi tace "ya mai shari'a wannan memorin shi ne shaidata dukka abinda nafada yana ciki. Mai shari'a yabada umarnin akawo na'urorin dazasu haskawa dukkan jama'ar da ke gun abin da ke cikin memorin, nan da nan aka kawo jama'a suka baza idanuwa cike da mamaki, har lokacin ummi bata daga kanta ba kuma babu wanda yayi mata magana. Abinda allon talabijn din yafara nunawa shine ummi ce tsaye a wani guri ita kadai, ta sha ado tayi kyau dayawa ,wani matashi yabullo ta bayanta yace "ummi gani na zo. Ta waiwayo tadubeshi tana murmushi tace "sannu dazuwa yaya. Yayi murmushin shima yace "yauwa ummi ya akai naga fuskar ki ckin damuwa ? Daga gani wani abu yana damun zuciyarki, gaya mim ko meye zan taimake ki in dai zan iya. Tayi murmushi tace "na san za ka taimakeni yaya shi yasa na fiddo maka damuwata, duk da cewa magana ce nazo maka da ita mai tsananin nauyi. Yabushe da dariya yace "kada nauyinta yadameki maganar dakika iya dauka nikuma sai ta gagreni ? Dubeni da kyau fa ummi. Ta jinjina kai. Yaci gaba da fadin "ummi tun lokacin dana ganki zuciyata take bala'in son ki, kina ta shareni kin ki ba ni hadin kai, kin sha walakantani a gaban yarana ina kyaleki, kowa na mamakin yadda naki tsayawa in dauki kwakwaran mataki akan ki, na san ke da kankikin san kina yaudarar kanki ne kina ganin kamar kinfi karfi na ne shiyasa ban dauki mataki akan ki ba, ba haka bane ummi da ace na yi niyyar rabaki da rayuwarki gaba daya da yanzu na gama dake, da ace na yi niyyar dauke ki in boye da yanzu na yi, amma dayake duk ba wannan manufar ce a zuciyata ba na sa miki ido duk dacewa kullum kwanar duniya azabtuwa nake da soyayyarki, Allah ne yasa min sonki a zuciyata ba tare da manufar komi ba face in aure ki, ban taba sha'awar auran diya mace ba sai ke, tun daga ran da na ganki sai naji kawai ina sha'awar ace na gina gda na ajiye matar aure nima ta haifa mini 'ya'ya yadda maza keyi sai gashi ban samu hadin kanki ba. Aka hasko fuskar ummi tayi murmushi tace "ba komi ka kwantar da hankalin ka yaya lokaci ya yi da za kasamu hadin kaina yadda kake bukata. Yace "Za ki aureni ummi ? Ta amsa "zan aureka in dai kai min wani aiki shi ne sharadin aurena da kai. Yace "wani irin aiki ne wanann ummi gaya min shi komi wahalar shi zanyi in dai zai sa ki aureni, aurenki shi ne cikar burin rayuwata a duniya, ba ni da bukatar komi domin na mallaki dukiya, mace sai wadda na zaba in yi amfani da ita, ke kadai ki ka tsaya mina zuciyata ba na son bata miki rai na fi son in aureki in zauna dake a matsayin mata ta, yanayi ne daban taba fuskanta ba a rayuwa ta. Unmi tace "wannan damuwa ta ka ta zo karshe in dai kayi min abinda nakeso zan mallaka ma kaina a matsayin matar aure. Yace "To fada min meye wannan aikin ko zan rasa raina zan miki. Tayi murmushi tace "Akwai wani mutum mai suna Abakar ana cemasa dr. khalifa. Shi nake so kawai ka kashe mini in dai khalifa yabar duniya kazo a daura mana aure. Yavushe da dariya mai karfi yace "shi knan ko da wanda za akashe bayan shi ? Ta Girgiza kai "shi kadai ne ba na son gani a duniya. Yace "an gama yaushe kike son a kashe shi ? Tace "A DARANSU NA FARKO da amaryarsa kuma ina so a kashe shi ne ta sigar da za ayi zaton ita amaryar ta sa ce takashe shi, in dai kayi min haka ka biya dukiyar auran ummi. Yasake bushewa da dariya yace "in dai kisan kaine ko ta wacce hanya mun iya ta sai dai in bamu sa kammu ba. To daga wannan shafin sai aka hasko dakin da aka kai fatima, fuskar ummi ce ta bayyana yaya na binta a baya tabude mai murfin kwaba yashiga. Sai kuma aka hasko ummi t shiga daya murfin kwabar ta rufe. A wani shafin kuma an hasko fuskar dr. khalifa ne ya bude kofar kwaban da yaya ke ciki, sai ga yayan ya fito tsulum ya tsaya gaban dr. khalifa cikin zafin nama yadamke masa baki ya hantsila shi kan gado yasa filo yadanne bakinsa. Sai aka hasko fuskar ummi ta fito ta maida murfin kwaba ta rufe ta hau kan gadon da karamar wuka a hannunta ta nunawa dr. khalifa daf da kunnansa takai bakinta tace "Ni ce ajalin ka. An hasko fuskar khalifa yanata wutsil wutsil bashi da damar magana. Sai kuma aka hasko yaya ya amshi wukar hannun ummi ya chakawa dr. khalifa sau biyu, sai suka fice daga dakin suka rufe kofar shi da ummi. Bayan wannan, Sai akaga fuskar yaya a zaune kan kujera unmi na gefensa yace "Aiki dai ya kammala kuma ya yi kyau ummi ya batun aurammu ? Ummi ta harareshi tace "wai kai meyasa ba ka da hankali. Yaya yazaro ido "Ni ne ba ni da hankali ummi ? Tace "To ina kaga hankali. Yayi murmushi yace "Ni kuwa nake da hankali. Ta girgiza kai tace "babu rashin hankalin daya wuce kace kai dinnan kanada hankali kai daman ka yarda zan aureka ? Ya kura mata ido yace "ummi ni kikawa haka ? kin san waye ni kuwa ? ki guje shiga cikin hadari. Tamike tsaye tace "shi yasa nace ba ka da hankali kamar ni in rasa wa zan aura sai dan ta'adda, ko ka manta kai dan ta'adda ne, ka gaggauta fiddani daga zuciyarka domin bazaka taba samuna ba. Yayan yamike tsaye yanuna ta da yatsa yace "kin yi babban kuskure ummi sai kinyi da na sani da kika mini domin baki yaudareni ba illa kanki. Ta kyalkyale da dariya tace "yaya ba zan yi da na sani ba har abada domin ka mini aikina dr. khalifa dai ya mutu kuma ba zai dawo ba buri na knan yadda na rasa shi kowa ma yarasa ka ga zancan nadama ma gareni bai taso ba, in kuma za ka kashe shi ne to bismilla. Yace "Ba zan kashe ki ba sbda na yi alkawarin ba zan kashe ki ba ummi amma xan ba ki mamaki daman jikina ya ba ni za ki yi min wannan butulcin shi yasa na shiryawa hakan, kin z hannu ummi. Daga wannan ranar ba za ki kara yaudarar wani a duniya ba, idan ma kin ci gaba da rayuwa ni daman nawa ta kare. Iya abinda memorin ya kunsa knan TV tayi dif kamar yadda kotun tayi shiru kamar ba kowa duk da yadda tacika makil da mutane, abin mamaki har yanzu kan ummi na kasa bata dago ba. Bayan wani dan lokaci mai shari'a yadago kansa bayan ya ajiye biron da yake rubutu yace. "Kotu ta gamsu da bayanan da jidda tazo dashi tare da hujjojin dakowa yagani a zahiri, don haka ba tareda bata lokaci ba nan take wannan kotu ta sallami fatima kuma ta bada umarnin a kawo ummi da wanda yakashe khalifa, shari'a ta dawo kansu wannan yakawo karshen zargin da akewa fatima na kisan mjinta Dr. Abubakar Saddiku a bisa kwararan hujjoji na shari'a. A DAREN FARKO 38 Karfe takwas na dare agogo ya nuna, malam musa mahaifin su fatima na zaune kan tabarma da rediyo gefensa yana jin shirin iya ruwa fidda kai da akeyi gdan rediyon kano. Inna tafito daga dakinta tazauna dab da shi tce "malam ni fa lamarin nan na fatima ya dameni. Yarage sautin rediyon idanunsa na kanta yana mata kallon rashin fahimta yace "me kuma yafru ? Tace "ka ga yau satin ta biyu da fitowa daga kurkukun nan amma har yanzu ta ki daina kuka idan an tmbayeta sai tace wai babu komi, ni abin nata har ya fara ba ni tsoro. Malam yace "kira min ita. Ta kwalawa fatima kira tafito a sanyaye ta tsuguna a gefe yace "Haba fatima wannan kukan da kike yana nuna cewa tamkar ba ki ki yarda da kaddara bane shi duk abinda Allah ya hukuntawa bawansa va makawa sai ya faru, godiya ya kamata muyi wa Allah daya takaita mana al'amarin ya tsaya a haka, addu'ar da muke yi ce tayi tasiri da karshen al'amarin yazo, ko meye na tsananta damuwa, tunda kika fito daga kurkuku kike kuka kin ki cin abinci isashe, kin ki magana kin daina barci isashe to yaya kike son mi miki ? Fatima tayi ta yi tahadiyi kukan dake makale a idanunta ta kasa ta dora kanta a guiwarta hawaye suka dinga ambaliya a fuskarta, tace "kuyi hakuri baba wallahi ina jin ciwon damuwarku sakamakon damuwar da nake ciki wadda tayi sanadin damuwarku ban san yadda zanyi indaina kuka ba tabbas da na daina amma ba yadda zanyi nima ban san lokacin da nake kukan ba, zuciyata ce ba za ta iya jurewa abubuwan dasuka faru ba, ina cikin bakin ciki da damuwar abinda ummi tayi min nakasa sabawa da damuwar rashin khalifa, ummi bata yi min adalci ba da tasa aka kashe khalifa na san tana sonsa amma ita tanuna min ta hakura dashi ta gaya min cewa idan bai aureta ba kashe zhi za tayi da..... Malam ya katseta yace "Fatima khalifa ya rsu kuma ba zai taba dawowa ba har abada, tunda aka halicci duniya bbu wanda yataba dawowa bayan ya mutu haka khalifa ma ba zai dawoba, kin g kuwa idan hakane babu amfanin aci gaba da tattaunawa da maganar, zai fi kyau miyi hakuri, wannan al'amarin daya faru mu barshi a matsayin kaddara, Dr. khalifa babu abunda za muyi masa illa addu'a, Allah yaji kansa yakai rahama kabarin sa, kuka da zaman damuwa ba zai sa yadawo ba kuma ba zai goge abin da ummi tayi ba, da ace zai goge ko yadawo mana da khalifa da sai ai tayi, kiyi hakuri Allah yabaki wani mijin. ***** Tun a lokacin da kotu tagama yanke hukunci ummi tafadi bata kara sanin inda kanta yake ba, a bisa dole aka kaita asibiti tun tana numfashi har ya kaance ba ta iya numfashi da kanta sai da taimakon oxygen. Kowa sai Allah wadai abinda ta aikata akeyi tare da mamai mai tsanani, abinda yafi zama abin mamaki shi ne yadda ummi ta tayar da hankalin ta bayan mutuwar khalifa, ta fi kowa nuna damuwarta akan mutuwar ta sa, tunda aka binne dr. khalifa ummi take kuka ta rasa sukuni, kullum ckin zirga zirgar masu taimakon ta don fidda fatima daga zargi tare da binciko wanda yayi wa khalifa kisan gilla, abin mamaki wai itace ummul haba isin kisan, wannan shi ne a na zatom wuta a makera sai ga ta a msaka. Hakika fatima ta ba ma kowa mamaki ta bar ma mutane abin tattaunawa kowa na fadin albarkacin bakinsa ciki dai har da iyayan ita kanta ummin ballantana wadanda suka haifi khalifa, mama ita ke tare da ummi kullum tun kashe dr. khalifa har yau ita tafi kowa sanin damuwar da ummi ke ciki da irin kukan da takeyi a lokuta da dama ita maman ce ke lallashin ummi amma ckin wani irin yanayi ya bayyana cewa ummi ce ta kashe wanda take kokawa mutuwarsa kukan da batayi ba a lokacin da mahaifin ta yarasu, abin tambayar anan shi ne shin me yasa ummi take kukan mutuwar khalifa ? bayan ita takashe shi, sbda bata son rayuwarsa a doron kasa a bisa gurguwar hujja wai don ta rasa shi kowa ma sai dai yarasa idan akace don ta yaudari mutane take wannan kuka tana zargin daman asirin ta zai tonu ne, kokuma ta yi abin ne don ya dameta, shiyasa take kokawa kanta don ta san ta yi babban kuskure da ganganci a rayuwarta. To koma dai meye Allah kadai yasan dalilin kukan ummi bayan kisan datasa aka yiwa dr. khalifa da kanta. Ga ta nan dai a bisa gadon asibiti batasan inda kanta yake ba, karkashin kulawan jami'an tsaro, likitoci sun bada sakamakon binciken dasukayi akan ummi cewa damuwa tasa tashiga wannan halin, akwai yiwuwar tadawo normal akwai yiwuwar tarasa ranta, sbda tsananin damuwar datake ciki yayi yawa. Mahaifiyarta hajiya hauwa ce me jinyarta, hankalinta a tashe sosai yake sbda yadda ake yayata labarin a kafafen yada labarai na jihar har da makota, tayi kuka ta yi kuka har ta ba uku lada, ba a barin kowa ganin ummi sai dai tasa ummin a gaba tana kuka, tunda aka kawo ummi bata taba farkawa ba, numfashinta yahau ya sauka sai dai wani lokacin tana motsawa kamar za ta farka sai kuma tacigaba da barcin da in barda ana ganin numfashinta sai kace ta mutu ,kunyar mutane yasa hajiya hauwa ba ta iya fita ko ina batasan yadda za ayi ta iya hada ido da iyayan khalifa ba, dansu kwaya daya ummi ta yi sanadiyar barinsa duniya sbda wani hujjarta mara tushe ballantana makama. Tuni dai yan sanda sun sami nasarar chafke matashin nan me suna yaya wanda ya tabbatar shi yakashe dr. khalifa da hannunsa a bisa umarnin ummi, bai wahalar da shari'a ba ya amsa laifin sa har yayi magana da yan jaridu cewa ai dama kawo kansa hukuma ne kawai bai yi ba amma zaman jiran kamu yake tunda shi da kansa ya bayyanawa duniya ta yadda al'amarin yakasance kuma yabari aka ga fuskarsa to ai ya yi talla da laifinsa knan. A gdansu khalifa abin ya zamo tamkar na jajantawa yadda jama'a suka dinga ta zuwa bayan 'yan jaridu dake zuwa neman labari, Abba na iya magana da 'yan jarida ita kam mama wannan al'amari ya dawo mata da mutuwar khalifa sabo fil a zuciyarta, tayi kuka ta yi kuka kukan da bata taba irinsa ba a rayuwarta, jama'a na bata hakuri tana fadin, "ku kyaleni in yi kuka abin kukan ne ya sa mun, ummi ta cuci kanta me yasa ta hau dokin zuciya. Wasa wasa lamarin mama tadaina barci tsabar takaici ne fal a zuciyarta, dan na su kwara daya shi ne don masifa sai da aka salwantar. Wannan daran ma zama tayi daram a dakin abba tazuba tagumi tana kallonsa yana barci ita kuwa ta kasa tayi juyi ta yi juyin shiru, ta gaji ta tashi tazauna hawaye wani na bin wani, tadunga tuno yadda al'amrin yakasance bayanmutuwar khalifa. A DAREN FARKO 39 UMMI takan zauna tana kuka kamar ranta zai fita, watarana mama ta isketa a zau? e a harabar gdan tana sana'ar ta ta, mama tace "ummi ya ya kika fito nan kina kuka? kowa yana kallonki duk kukan na ki ya wuce ckin gida sai kinzo waje. Ummi tace "mama wai ba ni da dalilin kuka ne? duk wanda yashigo gdan nan abin mamaki ne don ya ganni ina kuka? Wallahi mama tun daga ranar da aka sa khalifa a kabari har yau har nima in mutu ba zan daina kuka ba. Mama tace "haba ummi a matsayimmu na musulmi dole mu dogara ga Allah a bisa kaddarar da Allah yadora mana, ni ce fa na haifi khalifa wa ya fini sanin ciwon sa? a cikina ya rayu nayi nakudarsa na raine shi, bbu wanda zai nuna min son khalifa tunda na hakura na karbi kaddara ya dace kema kiyi hakuri. Ummi tadago jajayen idanunta tadubi mama tace "na san da haka mama amma kin san wani abu daya, kuna kukan rashin khalifa ne don ku kuka haife shi nikuwa kukan danake daban ne da zan iya bayyana miki wani gagarumin sirrin dake zuciyata da daga yau na san ba za ki kara cewa indaina kuka ba mama. A wan? lokacin da ummi ta fadwa mama wannan magana babu abunda tasa a ranta face sirrin da ummi ke nufi bai wuce na soyayyar da take wa khalifa ba. Abba dake ta barci yamike zaune kamar an tashe shi ya zubawa mama ido yace "maijidda wanan tunanin zai ci gaba da hanaki barci a kowane dare idan har ba za kiyi hakuri ba. Mama tafashe da kuka tace "Alhaji ta yaya tunani da damuwa za su fita daga xuciyata, wane irin bakin ciki ne wannan? Yace "kiyi hakuri Allah ne yakaddara kwanan khalifa ya kare shiyasa suka samu nasarar kashe shi, kuma da sukayi hakan meye meye ribar da suka samu banda faduwa, tunda aka kai khalifa kabari ummi bata sake samun natsuwa ba babu abunda yaja mata hakan face hakki, haka shima wanda tasa yayi kisan hakki ne yasa ya tonawa kansa asiri da kansa. To kinga lah za muyi wa godiya muyiwa khalifa addu'a . ***** Jiddah ce tadaga labulen dakin inna tare da sallama, inna ta fadada fara'arta tace "maijidda ke ce tafe da yamman nan, daga ina? zauna ga kujera nan. Bayan sun gaisa tace ina fati;a? Inna tace "Tana daki shiga. Ganin fati a kwance yasa tabata rai tace "wai don Allah fatima sai yaushe za ki kwantar da hankalin ki ki dinga walwala? dubi yadda kika rame kika yi duhu kullum idanuwan ki ckin zubar hawaye har sun zama jajaye fati me yai zafi haka? Fatima tamike zaune tace "jiddah duk wadannan abubuwan dakuke ganin laifina da rashin dauriya na kune baku san ina dauriya akan su ba, jiddah tun da nake rayuwa a duniya ban taba kwatanta so ba sai akan khalifa, ko da cewa a baya na yi niyyar auran musbahu na ami? ce ne sbda da darajar iyayena amma ko sau daya ban taba jin digon soyayyarsa a zuciyata ba, ni kadai nasan asarar dana tafka wadda ba za ta taba mayar da ko da kwatankwacin mijina ba ballantana fa daidai dashi . Jidda tadafa mata kafada tace "kiyi hakuri yadda Allah yabaki khalifa ya amsa abinsa haka zai musanya miki da wanda zuciyarki za taso, lamarin na ubangiji ne babu abunda zai fi karfinsa in dai bawa zai dogara dashi to ya isar masa. Fati tace "jidda har ban san kalaman da zan yi amfani dasu gun gode miki ba, kin yi namijin kokari a gareni Allah yayi miki sakayya da mafificin alherin sa na duniya da lahira. Jidda tace "fatima godiyar nan ta isa na gamsu Allah shi ne abin godiya daya nufeni da in yi hakan da bai ba ni iko ba ban isa in yi ba, yanzu wata alfarma nake son ki yi min. Fati tace "ki fada jidda ko mene zan miki in dai xan iya, kin fi karfin komi a gareni. Jidda tace "sanin hakan danayi shiyasa nazo, a safiyar yau din nan ne mahaifiyar ummi taxo tana rokona in taimaka in zo in roke ki ki je asibitin da ummi ke kwance ki dubata domin ta farfado amma tana ta kuka tana rokon a kawo mata ke da iyayan dr. khalifa za ta fada maku wata maganar, dafarko nace da hajiya babu ruwana sai nagata kama kuka tana rokon in taimaketa tace wllhi jidda nima ba laifina bane ba ni da masaniya ko ta kusa ko nesa game da abinda ummi ta aikata,. Fatima ta jinjina lamarin sosai a ranta, yanzu kam a duniya ba ta da makiyin daya wuce unmi, ji tayi kamar za ta hadiyi zuciya ta mutu sbda bakin ciki me za tayi da wadda tarabata da masoyinta, kai hakika ummi ta gama cutar ta har me za ta gaya mata. Babu yadda ta iya da jidda tana ganin kimarta da yawa don haka ya amsa mata cewa za ta, ta sanar dainna da malam suka mata izinin zuwa, dogon hijjabinta me hannu da nikab tasa ravon ta da fitowa waje tun ranar da aka sallamo ta daga kurkuku, hawaye suka dinga zuba daga idonta har suka iso asibitin., a lokacin taga mama suma suka iso su biyu jidda takira hajiyar ummi a waya tace dasu sun zo tafito tashiga dasu dakin da ummin take. Duk yadda zuciyarsu ke cike da tsanar ummi da bakin ciki sai da jikinsu yai sanyi, sakamakon yadda suka ga ummi ta yi wata muguwar rama kamar an sauya ta, ta yi baki ta fita daga hayyacinta, babu wanda yazauna sun kame ne suna kallonta. Ummi ckin rawar murya hawaye wasu na bin wasu tace "Abba, mama, fatima na gode kwarai da kuka danni zuciyarku kuka zo nan, na bukaci zuwanku ne don kuga halin danake ciki kafin Allah yakarbi rayuwata, domin ni tawa ta kare ba zan kai labari ba ba kuma so nake ku tausaya min ba don ni ba abin tausayi bace, kuyi hakuri masu karatu a littafin babu page 47-51 Kwanan ummi goma sha shida a gadon asibiti karkashin kulawar lokitoci da jami'an tsaro tarasu, bayan aman jini ta hanci da baki data yini tanayi saita dinga sai tadinga zabura tana gwara kanta da bango tana ihu, "Na cuci kaina, shi ne kadai abi? da bakinta yake furtawa har tadaina numfashi, lokacin da labarin mutuwarta yazo kunnan fatima ta yi kuka har sai da zazzabi da ciwon kai suka rufeta.. ***** Wai shin masu karatu kutambayeni ina musbahu yashiga mana? ku biyoni kuji. Lokacin da musbahu ya tabbatar ya rasa fatima sai ya kaddara a ransa cewa dama ba matarsa bace, . Musbahu gdan kawun sa malam habibu yafara zuwa ya sanar dashi abinda yafaru, kawun ya ji b dadi a ransa amma ba yadda za ayi in dai mutum mai hankali ne da adalci babu yadda za ayi yayi wani zargi akan malam da inna don sun rike musbahu tsakani da Allah, Allah ne bai kaddara fati rabonsa bace. Musbahu ya shaidawa malam cewa zai tafi garin bauchi gun yayar mahaifiyarsa ne sbda yana so yayi nisa da kano a dalilin ba ya so yaga daurin auren fatima. Karfe biyar da rabi na yamma yashiga gdan goggo mairo dake ckin garin bauchi tayi mamakin ganinsa tace "ango na amarya kaine tafe? Yace "Gwoggo ina wuni mun sameku lfya. Tace "lfya kalau yashi kaje dakin au sagiru yana nan yana barci kayi wanka kayi sallan xan aiko ma da abinci idan kaci sai kazo mu gaisa sosai. Sagiru kusan sa'an musbahu ne shi ne dan goggo na biyar ya biyo mata biyu maza biyu,. Tun a ranar yafara devewa musbahu kewar damuwar dayake fama da ita, sbda mutum ne me ban dariya, da alheri ga son mutane. Musbahu ya bayyana masa abin da yarabo shi da kano, sun tausaya mai sosai ganin damuwar dayake cki yasa nan take goggo tace ga diyarta nan hafsa in dai yana son ta ta ba shi, musbahu yayi dan jim bai ce komi ba, goggo tace "ko bata yi maka bane in dai ba ka son ta babu dole. Yace "ba haka bane goggo ina tunanin yadda malam yace ya bani fatima tace ta amince sai da na saki jiki da ita nabata amanar soyayya ta sannan tace ba ta so na, dr khalifa take so shi ne ra'ayinta nikuma ra'ayin iyayanta, nayi mata uzuri cewa ba ita ta zabeni ba niyyar biyayya ga iyaye tayi . Gwoggo mairo tayi murmushi irin nasu na manya tace "musbahu duk wannan abinda yafaru kaddara ne Allah ya hukunta cewa ba matarka bace, idan xa ka lura duka kwana nawa yarafe a daura maku aure khalifan ya bayyana, da ace matarka ce ba zai bayyana ba ko ya bayyana kuma ba zaiyi tasiri a zuciyarta takalle shi da sunan so ba. Ba wai ina gaya ma hakan ne don kaso hafsa ba, in kana raayin hafsa ga ta nan in ba ka ra'ayi kayi zamanka har Allah ya baka wadda kake so. Musbahu yakara dukar da kai yace "wallahi goggo hafsa tafi karfin namiji yaki ta, in ta amince dani ma ta yi min alfarma domin ta girmi ajina. Goggo tace "karka sake fadar haka kaje gareta ku daidaita kanku, Allah yatabbatar mana da alheri. A cikin sati biyu musbahu da hafsa suka fahimci juna, yasameta yarinya mai sauki da son mutane kamar mahaifiyarta, ga ladabi da biyayya, kowa ya yi farin ckin wannan al'amari a dangin su, nan da nan aka tsaida magana babansu hafsa yace zai ba musbahu aron gda su zauna kafin su koma kano, ba wani kudi musbahu yakashe ba illa iya abinda yayo sai da goggo tai masa fada cewa daya suke dashi da hafsa a gdan nan. Bayan wata guda aka daura aure sukayi biki sosai suka kashe kudi, musbahu har mamakin gatan da suka nuna masa yake, aka gama biki lfya aka kai amarya dakinta, a ranar da zai shiga dakin ne yadinga tunanin abubuwan daya tanada zaiwa fatima a ranar da aka kai masa ita, ashe ba matarsa bace yanzu haka tana chan da angonta ta ma manta dashi shikuwa yana fama da ita a zuciyarsa. Sai da yadinga addu"a Allah yataimake shi yarabashi da tunanin fatima kada ya cutar da hafsa sbda ya lura hafsat ta yi dammarar zaman aure dagaske tare da biyayya, ckin ikon Allah yataimake shi yasamu natsuwa a zuciyarsa yamaida hankali sosai gun kyautatawa matarsa sukayi zamansu lfya kowa yana sha'awar auran na su. A DAREN FARKO 40 Kusan watanni shida knan da rasuwan dr. khalifa an dan samu cgaba a rayuwar fatima sbda ta fara rage damuwa har ta shiga wataislamiyya nakusa dasu da akeyi alhamis da juma'a, ta kuma fara tunanin komawa makaranta a halin yanzu ba ta da aminiyar da ta wuce jidda koda yaushe suna tare itama jiddan bata koma london din ba ta dawo da karatu? ta BUK tana karanta mass comm. kasancewarsu tare da jidda ya taumaka kwarai gun debewa fatima kewa sai dai har yanzu idan tatuno dr. khalifa takan yi kuka mai tsanani sbda soyayyar da take masa tayi mata yawa a zuci, shi yasa yau da jidda tazo mata da wata magana sai da taji kanta yana mata tsawa. Ta zubawa jidda iso kawai tana nazarin fuskarta bata katseta ba sai da taji tayi shiru sannan tamike zaune tace "jidda maimaita abinda kika gaya min yanzu. Jidda tabata rai tace "kina nufin baki ji abinda na gaya miki ba? "Na ji ina so in kara ji ne. Jidda tace "cewa nayi yayana usman ya aikoni in mika mai kokon bararsa gareki da fatan za ki amsa mai bukatarsa. Fatima tayi ajiyar zuciya tace "ni kam jidda na yi mamaki danaji wannan maganar a bakin ki, na yi zaton ko yaushe ke nake gaya wa cewa babu wani namijin da zan iya sawa a zuciyata in haka ne kuwa bai dace ki zo min da batun wani namiji ba. Jiddah tace "Fatima kin san dai ba zai yiwu ki zauna babu aure ba don dr. khalifa ya rasu dole sai dai kiyi hakuri ki amshi kaddarar da Allah ya hukunta miki yarda da kaddara shi ne cikar imanin musulmi mumini. Ko kusa fatima ba ta jin dadin hirar don haka tace "To na ji ba ni lokaci zanyi tunani. Ganin yadda fuskar jidda ta nuna rashin jin dadin maganar tasa tace "kiyi hakuri jidda ba cewa nayi ba na son dan'uwanki ba wlh zuciyata ce ke cikin matsanancin hali har yanzu karfin hali nake ni nasan abinda nake ji game da ciwon kisan da akayi wa khllifa, ,na kasa sabawa da wannan damuwar, duk namijin danace xan aura a yanxu na cutar dashi domin ba zan ba shi kulawar data dace in bashi ba, wannan shi ne dalilin dayasa na fidda batun aure a zuciya ta, zan yi zamana haka har lokacin da Allah zai karvi rayuwata nima. **** To a bisa wannan ra'ayin fatima take tafiya da gaske ba ta son wani namijin yasake shiga rayuwarta, ba ta son sake soyayya dakowa sbda wahalar datake sha, amma ina yadda kasan kofa aka bude ma maza nasu sota, wasu su kan biyo tagun malam ganin bbu fuska ta fuskar fatima, wasu ma ta gun tsohon surukinta Alhaji muhammadu mahaifin dr. khalifa kasancewar zumuncin su ya dada karfi, Abban yana da tacewa a cikin rayuwar fatima, ya maida ita kamar diyar sa dan ma dai ba t son zuwa gdan ne a dalilin yawan kukan da take,. Bayan dawowar ta daga islamiyya yau ta idar da sallar azahar inna ta shaida mata cewa mama ta aiko nemanta, nan da nan rant yabci, to kawai tace tamike tayi wanka tasa wata doguwar riga ta shadda tasa dogon hijjabi fuskarta ba fara'a tashiga gdan su mama ta tsaya a harabar gdan tana kallon dakin dr. khalifa, har yanzu bbu abunda aka taba a ciki? sa har motocin sa suna nan cikin tamfal ta jima tsaye a vun daga bisani tagoge hawayen daya gangaro mata tawuce cki tasamu mama a cikin dakinta tana kwance bisa gado da carbi a hannunta tana ja. Ganin fatima yasa tamike cke da fara'a tace "sannu da zuwa diyata. A sanyaye tazaun a kasa ta gayar da ita, mama ta zuba mat ido tace "fatima kullum kara ramewa kke kina duhu kullum b ki da kuzari da walwala wai shin haka raywa zata tfi, tunda fa ba mu muka halicci kammu ba ba mu da iko kuwa da kammu dole ne muyi hakuri da abinda Allah ya jarrabe mu. Tadinga sharar kwalla tana fadin "wallahi mama ban san yadda zanyi in daina damuwa b, damuwa ta min yawa ji nake kamar nim mutuwa zanyi. Mama tace "mutuwa lokaci gareta fatima idan kwana yakare kowa zai mutu, kidaure kidin ga sakin ranki kina walwala kuma ya zama wajibi a cikin masu sonki ki fidda guda daya ki aura, samun abokin rayuwa zai rae miki damuwa. Tadago tdubi mama tace "aure fa kikace mama, har da ke a masu cewa in yi aure kema ba ky kishin khalifa? Mama tayi murmushin karfin hali tace "Allah sarki fatima to idan nayi kishin khalifa ya zanyi, zan iya dawo dashi duniya? Ta girgiza kai. Mama taci gaba da fadin "A daran jiya Barrister Nuraddeen ya zo gdan nan gun alhaji yana son ya tambayar masa malamko zai ashi auranki, abba yace in tambayar masa ke in kin amince ba ya da matsala da barriater nura sbda ya san iyayansa, da rayuwarsa gaba daya ba bukatr sai anyi wani vincike a kansa. Kanta yakara mata nauyi zuciyarta takara kuntata tarasa abinda za tacewa mama da abba sunfi karfin komi a gareta, ga jidda na naci akan yayanta usman itama jiddah ta fi karfin ta wofantar da maganarta sbda sadaukar daranta da tayi don ganin ta ceci rayuwarta. Mama tace "kina da damar da zkije kiyi tunani, idan har mce takasance mai hankali to kada tabi ta kyale kyalen duniya gun zabar miji tazabi nagari kawai, ko dayake zabi yana gun Allah idan mutum ya dogara da Allah sai ya zaba masa miji na gari wanda zai rike shi tsakani da Allah. ***** Fatima tadawo gda cke da tunani a ranta abi? da ta lura dashi shi ne zabar mijin aure ya zamo dole in ba haka ba ba za a kyaleta ba, kuma abin takaici suna bullowa ne ta hanyar dasuke da kima a gunta. Ta bayyanawa innarta yadda sukayi da mama dakuma maganar usman yayan jidda. Inna tace "fatima matukar kina son kwanciyar hankalin mu to ya zama wajibi ki fidda miji ki aure mu ma mun gaji da surutun da akeyimana a dangi da mutanan unguwa. Fatima tamike tashige daki takira jidda a waya bayan sun gaisa tace "ki turo min Usman in gan shi. Jidda tace "sai yau kikaga damar bshi izini yazo. Haushi yasa fati kshe wayarta tana tsaki. Bayan sallar isha'i jiddah takirata tace Usman yna bisa hanya,. wanka tayi ta murza mai tashiga atamfa super ta tsaya tana kallon kanta wai yau itace za tayi zance. wayarta ta kama ringn tadaga a sanyaye tayi mai sallama, Allah yasa da fatima nake magana, Abinda yce mata knan. Ta amsa "Ni ce. Yace "to nima ni ne usman ina jiranki a kofar gda tunda yau an min izinin zuwa..Tsaye ta iske shi jikin motarsa yana danna handst, gabanta yafadi hasken fitila ya haske mata shi tun daga sama har kasa, kananan kaya ne a jikinsa, za suyi tsawo daya da dr. khalifa, sajensa ya kayatar da fuskarsa in barda haka ba za a kirashi maikyaun fuska ba. Ya amsa sullamar da tayi masa ckin fara'a yace "Gimbiya fatima kn wahalar dani da yawa, da kin san yadda nake fama da tunaninki a zuciyata da kin tausaya min baki min wannan jan ran ba. Itadai batsan abinda za tace masa ba tayi shiru kanta a kasa, yaci gaba "fatima ina fama da matsananciyar soyayyarki a zuciyata don Allah ki ba ni hadin kai ina bukatar ki ckin rayuwata, ina da damuwa mai yawa. Tayi wal da ido a lokacin ne suka hada iso tace "ban fahimci abinda kake nufi ba. Ya gyara tsayuwarsa yace "fatima na san kinsan uwa daya uba daya mu*e da jidda,na yi aurena shekaru biyu da suka wuce a nan kano matsalar da na samu itace matata farida batasan me ake kira aure ba, ina nufin duk wasu hakkokin miji da suka rataya wuyan mace farida bata san su ba ko kuma ta sansu ba za ta sauke bane sbda dalilin da ita tasani... AYYAH KUYI HAKURI RUBUTUN SUNYI DAMEJI BA NA IYA GANI... Abinda ke faruwa a gdan usman ba ya yiwa kowa dadi a danginsu sbda fitinar matarsa tayi yawa, ko dayake tun kfin auran an sha gaya msa gdan dayake neman aure ba gdan tarbiyya bane, mahaifiyar su farida sai abin da tace da babansu yake yi, kuma a haka ta trbiyyantar da diyanta mata, usman yawatsar sbda soyayya dayasa ransa . Hjiyr su farida tan da tsananin son abun duniya, son da farida ke ma usman ne yasa ta amince za ta ba shi , yayin da dabi'un gdan ke damun iyayan usman, babansa ya ce ba zaiyi aure ba sai ya samu aiki ,bayan ya samu aikin akayi bikin inda babansu yabashi gdan dasuke cki a zoo road. Da farkon auran an mori soyayya, a cikin wata na uku kachal da auran usman yafara fuskantr matsala da farida dayawa tatatara mai kawayenbanza a gda, ko da yaushe gdansa cike da "yammata wani lokacin har da zawarawa da matn aure irinta wadanda suka fi karfin mazajen su, sai yawon gdajen kawaye, abin takaici wasu yammatan har da samarinsu ke zuwa daukarsu a taya su hira a shiga har falonsa, girke girken abinci, abin takaici ba zai zo yasamu gdan sa ba baki ba sai dai yashige daki yazauna. Yayi kokarin yim hakuri ya kasa yashiga nunawa farida rashin dacewar abinda take, ranar da ya fara mata maganar fiddo da ido tayi tace "ina ruwanka dasu man? kadubi fa yadda suke girmama ka amma kace su daina zuwa, ni kadai zan dinga zama a gdannan ga unguwa shiru,ni ban saba zaman kadaici ba a gdan mu sai dai kayi hakuri. Daga nan tashiga yin allurar hana daukar ciki ba da sanin sa ba, tadaina zama a gdan tadaina mishi abinci sai randa taga daama, ya yi ya yi ya saita ta ta ki, shi dalilin daysa yafara tunanin aure don yasamu sauki tawani bangran, lokacin daya furt a gdansu kowa yai murna sbda tausaya masa da halin dayke cki, sai dai abin fargabr wace mace zai aura su zauna lfya da farida a yadda ba ta da kunyar nan ta raina kowa. Shima din bai san wa zai aura ba ya maida hankalinsa ga addu'a, kwatsam ydor idonsa akan fatima lokaci guda yaji wani salon soyayar da bai taba jin ta ba., a gdansu ya ganta wataran t zo gun jidda, byan tfyarta ykira jidda yasha kunu yana tmbyrt shin fatima ta tsaida mijin aure ne, tayi dan jim tace "yaya sonta kake? Yace "son ta nake ko ba za ta amince min ba. Tace"ko ban sani ba amma dai ina fargabar hakan zan sanar da ita. Fatima tashiga zuciyar usman kwarai dagaske yashiga addu'ar Allah ya mallaka mai zuciyarta don yna hangen maslaha a tare da aurenta, Allah yataimakeshi aikin dayake fafutukar nema Abuja yasamu a wannan satin, fatan sa idan fati ta amince yatafi da ita su zauna. chan yabar farida takarata a kano. Yabar fatima a gdansu zuciyarta ba wani kwantawa yayi da auran usman ba, ta kwanta tana tunanin yaya za tayi knan. washegari da yamma barrister nuraddin kuma yazo da tasa bukatar datafi na usman zafi, lamarin dayasa taji kamar tayi ta kuka sbda damuwa. Yace "fatima ina fatan sakona ya zo gareki, Allah ya jarrabi zuciata da tsananin soyayyarki da bukata mai zafi a kan auranki ina fatan zan samu hadin kanki. Kwarjinin barrister yahanata hada ido dashi hasalima batasan abinda za tace masa. Tadai cije tadaure tace Allah ya tabbatar mana da alheri. Ya dan ji sanyi a ransa yayi murmushi yace "knan kin ami? ce da soyayyata fatima? Taji dam a zuciyarta ita dai ba za ta iya cewa a'a ba idah kuma tace eh ta yi karya. Bata sake cewa komi ba yawuce gaba tayi mai rakiya yace "fatima ban san abinda kika fi so ba ballantana in kawo miki ga wadannan kudin kisayi duk abinda ranki ke so. Tadubi sabbin kudin a razane tace "ina zan kai wannan kudin barrister, don Allah kabarsu ni ban bukatar komi. Yace"nima ban ce kina bukata ba na ba ki ne a matsayin kyauta kuma ba a mayar da hannun kyauta baya, na hadaki da girman Allah ba dan ni ba ki karba. Hannu biyu tsa tare da risinawa takarba tace "na gode Ubangiji Allah yasaka da alheri. Ya lumshe ido yace na ji dadin wannan addu'ar ta ki. Zai shiga motarsa knan malam yadawo daga anguwa, fatima tashige gda dasauri yayin da barrister yazube a gun yana gaida shi, da fara'a malam musa ya amsa tare da kara masa godiya akan namijin kokarin daya musu a kotu, yace ba komi sai dai ya zo ne yana son fatima kuma ya ji ta bakinta ta amince taimakon dayake son a masa shi ne a bashi ita dawuri don tfya ce a gabansa. Malam yace "ba komi yabashi kwana biyu zai neme shi. Bayan tfyar barristr malam yashiga gda da kudin daya basu masu yawa ga wanda fatima tashigo dasu, inna tace "wallahi malam nikam na kagu a aurar da fatima a huta da wadannan fitinannun. Wannan zuwan da ake wannan yazo da katuwar mota, gove ma wani yazo an dau ido an sanya mana a unguwa, ni dai tafidda wanda tafi so tsakanin lauya da usman a daura auran a kaita kowa ya huta. Malam musa yace "nima abinda nake bukata knan a yau din nan za ta gaya min wanda takeso.. Fatima na kuka tace "don Allah baba kuyi hakuri zuwa da safe zanyi istihara duk wanda Allah ya zaban min shi ne zabina nikam ba ni da zabi. Duk inda aka ce Allah angama magana gaba daya takashe musu jiki dole suka kyaleta. A DAREN FARKO 41 A wannan daren fatima *wana tayi tana kai kukanta ga Allh tana rokon yazaba mata mijin da zai fi alheri a tare da ita, da mutum biyun nan takwana a zuciyarta amma da usman ta tashi ba brriater b. Shi taji ya fi kwanciya mata a rai duk da cewa shi yana da mata amma hakan taji shi taji tafiao, don haka kai tsaye ta sanar da babanta cewa yab barrister hakuri ta tsaglyar da Usman a matsayin mijinta,suka sanya mata albarka tare da fatan Allah yasa hakan shi ne mafi alheri a tare dasu. Duk yan gdansu usman fatansu ftima ta ami? ce ta auri usman sbda ba karamar damuwa bace dashi a gdansa, ba kamar jidda wadda duk tafi kowa tsanar farida ko gaisuwa ba ta hadasu har faridan ta daina zuwa komi na danginsu itama ba mai zuwa inda take dama ba haihuwa ba ta mike kafa ne tana abinda taga dama. Lokacin daya samu tabbas daga mahaifin fatima cewa an bashi ita yaturo manyanaa, hannu yadaga yana wa Allah godiya, nan da nan aka kai kudin aure aka sa ranar aure nan da sati hudu daurin aure da biki gaba daya. Ya shiryawa fatima gda da lefe mai ban mamaki, har aka kusan biki farida bata sani ba domin yanzu yawonta ya kara kaimi tunda juma'a kawai usman ke zuwa kano yakoma abuja ran lahadi, sai da yarage saura kwana uku kachal daurin aure wata kawarta nafisa tazo gdan da yamma tace da ita. 'Farida anya kuwa kin san me ke faruwa dake naga kiba ma kikeyi ba kisan tashin hankalin daya tunkaro ki ba ko? Farida tayi mata wani irin kallo na rashin fahimta tace "me kike nufi. Nafisa tabude jaka tafidda katin daurin auren usman da fatima ta dora mata a cinya ya ta ce. "Karanta anan za ki fahimci me nake nufi. Farida ta tashi zaune hannu na rawa ta dauki kati ganin sunan mijinta yasa ta gwalalo idanu tace "nafisa a ina kika samu wannan katin? Tace "a gari mana ana nan ana ta rabawa jama'a na gayyata ni nasan tunda baki mana zancan ba jiya a gdan hajiya ladidi na san baki sani ba. Gumi yadinga ketowa farida ta kasa motsi sai numfashi take fitarwa da kyar dga bisani tatashi tace "nsfisa bar masa gdansa zanyi. Nafisa tace "wannan shi ne aikin banza harara a duhu, kina zaton yanzu kina gaban usman ne, idan ma kin tafi cewa zaiyi ya huta, tashi zakiyi yanzu muje gdansu amaryar mu ci mutumcin su muyi musu kaca kaca mu firgitasu ta ydda ba xa tayi sha'awar shigo miki gida ba, shi kuwa bakin munafikin idan yadawo ki nuna ki nuna mai hauka ki ganar dashi kuransa ta yadda zai shiga taitayin sa dole a fasa auran. Farida tazauna daram a kan wannan shawarar don jin zuciyarta take kamar za ta fashe. **** A ckin motar da usman ya siyawa farida suka fito tare da nafisa, farida ce ke tukawa fuskarta a tamke kamar za ta fashe tana ci gaba da daukar shawarar nafisa har suka isa kofar gdansu fatima kasancewar nafisan ta binciko komai. Cike da isa suka shiga, sukayi sa'a fatima ce kadai a tsakar gda tana wanke wanke. Mamaki ya kamata ganin mutane sun shigo musu gda ba sallama. Farida ta nunata da yatsa tace "ke ce fatima? Tace "eh ni ce lfya. Kawai fatin bata ankara ba taji farida ta cafko mata wuyar riga da karfi ta jijjiga ta tace "ni ce farida matar usman idan ma baki sanni ba yau ki sanni ganina ya fi ji na. Inna tafito dagudu daga bandaki tana salati tace "ke yar nan lfya za ki zo har gda kiyi mana tijara? Farida tasaki fatima tanuna inna da yatsa tace "ke yi min ahiru munafuka idan kina neman kai da wannan figigiyar 'yar taki ne ki kawota gdana kusha mamaki kwadayayyu kawai. Fatima tayi tsalle itama za tadamki farida, inna tariketa tace "kyaleta fatima duniya ce suk abinda kayi za ayi maka, kishiya dai duk bala'in ta za amata gda dai sai kin shiga takashe ki jahilar banza da wofi. Nafisa tace "ai ba cewa mukayi karta shigo ba, mun fi so ma tashigo mu nuna mununa muku su waye mu shi yasa yanzu muka fara zuwa har gda mu sanar daku. Farida tace "ga ku ga gdan usman nan daidai kushigo kugani idan idan kuna tsammanin barazana muke muku. Suka fice a fusace suka shiga mota, farida ta fizga da karfi suka fita daga layin suna kyakyata dariya. Karfe ukun yamma uaman yashigo gdan a gajiye yake sosai sbda yau shi yatuko kansa, tun daga hanya yake tunanin yadda zai fuskanci farida da maganar auransa, duk abinda ake ciki, ya sha alwashin yau zai sanar da farida, tun da aka fara batun auran tunanin dayake knan bai san tashin hankali gashi ita kuma anan takware. A falo ya sameta baiyi mamakin kin amsa mai sallamar datayi ba, dan haka shima bai kalleta ba yawuce da jakarsa zuwa dakinsa yashiga wanka. Farida tashigo a zafafe zu-iyarta kamar wuta don tsabar bala'i hatta idanuwanta sunyi jawur, idanuwanta suka fara dira kan wayarsa ta dauka hoton fatima ne yafara yi mata maraba ta sha ado ta yi kysu abinta har ba a magana. Wato ma har akan screen usman yake dora hoton fatima, batayi tunanin komi ba tadaga wayar ta dokata akan tayal ta tarwatse gaba daya, daidai lokacin usman yafito wanka hankalinsa yatashi dayaga barnar da farida tai masa, ya zubawa wayarsa ido mai tsaadar gaske yarasa abinda zai ce mata sai ya tsuguna zai kwashe sim din sa, ta daddage ta hankada shi tace "wa to ma ka maidani mahaukaciya ba ka a lokacin kulani ko? Ya tattara ta ya watsar gefe guda yace "Ba ki da hankali wa zai saurari marar hankali, abinda zan gaya miki ki gaggawar shiga hankalinki tun kafin ki jawa kanki abinda za ki zo kina nadama. Cikin daga murya tace "awai nadamar data wuce na aurankada nayi, ka cuceni ka ci amanata ban taba zaton kana ckin munafukan maza ba sai yau... Saukar mari mai karfi tajia. kuncinta wnda ya gigi ta tafita dagudu tadauko wuka, ,ganin haka yasa ya muedeta zai amse wukar, taja wukar da karfi tazuge mai hannu, jini yafara zuba duk da haka sai da ya karve yace "ba ki da hankali farida, ba ki da hankali. **** Tafiyar su farida da nafisa gdansu fatima akayi jugum ana tunanin wannan bakon bala'i ,fatima kuka take tana fadin "inna ba zan iya da wannan masifaffiyar matar ba na fasa auran usman don Allah ki kirashi a waya yanzu ki gaya masa na fasa auran sa yazo ya amshi komi na sa yazauna da matarsa, kina ji har cewa take sai ta zamo ajalina. Inna tace "ke ba komi irin barazana ce yau kika fara jin inda akai irin wadannan abubuwan, to ki dogara ga Allah matar usman ba kowa bace akan wasu matan don duk abinda kayi wani ya ninka naka kuma anga karshensa, haka duniya tagada, duk wannan abinda tayi ta yi ne don a tsorata ace an fasa idan an fasa din taci galaba daga nan ta samu damar takawa yadda take so, ki kwantar da hankalinki addu'ar da muku da wadda kikeyi insha Allah za tabaki kariya ba abinda zai sameki sai alheri, ba na son ki gayawa kowa ma. ***** Jikin fatima yayi sanyi sosai har dare ba ta da kuzari, lokacin da usman yazo ma haka tafito masa fuskarta ba walwala sai yaji duk abin duniya ya yi masa zafi. Yace "fatima meke faruwa ne akwai damuwa a tare dake don Allah ki gaya min,. Tadago tayi mai wani irin kallo tace "dama haka matr ka take? Gabansa yafadi yace "me yafaru? Ta labarta masa duk tijarar da farida da kawarta sukayi musu, ransa yabaci yace "na ji dadi datazo har gda ta nuna muku mugun halinta, ai da farko na fara gaya mikikikace ba kya son ji, don Allah kiyi hakuri zan dauki mataki a kanta, barazaana ce kawai don ta tsorataki babu abunda ta isa tayi miki ke ba a garin ma za ki zauna ba a ina za taganki ballantana tayi miki wani abu. Ganin fatima ta ki sakin ranta hankalinsa ya dada tashi, sai kawai gani tayi ya durkusa a gurin yana bta hakuri, tace "haaba haba usman ba girmanka bane. Yaki mikewa tsaye yace ba zai tashi ba sai ta ce ta hakura, dasauri tace "na hakura na hakura. KARSHE karfe sha daya aka tabbatar musu da cewa an daura auran usman da fatima, farida tayi kasa tana birgima tare da fadin "ahikenan na shiga uku na gama yawo. Isha ta daga ta tace tashi baki shiga uku ba, fatima abin da za ayi shi ne idan usman yadawo gdan nan kinuna masa kuranki da nadamarki, ckin ruwan sanyi sai mu gasata mu korera da kissa. Gaba daya sukayi na'am da wannn shawara. Karfe goma sha biyun dare usman ya iso gdan, har zai wuce dakinsa sai dai yafasa ya murda kofar dakin farida,. Ga mamakinsa sai yaga ta saki fuskarta ta amsa mai sallama tare da mai sannu daxuwa. Usman ya saki baki galala yana kallonta cike da mamaki da farin cki a zuciyarsa. Da gari ya waye ne take tmbayarsa ina za akai amaryar bataga anyi shirin komi a gdan ba. Yace "ai abuja za mutafi da ita anjima tunda kin ga gdan nan ya yi muku kadan. tace ai ma hakan yayi daidai kaima za kafi jin dadin zaman abujan amma dai zanyi rakiya ko tunda dama ban taba zuwa ba. Yayi dan jim bai so hakan ba amma ya daure yace "shknan sai ki shirya mutafi. **** Karfe go;a sha biyun ranar talata an gama shirya amarya fatima za a tafi abuja, shi kuwa ango da uwargda suka taho a sabuwar motarsa. Babbar hudubar hajiya itace "kin san dai baki taba budar ido kin ganni dakishiya a gdan nan ba, haka yan uwanki idan kim saki baki kin zamo wadda tarako mata duniya, xa kizo kina nadamar da za tasaki kuka da idonki. Farida tasaki ranta sosai kamar ba ita ba ta gayar da dangin mijinta tare da tmbayar ina amaryar take za taje su gaisa,jidda da tafi kowa tsanar farida tayi tsagal tace "kin ga malama ba ruwanki da amarya kiyi harkarki tayi ta ta. Farida tayi murmushi tace "haba jidda meye don na ce zanje mugaisa. Daya daga cikin yayyan usman hajiya hadiza tace "kin ga dakin nan shiga ni ban son hayaniya. Tamike tashiga dakin da aka nuna mata tayi sallama, suka amsa tace "na san baku sanni ba ni ce farida matar usman na rakoshi taryar amarya ne. Daya a cikinsu tace "ai kin kyauta mun gode sosai. *** Farida ta kwana ne a dakin usman sbda ta marairaice masa yan uwanta dana fatima tsangwamarta sukeyi, har ckin ransa ya amince da ita har yaji a ransa ba dadi, yace to tadawo dakinsa tazauna kawai. Tayi ta amfani da damar data samu gun jan ra'ayinsa yana bata kulawa, da safe ma bata barshi ya fito daga dakin da wuri ba duk da ya san da yan baka a gdan amma sai yadinga ji da farida bai son damuwarta, har su jidda suka gama hidiman cin abincin su da wanka. Farida dashi usman din suka shigo, farida tai saurin zama kusa da ita takamo hannunta tace "haba amarya wani irin kuka ne haka kamar zamanin da, sbda fa in deve miki kewa nazo in dan tayaki zama kafi? ki saba don Allah ki hakuri ki saki ranki. Farida ta kalallame usman tahana shi sakewa da fatima da zarar zai shiga dakin sai tabi shi tana fadin, "man muje muga halin da amaryarmu ke ciki. Shi duk bai san kishi bane ya dauka dai kyautatawa ne shiyasa yake biye mata. Farida tabar usman a falo tashiga daki ta fada toilet takira wayar isha take tambayarta yaya za tayi tahana uaman kwana da fatima. Isha tace "shiga za kiyi dakin ke kadai ki nuna mata wuka ki cemata wallahi idan tayarda usman yashigo lallai sai kin kasheta, idan usman yashigo lallai tai ta ihu har sai ya fita, to da zarar ya fito ke kuma sai ki janye ra'ayinsa kuyi daki, gobe kuma sai mu shirya mata wani tuggun a haka har yagaji da ita yakoreta kiyi zamanki a abuja. Farida ta kyalkyale da dariya tace 'kai Allah yabar mana ke isha kin iya tsara tuggu shiyasa nake sonki. Tace "sai kinji ni aminiyar... Ba karamin frgita farida tayi ba, jikinta yadauki rawa sakamakon ganin usman tsaye a kanta yana mata wani irin kallo. Ya zabga mata wata muguwar harara yace "kaiconki Farida,zuciyarki tana miki saka da mugun zare, dama biyoni kikayi don ki rabani da matata ko? Allah bai baki sa'a kin kori fatima ba kanki kika kora, don ina son ki tattara ki bar min gdana na sake ki. Faida takwala kara zata fara yi mai hauka yafice yashige dakin fatima ya sama kofar key,. Fati tatashi a tsorace tana kallonsa, nan da nan idonta yaciko, yayi murmuahi yace "haba fatima sai kace kinga dodo. Tashiga mai magiya, ko kula ta baiyi ba yakashe fitila, tun tana kokarin kwatar kanta har tagaji tahakura. **** Da kyar fatima tatashi tayi sallan asuba taci gaba da barci, bata farka ba sai sha dayan safe. Ta tsuguna tagaishe shi cke da fara'a ya amsa, tace "ina anty farida mu gaisa? Yayi tsaki yace "ba ta gdan. Ina tatafi? Bansan inda tatafi ba. Tayi mai wani iein kallo wace irin magana ce wannan? Yajawota jkinsa dakarfi yahadeta da kirjinsa takama kuka tana kici kicin kwacewa. Yace "dama kin hakura kin hadu da cingam. Hankalin fatima yakara tashi ganin yadda yake neman cire mata riga, Allah yabata sa'a tafisge kanta ta gudu ckin dakinta. Kafin tarufe kofar ya danna kai yatsaya yana mata dariya, yace "kin fiye tsoro fatima. Ta durkus tana fadin "Don Allah kayi hakuri na tuba. Yarungumeta tsam yana shafa mata jiki, yace "wai don Allah fatima so dadi gareshi ko wahala? Me yasa ciwon so yakeda daci a zuciya? Me yasa soyayya ba ta barin zuciya tazauna lafiya. Ba ni wannan amsar". Alhamdulillah. Daga taku RABI'ATU NASIDI ABUBAKAR.